Author : AYSHA ALI GARKUWA Category : Romance
binciken da zaiyi ya gama sannan ya kalli Usman d'in dake konce a rigingine ya lumshe ido hawaye na bin fuskar shi sannan ya juyo ya kalli Hamma Umar dake zaune ya zuba mishi ido yana rik'e da hannun shi sannan ya kalli Abba dake k'ok'arin gyara wa Usman d'in konciya cikin kula doctor Ibrahim yayi ajiyan zuciya sannan yace.
"Alhaji Hassan ko kuna lura da Usman sannan kunsan meke damun shi akwai matsalar da yake boyewa a zuciyar shi sannan kuma yasan zuciyar shi bazata iya d'aukar nauyin ba Usman akwai abin da yake matukar so bai samu ba,
domin na duba na'urar dake cikin k'irjin shi tana zaune yadda ake so tana kuma taimakawa kamar yadda ta saba tana kuma harbawa jinin dai-dai misali kuma zataci gaba da aikin har nan gaba shekara 1 a lokacin zai cika shekara biyar da sata sannan za'a koma a canzata kamar yadda aka saba,
yanzu wata matsalar ce ta daban kuwa ke damun Usman kuma zata iya jawo komai a rayuwar shi."
yana rufe bak'in shi Usman ya bud'e idanun shi cikin salon sa na abin dariya ya fara magana cikin dariya da son badda matsalar tasa yace.
"Uhummm wai ina son wani abu,
toh niko mai zanso wanda Abba da Hamma Umar basu samamin shiba ni ba abin da nake so."
Ido Nenne ta tsura mishi cikin tsananin tunani lokaci d'aya kuma ta fara tuno wani abin,
Hajjajo kuwa ba abinda takeyi sai kuka,
shi kuwa Hamma Umar ido ya tsurawa d'an uwan nashi cikin sanyi yace.
"Me yake saka tarin da a man jini?."
murmushi yayi tare da d'an shafa sajen shi yace.
"You naga Anyi tayin maganin asibiti ba canji shine jiya naje na karb'o na wmzamai shine na jik'a nasha ,
sai gashi yana k'ok'arin fecewa dani barzaq."
Murmushi ya kuma yi sannan yace.
"Amman fa gsky naji sauk'i dana amayar da jinin."
haka ya rink'a shashantar da abin shi kuwa doctor Ibrahim ya tabbar akwai matsala tare dashi.
su ya Adam kuwa sun d'an samu nitsuwa ganin Usman d'in ya mik'e,
Hamma Umar kuwa har yanzu zuciyar shi na cike da fargaba,
Abba kuwa bayan doctor Ibrahim yabi suka fita tare yana k'ara mishi bayani,
bayan su Abban sun fita ne Hamma Umar ya d'an juyo kusa da Ummul tafin k'afafun ta ya kamo yasa hannun shi ya rink'a murzawa yana jan yatsun k'afafun nata tare da kiranta.
"Ummul ! Ummuuul !."
sai kuma ya dawo ta kanta hannun shi yasa ta k'asan wuyanta yana d'an murzawa,
nanma shiru sai ya manna hancin shi da nata sannan ya rufe bakinta da nashi,
cikin lumshe ido ya rink'a fesa mata numfashin sa sannan yana zuk'o numfashin ta bak'in ta gaba d'aya nashi numfashin ya rink'a fesa mata cikin sa'a tafizgo numfashin sannan a razane ta kamo wuyan shi baki ta bud'e da nufin zata sake k'ara,
sai yayi maza ya rufe mata bak'in da tafin hannun shi,
haka yasa ta bud'e idanun ta sannan ta rink'a kallon su d'aya bayan d'aya,
zame bakin ta tayi cikin sanyin muryar tace.
"Ya Usman ! ya Usman ."
ido ya d'an rumtse sannan yace.
"Na'am Ummul ."
jin muryar shi ta mik'e da sauri taku d'aya tayi ana biyun ta koma ta zauna ido na zubda k'ollah dan azaban ciwon da raunin jikinta ke mata,
cikin sauk'e ajiyan zuciya Hajjajo tace.
"Ke kuma meya sumar dake? sannan yanzu tafiya ma na gagararki."
batayi magana ba sai kawai ta kama kuka,
ganin haka Nenne tace.
"Toh sarkin kuka ya isa haka taso mu tafi kiyi wonka sai kici abinci kiyi bacci."
mik'e wa tayi cikin zubda k'ollah tafiya ta farayi cikin d'ingisa k'afafun ta tana d'an waresu tare da cije lips d'in ta,
ganin haka tuni Nenne tayi gaba dan ta gano matsalar yartata itama Hajjajo shiru kawai tayi dan ta fahimci matsalar,
shi kuwa Hamma Umar kanshi ya sunkuyar cikin tarin kunya da tausayin Ummul d'in sai hawaye yaji yana bin hab'arsa dan gani yake kamar ya gwada mata rashin tausayi tunda yasan yarinya ce,
kunya yakeji ta rufeshi kamar k'asa ta tsage ya shiga,
ganin hakan yasa su ya Adam duk suka zame suka fita itama Hajjajo kitchen d'inta ta shiga ta fara had'a wa Ummul had'in su na tsoffin shuwa'arab sannan tayiwa Usman d'in ma had'in shi na musamman ta kuma dafawa Usman abincin da zaici da kanta.
A part d'in Nenne kuwa suna shiga kai tsaye bedroom suka wuce kan gado Ummul ta konta ta kife kanta tana kuka,
ita kuwa Nenne toilet ta shige ruwan d'umi ta had'a mata mai k'unshe da sinadarai na gyaran jiki sannan ta had'a mata wani juk'o na musamman a cikin buta,
tana fitowa taje kusa da ita cikin kulawa da tausayawa irin ta uwa da yarta ta kamo hannun ta ta zaunar da ita kafad'an ta ta dafa a hankali tace.
"Ummul Allah ya miki albarka kiyi hak'uri mamana ki d'aure kinji ko ki denan kukan nan ya isa yanzu kin girma ya kamata kiyiwa kanki fad'a tashi kije kiyi wonka ki zauna cikin ruwan d'umin sannan kiyi amfani da ruwan butar nan."
kukan ta kumayi cikin shogwob'a dan ganin Nennen ta na lallashin ta,
da kukan ta shiga tayi wonkan sannan ta k'asa kanta lokaci d'aya taji jikinta duk ya wore,
tana fitowa ta samu Nennen ta jona borner a ajikin wuta tana fitowa ta zuba mata wasu turaruka masu tsananin k'amshi sannan ta kalleta cikin kulawa tace,
zoki tsuguna kiyi hayak'i da wannan."
"toh " tace sannan ta matso gaban borner ita kuwa Nenne ta fita parlour,
tsuguna wa tayi a kanshi hayak'in na shiga jikin ta wani irin k'amshi na ratsata,
tana mik'e wa ta Jita garau hakan yasa ta kimtsa sannan ta koma bak'in gadon ta konta cikin jin wani irin baccin gajiya,
Tana konciya Nenne na shigo wa had'in kaza ta karb'a mata wanda Hajjajo tayi mata sai ruwan tsumi mai dad'in sha,
ajiye wa Nenne tayi sannan tace.
"Taso kici abinci saiki kontan."
ba musu ta sauk'o taci tasha dan tana jin yunwa,
kuma yau tana jin dad'in yadda Nennen ta ke kula da ita wanda tunda ta nuna bata son Umar Nenne ta dena kulata sai yau d'in,
tana gamawa ta koma ta konta tana kallon Nenne dake shirin shiga wonka cikin sanyi tace.
"Nenne zazzab'i nake ji da ciwon kai."
ba tare da ta kalleta ba tace.
"Toh bari in gayawa Umar d'in yazo ya dubaki."
fuska ta tsuke dan bata son abinda zai had'a ta dashi inuwa d'aya kuma gashi ta jawa kanta,
bayan Nenne tayi wonkan ne ta shirya ta nufi d'akin Abba a tsakar gidan ta kalli Aliyu yana shirin shiga part d'in Hajjajo kiran shi tayi sannan tace.
"Jeka kira Hamma Umar d'in ku kace Ummul bata da lafiya yaje ya dubata."
"Toh" yace sannan ya nufi parlour Hajjajo yana zuwa ya samu Hamma Umar d'in yana zaune gefen Usman yana b'are mishi lemu,
gefen shi ya zauna a hankali yace.
"Hamma Anty Ummul bata da lafiya Nenne tace kaje ka dubata."
kai ya gyad'a sannan yaci gaba da bawa Usman d'in kulawa,
bayan ya gama bashi abinci ya bashi maganin sannan suka tafi part d'in su suna zuwa ya had'a mishi ruwan wonka,
har cikin bathroom d'in ya rekashi kamar zaiyi mishi wonkan,
murmushi Usman yayi tare da cewa.
"Hamma yau wonkan ma zaka min ne?."
"Kanaga ka girma ko?."
kai ya sosa sannan yace.
"Gaskiya dai Hamma na girma mai min wonka zai iya makancewa."
K'eyan shi ya d'an buga sannan ya fita,
shi kuma Usman wonkan yakeyi yana zubda k'ollah cikin tausayawa kanshi da d'an uwan nashi,
bayan ya fito Hamma Umar ya shirya shi sannan ya kontar dashi kan gado ya zauna gefen shi yana shafa kanshi cikin sanyi yace.
"Ammmi ta kiraka kana wonka nace mata kace min yanzu ka girma."
ido ya lumshe yana jin dad'in yadda d'an uwan nashi ke kula dashi k'aunar shi na ratsa mai zuciya,
ido ya lumshe cikin jin bacci yace.
"Hamma ?."
"Na'am Usman d'an uwana."
kai ya jinji na sannan yace.
"Ina sonka d'an uwana."
kanshi ya rink'a shafawa yana cewa.
"Usman duk duniya bani da tamkar ka ina sonka k'anina bani da buri a duniya daya wuce inga ka samu lafiya fatana a koda yaushe in ganka cikin farin ciki."
ruggume juna sukayi sannan a hankali Umar ya kontar dashi sannan ya rink'a yi mishi karatu qura'ani a cikin kunnen shi murya cike da rauni,
lokaci d'aya bacci ya tafi da Usman d'in,
shi kuwa Hama Umar a hankali ya gyara mishi konciya sannan ya fito kai tsaye harabar gidan ya koma motar shi ya bud'e ya d'auki magungunan Ummul sannan ya nufi part d'in Nenne,
yana shiga parlour ya samu ba kowa sai kuma yaji muryan Ummul dake magana da Anty Halima da woyar Nenne,
cikin yin sallama ya shiga yana shiga ya zauna gefen Ummul d'in sannan yasa hannu ya karb'i woyar ya katse kiran ,
ita kuwa a fusashe ta juyo gare shi a nufin yin tsiwa,
sai kuma tayi shiru jin yadda ya jawota jikin shi ya ruggume ta tsam a jikin shi sai sauk'e ajiyan zuciya yakeyi murya can k'asa yace.
"Kun bani tsoro keda Usman in na rasaku bansan makomata ba Ummul Khairi ina tsoron abinda zai rabani daku,
In babu Usman bansan ya rayuwa zata juya min ba."
sai kuma ya k'ara matsota jikin shi d'umin jikinta na ratsa shi,
ita kuwa tureshi takeyi tana k'ok'arin matsawa,
jawota ya kumayi a hankali ya tallabo kanta kissing d'in ta yayi da kyau sannan yace.
"Kiyi hak'uri my Khairi bazan sake wahala da keba."
shiru tayi tana jin yadda yake fidda numfashin da sauri-sauri a haka har ya fara sauk'e ajiyan zuciya a hankali nitsuwarsa ta dawo jikin shi sannan ya bata maganin ya kontar da ita ya shafa fuskar ta sannan ya fita.
A haka Hamma Umar ya wuni kula da k'anin shi da matar shi da derema haka ya kwana kula da Usman yayin da kewar Ummul ke cin jikin shi da zuciyar shi,
koda gari ya waye haka ya wuni kula dasu,
kuma Alhamhadullih duk sun mik'e musamman Ummul dan shi kam Usman k'arfin haline da son kontar da hankalin Hamman nashi,
bayan Anyi salla isha ne Abba yace Hamma Umar su tafi tunda duk jikin su da sauk'i,
bayan ya fita ne ya d'auko jakar Ummul ya bawa Aliyu ya kai mata cikin gida sannan yace .
"In kaje kace tazo."
"Toh" yace sannan ya nufi cikin gidan,
a parlour Nenne ya samu su ya Adam cikin mamaki ya Sadik yace .
"Jakar nanfa daga ina.?."
"Ta Anty Ummul ce."
Ya bashi amsa ya Adam ne ya kalli Ummul d'in cikin tsuke fuska yace.
"Ba yanzu zaku tafiba?."
Kai ta juya ido cike da k'ollah tace.
"A a ni bazan komaba bani da lafiya."
A hatsale ya bugawa Aliyu tsawa .
"Maza ka meda jakar cikin motar Hamma Umar d'in ke kuma tashi kibi mijin ki ku tafi."
shi kam Aliyu tuni ya juya da jakar ita kuwa hannun ta rink'a yarfa wa tana buga k'afafun ta tare da bud'e baki da k'arfi tana.
"Ai Hamma Umar d'in ya yarda kuma bani da lafiya shike nan dan an tsaneni sai ayi ta korata a gidan mu."
Kanta yayi da sauri yana zaro bel d'in k'ugunshi,
ya Sadik kuma cewa yake.
"Yauwa zaneta tunda bata jin magana."
Ihu ta saki jin sauk'ar bel d'in a jikin ta a guje ta fita tana kuka,
bayan Hamma Umar d'in ta tsaya tana tsalle da dire-dire tare da rik'e hannun shi ,
Abba ne ya fito dan jin kukanta yana zuwa ya kalli yadda takeyi sai murmushi yayi dan a fili yarintar Ummul take ganuwa,
shi kuwa Adam tsawa yake buga mata yana.
"Ki wuce ki shiga cikin mota."
Abba ta kalla dan ko zaice ta dawo sai kuma ta shiga motar ganin yadda ya had'a fuska yana kallon ta,
shi kuwa Abba cikin bada umarni yace.
"Farouq shiga ku tafi.
"toh."
yace sannan ya shiga,
Aliyu kuwa dariya yayi tare da d'aga tafin hannun shi ya saitasu da kanshi yana kad'a hannun tare da zaro harshen yana kad'awa Ummul cikin tsokana yace.
"Bana gaya mikiba yanzu ke ba y'ar gida nan bane yanzu dagani sai Nenne na."
ya k'arishe maganar yana rawa,
Usman ne ya d'an roggoshi keyarshi yace.
"Aliyu wato kaine d'an tada zaune tsaye ko."
ita kuwa kuka tasa tana cewa.
"Ya Usman ba kaga Aliyu ba."
Murmushi yayi yace.
"Muna sonki Ummul d'in mu ke y'ar gidan nance har Abadan."
K'ollah ta zubda tare da cewa.
"ya Usman kai kad'ai kake sona, nima ina sonka."
Ido ya lumshe sannan yace.
"Allah ya d'aiyiba."
murmushi sukayi dukan su,
shi kuwa Hamma Umar hannun Usman ya jawo ya d'an sunkuyo kanshi a hankali yace.
"Ka kula da kanka d'an uwana ina son ka ina tsoron abinda zai cutar da kai."
Murmushi yayi tare da cewa.
"Nayi lafiya fa."
Haka sukayi sallama suka tafi,
Ita kuwa suna fita harabar gidan ta bud'e sabon shafin kuka,
sunyi tafiya mai d'an nisa,
Hamma Umar yana tuk'in hankalin shi na cikin tunanin halin da k'anin shi ke ciki,
kamar a mafarki yaji Ummul tasa hannunta ta d'amk'o........
By
*GARKUWAR FULANI*
濠电姷鏁告慨鐑藉极閸涘﹥鍙忛柣鎴濐潟閳ь剙鍊块幐濠冪珶閳哄绉€规洏鍔戝鍫曞箣閻欏懐骞㈤梻鍌欐祰椤鐣峰Ο琛℃灃婵炴垶纰嶉浠嬫煏閸繃鍋憸鐗堝笚閸嬫劗鈧懓澹婇崰鏍礈娴煎瓨鈷戞慨鐟版搐閳ь兙鍊濆畷鏉课旈崨顓囷箓鏌涢弴銊ョ仩闁告劏鍋撴俊鐐€栭崝锕€顭块埀顒傜磼椤旂厧顣崇紒杈ㄦ尰閹峰懘宕崟鎴欏劦閺屾盯鎮╅崘鎻掝潚婵犵绱曢弫璇茬暦閻旂⒈鏁嶆慨妯夸含閺夋悂姊绘担鍛婂暈闁瑰摜鍏橀幊妤呭箚閺夊簱鍋撶€靛摜纾介柛灞捐壘閳ь剙鍢查湁闁搞儯鍔婃禒鍫㈢磼鐎n収鍤︽繛鎴欏灩缁€鍐┿亜閺冨洤顥嶉柟鑺ユ礀閳规垿鎮欓弶鎴犱户闂佹悶鍔屽﹢杈╁垝鐠囨祴妲堥柕蹇ョ磿閸樻捇鏌℃径灞戒沪濠㈢懓妫濊棟闁挎柨顫曟禍婊勩亜閹哄棗浜惧銈嗗灥椤︻垶锝炶箛鎾佹椽顢旈崟顓у敹闂佺澹堥幓顏嗗緤閻戞ɑ鍙忛柛銉墯閳锋垿鏌i悢鍝勵暭闁哥喓鍋ら弻锝夊焺閸愨晝顦伴梺璇″枟椤洭鍩€椤掑﹦绉甸柛鐘愁殜閸╂盯骞嬮敂鐣屽幍缂備礁顑嗙€笛囧箲閿濆洨纾奸柣妯挎珪瀹曞矂鏌″畝鈧崰鏍х暦濮椻偓瀵濡烽妷銉ュ挤闂佽瀛╅鏍窗閺嶎厼鐤柛褎顨呴悡婵嬪箹濞n剙濡肩紒鐙呯秮閺岋絽螣绾板崬濮曠紓浣瑰敾缁绘繂顫忕紒妯诲濞撴凹鍨遍弫顖氼渻閵堝骸浜滄い锕傛涧閻e嘲鈹戠€n亜鍞ㄥ銈嗘尵閸犲孩绂掕椤啴濡堕崨顖滎唶闂佺粯顨呴敃顏堝箖閿熺姴唯闁挎柨澧介鏇㈡⒑閻熼偊鍤熷ù鍏肩箞椤㈡棃宕煎┑鍥发闂備焦瀵х换鍌毭洪悩璇茬;闁规崘鍩栭崰鍡涙煕閺囥劌澧版い锔哄姂濮婃椽骞愭惔銏紭闂佹悶鍔庨崕銈囩矚鏉堛劎绡€闁稿被鍊栧銊╂倵閸忓浜炬繝鐢靛Т閸犳岸鍩€椤掆偓椤﹁京妲愰幘璇茬<婵炲棙鍨垫俊浠嬫⒑閸濄儱浠滄い顓炲槻椤繑绂掔€n亞顦板銈嗗笒閸婄敻寮ㄩ搹顐ょ瘈闁汇垽娼у瓭濠电偞娼欓崐鍨嚕椤愶箑绀冮柍鐟般仒缁ㄥ姊洪崷顓炲妺闁搞劎鏁婚崺鈧い鎺嶇劍閸婃劗鈧娲栭幖顐︽偩濠靛绀嬫い鎴eГ鐎氬ジ姊绘担鍛婂暈缂佸搫娼″畷鏇㈠础閻愨晜鐎洪棅顐㈡处缁嬫帡鎮¢弴銏″€甸柨婵嗙凹缁ㄥ吋銇勯妷褍浠х紒杈ㄥ浮瀵噣宕掑顓犱邯闁诲孩顔栭崰妤呭箰閾忣偅鍙忛柍褜鍓熼弻宥夊煛娴e憡娈梺鍛婃⒐鐢绌辨繝鍥ㄥ€锋い蹇撳閸嬫捇寮介鐐殿槷闂佹寧娲栭崐鍝ョ矆閸喓绠鹃柟瀵稿仩婢规ɑ銇勯妷锕佸閾绘牠鏌ㄥ┑鍡樺櫣闁哄棛鍋ら弻宥夋煥鐎n亞浼岄梺鍝勬湰缁嬫垿鍩ユ径濠庢建闁割偅绻€缁憋絽鈹戦悩鎰佸晱闁哥姵鐗犲畷鎰板锤濡も偓閽冪喐绻涢幋娆忕仼婵☆偅锕㈤弻娑滎槼妞ゃ劌鎳庨锝嗗鐎涙ǚ鎷洪柡澶屽仦婢瑰棝藝閿斿墽纾煎璺猴功缁夋椽鏌e☉鍗炴灈閾伙絽銆掑鐓庣仯闁哥偟鏁诲娲川婵犲啫顦╅梺鍛婃尰缁嬫垹鍙呴梺鍦檸閸犳鎮″☉妯忓綊鏁愰崶銊ユ畬婵犳鍠栫粔鍫曞焵椤掑喚娼愭繛鎻掔箻瀹曟繈骞嬮敂琛″亾娴e壊娼ㄩ柍褜鍓熼獮鍐閵堝懐顦梺鍦帛鐢寮抽姀銏㈢=闁稿本鑹鹃埀顒佹倐瀹曟劙鎮滈懞銉ユ畱闂佸壊鍋呭ú鏍婵犳碍鐓欓柟顖嗗拑绱為梺鍝勬4闂勫嫭绌辨繝鍥舵晬婵犻潧瀚ч崑鎾诲焵椤掑嫭鐓涢悗锝庝簽鏁堥梺鍝勭焿缁绘繂鐣烽崼鏇炍ㄩ柕澹倻妫梻鍌欑閹碱偊骞忕€n喖绀堥柣鏃傚帶閽冪喐绻涢幋娆忕仼缂佺姵鐩濠氬醇閻旇 濮囬梺璇茬箰閻楀繒妲愰幘瀛樺闁圭粯甯婃竟鏇㈡⒒娴e憡鍟為柛鏃撶畵瀹曟澘螖閸涱喖浜楅棅顐㈡处閹告挳寮ㄦ禒瀣厽闁归偊鍘奸悘銉╂煕閻旂顎滈柛濠冩綑閳规垿鎮╅鑲╀紘濠电偛顦扮粙鎾诲焵椤掍礁鍤柛鎾跺枛瀹曟椽鎮欓崫鍕吅闂佹寧娲嶉崑鎾绘煟閹垮嫮绡€闁哄本鐩崺鍕礃閿旀寧鍕冨┑鐘灱椤煤濠婂懏顫曢柟鎯х摠婵挳鏌﹀Ο渚Ш濠㈣泛瀚槐鎾寸瑹閸パ勭亶闂佽崵鍠嗛崕鐢稿箖妤e啯鍊荤紒娑橆儐閺咁剟姊虹紒妯虹仴婵☆偅鐟╁鎻掆攽鐎n偀鎷洪梻鍌氱墛缁嬫挻鏅堕弴銏$厵鐎瑰嫰鍋婇崕蹇涙懚閻愬绡€濠电姴鍊绘晶娑㈡煃闁垮鐏撮柟顔肩秺楠炰線骞掗幋婵愮€虫繝鐢靛仜閹冲繘宕濆▎鎾宠摕闁绘梻鍘х粈鍕煏閸繃顥滄い蹇ユ嫹
*RUBUTACCEN AL,AMARI*
Page 2闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻锝夊箣閿濆憛鎾绘煕婵犲倹鍋ラ柡灞诲姂瀵挳鎮欏ù瀣壕闁告縿鍎抽惌鍡涙煕椤愩倕鏋戦柛娆忕箲娣囧﹪顢涘鍙樿檸闂佺粯鎸婚崝娆撳蓟濞戞埃鍋撻敐搴濈盎闁逞屽墯閹倿鍨鹃敃鍌氶敜婵°倓绀佸▓婵嬫⒒閸屾氨澧涚紒瀣灴閿濈偛鐣濋埀顒傛閹惧瓨濯撮柛婵嗗閳ь剙鐭傞弻娑㈠Ω閵壯冪厽閻庢鍠栭…閿嬩繆閹间礁鐓涢柛灞剧煯缁ㄤ粙姊绘担渚劸闁哄牜鍓涚划娆撳箣閿旂粯鏅滈梺璺ㄥ櫐閹凤拷0闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻锝夊箣閿濆憛鎾绘煕婵犲倹鍋ラ柡灞诲姂瀵挳鎮欏ù瀣壕闁告縿鍎抽惌鍡涙煕椤愩倕鏋戦柛娆忕箲娣囧﹪顢涘鍙樿檸闂佺粯鎸婚崝娆撳蓟濞戞埃鍋撻敐搴濈盎闁逞屽墯閹倿鍨鹃敃鍌氶敜婵°倓绀佸▓婵嬫⒒閸屾氨澧涚紒瀣灴閿濈偛鐣濋埀顒傛閹惧瓨濯撮柛婵嗗閳ь剙鐭傞弻娑㈠Ω閵壯冪厽閻庢鍠栭…閿嬩繆閹间礁鐓涢柛灞剧煯缁ㄤ粙姊绘担渚劸闁哄牜鍓涚划娆撳箣閿旂粯鏅滈梺璺ㄥ櫐閹凤拷
*NA*
*AYSHA ALI GARKUWA*
濠电姷鏁告慨鐑藉极閸涘﹥鍙忛柣鎴濐潟閳ь剙鍊块幐濠冪珶閳哄绉€规洏鍔戝鍫曞箣閻欏懐骞㈤梻鍌欐祰椤鐣峰Ο琛℃灃婵炴垶纰嶉浠嬫煏閸繃鍋憸鐗堝笚閸嬫劗鈧懓澹婇崰鏍礈娴煎瓨鈷戞慨鐟版搐閳ь兙鍊濆畷鏉课旈崨顓囷箓鏌涢弴銊ョ仩缂佺姵鐩弻宥嗘姜閹峰矈鍞归梺绋款儐閹瑰洤顕i幘顔肩厬闁告繂瀚峰Σ鍛娿亜椤愶絿绠為柟铏矒閹粙妫冨☉妯哄挤闂傚倸鍊搁…顒勫磻閸曨個褰掑礋椤撶偟绛忛梺鍏间航閸庢娊銆呴弻銉︾厱闁圭偓顨呴幊鎰版晬濠婂牊鐓涘璺猴功婢ф垿鏌涢弬璺ㄐч挊鐔兼煕椤愮姴鍔滈柣鎾寸洴閹﹢鎮欓幓鎺嗘寖濠电偞褰冮悺銊┿€冮妷鈺傚€烽柛娆忣槸閺嬬娀姊虹化鏇熸澒闁告挻绻堥獮蹇涘川閺夋垹顦梺鑲┾拡閸忔﹢宕戦幘缁樺€婚柤鎭掑劗閹风粯绻涙潏鍓ф偧闁硅櫕鎹囬、姘煥閸涱垳锛滈柣搴秵閸嬪嫬霉椤旂瓔娈介柣鎰綑婵洦銇勯鐘茬仼闁伙絾绻堥崺鈧い鎺嶈兌椤╂煡姊洪鈧粔鐢稿煕閹烘嚚褰掓晲閸ャ劌娈屽銈嗘礃缁海妲愰幒鏃€瀚氶柟缁樺坊閸嬫捇宕稿Δ鍐ㄧウ婵犵數濮撮崯顖炲磿閻斿吋鐓忓┑鐐茬仢閸旀粓寮堕崼婵堝闁宠鍨块幃娆撳矗婢舵ɑ锛侀梻浣规偠閸斿酣骞婇幘鍦罕婵$偑鍊栭悧婊堝磻閻愮儤鍋傛繛鍡樻尰閸嬧剝绻涢崱妤冪妞ゅ繆鏅涢埞鎴︻敊閼测晛鈪甸梺鍝勭焿缁蹭粙鍩為幋锕€绠涙い蹇撶墕娴犳劙姊绘担鍛婃儓閻炴凹鍋婂畷婵嗙暆閸曨偆鍙€婵犮垼娉涜癌闁绘柨鍚嬮崐缁樹繆椤栨稒銇熼柛鐔奉儔濮婅櫣鎷犻崣澶婃敪濡炪値鍋勯ˇ顖滃弲濠殿喗銇涢崑鎾绘煛娴g鏆e┑顔瑰亾闂佺偨鍎寸亸娆戠不濮橆兘鏀芥い鏃傛櫕缁犳捇鏌i鐐靛妞ゎ剙锕、鏃堝幢濞嗘埊绱冲┑鐐舵彧缁插潡骞婇幘璇叉瀬濡わ絽鍟埛鎺楁煕閺囥劌浜滄い蹇d簽缁辨帒鐣濋崘顔兼懙缂備胶绮换鍫濈暦閸洘鍤嬮柛顭戝亝閻濇牕鈹戦敍鍕杭闁稿﹥鐗滈弫顕€骞掑Δ鈧壕褰掓煙闂傚顦﹂柡鍕╁劤閳ь剙鍘滈崑鎾绘煕閺囥劌鍘撮柟閿嬫そ濮婃椽宕ㄦ繝鍕窗闂佺楠稿畷顒勫煝瀹ュ牏鐤€婵炴垶鐟ч崢閬嶆煟鎼搭垳绉靛ù婊勭箞钘熼柣鎰暩绾惧ジ鏌¢崘銊モ偓鎼佸几濞戞埃鍋撳▓鍨灍闁规瓕娅曢幈銊╁焵椤掑嫭鐓冮柍杞扮閺嗘瑩鏌涢弮鈧敮妤佺┍婵犲洦鍊锋い蹇撳閸嬫捇寮介鐐殿槷闂佹寧娲栭崐鍝ョ矆閸喓绠鹃柟瀵稿仩婢规ɑ銇勯妷锕佸閾绘牠鏌ㄥ┑鍡樺櫣闁哄棛鍋ら弻宥夋煥鐎n亞浼岄梺鍝勬湰缁嬫垿鍩ユ径濠庢建闁割偅绻€缁憋絽鈹戦悩鎰佸晱闁哥姵鐗犲畷鎰板锤濡も偓閽冪喐绻涢幋娆忕仼婵☆偅锕㈤弻娑滎槼妞ゃ劌鎳庨锝嗗鐎涙ǚ鎷洪柡澶屽仦婢瑰棝藝閿斿墽纾煎璺猴功缁夋椽鏌e☉鍗炴灈閾伙絽銆掑鐓庣仯闁哥偟鏁诲娲川婵犲啫顦╅梺鍛婃尰缁嬫垹鍙呴梺鍦檸閸犳鎮″☉妯忓綊鏁愰崶銊ユ畬婵犳鍠栫粔鍫曞焵椤掑喚娼愭繛鎻掔箻瀹曟繈骞嬮敂琛″亾娴e壊娼ㄩ柍褜鍓熼獮鍐閵堝懐顦梺鍦帛鐢寮抽姀銏㈢=闁稿本鑹鹃埀顒佹倐瀹曟劙鎮滈懞銉ユ畱闂佸壊鍋呭ú鏍婵犳碍鐓欓柟顖嗗拑绱為梺鍝勬4闂勫嫭绌辨繝鍥舵晬婵犻潧瀚ч崑鎾诲焵椤掑嫭鐓涢悗锝庝簽鏁堥梺鍝勭焿缁绘繂鐣烽崼鏇炍ㄩ柕澹倻妫梻鍌欑閹碱偊骞忕€n喖绀堥柣鏃傚帶閽冪喐绻涢幋娆忕仼缂佺姵鐩濠氬醇閻旇 濮囬梺璇茬箰閻楀繒妲愰幘瀛樺闁圭粯甯婃竟鏇㈡⒒娴e憡鍟為柛鏃撶畵瀹曟澘螖閸涱喖浜楅棅顐㈡处閹告挳寮ㄦ禒瀣厽闁归偊鍘奸悘銉╂煕閻旂顎滈柛濠冩綑閳规垿鎮╅鑲╀紘濠电偛顦扮粙鎾诲焵椤掍礁鍤柛鎾跺枛瀹曟椽鎮欓崫鍕吅闂佹寧娲嶉崑鎾绘煟閹垮嫮绡€闁哄本鐩崺鍕礃閿旀寧鍕冨┑鐘灱椤煤濠婂懏顫曢柟鎯х摠婵挳鏌﹀Ο渚Ш濠㈣泛瀚槐鎾寸瑹閸パ勭亶闂佽崵鍠嗛崕鐢稿箖妤e啯鍊荤紒娑橆儐閺咁剟姊虹紒妯虹仴婵☆偅鐟╁鎻掆攽鐎n偀鎷洪梻鍌氱墛缁嬫挻鏅堕弴銏$厵鐎瑰嫰鍋婇崕蹇涙懚閻愬绡€濠电姴鍊绘晶娑㈡煃闁垮鐏撮柟顔肩秺楠炰線骞掗幋婵愮€虫繝鐢靛仜閹冲繘宕濆▎鎾宠摕闁绘梻鍘х粈鍕煏閸繃顥滄い蹇ユ嫹
*H*annun ta tasa ta damk'o siterin ta rink'a juyashi tare da murza shi da k'arfi tana.
"Allah ka tsaya ni in sauk'a ehe,
ni bazan koma gidan kaba ka sauk'e ni a nan zan tafi gidan Anty Halima."
murza kan motar take da k'arfin ta,
tuni motar ta fara yawo a tsakiyar titi ga ababen hawa dake ta gaban su da bayan su da gefe,
gaba d'aya motar kanta ya kufce,
a firgice yace.
Innalillahi Ummul kin san abinda kikeyi kuwa?."
fizge hannayen ta yayi da k'arfi cikin tashin hankali ganin ya nufi kan wani mai a dai-dai ta yana k'ok'arin hawa kanshi ita kuwa tak'i sakewa sai murzawa take tana.
"Ka sauk'e ni a nan bazan koma gidan kaba bana sonka na tsaneka."
Ido ya zaro cikin tashin hankali ganin saura k'iris ya taka wani mai reke da yake gefen titin gaba d'aya mutanen wurin sai rik'e kai sukayi suna.
"Innalillahi subahanallahi."
shi kuwa Hamma Umar cikin firgici da tsoron ganin zata sashin kisan kai gaba d'aya jikin shi sai rawa yake yi,
cikin b'acin rai ya fizge hannayen ta sannan ya tura ta jikin sit d'in ta koma ta bugi jikin marfin motar sannan ta sake tasowa tana k'ok'arin sake rik'e kan motar,
tsawa ya buga mata cikin zafin rai ya ware tafin hannun shi ya zuba mata mari d'aya wanda saida taga taurari na yawa a sararin samaniya kunnen ta saida ya bada sautin kiuuuu sannan ta kuma jin yayi dum lokaci d'aya zanen yatsun shi suka taso a farar fatarta tuni fuskar tayi jazir gaba d'aya ta rasa ina take dan marin ya gigitata,
shi kuwa da k'er ya samu ya tsaida motar jikin shi na rawa zuciyar shi cike da tsoron karta sashi kisan kai yayi parking a gefen titin cikin sauri ya fito ya nufi gun mai reken da mai a daidaitan hak'uri ya rink'a basu,
da sun hatsala amman ganin yadda yake basu hak'uri yasa sukace.
"ba komai Allah ya tsare gaba a rink'a kula."
"Toh nagode."
yace dasu sannan ya koma cikin motar ya shiga ya zauna fuska a tsuke tamkar bai tab'a dariya ba,
jan motar yayi da gudu ya kama hanyar damaturun,
ita kuwa tunda ya zabga mata marin ta kife kanta kan cinyoyin ta ta rink'a kuka mai cike da takaici,
bai kulata ba,
ita kuwa kukan taci gaba dayi tana sheshshek'a,
a haka har suka isa cikin damaturu a inda suna shiga hadari na tashi iska mai sanyi ya rink'a busawa tako ina sai walkiya ake da d'an rugugi alamu irin hadarin karshen damuna ce,
suna isa yayi parking sannan ya koma ya zauna ya jingunu da jikin kujerar yana jin yadda take kuka,
a zahiri mamaki yake irin tsanar da Ummul ke mishi sannan itace da laifi itace da kuka kuma
har cikin ranshi yaji zafin marin da yamata,
ajiyan zuciya ya sauk'e sannan yasa hannu ya d'an dagota ya jingina ta da jikin shi hannun ta ya kamo cikin sanyi ya cusa hannun kan k'irjin shi sai kuma ya kalleta a hankali yace.
"Kiji yadda kikasa zuciya ta bugawa dan tsoron karki sani nayi kisan kai Ummul nine ba kyaso amman k'iyeyyar har tana k'ok'arin saki in kashe wasu a banza."
sai kuma yayi shiru sannan yasa tafin hannun shi yana shafa fuskar ta a hankali yace.
"Kukan ki nasa zuciya ta tayi nauyi sabida sai inga kamar na k'asa rik'e amanar dana d'auka ne kiyi hak'uri ki gafar ceni banyi niyar tab'a lafiyar jikin kiba."
tureshi ta rink'a yi tana janye hannun ta,
shi kuwa rik'e hannun yayi a hankali ya bud'e d'an durowan gaban motar wani d'an k'ara min kontena ya d'auko bud'e wa yayi sannan ya d'auko wani zoben Diamonds sai shek'i yakeyi tamkar tauraro yatsarta ya d'an d'ago a hankali ya zira mata zoben cikin sanyi yace.
"Kinyi kyau matata yatsarki ta haska zoben."
fizge hannun tayi dai-dai lokacin da ruwan sama ya fara sauk'a ,
bud'e motar tayi ta fice cikin kuka ta koma can tsakiyar harabar gidan ta tsaya tana kuka,
ganin haka ya fito ya rufe motar cikin sauri yaje gabanta hannun ta ya rik'o tare da cewa.
"Kiyi hak'uri zomu shiga cikin gida kar ruwan ya tab'a mu,
kinsan ni bana son ruwan sama ya tab'a ni zai sani zazzab'i."
cogewa tayi fir tak'i shiga daya kamo hannun ta sai ta dasa mai ihu,
ganin haka ya rufe gidan sannan ya wuce ya shiga cikin gida a zaton shi ko zataji tsoro ta biyoshi,
Abu kamar wasa ya shiga,
ita kuwa sai tsuguna wa tayi a wurin ruwan yana ta sauk'a a kanta duk ta jik'e tayi jilik sai d'iga takeyi ga tsawa da walkiya da akeyi,
parlour ya fito rik'e da leima ya nufi gunta,
yana zuwa ya jawota jikin shi cikin rawan sanyi yace.
"Khairi kiyi hak'uri mu shiga cikin gida kar mura ta kamaki d'an Allah mushiga ciki bana so ruwan ya tab'ani."
Jin haka ta fizgota leimar ta cillata gefe haka ko iska ya debeta yayi woje da ita,
shi kuwa da sauri ya d'ago hular rigar shi da take konce a kafad'an shi ya rufe tsakiyar kanshi dan in ruwan sama ya bugi kanshi yana sashi zazzab'i da ciwon kai mai tsananin,
hannun shi kuwa ya hard'e a k'irjin shi tuni ya jik'e cikin rawan sanyi da karkarwa ya jawota jikin shi a hankali yace.
"Toh aikin rama mu tafi cikin gida kiyi hak'uri k'anwata."
cikin kuka tace.
"Ban rama ba kam,
kuma bazan shiga gidan kaba sai in zan rama marin da kayi min."
murya na rawan sanyi yace.
"Na yarda mu shiga saiki rama."
baki ta tura sannan tace "toh."
hannun ta