Author : AYSHA ALI GARKUWA Category : Romance
ki na zubda hawaye kuma ba zakici abinci ba."
da sauri tace.
"Wallahi nayi shiru kuma na share hawayen kuma wallahi zanci abincin."
"Kin tabbata ?."
"Ehh wallahi."
"Na tabbayi Hamma Umar?."
"Ehh gashi ka tabbaye shi."
Sai kuma ta mik'awa Hamma Umar d'in woyar tana cewa.
"Bani zansha shayin."
Mik'a mata cup d'in yayi sannan ya karb'i woyar tashi,
yana kallon fuskar ta,
shi kuwa Usman dariya ya d'an yi cikin sanyi yace.
"Hamma na tayi shiru ko? ta karb'i tea d'in ? ta fara sha ne?"
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ehh ."
Dariya Usman ya kumayi sannan yace.
"Hamma na kai baka saba lallashin wani d'an adam bayan ni a duniya ba shiyasa ka k'asa sata tayi shiru Hamma dole ka koyi lallashi fa tunda Allah ya had'a ka da Ummul."
murmushi kawai yayi sannan yace.
"Toh."
Bayan ya katse kiran ne ya juyo ya kalli Ummul da tuni ta shanye tea d'in sai zufa keta tsatstsafo mata tako ina sai damk'e cikin tayi tana murk'ususuwa,
mik'ewa yayi ya tsaida ta sannan ya rink'a jijjigata har saida yaji tayi gyatsa sannan ya meda ita kan gadon ya kontar da ita,
d'akin shi yaje jim kad'an ya dawo hannun shi rik'e da magani ,
shida kanshi ya bata tasha sannan ta koma ta konta,
shi kuwa rafan kud'i ya ajiye mata a gefen ta wanda zasu kai dubu 100 sai kuma wata y'ar counter near yar k'arama sarkace da y'an kunne sai zobe,
zoben ya zaro sannan ya kamo hannun ta ya zura zoben a yatsarta dake kusa da y'ar karamar yatsar ta sannan yace.
"Gashi insu Anty Shuwa sunzo ki basu wannan kud'in da sark'ar."
Harara tayi mishi k'asa-k'asa sannan ta zare zoben ta jefar gefe,
shi kuwa parlour ya koma ya zauna,
ya zauna kenan su Anty Shuwa suka iso bayan sun gaisa ne sai ya fita shida ya SADIK daya kawo su.
Su Anty Shuwa kam tunda suka samu Ummul a konce ba lafiya sai sukayi zaton ta zama cikekkiyar matar aure,
yayin da Usman ma tunda Hamma Umar yace mai Ummul bata da lafiya kuma tana ta kuka sai ya d'auka Hamman nashi ya zama oggone a daren jiyan,
so haka suma su Anty Shuwa amman Anty Halima ita ta gane sarai ba abinda Hamma Umar yayiwa Ummul kawai ya bada tukuicin ne.
haka suka wuni suka yi tayiwa Ummul nasiha ta kuma ci abinci so ta samu tayi k'arfi,
sai yamma lis suka tafi.
bayan sun tafi kuma ta wore ras ta fito parlour dan a cewarta yanzu lokaci yayi da zata fara gasa Hamma Umar d'in.
Da dere yayi Hamma Umar yana d'akin shi bayan ya yayi wonka ya fito yayi shirin bacci har ya konta sai kuma ya mik'e ya nufi d'akin ta yana zuwa ya zauna gefen ta a hankali ya....
*Dedde na Allah ya baki lafiya*
By
*GARKUWAR FUlANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*RUBUTACCEN AL,AMARI*
Page 1⃣5⃣
*NA*
*AYSHA ALI GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*Alhamhadullih jikin Dedde na da sauk'i sosai ta samu lafiya nagode wa Allah daya bata lafiya kuma nagode muku masu kirana da masu turo min messages da yi mata addu'a a groups da masu bina pc, UWA uba wad'an da sukayi tattaki suka zo dubiya duk nagode da addu'oinku gareta ngd matuka Allah bar zumunci 🤝😘😍🤝*
*K*allon ta yayi cikin mamaki ganin yadda take konce duk ta duk'unk'une wuri d'aya gaba d'aya ta takura kanta ga kayan jikin ta duk ta konta dasu hatta hijabin kanta bata cireba ta nad'e guiwowin ta har suna tab'a k'irjin ta sai hannun ta data sa ta kame kafad'un ta sannan ta cusa kanta cikin pillow da kaga ganta kasan bacci takeyi amman cikin tsoro duk ta takure hatta numfashi ta da kalan tsoro take fidda sautin shi,
gyara zaman shi yayi yana fuskan tarta a hankali yasa hannu tare da kamo hijabin ya fara k'ok'arin zare mata shi a jikin ta,
ita kuwa cikin baccin tsoron da tunda tazo gidan a haka take rayuwa cikin tsoro dan ita bata tab'a kwana ita kad'ai a d'aki ba a rayuwar ta gata da tsoro amman kuma k'iyeyyar Hamma Umar d'in ta hanata kusantan inda yake ta gommace ta rayu cikin tsoro,
a hankali ta d'an motsa tare da k'ara jawo hijabin nata duk cikin bacci,
shi kuwa ganin ta d'an motsa ne yasa ya d'an janye hannunshi yayi shiru yana kallon fuskar ta,
can zuwa wani lokacin kuma ya d'an k'ara matsota sannan yasa hannun ya fara zaro hijabin har ya cire shi a kanta,
dai-dai sanda ya cire ita kuwa ta bud'e idonta,
gaba d'aya jikinta rawa yakeyi tamkar mazari sai wani irin zaro idanu tayi cikin tsoro ta mik'e tare da fizgewa tana tuttureshi,
shi kuwa Hamma Umar kamota yayi da k'arfi ya maidata kan gadon pillow ya jawo sannan ya kontar da ita kan pillow sai kuma yasa hannu a hankali ya fara zuge zip d'in rigarta,
ganin haka yasa ita kuwa tayi wani irin yunk'uri tare da sa hannu bibbiyu ta tureshi da k'arfi har saida kanshi ya bugi jikin gado da sauri ya dafe kanshi da hannun d'aya d'ayan kuma ya kamota ya rik'e gam,
cikin sanyi yace.
"Ina zaki je?
ki nitsu mana zakiji wa kanki ciwo fa zoki konta ba abinda zai sameki gani a kusa da ke."
hannu tasa tana ta kiciniyar b'amb'are yatsun hannu shi cikin tsiwa tace.
"Bana so ka sake min hannun na ka fita harkata ba ruwan ka da ni ka barni inje duk inda naga dama kar woni zo ka mak'ale ni kace zaka min dad'in baki ni bana sonka bana son ganin ka."
jawota yayi jikin shi cikin tsura mata ido yace.
"Bakya sona fa kikace khairi nifa d'an uwan kine."
"Eh bana sonka bana son ganin ka na tsanekaaa."
lips d'in shi na k'asa ya kamo ya rink'a tsotsa a hankali yana jin zafin kala manta ,
sai kuma ya k'ara matsota tare da zare rigar sannan yasa hannun yana kunce d'aurin da tayiwa zanin ta,
ita kuwa gaba d'aya sai wujijjigashi takeyi tana ta kici niyar kwace kanta amman ta kasa kawai sai ta sunkuyar da kanta tare da kafa bakinta a damtsen hannun shi ta datsa mishi cizo mai zafi dan gaba d'aya ta tsinke da Hamma Umar d'in,
yana jin yadda ta dasa hak'oran ta a damtsen hannun shi zafin yana ratsashi madadin ya saketa sai ya k'ara matsota jikin shi ido ya rumtse da k'arfi cikin wani irin yanayi yace.
"Zaki kasheni kike so? Ummu kiji tsoron Allah fa meyasa kika zab'i ki azabtar dani bayan kin san ni mijin kine."
Ita kam ganin bata da k'arfin kwatar kanta yasa ta saki kuka mai cike da tsoro murya a birkice tace.
"Ka sani wallahi ni bana sonka bana son ganin ka,
ka fita hanya ta."
Ido ya lumshe dan hak'ik'a yana jin ciwon yadda take cemai bata sonshi cikin sanyi yace.
" Khairi bakya sona ko ?"
"Ehh bana sonka."
Kai ya jinjina sannan yace .
"Kin dai san ni mijin kine ke kuma matata ce so kin san akwai hak'k'ina a kanki ko? kin kuwa san zaman aure mukeyi ni kuwa ba waliyi bane."
tureshi ta k'ara yi cikin kuka tana Jan hijabinta tana k'ok'arin rufe jikin ta murya na rawa tace.
"Ni bana sonka kuma ba zaman auren da zanyi dakai dan bazan karya al'k'awarin da nayiwa Mustapha ba ni ka sake ni."
ajiyan zuciya ya rink'a sauk'e wa cikin yanayin cushewar tunani ga yanayin canji daya tsinci kanshi a ciki shi da kanshi bai san yana da wannan halittar ba dan a zaton shi da zai iya rayuwa ko ba mace amman gaba d'aya tunda akayi auren yake jin bak'in al'amura a jikin shi,
saketa yayi cikin sanyi ya mik'e ya tsaya a bak'in gadon yana mai jin zafin kanshi data gwora da jikin gado da kuma cizon da tayi mishi,
hannun yasa ya kamo hannun ta a hankali yace.
"Ki dena kwana da bra a jikin ki yana haddasa ciwon k'irjin yana kuma iya jawo cancer ko ya sa miki toshewar numfashin,
ki dena kwana da kayan masu nauyi a jikin ki,
ki rink'a yin al'wala kafin ki kwanta ki kuma yi addu'ar bacci."
Baki ta tab'e cikin jin haushin sa tace.
"Nida jikina ba ruwan wani dani inyi yadda nike so kuma dole in kula da kaina tunda ina rayuwa da kai gida d'aya."
Murmushi yayi gano wai danshi take kwana a hakan,
hannun ta yaja har zuwa cikin bathroom a hankali yace.
"kiyi al'wala."
baki ta tura sannan tayi al'walar nan ma dan tasan hakan koyarwa ce ta annabi,
bayan tayi al'walan suna fitowa ta zauna bak'in gadon cikin tsiwa tace.
"Zanyi bacci fa."
Kai ya gyad'a sannan yasa hannu ya kontar da ita blanket ya jawo ya d'an rufeta ,
hannun shi na cikin blanket d'in ya sunkuye kanta a hankali yace.
"D'an d'ago bari in cire miki bra d'in."
harara tayi mishi k'asa-k'asa cikin tura baki tace.
"Ni ai ba karuwa bace."
sai ta kuma ture hannun shi sannan ta juyo ta konta ta a kife,
shi kuwa Addu'a yayi tare da shafe jikinta kamar yadda ya saba yiwa Usman ,
sannan ya kalleta ahankali ya juya ya fita,
a parlour ya konta tare da son jin d'umin ta Amman yasan hakan bazai samu ba,
haka ya kwana cikin halin takura.
Haka rayuwa taci gaba da juya musu duk wata kulawa da gata Hamma Umar yanayiwa khairn shi yayin da ita kuwa take ta azabtar dashi ,
ta yadda baya samun ko magana mai dad'i ma bare ya samu hakkin shi dake kanta duk da yana yawan zuwa inda take amman haka ba abinda yake sama mishi sai azaba da bak'in ciki ko tafin hannun ta bai isa ya murzaba sai yasha bak'ar magana.
Yau Monday kuma Yau kwanan su takwas da tarewa kenan,
yau tunda sassafe Hamma Umar ya shirya komai tsab kamar yadda yasaba sannan ya shiga wonka sauri sauri ya shirya dan yau zai fita zaije gidan governor dan duba lafiyar shi duk da dai bai gama hutun auren nashi ba amman zaije dan duba lafiyar shi ,
bayan ya gama shirin shi tsab sannan ya fesa turaren shi mai tarin k'amshi laptop nashi da phone dinshi ya d'auko sannan ya fito parlour kan dinning table ya ajiye su ,
sannan ya jawo cups guda biyu tea ya had'a ,
sannan ya d'an juya rik'e da cups d'in ya nufi cikin parlour gaban Ummul d'in ya d'an tsaya cikin sanyi yace.
"Khairi taso kisha tea sauri nake zan fita yanzu zan dawo."
kallon shi tayi sannan ta kalli yadda tea d'in yake ta tiriri da alamun ruwan yana da zafi sosai ido ta lumshe cikin jin dad'in shawarar da shaid'an ya kawo mata fuskar shi ta kuma kalla cikin mugunta ta mik'e ta tsaya a gaban shi,
hannu tasa ta karb'i cup d'in tare da tsura mishi ido,
shi kuwa kanshi ya sunkuyar tare da d'an juya tea spoon d'in dake cikin cup d'in,
itako murmushi mugunta tayi,
cup d'in ta d'ago tare da watsa mishi ruwan zafin a fuskarsa ,
ba zato ba tsammani yaji ta watsa mishi tea d'in a fuskar da jikin wani irin zafi da rad'a d'i yaji yana ratsashi,
jin zafin ruwan daya sauk'a a jikin shi yayi wani irin yunk'uri ya hankad'ata da k'arfi saida ta fad'i k'asa,
sai kuma cup d'in hannun shima ya sub'uce yayi k'asa,
hannun shi ya rink'a yarfawa yana d'an jujjuya kai yana jin zafin na ratsa fatarshi har cikin zuciyar shi yake jin zogin,
a take fuskar shi tayi jazir sai zufa keta keto mishi tako ina,
ita kuwa Ummul yana tureta tana fad'uwa ta kife kai tare da sakin kuka,
kuka ta saki da k'arfi shi kuwa jin kukan yayi sauri yayi kanta yana zuwa ya d'ago ta ya sa hannu biyu ya rik'e kafad'un ta ido ya zuba mata cikin wani irin yanayi ya lumshe ido murya a sanyaye yace.
"Kiyi hak'uri Ummulkhari bawai na tureki dan zafin ruwan da kika watsa min bane,
a a wallahi na tureki ne dan kar ruwan ya fantsalu ya dawo jikinki ya k'onaki ,
kiyi hak'uri."
Ido Ummul ta zuba mishi tare da k'ara sautin kukan nata tanayi tana mita,
a cikin zuciyar ta kuwa tabbas ta cika da mamaki har cikin ranta taji mamakin yanayin da Hamma Umar keyi mata magana a yanzu bayan k'onashi tayi sannan kuma shike bata hak'uri har kuma yana cewa ya tureta ne dan kar itama ta k'one,
kuma a zahiri da kaga fuskar shi kasan yana jin zafin k'unan amman bai bi ta kanshi ba ya tsaya bata hak'uri,
shi kuwa Hamma Umar har cikin ranshi bawai ya tureta dan ta watsa mishi ruwan zafin bane kuma yaji zafin yadda ya ture harta fad'i har takai da tana kuka,
a hankali ya kuma matsota yana kallon bakinta da take ta kuka da iya k'arfin ta ya lura so take ta tara mishi mak'otan su,
kuka take tana.
"Allah zai saka min ka rabani da kowa nawa kazo kana azabtar dani na tsane k...!"
a hankali ya sunkuyar da kanshi cikin sauri ya manne bakin shi da nata lips d'in ta yayiwa rik'on taushi ida nunshi ya lumshi tare dasa hannun shi d'aya ya zagayo k'ugunta ,
ita kuwa ido ta zazzaro woje cikin tsantsar firgita da tsoro ga tarin mamaki Hamma Umar ne ke manne bak'in shi da nata ,
gaba d'aya ya rufe bak'in manata ya hanata kukan bare rakin da takeyi da son tara mishi mutanen,
shi kuwa Hamma Umar idon shi a lumshe ya sab'ule lips d'in ta a bak'in shi cikin lumshe ido ya juya ya koma bedroom d'in shi ,
wonka ya sake yi sannan ya canza kaga ,
ya fito parlour kan dinning table yaje phone d'in shi ya d'auka kanshi a sunkuye yazo gefen ta ya tsaya yana jin yadda take yin kuka a hankali yace.
"Ayyah Khairi kiyi hak'uri kibar kukan nan kinji bari inje in dawo ki gaya min me kike son in miki."
mik'ewa tayi ta nufi bedroom d'in tana kukanta na rashin gaskiya,
haka ya fita yana mai tuhumar kanshi daya gaza rik'e amanar daya d'auka.
Tunda ya fita bai samu ya dawo ba sai 9:34 pm ,
yana shiga cikin gidan bedroom nashi ya shige wonka yayi sannan ya fito d'aure da towel a parlour ya d'an zauna jin gidan shiru kamar ba kowa a ciki,
mik'a yayi tare da lumshe ido tabbas yana buk'atar kulawar Ummul amman haka ya faskara zuwa yanzu ya fara k'asa yin control d'in kanshi,
a yanzu kuwa ya gane cewa shi mutunne mabuk'aci mai son kulawar matar sa,
a hankali ya mik'e ya nufi d'akin nata cikin sa'a ya samu k'ofar a bud'e take a hankali ya murd'a hannun k'ofar tare da turawa ,
yana shiga ya haggota kwance kan gadon,
k'ofar ya maida ya rufe cikin sanyi ya zauna gefen ta a hankali ya kwanta tare da sauk'e ajiyan zuciya jikin shi ya manna da nata a hankali yasa hannu ya jawota jikin shi ,
kan k'irjin shi ya kifeta a hankali ya fara shafa gadon bayan ta murya can k'asa cikin rad'a yace.
"Ummul khairi ! Khairi ki tashi."
ido ta bud'e cikin yunk'uri tare da yin mutsumutsu tana.
"Wallahi bana so ni ka fita harkata."
A hankali ya k'ara matsota bak'in shi ya saita cikin k'annen ta iska ya d'an hura mata cikin rauni da rawan murya yace.
"Ki tausawa min Ummul khairi ki jik'aina ki tallafa min ki bani hak'k'ina Khairi karki zamto silar sani cikin wani hali."
tureshi takeyi tana
"Ni ba ruwana da halin da zaka shiga in saka cikin wani halin ko kasa kanka ka sakeni in auri wanda nake so kamai kaje can ka nemi wacce zata soka."
cikin rawan murya kamar zaiyi kuka yace.
"Khairi ki tausayawa mijinki Ummul nifa d'an uwanki ne zakiso na cutu plzz kiyi hak'uri ki amince dani Ummul bazan cutar da keba karki cutar dani ki barni na rab'i jikin ki ,
in ban rab'eki ba wa zanje in rab'a?."
jin yadda yake magana yana cakud'ata da juyata yasa ta rink'a kuka tana birgima har saida ya saketa sannan ya zauna gefen ta yana mai karkarwa,
ita kuwa ganin haka ta mik'e ta koma parlour.
Daga wannan ranar haka suke rayuwa kullum da salon azabar da Ummul ke shirya wa Hamma Umar d'in shi kuwa gaba d'aya yana rayuwa ne cikin tarin bukarta yayinda hakan ya k'ara bawa Ummul damar juya shi haka kwana ki suna tafi mokonni sunja har sun fara irga watanni,
Hamma Umar kuwa har yau baisan menene dad'in aure ba shi kuwa bai iya kai k'araba bare ya kai karanta,
Anty Halima na yawan kiran Hamma Umar tace ya Ummul ta nitsu ko? sai yace mata ehh ba komai fa,
ita kuwa Anty Halima bata gamsuwa hakan yasa tana yawan zuwa weekend toh hakan yasa kab ta lura da zaman da suke yi.
ya Usman kuwa tunda akayi auren yak'i zuwa a cewarsa sai Ummul ta dena kuka,
Hamma Umar kuwa rana d'add'aya ne baya zuwa cikin pataskum shida k'anin shi sunyi ta hira yana kula dashi kamar da sukan je gun Amminsu,
su wuni.
Yau Saturday tun safe Anty Halima da Hajjajo da inna da Aliyu suka shirya zasu je gidan su Hamma Umar d'in ,
Hajjajo kuwa ta dage sai dai Ya Usman ya kaisu ,
dolen shi a hakan badon yaso ba ya kalli Hajjajo tare da cewa.
"Toh sai ku jirani na shirya ai Hajia Yawo."
murmushi tayi tare da cewa.
"Zamu jira jeka shirya,
dan ni nafi yarfa da tuk'in ka kaida Umaru,
Adam gudune dashi Abubakar ko motarsa kamar zai fire in mutun ya shiga."
Murmushi kawai yayi ya tafi part d'in su,
yana zuwa wonka ya shiga amman ya kasa sai kife kanshi da yayi a jikin gini ya rink'a wani irin kuka mai cin rai zuciyar shi na harbawa da k'arfi zuwa yanzu Ya Usman shi kad'ai yasan idan yayi tarin yakan ga jini amman yak'i gayawa kowa dan ya naga shi lokacin sane ya kusa.
Haka yasha kukan shi sannan ya shirya ya fito suka tafi idanun shi na cike da begen ganin Ummul d'in.
A gidan Hamma Umar kuwa yau kwana yayi cikin takura haka ya wayi gari a buk'ace
bayan ya dawo masallaci d'akin shi ya wuce da niyar ko zai samu yayi bacci amman ina baccin yak'i zuwa,
dole ya fito ya nufi d'akin nata yana shiga ya haggota tana zaune bakin gado cikin sanyi ya zauna gefen ta,
shiru yayi yana kallon ta,
ita kuwa tab'e