Auran Wahala Ko Saki Complete

Author :  Ayshakhair Category :  Love

Chapter   5 / 13

12K to 15K   out of 37.6K words

typing gbe๐Ÿค—
[6/17, 8:32 PM] .: ยฎeal pure moment of life writers


๐Ÿ˜ฐ๐Ÿ˜ญ AUREN WAHALA KO SAKI?! ๐Ÿ“๐Ÿ˜ญ๐Ÿ™†๐Ÿผโ€โ™€


( Story base on fictional writing๐Ÿ“)

MALLAKAR AYSHKHAIR ๐Ÿ’—

WRITTEN BY AYSHKHAIR

Page 29&30๐Ÿค—


Da sauri taje kitchen ta d'auko ruwa Mai sany'i a fridge sannan tafito da hanzari ta kwaramai a fuska sai da yakai kusan 10mns sannan yaja wani dogon lumfashi sannan ya bud'e idanunsa a hankali ya saukesu akaina danake kwance Babu motsi da hanzari yamiqe Yana Mai fad'in Aymanah!

Hajia mabaruka tayi saurin riqeshi sannan tace:

"Mubbashir wacece ita Wai?"

Kallonta yayi sannan yace:

"Hajia Aymanah ce matata "

Zaro idanu tayi tace:

"Matarka Mubbashir Mai sameta en fashine suka shugo gidan?"

Girgiza Kai yayi tamkar wani yaro yashiga girgiza Mata Kai hawaye na bin kuncinsa sannan yace:

"Hajia nine na sanyata cikin halin Nan ......

Nan yavata labarin duk abinda yafaru riqe baki kurum hajia mabaruka tayi sannan ta nisa tace:

"Mubbashir angayama kishi Kuma haukane? Kai dabban wani garine zaka gayama Aymanah asalin labarinka?Kasan kuwa boko jatau yace mun duk sadda ka furta Mata asalinka daga ranar asirin da aka Mata da kulle bakin iyayenta da'akayi zai karye ko? Kuma zaka soma fuskantan qalubale kalakala Koh? Kasan Aymanah ko mujima ko mu dad'e Boka Jatau yace auranku zai rabu ko? Inkuma Bai rabuba cikin ku akwai Wanda zai mutu ko? Gashikuma bisa dukkanin alamu Aymanah Bata da sauran rain tattare da ita!sannan Boka yace zata haskaka a duniya Kuma Wanda zata aura Nan gaba zai sota tamkar ransa Kuma shine zai iya Zama ajalinka! Amman Kuma Mubbashir kayi wauta wlh Kai saikace abuge kake dazaka gaya Mata asalinka yooo ko abugen kake kasoma gaya Mata waye Kai? Eh? Ina tambayanka?!


Mubash Wanda tun sanda Hajia tasoma bayani shuru yayi Yana nazarin maganganun ta kasa cewa komai yayi sai dai ya qudurci anniyyan inhar Aymanah ba mutuwa tayi ba inhar ta farka tasoma nunamai qiyayyah sai ya gasata sai ya mayarmata da rayuwanta cikin qunci da baqin ciki, sai ya tozartata yadda ko auransu ya rabu Babu namijin da zai so ya aureta sai ya nakasata! Wannan shine shawaran da Mubbashir ya yanke akaina! Baice komai ba yabi ta bayan Hajia ya zo daf Dani ya d'aukeni yayi mota Dani sakani a gidan baya yayi Wanda kafun ya saninma cillani yayi ciki ya shiga drvn side yaja motar da gudu yabar layin gudu yakeyi sosai kaman Mara hankali har muka Isa asibity da sauri yasa likitoci suka amsheni aka shiga emergency Dani Dan ceto Raina!


Mubbashir yafi qarfin awa d'aya dai safa da marwa yakeyi Amman shuru kakeji Babu likitan da yafito chan Kuma d'ayan gefensa maganganun Hajia mabaruka ne kawai ke kwany'a a kwakwalwansa!

Kaman daga sama yaji an tab'a shi da sauri ya waiga Dan ganin waye, Dr Abdulmalik ne yad'an sakan ma mubash murmushi sannan yace kabini office Dina!

Sumsum mubash ya bishi sannan suka shiga suka zauna likitan yad'an kalla mubash sannan yace:

"Ya'akayi hakan tafaru?"

Kallonsa mubash yayi sannan ya sadda Kai yace:

"Nima bansaniba dawowa nayi na isketa a hakan pls Dr howz she?"

Dogon lumfashi likita yaja sannan yace:

" While duk ma Wanda ya Mata wannan aika aikan shida Allah Kuma zaiga saka mako!

Da sauri mubash ya kallesa Dan sanin kodai likitan yad'ago shine yasan shine ya aikatama Aymanah hakan? Kafun ya baiwa kansa amsa yaji likita nafad'in:

"Babu abinda yafi qarfin Allah, Kuma thank God ka kawota asibity da d'an wuri da Kun qara 2hrs Baku kawota ba da saidai nace am sorry she will be gone forever! Amman dake kwananta na gaba Allah yasa munyi nasaran ceto ranta saidai am sorry to say we lost d child munyi iya k'ok'arinmu wajen ganin babyn is save Amman Allah baiyiba so tayi miscarriage Wanda babyn is just for 1wk Dole yasa muka Mata wankin ciki gudun Kar taqi samun wani Juna biyun Nan gaba"

Mubasshir tsuru! Kawai yama likita Yana sauraransa ,


Babu abinda yake tunani sai cikin da akace Aymanah nadashi Kuma ya zube toh Ina kwayoyin da yake samata kullum acikin juice ya Bata Tasha kafun sun kwanta?basa aikine komai? Ganin hankalinsa baya wajensa tuntuni likita ke magana Amman bisa alamu baijin komai yasa likitan ya tabashi, da d'an sauri mubasshir ya kalla likitan sannan cikin in'ina yace:

"Cii... Cii.. ciki fa kace fa likita?!

Da d'an mamaki Dr Abdulmalik yace:

" Eh ko batada aure ne?

Tsaki mubash yayi sannan yace:

"Tana da shi Mana ni kawai ban shirya Zama uba bane ammm likita babu yadda zaayi amata alluran daina samun shigan ciki kwatakwata? Ne ?!

Dr zuba Mai many'an idanunsa yayi har Yana cire tabaran idanunsa Yana mamakin mubash dama haryanzun akwai mutanen da basa son haihuwa? Dama akwai su har yanzun? Baya mantawa jiyannan wata Mata da mijinta sukazo suna kuka shekarunsu 10da aure Amman Basu da haihuwa ko d'aya Kuma dukkaninsu lafiyansu Lau Haka yabasu haquri har matan tace abata yaran marayu tariqe suka tafi da Yara biyu Amman Wai shi wannan gashi yasamu Amman Kuma yake cewa a hana matar sa haihuwa baki d'aya wannan Allah yasan abinda yagani ne yasa cikin nata yazube da qilan ya tozarta matar tashi dakuma yaron Kai kaicho da wannan mutumin! Fad'in Dr Abdul Amman a fili sai yace;

"Ammm malam jimana! Dan Allah kana da hankali kuwa? Ko ancema ni nayi Kama da likitocin dake sab'ama ubangijin sune? Ko Kuma ancema anan asibityn ana cutar da mutanene?kagan tun wuri kafun na Kai qaranka wlh kacire wannan qudurin a ranka Yama zaka ce Wai azubda cikin matarka ! A hanata samun shingan ciki kwatakwata Anya kanada karatun addini kuwa? Toh ba daniba yimaza ka ficemun a office!


Mubash tsaki yayi snanna yace:

"Badamuwa zan fice ma a office tunda bana ubana bane Amman kasani dakasan koni waye ko kud'i aka biyaka baraka furta wannan zantukan naka agareni ba Amman I won't blame u! Rashin sanine zanma uzuri Kuma Sha nakedai banan bane kurum asibity badai ko? So Mai aciki inkaqiyi dubunka zasuyi mtswwww!"

Ya wuce ya bud'e qofa yaja da qarfi ya kulle qofar inda yabar Likita Abdul wangal da baki yana Mai tsananin mamakin wannan mubash d'in yafi qarfin minti talatin Yana wangale baki had'i da mamaki da kyar yad'an ja lumfashi sannan ya furta a fili:

"Toh Allah ka shirya kasa mufi qarfin zuqatanmu Kuma Kar kabasa nasara akan wannan kekkyawan qaramar yariny'an! "

Da Haka likita Abdul ya maida hankalinsa kan files d'in dake ajiye birjik Akan teburin sa, ya soma bud'ewa Yana Mai dubawa!


Mubash ko Yana fita d'akin da aka kwantar Dani ya shigo ya iskeni kwance ana qaramun ruwa kaina Kuma anmai gyara ansa bandeji kallona yayi Yana mamakin yadda narame nakuma yin haske tamkar wacce ta mutu!

Kujera ya samu ya zauna Yana qaremun kallo Wanda ni a lokacin nafarka Amman alluran baccin da akamun yasa bacci Kuma saceni, kallon qurilla ya shiga yimun sannan yasoma fad'in:

"Wlh qaryanki yasha qarya Aymanah Baki Isa kiyi ciki ki haifeshi Dani ba! Kuma na maki alqawari yadda kike mugun son yara saidai ki gansu a maqota kuma inhar maganan Boka Jatau ya tabbata na rabuwan auren mu toko Wanda Zaki aurama baraki ajiye kwai dashi a doran duniya ba sai nasa gabad'aya ancire maki mahaifarki na naksa wani Abu a tattare dake yadda Babu namijin dazai so ya auro juya takasa bashi 'ya'ya yadda banson ki haihu Dani hakan Kuma bazan Bari ki haihu da wani ba wannan alqawari ne Kuma ki zuba Ido kiga inban cimma mashi ba! "

Dahaka ya miqe ya b'anb'aremun ledan ruwan da'ake mun qari sannan ya cire Wanda aka samun a hannu batareda ya damu da bunbulin jinin dake fitowa a hannunba kasan cewan tugewan da yayi da k'arfi d'auka ta yayi cak ya sab'ani a kafad'ar sa ya fito Dani Yana tafiya Dani kusan kowa ya gansa sai ya dumfanosa da magana Amman ganin yadda yadda ya had'e Rai tamkar mala'eekan mutuwa ya sasu kowa Kama bakinsu suna Mai binsa da kallo har yafita a haraban asibitn motan sa yavud'e ya cillani a gidan baya sannan ya shiga yaja motan da wuri motanen wajen sai Allah wadai da halinsa sukeyi shiko Likita Abdul Koda aka gayamasa girgiza Kai kawai yayi Yana Mai tsananin tausayina Yana Kuma mamakin irin rayuwan da zanyi Nan gaba da Mubbashir!


Tafiya Mai nisa da uban gudu kawai mubash yakeyi Wanda Ina kyautata zaton munbar Kano Dan wani qauye yashiga Yana ta tafiya chan ya tsaya awani gida dake da ginin qasa fitowa yayi yaje ya bud'e gidan sannan ya sab'oni a kafad'arsa yayi cikin gidan Dani!


******************


"Ummah nikam kwana biyu na rasa dalilin da yasa nake yawan mafarkin Aymanah!, Kusan kowani bacci nayi Kona ranane sai na yi mafarkinta! "

Hajia Azma shuru tayi tana Mai sauraron d'an nata Kuma tana nazartan fuskansa sai da yakai aya sannan ta nisa tace:

"Toh babana kasan wasu mafarkan suna da sak'onnin da suke isarwako? Amman kafun Nan inaso ka gayamun lokutan dakafiyin mafarkin sannan kagayamun Mai kake gani acikin mafarkin naka!

Shuru Hydar yayi sannan yad'an runtsa Ido ya bud'esu akan fuskan Ummantasa wacce take jiran sauraron amsan tambayoyin ta yace:

"Ummah nafiyin mafarkin Nan gab'anin sallan asubahi da Kuma la'asar! Sannan Kuma acikin mafarkin Ina ganin Aymanah awani gida Mai shegen mugayen abubuwa aciki Ina ganinta rakub'e a bayan wani gado na Kara tana rakub'e jikinta tana kuka da Kiran sunana kullum sai naganta acikin wannan gidan Kuma tana ihun Kiran sunana tana cewa inzo in taimaketa zai kashe ta zai kasheta zai kasheta!

Sau uku take maimai tamun wannan maganan sannan sai na tambayeta waye zai kashe ta inzata gayamun sunansa sai kawai Naga hannun daga inda bansan ko ta Ina bane ya caka Mata acikinta ta kwala ihu! Wannan ihun shike tashina a firgice acikin baccina Wanda Kuma daganan bazan sake samun bacci ba! Ummah Dan Allah nikam jikina Bai kwanta da wannan mafarkanba yau kwana 5 Kennan Ina yin wannan mafarkin Dan Allah ki Kira su Marmy kiji ko lafiya take!


Nisawa sosai Hajia Azma tayi tana Mai mamakin wannan mafarkin na Hydar Kuma tasan tabbas wannan mafarkin Yana isar da sak'one Amman takasa gane kowani saqone kallan sa tayi taga duk ya firgice d'an murmusawa tayi sannan tace:


"Babana kwantar da hankalinka in Sha Allah Aymananka na Nan cikin k'oshin lafiya! Yawancin mafarki ba gaskiya bane saidai kasan ance mafarki Kashi uku ne akwai Wanda Allah ne kesawa mutum yayi Dan yanason ya isar ma mutum da busharan wani Abu sannan akwai mafarki Wanda shaid'anne ke assasawa sannan akwai mafarki da wannan aljanune ke sawa mutum nayi Wanda zakaga ana saduwa dake acikin mafarki ko Kuma mutum nafin nama dadai sauransu!


Karka damu zan Kira Marmy Kuma zan kira malam Abdulrahman Dan ya fassaramana wannan mafarkin dukda fassara mafarki ba kyau Amman wannan mafarkin nikaina jikina Bai aminta da shiba Dan Haka in Sha Allah zan sa malam ya Mana fassaran mafarkin kaji Babana!


Gyad'a Kai kurum Hydar yayi Yana Mai tsananin son kawai yaji muryan Aymanah ko ya ganta kawai cikin qoshin lafiya! Miqewa yayi yace:


"Ummah gobe zan bi fu'ad da Fahad gombe inaso naje "

Murmushi kawai ummah tayi sannan tace:

" Toh babana Allah kaimu"

Daganan yasakai ya fice ita Kuma Hajia Azma tashiga duniyan tunanin wannan mafarkin Da d'anta yayi wayanta ta janyo ta danna ma malam Abdulrahman yakira bugu d'aya ya d'auka bayan sun Gama gaisawane tasoma gayamasa tiryan tiryan mafarkin da Hydar yayi sannan tace tana so ya fassaramata mafarkin!

Nisawa malam Abdulrahman yayi sannan yace:

"A gaskiya Hajia Azma 'yar Nan Taku......... ..




Share!


AYSHKHAIR
[6/17, 8:32 PM] .: ยฎeal pure moment of life writers


๐Ÿ˜ฐ๐Ÿ˜ญ AUREN WAHALA KO SAKI?! ๐Ÿ“๐Ÿ˜ญ๐Ÿ™†๐Ÿผโ€โ™€


( Story base on fictional writing๐Ÿ“)

MALLAKAR AYSHKHAIR ๐Ÿ’—

WRITTEN BY AYSHKHAIR


Page 31-32๐Ÿšถ๐Ÿฝโ€โ™€


_Diga page dinnan sai bayan azumi zan cigaba in Sha Allah Kuma kuyi haquri najina shuru 2days nayi tafiya ne shiyasa_



Malam Abdulrahman ya nisa sannan yace:

A gaskiya Hajia Azma wannan Yar taku tana cikin qangin rayuwa Wanda mijinta shi ya jefata cikin wannan halin sannan Kuma a halin yanzun ya d'auketa yayi nisa da ita a qasan Nan gaba d'aya sannan Babu Mai iya ceton ta face shi d'anki Hydar Amman shima zai fuskanci gwagwarmaya Mai tsanani kafun Allah da yardar sa zai sa ya taimaki rayuwan ta, wannan shine fassaran mafarkin da Hydar yayi"


Wani kalan nisawa Hajia Azmah tayi sannan tace:


" Shikenan malam nagode Amman tambayata Anan shine kana da masaniyar inda yakaita?"

" Banida shi Allah bai bani ikon sanin qasan ba Amman tabbas ya nisantata da qasan nan"


" Malam nagode sosai Allah ya saka da alkairi"


Malam yace " ameen sai kuyi sadaka da farin goro da Kuma fura"


" Ok Tam in Sha Allah malam mungode"


Nan suka katse wayar inda Hajia Azmah tabi wayan da kallo tana Mai tunanin irin rayuwar da 'yar k'aninta Aymanah ta fuskanci kanta aciki! Nisawa tayi sannan ta danna lanban Marmy bugu d'aya biyu Marmy ta d'aga bayan sun gaisa Hajia Azma ke tambayan ta :

"Marmyn Yara Aymanah fa?"

Marmy tad'anyi murmushi sannan tace:

"Aymanah tana lfy yau kusan sati kenan Muna trying lanbanta baya shiga, Marwa mukasa taje gidan sabida batayi resuming skul ba tace dataje wata Mata ta iske Kuma tace Mata Wai sunyi tafiya ina gani kamar honeymoon sukaje"๐Ÿค—

Marmy ta ida maganar tana murmusawa

Ras gaban Hajia Azmah ya bugo da kyar ta iya daidaita kanta sannan tace:

"Ok a gaida mutan gida sai anjima"

Ba tareda ta jira abinda Marmy zatace Bata ta kashe wayan sanan ta nisa tana maima Aymanah aduan Allah kareta a duk inda take, Marmy kuwq bin wayan da kallon mamaki takeyi dan ba Haka suka Saba waya da Hajia Azma ba intakira to tabbas sai an baiwa kowa a gidan waya angaisa Amman yau Sam batayiba da kyar Marmy ta nisa tabar falan Dan shiga side din mamanmu!



******************


Bud'e idanuna nayi na kafe su Akan silin d'in d'akin Wanda Babu komai a kan kwanon inba katako ba a hankali nasoma bin d'akin da kallo har na sauke idanuna kan mubash Wanda ke kwance bakinsa d'aukeda sigari Yana Sha Yana busarwa bisa alamudai ba bacci yake yi ba kawai lumshe idanun sa yayi hannunsa nabi da kallo Wanda yake riqe da kwalban giya qasan Kuma kwalin sigarine Baja baja Wanda bisa alamu dai kamar yamusu Shan hauka ne, runtse idanuna nayi had'i da toshe hancina sabida warin giya da taba sunfara isan cikina, a hankali Kuma komai yasoma dawomun tamkar sabo wani kalan fitinannan ihu nasaki Wanda yayi sanadiyar miqewar mubash a firgice Yana waige waige.


Karaf idanunmu suka had'e inda Naga mubash ya sauya kamanni idanunsa sukayi jajawur hancinsa da bakinsa sai fidda hayaqi sukeyi kallona yakeyi Rai b'ace Niko zaro idanu kawai nakeyi kasan tuwan nasan banida qarfin kwatan kaina a hannun mubash yaukam Dan jikina duk a mace yake a hankali nake ja da baya baya ganin Yana dumfanata a Haka har nakai quryar kadon inda Babu hanyan guduwa hannuna biyu na had'e na rufe fuskana dashi da sauri had'i da kwala ihu ganin mubash nashirin kwalamun kwalban giya akaina yaukam inaga lokacin mutuwata tayi sabida mubash a bige yakeko ya kasheni ya kashe banzane kawai wlh,bansan tunanin dayayi ba chan naji baa kwalamun ba hakan yad'an sani rage karkarwan jikin danakeyi had'i da d'an bud'e idanuna kallanshi nayi tsaye akaina kurum ya quramun idanu chan Kuma ya ja tsaki ya matso daf Dani har inajin warin giya da taban ajikina Kai kace nice nasha cikin muryar mashaya had'ida warin baki yace:


"Hhhh Dan qusar ubanki angaya maki zan kasheki yanzun ne?๐Ÿคฃhhhh toh ai Inna kasheki wlh babban gata namaki sabida inkinmutu Zaki huta da komai Kuma nasan zakiyi kwanciyan kabari Mai kyau sabida kasheki nayi Dan Haka karkiyi tunanin mutuwanki Nan kusa sabida sai na tabbata kin d'and'ani azaba da quncin rayuwa Wanda har sadaka da aduaa Zaki Suma yi Dan mutuwa ya zo ya tafi dake Dan itace kawai hutu a gareki Dan Haka Aymanah kishirya zaman Auran wahala ba mutuwa Kuma Babu saki sannan baki bajin dad'in rayuwa har abadan abadan sannan kisani keda gata wlh har abada baki bakowa saini sharp shooter sannan kishirya ganin bad'ala ta da komai infact kema a sannu sai na d'auraki akan turban sabida ko kinmutu Zaki mutu a fasiqa mazinaciya Kinga ranar qiyama kina wuta Nima ina wuta bake ba aljanna bani ba aljannah so muzuba mugani"


Bansan sa'ilin da bakina yafurta:


" Ai dayake ancema ubankane keda Aljannah da wutaba har zaka yanke hukuncin inda zan shi.......,.


Wani wawan marinda ya tsinkeni dashine yasani kasa cigaba da maganata d'ago Dani yayi had'i da damke gashin kaina Wanda har cikin Raina nakejin wannan damqar yace:


"Har na Isa nayi magana kimayar mun? Toh wlh ko uwarki Asma'u da kishiyar ta Khadija da shi ubanki Mubin Basu isaba infact baaa haifesuba ace na fad'a sumaidamun bare ke kucaka Yar kwaro kimayarmun yau saina nuna maki kuranki wawiya jaka"


A Haka ya ruqa Jana a qasan d'akin har ya fiddoni waje inda Babu gidaje Sam sosai inba daji ba wurin wani bishiyan mangoro yakaini ya wullar Dani sannan ya shiga wani d'aki baijima ba ya fito da igiya inaji ina kallo mubash ya d'aureni qam ajikin wannan bishiyar Wanda baida leaves (gany'e)ko kad'an akai abushe take bishiyar gawani uban Rana daakeyi bisa alamu ranar na ruwane dayagama d'aureni yayi ficewar sa a gidan gaba d'aya!



Azaba da wanikalan azaban ciwon Kai ne yaketa d'awainiya Dani mubash mugune wlh tsinanne in Sha Allah fuskan annabi da tasa bazasu tab'a had'uwa ba!


A taqaice dai Haka iska Mai had'e da guguwa suka soma tashi qasa sai shigan idanuna sukeyi kankace Kobo har an tsinke dawani kalan ruwa Wanda yake had'e da qanqara innalillahi wa'inna ilahirajiun hasbiyallahu walni'eemal wakil kawai nake ta nanatawa abakina Wanda daka qarahema gazawa nayi bana Koda kwakwaran motsi..........




Manage sai bayan azumi in Sha Allah๐Ÿšถ๐Ÿฝโ€โ™€๐Ÿšถ๐Ÿฝโ€โ™€


Maison jin qarashen lbrn Kuma sai yabiya naira 200kacal sannan ๐Ÿคฃ๐Ÿšถ๐Ÿฝโ€โ™€


Happy ramadan
[6/17, 8:32 PM] .: [6/17, 7:15 PM] Indo Dalil๐Ÿ˜: *ยฎeal pure moment of life writers*


๐Ÿ˜ญ *AURAN WAHALA KOH SAKI*?! ๐Ÿ“๐Ÿ˜ญ๐Ÿ™†๐Ÿผ


_story base on fictional writing_

*_Written by Ayshkhair_*โœจ


๐Ÿค—*_kuyi haqurina najina shuru sosai pls typing dinne wani zubin fita Rai gareshi๐Ÿ˜ซAmman zan daure naruqa maku in Sha Allah dafatan kunyi salla lfy? ๐Ÿ˜—sainazo amsan goron sallana eheee_ ๐Ÿ‘ฏ๐Ÿผ



Page 33&34



Wasa wasa kwana 3 d'aure awannan bishiyan baci inba ruwan saman danake samu anayi ba shine nake taran bakina na Sha ruwa gaskiya mubash mugune iya mugu bazan tab'a

5 / 13