AURE KO BOKO 1&2 BY TAKORI

Author :  Takori Category :  Romance

Chapter   15 / 16

42K to 45K   out of 47K words

ta ce, “Umh”. Kawai in ta girma kowa ya sani, ba sa son baki ya kama ‘yarsu.
Sai karfe goma suka yi sallama kamar ba za su rabu ba, domin gobe da asubah za su dauki hanya don ta samu ofis a kan lokaci.

*****

Suka ci gaba da rainon diyarsu Safiyya tare da ba ta kulawa ta musamman, bayan soyayyar iyaye ita wannan ‘yar suna jinta sosai a ransu, saboda rauninta.
Watannin Safiyyah hudu, duk wanda ke tare da su ya san cewa ba ta gani. Ga wani irin kyau da Allah ya ba ta. Tausayi da kyawunta shi ne ke sayo mata soyayya a zukatan al’ummah.
Hanan ta gaya mata cewa, tun bayan haihuwar Safiyyah Daddy ya sanya ta a ma’aikatan NCC da aka tura karo kwas a kan harkar Telecommunication kasar Manrovia, ba ta so tafiyar ba, amma Salim ya karfafe ta da cewa, ta je, wannan zai ba ta damar rainon cikinta cikin kwanciyar hankali har sai ta haihu. Don kuwa ya shirya karbar dansa, in ya so iyayensa su zabi abin da ya fi musu amfani tsakanin barinsa da matarsa ko su raini abin da ta haifa masa. Kwas din zai dauke su watanni shidda.
Bayan tafiyar Hanan suna waya akai-akai, kuma ta gaya mata ta shiga EDD dinta.
Yau Hanan ta kira ta ne da kyakkyawan albishir na ta sauka lafiya, ta haifi diya mace mai tsananin kama da mahaifinta. Nan da watanni biyu za ta kammala kwas dinta ta dawo gida ta fuskanci Daddy.
An ce dai ba'a murna da haihuwar dan gaba da fatiha, amma Halimah sosai ta ke murna. Jin ‘yar ta ke kamar Safiyyah a zuciyarta musamman da Hanan ta turo mata hotunanta. Kyau har zuba yake, da ma an ce shegun ‘ya’ya kyawu ne da su. Ta gaya mata Salim ya je Manrovia ya ga babynsa ya ba ta kudi masu yawa don ta shayar masa da baby.
Ba dai haka aka so ba wai kanin miji ya fi miji kyau. Halimah ta kara tunatar da ita yawaita istigfari, hailala da salatin Annabi, to calm Allah’s anger against them. Ita ma tana taya su da roka musu gafarar Ubangiji.
****

BAYAN WATANNI BIYU
Gidan Proffessor Numan.
Asokoro, Abuja, Nigeria.
Direban da ya dauko Hanan da ‘yarta daga filin jirgi ya yi horn a tankareren get din gidan Prof. Numan, Seun ya zo ya fara shaida motar sannan ya bude suka shiga. Duk da cewa gabanta mugun faduwa yake yi, amma tana ta jan addu’a wadda Halimah ta koya mata. Ta ce, ita za ta yi ta karantawa a lokacin da za ta fuskanci Daddy. Direban ya bi bayanta da jakunkunanta.
A kasaitaccen falonsa ta fara yin tozali da shi. Dauke ta ke da yarinyar a kafadunta wadda ta radawa suna Yusra. Barcinta ta ke hankali kwance, ta zuge sliding door din da ta raba falon farko da falon da Daddy ke ciki.
Zaune yake yana ta aiki kamar yadda ya saba; bisa computer ne, bisa takardu ne, bisa macbook ne duk dai babu wanda ba ya yi. Yana yi yana duba agogo don jiran isowar ‘yar sa Hanan.
Da sallama ta shigo, ya daga kai ya dube ta da murmushi.
“Welcome back daughter…....”
Ta karaso ta rungume shi da hannu daya yayin da dayan ke dauke da baby.
“I missed you Daddy…”
“Missed you too daughter, how is Manrovia…?”
Sauran maganar ta makale a makoshin sa, sakamakon kuka da yarinyar hannun Hanan ta canyara. Cikin mamaki da al’ajabi ya dubi Hanan sosai wadda ta zauna gefe ta fiddo nono ta sa wa ‘yar a baki.
A firgice Prof. ya mike tsaye, “Me zan gani haka? ‘Yar wa ki ka dauko? Na ce daga ina ki ka dauko ta?”
Hanan ta sunkuyar da kai ta soma hawaye, ba ta ce komai ba. Ya sake maimaita tambayar sa, wannan karon a matukar fusace, Hanan ta soma shivering (karkarwa) kamin ta tattaro courage ta ce, “I’m sorry Daddy, ‘ya ta ce, ni na haife ta!”
Wani gigitaccen mari ya dauke ta da shi, ya sake dauke daya kuncin nata da wanda ya fi na farko, sannan ya nuna ta da dan yatsa.
“Karya ki ke ki tozarta ni. Ashe karuwanci ki ka tafi ba inda na tura ki ba? Fitar min da ita daga gida kafin na kashe ta, hukunci ya hau kaina”.
Kuka sosai Hanan ta saki, “Daddy ni ce ‘yarka Hanan, ‘yar da ka raina ba tare da taimakon uwa ba. Ka tuna girman amanarmu da Allah ya dora maka. Wannan yarinya da ka yi aiki da fadar Allah da ManzonSa da ba ta zo a haka ba. Ni ban yi karuwanci ba, ban taba sanin Da namiji ba bayan tsohon mijina, Salim. Kuma shi ne uban ‘yar sa, ka yi min alfarma ka bar ni in shayar da ita. Ranar da na yaye ta zan ba shi ‘yarsa in ci gaba da zama karkashin biyayyar ka”.

Tun daga yatsar kafarsa har gashin kansa gumi yake. Ji ya yi jikinsa ya yi bala’in sanyi. Wani abu mai kama da nadama na son ziyartarsa. Zama ya yi a kujera ya dafe kansa da hannu bibbiyu. Yayin da Hanan ta sauko daga kujera ta zube gwiwoyinta a gabansa tana hawaye dauke da ‘yarta.
“Daddy, ka hana mu aure, ka hana mu zaman gidan miji saboda boko. Mu din kuma ba waliyyai ba ne ‘yan Adam ne ajizai, wadanda shaidan ya yi alkawarin ja ga halaka muddin ba mu bi fadar Allah ba. Ubangiji ya yi maka umarnin ka yi mana aure daga shekarun fara balaga, amma Daddy ka ki hakan. Na zo na yi aure ba bisa yarda da amincewarka ba, ka bar ni babu kulawa a gidan aure kamar ba ni da kowa. Dangin mijina suka kasa karbata sabida rashin gatan iyaye. Mijina ya sake ni a kan dole, ba don yana so ba sai don bin iyayensa.
Daddy ka san bond din da ke tsakanin mata da mijinta? Musamman wadanda suka rabu ba bisa wata kwakkwarar hujja ba? A lokacin ne Ubangiji ke sanya musu kaunar juna wadda in ba a yi sa’a ba, sai ta kai su ga tabewa da halaka, wanda wannan shi ne hakikanin abin da ya faru da ni.
Daddy mu marayu ne, amana a hannunka ka yi tunani da mahaifiyarmu na raye, za ta amince da rayuwar da ka sanya mu a ciki?
Kudi dai Daddy na duniya ban san wane iri ka ke so ka yi ba. Ilmin boko na duniya ban san wane iri ka ke so mu yi ba. Ba ka bai wa masu bukata aiki sai mu da ba ma bukata. Ba ka tunanin lahirar mu, kullum cikin rayuwar duniya da neman kudi kawai ka ke cusa ni. Ba ka la’akari da kasancewata diya mace mai rauni, wadda halittar ta ta karfinta da juriyarta ba kamar namiji ba ne. Na samu komai da dan Adam ke bukata a rayuwa ban da aure. Ka gaya min in ban yi zina ba me ya rage min a duniya?
Sis Leemah. Ka yanke ta daga jikinka kawai saboda ta zabi ta raya sunnar Annabi, ba don ta kasance mai tsoron Allah ba babu shakka abin da ya same ni shi zai same ta. Ta jure duk wasu azabobinka shekara da shekaru, amma wallahi ta fi ni kwanciyar hankali a halin yanzu, tunda tana cikin rahmar aure tare da mijinta da ke sonta saboda Allah, da tsarkakkiyar zuri’a wadanda a ko’ina za ta yi alfahari da tutiya da cewa, ta hanyar sunna ta same su…”
Ta kama kafafunsa jikinta na karkarwa.
“Ka bar min ‘yata ina sonta. Ita ce sanyin idaniya ta. Na yi maka alkawarin zan ci gaba da yi maka biyayya har PhD zan dora in dawo in ci gaba da aiki har iya inda ka ke so. Amma don Allah ka yi min alfarma ka bar min ‘yata in raine ta in ta kai munzali ita in yi mata aure ta haifa min tsarkakkiyar zuri’a. Ka yafe min, ka sa min albarka. Na tuba na bi Allah na bi ka… ba zan kara yin zina ba!”
Ta hade hannayenta biyu cikin roko, fuskarta sharkaf da hawaye.

Prof. Bai ce mata komai ba ya juya cikin wani hali zuwa dakin sa.
Daga ranar bata kara ganin shi ba, ya shige daki ya rufe kamar wanda ya shiga halwa, bata san me yake ci a dakin ba ofis ma baya zuwa. Tun tana zuba idon zai kwace mata 'ya har ta saki jikin ta ta cigaba da hidimar 'yar ta cikin gidan.
A kwana na biyar ne rannan ta shiga wanka ta bar Yusra kwance akan gado tana ta tsala kuka. Prof. Yayi shirin ofis zai wuce ta gaban dakin Hanan amma kukan Yusra yasa dole ya dakata, yana jin wani iri a zuciyar sa. Hakika a kwanakinnan biyar ba abinda yake a daki sai neman gafarar Allah, ya yarda duk abinda Hanan ta fada gaskiya ne, kuma rashin mai gaya masa gaskiya akan iyalinsa shine babban abinda yayi tasiri a kansa.

Abin da ba ta taba zato ba, abin da ba ta taba tsammana ba. Daddy ya shigo dakin ta. Hannu biyu ya sa ya dauki 'yar. Idanunsa cike taf da hawaye, kamar ta daya da Safeeyah. Ya rungume ta a jikinsa tsawon lokaci bai ce komai ba. Hanan dake tsaye bakin kofar toilet daure da tawul don farin ciki ko motsi ta kasa yi.
Sannan ya ajiyeta a kan kujera yana kallonta, ya juya ga Hanan dake tsaye yace.
“Ki ba ta nono ta sha, tun daga daki na nake jiyo kukan ta”.
Hanan gigicewa ta yi don murna, ta kasa ba wa ‘yar nono sai jijjiga ta ta ke tana fadin, “Daddy, ka yafe mana? Za ka dawo da Sis Leemah? Za ka bar ni in koma gidan mijina? Za ka bayyana kanka a matsayin ubana ga dangin mijina?”
Tambayoyin ta ke jejjerowa a jere, ko numfashi ba ta shaka. Prof. bai ce mata komai ba, ‘yar cikinsa da ya haifa ta shayar da shi ilmi, ilmin rayuwa wanda bai taba zama ya ankara da shi ba.
Da gaske akwai mutane irinsa da yawa a wannan zamanin, wadanda suka riki boko da career da muhimmanci fiye da bautar Ubangijinsu, fiye da feelings din ‘ya’yansu. Neman duniya ya danne na lahira, burinsu kawai ‘ya’yansu su fi na kowa. Ba ruwansu da halin da ‘ya’yan talakawa ke ciki. Duk wani vacancy mai maiko na ‘ya’yansu ne, dan talaka ya mutu don rashin aikin yi ba damuwarsu ba ne.
Ga result (sakamako) na fifita duniya kan umarnin Ubangiji yau ‘yarsa ta kawo masa har gida, wanda ba zai taba kankaruwa daga jikinsa ba, jikar sa… 'yar gaba da fatiha…. Wai don ma Allah ya takaita korar da ya yi mata lokacin da mijinta ya sake ta, bai sa ta shiga duniya ba.
Tunani na karshe da ya kutso cikin kwakwalwarsa shi ne, HALEEMAH… his innocent daughter Haleemah!!! How cruelly he treated her… how he abandoned her… how he scolded her… how he sent her away, da zaluncin da ya yi mata kawai don ta zabi AURE a kan BOKO! Yau ya tabbata sai Ubangiji Ya tsayar da shi hisabi tsakaninsa da Haleemah, idan har bata yafe masa ba!
*****








BABI NA GOMA SHA UKU
Karfe goma na safe Hashim ya iso café (business center) dinsa. Abin da ya ba shi mamaki dirkeken kwadon da ya rufe kofar shagon ya tarar a gefe a yanke. Kofar shagon kuma a sakaye, wato an sakaye ta.
Cikin wata irin mummunar faduwar gaba ya finciki kofar iya karfinsa ya shiga. Fetal! Sunan wani fili. Duka computers, printers, scanners, photocopying machines, lamination machine da duk wani abu mai daraja da ke cikin shagon babu shi. Kwashewa aka yi? Tashi sama suka yi? Allahu A’alam, amma da ya tuna da yankakken padlock da ya baro a kofa sai ya gane shigowa aka yi ta karfin tsiya aka yashe shi.
Daga tsayen da yake ya sulale a kan kafafunsa. Yanayin da yake ciki ya fi dacewa da a kira shi suman ido biyu. Ya fi karfin awanni biyu a haka, kafin nutsuwa ta zo masa sakamakon kalmar innalillahi wa’inna ilaihi raji’un da ta samu muhalli a kan harshensa.
Sai kawai ya mike ya sabi hanya, tafiya yake tun daga filin tsohuwar jami’ar Bayero ba tare da ya san inda yake jefa kafarsa ba. Ya wuce Kofar Famfo, ya wuce Kofar Duka-Wuya, ya wuce Kofar Gadon Kaya, ya wuce Hauren Shanu, ya wuce Kofar Na’isa, ya wuce Kofar Dan’agundi, ya wuce ta cikin Sabuwar Kofa ya bulla Yakasai. Tun karfe sha biyu na rana har karfe biyar na yamma kafin kafafunsa su kawo shi gida.
Halimah na yi wa Safiyyah wankan yamma yadda ta ke yi kafin babanta ya dawo, ya same ta tsaf tana kamshi. Tsuke cikin kyakkyawar suttura, sai ga shi ya fado gidan kafafunsa futu-futu kamar an kwato shi daga bakin kura.
“Baban Safiyyah, lafiya?”
Ta fada hankali tashe.
Ya ja kujera ‘yar tsugunne wadda sun gaje ta ne daga Inna ya zauna yana maida numfashi. Kawai Halimah sai gani ta yi hawaye sun zubo masa.
“Ba ni wayarki zan yi reporting wa police, wayata babu kudi”.
Halima ta kara shiga tashin hankali.
“Police Baban Maama? Fara gaya min mene ne don Allah?”
Ya mike tsaye, “Ki bari in je police station in dawo”.
Sai da ya je ya dawo ne yake gaya mata komai. Halima ta runtse idonta, ta ce,
“Ya Salamu sallim!”

‘Yan sanda sun yi iya kokarinsu, amma kullum abu daya suke gaya musu, “Ana kan bincike”.
Ba shagonsa kadai aka yashe ba, har na kusa da shi da na gabansu. Tun suna jelen ofishin ‘yan sanda har sun gaji sun bar wa Allah komai.
Kasar Najeriya da shuwagabanninta suka kara sire wa Hashim. A kullum sai ya zauna yana kiyasce-kiyascen abin da zai yi idan Allah ya ba shi shugabanci komai kankantarsa. Wani irin determination ya shige shi a kan leadership (kwadayin shugabanci) da kuma kwadayin siyasa (political inclination). Har zama yake ya yi ta rubutun abubuwan da zai yi idan da a ce shi ne ke da shugabancin Nigeria, da kuma matsalolin masu ilmi irinsa da matasa ke fuskanta.
Rannan Halimah ta dauki daya daga cikin rubuce-rubucensa tana karantawa. Taken rubutun shi ne babban abin da ya dau hankalinta; NIGERIA’S TRAUMA IS POLITICAL DICHOTOMY… there is always a dichotomy between what our politicians say and what they do… insecurity overwhelmed us… thugging, insurgency, robbery, kidnapping, unemployment are the major problems of our youths......
Haka ya yi ta jero matsalolin matasa wadanda suka addabi al’umma, wanda unemployment shi ne silar mayar da su heartless suke cutar al’umma. Abubuwan da zai yi wa matasa idan ya samu damar shugabanci komai kankantarsa.
Ya koma shiru-shiru ya rage walwala, kullum cewa yake,
“Halima ba ni da sa’a!”.
Ita kuma sai ta ce, “Bar fadin haka Baban Maama, haka rayuwa ta ke, WATARANA ZUMA, WATARANA MADACI, ko kai ne beran masallaci saboda talauci, haka nake sonka. BA ZAN DAINA SONKA BA!” (Sunan littafin Watarana Zuma....na canza shi zuwa AURE KO BOKO?)
Hatta wasan da yake yawan yi wa Maama (Safiyyah) ya rage shi, ya rage fita, daga sana’ar kajin Halima suke ci suke sha. Halimah ta fahimci he is a bit depressed don haka ta dage wajen counselling dinsa, yi masa nasiha a kan muhimmancin yarda da kaddara, kunna masa wa’azin malamai masu tuni da cikar imanin bawa bai yiwuwa har sai ya yarda da kaddara mai dadi ce ko mara dadi. Ta kara dagewa wajen kyautata masa tare da faranta masa a shimfida.
Hashim ya yarda da fadar Manzon Rahma cewa, rabin addinin mutum shi ne dace da samun mace ta gari. Halima ba ta gaza ba har sai da ta samu Hashim ya saki ransa, ya koma cikin nutsuwarsa, ya fara fita ‘yar buga-bugarsa yana samo musu dan abin da ba za a rasa ba. Wani abu sai kasata Najeriya. Mutum mai kwalin digiri na uku kenan, babu irin cike neman aikin da ba ya yi online amma in magana ta fara kankama a karshe wanda ke da kafa (wanda ya san wani) shi za a ba wa aikin ko da kuwa kasa yake da shi a qualification.
Tuni Hashim ya daina neman aiki, aikin gwamnati ya fita ransa, ko aikin koyarwa a makarantu ya daina nema. Zuciyarsa ta kekashe

15 / 16