Dan Minister 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mrs Nashe Category :  Love

Chapter   6 / 12

15K to 18K   out of 35K words



Baffah yace sani kaban kunya wlh kabani mamaki sani da iliminka da hankalinka kake kula tsohuwar Nan Kuna Raba abin kunya gaban yaranku Kai sani bakaji kunyaba ko mukamin da kake dash na MINISTER baka dubi girmanshiba saboda San danka yarufema Ido ka daka ta tsohuwar nan kuka dinga Raba abin kunya gaban su nabil ita ai yadace Kai Mata uziri akwai tsufa na damunta da rashin ilimin Kai kumafa wlh kaiwa kanka fada kayi kokari ka hada Kan yarannan su zauna lfy Kar na karajin makamancin haka yasake faruwa

Yace to baffah kayi hakuri Amma gaskiya inajin tausayin nabil wlh

Baffah yace au du abinda nake fada be shigi kunnan kana ko

Katashi ka tafi kaima da mgnar da zamuyi da fatima


























New writer's

Hakan Take
*Husba'ahfama* 鉂ゐ煈� *'YAR KWALLIYA* 馃コ馃拑

馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹
馃憼

馃拕馃拝 *DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃




Written by *Husba'ahfama*


*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*

Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*













9-10







MINISTER yace baffah kayi hakuri wlh tsohuwar ce bata da mutunci Dan Haka nake ajje komai agefe nake kulata yanzufa kaji me tace Wai MINISTER take Kira da Miss miss Wai mukamin Miss Miss aka bani Dan Allah Kar ta Kara kwanar Mana agida ta koma inda ta fito har jikar tata

Baffah yace Ni dai azamana na mahaifinka ka dena shiga harkar yarannan kayi kokarin hada kansu ba Wai kana hura wutaba Kana nuna bakaso tin daga jiya Allah yafara nuna maka ishara Akan auransu tashin farko anfasa maka goshi yau baya gaba in ka kuma shiga har karsu bakasan me ze faruba karabu da iya Kar ka daka ta halinta kaso shatuwa kamar yanda kake san nabil gaba bakasan wana alheri zata za me mukaba azuriarka gaba zakaji kunyar abinda ka aikata infa kaji nasihata in Kuma bakajiba to Allah yaba da sa,a tashi ka tafi

Bayan minister yafita

Baffah yace Fatima Allah yaimiki albarka Allah yabaki hakurin Kula da yarannan nasan daga ke har Amina Baku da matsala yanzu Dan Allah kiga me yarannan sukayi yau kowa acikinsu Yana Ji da danyan Kai ita rikwan Kaka uwa ba kwaba shikuma rikwan namiji uba bakwaba ga nabil da shegiyar zuciya da zafin Rai ga shatuwa da tsokana da taurin Kai shi ma Kuma nabil din akwai taurin Kai in Abu yafi karfinki atsakanunsu kina kirana ki sanar da Ni zan zo Dan sani ba ze musu fada na tsakani da Allah ba se yasa San zuciya aciki nashi ze so ita Kuma iya dole yau na jata mubar gidannan yakin badar din da akayima jiya da yau ya isa haka ai in har akabar iya agidannan bazamu iya gyara ko maiba yanzu kije kisa akai mata abinda takeso taci se mu tafi du abinda yashige Miki duhu Akan abinda na fada miki kiki rani kijin Allah yabamu sa,a Akan niyarmu ta alheri Kan yarannan

Tace ameeen baffah Ni yanzu damuwata yanda nabil da shatuwa zasu na kwana waje Daya wlh abinda kamar wuya Dan bakaga rigimar da mukayi dshi Akan su iya sun kwanar Masa adaki cewa yayi yabar bangaransa gaba Daya Kuma baya San komai na wajan shi sabo ze canja se da nacimai mutunci sannan yahakura Kuma kasan alhaji bayansa ze goya

Shawara baffah yai tabawa hajiya Fatima sannan yadada samun minister yadada jamasa kunne sosai Amina itama yafada Mata gudunmawar da yakeso tayi atsakanin nabil da shatuwa

Iya ankai ruwa Rana da ita sosai Kan ta yarda ta koma mazagai ta rabu da shatuwa bakara min kuka iya tashaba na rabuwa da jikarta har tausayi tabawa su baffah ana haka nabil yashigo falan yasamu iya tana kuka Baki yatabe yaja tsaki kawai se gani sukayi iya tatashi tsaye tabi ta bayan nabil babu zato babu sammani Dan Babu Wanda yakawo me zatayi tatakarkara ta dimawa nabil dundu a gadan baya se da yagantsare Dan abin yashige shi beyi zatoba se saukar hannunta yaji

Iya tace Dan kwal uba ai ga Wanda du yaja komai Nan yarabani da jikata muna zaman zaman mu Kuma Zan tafi saura ka Kuma karyamin ita Kuma har yanzu ban huceba se nayi zaman Yan bori akanka ko yaushene me zubin karfafa me shigar Mata dandudu kawai yau Kuma irin shigar da akayi kenan kuma ubanka nagani yaki ya hanaka Dan miss miss din uwa kawai takalli hajiya Fatima yarnan bakiya Saar Daba da mijiba du Basu da mutunci ke Kuma gaki saliha me kirki Amma auran Dole aikai Miki da uban Dan daudun Nan ko Dan Baku dace da junaba

wani irin juyowa nabil yayi cikin zafin nama da bacin Rai yadaga hannu ze damkota iya baffah yai maza yashiga tsakani

Yace haba nabil Kai ta hakuri kaji yau fa zata tafi shikenan Kuma in tatafi se Allah yasake hadaku Kar ka kulata yanzunma tsautsayine Bata saniba Tai maka

Baffah mgn yaiwa minister da Ido kar ya kula iya Dan yaga ranshi yabaci da abinda iya taiwa nabil

Nabil fita yayi daga gidan ko tafiyar baffah da iya be tsaya yagani ba cikin bacin Rai Yana ta huci zuciyarshi na Masa zafi ga baffah yahana shi yai maganin iya

Hamdalah hajiya Fatima tayi azuciyarta da nabil yafice gaba Daya daga gidan ahankali tace alhamdulillah gwara da ka tafi Dan Naga itama shatuwa kadan take jira Kai mgn ta kulaka ga alhaji shima ransa abace yake iya ta taba Dan gwal dinsa

Shatuwa Bata tashi yin kukaba se da taga da gaske zasu rabu da iya hankalinta yatashi Tai ta kuka rikicewa tayi se sun koma tare Dakar akasamu aka rabasu iyama kukan tafara Haka motar taja tafice daga gidan iya se waige take baffah yasha mitar iya Kan su je mazagai shidai ba da hakurine nashi har Allah yasauke su lfy

Nabil da yafita wajan da yake shakatawa yatafi yasamu abokansa acan suna ganinshi sukayo kanshi suna murnar ganinshi da murnar zasu hule tinda ga me kashe musu kudi yazo abokan nasa nasan suyi Masa maganar amaryarshi Amma kowa najin tsoro Kuma sunga yanayinsa Yana cikin bacinrai haka kowa ya hakura yaja bakinsa yai shuru

Da hannu yakira wani daga cikin abokan nasa yazo yabashi damin kudi yace gashinan kowa kabashi yai abinda yakeso in Basu isaba azo akarbi wasu

Yace to mutumina Dan Haka nake sanka kake burgeni baka halin karanta guri in bakai sunansa lami Ni da dashawarar da nakeso nabaka in zaka Dan bani lokaci yau Naga kamar kana cikin bacin Rai kaima kahau layi karabu da bacin Rai kadan Sha abinda muke Sha ko kadanne yau ka gwada lokaci Daya in kasha zakaji kafin yakarasa

Nabil ya daga Masa hannu cikin bacin Rai yace bani da raayin Shane tintini da inaso kaima kasan ko ana siyarwa nera nawa Ina da kudin siya Ni kwata kwata shaye shaye baya burgeni Kuma baya cikin tsarin rayuwata

Yace to ko finah ce yau Daya gatacan na kirama ita kuje ku huta da ita tinda kaga yarinyar na mutuwar sanka

Nabil yace tinkan nai maka rashin mutunci Kai maza ka bace daga wajannan Ni kake hadawa da mace ka kwasan wana Hali Mata suka jefani Kuma shine zaka zo kana bani wannan muguwar shaawar akan mace Kai maza kabace a idona

Jiki nabari yabar wajan

Finah na gefe du abinda yafaru tsakaninsu akunnanta da I danta ga taji labarin auran da yayi kishine ya rufeta afili tace in dai Ina raye nabil se kazama nawa se mun koma Abu Daya da Kai muzuba mu gani Ni da kai

Shatuwa ce kwance Kan makeken gadan nabil tana ta kuka idanta ya kunbura sosai sabo da kuka

Amina ce Tai sallama ta shiga tace kanwata har yanzu kukan kike tayi Baki hakuraba nanmafa gidane Babu abinda ze sameki kinji Kuma bawani dadewa zakiyiba za a Mai da ki wajan iya Kuma naji baffah na cewa da iya zata dawo Nan gidan gaba Daya da Zama saboda ke

Murna shatuwa ta fara tace dagaske kike

Kai Amina ta daga Mata

Nan Amina tasamu tafara janta dahira har tasaki jikinta Nan tasamu ta fara yi Mata tambaya Akan karatu

Shatuwa tace nifa Babu wata makaranta da nake zuwa iyace makarantata itace me koya min karatu Kuma iya tahana asani ako wace makaranta Dan bataso adakeni Nima Kuma banasan karatun Bari na biya Miki abinda iya ke koyar Dani kiji

Kema Kya karamin daga in da na tsaya

Biya Mata tafara ai ko nisa batayi da shirmen karatun taba Amina ta tsaidata tace ya Isa Haka shatuwa kinaso kema ki zama Yar birni Kuma Yar gayu kamar Yan matan garinnan ko da yake ban kaiki yawo Kinga yanmatan garinnan ba da sun birgeki sosai to kalarsu nake so ki Zama Zan sa akawo Miki me akoya Miki karatu daga na boko har na isilamiya Nima Kuma in nazo Zan na koya Miki Amma yanzu ki ajje karatun iya da ta koya Miki agefe har ki iya Wanda zaa na koya Miki kinji kanwata

Tace to ke ya zan na kiranki dashi

Tace anty Amina su nana yanzu abinda nakeso da ke wanka nake so muje na hada Miki ruwan da kaina kiyi muga kitsan kanki

Shatuwa na bude gashin kanta

Mamaki Amina ta fara yarinya me gashi Amma saboda rikwan iya ce ita kitsan kanta ya dankare ko tsagar kitsan baagani gawata uwar kasa akanta

Amina tinani tafara azuciyarta tafara mgn tace gaskiya da matsala yanzu Kai nasa ta budemin nagani to Kuma sauran wajanfa ga yarinya kyakkyawa Amma rashin kula yasa kyanta yabuya da zata yarda in na tsefe Mata Kai wlh dada kaina Zan Mata wanka yau dai Daya nayi Mata du abinda yadace na Kuma nuna Mata yanda zatana yi gaba yanzu yanda Zan Mata ta yardar ne matsalar

Zama Amina tasa shatuwa tayi ta tsefe Mata Kai tashiga bandaki tahada Mata ruwan wanka shima se da takirata tahada komai agabanta takuma nuna Mata du abinda yadace saboda gaba in zatayi tace yau komai Ni Zan Miki da kaina gashin kanki Zan Fara wanke Miki daga baya maje gidan gyaran gashi agyara Miki shi nifa yau ni zan miki wanka da kaina kinji

Shatuwa kitayi tadai yarda ta wanke Mata gashin Kanta lfy se da akazo wanka da gyaran jiki da du inda yadace aga Babu gashi da kazanta jikin mace shatuwa Taki yarda Dakar da rarrashi ta yarda Amina Tai Mata du abinda yadace ta Kuma nuna Mata kalar du wani Kayan da mace in tatashi wanka zata na anfani da shi da Kuma to du inda yadace aikuwa Amina bakaramin wankar shatuwa tayiba ta wanketa tas sannan ta barta Shatuwa se runrufe kirji ake abinma dariya yabawa Amina ganin ita kirjin tafi damuwa dshi

Suna fitowa shatuwa tasa hannu tarufe Ido tasa dariya tace wlh kunyarki nake ji anty Amina Kuma fa naji Dadi ako Ina na jikina sakayau nake jina ga wata iska me Dadi nashiga jikina nifa amazagai bana wani wanka sosai Kuma iya bata min fada Kuma fa Ni banasan kitso wlh

Amina tace ai Dole kice bakyasan kitso Daman ku Masu gashi bakwaso ataba muku Kai du wannan me saukine akwai inda Zan na kaiki ana wanke Miki gashi agyara Miki akai akai Kinga Babu mgnar yin kitso se haka in kina so wataran se ana miki Kuma mu anan wanka kullin akeyinsa safe da yamma da yammanma anfiso in Zaki kwanta kiyi inma sansamune Ni kullin sau uku nake so kinayi kinji kanwata zakifi Kyau da kanshi har maganar wanke Baki shima du yanda nakoya Miki da yanda nagaya Miki zakinayi kullin haka nake so kinayi Kinga yanzu kin Fara Zama Yar gayu Kuma Yar birni yanzu Kinga du yanda na koya Miki yanda Zaki shafa wayannan Haka zakiyi Banda kwalliya me yawa kinji kishirya inkin Gama kizo bangaran su mommy muyi Hira Kan natafi gida Kuma ko natafi akwai mommy zata nuna Miki du abinda Baki saniba Nima Kuma zanna zuwa wajanki akai akai muna gaisawa natafi Ina jiranki

Shatuwa Zama tayi tashafa du abinda Amina ta nuna Mata kamar abin arziki bayan tagama tadau jambaki da Hoda da jagira tazuba wata kwalliyar hauka itanan tafara Zama Yargayu kayan da Amina ta kawo Mata tace tasa su tasa wasu riga da siket ne na atamfa sunyi Mata Kyau sosai sun karbi jikinta abinda yabata kwalliyar fuskarta tsayawa tayi gaban mudubi tajuya takuma juyawa wani Dadi yakamata

tace Yasin du Wanda yaganni yau seya hargitse saboda mugun kyan da nayi

Amina tana shiga falan tasamu Hajiya Fatima azaune

Hajiya Fatima tace Amina ansamu ta hakuran ko har yanzu kukan take Allah yasa kinfara naki aikin

Amina tace eh ta hakura Kuma nafara aikina mommy ammafa akwai matsala sosai wlh yarinya kyakkawa Amma iya ta cuceta tabarta ba ilimi tana zaune cikin jahilci in kinji yanda mukayi da ita wlh se takaici yakamaki in yarinyarnan tagyaru wlh yarinya kyakkawa zaayi Kuma nabil seya rude Akan Santa se yasota sosai wlh Allah dai yabamu saa

Suna cikin hirarsu nabil yashigo ko sallama Babu bare gaisuwa yanemi waje ya zauna Yana kallan kofar shigowa yawani hade Rai kamar bega mutane awajanba

Hajiya Fatima tace Allah yakyauta Allah yashiryeka nabil Dan Allah yaushene zakayi hankali yaushene zaka Fara jin fadan da nake maka Akan sallama da gaisuwa yanzu kashigo Mana ko sallama Babu bare Musa ran gaisuwa Kuma me yakawoka wajena ko kamanta kana da Mata kamanta yamukayi da Kai jiyako tin wuri katashi katafi wajan matarka tinkan nakira baffah na gayamasa me kake niyar yi

Nabil yace haba mommy meyasa baka Sona yaushene Zaki Fara Sona kamar yanda sauran iyaye Mata suke San yaransu Dan Allah yaushene Zan samu kauna da kulawa awajanki yaushene mommy yanzu Dan Allah kin goyi bayana auran kandarar da akayimin na mara hankalin yarinyarnan da ita da kakarta Mara mutunci na tsaneta na tsaneta bazan kwana gu Daya da itaba

Hajiya Fatima tace nabil nikuwa nake sanka Kuma nake kaunarka Ni nake so kagama da duniya lfy nabil Babu uwar da zata haifi da a cikinta tace bata sanshi nabil kowace uwa burinta taga Dan da ta Haifa Yana hanya madaidaiciya hanyar da zata kaishi aljana Amma nabil kaki ganewa nabil kullin inamaka addu'ar shiriya Allah yashryeka Allah yaganar min dakai gaskiya kasan irin San da nake maka Kuma insha Allahu nasan Allah natare Dani Kuma ze cikamin burina ya amshi addu'a ta akanka har yanzu inasa ran zaka Zama yanda nake so na ganka insha Allahu nasan Kuma lokacin zakasan gaskiya nake fadamaka


Fitowa tayi zuwa bangaran Hajiya Fatima tana wata irin tafiya abin dariya ita adole tazama Yargayu du Dan aikin da yaganta na gidan tazo shigewa ta gabansa seyayi dariya aboye

wani daga cikin Yan aikin yace Allah kenan abinda kake wulakantawa arayuwa nabil Daman wataran se kunyi rayuwa tare Kai da kake wulakanta mutane musamman Mata gashi yanzu abin dariya kuga wanta ya aura azaman matarsa ai wannan tsohon arzikin yaburge Ni wlh

Dariya sauran sukayi Daya daga cikinsu yace ku dai yi ahankali Dan wlh kunsan Yana ciki bedade da shigowa ba Kuma kowa yaga yanda yake tafiya yasan ransa abace yake Babu ruwana

Hajiya Fatima na Kan yiwa nabil nasiha Sega shatuwa itama tashigo tana wata tafiya tana karkada idanu itama tashigo Babu sallama tanemi waje ta zauna irin zaman da nabil taga yayi yadora Daya Kan Daya itama shi tayi tana ta hura hanci ita ala Dole tahade Babu Wasa daga Hajiya Fatima har Amina kallan shatuwa suka koma yi

Hajiya Fatima tace ohh Ni Fatima du gautan jahne daga mijin har matar lanlai akwai aiki

Nabil Kare Mata kallo yayi besan lokacin da dariya ta kwasheshi yace tofa abin nayine Dan Kauye yashigo birni ba lfy se ya warke Dan Allah kiga wata kalar kwalliyar mahaukata Wai kenan gayu kikayi anan kenan gani kike Wai ke macace ko ahakan Allah yakyauta gaskiya baffah ka cuceni ka gama da Ni Wai arasa Wanda Zan aura azaman matar aure se wannan akuyanlen kuga wani kwalliya kamar anyiwi akuya kwalliya wlh bazan taba Sankiba kome Kika Zama aduniya na tsaneki bana san ganinki adalilinki da wannan tsohuwar na dada tsanar Mata aduniya

Tashi tsaye shatuwa tayi tadaka tsalle taje gaban nabil ta tsaya ta rike kugu tace Nima kamar yanda kake fada ka tsaneni Nima Haka na tsaneka ko ganinka bana san yi da idona kafara yiwa kanka dariya kafin kafara yiwa wani kaifa me shigar Kayan Mata dandaudu matamaza rabi mace rabi namiji adalilinka na rabu da iya me kaunata karabani da ita Ina ji Ina gani ta Ina Zan soka har naso Zama da Kai yasin baka isaba Kar Kuma ka kaini bango Dan wlh akwai abinda na dauko tin daga mazagai saboda Kai Dan na koyamaka hankali karka Bari nafara ma anfani dshi Dan yanda kabarni da jiyar hannunna kaima se na wahalar da Kai kaji jiki kamar yanda Nima naji wannan alkawari nane Ni bana yafiya Kuma bana manta ranar daukan fansa ga du Wanda ya tabani Dan Haka kabi ahankali kashiga hankalinka

Nabil tashi yayi yadauke shatuwa da wani gigitancan Mari me zafi yakuma dauketa da wani lokaci Daya tafara ganin duhu hannu yasa ze Kama hannunta me karaya dasauri hajiya Fatima Tai maza tarike Mai hannu se wani huci yake Dan bacin Rai

Yace mommy Dan Allah kibarni na karasa ragargaza hannun Naga me zatayi ita da kakarta kinafa ji mommy irin kalaman da take fadamin baa Mai damin da mgn baa Kuma yimin rashin kunya baa nunani da yatsa ban karyawa mutun hannuba Dan Haka kiki,yaye ko Dan gaba ki fita harkata har murabu Danni bazan iya Zama dakeba rikwan tsohuwa kazama kawai yau zanga yanda Zaki zo kice za mu kwana daki Daya wlh da yau sekinyi Dana sani arayuwarki

Shatuwa neman abin ramawa tafara yi da sauri Amina tazo takama hannuta tajata dakar suka bar falan Dan taurin Kai irin na shatuwa ko alamar hawaye

6 / 12