DR SAHEEB by Maman noorul Hudah

Author :  DR SAHEEB Category :  Romance

Chapter   7 / 12

18K to 21K   out of 33.7K words

tace"ni na tafi sai na sake zuwa"

Har gate suka rakata a nan take fad'a musu tayi wani saurayi sunan sa Mahmud

Murmushi fareeda tayi tace"Allah yasa shine mijinki"

Tace"amin"

Komawa gida sukayi bayan ta samu abin hawa

Fareeda ta zauna suna hira

Mummy tace"shikenan yanzu ranan Monday Zaki fara zuwa school ko?"

Tace"eh mummy"

Mummy tace"ok asa ido a karatu"

Kallon mummy tayi tace"mummy kamar kina da damuwa ko"

Tace"me kika gani?"

Farida tace"na gan cikin kwana biyunan sai kiyi zurfi cikin tunani"

Tayi murmushi tace"stress ne"

Fareeda ta kama hanunta tace"mummy nasan kina tunanin Dr ne tunda ya tafi baki ji shi ba"

Mummy zatayi magana fareeda ta katseta da cewa"ba sai kin ce komai ba nasan ke uwace ta gari kuma na dade da gane ran ki ya b'ace akan abinda saheeb yayi kuma kin d'au alkawarin koya me hankali Amma ai ke kika haife shi dole wata rana tausayin ki na mahaifiyarshi sai yafi karfin zuciyarki but ya zakiyi? kin kasance mace Mai adalci Wanda take so kwato min yanci"

Rungumeta mummy tayi tace"nagode da fahimtar ki Amma wallahi duk randa saheeb ya dawo ni dashi ne"

Fareeda tace"nagode mummy Amma karkiyiwa d'ankin komai sabodani ni na fita harkanshi bana son ganin shi na tsan...."

Shiru tayi sakamakon kallon da mummy ke mata

Murmushi mummy tayi tace"ki fadi zuciyar ki bazan gan laifin ki ba sweetheart"

Tashi tayi cikin jin kunya tace"mummy ni zan Shiga ciki in huta"

Mummy tace"ok"

Da misalin karfe 8:pm

Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/7, 4:28 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my fans
_____________
πŸ…Ώ5⃣5⃣_5⃣6⃣
_______________

Bismillahir Rahmanir Rahim

Da misalin karfe 8pm

Tana kwance tana posting hotuna a Instagram da charting a watsaap sai ga Iman ta shigo da sallama

Kallonta tayi tace"ana nan dai ana ta charting"

Tace"eh wallahi"

Iman tayi murmushi cikin sigar zolaya tace"mu dai Kar ayiwa Yaya mun kishiya"

Ai sai fareeda ta hade giran sama da kasa tace"gaskiya karki kara kira sunan shi a gabana bana so"

Iman ta sauke ajiyar zuciya tace"ki zo in ji mummy kin Yi bako"

Zaro ido tayi tace"bako kuma waye?"

Tace"kije zaki ganshi"

Tashi tayi tasa hijab ta sauko

Tun tana saukowa Dr musty ya gan ta wani canja ta Kara haske da kiba fatan jikinta sai kyali yake domin yana Shan hutu

Hade rai tayi domin ta lura dashi tun a asibiti yake ta wani irin kallonta

Zama tayi a kusa da mummy tace"mummy an ce nayi bako"

Mummy tayi murmushi tace"eh mustapha ne ya zo"

Turo baki tayi cikin shagwab'a da yanzu mummy ne ta shagwab'a ta

Tace"toh mummy ni miye hadi na dashi da za a kirani wajen ki ya zo"

Mummy tace"ke bana son shashanci kaishi falon baki ki bashi abin Sha"

Tashi tayi tana kunkuni ya bi ta a baya yana murmushi

Suna shiga falon ya zauna yace"haba my faree ba gaisuwa ne?"

Turo baki tayi tace"Ina wuni"

Bata jira ya amsa ba ta bar falon ta koma ta d'auko ruwa da juice sai snack ta dawo ta ajiye ta cigaba da lasar waya

Fisge wayar yayi yace"haba Mana babu kyau wulakanta mutum ai sai saurareni ko?"

Tace"toh Ina ji"

Yace"fareeda I will go straight to the point nidai na kamu da son ki tun randa aka kawo ki asibiti na please ki bani dama in nuna Miki nawa kalar soyyaya"

Tace"a gaskiya kayi hakuri yanzu bani da ra'ayin soyayyaya makaranta zan koma"

Yace"kina nufin in baki lokaci?"

Tace"no ka nimi wata saboda Kar in b'ata maka lokaci domin zan Kai 3years kafin in fara kula wani"

Yace"ko ten years ne zan jira amma taimako d'aya Zaki min ki bani number ki"

Zatayi magana yace"please"

Tace"ok"number ta kirame yayi saving sanan sukayi sallama"

Yana wucewa ta dawo falon ta gan daddy zaune
.

Murmushi tayi tace"lah Ashe ka dawo"

Yace"eh amma Ina kike na tambaya ance kinyi bako"

Tace"eh Dr mustapha ne"

Yace"me ya kawoshi"

Tace"daddy cewa yayi Yana sona zai aure ni"

Ai sai daddy ya zaro ido yace"


Maman
Noorul.hudah
Share
[1/8, 9:59 AM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and by expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my fans
____________

πŸ…Ώ5⃣7⃣-5⃣8⃣
______________

Bismillahir-Rahmnir Rahim

Yace"aure kuma?"

Tayi murmushi tace"Nima dai daddy haka nace me ya nimi wata ni karatun zanyi"

Yace"ai yafi ya nimi wata kawai"

Ba tare da ta kawo komai a ranta ba tace"ni wallahi bazan karayin aure ba"

Yayi murmushi yace"je ki kwanta gobe mayi hiran bacci Nike ji"

Tace"goodnite sweet dad"

Yace"nite my princess"

Yana Shiga d'akin shi ya tarar da hajiya kwance ta lumshe ido yasan ba bacci take ba domin kwanakin nan haka take

Yace"hajiya meyasa kike bari samari na zuwa wajen fareeda?"

Bude idonta tayi tana gyra kwanciya tace"laifi ne?"

Yace"hajiya nifa nasan komin daren dadewa yaron nan zai dawo kuma daya dawo zan sake musu aure domin ita kadai ce zata seta shi kuma hakan shine rufan asirin mu iyayenta baza su gane ba"

Tashi hajiya tayi tana kallon shi for the first time da zai gan b'acin ranta irin haka tace"wallahi alhaji baka Isa ba Koda maza sun Kare a duniya Kuma ko Kamal zai mutu wallahi farida tafi karfin shi sai dai ka nima wata matar ba fareeda ba oh saboda ita Bata da gata Yar talaka ce sai a had'ata da d'an iska toh in ma kana da wanan tunanin kayi gaggawan cire shi domin fareeda bazata kara Zama da Kamal ba"

Kallon mamaki yayi Mata cike da mamakin b'acin rai da ya gani a kwayar idonta yace"hajiya ba haka bane kema kin San bazan cuce fareeda ba saboda ita talaka bane nidai kawai Ina son had'a zuria da malam Abdallah ne na yaba da hallayensu wallahi da Ina da wani d'an bayan saheeb dana aurame fareeda dan allah ki fahimce ni"

A fusace tace"alhaji ka cire bakin ka a maganar fareeda da saheeb dan girman Allah wallahi in har ya dawo ya nuna ya tab'a saninta balle har yace"Yana sonta toh wallahi ni barrister Rukkaya zanyi shari'a da shi,kotu ne zai rabani dashi in kuma kana son in had'a da kai sai ka sanar min in bar maka gida tun yanzu"tana Gama magana ta ja bargo ta rufe har fuska

Kallonta yayi yace"ikon Allah abin ya Kai ga haka?"

Gyra kwanciya tayi ba tare da ta amsashi ba

Shiga bayi yayi ya fito yayi shirin bacci ya kwanta a gadon ya jawota jikin shi,ture me hannun tayi

Yace"haba hajiya toh miye na fushi aini tuni na janye wallahi ba ruwana Kar in rasa matata saboda shi kowa tashi ta fishe shi "

Juya me baya tayi yace"haba uwargida a gidan al-haji Musa al'amin ayiwa daddy afuwa wallahi na janye,wai dama hajiya kina da fushi haka?"

Shiru tayi shi kadai yayi ta zuba surutu itako zuciyarta tafarfasa takeyi tana jiran dawowan saheeb

Da haka daddy ya shawo kanta har ta fara bashi amsa

Itako fareeda tana shiga d'aki Dr musty ya kirata

D'agawa tayi tana jin muryarshi ta kashe wayar baki d'aya ta kwanta

Haka fa rayuwa ta cigaba da tafiya inda fareeda yanzu ta fara zuwa makaranta kuma tana koyar mota kallo d'aya zaka Mata ka gan wayyaya mace da aji zuwa yanzu sumanta ya d'an fito kuma tana zuwa ta gaida su mama sai dai har yanzu Basu San halin da ake ciki ba domin ce musu akayi mijinta yaje Karo ilimi a kasar waje

Mummy ko kullum sai dinki takeyiwa fareeda ga kayan lafe da akayi mata ta Bata abinta

B'angaren Saheeb ko

Zuwa yanzu hauka ce ya rage beyi ba domin ko abinci baya iya ci kullum cikin tunani fareeda daurewa kawai yakeyi domin karatun ma na niman gagaransa

Yanzu ma kwance yake Yana latsa waya tunanin gida ya dameshi Amma da ya tuna mummy sai ya ji bashi da kuzari

Lumshe ido yayi ko minti ashirin beyi ba bacci ya fara d'aukan shi sai dai fa ko nisa beyi ba ya fara mafalki
Zaune yake a garden sai gata ta fito sanye da riga da wando jeans da flowers a hanunta

Karasowa tayi ta rungumeshi ta baya ya lumshe ido yace"farheeb ai fushi Nike dake "
Ba tare da tayi magana ba ta hade bakin su ta fara tsoso

Lumshe ido yayi ya bude su ya jawota gabanshi ya kwantar da ita saman ciyawa Yana romancing dinta har zai shige cikin birnin dabsu ta tureshi


Cikin matukar bukatar ta yace"why?"

Tace"no"

Kokarina had'a bakinsu yake ta tureshi ta tashi

Yace"farheeb zo kiji Allah ki zo bazan Miki komai ba "

Wucewarta tayi sanda tayi nisa ta juyo tame murmushi

Firgit ya tashi daga bacci Yana mugun zufa kallon Wando shi yayi ya gan a mike take

Yace"na Shiga uku ni saheeb meyasa zuciyata zata kamu da sha'awar ta,aiko Imani ya gan ni dan wallahi nasan ban isa in koma gida da wanan maganar ba zan Bari in na Gama program dina in koma in nimi gafaran mummy da daddy ko ya Suka d'auki zance?"mikewa yayi kamar Wanda ya tuna wani abu yaje gaban wardrobe ya ciro wani waya

Numbers yake dubawa murmushi yayi yace"Iman let me call her"

Kiranta yakeyi Amma ba a d'aga ba har 4missed calls

Iman dake zaune da fareeda suna Hira,fareeda ta kalleta tace"ba wayar ki bane ki d'aga Mana"

Iman tayi tsaki tace"bansan ko waye ba international number ne"

Fareeda tace"ki d'aga may be is important"

D'agawa tayi tace*"hello"

Shiru tayi jin muryar da batayi zato ba kallon fareeda dake lasawa waya tayi

Shiko jin taki amsa me yace"

Pls comment and vote for me on watpad

Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/8, 9:59 AM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to Anty shamsiya
______________
πŸ…Ώ5⃣9⃣-6⃣0⃣
_____________
Bismillahir Rahmanir Rahim

Yace"Iman saheeb ne"

Tace"wani saheeb kenan?"

Yace"ke bansan iskanci saheeb ne Mana Yayan ki"

Tace"ni bani da wani Yaya saheeb yanzu,a dane kuma Allah yayi me rasuwa tun watanin shida da Suka wuce"

Cikin sanyi jiki yace"Iman abin har ya Kai haka"

Tace"Yama wuce"ta cire wayar a kunni tana kallon fareeda da tunda aka Kira sunan saheeb jikinta ke rawa

Kallonta tayi tace"fareeda meke faruwa don't worry saheeb bazai Miki komai ba"

Fareeda tace"no zan tafi gidan mu wallahi zai dawo ne Allah zan tafi"

Rungumeta iman tayi tace"dont worry bazai Miki komai ba"

Saheeb da be yanke wayar ba Yana jin komai Zama yayi ya bi wayar da kallo yace"iam in real trouble tsorona take ji,
Kenan tana gidan mu ya kamata in koma gida"girgiza kai yayi yace"kafin in bar kasar nan ya kamata inyi achieving wani abu dan haka is better in daure in naje gida in samu abin nunawa,but zan iya kuwa?saura fa shekara d'aya da wata shida,hmmn dole in d'aure may be in mummy taji nayi karatu kila ta ragamin"da wanan tunanin ya kwanta bacci ya kwashe shi

Washe gari fareeda taje d'akin mummy tace"tana son zata koma gidansu"

Mummy tace"wani abu ya faru ne?"
.tace"ah'ah"

Iman ne tayiwa mummy bayani abinda ya faru"

Mummy ta sauke ajiyar zuciya tace"dear ai shi ya kamata ya bar Miki gida ba ke ba in kin d'aukeni a matsayin mahaifiyar ki toh ki barmin wanan fadan domin fada Nan tsakanin d'an da uwane"

Tace"mummy na yarda dake"

Mummy tace"good"

Tun daga wanan ranan kullum sai saheeb ya Kira Iman Amma ceme take mummy tace"in tayi magana dashi Bata yafe me ba"wani lokaci ko ya kira bata d'aukawa

Hakan yasa ya fara charting dinta,tunda Iman ta gane Yana checking watsaap status dinta da Instagram da sauran media chart aiko nan ta Zama bata da aikin yi sai sa zafafan hoton fareeda Wanda shi kwata-kwata be gane ta ba sanda ya duba abinda take rubutawa kamar haka fareeda matar babban mutum "Aiko ranan da ya gane tana zuwa makaranta wuni yayi Yana amai zuciyarshi na zafi yace"kenan zuwa take kowa ya kalle min ita dubi dressing dinta yariyar da she is always in hijab Iman ta gurbata min ita"a daren ranan beyi bacci ba zama yayi ya dinga tunani

Yace"ai zuwa zanyi ayi ta ta kare a bani matata but zan d'aure in Gama program din"
________________
Bayan shekaru biyu abubuwa da dama sun faru ciki harda gamawa makaranta saheeb zuwa yanzu ya gane wani azababen son fareeda ke d'awainiya dashi domin ya gama lalacewa kullum cikin tunani daga Ina zai fara?yayi nadama sosai domin ji yake itace rayuwar shi

Fareeda ko zuwa yanzu suman ta ya dawo har ya fi nada tayi wani mugun kyau alamun hutu ya zauna
.Dr musty ko har yanzu beyi give up ba kullum sai ya Kira ta ga text masu zafi amma bata kulashi kuma Yana zuwa lokaci zuwa lokaci

Yanzu ta iya mota daddy ya siya Mata

Da misalin karfe 4:pm jirginhi ya sauka

Gidan shi ya tafi direct Aiko Yana zuwa ya tarar da komai inda ya barsu babu canji sai Kura da yayi

Murmushi takaici yayi yace"hmmm nasan na shiga tara yanzu daga Ina zan fara?"

Haurawa yayi zuwa d'akin ya gan sumanta da pant dinta da bra da rigarta da ya ya ga

Ai sai ya

Pls vote for me
[1/8, 6:41 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my fans
_____________
πŸ…Ώ6⃣1⃣-6⃣2⃣
Bismillahir Rahmanir Rahim
_____________

Ai sai ya fashe da kuka shi kanshi yasan ya shiga tara

Ganin kukan bazai fishe shi ba yasashi tashi ya fara share wurin yana cewa"nidai na Shiga ukuna na jefa kaina a matsifa kai rashin yafiya beyi ba"

Bayan ya share gidan saf ya gyra gado ya canja zanin gado domin wanan jinin har baki ya Zama sai zarni da d'akin keyi

Bayan ya gama ya Shiga yayi wanka ya fito ya shirya cikin shadda milk colour babu abinda ke tashi sai kamshi yayi kyau sai dai da an kalleshi za a gane Yana da damuwa

Gida direct ya nufa

Fareeda ne zaune a falo cikin wata riga da wando kanta sanye da hula tana kallo tana cin popcorn hankali kwance

Remote ne ya fadi kasa ta duka Dan d'aukowa kawai sai ta gan mutum ta center glass table dake falon a razane ta d'ago ta kalleshi

Zaro ido tayi jikinta na mugun rawa a take tayi wani mugun ihu

Ganin Yana tunkarota yasa ta ruga da gudu ta shige kicin ta rungume mummy

Tace"wallahi mummy ya dawo kasheni zaiyi ki taimakeni wayyo Allah na"

Mummy da hankalinta ya tashi tace"waye ya dawo ki fad'a min waye?"

Jijjigata takeyi Amma tuni ta sume

Cikin tashin hankali mummy ta kara riketa da kyau tana Kiran Iman Amma shiru

Jin ihun mummy yasa ta gane ba lafiya cikin sanyi jiki ya karasa kicin din

Yace"mummy meya faru?"

Ai mummy na jin muryar shi ta d'ago ta kalleshi tuni idonta ya kada

Tace"Ashe kaine,toh kayi gaggawar barin gidan nan ko ni in bar maka,meya dawo da Kai ko abu ka mance ne ka zo d'auka?toh kayi gaggawan yin abinda ka zo Yi ka bar gidan nan kana tsorata min diya"

Shidai shiru yayi hawaye ya cika idonshi

Mummy tace"ka fita kafin ranka ya b'ace"

Yace"mummy ki Bari in taimaka Mata ni bansan me yayi shocking dinta ba tana ganina ta gudu"

Mummy tace"so kake ni in bar maka gidan kenan?"

Cikin jin haushin fushin mummy yace"ni ki bari in bata taimakon gaggawa matata ce ai"
Be jira me zatace ba ya sungumi fareeda ya kaita d'akinshi

Mummy sai binshi take tana cewa"ajiye ta wallahi ranka zai b'ace ba"

Yana ajiyeta a gado mummy ta wanka me Mari guda biyu tace"karka kuskura ko da Wasa ka kara tab'a ta wallahi in ba haka ba kotu ne zata rabani da kai,ka fice ka bani wuri"

Tana Gama magana ta ratsashi Dan zuwa d'auko wayarta a hanyar barin part dinshi ta hadu da Iman tace"iman d'auko min wayata please zan Kira Dr musty"

Iman tace"toh"zuwa tayi ta d'auko ta kawo mata da gudu ta bata,komawa tayi d'akin shi sai ta gan yana kokarin bata taimakon gaggawa sai matse kirjinta yake

A zuciye taje ta turashi tace"Kamal Ina fad'a maka ka fita a idona tun kan ranka ya b'aci ka fita ka bani wuri"

Yace"mummy ko me zakiyi min kiyi min amma ki bari in taimakawa matata"shiru tayi Bata Kara magana ba domin itama tana son fareeda ta tashi amma Bata son ta ganshi ya Kara jefata wani hali

Cigaba yayi da aikinshi Sai dai still bata farfado ba
.zufa yake sosai

A haka suka ji sallamar Dr musty

Mummy ta kalli Iman tace"je ki shigo dashi"

Iman na fita tace"Kamal mun gode da taimako amma ka tafi yanzu Dr ya zo"

A fusace yace"waye Dr ta Kuma meyasa sai namiji?"


Kafin tayi magana Iman ta shigo da Dr musty

Idonsu na had'u dana saheeb ya

Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/8, 6:41 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my fans
_____________
πŸ…Ώ6⃣3⃣-6⃣4⃣
Bismillahir Rahmanir Rahim

Wani muguwar fadiwar gaba Dr musty ya ji had'iye wani miyau yayi amma sai ya basar yace"mum meke damunta?"

Mummy tace"ta suma ne sakamakon wani mugu da ta gani"

Yace"ok let me help"

Har zai karasa gadon kawai yaji an wani turo shi

Kallon saheeb yayi yace"Bari in dubata Mana"

Cikin b'acin rai yace"karka kuskura ka tab'a min matata"domin shi fa har ga Allah ya manta ya saketa

Wani kallo Dr musty yayi me yace"the last time I check ka saketa kuma nima yanzu ina cikin maniman aurenta"Yana gama magana ya ture me hanun

Ya fara aikin shi

Suman tsaye saheeb yayi tunawa da tabbas yayi sakin nan hawaye kawai ke fita a idonshi ya kalli mum da ko kallon shi batayi ba ta cigaba da shafa fuskar fareeda

Wani azababen kishi yake ji ganin Dr musty sai zakewa yakeyi zuciyar shi na tafarfasa

Bayan Dr musty ya mata allura Wanda sanda saheeb ya kusa had'iye zuciya ganin a gabanshi yayi mata a inda bayaso kowa ya gani

Kallon mummy Dr musty yayi yace"mum ya kamata a d'auke abinda bata son gani domin in ta farfado zai iya mayar da ita halin da take ciki which ba a so ya faru so duk wani abinda zai b'ata mata rai a d'auke shi"ya Kare magana da kallon saheeb Yana me wani kallo

Ba tare da mummy tayi magana ba ta kama hanun saheeb ta fara janshi zuwa waje tace"Kar ka Bari in Kara ganin ka kusa da ya'ta wallahi ranka zai b'ace "

Kallonta yayi yace"mum nifa d'anki ne"

Murmushin takaici tayi tace"and so?abinda Nike dubawa kenan da tuni nasa Yan sanda sun Kama ka"

Bata jira me zaice ba

7 / 12