AURE KO BOKO 1&2 BY TAKORI

Author :  Takori Category :  Romance

Chapter   16 / 16

45K to 47K   out of 47K words

ba abin da yake so yake mafarki irin SIYASA.
A daidai wanan lokacin Maama (Safiyyah) ta cika shekara guda, sabanin wasu makafin da idanunsu ke a bude garau gani ne ba sa yi, Safiyyah idanunta a rufe suke ruf! Tun a wannan lokacin Safiyyah ta san muryar uwarta ta san ta ubanta. Ta san ta lalubi fuskokinsu ta gane su. Ta san in ta ji muryar babanta ya dawo ta fito da gudu ta yi masa oyoyo! Ko da kuwa za ta ci karo da wani abun ta fadi ta buge ko ta ji ciwo ba ta fasawa.
Wata irin soyayyah suke yi wa Maama, ko sauro ba sa bari ya cije ta. Kullum tas-tas da ita cikin wanka da kyakkyawar suttura. Yadda Halima ke kula da ita ba ta kula da kanta haka.

******
“Duk inda za ki nemo min lambar wayar uban yaron nan ki nemo min yanzu-yanzu”. Prof. ya fada yana duban Hanan da rinannun idanunsa.
Wayarta ta dauko daga jakarta ta budo lambar Baban Salim ta mika masa.
A take ya dau lambar a wayarsa ya kira, sakatare ne ya dauka ba bata lokaci ya fada masa ko shi waye, kuma so yake ya ganshi, in zai yiwu a gida don family matter ne.
Minista ya san ko waye Zubair Numan, amma bai taba sanin yana da alaka da matar dansa ba. Sabida ba shi ya karbawa Salim auren ba kaninsa ne, kuma ba mazauni bane sannan irin mutanen nan ne ba masu kwakkwafi ba. Nan ya bada appointment karfe takwas na daren ranar.
Karfe takwas din kuwa a harabar gidan Ministan ta yi musu, shi da Hanan tana dauke da babynta.
Fargabar duniya ta ishe ta, don Daddy bai gaya mata inda za su zo kenan ba, da ta fara kiran Salim ta gaya masa.
Minista ya sa aka yi musu jagora zuwa falon saukar bakinsa na musamman. Ya sa aka cike gabansu da abin tarbar baki, amma sai ya lura chairman a masifar fusace yake.
A hakan suka gaisa, Daddy ya ce ya yi masa alfarma uwargidansa ta kasance a wajen don abin da ya kawo shi ya shafe ta.
“No problem”. In ji Minista, nan ya kira Hajiya Mubina. Ba jimawa ta shigo tana taku daidaya. Ganin Hanan zaune rungume da jaririya ya ba ta mamaki.
Daddy ya nuna Hanan, ‘Kun gane wannan?”
Hajiya Mubina ce ta ce, “Kwarai na gane ta mana, ba Hanan ba ce?”
Prof. ya ce, “Da kyau, ‘ya ta kenan ta biyu cikin ‘ya’ya biyu kacal da Allah ya ba ni, wadda dan ku ya aura ya saki babu dalili. Now, kun ga wannan…”
Ya nuna ‘yar hannun Hanan, “Ke ba ni ita nan”.
Jiki na rawa Hanan ta ba shi ita, ya dauka ya kai wa Minista har wajen zamansa. Da sauri ya karbi ‘yar ganin yana neman kwala ta da kasa.
“Jikarku ce ta gaba da fatiha na kawo muku, kun raba su ta karfi ba su rabu ba, ga sakamakon abin da suka zaba nan. Na gama nawa kukan, saura ku. Hanan tashi mu tafi, Allah ya ba mu alkhairi’.
Hanan ta ki tashi kamar an kafe ta, ZUCIYAR UWA! Ko kusa ba ta jin za ta yarda ta bar falon nan ba tare da ‘yarta ba.
“Daddy, Yusra fa?” Ta fada muryarta na rawa.
“Yusran uwarki? Kanwar uwarki ce ko kanwar ubanki? Za ki tashi mu tafi ko sai na fasa miki baki da hanci?”
Ya juya ga Minista, “Kai dan siyasa ne, muddin ka dawo min da ‘yar gaba da fatiha gidana sai na tona wa media ta ji. Wallahi ba ku san ni ba, ba wai bana son ‘yata ba ne, bata min rai kawai ta yi”.
Ya fizgi hannun Hanan ya tankada keyarta.
Minista ya sassauta murya abin tausayi.
“Amma Prof. kamata ya yi ka zauna mu yi magana ta nutsuwa ko? I never know she is your daughter, ce min suka yi ba a san salinta ba, ba ta da iyaye balle dangi. Ko ba haka ki ka ce ba?” Ya jefa tambayar ga maidakinsa.
Ta sunkuyar da kai hawaye na bulbula. Yau ina za ta kai dan shege a cikin jikokinta?
“Ka yi hakuri Prof. ka zauna mu fahimci juna. Na hada ka da girman Allah”.
Jikin Prof. ya yi sanyi, ya saki Hanan ya samu kujera ya zauna.
“Ka bari in kira Salim, ya zo ya tabbatar min ‘yar nan tasa ce, duk da biri ya yi kama da mutum, kuma ido ba mudu ba amma ya san kima. Ga kamanni sun bayyana kansu”.
Ya dauko waya yana goge hawaye ya kira Salim. Cikin sa’a shigowarsa gidan kenan.
Yana shigowa falon ya ja turus! Ya tsaya yana rarraba idanu. Uwar da uban suka bi shi da kallon takaici. Sai ya tsugunna yana gaida Prof. ya ki amsawa.
Minista ya ce, “Salim, is this your daughter?”
Ya nuna yarinyar da ke rike a hannunsa.
Kansa a kasa, bai taba jin kunyar iyayensa a duniya irin yau ba, jinsa yake tamkar tsirara a gabansu. (Kunyar duniya ma ke nan kafin ta lahira. Allah ka yafe mana kura-kuranmu, ka sa muna daga cikin bayinKa muminai, Ka kare mu daga dattin zina).
Cikin tsawa mahaifinsa ya maimaita masa tambayar. Kansa a kasa ya ce, “Eh, ni na haife ta, kuskure ne mun tuba mun bi Allah mun tuba”.
Uban ya ce, “Amma ka san you have tarnished the image of this house ko?”
Hawaye suka zubo wa Salim, ya ce, “Wallahi Daddy sau daya ne, Allah ne ya yi nufin kasancewar hakan. Mun tuba muna rokon Allah gafara, muna rokonku ku gafarta mana ku ma. Shaidan ne… kuskure ne...…”.
Ya fashe da kuka.

Minista ya maida dubansa ga Prof. cikin lallashi ya ce, “A karkashin sulhun da nake nema, ina rokon ka maida masa auran matarsa, tunda akwai sauran zama a tsakaninsu, ko nawa ka yanke sadaki zan biya. Mu taru mu yi ta istigfari, kuskure ne duk mun yi, ga shi garin kokarin kare martabarmu mun jawo rugujewar martabar gabadaya. Maida aurensu shi ne maganin komai, kuma rufin asirin yarinyar. Da kwanciyar hankalinmu gabadaya. Ka yi hakuri Prof. ka amshi wanan sulhun”.
Shiru Prof. ya yi, Minista bai yi kasa a gwiwa ba ya ci gaba da rokonsa, har sai da Hajiya Mubina ta sa baki ita ma, sannan ya koro musu sharudda na rikon auren diyarsa; za su rike ta da kulawa, mutunci da kyautatawa.
Za a sake dauro auren a garin Numan cikin danginsa ba a Abuja ba, don su daina zaton ba ta da dangi. Sannan babu gori tsakaninta da kowa nasu kan wannan yarinyar data haifa, duk Minista da Hajiya Mubina suka ce sun amince.
Ya yanka sadaki yadda ya ga dama, duk dai sun amince. Sannan ne ya amince za a mayar da auren jibi a Numan bayan saukowa daga sallar juma’a.
Salim da iyayensa suka yo musu rakiya har jikin motarsu. Hanan ta ki yarda ta kalli inda Salim yake, shi kuma sai kokarin su hada ido yake amma ta ki, har suka shige mota direbansu ya ja suka tafi.
Suna shigowa gida Hanan ta shige daki rike da Yusra ta kira Halimah ta labarta mata duk abin da ya faru. Halimah ta ji dadi, ta kuma taya ‘yar uwarta murnar samun maslahar rayuwarta, sannan ta ce da Hanan cikin wata irin kakkausar murya.

“In ki ka gaya wa Daddy kin san inda nake, ko kin san wani abu da ya shafe ni; BA ZAN TABA YAFE MIKI BA! Kamar yadda ba zan taba yafe masa ba har duniya ta nade’.

safiyya ta wayi gari da bakon dauro (kyanda). Wannan ya tada hankalin Halimah da Hashim ba dan kadan ba. Wadanda ko kuda ba sa so ya sauka a kan miskiniyar ‘yarsu. Ga shi ko kudin motar da za a kai ta asibitin Malam babu, balle kudin ganin likita, don haka Halimah ta ce, bari ta kai ta asibitin Murtala, za ta taka a kafa daga Yakasai zuwa can ba tafiya ce mai nisa ba.
Ta roki Hashim ya zauna a gida don akwai wadanda suka yi da ita za su sayi kaji biyar manya, in ya so sai su yi amfani da kudin wajen sayen maganin da aka rubuta musu.
Ba don ya so ba ya amince, don ya yarda ta fi shi gaskiya. Yana da wata kyakkyawar dabi’a ta kai ‘yarsa ko matarsa asibiti da kansa, sabanin wasu mazan da sai dai su hada mace da kudin mota amma ba za su kai ta ko ‘ya;yansu asibiti ba su tsaya su yi musu komai da kansu ba.
Halimah ko wanka ba ta tsaya yi ba sabida rashin nutsuwa. ‘Yar lele ba lafiya, ‘ya daya tamkar dubu, wadda tun a wadannan shekarun nata ta san soyayyar da iyayenta ke mata. Tana kuma tausaya musu duk da karancin shekarunta.
Duk da cewa atamfar jikinta mai tsada ce, amma ta fara kodewa. Tun cikin kayan haihuwar Maama ne. mayafin jikinta a cukurkude yake babu guga don ba su da ayon. Fuskarta ko basilin ba ta gani ba balle a kai fa zancen hoda. Duk da har yanzu kyawunta bai gushe ba, amma skin elasticity dinta ya kau, shekaru masu yawa sun karu a kan nata na ainihi. Rayuwar cikin wahala da rufin asirin Allah ake yinta, ta taimakekeniya tsakanin juna, wadda soyayyar da ke cikinta ce jigon kasancewarta ‘live’ har a yau. In suka fara soyayya kamar sabon saurayi da budurwa. Ga tausayin juna da karfafawa juna. They are not only husband and wife; su abokan juna ne kuma sirrin juna.
Halimah ta yi lullubi rike da hannun ‘yarta suna tafiya a gefen titi don zuwa asibitin Murtala. Wata mota ta danna horn daga bayansu, “Kun san makaho da ji”. Tuni Safiyyah ta gigice ta kwace hannunta daga hannun uwar ta yi kan titi a guje ba tare da ta san ina ta nufa ba. Halimah ta saki jakar hannunta ta dora hannayenta biyu a ka ta saki wani gigitaccen ihu a lokacin da ta hango wata mota Peageout 504 ta taho da mugun gudu ta yi kan Safiyyah.





Mu karasa a littafi na 3.
Yana tafe insha Allahu bada jimawa ba.




Gundarin labarin AURE KO BOKO yana cikin littafi na 3. Alkawari ne na dauka zai tsuma zukatan ku insha Allahu.


Taku har abada,
Sumayyah Abdulkadir.

YIWA KAI HISABI 1&2 da AURE KO BOKO 1&2 tare suka fito.

Ga mai bukatar tsofaffin littafai na, hardcopy ko softcopy, wadanda babu a kasuwa, ya tuntubeni a 07030137870 whtsp only......
















16 / 16