ta farka. Gwaggo Munari ce ta katse mata jin dad'i ta hanyar jijjaga kafad'ar ta, wannan karan da d'an karfi domin kuwa sun jima da isa Masarautar Fabarusa, yanzun haka kofar fada su ke, Uwalanze har ta fice daga motar amma Bintu na nan ta na baccin asara.
A firgice Bintu ta tashi jin jijjigar ta wuce hankali, ga busar algaita da ke tashi, har da hayaniya da wak'e dake tashi daga bakin mutan Fabarusa da su ka cika kofar fada domin ganin isowar amaryar Yerima Barde.
Ganin alamar Bintu ta tashi, Gwaggo Munari ta shiga gyara ma ta alkyabba yanda fuskar ta zai rufu da kyau, ta na fad'in
"Ko ke fa Gimbiya d'iyar Sarki mai dole, ai ke kuwa bacci be same ki ba"
Kalmar nan ta Gimbiya da jama'a ke kiran Bintu da shi sam ba ya mata dad'i, gani ta ke tamkar ana raina mata iyayen ta, ya ga wanda su ka haife ta amma fin k'arfi zai sa a raba ta da su? In dai haka zama Gimbiya ya ke Allah wadar da irin na Sa'ayrasa.
Ta na kan wannan tunani ne gilashin motar ya sauka, yayinda Jakadiyar Fabarusa ta bayyana a gare su, kana ta ce
"Gide mutan Fabarusa, na cikin gari hallo da na fada, kwan mu da kwarkwatar mu, mun hito domin tarbar amaryar zaki, Yariman mu abin alfaharin mu. Mu na neman alfarmar bayyanar wagga Gimbiya ta Sa'ayarasa, da ta kasance Gimbiyar Fabarusa da ga ranar jiya har illa MashaAllahu"
Gwaggo Munari na mai murmushi ta amsa mata da
"Gimbiyar ta mu, wacce ta kasance fure a gare mu, wacce babu shakka za ta wadata ku da kyawu gami da kamshi da ke tattare da ita, Gimbiya Fatima ta Sa'ayrasa ta amsa kiran mutan Fabarusa"
Jakadiya ta rangwad'a gud'a, tuni waje ya kaure da hayaniya,yayinda mata da yara su ka hau wak'a su na tafi, fad'i su ke
"Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k'aru!"
🐪🐫🐪🐫🐪🐫[8/29, 9:27 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
7⃣
Sidiya ce...✍🏼
Jakadiya ta bud’e kofar motar ta in da Bintu ta ke. Bayi mata guda goma shabiyu, wanda su ka kasu gida biyu sahu su ma jere kan sa sunkuye gaban motar su na jiran fitowar Bintu domin taka mata baya. Idan Bintu ta motsa toh dutse ma ya motsa, sai da Gwaggo Munri ta fito sannan ta zagayo gare ta, hannun Bintu ta lalabu cikin alkyabba, sannu a hankali, cikin azanci kai ka ce Gimbiyar ce da gaske ta fito da Bintu. Tuni bayin nan su ka zube gwiwowin su biyu a k’asa cike da girmamawa. Mata da yara masu waka ba su fasa ba. Cewa su ke
‘’Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!
Mun nema! An ba mu! Mun k’aru!!’’
Jakadiya kuwa ba ta fasa gud’a ba. Tuni hayaniya da sowar jama’a ya rud’a Bintu, har sai da Gwaggo Munari ta fahimta ganin yanda ta cize waje d’aya ta kasa tafiya. Cikin rad’a Gwaggo Munari ta ce da Bintu
‘’yo to ki ka cize nan Gimbiya kya iya wad’uwa ba ki sani ba, gide rufa mana asiri mu tai, ke kawai ki ta salati, hallo ka da ki kuskura ki kai kallan ki ga jama’a, hakan ka iya rud’a ki, maza soma ambaton Allah’’
Nan da nan Bintu ta tsinci kan ta ta na mai ambaton Ubangiji. Tsakiyar Uwanlenze da Gwaggo Munari, Jakadiya daga baya, biye da ita bayi goma shabiyu ne, su ka kutsa ta hanyar da aka tanada na musammam domin wucewar Gimbiya. Ba su zame koina ba sai cikin fadar Fabarusa.
Kansencewar Masarautar Fabarusa ta yi biyun ta Sa’ayrasa a girma da tsari, ba su Ladiyo ba, hatta Gwaggo Munari sai da ta yi da gaske wajan 6oye shawa’an ta ga Masarautar domin kuwa lokacin da su saka k'afar su a katafariyar fadar Fabarusa, sun ga abin mamakin gaske, wato bayan girman fadar na da ban al’ajabi, kuma yadda aka fasalta ko tsara ginin ta shi ma abin mamaki ne. A tak’aice sai da su ka zamo tankamar k’auyawan da su ka shigo birni. Gini ne irin na gargajiya wanda aka kafa harsashin ginin da manyan duwatsu ma su tsada, wad'an su kamu takwas wasu goma. Tsakanin kowace katanga akwai duwatsu masu tsada wad’anda aka yanka su bisa ga ma’auni san’annan aka dasa itacen al’ul daga gefan su. Tsuntsayen fada iri iri ke shawagi, musammam d’awisu da jin su ne su ka fi yawa.
Sai da su kusta sauro gomasha biyu kan su kai ga shiga cikin gidan Sarki, kowanne da na sa irin adon da kayan k’awa, wanda idan su ka shiga wannan su ka shiga na gaban sa sai su ka ashe na baya ba komai ba ne idan aka had’a sa da na gaban sa. 'Bangarn uwar gidan Sarki Abdulrahman, wacce ake kira Goggon nan aka sauke su. In da aka zaunar da Bintu bisa shimfid’a na musammam da aka ta na dar mata daga tsakiyar falo, yayinda su Ladiyo, Hansai, Lanta da Maman Cangwai su ka yi zaune daga gefe matsayin su na bayin Gimbiya.
Tuni Barori da Bayi su ka shiga kai kawo da hidima domin tarbar baki cikin aminci ta hanyar tabbatar da ba su bawa Masarautar su kunya ba. Kayan marmari na daga ‘ya’yan itace ne, nama na k’arama da babban dabba kai har da ma na d’awisu, su dubulan ne, caccabe, alkaki da nakiya komai bajau sai wanda jama'ar Sa’ayrasa su ka za6a. Gwaggo Munari na mai jinjina kai cikin ran ta take fad’in
‘’ma su abu da abun sa, gaskiya dukiya cikin wanga masarauta ba a cewa komai! D’iyar bayi ke kuwa Allah ya yankewa kakar saka, amre cikin wanga Masarauta shi an baiwa’’
Ciki su ka bud'e su ka ci su ka yi nak. Amma ita ko Bintu ruwa ma kasa sha ta yi bare ta kai ga cin abinci duk da kuwa azababban yunwa ne ya addabi cikin ta. Bayan an tabbatar su huta ne wata baiwa ta zo ta ce da su idan sun shirya za ta kai su ga masauk’in su domin Gimbiya Fatima ta shirya ta sami fitowa zuwa taron wankan amarya wanda za a yi nan ba da jimawa ba.
🐫🐪🐫🐪🐫🐫
[8/29, 9:30 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
8⃣
Sidiya ce.....✍🏼
Shiryayyan d’aki mai had’e da 6and'aki aka aje su Ladiyo, su Bintu kuwa d’aya daga cikin d’akunan Goggon nan a matsayin ta na uwar gida aka sauke su kan a gama wankan amarya a mik’a ta ga na ta 6angaran.
Su na shiga masaukin na su ba da jimawa ba, wata baiwa ta sake dawowa d’auke da kaya, gaban Bintu wacce ke zaune bisa gado har lokacin ba ta bud’e fuskarta ba baiwa ta zu6e, ta na mai aje kayan gaban ta, ta ce
‘’ an gaida Gimbiya Fatima, wagga kaya tsaraba ne da ga Goggo nan, ta ce a shedawa Gimbiya Fatima ta sanya su yayinda za ta hito wajan wankan amarya nan ba da jimawa ba’’
‘’Gimbiya Fatima ta amsa, ta na godiya’’
Cewar Gwaggo Munari. Bayan fitar baiwar Gwaggo Munari ta yaye alkyabbar Bintu, sai ga ta ta yi wuri wuri da ido.
‘’Gimbiya yanzun ga ba lokacin tuntuntuni ba ne, kin dai san dalilin da ya sa ki wanga Masarauta da kuma a gurbin wacce ki ka zo, gwara dai ki sake shawara ki nutsu in har ba so ki ke ki rasa ran ki sa’annan ki haddasa yaki da gaba wanda ka iya halaka ta mu Masarauta gaba d’aya’’
Fad’in Gwaggo Munari cikin gazawa da halayyar Bintu dan kuwa idan ba ta yi da gaske ba ko shakka babu asirin su mai tonuwa ne. A sanyaye Bintu ta ce
‘’ina tuba....’’
‘’ba tuban ki mu ke buk’ata ba!’’
Gwaggo Munari ta katse Bintu, kana ta k’ara da
‘’ Aikin ki mu ke buk’ata Gimbiya! Wanda za ki fara yanzu ta hanyar zama Gimbiya ba d’iyar bayi ba. Allah ya mi ki zubi irin na jinin mulki, kowa ya gan ki ya san hakan nan Allah ya yo ki, ba ki gada ba amma Allah ya baki su a halittar ki, Dan haka tak’ama da isa shi na ke so daga gare ki, ki saka a ran ki wannan dama ne da Allah ya baki dan jin dad'in rayuwa da kuma taimako ga Masarautar mu, idan asirin mu ya tonu gaba d’aya farin cik’in masarautar mu ne zai koma ga zubar jini, ina fatan kin fahimce ni?’’
Bintu ta gyad’a kai. Kana Gwaggo Munari ta dafa kafad’ar Bintu ta ce
‘’madallah da d’iya ta gari. Sai ki yi shiri yanzu su Ladiyo za su zo su had'a mi ki ruwan wanka. Hakuri za ki yi na san kin saba yiwa kan ki komai amma daga yau komai yi mi ki za ake yi, ki jure Bintu wata rana sai alkhairi’’
Bintu ta dad’a jinjina kai. Ana hakan kuwa su ka ji an sake turo kofa an shigo. Maimakon Ladiyo da Gwaggo Munari ta ce, Lantana ce baiwar da Yarima Nuhu ya za6a ta musammam domin kular masa da al’amran Bintu ta shigo ta zube gaban su. Gwaggo Munari na mai duban ta tace
‘’Lantana gide ke ce mai shirya ruwan wankan ne? yo to ina sauran? Kar dai sun tsaya kallan kauye mu ka biya ku fa sai mu makara!’’
Lantana waccen ita dama da ka gan ta ka ga zubin munafunci, dan ko magana ka ke da ita haka za ka ga ta na sinsin da idanu sam ba ta bari a ga kwayar idanun ta. Ta kada baki ta ce
‘’ai ga su nan tafe, sauri na yo dama na shirya ruwan wankan kada a makara’’
Jin haka Gwaggo Munari na mai mata nuni da bayan gidan da ke cikin d’akin ta ce
‘’yauwa madalla da ke, maza je ki ga bayan gidan can shirya mata gide’’
Sim sim ta shige bayan gida. Sai da ta fara taran ruwa sannan ta shiga had’a ruwan da turaruka iri iri kamar yanda su ka saba had’a ruwan wankan Gimbiyoyi. Ko da ta zo kan turaren karshe, sai ta faki idanun Gwaggo Munari ta tabbatar hankalin ta na kan su Ladiyo da shigowar su ke nan, ta na mu su bayanin yanda ta ke so su kasance wajan taro. Sannan ta jawo kofar bayi ta rufe. Gefan zanin ta ta kwance, ta dauko wani kullin magani, cikin sauri da azanci ta bud’e maganin ta na mai zazzage shi cikin ruwan wankan Bintu. Tuni wani irin bakin hayaki mai wari ya taso daga ruwan yayi sama, ita kan ta Lantana sai da ja baya ta na mai toshe hancin ta cikin tsoran kada fa su Bintu su ji duk da dai Yarima Nuhu ya tabbatar mata babu wanda zai ji warin bayan ita da ta zuba. Sai da ruwan ya dena kumfa da hayaki sannan ta mayar da sauran kullin maganin cikin zanin ta ta kulle, ta fito hankali kwance kamar ba ta aikata komai ba.
🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[8/29, 9:33 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
9⃣
Sidiya ce......✍🏼
Fitowar ta ba da dad’ewa ba Gwaggo Munari ta sanya Bintu wankan dole dan kuwa ba da san ran ta ba. Da taimakon su ladiyo da Hansai Bintu ta fito fes cikin doguwar riga ruwan d'orawa, rigar da Goggon nan ta aiko mata. Material ne mai tsada ke, sai kuma mayafi kore mai turawa da ratsin ruwan d'orawa. Gwaggo Munari ruke da hannun ta domin kuwa ita ta ke gane mata hanya su ka fito, Su Ladiyo biye da su yayinda aka mu su iso zuwa babban zaure in da mata da iyalan Sarki ke jiran isowar su.
Babban zaure ne wanda ya fi k’arfin a k’ira sa da zure sai dai ko d’akin taro, tsawon sa kamu d’ari, fad’in sa kamu hamsin. Haka kuma ko wacce kusurwa na zauren an masa ado da itacen al’ul a bisa ginshishik’an sa. Bayan ga dadduma mai kulliyar jikin damisa da ke shimfid’e tun daga fari har zuwa k’arshen zauren da kuma tintin masu adon jikin damisa da ke baje bisa daddumar, akwai duwatsu wanda aka auna sa’an nan aka yanka su da zarto ciki da baya daidai da juna, aka jera su zagaye cikin zauren tamakar kujerun zama irin na zamani. Haka kuma bangon zauren zane ya ke da tambarin Masarautar Fabarusa.
Cikin zauren su ka tadda dukkanin iyalan Sarki Abdulrahman tare da y'anuwa da abokan arziki wanda su ka zo domin ta ya su murna. Matan Sarki Abdulrahman uku wanda su ka had’a da Goggon nan (uwar fada), sai ta biyu wacce su ke kira da Goggo ta dole(uwar dole) sai ta ukun wacce ake kira Uwar Soro, wacce itace mai k’arancin shekaru cikin matan sarki. Kowacce hakimce, k’ishingid’e bisa tuntin. Gaban su kuma wani tulu ne wanda aka masa ado da azurfa cike da ruwa mai d’auke da turare da garin lallel.
Haka kuma ‘ya’ya da jikokin sarki da na su wajen daga gefe wanda d’irga su ba k’aramin aiki ba ne kasancewar ‘yay’an sa mata ma su aure da ‘ya’ya sun kai su goma sha takwas, kuma dukkanin su ba su yi k'asa a gwaiwa ba haka su ka zo da sassa da yankunan Jamhuriyar Nijar domin tarbar amaryar d’an uwan na su. Duk da dai ciki akwai mu su bakin cikin lamarin kasancewar ciki d’aya su ke da Yaremi Sadauki. Musammam Yaya Mai Soron Baki, babbar d’iyar Sarki Abdurahman da mai bin mata wato Yaya Jidda wanda su 'ya'yan Goggon nan.
Wajan da aka tanadarwa Bintu gaban su Goggon nan aka zunar da ita. Tun da ta yi wanka da ruwan nan na Lantana hankalin ta ya ke a tashe, gashi gaban ta sai fad’uwa ya ke, ta na son fad’awa Gwaggo Munari amma ta tsoran za ta yi zatan fad’an da aka mata ne be shige ta ba, dan haka a dole ta hakura da ikon Allah. Maimakon Gwaggo Munari ta zauna gaban ta, sai gani ta yi ta ja gefe daga wajan su Gwaggon nan. Cikin girmamawa ta mik’a gaisuwar ta tare da damk’a amanar Bintu gare su bisa ga al’ada. Goggon nan wacce a ran ta ta yi farin cikin fasa auren d'iyar Sarkin Sa'ayrasa da Sarki Abdulraman yayi, ta kuma yi bakin cikin aurar da aka aurawa Barde a maimakon d'an ta Sadauki, ta fara kar6ar amana ta hanyar saka hannu ta bud’e mayafin Bintu da ke gaban su, tuni Bintu ta yi k’asa da idanun ta cikin fad’uwar gaba. Sai da ta kalli fuskar Bintu na d’an wani lokaci ta na mai yamutsa fuska ta saki mayafin ba tare da ta rufe fuskar gaba d’aya ba. Kana ta ce
‘’ni Munzaratu jikar Sarki Abdulrahman na difa, d’iyar Sarki Abdulmuminu iii na Agadez, matar Sarki Abdulraman ii na Fabarusa, na bud’e fuskar amaryar dan mu, d’iyar Sarkin S’ayrasa, Sarki Sule Inuwa Magaji da zannuwa hamsin, kallabi hansin tare da bayi guda uku’’
Jakadiya ta rangwad’a gud’a, yayinda waje ya d’au sowa. Ita Bintu ta yi k’asa da idanun ta, ji ta ke kamar ta dan ta k’arasa rufe fuskar ta gaba d’aya. Amma me za ta ji? Goggo ta dole ce ta sa hannu ta k’ara yin baya da mayafin Bintu yanda za ta ga fuskar Bintu da kyau, kafin ita ma ta jero sunan ta da nasabobin iyayen ta, ta bud’e fuskar Bintu da silallan gwal. Ita kuwa Uwar Soro da tashi na ta bajintar da dawakai tare da rak’uma ta bud’e fuskar Bintu. Tuni Bintu ta zama mai arziki da kadarori, su Ladiyo cikin ran su sai mamakin baiwa da Allah yayiwa Bintu, su na jin ina ma dai su ne.
Bayan da matan Sarki suka gama budar ka, sai kuma sauran 'yan uwa da abokan arziki, yayye da k'Annan Barde su ma su ka nuna ta su bajimtar.
Bayan an gama ne Jakadiya ta mik’a wa matan Sarki tulu. Matan sarki su ukun nan su ka tsaya bisa kan Bintu su na mai tsiyayo mata ruwan cikin tulun kad’an kad’an bisa kan ta, yayinda Jakadiya ke bada wak’a jama’ar wajan na amsa mata
"Ayyare daure jure
ayyaraye daure jure!
zaman gidan wani tilas ne!
ba kan ki ne aka fara
ba da kan ki ne aka fara ne
da kin ci kuka kin k'oshi
ke yar tsohuwa mai 'yar tulu
Allah ya kar ki watan gobe
Mu ci gumba’’
🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[8/29, 9:37 PM] +234 803 440 2664: ®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!(2)
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
1⃣0⃣
Sidiya ce....✍🏼
Ana gama wankan amarya Bintu ta ja jik’akken mayafin ta ta rufe fuskar ta tana mai shar6ar kuka. Ba tare da 6ata lokaci ba d’aya bayan d’aya sauran iyalan Sarki su ka dinga zuwa Jakadiya na gabatar da su, har su ka k’are sannan aka rufe taro da addu’a. Da aka gama maimakon a kai Bintu d'akin auren ta, 6angare ne na musammam cikin gidan Sarki, sai wani 6angare aka sake kai ta na daban daga cikin 6angaran Goggon nan wanda ya kunshi d’aki biyu kowanne da bayi sai kuma falo. Nan za ta zauna har sai sanda ta kai budurcin ta d’akin mijin ta. Za6in bawai d’aya daga cikin bayin ta wanda za su na kwana 6angaran ta aka bata. Gwaggo Munari ce ta za6a mata Ladiyo dan kuwa ta fi yabawa da hankalin ta, sauran kuma wuni za su na yi, idan lokacin bacci yayi ko kuwa Bintu ta sallame su sai su koma 6angaran da aka tanadarwa bayi.
Yarima Barde kuwa duk