Ubayd Maleek 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Love

Chapter   5 / 37

12K to 15K   out of 110.1K words

iso tukuna aka bude musu suka shiga aka rufo.

Zubewa jekadi tayi tana kwasar gaisuwa cikin tsananin girmamawa da ladabi.

A natse itama NURUn ta durqusa qasa kanta na qasa ta yaye fuskarta cikin sanyin da nutsuwarta ta gaidashi batareda tayi Masa kirarin dataji jekadi nata jerowaba sbd Bata iyaba.

Kallo 'daya yayiwa NURUn ya tabbatarda nutsuwarta ya dauke Kai Yana amsa gaisuwarsu tareda Basu izinin miqewa.

Basu wani jimaba suka fito zuwa sashe sashe na cikin delah din Wanda wani sashen a mota suka jejje sbd nisa da girman DELAH din,

Ayau ta tabbatarda arziki ma Ashe na wani sunane Dan kuwa taga inda arziki yake magana,

Tabbas delah wani Depot ne na arziki Dan idanuwanta da tunaninta sunkasa daukar wasu abubuwan data gani ahakanma akecewa gizah ta dame delah tabbas idan mutum beyi da gaskeba a irin Nan tsaf imaninsa zai barsa sbd kwadayin dawwama acikin irin wannan daula ta mulki.

Sai magriba suka samu damar dawowa sashenta duk da haka bawai koina suka samu zuwaba Kai gaisuwa saidai duk inda sukaje babu Wanda yaga fuskarta andai tabbarmusu da sabuwar negestati ce.

Tarin tukuicin dukiyar data samu ayau din Bata bayyanuwa danma asalin tukuicin na tafe ne ranarda za'a tabbatarda budurcinta delah ta sheda.

Kallon uban dukiyar zinarai da situru tayi tana rintse idanuwanta cikin tsananin azabar gajiya Dan qafafuwanta har wani numfashin azaba sukeyi daqyar ta miqe ta daddafa tashiga toilet tayi wanka ta gasa qafafuwanta tana tsiyayar hawayen tausayin kanta da kewar iyayenta itafa shikenan yanxu haka zataita rayuwa daga ita sai bayi sai idan neges dinda take tasa ya buqaci ganinta a turakarsa.

Tunanin hakan yasa kukanta tsananta tafara kuka sosai cikin bayin tana cusa kana cikin qafafunta Dan zaune take cikin bathtub.

Da kanta ta rarrashi kanta tasake dauraye jikinta tayi alwala tafito tazo daqyar ta tsaya akan qafafunta tayi sallolin da duk basuyiba yau din tana idarwa da kanta ta sidado ta fito cin abinci da yunwama Kamar ta kusa kasheta.

Tana zama dakanta ta zuba abincin sbd duk basanan suna gurin sallah Suma Dan Suma Kam sun gaji hannu tasaka Bata tsaya saka wani cokaliba kadanma taci sbd cikinta daya qulle tasha lemun sabuwar abarba ta miqe ta nufi daki tana shiga ta kwanta kife take baccin wahala yayi gaba da ita.

Washe gari ma yini tayi daki kwance abinci kawai ke fiddo da ita Palo har dare bataga jekadi ba sai washe gari da yamma tazo bayan ta tabbatarda NURUn ta huta daga wahalar shekaran jiyan kafin suka fara gudanarda aikin dake gabansu.

Sannu ahankali jekadi take koyarda ita komai na al'amuran rayuwar gidan sarautarsu ta delah,

Duk wani abu dayakamata NURUn ta sani Kuma ta iya Ana kan koya matashi Kuma tana 'dan ganewa duk da hankalinta tashi yake idan Ana fada Mata wasu abubuwan ko koya Mata sbd batasan ta Yaya zata gudanar da rayuwarta ahakan ba,

Ta bangaren iyayenta kuwa tuni ta aika musu da dukkanin tarin dukiyar tukuicin data samu.

Ga kaleeb ta bangare daya kullum saita je takai Masa gaisuwa Wanda jekadi ce ta 'dorata akan hakan bawai Dan al'ada bace kawai tanason Gina qauna me qarfi ne tsakanin NURUn da kaleeb sbd sanin irin tsananin qauna dake tsakanin Kaleb da UBAYD MALEEK.

Sannu ahankali tafara sabawa da rayuwar delah ga jekadi ma data Dan shaqu da ita sbd tana Mata kallon uwa kokuma tacema Kaka musamman sbd itama jekadin tsakani da Allah taji tana qaunar NURUn sbd nutsuwa da biyayyarta ga rashin son hayaniya sai hakan kesake saka Mata nutsuwa da shigar NURUn rayuwar UBAYD koba komai UBAYD Kamar 'dane agareta sbd agabanta aka haifesa yagirma.

Tsawon watanta biyu a delah Amma haryanxu ko a zance bataji maganar waye aka bada ita gurinsaba,yaushe za'a kaita,Ina yake haryanxu shiru duk bataji komaiba Abu daya tasani shine jekadi ta fada Mata wata me kamawa za'a kaita wani guri.

Da farko hankalinta ya tashi Jin tafiya wani guri Amma sai jekadi tafara kwantar mata da hankali da cewar zasu dawo bawai zaman dindin bane itadai Sam hankalinta yakasa kwanciya ko bacci yanzu kasawa takeyi saitajin Kamar rabuwa zatai da gida har abada.

Ganin kwana biyu har wata rama ta sakota gaba da tunani da damuwa yasa jekadi takwai Kaleb zancen sai tunani ya shegesa yace anfasa Kiran zuwan UBAYD sbd idan yazoma kowa zai San shi keda negestatin Kuma Kamar yanda akasan MALEEK da ikonsa bazai taba karban negestati ba matuqar ba baya tareda matarsaba hakan zaisa afara tunanin sun rabu Wanda za'a iya amfani da wannan gurin muguwar manaqisar mulki akawo suka ga karban mulkinsa Wanda keleb bazai taba Bari hakan tafaru ba yafison koda za'a San ubayd da matarsa sun rabu zuwa lokacin sun samu wata Matar aure kawai za'a daura idanba hakaba da matsala babba Dan haka yasa aka matso da tafiyar NURUn tareda Bata damar izinin zuwa ganin iyayenta da daddaren yau.

Qatuwar baqar Mercedes Benz beymach ta ajiyeta gefen gidansu da qarfe goma sha biyu na dare Wanda shine lokacin barinsu fita delah tana kallon qofar gidansu jikinta yayi mugun sanyi taji idanuwanta sun ciko da hawaye ta ziro qafarta waje ahankali tareda fitowa.

Kai tsaye itace agaba jekadi na gefenta tana cewa"

Karkiyi kuka gaban iyayenki Zaki daga musu hankali Kuma laifine babba yin kuka was umarnin masarauta Dan haka ki kula.

Batace komaiba itadai burinta ta Isa cikin gidan taga ahalinta cikin sa'a kuwa har lokacin abal dinta da ammi na zaune tsakar gidan kan shimfida suna Shan iska sbd tsananin zafin da akeyi yau din meryam ma na kwance gefen ammi tayi bacci ammin na Mata fitar sauro.

Da budaddiyar murya jekadi ta rangado sallamar da har maqota anaji sbd asan da zuwan NEGESTATI ne.

Da ammin da abal lokaci daya suka miqe suna kallon qofar dasu NURUn ke shigowa wadda qamshinta tuni yafara cika tsakar gidan da hanzari ta qaraso ta fada jikin ammi tana riqo hannun abal duk alokaci daya tana sake hawayen farin cikin ganinsu batareda ta iya cewa komaiba.

Cikin tsananin farin ciki ammi ke Mata yare tana cewa"

Ya Allah NURU munyi kewarki matuqa.

Murmushin farin ciki kawai abal ke saki Yana kallonta ta cikin hasken farin wata Yana sake godewa Allah daya bashi ikon ganin 'yarsa 'daya tasamu gidan zamanta na rayuwa saura daya itama Yana fatan Allah yabasa ikon ganin yayi Mata aure ta tafi nata gidan.

Zama sukai tana tsakiyar iyayenta Meryam ma tuni NURUn ta tayarda ita sbd bazata iya tafiya basui mgn ba tana ganin NURUnta tafada jikinta da qarfi tana ihun murna Wanda ya tado da gimbiyar gidan wato padima ta fito cikin wani irin laushi tana jujjuya ido ta bude da kyau tana kallon mutanen idanuwanta suka sauka kan NURU tasake dubawa dakyau taga NURU ce da sauri ta qaraso tana cewa"

NURU????

Kece yanxu?

Dagowa NURUn tayi fuskarta daukeda murmushin kewar padiman ta taso suka rungume juna tana cewa"

Nayi kewar dukkaninku padima.

Zaman sukayi padiman nabinta da wani kallon kurulla da zallar mamaki tanson yin tunanin fahimatar wani abu kanta Yana toshewa da mamaki dakuma tausayi tausayin NURUn da rayuwarta ta lalace.

Shagala sukai sosai harsaida lokaci yaja jekadi tashigo da cewar zasu tafi Nan jikinsu duka yayi sanyi Amma hakanan suka bawa NURU qwarin gwiwa abal yabita da wasu irin adduoin Sanya albarka masu zafi wainda suka Sanya jikin kowa yin sanyi suna amsawa da Amin.

Har mota suka rakota tashiga padima sai kallon komai take cikin mamaki tana qaryata abinda idanuwanta ke gane Mata sbd tasan ba komai bane duk wannan akan irin rayuwar da ita zatayi a Nan gaba.

NURU kuwa Har suka Isa delah tunaninta bai daina zurfafaba gabaki daya yanzu kanta a toshe yake sai yanda akai da ita yanzu kenan.

Tana Isa sashenta daki ta wuce Kai tsaye ko tubewa bataiba ta kwanta tareda rintse ido.

Washe gari haka akai fita da ita zuwa gurin passport Wanda tun kafin su Isa aka tanadi komai babu Wanda yasamu damar ganin fuskarta sai Wanda ya dauka hotonta dagacan Kai tsaye delah suka dawo washe garima saida aka futa da ita zuwa wani gurin wanda acanma tasake tabbatarda mulki wani abune na daban sbd irin girman da ake Basu ko cikin ansan cewar bama daya daga cikin jinin sarautaceba ita din.

Ranarda ta cika kwana shida da zuwa gidansu ranar aka gama Shirin tafiyarta tsaf a washe gari itada jekadi jirginsu yabar Ethiopia zuwa qasar France.

***********

Breakfast sukeyi zaune su uku akan dining din Wanda suka kwana biyu Basu samu damar cin abinci tareda dad din nasuba sbd rashin zamansa a kwanakin sai yau,

Kallonsa AFIA tayi taga yanda yayi wani irin fresh fatarsa sai wani glowing takeyi tsabar hutu da arzikin dukiya duk da manyancinsa Amma Sam fatarsa taqi bayyana hakan idanma batai kuskure ba saitaga kamar bayan rabuwarsa da mum dinta wani nutsuwa yasamu.

Sake kallonsa tayi wannan karon suka hada ido ya zuba Mata manyan fararen idanuwansa cikin muryarsa me iko yace"

AFIA akwai wani abu ne?

Aje spoon din hannunta tayi ahankali tareda kallonsa gabaki daya cikin taushin murya da 'yar sakuwa tace"

Dad please for how long zamuyita zama haka mum Sarah kwanakin Nan batajin Dadi qafafunta sunfara gazawa Ina tsoron zamu koma rayuwa mu kadai dagani sai farhat sauran maids din babu wani kusanci ko shaquwa tsakaninmu dasu.

Ciki wani irin Isa ya kurba ruwan Black coffee dake cikin farin teacup din hannunsa ya ajiye tareda daukan tissue yakai bakinsa ya goge ahankali ya ajiye tukuna ya dago ya kalleta yaji zancenta ya taba zuciyarsa tabbas suna buqatan abokin zama kada kadaici yayi musu illah gasu yara qananu,

Sam baida sha'awar maidasu zama gizah gurin mahaifiyarsa sbd kada giyar sarauta da mulki ya shigesu Dan kuwa tabbas zai shigesu sbd girma da irin bauta musun daza'aitayi zai gurbata tunaninsu sarauta zatai musu muguwar shiga bazai taba son hakanba Dan haka a yanzu dai baida wani zabi bayan karban negestatin Kaleb Amma bazai taba Bari Susan da hakanba sbd bai karbetaba bakuma zai taba karbantaba zaidai kawo musu itane amatsayin abokiyar debe kewa.

Kallon afian yasake Yi tareda Dan sassauta fuskarsa batareda murmushin yafito dukaba yace"

Akwai abokiyar zama da debe kewa da Kaleb zai Aiko muku da ita ta musamman Dan haka karku damu damuwa ya qare ok??""yafada Yana shafa kan farhat dake kusa dashi tana cin pancakes da Zuma.

Cikin tsananin murna afia tace"

Dad daga delah ne za'a kawo Mana ita?

Gyada Mata Kai yayi cikin Jin dadin ganin farin ciki akan fuskarsu yace"

Yes my angels Dan haka kunada baquwa yanzu Dan haka no worries no sad face no complains.

Yes dady" farhat ta fada tana riqe hannunsa suka miqe tare suna barin dining din Dan yanzu haka yauma tafiya zaiyi zai Kwana biyu acan.

Har mota suka rakasa ya tafi dayake yau weekends ne ba school Yana wucewa suka dawo ciki cikin farin ciki sukaje suna fadawa mum Sarah sunada baquwa tananan zuwa.

Yana barin gida direct airport aka nufa dashi ya Jima Yana tunani kafin ya dauki wayarsa dake gefensa ajiye ya lalubo numbern jekadin kakarsa wadda yasan itace maganar negestati take gurinta Kira daya tana ganin me Kira ta daga cikin tsananin girmamawa hadda durqusawa duk da ba agabansa takeba tahau jero gaisuwa Yana sauraronta kafin ya dakatar da ita ta hanyar amsawa a gajerance cikin nauyin murya kai tsaye yace tanason bayani akan negestatin Nan tahau jero Masa asalin NURU da sunanta dakomai akanta cikin gajiya da zancen ya katse Kai tsaye yace"

Kada su afia su taba sanin waccece ita da matsayin datazo dashi.

Angama MALEEK ubayd sarki me kujerar delah gizah.

Yana kashe wayar ya kasheta gabaki daya tareda ajiyewa Yana daukar iPad karanta wani saqo.

Suna Isa airport ba Bata lokaci yashiga jet suka daga.

Sukuma a washe garin aranar jirginsu ya sauka qasar Kai tsaye babbar mota tazo daga gidan daukarsu daga ita sai jekadi ne Dan haka suna isowa makeken gidan na UBAYD MALEEK aptrmt dukkanin masu aiki suka fito suna musu barka da zuwa akai ciki dasu suna shigowa babban palon gidan dayasa NURU Shan jinin jikinta sukai kicibis dasu afia dasuka fito tarbonsu afia na ganin NURU ta tsaya cak tana kallonta cikin yanayi na Jin dadin wannan ai qawace ma aka kawo Mata tasaki fuska sosai tana cewa"

Jekadi wannan ce wadda zata tayamu zaman?

Da sauri cikin girmamawa jekadi tace"

Eh ranki ya dade itace.

Jin haka farhat ta riqo hannun NURU tana cewa"

AFIA tanada kyau sosai kaman Barbie Dina ko???

NURU bayan zare ido Babu abinda takeyi tana kallonsu hankalinta nakan gidan Wanda yasa taji tsoron duniyama gabaki daya na shigarta.

Dakin mum Sarah jekadi tasauka itakuma NURU dakin AFIA afian tajata tana sake tambayar sunanta duk Dadi ya isheta sbd take taji tanason NURUn.

##MAMUH*

HASKE WRITERS.

_ZAFAFA BIYAR_๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–

_SAFIYYAH HUGUMA_

_BILLYN ABDULL_

_MISS XOXO_

_HAFSAT RANO_

_MAMUH GEE_

_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._

ฦŠaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huษ—u____500

Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

ย  0903ย 234ย 5899

[9/6, 6:12 PM] Anty Rabi'at: _*Mamuhgee 7*_

Bin bayan afian take da kallo cikeda mamaki da 'dan Jin shakka shakka tareda tsoron binta zuwa dakinta sbd ko daga dirowar tasu ta fahimta tareda shedar da irin tsananin girman dasuke dashi na iko Dan duk Wanda jekadi ta russunawa Kai ba qarami bane me cikakken ikone na sarautar delah.

Suna Isa qofar makeken bedroom din afia ta bude qofar tareda fara shigewa tana juyowa fuska asake tace"

Welcome to my world beauty.

Tsayawa NURU tayi tana kallon dakin daga bakin qofa jikinta nasake yin sanyi da mutuwa sbd a wannan gabar takai qarshen shiga rikicitaccen tunanin inane wannan duniyar da aka kawota?.

Ganin kamar tashiga tunani da wasi wasi yasa AFIA kamo hannunta ahankali ta janyo hannun tana janyota cikin dakin ta tura qofa ta saketa ta nufi kan couch din dake dakin ta zauna ahankali tana waiwayowa inda NURUn ke tsaye har lokacin tace"

Kishigo karki tsaya anan Zaki gaji da tsayuwa.

Dan cika umarnin AFIA din ne kawai yasa NURU fara takowa tana qarasowa cikintsakiyar dakin fuskarta a qasa sbd yanzu Kam tafara tunanin bauta aka kawota tayi anan ba wai maganar negestati ba.

AFIA batason maimaita zance shiyasa ta miqe tareda fitowa dakin tasaka aka kirawo Mata jekadi tace tabiyota zuwa dakinta suna zuwa ta kalli NURUn kafin ta kalli jekadi Kai tsaye tace"

kiyi Mata bayanin banason wannan kakkamewan datake idan batada sakewa kokuma bazata iya sakewa damuba kawota baida amfani tunda sbd mu aka kawota anan Dan debe Mana kewa.

NURU dake sunkuye da Kai da sauri ta Dan dago ta kalli bakin afia din Jin ba maganar negestati ne yasa aka kawota ananba kenen Reno zatace kokuma aikatau kokuwa bauta zatace duk da taga afia din bazata wuce tsaranta ba Amma dai tana fatan koma tsaran meryam dinsu zataiwa bauta ba kamar afia datake tsaranta ba yafi mata tsari da nutsuwa akan zamowa abokiyar kwanciyar kokuma abokiyar nishadi neges dinta.

Kamar daga sama taji jekadi takira sunanta tana cewa"

Biyoni muje.

Sanyi jikinta yasakeyi ta juya anatse tabi bayanta tana sake sunkuyar da kanta harsun Kai qofa zasu fice afia tasauke ajiyar zuciya ta nufi kujera zata zauna tace"

Jekadi kibarta kawai kun gaji sbd doguwan tafiyan da kukai kuje da ita can ku huta kuci abinci da sauran abubuwan tukuna.

Yanda kikace haka za'ayi li'iliti(princess/gimbiya/'yar sarki)

Wucewa sukayi suka qarasa ficewa suka nufi can dakin da aka sauke jekadin.

Abinci suka fara ci Wanda NURU takasa ci sbd damuwa da tsananin tunanin Ina shin Ina rayuwarta ta dosa ne tare Kuma da fargaba haddama tsoro ta yanda za'ace anan za'a barta to tayaya zata iya rayuwa acikin wainda Bata saniba bama ta taba ganiba.

Ganin ta shiga damuwa da firgici sosai yasa jekadi Dan daka tawa tareda kallonta ta dauki cup din danyar madarar turawa me sanyi ta miqa Mata cikin kulawa tace"

Karba wannan Kisha zakiji dama daman damuwa sbd wata damuwar yunwa na shigowa cikinta.

Ba musu ta karba ahankali cikin sanyin murya tace"

Ameseginalehu(thank you/nagode)

Tana shanyewa ta miqe tashiga toilet din dakin tayo alwala tareda wankan da jekadi tace tayo Dan anan so biyu ko uku zata ringa wanka sbd ko masu aikin gidan tsaftarsu abin koyi da burgewace bare ta masu gidan.

Bayan fitowarta jekadi da kanta ta nuna Mata inda abin sallah ke shimfide Yana kallon gabas ta qarasa bayan ta Sanya doguwar jallabiya fara da lullubin sallah ta tada sallar.

Bayan ta idar duk sallolin da ake Binsu ta gyara zama jiki amace cikin damuwa.

Saida jekadi tayi sallolin itama kafin ta fuskanci NURUn tafara jero Mata bayaninda maleek ya buqaci datai na boye matsayin NURUn na negestati a zaman dazatai agidan kasancewar lefine zatayi nayiwa negestatin UBAYD MALEEK guda yasata Dan dauke kallonta daga NURUn tace"

Kicire damuwar komai ki kwantar da hankalinki sbd rayuwarki zata inganta zamanki anan din,

Kinzo Nan ne sbd Yaya 'yayan MALEEK UBAYD zama badan komaiba haka zalika maganar negestati gabaki daya anbarta inaga saikin dawo delah

Kwanciyan hankalinki shine na iyayenki dan haka yanxu Kam ma Kamar umarnin li'iliti AFIA ne ki sake acikinsu wata babbar sa'ar rayuwace Kika samu wadda kowace mace dake daular ethio ke marmarin samu Amma bazaki gane hakan ba wata qila sai gaban idan kinada rabo kenan Dan haka aikinki ayanxu kawai shine kulawa da 'yayansa cikin kulawa me kyau duk da li'iliti AFIA tsaranki ce bazaki iya Bata kulawaba Kamar farhat Dan haka farhat yanzu a qarqashin kulawanki take.

Tana gama fada ta miqe ta fice Dan komawa gurin AFIA ta sanar da ita inda NURUn zata zauna duk da Babu Wanda yasani ita tasan babban laifine Kuma bazai yiyuba tabari negestatin maleek ta kwana acikin masu aiki ko bayan shekaru dari ne idan har tana raye tasan wata ran saita fuskanci hukuncin hakan.

5 / 37