zuwa d’akin taro ba tare da sun bari manya daga cikinsu sun fahimci abinda ke faruwa ba.
Yarima Barde kuwa da dabara Yarima Jafar da Khalil su ka ja shi mota, gaba d’aya ya zame mu su tamkar mutum mutumi, ya d’auke mu su wuta. Cikin mota sai da su ka d’au kusan rabin awa babu wanda ya iya furta komai.
Dogarin Masarautar Fabarusa ya zo ya buga musu kofa, nan ya zube ya na mai sheda mu su umarnin Sarki Abdulrahman na a ma su iso gareshi.
‘’Su na cikin masallacin ne?’’
Yarima Jafar ya tambaya, in da Dogari ya ba shi amsa da
‘’A'a, sun wuce ga d’akin taron masarauta tunda jimawa, Yarima kad’ai ake tsimayi ranka shi dad’e.’’
‘’Mu na nan tafe.’’
Cewar Khalil, yayinda Dogari ya tashi da sauri ya na fad’in
‘’A iso lafiya.’’
Yarima Jafar na duban Yarima Barde ya ce
‘’Ka bawa zuciyarka hakuri mu amsa kiran Mai Martaba’’
Ko kallonsa be yi ba bare ma ya nuna alamar ya san da shi ake, kamar an aje dutse. Ganin haka Khali ya ce da Yarima Jafar.
‘’Ka san halin Barde a sama ya ke, ina zaifi mu lalla6a mu je a dai ga fuskarshi, in ya so sai mu nemi izinin tafiya ta hanyar ba da uzirinmu ga Mai Martaba.’’
Da wannan shawara su ka fito daga motar, amma Yarima Barde fitowa ta ma sa wuya, sai da Yarima Jafar ya ma sa tuni akan wanda ya sa a yi kiransa sannan ya fito cike da k’asaita, dama shi idan ransa ya 6aci nan fa sarautar ta sa ke bunk’asa. Ko da dogarawan da ke tsimayinsu su ka ga fitowarsa tuni su ka rufa musu baya, zuwa d’akin taro, kai kace Sarki Abdulrahman na Fabarusa ne da kansa ke tafe.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
3⃣
Dakin taron ya cika fal da jama’a, tawagar Aisar da shigowar su ke nan, na su 6angaran na shugaban k’asa su ka zauna. Haka ma hakiman Sa’ayra da Fabarusa, Agadez, Diffa da sauran Hakiman yanki da sassa na jamhuriyar Nijar wajan su na musammam su ka zauna. Haka kuma yankin Sarakuna wanda Sarkin Sa’ayrasa mai gayya mai taro ya hakimce, kusa da shi kuma Sarkin Fabarusa ne zaune cikin aminci. Hakan ba k’aramin farantawa jama’a rai yayi ba, wai ashe dai akwai ranar k’arshen gaba tsakanin Sa’ayrasa da Fabarusa? Shin dama akwai rana irin ta yau da za a ga Sarakunan wanga yanki zaune cikin aminci?
Busa na alkgaita ke tashi daga waje, jama’ar Sa’ayrasa kwan su da kwarkwatar su sun yi dandazo cikin d’akin taro, murna gun su ba a cewa komai domin kuwa a yau yunwa zai kau a k’asar su. Ganin shigowar su Yarima Barde tuni dogarai su ka hau yiwa ango kirari. Shi kuwa Yarima Barde sam ba cikin hayyacin sa ya ke ba, amma in aka d’auke Yarima Jafar da Khalil wanda dama sun san halin da abokin na su ya ke ciki babu wanda zai kalle shi ya ce ya na cikin wani hali, sai dai ma ayi tsammanin tsabar sarauta da miskilanci ne yake d’ibar sa.
Sai kuma Mai martaba Sarki Abdulmalik na Fabarusa, wanda kallo d’aya ya yiwa d’an na sa Yarima Barde bayan ya kai gaisuwar sa ga Mai martaba Sarki Sule na Sa’ayrasa, ya gane halin da ya ke ciki, kasancewar wajan mahaifin na shi ya yo gadan kafiya, cijewa da kuma yin burus kamar be san abun da ke faruwa da shi ba, amma in aka tona cikin zuciyar su, Allah kad’ai ya san tafasar da ta ke. Murmushi Mahaifin na sa yayi, cikin ran sa kuwa yacewa ya yi
"d’an mu Abubakar, alkhairi ne mu ka kulla ma ka ba sharri ba, nan gaba za ka gode ma na kwaran gwaske’’
Ganin Yarima Barde durk'ushe gaban Sarki Sule, haka ma abokan na sa biyu, hannun su na dama dunkule suna mai jinjina ga Sarki Sule, fadawan Sa'ayrasa su ka amsa ma su da
"Jinjine dama lafiya alher, gaishe ka Yarima Badde, an gaishe ku samari"
Sarkin Sa’ayrasa kuwa cikin nuna ya amsa gaisuwar ta su shi ma ya dan daga na shi hannun daman a dunk'ule. Yarima Barde ya shiga ran sa saboda kamala da kwarji na sa, ji ya ke ina ma ina ma, ina sirikin na sa ne na gaske, da ya san haka Sarkin Fabarusa zai aikata, da ya bayar da d’iyar sa ko da kuwa ba a san ran ta ba ne.
Ko da Yarima Barde ya had’a ido da Mahaifin na sa, sai ya yi saurin saukar da na sa idanun. Duk wannan abun da ke faruwa a kan idanun yayan Barde, wato Yarima Sadauki na Fabarusa wanda tun da ya ji abun da mahaifin na su ya aikata bisa ga auran da ya d'aura ya k'ara jin tsanar Barde ya dad'u a kirjin sa. Domin kuwa shi ya kamata Sarki ya d'aurawa aure shi da ya ke babban d'an sa ba k'anin sa, hakan da yayi shi ya nuna k'arara Sarki Abdulraman ya fi kaunar Barde, ya kuma fi fifita shi akan Sadauki. Hakan ne kuma Yarima Sadauki ba zai lamun ta, dan ya san ba k'aramin girma aka zubar ma sa ba a idanun jama'a, dole kuma ya d'au Mataki. Idanun sa kan Barde, cike da tsana ya ke duban sa yayin da aka yiwa su Barde nuni ga na su wajan zaman, wato kusa da Yarima Sadauki da abokan sa su ka zauna.
Tun shigowar su Yarima Barde idanun Yarima Nuhu ke kan sa, ji yake kamar ya je ya sheda ma sa wacece Bintu in ya so kowa ma ya rasa. Haka ma Aisar wanda ya san burin Bintu na ganin Yarima Barde ko da sau d’aya ne a rayuwar ta, wai ta rasa wanda za ta kira mai kyawun duniya sai wanga buzu! Cewar Aisar cikin ran sa yayinda wani bakin kishi ya ta so ya mamaye ran sa, shi dai fatan sa Allah ya sa ya sami damar ganin Bintu tin ka a tafi da ita cikin bayin da za su raka gimbiya Binta Fabarusa, ko dan Yarima Barde dole ya d’auke ta, sam jinin su be had’u ba, dan haka Bintun shi ba za ta yiwa matar Barde bauta ba, ko da kuwa duka dukiyar sa za a buk’ata domin mallaka ma sa Bintu, a shirye ya ke ya rasa komai.
Bayan an sami nutsuwa ne aka bud’e taro da addua’a, sannan aka shiga abun da ya tara su a wajan. Su Yarima Jafar sun so su nemi izinin tafiya, amma hakan be samu ba, sai hakura su ka yi su ka zauna kamar gumaka, ba um ba um um, ga abokan Yarima Sadauki da shi kan shi Yarima Sadauki sai harbin iska su ke. Barde kam duk be san ana yi ba.
Sarkin fabarusa ne ya fara jawabi, ya mai nuna farin cikin sa na kulla aminta da auratayya wacce ta kawo k’arshen gaba tsakanin Masarautar ta su biyu. Bayan haka ya gabatar da takardar shedar sun bayar da bashin da masarautar Sa’ayrasa su ka buk’ata, ya kuma ce tun da an zama d’aya, sa iya biya a tsanake sannu a hankali ba tare da tashin hankali ba.
Nan waje ya kaure da ihu da sowa na jama’a, kowa na nuna jin dad’in sa da kuma alfahari da halin girma irin na sarkin Fabarusa. Dogarawan Fabarusa su ka shiga jera kirari ga Sarkin Su, fad'i su ke
"Lafiya Sarkin yakin Sarkin musulmi
Lafiya maida garin wani kango
Lafiya Barden mahadi
Lafiya Sukukun bakaka
Lafiya Darzaza amalen sarakuna
Lafiya ba hau da wani ba sauke wani
Lafiya hana kangara
Lafiya Sakaka babban bako
Lafiya Bango madafar bayi
Lafiya hadarin kasa maganin mai kabido
Lafiya kwankwason jimina mai wuyar shafawa. Lafiya adali, lafiya salamun, salamun salamun"
Jikin sarkin Sa’ayrasa ba k’aramin sanyi yayi ba. Sai da waje ya lafa sannan Sarki Abdulraman ya k’are jawabin na sa da adduar zaman lafiya tsakanin Masarautar da kuma fatan Allah ya bawa shugaban k’asa lafiya.
Sai da sarkin Sa’ayrasa ya sa hannu a takardar ta hanyar amfani da hatimin masarautar ta sa, yayi na sa jawabin na nuna farin ciki da godiya ga masarautar Fabarusa, sannan kuma ya yaba da halin dattako na Sarki Abdulrahman dan har ga Allah ya bashi mamaki matuk’a. ya k’are jawabin na sa tare da fatan alkhairi tsakanin Masarautar biyu. Cikin ran sa ya na alhinin aurar da d’iyar bayin da yayi maimakon d’iyar sa, maimakon ya kawo k’arshen gaba, gudunmawar dad’a k’arfafa gaba yayi muddin sarkin Fabarusa ya fahimci yanda ya haince shi saboda san zuciya.
Daga tawagar shugaban k’asa Kwaminishinan da yayi jawabi ne ya mik’a gaisuwar shugaban k’asa tare da gudunmawar sa na buhuhunan hatsi, shinkafa da dabino ga masarautar ta Sa’ayrsa, wanda sam kyautar ta shi ba burge su ta yi ba, a fad’ar su sai da yunwa ta ci ta cinye su har su ka kai ga neman taimako gun abokan gaba sannan zai wani kawo musu gudunmawar sa na bogi. Kafin kwaminishna ya k’are jawabin sa, wayar Junaidu ta d’au k’ara, ko da ya amsa kiran tuni fuskar sa ta canza, cikin dabara ba tare da ya bari an san halin da ake ciki ba ya ja Aisar su ka yi waje.
A cikin mota ya ke sheda masa ai jikin Shugaban kasa ya dad’a tashi kiran da aka masa kenan, su za su fara yin gaba in ya so sauran tawagar za biyo su a baya gudun kada a d’aga hankalin jama’a. Aisar ya na ji ya na gani haka su ka bar yankin Sa’ayrasa, ya na mai kudirin dawowa da sun sami kan Shugaban k’asa.
Daga d’akin taro kuwa tawagar shugaban k’asa sai neman su Aisar su ka yi su ka rasa, bayan sun kira su ne su ke sheda mu su ai sun yi gaba saboda wani uziri da ya taso, duk da dai ba du sheda mu su ainihin abun da ke faruwa ba, sai da jikin su yayi sanyi matuk’a.
An kamala taro yayinda aka ci aka sha, dan kuwa yau take salla a masarautar Sa’ayrasa. Yarima Jafar ne ya nemi a kai su ga masaukin su da ke su dama nan Sa’ayrasa za su kwana su da tawagar Yarima Sadauki. Amma bakin ciki da kuma Allah Allah da ya ke ya bud'e ido ya gan sa a Fabarusa domin shedawa Mahaifiyar sa cin fuskar da aka masa ya sa Yarima Sadauki fasa kwana, nan ta ke ya juya shi da tawagar sa ba tare da sun jira Sarki ba. Su Yarima Barde kuwa da wasu dogarawa aka had’a su domin kai su masaukin su.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪[8/15, 3:55 PM] +234 703 989 3505: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
0⃣4⃣
Cikin sauri ta tashi tsaye ta gaishe shi da harshen (French) faransanci wanda da dama da shi su ka fi amfani a makaranta. Gaba d’aya ta manta da wani kunyar sa da ta ke ji yanzun da ta gan shi tsaye gaban ta dan kwarjinin da ya mata. Kan ta sunkuye tana wasa da ledar k’wilin ta ya amsa mata a takaice fuskar babu walwala ya ce ‘’me ki ke yi waje lokacin cin abunci?’’
‘’Gimbiya Binta na ke jira ta gama cin na ta sai ni ma na ci nawa’’ ta amsa zuciyar ta d’aya ba tare da ta d’aga kai ta kalle shi ba.
Cike da mamakin amsar ta ta ya ke duban ta, ita sam bata lura da kallan na ta da ya ke ba. Kana ya ce "wacece Gimbiya Binta?’’ jin tambayar na sa Bintu ta bud’e baki,cike da mamaki ta ce "laa ba ka san Gimbiya Binta ba? Yar sarkin Sa'ayrasa fa, wata fara tas kamar d’iyar larabawa, ta na da kwarjini matuk’a’’.
Badaban ran sa a 6ace ya ke ba, yanda ta ke kod’a Gimbiyar ta ta sai da ta kusa ba shi dariya. Amma sai dad’a tsuke fuska ya yi kafin ya k’ara da ‘’ban san wakike magana akai ba, amma abunda na ke so na sani shi ne shin dokar makarantar ce sai wata Gimbiya ta gama cin abunci kafin sauran d’aliban su ci ko kuwa?’’
Tuni Bintu ta fara shan jinin jikin ta dan kuwa tabbas idan hukumar makarantar ta ji wannan maganar matsala zai zame mata. Kana ta ce "iye! Na’am? Dama wai,dama ai..........’’.
"dama me?” ya katse ta ya na mai duban ta. Nan fa Bintu ta shiga cikwikwiya ledar hannun ta, ta rasa amsar da za ta ba shi.
"dokar makarantar ce sai wata Gimbiya ta gama cin abunci kafin sauran d’aliban su ci ko kuwa?’’ ya dad’a maimai ta mata tambayar cikin k’aguwa. Ganin ba ta da niyar amsawa rai 6ace ya furta "menene dangantakar ki da wannan da ki ke kira gimbiya ?ya sunan ki?’’
Cike da tsoro Bintu ta amsa ma sa "sunana Bintu, Bintu Bala Mahuta, ni d’iyar bayi ce, ni ce baiwar da ke kula da Gimbiya Binta ta masarautar Sa’ayrasa.....’’
‘’wannan ne ya bata damar hana ki abunci? Haka ake gudanar da lamarin wannan makarantar? Saboda zalinci? Toh daga yau ya k’are ni Aisar ba na san zalinci kuma ba zan juri ganin zalinci ba’’ ya na gama magana ya juya a fusace ya fara tafiya, ganin haka Bintu da tun da ya fara magana ta gama firgita, ba ta san sanda ta saki ledar k'wilin ta ba, ta bi shi da sauri tare da shan gaban sa, sai ga ta ta zube gwiwowi biyu a kasa. Da sauri ya ja ya tsaya ya na mai duban ta cike da mamaki ganin duk zafin ranar be hana ta saka tafukan hannayen ta biyu k’asa ba ta mai duk’ar da kai kamar wacce ta ke shirin shigewa k’ark’ashin k’asa.
Hankali tashe ta shiga jero masa magiya ta na mai fad’in "tuba na ke, ka gafarce ni, na tuba, ka yiwa Allah da manzon sa kar ka had’a ni da Gimbiya, aradu idan ta ji wannan maganar na kad’e har ganye na,ka min rai, na tuba....’’ ta k’arasa maganar na ta cikin kuka. Aisar kuwa kasa magana yayi ya na mai duban ta cike da tausayawa kana daga bisani ya ce ‘’tashi....."
maimakon ta tashi sai ta dad’a kask’antar da kai ta yi kasa ta na kuka, jin kukan na ta ya ke har ran sa. Idanun sa runtse ya ce ‘’ya salam wannan wata irin yarinya ce mai shegen taurin kai! ki-ta-shi-na-ce’’ a hankali yayi maganar kamar mai koyan magana. Sai a sannan ta tashi, amma har lokacin hawayen ta ke.
Kallan ta yayi na wasu dan dak’ikai, kafin ya mata nuni da inuwar da ya tadda ta zaune ya ce koma can ki zauna ina zuwa. Baki ta bud’e da niyar yi masa musu, amma ko da su ka had’a ido sai ta tsinci kan ta ta na mai fad’in ‘’toh’’ ta yi sauri ta koma k’ark’ashin bishiyar in da ta jingina jikin ta, ta na mai mayar da ajiyar zuciya ganin Aisar shi ma ya juya ya tafi.
Ta na mai addu’ar Allah ya sa ya hakura kar ya dawo har ta samu ta shiga d’akin cin abunci. Sai a sannan ta lura da ledar k’ulin ta a k’asa ta yi sauri ta d’auko ta ka6e dattin da ya mak'ale jikin ledar kafin ta tura cikin aljihun ta dan kuwa shi ma ya fita ran ta. Jim kad’an Aisar ya dawo d’auke da wata yar bakar leda, ya mik’a mata ledar tare da fad’in "gashi maza ki je ki sami waje ki ci’’ ledar ta bi da kallo, wani irin kamshi ke ziyarta hancin ta daga cikin ledar, tuni ta mayar da mugun yawu, ta na mai girgiza kai ta ce "ah ah na gode ai ba na jin yunwa dama’’ "ba kya jin yunwa?’’ ya maimaita cikin sigar tambaya. Kai ta gyad’a masa alamar eh. Amma mai za su ji? ‘’kulululu’’ sautin da ya fito daga cikin ta kenan wanda ya ke gasgata zargin Aisar na Batun Bintu ba ta jin yunwa yasasshen zance ne.
Cike da jin kunya ta sunkuyar da kai k’asa, duk 6acin ran sa sai da ya tsinci kan sa ya na mai murmusawa. ‘’kar6a ki ci maza kafin a koma aji’’ sai da ta d’an yi jim, kafin daga bisani ta sa hannu biyu ta karb’a ta na mai godiya, fad’i ta ke ‘’Godiya na ke, madallah, Allah ya saka ma da alkairi’’ ba ta jira jin amsar shi ba tayi gaba, hannu na rawa ta ke k’ok’arin bud’e ledar dan ganin abun da ya ke, ganin lafiyayya abuncin da ke cikin ledar tuni ta fara k’ok’arin fara kaiwa baki dan ta ma manta da Malam Aysar da ya bi ta da kallo cike da tausayawa har ta k’ure masa. Kai ya jinjina ya na mai shan alwashin maganin wannan zalincin da Gimbiya ta ke yiwa Bintu na hana ta cin abunci cikin d’alibai yan uwan ta. Shin dama har yanzu ana irin wannan zalinci? wannnan wani irin sakaci ne daga hukumar makarantar, da ga alama dai ba banza ta kawo shi makarantar ba, babu mamaki watan rufe makarantar ce ta tashi muddin ana irin wannan zalincin da sanin hukumar makarantar. Da wannan tunanin ya nufi ofishin Malam Hamisu. Yayi rashin sa’a ba ya nan dan haka dole ya hakura ya koma ofishin zaman malamai da k’udirin cikin ran sa.
Yanda Bintu ke cin abunci kamar wacce ta shekara ba ta ci ba ya sa ta saurin gamawa kafin su koma aji. Suna komawa kuwa lokacin koyarwar Aisar ne. Da shigowar sa ba tare da 6ata lokaci ba ya fara abunda ya kawo shi, wato koyarwa. Darasin na sa yau akan "Gaba" ne. Aisar ya fara da tambayar misalan yankuna ko masarauta masu tarihin gaba tsakanin su, ba jamhuriyar Nijar kad’ai ba har mok’otan su. D'aya daga cikin d’aliban ce ta d’aga hannu, in da Aysar ya bata damar amsa tambayar, ta ce "kamar gabar da ke tsakanin masarautar Sa’ayrasa da masarautar Fabarusa’’ Aisar na mai jinjina kai ya ce "haka ne ku tafa mata’’ aji aka d’auki tafi "raf