bayar amma shide LTG kawai ya jisu ne, yasan abune ma wuyaci.
Suna nan zaune a falon har kusan karfe uku na dare babu wanda ya runtsa.
Miƙewa Sabriyah ta yi ta faki idon kowa ta shiga dakinsu number Fu'ad ta kira.
Yana dagawa tafara zazzaga mishi ruwan Masifa.
"Calm down my Sabriyah, kin san bazan taɓa cutar da rayuwarku ba,kawai ni Tajuddeen din nake buƙata in kuma be zo ba Wallahi sena kashe su".
A firgice ta ce"dan Allah Fu'ad kar ka yi haka menene Abinda suka aikata maka in ma gaban ka kakeyi ai da ya Taj ne ba wai da su Umaisha ba".
"To in har kina so in rabu dasu dukkansu dole se kin sanar dani duk wani abinda suka shirya nasan sun yi planing din yi min ha'inci".
Tana share hawayenta ta ce"na yi alkawari zan faɗa maka komai amma dan Allah karka cutar da Umaisha da Iklas".
"Karki damu my Sabriyah, muddin kika min yanda na ce nima na miki alkawari bazan musu komai ba".
Kashe waya ta yi dan ta rasa takaicin waye zataji na Fu'ad din ne ko kuma na kanta da ta kasance wawiya ta yarda dashi.
Komawa falo ta yi ta zauna,tana jin duk tattaunawar da ake yi,amma duk wanda ya mayar da hankalinsa akan ta ze gane ba'a cikin nutsuwarta ta ke ba.
Kiraye_kirayen sallah asuba ne yasa su tashi suka je suka gabatar da sallah.
Bayan sun dawo daga masallaci ne, sojoji da yan sanda suka kimtsa kansu domin tafiya hatta su ACP Jawan da Sudais sun shirya.
Fitowa LTG ya yi cikin shirinsa na uniform din sojoji fuskar nan dama ba annuri ne akai ba yanzu yafi ko yaushe ban tsoro.
Addu'a sosai su Ammi suka musu.na samun nasara.
Kirane ya shigo wayar Sabriyah ta inda Allah ya taimaketa wayar na vibration.
Fakan idon su ta yi ta shiga kitchen da babu kowa a ciki daga waya kafin ya ce komai ta sanar dashi shirin da sukayi sannan ta kashe wayar ta,ko muryarsa bata son ji.
Kira ne ya shigo wayar LTG ɗagawa ya yi yasa akunne,bayan ya gama saurarar Abinda aka faɗa ne ya kashe wayar idonsa yana ƙara rinewa yana ja.
Kallonsu ya yi."kowa ya samu guri ya zauna ni kadai zan tafi".
A rude suka kalli shi"meyasa haka LTG?".
Sudais ya tambaye shi.
"Dan Allah karku hana ni,ya riga da yaisamu labarin shirin da ku ka yi,yanzu haka ya kashe yarinya ɗaya, bana son a sa'ke kashe wata,kar ku hanani,kuma kar wanda ya biyo ni".yana gama fadar haka ya fice a falon dan bayason ganin fuskar Ammin sa dake kuka".
Suna kiran sunanshi amma ko juyawa be yi ba,ya shiga motar ya fisgeshi yabar gidan.
Fashewa ta yi da kuka musamman idan ta tuna cewa Fu'ad kashe LTG ze yi kuma ita ce ta bada,taimakonta.da gudu ta bar falon tana kuka, direct part din LTG ta nufa ta tsaya tana kuka.
Ji ta yi tana sha'awar duba part din nashi.
Bedroom dinsa ta shiga wannan hoton da ranar ya hanata gani shi ta dauka tana kallo,zaro manyan idanunta ta yi kamar zasu faɗo ƙasa ganin wacce take jikin hoton.
Duk da bata da hoton kanta a yanzu Lokacin da take yarinya karama amma tana ganin wannan hoton ta gane cewa ita ce a jiki,ƙaryata kanta ta yi ta bude locker din nan taci karo da folder din hotuna fito dasu ta yi, ta fara gani hotuna ne gaba daya a jiki,da wanda aka yi drawing da kuma wanda aka dauka a camera,bata sake shiga firgice da rudani ba se da ta buɗe wani shafin da taga hotonta da wannan saurayin da take yawan gani a mafarkinta,yana rungumeta da ita aka musu hoton,a ƙasa an rubuta "Asrah din Tajuju"sa'ke folder hoton ta yi ya fadi a ƙasa.jikinta ne ya dau rawa kamar mazari,gani take yi kamar a mafarki taya hakan ze yu, ta ya za'a yi ya kasance ita ce wannan Asrah din da wannan ahalin basu da magana da ya wuce nata.wani irin Flash ta fara ganin a idonta,tana jin muryoyi ana magana.rufe idonta ta yi ta sa hannu ta toshe kunnenta,a cikin idonta ta hango wannan yarinyar da ta gani ajikin album din da anty amarya a filin garden suna wasa,anty amarya na binta a baya ita kuma tana guda tana yiwa anty amarya dariya.
Kokarin faɗuwa yarinyar ta yi,anty amarya ta ce "Asrah becarefull"riƙe yarinyar wani kyakyawan saurayi ya yi yana dagata ya daura a wuya.
"My Tajuju".
Da sauri Sabriyah ta bude idonta waral kamar fitila,nan take numfashinta ya fara fita da sauri sauri.
"Kenan ni ce Asrah?,ni ce Asrah din da suke nema?,taya hakan ze kasance?"faɗuwa ta yi akasa ta na me yin ihu"bani baceeeee"domin har yanzu ta gagara gaskata ita ce Asrah.
Da sauri kuma ta sa hannu ta bude shafi na ƙarshe a folder din hoton Asrah ne tana tsaye ba riga a jikinta,rubutun sunan Tajuddeen baro_baro ya fito a bayanta.
A tsorace kamar wacce taga fatalwa ta yarda folder din a karo na biyu.
Hannu tasa taja zip din rigarta ƙasa ta je gaban mirror dakin nashi ta juya bayanta kadan nan take sunan ya bayyana.
"Innalillahi wainna'ilaihi rajuun shikenan ni da kaina na tura muradin rayuwata wajen da za'a kashe shi,na tura tajujuuuuu na wajen da za'a kashe sa, muddin wani abu ya samu Tajuju to bazan taɓa yafewa kaina ba".
Kamar mahaukaciyar da ta gudo daga gidan asibiti take magana tana kuka kamar ranta ze fice daga jikinta.
Da gudu ta baro part din nashi tana sambatu,kowa na zaune a falo ana jimamin halin da suke ciki ta fito da muguwar gudu zata wuce su,ga kururuwar kukanta da ya cika gidan.
Da gudu Sudais ya yo kanta ya damki hannunta kamar wata me aljanu ta fara fisge_fisge tana "dan Allah ya Sudais kabarni, Wallahi ze kashe shi,ze kashe min shi!,na shiga uku na ze kashe min farin cikin rayuwata".
Ganin yanda take magana ne yasa suka yi tunanin ko aljanu ne suka shigeta, zaunar da ita Sudais ya yi amma ta sake yunkurin miƙewa.
Maida ita uncle Hameed ya yi ta zauna,wasiwasin abinda ya sameta suka shiga yi.
Abbie ne ya ce "Sabriyah menene abinda ya sameki,kuma waye kike cewa za su kace miki?"duk zuba mata ido sukayi suna son jin amsar da zata bayar.
Da karfi ta ce "Tajujunaaaaaaaaaaa"
Sa'ke zuba mata ido sukayi ɗan son tabbatar da abinda ta faɗa.
Anty amarya murya na rawa ta ce "Sabriyah bamu fahimci abinda kike son cewa ba".
Tana kuka ta ce "Fu'ad ze kashe min Tajuju na,nice!nice!nice"ganin yanda take jin kamar ana rike mata wuya ne yasa ta juya musu baya ta ja zip din rigarta kasa nan take sunan Tajuddeen ya bayyana a gadon bayanta.
Tirka_tirka,wani irin shock ne ya kamasu,basu taɓa shiga cikin matsananciyar al'ajabi ba irin wannan.
Kusan a tare gaba dayansu suka furta.
"Asrahhhhhhhhhh?".
Gyada musu kai ta yi tana kuka.
"Wallahi Fu'ad bashida imani ze kashe min Tajuju na,kuma muddin ya mutu Wallahi nima mutuwa zan yi in bar Duniyar nan".
Don't forget to comment, share and like.
Anan na kawo karshen book one,
Book two din na kuɗi ne ga duk me bukata ya min magana ta whatsspp number ta 09024503194.