Ubayd Maleek 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Love

Chapter   32 / 37

93K to 96K   out of 110.1K words

saidai tasan yanada wuya takasa Mata wannan alfarman tunda aikintane.

Zama NURU tayi kusada afia din tana kallonta dukkanin hankalinta akanta tace"

Gani menene??

Numfashi afia tasake sauke akaro na biyu tana kallon NURUn cikin nutsuwa da nuna damuwarta da mahimmancin da maganar take dashi agurinta tace"

Maganar mum dinace yau nazo neman alfarma dama taimako agurinki,

Kinsan yanda nakeson mahaifiyata dakuma yanda nasamu wannan sassaucin yazo gareta, Dan Allah ko Zaki min alfarmar cika sauran formalities na karbota a matsayinki na lawyer duk da nasan Baki Gama zama cikakkiyar lawyer din ba Amma dai kinada damar zuwa.

Akaro na farko yau Ina roqonki wata alfarma Ina fatan Kuma Zakiyi sbd Ni Dan nasan abinda mum tayi Miki Bata cancanci ki taimaka din ba Amma Kuma Ina roqonki kiyi sbd Ni da farhat.

Tsit NURU tayi tana dauke wuta sbd Bata taba tunanin wannan maganar ba bama ta taba kawo tunanin shiga cikin wannan al'amarin ba gaba daya

Musamman na mum din afian Wanda shigarta kamarba bazai yiyuba sbd ba ita ke ikon kanta ba hakama ita tayaya zata iya zuwa Kai tsaye wannan aikin?¿

Kasa cewa komai tayi ta dago ta kalli afia batamasan me zata ce Mata ba Dan neman alfarma agurinta da afia tayi kamar abune da bazata iya cewa aa ba hakama Kuma tanajin shakkar amincewar sbd batamasan ta Yaya zata sanar da Wanda yake ikonta zancen.

Ganin Shirun NURUn yasa afia shiga damuwa takira sunan NURUn tana cewa"

Bazaki iyaba right???

Zubawa afian ido NURU tayi tana sake shiga tunanin rasa abin cewa ta girgiza Kai ahankali ta bude Baki tace"

Afia Babu alfarmar dazaki roqa gurina nakasa Miki matuqar Bata sabawa ubangiji bace saidai ta Yaya za'a sanarwa dadynki Kuma Kinga.....

Katseta afia tayi da cewa"

Dad dakansa jiya gabanki yabada damar komai gameda case din mum din wannan maganar ta sirrice yanzu idan nace zamu dauko lawyer daga waje then komai zai iya sauyawa

So please NURU ki amince dan Allah dad Bai taba dakatar damuba ko hanamu harkan data shafi karatu bare yanzu aiki Dan Allah ki yarda Ina roqonki.

Dagowa NURU tayi takalli afian tareda Dan sauke ajiyar zuciya tace"

Na amince Amma sai dad dinki ya amince Zan nema izininsa.

Shiru afia tayi tana kallon NURUn tana nazarin abin data fada din saidai tunda ta amince batada zabin daya wuce itama amincewa da bayanin tace"

Thank you.

Miqewa tayi zata fice ta dakata da cewa"

Anjima Imran zai iso inshallah saikuyi mgna.

Ficewa tayi tabar NURUn zaune mamaki na kasheta Jin da Imran zasu tafi kenan.

Faduwa gabanta yayi sbd tunani biyu dasuka shigeta take,

Na farko ta Yaya zata fadawa MALEEK maganar zuwan harda qarin Imran ne abokin aikin,

Ma biyu tayaya zata iya fita daga ita sai Imran bazata iyaba sbd tasan Imran din sai yayi kokarin tado Mata da maganarsu data wuce wadda hakan baya cikin abindata shirya dawowa dashi.

Bangare daya afia nason daureta da jijiyoyin jikinta.

Daqyar ta iya tashi daga Inda afian ta barta ta nufi bedroom tafada toilet jekadi dake jinsu batace komaiba ta juya ta fice daga sashen Kai tsaye ta nemi numbern Mr Omar ta fada Masa komai yace idan yadawo zai sanarda maleek.

Qarfe goma Sha biyu na ranar Mr Omar ya sauka a airport na gizah na dawowarsa Dan yagamo abinda yaje Yi Kuma adaidai lokacin Imran jalal ya sauka a airport din cikin sa'a suka hadu dukkaninsu motar masarauta tazo daukansu shi Mr Omar drivern maleek yazo daukansu shikuma Imran drivern Anneti afia tasaka yazo daukansa.

Kallon kallone yashiga tsakaninsu Mr Omar ya saki wani murmushi Yana miqawa Imran din hannu yana kallonsa yace"

Barka da zuwa Barr Imran jalal and all the best.

Miqa Masa hannu Imran yayi Yana cewa"

Thank you Mr Omar.

Murmushi Mr Omar yasake sakewa Yana Dan kallon gefen Imran din yace"

Kai kadai kazo??

I mean nasan kasan kana buqatan wani lawyern ga aikin.¿

Sai alokacin Imran yasaki murmushi Yana kallon Mr Omar din yace"

Aikina ne Kuma nasan da hakan shiyasa lawyern da nake buqatan muyi aikin tare tana Nan Dama

Fata dai kawai idan zaka iya jimirin ganin hakan.

Wani irin Murmushi me Fadi Mr Omar yasake Yana sake cewa"

Good luck with that too."ya juya ya wuce Yana sake sakin murmushi yashige mota aka jashi sukabar Imran din a tsaye Yana bin motar da kallo kafin ya sauke numfashi me zafi yashiga tasa motar da akazo daukansa  suka wuce Suma Yana Jin tamkar zuciyarsa nason karbuwa da qiyayyar Mr Omar sbd koyaushe shine yake shiga hancinsa da kudundune Amma sbd qiyayya bata cikin abindayake Bari Yana shigarsa yasa yake yaqar hakan Yana dannewa sbd ya dauki qiyayya wani aikin wahala da kake dorawa kanka yazo Kuma ya ringa wahalar dakai ka rasa focus da sukunin rayuwa karshe ka wargaza kanka agurin qiyayyar wani.

Kai tsaye dukkaninsu masarauta suka nufo cikin sa'a kusan atare motocinsu suka iso Mr Omar ya wuce Kai tsaye sashen maleek daukeda sketch din dayazo dashi daga delah shikuma Imran afia ce da kanta ta bada umarnin kaisa sashen baqi na musamman kafin ya huta suyi mgn.

##MAMUH#*_Mamuhgee 45_*

*_Mamuhgee 44_*

_*LAVENDER RESTAURANT..*_

   _(Palace of mouthwatering food/delicacies)_

_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_

_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE.._*

_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.._*

_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283  akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021  to 3/10/2021 Nigeria @ 61_*

_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU._*

_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN. _*

_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇🏾RIGIJI GABJI_*

_*Nigeria @ 61 _*

_*COOKING COMPETITION!!!_*

_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo  na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine  da wasu prize suma saura kuwa  zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar_*

_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA_*

****************

Sai yamma lis ta fito suka hadu da Imran din suka nufi sassan Anneti sbd sosai yake girmamata itama duk cikin familyn lailah shine yaron datafi ganin hankalinsa fiyeda kowa har iyayensa shiyasa akwai mutuntawa a tsakaninsu ba laifi tana yaba Masa.

A palon Anneti din na farko suke zaune suna gaisawa tana sake tambayarsa family tareda jajanta Masa abin daya farun na lailah Yana jajanta Mata itama.

Duk maraice NURU na zuwa gurin Anneti din hakama yau Kai tsaye ta nufo sassan cikin sanyi da nutsuwa tareda jekadi tana sanye da doguwa riga dark purple suka qaraso sashen da sallama dauke abakinta tashigo

Dukkaninsu suka dago kowa na zuba Mata ido da nasa tunanin.

Ganin Imran datai shine abu na qarshe da Bata tsammanaba ta sunkuyar dakai tana kokarin juyar da hankalinta daga kansa ta nufi Anneti ta zauna kusada ita tana gaisheta cikin biyayya Kamar ko yaushe

Cikeda kulawa Anneti ta amsa tana miqewa Dan amsa wayar da ake Mata ta shige ciki tana cewa"

Ina zuwa.

Murmushin qarfin hali NURU tasaki tareda Dan waiwayowa ta kalli su afia din a natse tacewa imran"

barka da zuwa.

Boyayyar ajiyar zuciya ya sauke tareda dagowa ya 'dan kalleta ya dauke Kai Yana cewa"

Thank you.

Yi afia tayi Kamar batasan meya taba faruwa tsakaninsuba ta gyara zama tana fuskantar kowannensu tayi musu godiya tana cewa"

Anjima zata karbo takardun daga hannun Mr Omar yabawa imran.

Qala NURU Bata samu cewaba sai Dan yaqen murmushi datayi ta miqe tana cewa"

Zan koma.

Tashi sukayi dukkaninsu suka fito tare afia na kokarin Jan kowannensu da zance sbd su samu sakewa kada itadai asamu matsala agurin fitar mum dinta.

Suna fitowa kofar sashen gabaki daya daidai isowar MALEEK Mr Omar na gefensa Yana Masa wani zancen Wanda kullum baya rasa zance tsakaninsa da MALEEK.

Kwarjininsa da cika musu idon yayi yasa dukkaninsu sauke Kai Banda NURU data dago ta kallesa zuciyarta na narkewa saidai dukkaninsu Babu Wanda yasamu ko kallo daga garesa ya wucesu ya shige saidai abin mamaki Yana shiga din saiga dukkaninsu sun dawo Banda NURU wadda ta nufi sashenta zuciyarta ba dadi.

Ba wani fargaba ko tunanin komai afia ta sanarda dad dinta gameda zuwan Imran da aikin dasuyi din shida NURU tareda amincewar NURUn sai daidai lokacin ya dago ya kalleta da idanuwansa dasuka sata Jin tana neman fara rawar murya.

Ya maida kallonsa kan Imran ahankali kafin ya juyarda kallonsa kan Mr Omar ba wani zance Mr Omar ya kalli Imran yana cewa"

Bismillah muje abaka takardun.

Dan kallon maleek Imran yayi Dan Dole cikin girmamawa yace"

Ka huta lafiya" ya juya yabi kofa da Mr Omar yake nuna Masa suka fice.

Kasa sukuni afia tayi ta juya ta fice da sauri itama tana cewa"

Kafito lafiya dad.

Tana fitowa ta wuce sashen NURU Kai tsaye saidai Koda ta isa NURUn Bata wani cikin walwala sbd cewa tayi kanta na ciwo sai tabarta Dan tasamu ta huta sbd goben.

Juyar da Kai NURU tayi tana Dan rufe idanuwanta kallo daya maleek ya Aiko Mata Yana dawo Mata sbd itakai ta lurada kallon Wanda yasa duk taji Kamar zazzabi na neman kamata ta sauke qaramin numfashi ahankali tareda tashi zaune sbd sallar magriba datayi ta nufi toilet tashiga tayo alwala tana fitowa farhat na shigowa a Sanyaye tace"

Jeki kiyo alwala sweetie muyi sallah ko.

Zaune yake cikin palonsa bayan sallar magriba Yana kallon sketches din guda biyu dasuka nuna mutum dayane da Wanda yakaiwa Yan jaridar da Wanda yabada meriz ya sake kallon idanuwansa

Cikin nutsuwa Mr Omar yace"

Yakoob ne.

Dan waiwayosa maleek yayi cikin kamewa yace"

Ya aika sketches din gurin hukuma tareda bayanin komai da aka hada akan case din gobe ko jibi Inshallah za'a Kai karshen matsalar Ina buqatan komawa Paris.

Dan shiru Mr Omar yayi Yana Dan Sosa tsakiyar kansa kadan cikin Dan tausasa harshe yace"

Maganar shigar mushrah cikin maganar MSS LAILAH akwai hadari sbd abune na sirri dakuma hadari sbd neges nada mutane ko Ina

Akwai hadari zuwanta is too risky Kuma tareda umnn ummn Imran din ma is....

Wani Abu maleek din ya Dan hadiye batareda ya kalli mr Omar din ba yace"

Yaushe ne tafiyar daukan lailan??

Gobe ne Inshallah da karfe Tara na safe yace sbd jirginsu zai tashi karfe goma na safe.

Shiru yayi na wani lokaci kafin ya miqe tsaye ya fuskanci kofar shigewa palonsa na kurya cikin kamewarsa da muryar asalin MALEEK dinsa yace"

Kaji da aikin fitarsu lailan daga qasar ita wannan ko haske waje gobe bazata gani ba zanji wannan.

Dan sunkuyar da Kai mr Omar yayi Yace"

Maleek tariga ta amince da cewar zataje ko Zan sanarda jekadi dokar kada abarta fitowa din sbd kada taje din batareda ankarewar muba....

Kallo daya maleek yayi masa yayi saurin Dan soke Kai Yana cewa"

Nagane zanji da fitarsu lailan gobe

Saida safe ahuta lafiya.

Sidadewa yayi ya fice daga sashen gabaki daya Yana murmushin dayasan na menene shikadai sbd duk duniya ko motsi maleek yayi yasan me yake nufi bare kallonsa wannan wata baiwace da Allah ya hadasu akanta shiyasa Babu me iya sanin sirrin tsakaninsu cikin ransu Allah yasaka musu qaunar junansu Dan dai shi Yana qarqashin maleek din ne yasa maleek nasa kulawan yake a boye shikuwa dama ko ransa zai iya badawa akan maleek.

Yana fitowa gabaki daya daga sashen na maleek ya ciro wayarsa ya Nemo numbern jekadi ya Danna Mata Kira Yana kokarin daidaita kansa Dan cika aikin ubangidansa tana dauka Kai tsaye yace"

Zuwa anjima maleek na buqatan ganinta a rakata sbd tsaro.

Yanayin yanda yayi maganar yasa jekadin amsawa tana satar kallon NURU wadda ke zaune Palo farhat na jikinta suna kallon cartoon din da hankalinta baya wani kai duk da dai tana Dan murmusawa kadan idan akai abin dariya.

Sai da akayi sallar ishai suka tashi sukai sallah suna idarwa tasa aka jera abinci sbd farhat Dan ita Bata wani Jin yunwa tadaisha sabuwar madarar raqumi me dumi wadda kullum ake kawowa safe da dare daga sashen Anneti.

Suna gamawa suka nufi daki farhat ma dakinta ta nufa tayi wanka Da kanta ta shirya cikin kayan bacci tazo dakin NURUn ta haye gado ta kwanta.

Wanka NURUn tayo itama ta fito ta shafa Dan neu oil kadan ajikinta tareda shafa body mist da sprays masu sanyin qamshi ta daure gashinta da band qarami ta dauko rigar bacci me tsantsi tasaka ta nufi gadon zata hau taji knocking din kofar dakin ta juya ahankali tana kallon agogo kafin ta qarasa jikin kofar Dan tasan jekadice ta bude Kai tsaye.

Ajiyar zuciya jekadi ta sauke tareda kallon NURUn tace"

Maleek na buqatan ganinki yanzu.

Shiru tayi tareda kallon jekadin cikin mamaki a natse zatai magana saita fasa ta juya Takoma ta dauko sabuwar free jallabiya ta saka akan rigar baccinta dako bra batada ajiki ta zari qaramin gyalen rigar ta rufe kanta ta kalli farhat tana Dan shafa kanta yace"

Ina zuwa sweetie kinji.

zuro slippers tayi ta fito jekadi na gefenta suka nufi sashen nasa.

Suna Isa har kofar palon kuya jekadi ta rakata ta dakata daganan tareda kallonta cikin nutsuwa tace"

Afito lafiya" ta juya ta fice daga sashen gabaki daya masu tsaron gurin suka sake rufe sashen duka.

Bude kofar tayi a natse tashiga da siririyar sallama bakinta.

Sanyi da qamshin turarensa ne suka cika palon ba motsin komai sai tv dake aiki itama murya can qasa kaman Koda yaushe.

Baya palon Dan Haka ta daga Kai ta kalli kofar shiga bedroom dinsa sai taji shakkar qarasawa ciki Kai tsaye

Ta dauke Kai tana Dan sauke numfashi bugun zuciyarta na sauyawa ta daure ta taka ahankali ta Isa kofar dakin ta Dora hannu ahankali kan handle din kofar daidai ya bude kofar shima.

Tsayawa tayi cak tareda dagowa tana kallon fuskarsa dake fidda sirrin zallar kyawunsa.

Fararen idanuwansa ya zuba Mata Yana kallon fuskarta Batareda kowannensu ya motsaba.

Wani yawu ta hadiye tana sauke kanta qasa sbd Jin yanda suka matse sosai gashi qamshinsa direct yake shiga hancinta kamar yanda nata ahankali yake tashi Yana shigarsa.

Motsawa tayi ahankali zata kauce matsa daga kofar ya riqo hannunta ahankali tareda janta zuwa cikin dakin suka koma tareda rufo kofar ya saki hannunta ya nufi kujerar dake dakin ya zauna tareda daukan wayoyinsa Yana kashewa daya bayan daya batareda ya dagoba ya bude Baki cikin kamewa zaiyi magana ta qaraso gabansa cikin nutsuwa ahankali ta rigasa da cewa"

I'm sorry.

Dagowa yayi ahankali ya kalleta da fararen idanuwansa batareda yace komaiba ta dauke nata idon daga nashi tareda sake bude Baki zatayi magana ya miqe tsaye ya tsaya gabanta har suna Jin dumin numfashin juna ahankali can qasan maqoshi yace"

Uhum Ina sauraronki.

Shiru tayi sbd zuwa lokacin bugun zuciyarta yagama sauyawa ta rintse idanuwa ahankali ta bude tana sake motsowa cikinsa take wani yawu ya wuce Masa da sauri ta maqoshi ya kalleta zaiyi magana ta dago idanuwanta ta kallesa sai ya kasa maganar Ya kalli idanuwanta dake neman cikowa da hawaye ya lumshe ido yanajin mamakin saurin hawayenta dasuka bashi matsala aduk lokacinda yagansu

Ahankali ya daga hannunsa ya kamo qugunta ya qarasa mannota da jikinsa gabaki daya

Ta lumshe idanuwanta hawayen dasuka cikasu suka gangaro kan kumatunta yabisu da kallo yana zura hannuwansa cikin jallabiyarta ya zage zip din dake gaban rigar ta zame gabaki daya ta zube aqasa rigar baccinta ta bayyana ya kalli wuyanta zuwa qirjinta dake sama Yana qasa sbd numfashin datake fitarwa na bugun zuciyarta daya sauya

Kafin ya dago ahankali Ya kalli cikin idonta tasake rufe idanuwan sbd Jin hannuwansa cikin rigarta Yana zamewa

Rigarta na zamewa kasa ta shige jikinsa tareda qanqamesa sbd kunya da mutuwa da jikinta keyi ahankali.

Qanqamesa datayi shiya haifar Masa da tonuwar asirin zuciya da gangar jikinsa ya dago da fuskarta Yana kallonta idanuwanta a rufe taji bakinsa kan kunnenta Saida ya sakar Mata wani numfashi me dumin dayasa kafafunta sarewa ta zube gabaki daya ajikinsa ya riqeta dakyau Yana sauke numfashin kirjinta dake gugarsa dakyau can qasan maqoshi da wata irin murya taji yace"

*_Befik'iri wisit'i nenyi_*

  sumewa takusa Yi ajikinsa lokacinda kalmomin suka shiga kunnuwanta

Dukkanin jikinta ya dauki rawa ta bude fararen idanuwanta dasuka sauya take hawaye suka ciko cikinsu ta dago amatuqar sanyi ta kallesa tana kasa yadda da abinda yace saiga hawayenta na gangarowa

Ya Dora hannunsa a inda yasata rinte ido da sauri Yana dauke numfashin kafin tajin saukan bakinsa cikin nata tareda dagata sama gabaki dayanta ya Dora kan gadonsa har lokacin bakinsa na cikin nata wannan karon tun daga Nan tasan yau labarin dabam ne musamman dataji Yana sauyawa bakinsa gurin zuwa nishinsa na daukan sauti ahankali ahankali.

Karfe bakwai na safe afia ta qaraso sashen NURUn cikin shirinta tsaf duk da bada ita za'a ba ita airport zataje ta jirasu acan zatai bankwana da mum dinta.

Kallon farhat dake bacci ita kadai

32 / 37