BAYAN MUTUWA

Author :  Abdulaziz Sani Madakin Gini Category :  Adventure

Chapter   7 / 7

18K to 20K   out of 20K words

a iso birni misira sai suka
tsaya suka yada zango shi kuma makanu ya wuce gaba
izuwa birni misira. Bayan tafiyar makanu ne Inzal da
Karimat suka fara hira inda ya dubeta yace.
“To ke yanzu ta yaya zaki sami damar sato sarqa
dake wuyanta?” Koda jin wannan tambayar sai
karimat ta sauke ajiyar zuciya cikin alamun karayar
zuciya sannan ta dubi Inzal tace “Bani da wta dabara a
cikin zuciyata amma kuma ka sani cewa ni ban tava
karaya bisa kowane irin aiki da zanyi ba komai

110

BAYAN MUTUWA

wahalarsa da haxarinsa, kai kuma fa? Shin kana ganin
sato Amzad abune mai sauqi, alhalin dole Gimbiya
lashmin ta saka cikaken tsaro tunda tasan dole attajiri
Huzulu ya saka a farauceshi” Inzal ya numfasa yace.
“Maganarki gaskiyace amma ki sani indai gari
yayi duhu a lokacin da na shiga cikin birni misira to
ko da gaba xaya dakarun qasar suka kewaye xakin to
sai na shiga” Koda gama faxin haka sai suka ga wata
gada ta giftasu cikin hanzari Inzal ya miqe tsaye
zumbur yace.
“Ke jirani anan ina zuwa” A guje ya bi wannan
gadar izuwa cikin daji karimat ta bishi da kallo har sai
daya qule ya vace mata da gani faruwar hakan ke da
wuya sai taji motsin tafiya a can bayanta nesa kaxan
da sauri ta juya ta ruga ta vuya a can bayan bishiya
kawai sai taga wasu mutane sun nufi can hanyar da ta
nufi wani qaton kogo, nan take zuciyarta ta cika da
tambayoyi su wane waxannan mutanen kuma me su
ka zo yi alhalin gari ya soma duhu kuma akan hanyar
da babu mai binta domin hanya ce data nufi gidan

111

BAYAN MUTUWA

boka zullazi tana gama faxin haka sai ta bi bayansu da
sauri don kada su vace mata da gani amma da taga ta
soma hangosu sai ta riqa binsu a hankali don kar suji
motsinta su waigo su ganta.
Haka suka ci gaba har suka iso bakin kogon tana
ganin haka sai ta kuma voyewa a bayan wani dutse, ba
wasu bane waxannan matan face Gimbiya lashmin da
kuyangarta koda suka qarasa sai tace “Ya shugaban
bokaye buxe mun qofa” Kafin Gimbiya Lashmin ta
gama rufe bakinta sai ga tsaunin ya rabe gida biyu
wata qofa ta bayyana, su Gimbiya Lashmin suka shiga
bisa ga mamakin Karimat sai taga qofar bata rufe ba
don haka sai ta nufi wajen da azama ta shige, ai kuwa
tana shiga sai qofar ta koma ta rufe karimat ta juya a
xan tsorace ta kalli qofar amma sai ta dake ta juya ta
kunna kai cikin gidan.
Wani falo ne qawatacce wanda komai na cikinsa
anyisa da zallar zunare, wata karagace guda xaya jal
wacce aka yita da shuxin zinare aka yita, zaune akan
karagar wani dogon mutum ne mai matuqar kwarjini

112

BAYAN MUTUWA

da cikar haiba, gashin kansa sajensa gami da gashin
baki duk farare fat. Kallo xaya zaka yi masa kasan
cewar ya haura shekara tamanin a duniya koda ya
gango Gimbiya lashmin da Ilaila sun nufo shi hannun
Ilaila xauke da akwatin lu’u lu’u sai fuskarshi ta
faxaxa zuwa ga murmushi kafin su qaraso tuni ya
miqe ya taresu fuskarsa cike da murmushi.
Cikin girmamawa boka zillazi yace “Barka da
zuwa ya sarauniyar duniya, ki sani cewar ya Gimbiya
yau shekara sittin kenan ina zaune ina jiran wannan
ranar da za ki zo ki damqa mun wannan akwatin ta
zinare da hannunki, tabbas kin gama cika mun
wannnan burin nawa na duniya ke ma ki sani cewar
zuwa gobe da yamma naki burin zai cika” Da jin haka
sai Gimbiya lashmin ta yi murmushi ta amshi akwatin
lu’u lu’u daga hannun ilaila ta miqa masa koda ya
amsa sai suka ji an zabga wata tsawa mai qarfi wacce
ta tsorata Gimbiya lashmin amma sai suka ga boka
zallazi ya qyalqyale da dariya ya juya ya nufi inda aka
ajiye wata bishiyar qarfe ta zinare, yana zuwa ya xora

113

BAYAN MUTUWA

akwatin akan bishiyar faruwar haka sai akwatin ta
narke ta haxe da bishiyar kamar ba’a tava xorata a
wajenba kuma sai aka sake zabga tsawa a karo na biyu
wacce tasa gidan gaba xaya ya girgiza Gimbiya
lashmin da ilaila sai da suka faxi suka yi saurin
miqewa.
A lokacin boka zallazi ya waigo ya dubi su
Gimbiya ya yi murmushi sannan ya taho zuwa ya
garesu yace mata “Yake gimbiya kiyi sani cewar yau
ko raina kike so zan baki, domin kin cika mun burina
daya gagari iyayena da kakanina, nasan cewar baki da
buri daya wuce ki amso dukiyar Amzad daga hannun
attajiri Huzulu kuma ki kawo qarshen zalluncinsa,
kuma kina son mallakar amzad a matsayin abokin
zamanki na dindin” Koda Gimbiya taji haka sai ta yi
murmushi tace.
“Duk abinda ka faxa gaskiya ka faxa”.
“To nima dole na sallama komai nawa bisa sa’a
kuma wanda zai miki jagora wajen cika wannan burin

114

BAYAN MUTUWA

naki mutum xaya yana nan cikin kogon tare da mu”Jin
haka sai su Gimbiya lashmin suka soma waige-waige
amma ba su ga kowa ba sai tace masa.
“Kace mu huxu ne amma ni banga kowa ba, sai
mu uku” Jin haka sai ya qyalqyale da dariya kafin
kuma ya murtuke fuska yace.
“Ya karimat mai sa’a ya kamata ki fito haka ai ina
sane na bar qofar a buxe kika shigo” Koda jin haka sai
tabar bayan ginin data vuya ta fito su Gimbiya da
Ilaila suka qare mata kallo suka ga basu tava ganin
mace kamarta ba.
Boka zallazi ya tako ya qaraso zuwa gareta ya zo
ya tsaya yadda suna jin numfashin juna yace mata
“Yau shekara goma sha shida kenan ina jiran rana da
zaki xauki fansa iyayenki da sarki varayi ya kashe
miki to yau ga dama ta samu mudin zaki yadda ki
haxa kai da sarauniyata, shin za ki yi amfani da
wannan damar ne ko za ki zavi xan abinda attajiri
Huzulu yace zai baki? Ki sani idan kika taimaki

115

BAYAN MUTUWA

sarauniya zata baki dukiyar ba zaki kasheta ba har
qarshen rayuwari kuma ba zaki iya kasheta kuma zaki
zama maxaukakiya wato za ki zauna a cikin ma su
mulki riba biyu kenan kin jefi tsuntsu biyu da dutse
xaya”Koda boka zullazi ya zo nan a maganarsa sai
karimat ta yi murmushi tace.
“Ya maxaukakin boka ai ka fini sanin kaina shin
yanzu ta yaya zan bada gudumawa a cikin wannan
maxaukakin aikin?” Koda ya ji haka sai ya yi
murmushi yace.
“Zan baku wani taimako yanzu nan yadda ku uku
nan za ku tafi can fadar Darul uzur ku yaqi duka
dakarun ku kamo sarki varayi da attajiri Huzulu ku
kawo su cikin birnin misira a wulaqance ku yi masa
hukunci da kuka ga dama” Ya dubi karimat yace
“Yanzu zan baki amsar tambayarki” Yana rufe baki ya
nufi wata qofa ya buxe ya shiga jim kaxan sai ya
dawo xauke da kayan yaqi guda uku da takobi, mashi
da kuma wata hular qarfe zalla ya miqawa lashmin
takobin ita kuma karimat sai ya abata mashi sannan ya

116

BAYAN MUTUWA

miqawa ilela hular qarfe duk su uku suna riqe da
kayan yaqin sai suka ji wani irin qarfi na musamman
ya shiga jikinsu cikin matuqar mamaki lashmin ta
dubi boka zallazi tace.
“Ya kai babban boka wannan wanne irin kayan
yaqi ne haka na ma su qarfi sihiri. Na rantse da gemun
mahaifina yanzu ina jin zan iya shafe kwana da yini
ina yaqi” Ya bushe da dariya yace.
“Ai kwana bakwai za ki yi batare da kin gaji ba, ki
sani babu wani kaifi ko tsini da zai tava tasiri a tare
dake, wannan takobin dana baiwa gimbiya sunanta
saiful lujara, mashin dana baiwa karimat sunan shi
galilil haras, ita kuma hular dana baiwa Ilaila sunanta
Lamsara, ba a tava yin kayan yaqi da suka kai wannan
daraja da kuma sihiri ba, kuma sunfi shekara dubu
xaya da xari uku a hannun kakanin kakanina, yanzu
na baku wannan kayan domin ku kawo qarshen
zallunci attajiri Huzulu domin idan aka sake ya
mallaki birnin misira to zai mallaki tsafina da kuma
kayan yaqinan, ku sani kuma idan kun gama yaqi kun

117

BAYAN MUTUWA

samu nasara waxannan kayan yaqi za su vace su koma
can qasan teku su ci gaba da zamansu kuma har abada
ba za a kuma samun wani mahaluki da zai xauko su
ba har duniya ta gushe, maza ku tafi fadar darul uzur
domin aiwatar da wannan babban aikin” Koda jin
haka sai Gimbiya lashmin da karimat da Ilala suka
juya suka nufi hanyar fita.
Lashmin ta zare takobin saiful daga cikin kubeta,
ilela ta saka hular lamsara, ita kuma karimat ta
wulwula mashin galilin haras, bisa ga mamaki sai
sukaga sun fice fit ta cikin garu sun nausa da gudu
cikin daji wani irin gudu ban al’ajabi suke yi.
Saboda qarfin gudun ya kai na tauraruwa mai
wutsiya koma duk abinda suka riska a gabansu
tsalleke shi suke su wuce komai faxinsa da tsawonsa
maimakon su shafe rabin sa’a kafin su isa fadar Darul
uzut sai gashi cikin daqiqa biyar kacal sun isa ai kuwa
sai dakarun sarki varayi suka ta so musu aka
ruguntsume da wani azababben yaqi, kamar mace ta
saka tsintsiya ta share qofar xakinta haka Gimbiya

118

BAYAN MUTUWA

lashmin da Ilela da karimat suka karkashe dakaru
dubu uku da xoriya.
Sai gasu a cikin fadar tsulum sun bayyana a gaban
su attjiri Huzulu da sarkin varayi, cikin firgici sarkin
varayi da attajiri Huzulu suka zare makamai suka yi
xauki kansu lashmin da sara da suka, ko da
takubbansu suka haxu da saiful lujara da galili haras
sai suka narke suka zama ruwa abinda ya yi matuqar
ranazana su ke nan, nan suka zube qasa kafin su taso
tuni Ilela ya bayyana a gabansu ta gwara musu hular
lamshara nan take suka baje a wajen sumammu.
Lokacin da sarkin varayi da attajiri Huzulu suka
farfaxo sai suka tsinci kansu a zube a qasa a tsakiyar
fadar birnin misira, attajiri Huzulu na duba gabansa
sai ya yi arba da Gimbiya Lashmin da Amzad a zaune
akan karaga xaya yana kallonsa yana masa murmushin
mugunta, nan take Amzad ya miqa wa gimbiya hannu
ya ta saka masa sarqa a cikin hannunsa ya soma juyata
akan fuskar attajiri Huzulu yace.

119

BAYAN MUTUWA

“Wannan sarqa ta amso mun haqqina dake
wajenka kuma ta samar mun matsayi da xaukaka,
duka dukiyar daka tara yanzu ta zama tawa kai kuma
tsireka za ai bisa laifin fashi da makami tare da
abokinka sarkin varayi” Yana rufe baki sai ga sarki
sairan ya shigo fuskarsa cike da murmushi yace.
“Tabbas yanzu za a tsireka”
Masha Allah.
QARSHE.

120


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

7 / 7