kuwa da kayan d'akinta na yanzu Bilkin ce ta yi mata su sabbi Sai dai ai Basu kama k'afar wanda aka bata ba yanzu.
Kafin ta tafi Bilki ta ja ta d'aki ta fad'a mata zata yi aure a cikin sati mai kamawa ta taya ta da addu'a. Farinciki har cikin ran Alawiyya don kuwa bata yiwa uwardakinta sha'awar yin kome. Ta dinga yi mata addu'o'i masu sanyaya zuciyata tare da sake yi mata alkawarin matuk'ar tana cikin garin Katsina to Faruk da Amrah suna da Yaya tamkar uwarsu d'aya ubansu daya zata kula da su irin yadda ta kula da ita. Hankalin Bilki ya sake nutsuwa don kuwa ta gasgata Alawiyya. Ga su Faruk sun sake bada shaidar ba abin da bata yi musu.
Suka yi sallama suka rabu cikin sanyin jiki da fatan alheri.
*Na ce kina yiwa masu aikinki adalci da sassauci kuwa?*
*Ba ki san ta yadda zasu taimake ki a gaba ba. Kowanne dan adam akwai ranarsa, da ace Bilki bata yi mata adalci ba, da bata kular mata da yaranta a lokacin da babu idonta a kusa ba*.
Sai da daddare bayan sun kammala cin abincin dare tuni kuma Farha ta yi barci.
Ita da Alti suka faɗawa yaran batun auren da zata yi. Dukkansu yaran jikinsu ya mutu ba karsashi suka ce "Allah ya sanya alheri".
Amma k'asan zuciyarsu sun ji wani iri shike nan ta bar gidansu da dadynsu for ever?
Murya ba amo Amrah ta ce "Mahmah waye shi sannan a ina za ki zauna?"
Ba walwala ta ce "Uncle Asad ne sannan a Abuja zan zauna".
Amrah ta yi shiru ta rasa me take ji a ranta. Amma dai zuciyarta sai ayyana mata take yi mai kudine fiye da dadynsu amma kuwa Babansu ya fi kyau yafi kirki tunda shi ba ya dariya.
Kafin ta ce wani abu Faruk ya ce "Mahmah uncle police wai?"
Kai kawia ta daga masa tabbacin eh.
Ya rik'o hannunta ya ce "Amma takwarana ya fi shi kirki da kyau Mahmah".
Murya ba amo ta ce "Ba kyau na duba ba, sannan haka k'addara ta zaba mini kawai ku dinga yi mini addu'a".
A sanyaye suka ce to don hatta Faruk da yake ganin gara ta tafi inda ba zata dinga kuka ba, batun auren nata ya yi awon gaba da kuzarinsa. Wato kishi bala'i ne, ba ga yara ba, ba ga manya ba.😄Ba ga mazan ba, bare kuma mata masu duniya. Allah kasa mu wanye lafiya.
Washegari suka bar Katsina wanda su Bilkine suka kai yaran gidan Alawiyya akan da yamma su wuce gidansu tunda da sassafe suka tafi a dalilin zasu tsaya a Kano wajen Yaya Hamida.
Suna nisa da Katsina kewar ya'yanta na sake kama ta. Akan dole ta yi hak'uri mussaman da yara basu tayar da hankalinsu sosia ba, amma dukkansu sun yi kuka.
Haka Farha har suka kusa isa Kano kuka take yi akan a barta a wajensu ba zata koma Abuja ba. Sai da barci ya sure ta sannan ta yi shiru.
Taran safiya a gidan Yaya Hamida ta yi musu, suka karya sannan suka shiga daki Bilki ta sanar mata batun aurenta da Yaya Asad.
Take Hamida ta fara kuka tana fad'in tabbas na huce dan ke na ji wa'azi akan illar gaba mussaman ace jini guda ke yin ta. Amma ki sa ni sai da kwakkwarn dalili za ki ga k'afata a gidanki. Me za ki yi da wannan mugun marar mutunci dattijo da shi zai dage sai ya aure ki. Allah ne ya rufa miki asiri bai lalata ki tun kina yarinya ba, masu kakin nan fa kad'an ne na kirki amma wominzers ne na k'arshe. Ai ni tunda bai zo ta'aziyar uwarmu ba, sannan ya daurewa yar iskar Abidan nan gindi akan Yaya Sulaiman Wallahil Azim ba ni ba shi. Dan haka soyayyar da zan nunawa ya'yanki sai na nunawa su Amrah da Farha amma nasa kam kadaran kadaran hakan ma saboda ta jikinki suka fito." Save Restricted Contents Bot, [Sep 12, 2025 at 22:17]
Hawaye a fuskar Bilki ta ce"Ni ma ba sonsa na ke yi ba, Yaya Faruku ne ya matsa mini amma ko Baba ma ce masa na yi bana sonsa".
Yaya Hamida ta ce "Ni dai tunda kun shirya ke da su ba zan ce komai ba, amma ki sa ni Wallahi mu ba ruwanmu da su mussaman ma Asad mugun mutum mai bak'ar fuska da zuciya.".
Kan dole suka goge idonsu suka yi hirar sannan aka yanka cake din d'iyar Hamida ta biyu wanda ranar take yin birthday da sai yamma za'a yanka amma Saboda ayi hotuna da su Bilki da Farha aka yanka a lokacin.
Duk da Bilki harkar snacks ta k'ware Sai da ta tambayi wacce ta yi cake din tare da su samosa da springrols saboda dad'insu sannan da aka fad'a Mata Farashin sai da ta jinjina tare da karɓar lambar dan ta had'a ta da kawayenta na Kano da suke ta fad'in har yanzu basu samu wacce ta iya snacks irinta ba.
Deenah cakes and more -Kano
09038055790
IG @Deenah cakes and more
Snacks such as :
Birthday cakes
Cupcakes
Samosa
Springrolls
Meatpie
Frozen snacks
Event snacks.
Sai azahar sannan suka kama hanyar Abuja bayan Yaya Faruku ya azalzale su.
Shi Yaya Faruku har yanzu ba wanda yake fishi da shi tunda dama tun filazal na kowa ne.
Sai dare sosai suka isa gida.
Kushen Yaya Hamida akan Asad ya sake tsananta kinsa a zuciyarta sai dai ba zata iya ce wa ta fasa ba tunda ta ce ta amince, amma gabad'aya abin ya sake fita a ranta.
A daren ya k'irata yafi sau biyar bata daga ba ya damu k'warai. Haka da safe. Yayin da ita kuma zuciyarta ce ke ta yi mata rawa tare da wasiwasin ta zazzage shi kawia ta yadda zai hak'ura da kansa. Amma ko kusa ba zata iya yin haka ba tunda ta samu tarbiyar girmama babba tunda ga tushe.
Washegari k'arfe sha d'ayan safiya a gidan ta yi masa. Sanye yake cikin tsadadden farin yadin filtex.
Ya shiga falon ciki ya gaisa da iyayensa suka dan taɓa hira akan tafiyarsa Lagos. Bai wani jima ba ya fito ya dawo falon farko ya zauna. Daidai lokacin Amal da Noor tare da Farha suka fito suka nufe shi suna yi masa oyoyo. Ya d'an biye musu ya basu alawowi da cookies kowa ledarsa daban.
Noor ta ce "Dady yaushe zaka d'auke mu koma gidanmu?"
Ya jata jikinsa ya ce ki k'ara hak'uri, ba na ce miki yanzu Mahmah itace mominku ba?"
Ta daga kai.
"Good idan muka yi tafiya muka dawo zamu zo ni da ita mu d'auke ku har da Farha mu koma gidanmu gabadaya ".
Amal da tafi wayo ta ce"Shi ke nan sun zama y'an gidanmu?"
Ya ce "Haka nake nufi my Amal".
"To amma Dady Ammie da junior fa?".
Ya ce "Su anan zasu zauna kafin dadynsa ya dawo ya dauke su suma.
Murna ta kama Farha jin zasu koma tsalelen gidansu Noor ya zama nasu.
Ya ce "To ku je ku shirya yanzu lesson teacher dinku zai iso.
Ku faɗawa Mahma ta zo ta karbi sweet dinta tunda Ammi na hospital."
Suka tafi da sauri dan faɗawa Bilki sak'onsa da kuma dauko jakunkunan karatunsu.
Ya jima a zuane yana dakonta. Amma bai kosa ba mussaman da yake ta amsa waya daban daban.
Can ya ji fitowar yaransu suka wuce shi suna fad'in bye dad don suna ganin kafin Su kammala ya tafi.
Sun jima da fita kafin ya jiyo takunta hadi da k'amshin turarenta.
Cikin nutsuwa ta zauna a kujerar da take fuskantar wacce yake zaune.
Kanta na k'asa ta ce "Ina yini?"
Ya amsa da fad'in lafiya but not fine! Kin rikita mini tunanina Maigado! Me na yi miki, me ya faru kika daina daukar wayata sannan komai ya zo bakinki sai ki fad'a mini kai tsaye. What's going on?"
Ya tambaya a rude.
Kanta na k'asa bata yi magana ba.
Ya zuba mata ido ya ga gabad'aya ta yi wani iri babu kuzari a tare da ita.
Ya tabbatar zuwanta Katsina na kan gaba wajen sauyawarta.
Ya tausasa harshe ya ce "Maigado!
Bata motsa ba bare ta amsa.
Ya numfasa ya ce "Ya su Faruk junior?"
Murya ba amo ta ce "Suna lafiya Alhamdulillah!
Ya gyara zama ya ce "Ki ba ni lambar Babansu na roke shi ya ba ni su na sanya su makaranta a nan".
Ta d'ago a hanzarce don maganar ta zo mata a bazata, har cikin zuciyarta kuma ta ji dad'in hakan. Save Restricted Contents Bot, [Sep 12, 2025 at 22:19]
A sanyaye ta ce "Na gode sosai amma Babansu ba zai bada su ba, suna karatun ma a can".
Ya dan ji dad'in ganin yadda ta dan fara warewa.
Ya ce"To kuwa da zarar sun kammala sakandire dolensa ya bada su don su shiga manyan jami'o'i. Babbar ta kusa kammalawa ne?"
"A a da saura yanzu ma shiga aji biyar(s.s.2)."
"To ai kamar yanzu ne".
Faruk so nake ya yi b'angaren likitanci. Ai yana da kokari ko?"
Ta murmusa tare da fad'in "Wannan Yayan nawa ai sai a hankali ban san zuwa gaba ba. Amrah ce hazik'a irin Abida!
Ya yi maza ya ce"Ma sha Allah! Da ikon Allah kuwa zata yi karatu a d'aya cikin best universities da ake ji da su a duniya".
Da walwala a fuskarta ta ce"Allah ya ida nufi".
Haka ya dinga yi mata hirar yaranta nan da nan ta warware suka yi hira irin wacce basu taba yi ba.
Ganin ya shawo kanta ta ware ya sanya ya yi mata sallama ya tafi bai yi mata maganar soyayya ko aure ba.
Sai da daddare suna waya ta ce "Baban Bilkisu ko za'a bari auren nan sai ka dawo daga tafiyar da zaka yi don gaskiya ni bana son tafiyar".
Zullimi ya yiwa zuciyarsa k'awanya ya ce"Ki yi hakuri kin ji ai ba dadewa zamu yi ba."
Ta yi shiru tabbacin bata yarda ba.
Ya ce "za'a daura auren juma'a mai zuwa ba za'a sauya ba. Zan nemi wajen aiki su tura wani zuwa kwas din, gwara na rasa k'arin girman da na rasa ki Maigado ".
Murya a mak'oshinta ta ce"Ni gaskiya ka tafi, idan ka dawo a daura. Tsakanina da Allah jibi ya yi mini kusa da yawa"
Yana kwance ya zabura ya zauna a tsakiyar gadon.
A kidime ya ce "Saboda me Maigado, me ya faru, me ya canja miki shawara haka? Dan Allah kada ki zama mai yin magana biyu. Allah ne shaidar yadda nake son ki nake tsananin son na aure ki, ba kya jin tausayin zamana haka Maigado? Fad'a mini me na yi miki da ya sanya kika sake shawara?"
Ya yi mata tambayar cikin rarrashi da kwantar da harshe.
Ya bata tausayi ainun. Amma duk da haka ta ce "Gaskiya Baban Bilkisu baka son y'anuwana duk cikinmu da ni kawai kake yin mu'amala mun sake gane hakan ne da Mami ta rasu ba ka zo mana ta'aziya ba sai ta waya, wayar ma a layin Baba ka k'ira aka hadaka da ku, idan ma baka k'asar da gaske me ya hana da ka dawo baka zo mana ba?"
Sannan a matsayinka na babba baka tsawatarwa Abida ta koma d'akinta ta zuaan da mijinta lafiya tunda bai yi mata komai ba, sai ka zuba mata ido saboda kawai baka son Yaya Sulaiman ".
Ya yi shiru ya kasa ce mata komai amma gabad'aya kansa ya kulle. Ya nisa ya kasa furta kalma ko guda don ya tabbatar zuwanta Kano Hamida da sauran suka soki lamarin aurensu tare da gabatar mata da hujjar da ita a da bata gano su ba. Ya yi imanin kitsa mata wadannan kalaman aka yi don da ta k'ulla ce ba zata zo masa ta'aziyar Rukayya ba, tunda kaf ya'yan Baba k'arami ita kad'ai ce ta zo masa ta'aziyar Sai Saddiqa Wanda ya tabbatar ita ta matsa mata suka taho tare, amma ko Ansari waya ya yi masa duk da shi su na d'an gaisawa jifa jifa.
Murya ba amo ya ce "Wallahi Billahi Maigado bana k'asar nan mami ta rasu. Sai da aka yi watanni biyu da rasuwar kafin na dawo. Ba wai dan ina jin haushinta ko dan ina fishi da ku ba ne. Dan Allah ki yarda da ni. Batun Abida kuma kowa da nasa kason na laifi da mu, da ita, da shi Sualiman din da ya gudu. Shi ma da ace Baba k'arami na da rai bai isa ya yiwa Baba Babba fishi irin haka ba. Ni yanzu ba tone tone zamu yi ba. Don kuwa Abidan da kuke ganin mun zuba mata ido ai a cikin nadama take mai tsananin gaske. Kada mu saka matsalolin gidanmu akan lamarinmu Balkees pls. So nake al'amarinmu ya yi tasirin da zai zama tsananin sulhu da afuwa a tsakaninmu. Yanzu ba kya tunanin irin murna da farincikin da Baba Babba yake ciki a kanmu, kin ce masa kin amince sai kuma ki dawo ki ce kin fasa? Yayanki Faruku yana ta rawar jiki da farincikin kin yarda ya isa da ke, sai kuma ki watsa masa k'asa a ido ki kunyata shi? Ki yi hakuri, in sha Allah sai na zame miki alheri, sai gidanmu ya dawo tamkar yadda muka taso muka ga iyayenmu sun kafa Shi, hakan kuma ba zai yiwu ba sai kin ba ni hadin kai, kin yi hak'uri kin jure duk wata gutsuri tsoma. Save Restricted Contents Bot, [Sep 12, 2025 at 22:22]
Sannan duk inda Sualiman yake da ikon Allah zai dawo cikinmu ya rayu da mu, zan yi kokarina ya dawo gida, don kuwa tabbas ban ji a jikina ya rasu ba."
Jikinta ya yi sanyi ainun. Ta rasa yadda zata yi a kan dole ta ce "To".
Ya dinga yi mata godiya har ta ji wani iri. Don sai ya bata tausayi yadda ya kwantar mata da kai tamkar ba babban dan sanda ba.
Ganin ya shawo kanta ya sanya ya ce "Bari na bar ki, ki yi barci Maigadona, zamu yi magana da asuba in sha Allah stay blessed and I do luv you my dear. Save Restricted Contents Bot, [Sep 13, 2025 at 12:55]
Daga haka ya katse wayar ba tare da ya jira amsawarta ba.
Sai da ya yi matuk'ar tura sako mai nauyi a zuciyarta kalaman nasa sun saka ta cikin nishadi da nutsuwar hakura ta karbe shi a matsayin mijinta. Ta yi shiru tana tunanin yadda zata kasance a matsayin matarsa.
Yayin da shi kuma ya kasa kwanciya. Tabbas da aiki a gabansa tunda a bayyane k'arara iyalin Baba k'arami suke gaba da shi. Sannan dukkan fishinsu akansa suka d'ora. Zai yi komai dan ya auri Bilkisu don hakan ne kad'ai hanyar da zai daidaita Shi da su dari Bisa dari don Idan tana hannunsa dolensu su yi mu'amala da gidansa sabanin Idan watace ko da sun shirya ba lallai su zo gidansa ba, sai da kwakkwaran dalili.
Da k'yar barci ya sure shi. Da asuba yana idar da salla ya k'ira ya dinga tarayyarta da rarrashi da maganganu masu nauyi kafin ya k'yale ta bayan ya tabbatar jikinta ya tsumu da manyan kalamansa.
A daren ranar Baba ya sake zama da Asad tare da Farouku.
Ya kaurara murya ya ce "Na yi magana da Bilkisu ta kuma ba ni tabbacin ta amince da batun aurenku! Amma ka saurare ni da kyau. Duk cikinku kai ne babba, ba sai na maimaita abin da ya faru na rikicin da ya gitta a tsakaninmu ba. Na yi faricinciki da Ubangiji ya k'ulla wannan alherin a tsakaninka da
kuwa a duniya ba abin yake saurin yafe gaba irin auratayya. Yana daga cikin dalilan da Annabin Rahma ya auri mata daban daban daga kabilu mabanbanta, duk kuma kabilar da ya auri y'arsu gab'ar da suke yi da musulunci tana zagwanyewa.
Dan haka ka yi iya k'ok'arinka ka daidaita zumuncinku da ya yi rauni da y'anuwan Bilki. Ka buda musu k'ofar da zasu zo gidanka su sake, haka nan ka yi atiya kokarinka wajen ganin kun sake hadewa kuna zumunci ko da bana raye. Sannan ka cigaba da bincike akan Sulaiman. Kana ganin dai yadda Abida take zaune bata kaunar ayi mata maganar ko zata yi gaiba, a haka ta kwashe shekaru kusan hud'u babu shi, babu alamarsa ga ya'yansa nan basu san shi ba!
Baba ya yi shiru a dalilin kuka na neman kubuce masa.
Sai da Asad ya dinga ba shi hak'uri sannan ya dan nutsu.
Ya numfasa ya ce "Bilkisu ta ce 'Na sanar maka da d'iyarta d'aya zata zo gidanka da kuma Alti.
Mamaki ya kama shi ya murmusa ya ce "Baba ka fad'a mata idan wad'anccan na Katsina ma Babansu zai ba ni to ta zo mini da su zan rikesu gabad'aya".
Sai Monday Kuma in sha Allah.
*Surayya Dee,*
[10/3, 4:03 PM] Mrs awwal 🫶💍💛: [Sep 15, 2025 at 09:44]
Yake furzarwar da k'arfin gaske wanda ya ja hankalin Hawwa da take samanta wanda itama ta ga sanarwa tunda ya koya mata kallon labaran k'asa.
Amma Amrah da Faruk tuni suka yi barci dan haka basu ji hirjinsa ba.
Gulma da son ganin halin da yake ciki ya sanya Hawwah gangarowa a sukwane.
Sai dai yanayin da ta ganshi yana ta sa'a'i tare da suratai ya yi matuk'ar sanyaya mata jiki don kuwa muraran tashin hankali da yake zuciyarsa ne ya bayyana masa a gangar jikinsa.
A sanyaye ta ce "Baban Amrah nutsu ka zauna mana kada ka fadi ka hadu, da jinya fa".
A matuƙar gigice ya ce "Idan har irin wannan suyar mata suke ji idan mijinsu zai ƙara aure to la shakka sun cancanci a yi hak'uri da su a kuma rarrashe su iyakacin rarrashi. Hawwah so nake na mutu ko na huta da azabar ciwon da k'irjina yake yi mini. Da ace nasan haka Bilina ta dinga jin radadin aurenki da na yi a zuciyarta da ban auro ki ba,