tara na dare ta zuge labulayen dakin ta don ta samu ta shaki fresh air. Wani abu ne guda daya ya dauki hankalin ta, a cikin wata bakuwar mota ta hangi Hanan tare da wani kyakkyawan saurayi, abinda idanunta suka gane mata ba karamin kidimata ya yi ba.
Hanan ta bude kofa kafarta daya na waje, yayin da jikinta ke cikin motar suna sumbatar juna ita da saurayin. Sun jima a haka kafin Hanan din ta fito tana daga masa hannu, yana daga mata ya ja motar ya bar gidan.
Da sauri ta saki labulen gabanta na wani irin bugu na tashin hankali. Hanan ta murda kofar dakin ta shigo tana cilla jakarta tana cafewa, da gani cikin nishadi ta ke. Amma kallon fuskar Halimah kawai ta yi ta shiga taitayinta. Halimah ta hadiyi miyau da kyar, ta ce.
“Hanan, waye ya sauke ki a mota yanzun nan?”
Hanan ta yi shiru, Halimah ba ta jira amsarta ba, ta kwashe ta da mari, tace,
“Me na ga kuna yi cikin mota haka?”
Da farko Hanan ta nuna firgici, don ba ta taba zaton Halimah ta gansu ba. Sai kuma ta fuske ta dubi cikin idon Halima tana hawaye ta ce.
“Saurayi na ne… an ce ba za mu yi aure ba… bautar ofis kawai za mu yi muna tarawa Daddy kudi… bayan ni kuma mutum ce ba mutum-mutumi ba. In ba mu yi romancing a mota don rage wa kanmu zafi ba so ake mu je mu kama daki a hotel ko me? Mts!”
Ta yi tsaki tare da ficewa daga dakin, ta banko wa Halimah kofarta.
Da kyar Halimah ta lalubi gefen gado ta zauna. Ga wadda ta fi ta iya protest, sai dai nata akwai tarin kuruciya a ciki da karancin ilmin addini. Amma sai ta ga cewa tunda har Hanan ta bude baki ta fadi haka, ya tabbata aure ta ke so itama, ba ta da yadda za ta yi. Sai ta ga cewa kamar wata sassaukar hanya ce Allah ya kawo mata wajen gabatar da bukatarta ga Daddy, idan har Hanan za ta ba ta hadin kai su duka su taru su ce aure suke so.
Fita ta yi zuwa dakin Hanan, don sauri har tana tuntube. Ta same ta tana canza kayan jikinta, ga yatsun Halima sun kwanta lambam a farar fuskarta, ta tausasa murya ta ce,
“Ki yi hakuri Hanan!”
Jin da sulhu ta zo ba da wa’azi ba, ya sa Hanan ta dakata da abin da ta ke yi, ta dan ba ta hankalinta. Halimah ta yi mata murmushi ta ce, “Wajen ki na zo, magana za mu yi ta fahimta”.
Hanan ta koma bakin gado ta zauna, Halimah ta zauna a kusa da ita, ta dubi Hanan ta ce, “Na samu miji, aure zan yi Hanan”.
Hanan ta bude baki tana kallonta, da kyar ta iya cewa, “With Daddy’s consent (da amincewar Daddy)?”
Halima ta ce, “Har yanzu ban samu guts din gaya masa ba, amma tabbas aure zan yi”.
Hanan ta motsa baki a hankali kamar mai ciwon hakori ta ce,
“Ni sau nawa ina samun mijin yana korar su? Amma wallahi wannan karon ba zan iya rabuwa da Saleem ba”.
Halimah ta sanya hannunta cikin na Hanan ta ratsa yatsun su (fingers cross) Sannan ta ce,
“Then we have to unite and protest!”
Hanan ta dan fiddo ido cikin tsoro ta ce, “Ina tsoron Daddy, kin san dai tunda muka taso maganarsa daya ce ba zai aurar da mu ba, saboda baza'a iya rike masa mu ba, amma zai yi mana komai a rayuwa…”.
“Kina tsoron Daddy, amma ba kya tsoron Mahaliccinki? Wannan abin da ki ke aikatawa is an act of fornication (nau’in zina ne) wanda ba komai ya janyo miki ba sai rashin aure. Hanan, mu karfafi kanmu mu fuskanci Daddy, ni na gaya miki a karshe zai hakura ko da da farko ya nuna rashin amincewar sa, kada ki manta shi ya haife mu, ba shi da abin da ya wuce mu.
Duk hukuncin da zai mana a kan hakan ba zai yanke mu daga jikinsa ba. Iyaka ya yi fushi na dan lokaci ya huce. Idan ba za ki ba ni goyon baya ba mu kwaci ‘yancin mu da addini ya ba mu ba, ni zan yi aure na in tafi in barki a gidan nan ke kadai. Ya rage naki”.
Tana gama fadin haka ta mike za ta bar dakin. Har ta kai bakin kofa hanan ta kira sunanta. Dakatawa ta yi ba tare da ta juyo ba.
Hanan ta tako a hankali ta zagayo gabanta, idanunta fal hawaye ta ce,
“Ba zan iya zama a gidan nan babu ke ba. I’m with you sis Leemah”.
Sai hawaye ya gangaro daga idonta.
Halimah ta kai hannu tana share mata.
“In dai Saleem da gaske yake ki gaya masa ya fito. A goben nan za mu tunkari Daddy a yi ta ta kare. Amma sai kin cire tsoron Daddy a ranki Hanan za mu yi nasara”.
Hanan ta gyada kai, ta ce, “Insha Allah”.
*****
BABI NA SHIDDA
Prof. Zubair Muhammad Numan, yana zaune a balcony din shan iskarsa kan wasu kujeru sakar kaba, yana sauraron radiyon da ke gefenshi, inda ake labaran VOA na harshen hausa, misalin karfe goma na safe, kasancewar ranar asabar ce babu aiki. Halima da Hanan suka shigo a tare, kowacce sanye da bakar jallabiya kamar wasu takarun Makkah, kai a kasa salalaf-salalaf suka shigo inda yake, kowacce ta je gefen kafarsa daya ta zauna.
Ya rage sautin radiyon ya ba su hankalin sa.
“What happened my daughters?” Saboda bai saba su zo su zauna a kasa don yana kan kujera ba, sai dai su zauna a hagu da daman sa.
Halimah ta ambaci sunan Allah Al-Hakeem gwanin hikima, don ya bata hikimar zance, Zarah ta taba koya mata wasu ayoyi daga Suratul-Daha in kana so a fahimce ka, tace a hankali;
"Rabbi sharahli sadry, wayassirly amri, wahlul uqdatan min lisany, yafqahu qauly...... sannan ta kwarara zuciyarta, ta soma magana cikin sanyin murya.
“I’m sorry Dad, I’m very sorry Daddy, idan abinda zan fada bai maka dadi ba. Na zo yau in gaya maka cewa, na tsayar da miji. Suna so a ba su lokaci su zo tambaya”.
Tana rufe baki, Hanan ta dora nata.
“Daddy, ni ma na samu miji, dan gidan Minister Usman ne, sun ce suna so su zo tambaya in an ba su appointment”.
Kowacce ta sunkuyar da kai kasa, gabanta na dukan tara-tara ba uku-uku ba. Don ba karamin practice da rehearsal suka sha a daki ba kafin su shirya wadannan gajerun kalaman.
Prof. ya yi musu kallon tsaf, sannan yayi dan murmushi, ya ce,
“Wato kun je mazan banza sun hure muku kunne ku yi min rashin biyayya ko? Sau nawa zan gaya muku ba zan iya aurar da ku ba? Yanzu har kun yi girman da za ku dubi tsabar idona ku ce min aure ku ke so Halima da Hanan? Me ku ke so? Me za ku samo a gidan auren wanda babu shi a gidanku? Ku tashi ku ba ni waje tun ban sa kafar wando daya da ku ba”.
Halima ta hadiyi miyau da kyar tace "Dad! Na gaya maka aure nake so, shekaruna 24, sai na tsufa na rasa mashinshini saboda biyayyar ka? Kace karatu, mun yi kowanne irin karatu, kace aiki, gashi muna ta yi maka, mun tara maka kudi wadanda zasu isheka har karshen rayuwar ka, a yanzu hakkin mu na 'yan adam muke bukata, 'yancin da Allah ya baiwa kowa na raya sunnar Manzo, ko don mu bamu da UWA? Bamu da wani majibinci da zamu kaiwa bukatar mu bayan kai?" Ta fashe da kuka.
Hanan ma ta zaburo "Daddy na yi hakurin Allah na yi na manzo, ka yi min aure ina son Salim bazan iya hakura da shi ba".
Don bakin ciki ya rasa me zai ce musu, anya 'ya'yan sa da ya sani ne wadannan? Hanan da Halimah masu kunya da kawaici? Wace irin fitsara suka koyo haka? Aure wane iri? Ba dai a gidan sa ba! Shi da girman sa bai damu kan sa da wani aure ba sai su? Da me ya rage su?
Sai kawai ya tashi ya bar su a wurin, don ya tabbata in ya cigaba da kallon su a gaban sa zai iya illata su. Auren banza auren wofi me zasu je su samo a gidan auren wanda baya basu? Su yara ne basu san wani me auren ya kunsa ba (a tunanin sa fa).
Tun daga ranar Hanan da Halima suka hada baki suka daina cin abinci, suka daina zuwa ofis, ko falo sun daina fitowa, kullum suna kwance a gadon dakunansu kamar ruwa. Shi ma Daddyn ya yi fushi mai tsanani ba ya neman su. Damuwarsa daya ce, ofis da suka daina zuwa. Ba ya son ya bai wa bare ko ‘ya’yan talakawa wadannan guraben aikin a NCC, ya fi so daga shi sai ‘ya’yan cikinsa su ci gaba da cin gajiyar NCC su kadai, ga ‘ya’yan sun yi masa murabus za su bula masa kasa a ido.
Kwarai yake cikin damuwa, musamman da kukunsu Helen ta same shi har falonsa ta gaya masa yau kwana uku tana kai abincin Halimah da Hanan dining amma yadda ta kai haka ta ke daukowa, ba sa tabawa. Ba ta san me suke ci ba, tana tsoron kada ulcer ta kama su. A kwance suke wuni, a kwance suke kwana, in ta musu magana ba sa amsa mata.
Hankalin Prof. ya fara tashi, zai iya jure komai, amma ban da zamansu cikin yunwa. Shi kuma har gobe bai shirya rabuwa da ‘ya'yan nan nasa ba. Ya damka su ga wani banzan namiji da bai san darajar su ba. Me zai gaya musu su gane bayan wanda ya yi shekara da shekau yana gaya musu, amma rana daya suka sa kafa suka yi fatali da shi?
Haka ya danne bacin ransa yau da ya dawo ya shiga dakin nasu. Halin da ya riske su a ciki ya yi matukar daga masa hankali.
Kwanaki uku kacal bai gansu ba, amma har kasusuwan wuya sun yi. Sannan kwanaki uku kenan da fatar jikinsu ba ta ga ruwa ba balle sabulu. Idanunsu sun yi zuru-zuru sun zurma ciki da yunwar da suka sanya kansu. Ruwan lipton kawai suke sha, wanda suke jonawa a kettle a dakunansu. Shi kuma lipton ma’abota shanshi sun sani ba ya maganin yunwa, sai ma ya rarake ciki.
Ya ce, “Is that serious to this extent? Ku same ni a falo mu yanke magana ta karshe”.
Suna tangadi da dafa bango kamar wadanda suka sha kayan maye suka bi bayan Daddy falon sa kamar yadda ya bukata.
Sai da suka zauna a gefen kafafunsa sannan ya fara da tambayar Hanan wane ne mijin da ta samo, kuma a ina suka hadu? Kada ta boye masa komai, ta gaya masa gaskiya.
Hanan ba ta boye ba, ta gaya masa haduwarta da Saleem a wajen dinner din kawarta, da inda yake aiki, wato shell company da kuma ko wane ne mahaifinsa. Ta kare zancenta da cewa, kuma shi da gaske aurenta zai yi, idan har Daddyn ya ba shi dama.
Ko babu komai Prof. Zubair ya dan ji sanyi a kan zabin nata, jin cewa ba karamin gida ta samo mijin ba. Domin Minister Usman sananne ne a Nigeria. Halimah ma ya yi mata tambaya irin yadda ya yi wa Hanan.
Halimah ta sunkuyar da kanta, kirjinta na bugawa. She is not sure… ko Daddy zai yi farin ciki da zabinta. Ga alama ya karbi na Hanan. A hankali cikin sanyin muryarta ta ce,
“Daddy, Hashim ne!”.
Kwata-kwata hankalinsa bai kawo masa wanda ta ke nufi ba. Ya ce, “Wane ne ubansa?”
Wannan tambaya ta yi wa Halimah rashin dadi. A raunane ta ce, “Mahaifinsa ya rasu”.
Ya yi dan jim, sannan ya ce, "Waye mahaifin nasa nake tambayarki?”
Halimah ta karfafi zuciyarta ta fito fili ta gaya wa mahaifinta ko wane Hashim ta ke nufi, ba wani ba ne sai Personal Assistant din ta Engnr. Hashim Yakasai.
Wani ashar Prof. ya saki, ya kara da cewa, “Ban san ba ki da hankali ba sai yau, domin a da kallon wadda ta fi kowa hankali da tsinkaye nake miki".
Halimah ta soma kuka tana rokon mahaifinta, ta kama kafarsa ya fizge ya tashi ya barta a wurin tana gursheken kuka.
Hanan ce ta kamata zuwa daki, kafin azahar sai ga Halima tana suma idanunta na kakkafewa. Hanan ta firgita, a guje ta fita falo tana kuka tana rokon Daddy ya zo ya ga Halimah. Da farko ya ki ko kallon inda ta ke, sai ga kukunsu a guje tana gaya musu Halimah rai ya yi halinsa… she is no more… tana cilla hannuwa tana kiran Jesus ya taimake ta.
Zuciyar UBA… Jin cewa Halimah ta mutu bai sa shi yin nadamar hukuncin da ya yi mata ba, don da ya hada jini da talaka mai ci a karkashinsa gara komai zai faru da ita ya faru. Zuciyar sa ta yi laushi ne da ya tuno ko wace ce Halimah a gare shi. Ta rayu cikin biyayyarsa da kaunarsa a kulliyar rayuwarta. Ta fi Hanan yi masa biyayya… hatta aikin nan ba so ta ke yi ba, tana yi ne don amfaninsa. Albashinta bata taba komi a banki take barin sa....tace shi take taramawa. A hankali ya mike ya bi bayan Hanan wadda ta rufa a guje (helter-skelter) zuwa dakin Halimah.
Tsintsiyar hannunta ya kama ya saurara, sai ya fahimci da sauran numfashinta, watakila dai doguwar suma ta yi, da kansa ya dauke ta zuwa mota, ya yi asibitin da suke zuwa da ita.
Suna zuwalikitoci suka karbi Halimah, aka rufu a kan ta. Kwana uku ana abu daya, Halima ko ta farfado sai ta kara sumewa, Hashim bai san abindaake yi ba don a zaton sa har lokacin Halima na hutu ne.
Ba karamar jinya Halima tayi ba, kafin ta soma shaida wadanda ke kanta, gabadaya ta fita hayyacin ta, kwana bakwai cur tana kwance gadon asibiti sai ruwa da ake kara mata akai-akai da allurai. Daddy ba karamin tsorata yayi ba, ya yarda da gaske take soyayyar, Hanan ce mai jinya, duk sanda Halima ta farka sunan Hashim take ambato tana rokon Hanan ta kira mata shi su yi sallama mutuwa zata yi. Bazata iya cigaba da rayuwa ba shi ba. Hanan sai kuka. Don ita bata son zancen Hashim dinnan itama, ta kuma yarda da gaske Halima take zata iya rasa arayuwar ta a kan sa.
Don haka ta dau wayar Halima ta kira Hashim da sunan da Halima tayi saving din lambarsa "Cheriè". Hashim na dagawa yace "Sweatheart, kina so ki kashe ni ne? Ba kira ba messege? Ni in na kira bata shiga, saura kadan ki ganni a kofar dakin ki, hutun nan ya isa ki dawo haka! I can't afford missing you....i love you....". Hanan tayi maza ta cire wayar daga kunnen ta, he's so caring dole ya tafi da rayuwar diya mace. Sai ta ji bazata iya karya zuciyar sa ba, don ko ya zo Daddy ba bari zai yi ya shigo ba, ya kafa ya tsare da kujera a gaban gadon Halima kullum. Shima bai zuwa ofis, komai akan sakatare da Hashim yake.
Jinyar Halima ta ki ci ta ki cinyewa. Daddy bai da niyyar janye ra'ayin sa itama bata da niyyar janye nata. A binciken likitoci kuma sun ga cewa jinin Halimah ya yi mugun hawa, zuciyarta kuma ta tabu. Suka yi wa Daddy nasiha a kan ya yi hakuri ya yi mata abin da ta ke so don tserar da lafiyarta. Yaran yanzu ne ka haife su, amma sai dai ka bi su ba dai su bi ka ba. Daddy don bakin ciki kasa kallon Halimah ya yi lokacin da ta sake farfadowa, wannan karon ta dan jima bata kara suma ba, don haka aka kai ta aminity room.
Daddy ya tura kofa ya shiga dakin da Halima ke kwance. Tsayawa ya yi a kanta yana kallon irin zabgewar data yi, gabadaya ta lalace ta fice hayyacinta. Babban takaicin sa wai akan Da namiji. Da namijin ma wanda bai isa ya mallake ta ba, mai ci a karkashin ta, yayi kwafa ya dube ta cikin ido ya ce.
“To Halimah, zan miki abin da ki ke so, wato auren dan talakawa, dan aikinki, boyi-boyin ki. Amma bisa sharudda uku kwarara in kin amince”.
Halimah ta daga kumburarrun idanunta tana sauraron Daddynta.
A yadda yanayin fuskar Daddy ya