AURE KO BOKO 1&2 BY TAKORI

Author :  Takori Category :  Romance

Chapter   12 / 16

33K to 36K   out of 47K words

Kamar yadda ka ce din ne your achievement is mine, to a barshi a hakan”.
Hashim tausayin Halima ya lullube shi. A take wani tunani ya zo masa, ya ce, “Halima ko in kai ki ki ga Daddy ne? Just greetings, mahaifi ne in ya bar ku bai kamata ku ku barshi ba, binsa za ku yi ta yi da neman gafara har sai ya huce”.
Halima ta girgiza kai da sauri, “Cewa zai yi wani abu na je nema a wajensa, ko wahala ce ta ishe ni na dawo masa. Ni kam alhamdulillahi I’m contented with my life as such. Damuwa ta daya ce rashin sanin halin da Hanan ke ciki. Haka kawai Hanan ba za ta manta da ni ba”.
Hashim ya ce “Kowacce fassara zai yi mana ki ba shi hakkinsa na haihuwa ki je. Allah shi ne shaida ba mu je don neman komai ba, sai don sauke hakkin da ya rataya a kanmu. Na hakkin haihuwa, wanda da shi zai yi hisabi ranar gobe kiyama. It’s almost four years rabon ki da mahaifin ki, ya kamata mu je din don wani lokacin na kan yi tunanin har da rashin albarkarsa cikin auren mu cikin abin da ke kara mana matsaloli a rayuwa”.
Halimah ta daga kai a hankali ta dube shi, ya gyada mata kai cikin karfafa zancensa, “Yes, rashin albarkar iyaye a cikin aure na hana ci gaban rayuwa. Kuma yana kwashe albarka, yana hana kwanciyar hankali, yana jawo rashin nasara a rayuwa…".
Hawaye ya fito daga idon Halima, ta ce, “Idan kuma ya ce mun zo neman aiki ne fa?”
“Whatever he will say”. In ji Hashim, “Ki tafi da kyakkyawar niyya, ki sa a ranki gafararsa kawai ki ka je nema”.
Halima ta kwantar da kai a kafadun Hashim ba ta ce komai ba, amma yanayinta ya nuna amincewa.

****

Allah kadai ya san irin fafutukar da Hashim ya yi tsawon sati guda kafin ya tara musu kudin motar zuwa Abuja. Lokacin da Halimah ta zo hada kaya kala biyu da za ta tafi da su, rasa wanne za ta dauka ta yi, duk sun mutu sun kode, amma dai wankakku ne, sun yi mugun jin jiki dai, don rabon da ta dinka suttura shekaru uku ke nan da suke cikin sukunin cinikin kaji da ta dinka wasu atamfofi (chiganvy) guda biyu da sallah, sauran kayanta tun na ‘yammatancinta ne.
Da a ce Halima ta san yadda ta koma a fuska, sai ta fi damuwa fiye da damuwar rashin kyakkyawar suttura.
Tun asubah suka bar gida zuwa tashar Na’ibawa, inda suka hau motar haya zuwa Abuja.
Wajejen azahar suka shiga Jabi Motor park, daga nan suka samu taxi suka nufi Asokoro.
Halima ta daga kai tana kallon garin da ta yi dabdalar kuruciyarta, komai ya sake mata cikin shekaru hudu. An samu ci gaba sosai a birnin tarayyar Nigeria. Kirjinta ban da balli-balli ba abinda yake yi. Lokacin da mai taxi ya yi parking kofar katafaren gidansu ji ta yi zuciyarta kamar za ta tsago allon kirjinta ta fito.
Mai taxi ya sauke su, Hashim ya kirgo kudinsa ya ba shi. Halima na barin kafadunsa na dama suke tafiya zuwa entrance na gidan. Hashim ya kwankwasa kofan, maigadin gidan wanda tsohon soja ne ya zo ya bude.
Kallon sama da kasa ya yi musu, ko kadan bai gane Halimah ba. Sakamakon shekaru biyar sun karu a kan ainahin ashirin da hudun ta, kodaddun sutturun jikinsu ya fara kallo, they look shabby, ba irin mutanen Prof. Bane, don haka a wulakance ya ce,
“Me ku ke nema a nan?”
Halimah ta yi murmushi, ta ce, “Seun, ba ka gane ni ba?”
Kokarin rufe kofarsa ya fara yi don ba shi da lokacin irin su.
Halima idonta cike taf da hawaye ta ce, “ABCDEFG…H for Halimah, H for Hanan…” Karatun da Seun, yake koya musu suna yara idan Daddy ya fita.
Seun ya zaro ido ya ce, “Halimah ke ne?”
Hawayen da suka cika idonta suka karasa gangarowa. Da sauri ya bude musu kofa yana fadin, “Oh my dear! My daughter Halima… where have you been?”
Ba ta ba shi amsa ba ta tambaye shi Daddy na nan?
Ya ce, “Ku shigo maza bai dade da shigowa ba, kuma yanzu zai fito ya tafi U.S”.
Kofofin shiga gidan duka a bude suke, don haka suka sa kai cikin dari-dari. Kai tsaye Halima falon da ta san Daddy ya fi zama ta kankame hannun Hashim suka shiga.
Ilai kuwa a nan suka same shi ya barbaza takardu a gabansa da farin gilashin kara karfin gani a idanunsa. Babu wani canji da Halima ta gani a tare da shi, yana nan a kyakkyawan bafillacensa, gani ma ta yi kamar an kara masa kuruciya, ko dayake an ce mai kudi ba ya tsufa.
Su biyu suka yi sallama, ba tare da sun jira ya amsa musu ba suka sanya kai, suka nemi can gefe suka zauna manne da juna.
Prof. ya cire gilashin idonsa don gani ya yi kamar yana ba shi false vision; ko ta zama tsohuwa ‘yar shekaru tamanin ba zai kasa gane ta ba. Tunda kuwa a kan hannunsa aka haife ta, ya kuma raini abarsa da kansa.
Kasa cewa komai ya yi sai kallonsu yake ita da Hashim din, Halimah ta rarrafo daga inda ta zauna ta zo ta zube a gabansa tana kuka.
“Daddy na zo neman afuwarka da albarkarka. Ka yafe mini, ka sa min albarka’.
Prof. ya yi wani murmushin keta. Ya dube ta a wulakance tare da cikin da ke manne da ita, ya ce, ‘Har kin dawo haka so soon? Ai kin zo da wuri, har wahalar ta ishe ki ne, ko kuwa talaucin ya ishe ki? Ko wanda ki ka zaba a kaina din ya sake ki kamar na ‘yar uwarki sabida rashin dangi?”
Makogaron Halimah ya bushe rayas! Yawun bakinta ya kafe. An saki Hanan? Wannan last sentence shi ya fi tsaya mata a rai ba surutun Daddy na wulakanci ba. A hankali ta girgiza kai, hawaye na sauka daga idanunta, ta ce,
“Babu ko daya Daddy, I’m here just to ask for forgiveness and your blessing”.
'‘Har abada ba za ki samu ba!” Daddy ya fada in exclamation. Ya dora da cewa, “Har sai ranar da wuya ta ishe ki kika dawo gidanku, dawowa ta gabadaya, bana hada jini da talaka, kuma ba zan taba ba insha Allahu… kai kuma… (ya nuna Hashim da dan’alinsa), ka yi ta zama unemployed kenan muddin ba ka dawo min da ‘yata ba, ka sake ta ko nawa ka ke so zan ba ka ka auri wata you can marry thausands of Halima not my daughter, zan kuma samar maka aiki mai babban matsayi a babban bankin Najeriya CBN. In kuma ka ki, to ku tattara ku tafi, kada ku sake tako min nan. Duk ranar da ku ka sake shigo min gida, kai ba da takardar saki ba, ita ba da nadamar yin aure ta bar ni ba, sai na sa karnuka sun yagalgala minku. Ku tashi ku ba ni wuri tun muna iya shaida juna ni da ku”.
Hashim ya tada Halimah wadda ke ta gunza kuka suka mike. Daddy ya kira waya, ga dukkan alamu da maigadinsa Seun yake magana.
“Idan ka bari suka sake shigo min gida, a bakin aikinka”.
Suna kokarin fita daga falon Halima na waiwayensa, Daddy ya ce,
“Kada Allah ya sa ki haifo abin da ke cikin ki lafiya”.
Wannan magana ta fi kowacce kona ran Hashim. Da sauri ya juya ya ce, “Allah na kowa ne”.
Ya so ya gaggaya masa raddi a kan maganganun da ya yi musu, ya tuna cewa; Baban Halimah ne, ba zai taba iya cin mutuncin wani da ya shafe ta ba balle iyayen da suka haife ta.
Da sauri ya ja Halimah suka tafi, a bakin get Seun ya faki ido ya jefar da wata farar takarda a gabansu. Halimah ta sunkuya ta dauka, lambar waya ce a jiki, a kasa ya rubuta ‘HANAN’.
Kallon godiya ta yi wa Seun, don ta san Daddy na kallonsu ta CCTV dinsa.

*****







BABI NA GOMA SHA DAYA
Tunda suka dawo daga Abuja wanda a tashar mota suka kwana ranar, ba ci ba sha don iyakacin kudin mota ne a aljihun Hashim. Halimah ta kwanta rashin lafiya. A karan-kanta ba ta san ciwon me ta ke ba, tana dai kwance ne kawai ba ta umh ba ta mh-umh. Amma ta san tana jin wani iri zafi a zuciyarta. Ya yi-yayi su je asibiti Halimah ta qi, don ya karbi albashin lesson din yara, ta ce, maimakon ya kashe kudin a asibiti ya je ya sayo mata ‘yan rigunan jarirai da su. Ta ba shi list din da aka ba ta na abubuwan bukatar haihuwa a Antinatal ta ce ya sayo ko rabinsu ne, diaper da shawul da rigar sanyi saiti guda biyu.
Ya ce, kudin duka dubu goma ne, kuma ba su da abinci a gidan. Halimah ta ce, bakin da Allah ya tsaga ba ya hana shi abin da zai ci.
Don haka ya tafi kasuwar Kofar Wambai da tambaya ya samu shagon kayan haihuwa masu arha ya sayo fiye da rabin list din.
Kamar yadda Halima ta ce, bakin da Allah ya tsaga ba ya hana shi abin da zai ci, hakan ce ta faru. A daren ranar sai ga Sa’adatu da mijinta Lawan sun kawo musu ziyara. Kallo daya Sa’adatu ta yi musu ta tabbatar yunwa suke ji, jikin Halimah har rawa yake yi, amma sabida karfin hali irin nata sai fara’a ta ke tana daga kwance.
Mijin Sa’adatu shi ma ba wani karfi gare shi ba, amma dai za a ce ya fi Hashim tunda ba su rasa abin da za su ci ba don yana hadawa da aikin kafinta, ko yanzu a bayan Vespa dinsa ya goyo ta.
Sa’adatu juyawa ta yi tana share hawaye, ta san duk rashin Inna ne, duk runtsi Inna ba za ta bar nata ya tozarta haka ba. Hashim ya dade da yanke alaka da Dr. Rabi’a da ma ita ce mai taimaka masa, amma tun rasuwar Inna da suka yi baram-baram a kan Halimah ba ta sake ba shi komai ba. Ta ce ya je ya karata da mai farar kafarsa tunda ya zabe ta a kanta. Shi ma kuma ko da wasa ko hanyar gidanta bai kara bi ba.
Sa’adatu ta dauko mayafin Halimah ta mikar da ita zaune ta yafa mata, ta ce lallai-lallai asibiti za ta kai ta da kanta tunda ba ta san muhimmancin lafiyarta ba, shi kuma Hashim din ya biye mata sabida ba ya son takura mata, duba da halin da zuciyarta ke ciki tun dawowarsu daga Abuja.
Asibitin Malam ta kai ta, ai kuwa nan da nan aka rike ta aka ba ta gado, don sun ce she is 60% dehydrated (ruwan jikinta ya kone kashi sittin cikin dari), sannan ulcer ta kama ta, ga rashin wadatar jini. Duk abin da aka caza Sa’adatu ta ce mijinta ya ranta mata za ta biya shi karshen wata in ta dauki dashinta.
A wannan ranar Hashim gefe ya koma yana kuka, yana jin kansa useless, yana jin kwalayen ilminsa useless, tunda duk a sanadin babunsa Halima ta shiga wannan hali, Haliman da ya daukar wa alkawarin mayarwa tauraruwa a cikin mata. Ya yi kudurin yi mata kyakkyawar sakayya a kan sacrifice (sadaukarwa)rta gare shi. Ga shi bai samu damar cika ko daya cikin alwashin da ya dauka ba. Bai taba tsammanin rayuwa za ta yi musu juyin waina kamar wannan ba.
A lokacin da Prof. ya sallame su ya yi zaton kwalayen ilminsa ba za su barshi ya tozarta ba.
Ga shi dukkan mafarkansa ba su taba zama reality ba.
Ga Haliman kwance rai kwakwai-mutu-kwakwai, ko nauyin asibitinta ya kasa dauka.

Tafiya ya kama yi a gefen titi, bai san inda yake jefa kafarsa ba. Ya san dai zuwa zai yi ya tashi ‘yan hayar gidansa ya sa gidan a kasuwa don ya kula da Halimah da abin da za ta haifa, ya ja jari da wani abun cikin kudin, ya sayi ragon suna ya ajiye don abu na karshe da ba zai taba yarda ya faru ba a rayuwarsa, shi ne Halimah ta haihu bai yanka wa dansa ragon suna ba.
Lokacin da ya ba wa maigidan notice din su tashi, cewa ya yi ai kudin shekara suka biya, kuma yanzu watanni biyar ke nan, sai dai in ya maido musu rabin kudinsu ko ya bari zuwa karshen shekara su tashi.
Hashim kamar ya yi hauka, ya ce su tashi ya sayar da gidan, zai cira a ciki ya ba su.
Dillalin gidaje na unguwar Janbulo ganin yadda Hashim ya ke a uzurce da son saida gidan da gaggawa lokacin da ya je ya same shi, sai ya yi wa gidan tayin wulakanci, kashi talatin cikin dari na kudinsa na zahiri. Without a second thought Hashim ya ce ya sayar da gidan da ya zubar da guminsa da lokacinsa ya mallaka a kudade naira miliyan biyu kacal.

Makotan Hashim sune shaidun sa, suka sa hannu shima yasa, cinikin gida ya tabbata, gidan Janbulo ya tashi daga mallakar Hashim.
Hannu da hannu suka ba shi kudinsa, don Hashim ko account ba shi da shi yanzu, banki sun rufe shi, jimawa da ya yi ba ya amfani da shi.
Ya zubo kudinsa a babbar leda ya yana tafiya da sassarfa a gefen titi cike da farin ciki yana kiyasi, kiyasin abubuwan da zai saya wa Halimah da babynsu; Katon ragon sunan da zai saya; dandasheshen leshin da zai saya mata ta daura ranar suna; da kiwonta da zai dawo mata da shi ta yi ta cin kwai da nama ta samu jini a jikinta ta maida wannan komadar. Da shagon kayan masurufin da zai sake bude…....... sai ji ya yi da mugun karfi an warce ledar hannunsa, daya ya cilla wa daya sun haye lifan sun bace a titin kamar kiftawar ido.
Saboda gigicewa Hashim takawa ya yi da gudu iya karfinsa a kan titi ko zai cimma wadan nan marasa imani, amma yana hawa tsakiyar kwalta ya ji an yi sama da shi an wulwula shi, sannan ya fado tim! Tsakiyar titi jina-jina.
Duk da muguwar buguwar da ya yi ta ko’ina, amma bai fita a hayyacinsa ba, fadi yake, “Matata tana asibiti, don Allah ku taimake ni ku kai ni Aminu Kano”.
Wanda ya buge shi din ya ce, “Kai ma ai asibitin ka ke bukata, na yi zaton ba ka da hankali da ka hawo tsakiyar motoci kana gudu, ashe da hankalinka, tunda har kana sane da matarka da ke asibiti”.
Suka kakkama shi suka sanya shi a motar mutumin suka nufi Aminu Kano da shi.
A A&E aka karbe shi inda suka yi masa treating ciwuwwukan da ya ji, suka yi masa dorin karaya a kafa, wanda ya kade shi duk shi ya biya komai. Har ya gaji da surutun Hashim a kan matarsa da ke asibiti rai a hannun Allah, ya taimaka masa ya kai shi wajenta.
Da zai tafi ne ya ji tausayin Hashim ya kama shi, da ma har yanzu akwai mazan da ke son matansu haka cikin al’ummar Hausawa? Ya ce da shi,
“Gaya min dakin da matar taka ta ke, in je in gaya musu, ni zan wuce gida, ka yi hakuri ba ni da laifi domin kuwa gabana ka sha ina kwarara gudu”.
Hashim ya gaya msa tana gynae emergency ya tambayi nurses din Halimah Zubair da aka kawo dazu, tunda suna da sunan kowace patient tare da su, tana tare da kanwarta Sa’adatu da mijinta Lawal
Ba jimawa sai ga mutumin tare da Lawal da Sa’adatu hankali tashe. Sa’adatu ta fashe da kuka ganin mummunan yanayin da yake ciki, har da karaya. Lawal yana ta tambayarsa garin ya ya? Ya kau da kai ya labarta musu komai har mutumin da ya kade shi yana jin su.
Sa’adatu ta ce, “Yaya me ya kai ka? Wa ya aike ka ka sayar da kadarar da ta rage maka? Ka ke samun sanyi daga karkashinta?”
“Kaddara Sa’adatu, kaddara!” Ya fada yana lumshe idonsa.
“Ya ya jikin Halimah? Ta ci abinci?”
Lawal ya gaya masa tun kawo ta barci ta ke yi, amma an sa mata ruwa da jini, kuma likitoci na ta kokari a kanta. Sun ce babyn ma ba ya motsi yadda ya kamata sabida ba

12 / 16