DR SAHEEB by Maman noorul Hudah

Author :  DR SAHEEB Category :  Romance

Chapter   3 / 12

6K to 9K   out of 33.7K words

yayiya fara binta tana gudu jikinta na rawa babu halin fita ya kulle kofa

Gajiya yayi ya zauna tace"bani makulli in tafi

Yace"Anki a bayar Zama tayi a kasa tana kuka"

Ko kulata beyi ba ya kwanta abinshi

A ranan batayi baccin kirki ba

Washe gari Yana fita sallah asuba ta fita tana sauri kallon da fauziya ke Mata ne yasata Shan jinin jikinta

Fauziya tace"andai shiga uku wallahi anji kunya ana cin mutunci hijabi yanzu simi_simi an sako hijab ya naja kasa kuma ga uban nikab gashi ana kwana a d'akin maza mu akeyiwa kallon Yan iska Ashe Yan iska na gefe toh Allah ya kyauta"

Samun kanta tayi da fashewa da kuka ta shige office dinsu

Zama tayi ta hade Kai da guiwa tana kuka

Itako fauziyya ta d'au alwashin sai ta sanar da farouq ai dama anguwansu d'aya

Bayan ta sha kukan ta ta saka hijabinta tasa nikab ta bar asibitin

A hanyarta na fita ta had'u dashi Yana shigowa kallon kwayar idonta yayi

Yace"ke ninja zo Nan"

Ko kallon inda yake batayi ba balle yasa rain zata tanka shi

Yace"who is she meyasa kullum sai na ganta "

Adaidaita ta hau ta tafi gida a ranan iyayenta Basu gane kanta ba

Mama tace"hanya baza a hakura da aikin Nan ba?'

Tace"ah'ah mama inshaallah babu abinda zai faru"

Mama tace"toh Allah ya Kare"

Tace"Amin "

Da daddaren ma baba ne ya kawota ya sauketa a gate

A nurse station dinsu ta tsaya zatayi sighning wani takarda da zai tabbatar ta zo aiki da lokacin da ta zo sauri takeyi taje ta cire hijabi

Shigowa yayi cikin 3quter da armless da wayoyi a hanunshi sai makulin mota

Ganinta tsaye yasa ya karasa inda take yace"yau sai na gan fuskar ninjan Nan "

Yana zuwa be b'ata lokaci ba

Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/3, 11:08 AM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my Husband

_______________
πŸ…Ώ2⃣1⃣_2⃣2⃣
______________

Bismillahir Rahmanir Rahim

Beyi wata wata ba ya d'aga nikab din yana ganin itace

Yace"so it you?"

Tsaki tayi ta ratsashi ta shige ta cire hijab ta fito ta zauna

Shiko office yaje ya zauna yana tunani yace"so itace me nikab no Wonder su duna har yau basu ganta ba yanzu dai na gane zan sanar dasu"sai dai hanya zan Bari su suyi kuwa?"

I don't know why iam feeling bad about it

Girgiza kai yayi yace"I will rape her myself"

Da wanan shawara ya samu kwanciyar hankali

Cikin daren ranan har bacci ya d'auketa sai aka kawo wata petient da alamu dai amarya ce domin kafarta da hannuwanta duk sun ji desighn gashi ta Sha kitso a sume angon ya kawo ta

Toh a lokacin Dr Dauda Yana cikin labour room

Tashi fareeda tayi taje office dinshi Amma baya zaune hakan yasa ta tura kofar d'aki zaune ta ganshi yana Shan tab'a

Tsaki tayi,murmushi yayi yace"kin zo ne in sake Miki abinda nayi jiya ai dama na dade da sanin shiru shiru irinku masu saka manyan hijabi dayawan yan iska ne"

Tsaki tayi tace"ga ka babban d'an iska tunda kana busa sigari Kamar salansa Mara tarbiya shasha-sha sakare"ai sai yaji Kamar mummy ce gaban shi

Hararanshi tayi tace"ka zo an kawo petient ne kuma Dr Dauda na labour room da fauziya"

Tashi yayi ya Shiga bayi ya fito yasa Kaya ya fita

Tabi bayanshi d'akin da aka kwantar da amaryar Suka shiga

Kallon fareeda yayi yana saka handclufs a hanun yace"duba ta

Bude Mata kafa fareeda tayi ta gan irin b'arnan da angon yayi ai wani razana tayi tace"Amma wanan mutum ne kuwa? Wanan ai mugunta ne jifa inda ya Mata caka-caka sai an Mata d'inki"fad'a sosai fareeda keyi ita tayi d'inki

Shiko Zama yayi yace"wai ke Ina ruwan ki ba matarsa bace?"

Tace"Dan matarsa ce aka ce yayi Mata irin wanan muguntan haba jibi fa "

Murmushi da shi kadai yasan ma'anarsa yayi yace"kema wata rana haka za a Miki"

Bata tanka sa ba tasawa amaryar drip ba a jima ba ta tashi a firgice tana ihu tace"dan girman Allah kayi hakuri wallahi na fasa auren"kuka take sosai jikinta na rawa Wanda yasa tsoro ya cika zuciyarta rungume shahida tayi tana Taya ta kuka

Cikin shasheka shahida tace"wallahi karkiyi aure da zafi"

Cikin tausayawa fareeda tayi ta shafa kanta tayi Mata allura

Saheeb ya mike yace"I think iam not needed here"

Binshi tayi a waje ta tarar da ango na gyangyadi Aiko Nan ta zazzaga mishi rashin mutunci

Shiko SAHEEB office ya tafi cike da farin cikin samun mafita

Washe gari da misalin karfe 6:am

Toh fans me kuke ganin zai faru❓
Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/3, 11:08 AM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my paid groups

____________
πŸ…Ώ2⃣3⃣_2⃣4⃣
________________

Bismillahir Rahmanir Rahim

Da misalin karfe 6:am ta bar asibitin a hanyar zuwanta gida dai_dai lungun hanyar gidan su tana cikin tafiya kawai taji wasu katti biyu sun tare Mata hanyan

Kafin tayi tunani yin wani abu kawai Suka fito da hanki Suka Shaka Mata wani Abu a take jikinta ya saki

D'aukanta d'aya daga cikinsu yayi yasa ta a kafada Suka kaita mota da gudun gaske Suka fisgi motar da mugun gudu

Gidan saheeb sukayi da ita direct suka bude gate

Ciki Suka kaita suka bude kofar falon suka d'aure hannunta da kafafun ta

Kiranshi sukayi Yana d'agawa duna yace"mun Gama aiki oga"

Murmushi yayi yace"nagodae sosai zan turo muku kudin ku ban amince ku Mata komai ba ku kulleta ku fito"

Duna yace"angama"kulleta sukayi Suka bar gidan

Zaune yake a dining bayan yayiwanka

Mummy ne ta sauko da daddy Suka zauna

Abinci yake ci daddy yace"Kamal ba dai matsala dai ko?"
Yace"daddy babu"

Daddy yace"toh saura aure"

Hade rai yayi yace"gaskiya daddy ba yanzu ba"

Mummy tace"Niko wallahi bazaka wuce ko wata biyu ba kayi aure ba"

Daddy yayi murmushi yace"aini nayi shirme wallahi da akwai yar megadina malam Abdallah toh Yana da ya' naso ne in had'a su domin na yaba da tarbiyarta sai dai Kash jiya ya kawo min katin aurenta Nan da sati uku"

Furzar da kwai bakin shi yayi yace"what ni za a had'a da Yar megadi Kamar Mara gata?"

Dakuwa mummy tame tace"matsayi ka fita a gurin Allah? kila ma ta fika daraja shashasha sakare"

Yace"nidai zagin kenan kullum"

Daddy yayi murmushi yace"Kamal please ka daina Raina d'an Adam babu kyau"

Tashi yayi yace"har naji na koshi"

Binshi daddy yayi da kallo kafin ya sallami mummy ya tafi aiki dama tuni Iman ta tafi makaranta

Ko minti ashirin beyi da shiga ciki ba sai gashi ya fito cikin riga da wando jeans yayi kyau sai ya fito a fulanin shi Wanda wasu ke d'auka shi balarabe ne"

Mummy ne ta kalleshi tace"sai Ina kuma?"

Yace"asibiti zani bazan dade ba"

Tace"Kai dai baka da kunyar karya"be Kara magana ba ya fita

Gidanshi yayi direct Yana zuwa ya ganta d'aure a falo murmushi yayi

Yace"you enjoy slapping people you will regret it"

Karasawa yayi ya gan hijab dinta a kasa gata tana bacci

Wani mugun fadiwar gaba ya ji domin a tunanin shi ko su duna da manga sun Mata wani abu ne"

Dogon gashin da ya rufe Mata fuska ne ya gyra ya kura Mata ido yace"today you will be mine"

Itadai bacci takeyi,fridge yaje ya ciro ruwa Mai sanyi ya kwara Mata firgit ta bude ido

Wani marayan kuka ta saki tace"Dan girman Allah ka taimake ni"

Kuka take tana rike ciki shiko yace"kenan yaran Nan sunyi Mata wani abu kenan?"

Waya ya ciro ya Kira duna yana d'agawa yace"ubanwa yace"ku keta Mata haddi"
.zaro ido yayi yace"megida babu abinda mukayi Mata fa"

Kallonta yayi sai kawai ta fara kwarara amai

Wani tsaki yayi domin ya gane me ke damun ta


Yace"aiko kwana nawa zakiyi har ki gama kina nan gidan da bakiyi ba sai yau da Nike son executing plan Dina"

Cikin kuka tace"ka min allura please zan mutu"

Yace"ki mutu Mana in kin mutu sai me?"

Komawa yayi ya zauna a kujera Yana chart Aiko juyowa da zaiyi ya kalleta ya gan har ta sume

Tsaki yayi ya mike ya d'auki makullin mota yaje phamacy ya siyo allurai ya dawo ya d'auke ta ya kaita d'aki ya kwantar da ita a gado yayi Mata

Ruwan dumi ya kawo ya saka towel ya fara matsa Mata a Mara

Nan fa bacci wahala ya d'auketa dan tunda ya Mata allura ta farfado

Fita yayi ya siyo abinci ya kawo ya ajiye Mata

Ba ita ta farka ba sai wuraren karfe hud'u duk tayi stain

Zama tayi akasa ta had'a Kai da guiwa ta saki wani kuka me shigarai babu abinda take tunawa sai halin da iyayenta zasu shiga in Suka ji shiru

Ganin kukan ba zai fisheta ba ta fara adduoi

B'angaren su baba ko babu inda Basu shiga niman fareeda ba har asibiti baba yaje aka tabbatar me ta bar asibitin tun asuba

Fauziya ko tace"ai nasan za a rina ni ban yarda da fareeda ba naje har gida na fad'awa farouq be yarda ba nasan yanzu zai yarda uztaziya ce ko Yar duniya?"

Baba dai be kulata ba ya bar asibiti

Abu kamar Wasa sanda suka zaga anguwa kap ba labarin fareeda Nan fa hankalin su ya mugun tashi babu abinda mama takeyi sai wani irin kuka

Humaira ma ta zo itama kuka take domin tasan ba lafiya

Baba dai dauriya yakeyi Yana lallashin mama Amma shima ji yake kamar yayi kuka

Zama kawai sukayi kowa yayi tagumi masu jaje da gulma sun sasu a tsakiya

Ba karamin kuka fareeda ta ci ba ga ciwon ciki yasata gaba ko ta kan abinci daya ajiye Bata bi ba

Shiko wajen Mahmud yaje ya bashi labari

Mahmud yayi dariya yace"ka ce zaka kwashi gara in nine Kai sati biyu zatayi kafin in saketa"

Murmushi yayi yace"ko so d'aya ya isheni nifa bawai iam interested bane na so in Sa ne but bansan abinda yasa ba Ina jin bazan iya Bari wani yayi ba"

Mahmud yace"ko za a d'an min ne"

Hararanshi yayi yace"tunda matar ka ce"

Mahmud yace"na gan kaima ba matar ka bace"

Share shi yayi ya
cigaba da latsar waya

Fareeda ko bayan ta gaji da kuka ta zauna tana salati tana Kiran sunayen Allah gashi ya rufeta a d'akin

*Wacece fareedat?*

Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/3, 7:16 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my paid groups

______________
πŸ…Ώ2⃣5⃣&2⃣6⃣
______________

Bismillahir Rahmanir Rahim

A gurguje please

Fareedat Abdallah shine cikekken sunanta ya'ce ga malam Abdallah da mahaifiyarta Rabiah

Malam Abdallah mutum ne me niman na kanshi domin baya son raini yana da niman na kanshi baya raina sana'a

Auren soyyaya sukayi da matar shi Rabia shekaru talatin da suka wuce sai dai Kash sanda suka shekara tara Basu ajiye kwansu a duniya ba domin Rabiah in tayi ciki zubewa yakeyi a cikin shekarun Taran nan tayi b'ari 7

A lokacin Yan uwan malam Abdallah suka tada da hauka sai ya Kara aure ko su suyi me

Aiko rufe ido yayi yace"bashi da ra'ayin yin aure kuma suna zaman lafiya da matarshi ai shi ba jahili bane da zaiyi aure dan kawai matarshi allah be kawo lokacin da zata haihu ba ai ba laifinta bane

Babu inda basuyi ba har ya Kai ga ita Rabian da kanta tace"yayi auren Amma yaki kuma maganarta ya mugun b'ata me rai kuma ya sanar da ita akan in ta Kara cewa yayi aure sai ya mugun sab'a Mata hakan yasa taja bakinta tayi shiru ta zuba me ido

Wanan dalilin yasa Yan uwan malam Abdallah suka fita harkar shi,shima be damu da ya nimi sulhu ba

A haka dai suka cigaba da rokan Allaj cikin ikon allah sa ga Rabia ta samu ciki laulayi sosai takeyi kullum suna asibiti gashi ba wani sana'ar kirki yakeyi ba gadi ne a Wani company Al-amin ventures

Aiko cikin ikon Allah cikin ya tsaya inda bayan wata tara ta haihu yar'ta mace ranan suna yariya ta ci suna fareedat sunan mahaifiyarshi

Malam Abdallah ya kwashi son duniya ya d'aurawa fareedat Yana sonta domin itace duniyar su

A haka tayi primary and secondary school har ta gama cikin ikon allah ta samu admission taje school of midwifry minna kasancewar tana da illimi ga kokari duk wani tanadi da malam abdallah keyi akan fareeda yake karewa a lokacin da take makarantahar kwana da yunwa sukeyi wata ran dan kawai ta samu tayi karatu

Bayan ta gama makaranta ta zauna babu aiki sai islamiya take zuwa nan ne Allah ya had'ata da malamin hadda su farouq har suka kulla soyayya inda yanzu ana maganar aurensu farouq shima dai ba wani kudine da shi ba Amma Yana da rufin asiri domin Yana aikine a wani company

Baba ne ya Kai takardunta wajen alhaji Musa megidanshi Aiko yayi sa'a lokacin ya budewa d'an shi dake turai asibiti suna niman ma'aikatan a take ya Bata aiki ba karamin godiya baba yame ba

Fareeda ta kasance yariya Mai tarbiya,ga girmama na gaba da ita shiyasa Bata d'aukan raini wajen kowa tana da kamun Kai ga addini domin in ba a wajen aiki da ya Zama mata dole ba da wuya ka ganta babu nikab

Fareeda bata da wata kawa da ta wuce humaira domin tare suka taso kuma tasu ta zo d'aya fareeda bata son mutum me raini

Fareeda tana da saurin hannu domin irin mutane nan ne da babu wuya sun Kai duka in rai ya b'ace domin tun tana karama ake fama da ita a anguwansu sai dai in akaji tayi fad'a toh tana da gaskiya ne

Fareeda ta tsani mutum ya raina ta

Fareedat fara ce sol tana da d'an kiba sai dai bata da tsayi

Tana da tsoro kuma ga karfin hali

Fareedat na matukar son farouq domin burinta ta auri uztaz Wanda keda addini Aiko allah ya Bata farouq

Farida na matukar tsoron first night domin ko Hira ake ko kuma tana karantawa a littatfai taji anyi zance first night jikinta rawa yakeyi

Tana da suma sosai kuma Bata son kiso ta fison tayi ta tufkesu tana matukar son inda sumanta yake shiyasa take son gyrashi domin wani tsansi ne dashi ko an kitseshi sai ya kwance

Wanan kenan sauran maji nan gaba

*Cigaban labari*


Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/3, 7:16 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of gorgeous, interllingent,and expert writers we the best among the rest.

Dedicated to my paid groups

______________
πŸ…Ώ2⃣7⃣-2⃣8⃣
_________________

Bismillahir Rahmanir Rahim

A haka bacci ya d'auketa a ranan saheeb be dawo ba sai washe gari

Tana ganinshi ta fashe da kuka tana rokon shi

Yace"wallahi kiyi shiru ki bar b'atawa kan ki lokaci domin ko talakar ubanki bazai kwace ki ba sai na d'ana ki sai nasa ke da iyayen ki kunyi nadama "

Rokonshi take tana kuka cikin kuka tace"wallahi na tuba kamin Rai ka rama Marin ka nidai Dan girman Allah ka Bari in tafi wajen iyayena"ta kare magana da sakin wani kuka"

Yace"ki bar b'atawa kanki lokaci dan wallahi sainayi mikin abinda ko kudi aka bawa namiji ya aure ki bazai aure ki ba"

Tace"wallahi karya kakeyi babu abinda zaka min da Allah beyi ba mugu kawai ka sato ni ka raba ni da iyaye na kuma da kake cewa talakar ubana ai kaine babban talaka tunda komai kudin ka baka iya taimakawa na kasa da kai"

Yace"wai ke bazakiyi shiru ki bar zagina ba kila in tausaya Miki?"

Cikin kuka tace"dan Allah kayi hakuri nidai Allah ya isa na"

Murmushi yayi yace"watoh taurin kan a jinin ki yake ko?"

Zama tayi ta ma manta babu ko d'an kwalli kanta zufa take duk da sanyi ac dake d'anki ga dogayen sumanta ya barbaje a fuskarta "

Karasawa yayi ya gyra suman,d'angowa tayi ta kalleshi

Yace"harda gashin doki kike sawa Yan iska sai ayi ta pakewa dasa hijab"

Tsaki tayi ta ture hanunshi ta turashi ta nuna shi da yatsa tace"karka Kara tab'a min suma domin Ina matukar son gashina a rayuwata Dan haka bazan bari kazami irinka ya tab'a min ba,wanan aikin uztazuna ne"

Yace"Allah ko?"mikewa yayi yace"anyways I don't have your time zan tafi,but kwana nawa kike yin period?"

Hararanshi tayi tace"ban sani ba"

Yace"ok then zan baki 1week sai Nan zan dawo nasan ko kece kamfanin manja kin gama a lokacin Zaki san koni waye bani da mutunci"

Kuka ta fashe dashi tace"nidai Allah ya isana ka barni in tafi wallahi mamana bata da isheshen lafiya na tuba"

Ko kulata beyi ba saima cewa yayi in kin ji yunwa akwai komai a kicin in kuma da yunwa zaki zauna inda kikayi jiya it your choice na tafi"Yana gama magana ya bar gidan

B'angaren su baba ko duk inda ake sa ran za a gan fareeda abin ya faskara

Mama ko sumanta biyu yanzu ma haka a kwance take da drip a jiki domin jinin ta yayi mugun hawa

Baba ma karfin hali yakeyi ga surutu ya cika anguwa

Shima farouq hankalinshi yayi mugun tashi domin already fauziya ta riga ta gurb'ata me tunani kuma ko kad'an beson yan'uwanshi su San zance balle mahaifinshi da fauziya ta fad'a maganar a gaban shi

Haka fa aka cigaba da niman fareeda inda yau kwana 6 kenan baba ya rame yayi baki alhaji al'amin kuwa har station yaje da hoton fareeda Amma ba progress

Mama ta fita haiyacinta tayi baki baba ma ko abinci be iya ci

B'angaren fareeda ko duk dabaran da zatayi Dan ta gudu tayi Amma babu hanya domin kofofin gidan securities door ne haka ta hakura ta cigaba da addu'a ganin Zama da yunwa bazai taimaketa ba yasata fara dafa abinci duk da dai badan dadi take cin shi ba

Wani tsanan Dr takeji domin ko ba a fada Mata ba tasan mahaifanta na can suna kukan rashinta bazata tab'a yafewa Wanda yayi sanadiyan zubar hawayen iyayenta ba,kuka ko tayi shi har ta gode allah

Tashi tayi bayan ta gama cin indomie da ta dafa ta haura sama ta Shiga toilet tayi alwala

Fitowa tayi ta shimfide dadduma ta tada sallah domin ita kwana uku takeyi

Bayan ta idar tayi ta addu'a

Washe gari da safe

Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
[1/4, 12:54 PM] Maman Noorul Hudah: πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
*_DR SAHEEB*_
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah

🌟 GORGEOUS WRITERS FORUM🌟

Home of

3 / 12