Bintu Diyar Bayice Jinin Gado By GARGA'DI

Author :  GARGA'DI Category :  Romance

Chapter   21 / 24

60K to 63K   out of 70.2K words

wannan bikin da ake masa ya na daga na sa 6angaran. Su Yarima Jafar da Khalil tun suna iya jure shirun da ya mu su har su ma su ka gaji su ka yi na su gurin. Da ya gaji da zaman ne ya watsa ruwa yayinda ya sanya jallabiya, kai tsaye in da ya saba zuwa duk sanda ran sa ya ke 6ace ya nufa, wato lumbun da yake k’yatare da 6angaran matan Sarki. Nan bisa dutse ya kusa raba dare, sai da ya ji idanun sa sun masa nauyi sosai sannan ya tashi a hankali ya nufi 6angaran sa. Ko da ya zo giftawa ta 6angaran da ya san babu shakka nan aka sauki amaryar da aka aura ma sa, sai ya tsinci kan sa ya na mai mummunar fad’uwar gaba. Hakan ya sa shi wucewa da sauri ya na mai ambaton ubangiji. Bakin kofar sa ya tadda dogarai da bayin sa sun yi jugum jugum kasancewar ya mu su hani da biyo shi, ganin sa su ka fara masa kiran lafiya su na mai fad’in

‘’takawa sannu Yarima Barde, lafiyarka dama da hauni, dama da hauni lafiya, salamun salamun’’

Ganin ya zo daf da shiga kofar da za ta sada shi da 6angaran sa, su ka taka masa baya, har ila yau fad’i su ke
‘’gicciye dama Yarima, gicciye salamun’’
Tsayawa Yarima Barde ya yi, ya d'aga mu su hannun alamar baya buk’ata su biyo shi kafin ya sa kai ya shige ciki. Ya bar su waje su na kallan kallo, dan kuwa sun san lamarin auren Yarima Barde kan su zai k’are duk da dai ba su suka kar zuman ba, rataya aka ba su.

Washagari da sassafe jama’ar Fabarusa, Samari da ‘Yan mata har da tsuffin cikin adon su na burgewa su ka yi dandazo kofar fada domin kallan hawan angonci bisa al’ada. Amma Yarima Barde ya yi k’yememe ya ki fitowa ko da kuwa kofar 6angaran sa ne bare a sa ran zai hau. Ko da su Khalil su ka je da numin bashi baki, a bakin k’ofa dogarawa ma su tsaran kofar Yarima Barde su ka fad’a mu su buk’atar Barde na kada a bawa kowa damar isa gare shi. Dan haka sai hakura su ka yi, Magatakarda ne yayi shela ga jama’a cewar Yarima Barde be shirya yin hawan angoncin shi a ranar ba, su yi hakuri sai zuwa ran da ya shirya za a sheda mu su. Da kyar kamar ba su hakura ba su ka watse, dan ba k'aramin cin burin hawan angoncin Yarima Barde su ka yi ba, kasancewa akwai k’auna tsakanin sa da Talakawa, musammam ‘yan mata da samari, Yarima Barde na su.

"Bayan hayaniyar kofar fada ta lafa, jama’a sun watse su Gwaggo Munari da sauran tawagar Sa’ayrasa su ka yiwa iyalan Sarkin Fabarusa sallama, an had’a mu su koma ta arziki sannan su ka d’auki hanyar komawar su gida S’ayrasa, in da su ka bar Bintu tare da bayin ta, wato Ladiyo, Hansai, lantana da Maman Cangwai a sabon Masarauta. Gwaggo Munari ce ta shedawa Iyalan Sarkin Sa'ayrasa irin tarbar da aka mu su da tarin dukiyar da Bintu ta samu. Gimbiya K’amariyya kuwa sai da ta had’a da kwanciyar asibiti. D’aya daga cikin bayin da su ka juyo ne ta isar da sak’on Lantana ga Yarima Nuhu. Sakon na cewa ta aikata komai yanda ya umarce ta, kuma komai ya tafi daidai. Tsabagen dad’in sak’on na ta har kyautar zani da kallabi ya bawa baiwar domin kuwa in har maganar hakan ta ke babu shakka hakin sa ya cimma ruwa.


Kwanci tashi. Bintu ta cika sati guda Masarautar Fabarusa, amma ko da wasa Yarima Barde be ta6a takowa in da ta ke ba bare ma ta san kalar fuskar sa. Gata kuwa ta na sha gurin matan Sarki, musammam Goggon dole da Uwarsoro ,domin kuwannan su burin su ace amaryar Barde daga ta ta ce, Maman Cangwai ce ke saka Bintu a hanya kasancewar ita ta gane manufar su ba lalle alk’airi ba ne. Ita dai ta bi kowa sannu a hankali. Goggon nan kuwa mulki da jin kan ta kad’ai ya fi k’arfin ta, shi Yarima Barde ba gaban ta ya ke ba, bare uwa uba matar sa.




🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[8/29, 9:40 PM] ‪+234 803 440 2664‬: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


1⃣1⃣


Sidiya ce.....✍🏼

Da hantsi Sarki Abdulrahman zaune bisa kujerar mulkin sa, ana zaman fadanci sai ga Yarima Barde. Ganin sa Sarki be san sanda ya murmusa ba, dan kuwa ya lura wasan 6uya Yarima Barde ya ke da shi, idan har ba zaman fadanci ba ba ya ta6a yarda su had’u da Sarki duk dan gudun duk wate magana da ya shafi Bintu wanda tun da aka d’aura auren ba su sami kye6ewa da Sarki ba bare su tattauna batun.
Sanye ya ke cikin fararan kaya an masa d’inkin hannu irin na sarauta. Ya sha rawani irin na buzaye kai da ka gan shi ka ce daga sahara ya ke. da shigowar sa dogarai su shiga yiwa Sarki kiran lafiya su na mai sanar ma sa da isowar Barde
‘’ kimtsi gyara daidai alher, gyara kimtsi ga kyau’’

Gaban Sarki Yarima ya zube, hannun sa na dama dunk’ule ya kai jinjina ga Sarki, dogarai fad’i su ke
‘’jinjine dama lafiya alher, an gaishe ka Yarima Barde’’

Da ga gefe kusa da Yarima Sadauki ya ja ya zauna. Nan fa aka ci gaba da fadanci ana tattaunawa akan abin da ya shafi cigaban al’umma da ma kuma matsalolin al’umma da yanda za a magance su. Har aka yi aka k'are idanun Sarki na kan Yarima Barde. Ko da Sarki zai tashi sai cewa yayi da Barde su na san ya riske su a turakan su. Yayinda Sarki zai tashi dogarai su ka rufe sarki ta hanyar baza babban rigunan su yanda ba wanda zai iya ganin motsin sa bare tashin sa. Fad’i su ke

‘’ rangwame Tafsawa, sannu rangwame alher, lafiya Adali, lafiya Mataimakin Musulunci, gyara kyamtsi ga kyau’’

Haka su na masa kiran lafiya har ya kai ga ficewa daga fada. Bayan fitar sa ne Yarima ya kai gaisuwar sa ga sauran Hakiman, ciki har da wanda ke masa Allah ya sanya alkhairi. Ya zo fita kenan Yarima Sadauki ya shagaban sa, ganin sa Yarima Barde ya Murmusa ya na mai dunkule hannun sa na dama ya jinjinawa Sadauki sa’annan ya furta

‘’Sadauki ne kai’’

Cike da tak’ama, shi lalle Yarima mai jiran gado, Sadauki ya maida masa da martani yanda ya saba ta hanyar fad’in
‘’kai ma Barde ne, musammam sa’in da na hau kujerar mulki’’

Barde be fasa murmushin da ya ke ga d’an uwan na sa ba duk da kuwa ya san magana ya ke fad’a ma sa. Kana ya ce

‘’barka da hantsi, da fatan mu na lahiya’’
‘’lahiya lumi fa, ya kwanan amaryar dole? Ko da shike har yau ba mu ji labarin budurcin ta ba bare mu ce ango ya sha k’amshi, d’iyar abokan gaba ce duk da kuwa abun ba dambe ba ne ba, kada Barde ya ba mu kunya!’’

Ya na gama fad’in haka ya yi gaba. D'if Yarima Barde ya d’auke wuta, Khalil da ke tsaye daga bayan su, ya kuma ji dukkannin maganan da Sadauki ya fad’a ne yayi saurin ta6a kafad’ar Yarima Barde, kana ya ce

‘’ba kai an babba ba, amma babba gare ka Barden mahadi maida garin wani kongo’’

Jin haka ya san hakuri Khalil ya ke ba shi. Ya ko yi na’am da Khalil ta hanyar murmusawa ya na mai fad’in

‘’ina da muradin zuwa wucan gadi mutumi na, ko za mu sami dama tafiya kafin na sami saduwa da Sukuku Bakaka(Sarki)’’

Cikin jin dad’i Yarima Barde ya fara sakewa Khalil ya nemo Yarima Jafar domin su tafi wucan gadi.

Da yamma likis bayan Yarima Barde ya dawo daga wucan gadi ya isa ga Sarki. Turakar Sarki su ka d’an ta6a hira sama sama, kafin Sarki ya kawo batun Bintu ta hanyar tambayar

‘’ya amanar da mu ka ba ka? Shin an duba kuwa?’’

Barde na mai durk’usar da kai k’asa ya kasa magana. Ganin haka Sarki ya fahimci in da ya dosa, kana ya ce

‘’kar ka damu d’an mu, ka bi sannu a hankali ba laifi ba ne, amma dai mu na ruk’on ka da kar da mu zamo daga cikin azzalumai ta hanyar d'auka lokaci mai tsayi, wannan gona ta ka ce, kada ka manta akwai idanu dayawa bisa kan ta, da fatan za ka kula a wadata ta, san samu ma a ziyarce ta ko da kuwa daga yau zuwa kwana uku ne’’

Maganar Sarki ba k’aramin nauyi ta yiwa Barde ba, dan kuwa ji ya ke ina ma zai iya masa musu ko da kuwa na sakan d’aya ne, amma ina tsaintar kan sa yayi ya na mai fad’in

‘’an gama Sarkin yakin musulmi, bango madafan bayi’’

Sarki kuwa ba k’aramin jin dad’in yanda Barde ke masa biyayya ya ke ba, cikin ran sa ya na mai jin ina ma shi ne babban d’an sa ba Sadauki ba. Sai bayan da su ka idda salar isha’i sannan Barde ya baro wajan Sarki. Kai tsaye lambun nan da ya saba zama duk dare ya nufa, zuciyar sa na sak’a masa yanda zai yi ya gujewa had’uwa da amaryar da aka d’aura masa, wato kanwar budurwar sa.


🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[8/29, 9:43 PM] ‪+234 803 440 2664‬: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

1⃣2⃣



Sidiya ce.....✍🏼


6angarn Bintu kuwa kamar yanda ta saba, yau ma ta sallami dukkanin bayin ta, ya rage daga ita sai Ladiyo, wacce ita dama d’aki d'aya su ke kwana idan ta tabbatar kowa ya d’auke k’afa, tsabagen tsoro da rashin sabon kwana ita kadai. Bintu na kwance bisa gadon ta, tunanin Innar ta ta take da rayuwar ta na da wanda shi ya fi mata dad’i akan wannan daula da ta tsinci kan ta a ciki. Ladiyo da ke tsaye bisa taga idanun ta kan hanyar lambun da ke kyetare da 6angaran Bintu, sai ajiyar zuciya ta ke ba tare da ta san ta na yi ba saboda tsabagen muradin sake zuwa lambum da ya addabi zuciyar ta, ba dan komai ba ko dan ta ga wannan buzun da ta gani ciki mai irin sifar aljanu tsabagen kyauwu.
Gashi ran da ta fara shiga lambun satar hanya ta yi bayan Bintu ta yi bacci ta ga wucewar sa, kasancewar shi kad’ai ne ya sa ta yi tunanin kila talakan Sarki ne, wanda su ke da daurin gindi wajan fadawan Sarki ko kuwa d’aya daga cikin ‘ya’yan hakiman masarautar nan. Nan ta gan shi zaune bisa kan dutse ya na sakar zuci, har ta k’are masa kallo be san ta na yi ba tajuya tana tasbihi ga Allah bisa tsarin halitta da yayiwa bawan Allah nan.
A hankali ta kai kallan ta ga Bintu, kana ta ce

‘’gide Gimbiya ba ki da muradin ganin farin wata ne? aradu zaman cikin kurya ya ishe ni’’

Jin haka Bintu ta yi farat ta tashi zaune ta na fad’in
‘’yo to Ladiyo mu tai mana, ba tun yau na ke da muradin mik’e k’afa, kwankwatsi ni ma na gaji da zaman nan, hallo ki na ga babu matsala aka gan ni a rariya?’’
Abun da Ladiyo ke so ta samu duk da kuwa ba ta yi tsammanin haka daga wajan Bintu, ko da shike dama ai d’iyar bayi ce Ladiyo din ce ke sha’afa. Ta yi saurin dawowa gaban Bintu jiki na rawa ta ce da ita

‘’gide ai da yawa ba su san fuskar ki ba, ba na jin za su waye ki, kai in ki na son badda kama ma zai fi na ara mi ki d’aya daga cikin kaya na na bayi......idan fa Gimbiya za ta iya sanyawa’’
Ta k’arasa ne cikin d’ard’ar kada Bintu ta ce ta raina ta, duk dai ita kan ta ta san babu laifi Bintu ba ta canza mata ba, in har ba wai akwai mutane gun ba yanda ta saba mata tun tana baiwar ta hakan ta ke ma ta. Ga mamakin Ladiyo sai gani ta yi Bintu ta tashi cikin hanzari ta na mai fad’in
‘’kayya ku ji mu da Ladiyo da yasasshen zance, tuwo ne towo ba a sake masa suna, maza d’auko mu tai ko ba komai na sha iska’’
Cike da farin ciki Ladiyo ta da’aukowa Bintu d’aya daga cikin kayan ta na bayi, kan kace me sai ga Bintu ta koma gidan ta na da, wato shigar kayan bayin Sa’ayrasa, Ladiyo har ta na mata tsiyan ya ta ga kayan sun kar6e ta sun zauna jikin ta sosai, ko da shike daga jikin ne.

Bintu na duban kan ta cikin madubi, idanun ta cike da kwalla ta ce
‘’Allah Sarki wata rana, aradu Ladiyo na fi san rayuwa ta a da akan wagga sabuwar rayuwar’’
‘’yo to Bintu ina ga cigaba ki ka samu, wani sa’ilin sai na ji dama ni ce ke aradu da kin ga yanda ake tsiya da mulki. Mu tai dan Allah kar wani abun ya zo ya sa mu fasa hita’’
Bintu na me goge kwalla ta bi bayan Ladiyo. Daga waje su ka tadda bayi mata wanda Goggon nan ta bawa Bintu zaune. Ganin su sai da Bintu ta ja da baya gudun kar da su waye ta. Ladiyo ce ta yi maza ta ja hannun ta tana mai fad’in
‘’barkan ku da dare’’
‘’barka dai Ladiyo, an fito shan iska ne?’’
Su ka amsa mata amma idanun su na kan Bintu. Ladiyo ta ce
‘’eh Gimbiya na da muradin a bar ta ita kadai’’
Kai su ka jinjina su na mai musu fatan dawowa lafiya. Har sun yi gaba su tsaida su ta hanyar fad’in
‘’ba ku ji ba’’
Cak su ka tsaya, Bintu na mai rawan jiki, cikin ran ta fad’i ta ke
‘’shikenan sun gane ni’’
Ita kanta Ladiyo mutawar tsaye ta yi ta na jiran tsammani. D’aya daga cikin bayin ce ta matso gare su kana ta ce
‘’Ladiyo wagga baiwar ban waye ta, shin ko ita ce Lantana?’’
Ta na magana ne yayinda ta ke k'ok'arin ganin fuskar Bintu wacce ta 6uya cikin duhu. Ladiyo na mai sosa k’yeya ta ce
‘’ah ah wagga Batula sunan ta’’
‘’Batula?’’
Baiwa ta sake maimaitawa, Ladiyo ta jinjina kai kafin ta ja hannun Bintu su ka yi gaba ta na fad’in
‘’bari dai mu je mu dawo....’’
Ko da su ka k’urewa ganin bayin sannan su ka karya kwanar da za ta sada su ga lambu, har lokacin gaban Bintu be dena fad’uwa ba, haka kuma Ladiyo ba ta fasa mitar gulma irin na bayin Fabarusa ba.

Hankalin Bintu be kyauta ba sai da ta tsinci kan ta cikin lambu. Lambu ne mai ban sha’awa wanda ya sha ado da bishoyin kayin marmari iri daban daban. Hasken wata da yayi fari kal a tare da hasken lantarkin da ke daga cikin kowacce kusurwa na cikin lambun ba k’aramin k’ayata shi yayi ba. In ban da koken tsuntsaye da na kwari babu abun da ke tashi cikin lambun.

Tuni Ladiyo ta shiga raba ido ko Allah ya sa ta ga wannan mutumin, ita kuwa Bintu wani dutse ta samu ta yi zaman ta kai ta na fad’in

‘’kai Ladiyo wagga lambu ba dai ni'ima ba, ni dai na yi wajan zama daga nan’’
Ladiyo na mai raba idanu ta ce da Bintu ita dai za ta d’an taka to, yanzu za ta dawo. Nan bisa dutse ta bar Bintu yayinda ta kutsa cikin lambu domin neman wannan mutumin.

Barde kuwa da daman shi Ladiyo ke nema zaman Lambun ne ya ishe shi, gaba d’aya ya kasa samin nutsuwa. A hankali ya ke shawagi cikin lambu, wani irin wari ya ji yana bak'untar hancin sa sannu a hankali, tun ya na iya jurewa har ya kasa ya yanke hukuncin ficewa daga Lambun gaba d’aya dan kuwa warin ya fi k’arfin na mataccen dabba. Ko da ya d’auki hanyar fita daga Lambun nan ya ji wari na k’ara gabato shi. Nan bisa dutse yayi kaci6us da ita kishingide, idanun ta runtse tamakar mai bacci, hakan nan wani irin wari da tun da yazo duniya be ta6a jin irin sa ba ya daki hancin sa har sai da ya ja baya da sauri wanda k’aran sautin motsin na sa ya sa Bintu bud’e idanun ta yayinda ta kai kallan ta ga kyakkawan buzun da ke tsaye gaban ta, hannayen sa biyu bisa hancin sa da alama yana k’ok’arin kare hancin daga jin wari ne.


🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪



GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.


1⃣0⃣



Sidiya ce....✍🏼


Ana gama wankan amarya Bintu ta ja jik’akken mayafin ta ta rufe fuskar ta tana mai shar6ar kuka. Ba tare da 6ata lokaci ba d’aya bayan d’aya sauran iyalan Sarki su ka dinga zuwa Jakadiya na gabatar da su, har su ka k’are sannan aka rufe taro da addu’a. Da aka gama maimakon a kai Bintu d'akin auren ta, 6angare ne na musammam cikin gidan Sarki, sai wani 6angare aka sake kai ta na daban daga cikin 6angaran Goggon nan wanda ya kunshi d’aki biyu kowanne da bayi sai kuma falo. Nan za ta zauna har sai sanda ta kai budurcin ta d’akin mijin ta. Za6in bawai d’aya daga cikin bayin ta wanda za su na kwana 6angaran ta aka bata. Gwaggo Munari ce ta za6a mata Ladiyo dan kuwa ta fi yabawa da hankalin ta, sauran kuma wuni za su na yi, idan lokacin bacci yayi ko kuwa Bintu ta sallame su sai su koma 6angaran da aka tanadarwa bayi.


Yarima Barde kuwa duk wannan bikin da ake masa ya na daga na sa 6angaran. Su Yarima Jafar da Khalil tun suna iya jure shirun da ya mu su

21 / 24