Author : Abdulaziz Sani Madakin Gini Category : Adventure
xaya daga cikin aljanun yana
qyaqyata dariyar farin ciki, take aljanin ya zube qasa a
gaban sa shi kuma sai ya haye bayan aljanin ya tashi
dashi sama.
Gaba xaya sauran aljanun ma sai suka tashi
saman suna masu rufa masa baya. Kafin cikar daqiqu
sun luluqa izuwa qololuwar sararin samaniya.
71
BAYAN MUTUWA
Suka vace vat! A cikin gajimare,a sannane
sarkin yaqi ya miqe tsaye zumbur ya shiga karanta
waxansu xalasiman tsafi yana tofawa yaransa
waxanda suka haukace da waxanda suka suma
sakamakon ganin waxannan mugayen aljanun.
Da qyar da sixin goshi ya dawo da su cikin
haiyacinsu sannan suka sauko daga kan wannan
tsaunin suka koma izuwa cikin gari cikin tsananin
fargaba da tashin hankali.
Amzad yana cikin xakinsa a kwance ya yi
shiru lokaci zuwa lokaci yana juyawa ya kalli
mahaifiyarsa dake kwance, tana barci cikin kwanciyar
hankali ga mamakinsa sai ya ji wani daxi ya lulluve
masa zuciya.
Tun tsawon lokacin daya taso a duniya bai
tava ganin mahaifiyarsa yana yin barci mai daxi da
nutsuwa kamar daren wannan lokacin ba. Hakan yasa
shi ya miqe a hankali ya komo tsakiyar xakin ya
zauna yana dube-dube.
A lokacin mamaki kuma ya kama shi, ba
komai ne yasa yake wannan mamakin ba face har
yanzu ya kasa gano dalilin daya saka Gimbiya
72
BAYAN MUTUWA
Lashmin ta yi musu wannan taimakon, tabbas yasan
ruwa baya tsami banza.
Duk da haka kuma sai ya ji wani tsoro ya
lulluve masa zuciya, ba komai ne yasa fargabar a
zuciyarsa ba face tunano attajiri Huzulu da kuma
tsananin hatsabibancinsa, tabbas yasan ba zai barsu a
haka ba, saboda har yanzu yana tuna irin arangamar da
suka yi da shi a farkon lokacin da aka kai masa
samace akan Amzad ya kai qarasar gaban sarki domin
kwato musu dukiyarsu.
Sun haxu da attajiri Huzulu ne a kasuwa yana
zaune a wata rumfarsa shi kuma Amzad ya koro
jakunan xauke da qasa yana zagaya kasuwa da su,
cikin sauri ya saka aka kirawo masa Amzad, bai yi
wata-wata ba ya shiga rumfar ya same shi.
A wulaqance ya dubi Amzad yace masa “Har
girman wuyanka ya kai da zaka shigar da ni qara
gaban sarki? To ka sani kai baka isa ka amshi ko sisi
daga wajena ba, kuma duk duniyar nan babu wanda
zai iya kwato maka koda sisin kwabo daga hannuna”.
Jin haka sai Amzad yace masa.
“Ai duk taqamarka baka fi qarfin hukuma ba”
Jin haka sai attajiri Huzulu ya qyalqyale da dariya.
73
BAYAN MUTUWA
“Yaro man kare, tabbas har yanzu baka san
wane attajiri Huzulu ba, don haka idan kana cin qasa
ka kiyayi ta shuri, na kara da mahaifinka ma bai samu
nasara ba bare kuma kai, ai tsiya dai ka gamu da ita
kuma haka za ka ci gaba da rayuwa a cikin tsananin
talauci har zuwa qarshen rayuwarka, ni kuma attajiri
Huzulu hasken rana ne idan na fito tafin hannu baya
tava kare shi” Jin haka yasa Amzad ya juya cikin fushi
yana faxin.
“Ni kuma zan tabbatar maka sarki goma
zamani goma, duk yadda ka kai ga samun nasara akan
wasu to ni zan samu nasara akan ka” Ya fice daga
rumfar yabar attajiri Huzulu zaune cikin vacin rai.
Amzad ya sauke numfashi a hankali sannan ya
soma girgiza kansa, tabbas yasan shu’umanci attajiri
Huzulu kuma yasan ba zai tava barin su ba dole ya
nemi kawo musu hari, don haka a daren yau ya
kamata ya yi tunanin mafita tun kafin gari ya waye.
**
Al’amarin gimbiya Lashmin kuwa lokacin da
ta baro turakar mahaifinta sarki sairan cikin tsananin
baqin ciki sai ta koma can tata turakar ta zauna tana
74
BAYAN MUTUWA
tunani da nazari. Da farko sai ta miqe tsaye zumbur da
nufin ta fito ta kirawo dakarun dake tsaron lafiyarta su
rakata izuwa can gidan sarki dake bayan gari domin
taje ta nunawa Amzad wanan sarqa tasa dake
hannunta ta tuna masa da duk abinda ya faru sa’adda
suna yara.
Domin su qulla sabuwar soyayya a yanzu
amma data tuno da batun attajiri Huzulu sai ta fasa
fitar ta kama kai kawo a cikin turakarta kawai jira take
taga dawowar sarkin yaqi domin ta ji abinda ya faru.
BAYAN MUTUWA 6
Ai kuwa tana cikin wannan haline shugabar
kuyanginta ta shigo cikin turakarta a ximauce da sarki
tace.
“Ya shugabata ga sarkin yaqi can ya shigo
falonki da gudu yana ta faman haki”.
75
BAYAN MUTUWA
Koda jin haka sai Lashmin tayi murmushi tace
ai nasan haka zata faru.
“Bari naje naji daga bakinsa” Nan take
Gimbiya Lashmin ta nufi babban falo na turakarta da
sauri. Da zuwa sai ta iske sarkin yaqi a tsaye yana kai
kawo cikin alamun tsananin damuwa.
Koda sarkin yaqi yaga Gimbiya ta fito sai ya
taho gareta da sauri ya zube qasa bisa gwiwoyinsa
saboda biyayya sannan ya buxe baki da nufin ya yi
mata bayanin abinda ya faru amma sai yaji ta tari
numfashinsa tana mai cewa.
‘Kada ka vata miyan bakinka ya kai sarkin
yaqi, na sani cewa attajiri Huzulu ya gudu daga
kurkuku a halin yanzu, abin da nake so na sani kawai
shi ne shin aljanune suka zo suka kuvutar das hi ko
kuwa dakarune na mutane?” Cikin tsananin mamaki
sarkin yaqi ya xago kai ya dubi Gimbiya Lashmin
yace.
“Ya shugabata yaya aka yi kika san duk
wannan al’amarin?” Lashmin ta yi doguwar ajiyar
zuciya tace.
“Ai mutum baya fita yaqi sai ya yi tanadi
gami da nazarin abokin gabansa, dole kasan
maqiyinka ka kuma san qarfinsa da qarfin shirinsa
76
BAYAN MUTUWA
kafin ka tunkare shi, ko ba haka bane?” Sarkin yaqi ya
gyaxa kai yace.
“Wannan haka yake ya shugabata” Gimbiya
Lashmin ta zuba masa idanu tana kallon shugaban
sarkin yaqi qasar cike da jimamin abinda ya faru kana
kallonta kasan ranta ba qaramin vaci ya yi ba,
musamman domin tun tsawon zamani babu wani
mahaluki daya tava guduwa daga wannan kurkukun
sai yau da attajiri Huzulu ya tsere.
Suka yi shiru na wani lokaci kafin can ta furza
da numfashi cikin vacin rai.
77
BAYAN MUTUWA
G
imbiya Lashmin taje ta zauna akan
wata kujera sannan ta dubi sarkin
yaqi ta yi masa umarnin shima ya
zauna, ya miqe ya zauna akan kujerar
ba tare da vata wani lokaci ba ko gardama ba sai ya
miqe ya zauna akan kujerar dake fuskantar tata.
Take sai wata kuyanga ta kawo musu
shayi,kowannansu ya karva suka fara sha, sai da
gimbiya Lashmin ta kurvi shayin sau uku sannan ta
ajiye kofin akan teburin dake gabanta sannan ta dubi
sarkin yaqi a cikin nutsuwa tace.
“Tun ina yarinya qarama yar shekara bakwai
na gane cewa attajiri Huzulu yafi qarfin kowa a
qasarnan domin hatta mahaifina tsoronsa yake ji, tun a
sannan na fara tunanin hanyoyin da zan bi na yaqe shi,
bisa dole na riqa bincike cikin sirri akansa har sai dana
gano iya qarfin arziqinsa.
Iyakakar qarfin sihirinsa na tsafi da kuma
dukkanin mutunen dake yi masa biyayya a cikin
78
BAYAN MUTUWA
qasarnan da wajenta, hakan yasa na gano ba zan iya
yaqarsa ba ko kawar da shi ba face na nuna masa kaidi
irin na mu na mata, wato fanin siyasa da kuma gano
babban lagonsa guda xaya.
Ta hanyar siyasa na soma dakushe girmansa
da kimarsa a idon mutane, bisa wannan daliline nasa
aka kamashi aka kai shi kurkuku, ina sane zai iya
guduwa daga kurkukun amma kuma bazai yi saurin
xaukar mataki ba a kaina saboda ana kasheni yanzu
kowa yasan shi ne,haka idan yace zai zo ya yi juyin
mulki a qasar farat xaya mutane za su gane cewa
bashi da gaskiya kuma har abada ba zai samu haxin
kan sub a.
Dole yanzu ya voya a wani wurin sannan ya
fara tunanin hanyoyin da zai bi yaga bayana da
mahaifina da kuma Amzad, kaga kenan a karon farko
ya zama mai laifi ya gudu daga kurkuku, guduwarsa
daga kurkukun zatasa jama’ar gari su fara zarginsa da
rashin gaskiya a lokacin da ni kuma nake ci gaba da
tafiyar da shari’arsa dake tsakaninsa da Amzad ina
fitowa da dukkan tuggun daya shiryawa mahaifinsa
qarara a baina jama’a kowa yana ji, hakan zai saka
kowa yasan rashin imaninsa da rashin gaskiyarsa.
79
BAYAN MUTUWA
Hakan zai sa jama’ar gari su tsane shi,tofa a
daidai wannan lokaci ne zai harzuqa yace zai yi
amfani da qarfin sa wajen ganin ya gama dani da
kuma mahaifina ya yi juyin mulki.
Ni kuma a sannan ne zan kawo qarshensa ta
hanyar amfani da babban lagonsa dana gano, yakai
sarkin yaqi kayi sa ni cewa bazan iya gaya maka
komene ne wannan lagon na attajiri Huzulu har sai
bayan n agama dashi sannan zaka ga lagon nasa da
idanunka.
Yanzu zaka iya tafiya izuwa gidanka domin
kaje wajen iyalinka su ganka su sami nutsuwa, ina son
ka kwantar da hankalinka ka sani cewa babu abinda
zai sake samun waninku har izuwa sa’adda zamu ga
bayan wannan babban maqiyin na mu wanda ya kashe
mahaifinka”.
Koda Gimbiya Lashmin ta zo nan a zancenta
sai mamaki ya turnuke sarkin yaqi yace.
“Yaya aka yi kika san cewa attajiri Huzulu ne
ya kashe mahaifina alhalin ni kaina bansani ba sai a
yau xinnan da ya faxa min da bakinsa acan kurkuku?”
Sa’adda Lashmin taji wannan tambaya sai ta yi
murmushi tace.
80
BAYAN MUTUWA
“Shin ka mance na gaya maka cewa tun ina
yarinya nake bincike akan duk abubuwan da attajiri
Huzulu ke aikatawa? To kasani cewa tun a sannane
ma na gano cewa hatta dakarun sumame da suka tava
kawowa sarki hari sa’adda muka fita wani rangadi
attajiri Huzulu ne ya aiko su, kuma a wannan ranar ne
Nazmir mahaifin Amzad ya ceci rayuwar sarki shi
kuma Amzad ya ceci rayuwata.
Kaima da qyar ka tsira da rayuwarka bayan
an harbeka da kibiya a gadon bayanka, mahaifin
Amzad ya saka anyi wani sihiri ga Amzad wanda ya
saka ya mance da duk abinda ya faru tsakanina dashi a
wannan rana, kuskuren da mahaifina ya yikenan da
nima bai sa anyi mini irin wannan sihirin ba domin
daidai da rana xaya ban tava mantawa da Amzad ba a
cikin zuciyata. Ina tuna kamannin fuskarsa bayan
kowace daqiqa guda.
Sarqar wuyansa kuwa wacce na fizgo a
lokacin da aka rabamu har yau har gobe da ita nake
kwana da ita nake tashi ban tava rabuwa da ita ba”
Koda Gimbiya Lashmin ta zo nan a zancenta sai
hawaye ya zubo mata nan take ta zura hannunta izuwa
cikin rigarta ta zaro wannan sarqa ta Amzad ta
nunawa sarkin yaqi.
81
BAYAN MUTUWA
Koda sarkin yaqi ya yi arba da sarqa sai ya
kamu da tsananin mamakin gami da al’jabi kuma ya
kamu da tsananin tausayin Gimbiya Lashmin.
Nan take shima hawaye ya zubo masa yace
“Ya shugabata tabbas qwaqwalwarki daban take data
kowa a wannan zamani, basirarki da hangen nesanki
sunfi gaban tunani. Tabbas a gaban idanuna kika cire
wannan sarqa daga wuyan Amzad a lokacin kina da
shekara bakwai a duniya shi kuma baifi shekara taraba.
Ina kwance a qas jini yana zuba a gadon
bayana na xago kain naga sa’adda Amzad ya savaki a
kafaxarsa ya ruga dake izuwa cikin qofar birninmu,
bazan tava mantawa ba a wannan lokaci ma said a
kibiya ta sokeshi a hannu ya kwallara uban ihu amma
duk da haka bai yarda ke qasa ba sai yaci gaba da
gudu dake xauke har sai da ya tserar dake, shin yanzu
saboda haka ne kema yanzu kike son ki qwato masa
dukiyarsa daga hannun attajiri Huzulu?” koda jin
wannan tambayar sai Gimbiya Lashmin ta share
hawayenta sannan ta girgiza kanta tace.
“A’a bawai don na yi masa sakaiya bane bisa
ceton rayuwata da ya yi sai saboda tun a wannan ranar
na kamu da tsananin son sa, ina mai tabbatar maka da
cewar idan kaga ban auri Amzad ba to sai dai idan
82
BAYAN MUTUWA
bana numfashi a doron qasa” Koda jin wannan batu
sai hankalin sarkin yaqi ya dugunzuma ainun hawaye
ya sake zubo masa yace.
‘Babu yadda mahaifinki baiyi ba akan kada
wannan ranar ta zo, bisa hakane ya nisantaki da
Amzad ya toshe duk hanyoyin da za ku iya haxuwa
muma ya gargaxemu akan kada mu kuskura mu yi
zancen Amzad tare dake ko mu sanar dake inda yake,
saboda bayanin da Bokansa ya yi masa na cewar indai
kika yi soyayya da Amzad a qarshe babu ribar da za a
samu face nadama da baqin ciki...” Caraf! Sai
Gimbiya Lashmin tace.
“Duk nasan da wannan al’amarin domin shi
kansa sarki ya shaida mini hakan da bakinsa amma na
zavi nadamar da baqin ciki kowane irine da dai a
rabani da masoyina. Idan ma ba mu yi soyayya ba ta
rayuwar aure a wannan rayuwa ta yanzu ba to lallai za
mu yi ta a bayan Mutuwa saboda na yi imani cewa an
halici ruhinmu da zukatan mu domin su so juna. Ina
mai tabbatar maka da cewar idan ma mun mutu ba mu
yi aure ba za a sake tashin mu a wani vangaren daban
na duniya kuma sai mun haxu da juna mun yi aure
kamar yadda Amzad ya mance da ni a yanzu, muna
83
BAYAN MUTUWA
haxuwa ni ce zan shaida shi tunda ni ban tava
mantawa da fuskarsa ba.
Ruhina da ruhim Amzad ba za su tava
rabuwa ba, lallai akwai RAYUWA BAYAN
MUTUWA ni dashi” Ko da Gimbiya Lashmin ta zo
nan a zancenta sai ta fashe da kuka ta faxa akan qirjin
sarkin yaqi ta rungume shi.
Nan take tausayinta ya turnuqeshi shima ya
qanqameta a jikinsa yana mai kuka gami da
rarrashinta.
Sai da suka shafe tsawon ‘yan daqiqu suna
manned a juna sannan sarkin yaqi ya janyeta daga
cikin jikinsa ya dubeta yace.
“Ya shugabata yanzu yaushene za ki nunawa
Amzad wannan sarqa tasa domin ya tuno da duk
abubuwan da suka faru a baya tsakaninki dashi ku
kafa tubalin soyayyarku?” Koda jin wannan tambaya
sai farin ciki ya lulluve Gimbiya Lashim ta qyalqyale
da dariya daga can kuma sai ta nutsu tace.
“Bazan nunawa Amzad wannan sarqaba sai
bayan na kawar da babban maqiyinsa wato attajiri
Huzulu, sai naga cewar duk dukiyar ta dawo hannunsa
yana cikin daula da kwanciyar hankali a sannanne
84
BAYAN MUTUWA
nima zan sami nutsuwa har na iya aza tubalin
soyayyarmu na baiyana shi a fili kowa ya gani”.
Koda jin wannan batun sai sarkin yaqi ya yi
doguwar ajiyar zuciya sannan hawaye ya suvuce masa
yace.
‘Na ji ajikina za ki iya samun nasara akan
azzaluminnan attajiri Huzulu amma maganar Bokan
mahaifinki tana yawo a cikin ruhina, zuciyata tana
bugawa da qarfi tana tabbatar mini da cewar wannan
tubalin soyayya naku ke da Amzad ba zai kai ga
ginuwa ba, tabbas rushewa zai yi”.
Koda jin haka sai Gimbiya Lashmin ta sake
faxawa kan qirjin sarkin yaqi ta fashe da sabon
matsanancin kuka sannan tace.
“Ni ma na sha yin mugun mafarki akan haka,
mummunan abinda nake gani a cikin mafarkin nawa
bazan iya gaya maka shi ba, sai dai zan faxa maka
wani daga cikinsa sauran kuma na barshi ya zama sirri
a cikin zuciyata” Ta xan yi shiru na taqin lokaci tana
kallon sarkin yaqi sannan ta ja numfashi tace masa.
“Na tava yin wani mafarki bayan na kwanta
barci na gani tare da ni da Amzad muna zaune a cikin
wani lambu muna hira cikin tsananin soyayyar juna da
kulawa, kwasam sai muka ga wani mahari ya kawo
85
BAYAN MUTUWA
mana sumame ya na zuwa ya kawo wa Amzad sara da
zumar cire masa kai amman bai samu nasarar yin haka
ba sai ya kauce saran ya bi iska.
Suka tsaya suka yi carko-carko kamar wasu
zakaru suna kallon junansu, nima ganin haka ba
qaramin xaga min hankali ya yi ba cikin sauri na miqe
ina kallon wannan mahayin wanda ya rufe fuskarsa da
qyale sai idanunsa kawai ake gani cikin tsawa nace
masa.
“Kai wane?”
Ya xauke kai daga kaina yana kallon Amzad
yace masa.
“Ba ke na kawo wa hari ba, wannan baqin
azzalumin masoyin na ki na kawo wa hari, kuma ba
zan tava barinsa ba har sai na farauce rayuwarsa” Jin
haka sai Amzad ya juyo a fusace yana kallonsa.
“Kai wane?” Shima ya tambaye shi.
“Masoyiyarka zata san ko ni wane bayan na
halaka ka” Yana gama faxin haka sai ya sauko daga
kan dokinsa ya yi xauki zuwa kan Amzad nan suka
soma fafatawa ni kuma na tsana ina kallon yanda suke
wannan faxan cikin tsananin fargaba da tsoron abinda
ka iya faruwa akan masoyina.
86
BAYAN MUTUWA
Ganin yadda wannan jarumin yake neman
farauce rayuwar masoyina Amzad sai na suri wuqa
nima na kai masa xauki, nan fa wani sabon gumurzu
ya varke, shima mahayin ya zare wata takobi ya far
mana da wani azababen faxan nasa mun xauki lokaci
mai tsawo muna wannan azababen faxan kafin ya
samu nasarar sarar Amzad a qirji nan take ya faxi
qasa ganin haka ya xaga takobinsa sama da zumar
suke shi, ina ganin haka na faxa kansa na bashi kariya
nan take ya suka mini takobin ta huda qirjina ta volo
ta shiga cikin jikin Amzad da wani murmushi na dubi
Amzad nace mas.
“Masoyina ba zan tava aminta ka riga ni
mutuwa ba, zan so mu mutu a tare lokaci guda
wannan shi ne cikar burin soyayya da qaunar juna”
Shima ya yi murmushi.
“Tabbas kin nuna min ke masoyiyace ta
gaske wacce ba za a tava mancewa da ita ba, ina ma
zan yi nisan kwana dana nuna wa duniya cewar mu
masoyane waxanda ba a tava yin kamarsu ba, amman
a yanzu hakan ma ina godiya ga abin bauta domin duk
wanda ya samu tarihin wannan soyayyar tamu zai san
lallai duk wajen da masoya suke mun kai”.
87
BAYAN MUTUWA
Tana kawo nan ta yi shiru tana duban sarkin
yaqi, wannan karon idanunta sun ciko da hawaye.
Su duka suka yi shiru duk jikin sarkin yaqi ya
gama yin sanyi a hankali Gimbiya Lashmin ta ce.
“Idan har wannan mafarkin nawa ya faru da
gaske to tabbas haka qaddararmu take ba za mu iya
sauyawa ba, yakai sarkin yaqi ina neman alfarma guda
a wajenka” Koda jin haka sai sarkin yaqi yai sauri ya
janye jikinsa daga cikin na Gimbiya Lashmin ya dubet
a cikin kaxuwa yace.
‘Ke kuwa wace irin alfarma kike nema a
wajena?” Gimbiya Lashmin ta goge hawayenta sannan
tace.
‘Idan har ni da masoyina Amzad mun mutu a
lokaci guda to duk yadda za a yi kar ka bari a binne
mu a kabari daban-daban, ka tabbatar da cewar an
binnemu a cikin kabari guda kuma hannuna na daman
a cikin hannunsa na dama wannan itace kaxai alfarmar
da nake nema a wajenka.
Ina son yanzu ka yi min alqawarin cika min
wannan burin nawa” Koda jin wannan batu sai
hawaye ya zubowa sarkin yaqi yace.
88
BAYAN MUTUWA
‘Kamar yadda na rinqa tsaron lafiyar
mahaifinki da taki tsawon shekaru na yi alqawarin zan
cika miki wannan burin naki indai na kai wannan
lokacin amma ina fatan cewa ke da masoyinki ba za
ku mutu ba harsai kunyi aure kun bar zuri’a tagari”.
Dajine fetal iya ganin mutum wanda ke xauke da
tsaunika,bishiyoyi da duhuwoyi masu ban tsoro. Shi
dai wannan daji tazararsa da birnin misira ya kai
tafiyar kwana goma sha shida.kuma fatakema sai sun
haxa babbar runduna sanna suke iya ketawa saboda
mugun fashin da ake yi a wajen.
Kai tsaye wani mahayin doki ya ratsa farkon
wannnan daji ya nausa cikinsa ba tare da wani jin
tsoro ba tamkar yana tafiya a cikin harabar gidansa,
abin tambayar shi ne shin ya san dajin kuwa ko kuwa
yana da wata alaka da yan fashi dake cikin dajin?
Haka dai wannan mahayin yaci gaba da kutsawa cikin
dajin ba tsayawa ba waige har sai daya shafe sa’a uku
yana tafiya a cikinsa yana kallon tsiran dabbobin daji
msu gifta masa da kuma tsintsaye da kai komo a cikin
89
BAYAN MUTUWA
sararin samaniya. Kwatsam sai yaga waxansu mutane
suna faxowa kasa daga saman bishiya waxanda
adadinsu ya kai xari kuma suna sanye da wani koren
tufafi wanda ya saje da ganyen bishiyar wajen babu ta
yadda za a yi mutum ya gane cewar akwai mutum a
wajen.
Nan da nan waxannan mayaqa suka yiwa mahayin
qawanya. Nan take rabinsu suka zare kebiyoyi suka
xana akan baka suka ritsashi, wasu kuma suka zare
takubba. Bisa dole mahayin ya ja linzami dokinsa ya
tsaya cak. Shugaban dakarun ya dube shi da kyau yace
masa.
“Waye kai kuma ina zakaje?” Ba tare da nuna
wata alamar firgita ko tsoro ba mahayin ya yi
murmushi yace.
“Ni manzo attajiri Huzulu ne