"to ai bakai ka aikeni ba bare ka hanani tafiya" nace a zuciya ta tare da cigaba da tafiya ta bako wai waye.
Cije le'be yayi tare da girgiza kai, ransa ba'kin 'kirin, yana hangen yadda samarin 'kyauye suka kafe ta da ido.
Wani har da hanci wurin kallon.
Shige wa gida yayi don ba'kin ciki tare da buga 'kofa garau.
Zama yayi a fararen kujerun sa na far fada, tare da jingina ya rintse ido, tuno ranan da yayi mummunan ganin yayi.
Dafe zuciyar sa yayi saboda yadda take mugun bugawa.
•••••••••••••
"Mama gashi" cewar Joy a bakin kitchen, waigo wa mama tayi tare da cewa "baki gansa waje ba?, uhum" kawai nace.
"To taimaka ki mi'ka masa a gida, nasan yana nan".
" To" nace tare da fita gidan, koda naje 'kofar gidan nasa na dad'e ina tunanin yadda zan shiga.
Kudum bala nayi na daure na tura 'kofar gaba na na fad'i.
Shiga nayi na gansa zaune idanun sa a rufe, jin motsin tafiya yasa ya bud'e idanun sa dasu kai jajazur dasu.
Ganin itane yasa ya maida ido ya rufe, zuwa gaban sa nayi na aje zan juya ba tare da nace dashi komai ba.
Yace "d'auki" kallon sa nayi still idon sa na rufe, juyawa nayi don tafiya ta.
"Nace ki d'auka ko?" cikin tsawa, niko taurin kai sai nai kamar banji sa ba nasa kai.
Banyi taku uku ba naji an ri'ko hannu na, waigo wa nayi ya wurgamin wata matsiyaciyan harara tare da sakin min hannu nawa, yayi min nuni da zo'bon da na aje.
Tura baki nayi ina cewa "mama tace na kawo ni, amma kafin ki sayo mai na sanar miki?".
Ya tsina fuska nayi sa'an nan nace kamar mai ciwon baki " gani nayi ai bakai ka aiken ba" tare da zum'bura baki.
"To sai ki d'auka kisha, don ni banshan 'kazan ta" kallon sa nayi shima ya d'ago daradaran idanuna sa.
"Eh, yadda kikajin nan" "ummm, hakan yayi" nace tare da matsawa na d'au zo'bon zan wuce.
"Shanye shi anan " yace fuska a d'aure kamar wanda bai ta'ba dariya ba.
Tsoro ne ya kamani na kafa kai bayan na bud'e goran .
Bige goran yayi ya zube min a jiki, sanyin zo'bon har cikin kaina.
Kallon sa nayi shima ni yake kallo, fuska babu walwala yake "duk ranan da na sake ganin ki da irin wad'an nan tsuma ko makaman tansu, tabbas rai zai mummunan 'baci".
" Fita min a gida" yace cikin tsawa daya firgitani, da gudu na fita.
"Sai yanzu naji sa'ki a zuciya ta, na fanshe haushi na" yace tare da shige wa d'aki, alwallah ya gaba tar don anfara kiran sallan magariba, ya fito don tafiya massalaci.
•••••••••••••
"Mugu kawai" nace lokacin da na shigo gida, "kada wa Joy?" cewar mama daga kitchen.
"Ba kowa" nace tare da nufan d'aki ina jin ta tana cewa "kin zama mahaukaciya ba ai dole" bance komai ba na bud'e gana mazgo na don canza kayan jikina.
Kallon kayan nayi ina tunanin maganan sa, don gaskiya na tsora ta sosai.
Ganin haka bai min ba na zazzage kayan ciki kaf a tsakar d'akin.
Da 'kar na samu wani dogon riga mai gajeran hannu ya wuce guwa nasa ina mai cewa "ka nunan kayan da zam saka tunda kasayo min" ina mai murgud'a baki kamar yana gaba na.
°°°°°°°°°°°°
Shiru- shiru har 9:30pm mama bata gansa ba, don haka tace "tashi ki kaima doctor abincin nan".
Zabura nayi tare da cewa " Allah mama bazani ba, doctor d'in nan fiti nan nene" zata sake magana sai ga Aisha ta shigo.
"Yauwa tunda ban isa da d'ayan ba nasan wannan baza ta'ki ba" ya tsina hanci nayi tare da ta'be baki.
Dariya Aisha tayi tare da cewa "waya ta'ba min besty? eyeh? mai mukayi ne mama" duk cikin tsokaana tayi.
Hararan ta nayi tare da gyara kwanciya ta.
"Uhum mama bani sa'kon mai zan miki kiga cika aiki yanzu tunda wata bata son albarka".
Tsaki nayi mama tace " ma'kocin ku likitan nan zaki mi'kawa abinci".
"Aiko yanzu na barsa waje yana shan iska, yauwa kai mai" mama tace tana mi'ka mata.
'Kar'ba tayi ta fita, bata jima ba ta dawo ko nace suka shigo tare hannu ta d'auke da kwanon abinci.
Waiga dukan mu mukayi kallon d'aya na masa na d'auke kai da sauri saboda hararan da yayi min.
Duk da dare ne akwai farin wata kamar rana.
Turo baki nayi, "Auwal ya haka?" lokacin da Aisha ta aje abincin.
Murmushi yayi tare da cewa "nagode mama naci abinci ko?" yace yana zama kusa dani kad'an.
Cikin 'kasa da murya yadda babu wanda zaiji yace "bakijin magana ko?" kallon su mama nayi naga hakalin ta naga abincin da aka aje Aisha cema naga tana kallo na.
"Bani da wasu sai irin su" nace a hankali, zaiyi magana mama tace "yanzu ka kyauta?, haka mukayi da kai?".
" Ayi ha'kuri gobe zanci" yace yana murmushi kad'an, "to nayi".
Fira suka d'an ta'ba da mama ya tashi yayi mata sai da safe ya fita, ba tare da ya kalleni ko ya sake kulani ba.
Kamar ma baiji mai nace ba..
Washe gari ina cikin barci safen da na saba, naji muryan sa yana ce da mama " mama yanzu naga waccen yarinyan da suke tafiya makaranta da Joy ta tafi, nace lafia bata tafi ba, ko ta riga ta gaba ne?".
"Wai Joy ai tayi kwana biyu bata zuwa, nayi nayi ta'ki, kuma ko jiya bayan kafita maganan makaranta yarinyan tazo mata, amma fir tace baza taba, ko naji tana ce da ita next week zata".
" To mai yasa?, oho gata can bata da sana'a kullum sai barci, don ko church yanzu taba tafiya, nai magana har bakina yayi tsini amma ta'ki haka ma zuba mata ido".
Inajin su sukai ta magana, har takai ga yace mama ta tasoni, zuwa ko tayi tashi na d'in nayi kamar ina barci.
Kiran suna na ta fara, da yake ban cika nauyin barci ba da safe, nafi barci harda minshari da dare, don saboda tsaban barci kana iya saceni ka gudu.
Tayi kira yakai uku na'ki ko motsi, sai ta fara jijjigani amma ko didim.
Auwal na tsaye yanaji gashi ya tsaida Aisha a waje .
Don haka sai ya shigo d'akin kawai yana cewa "mama bani ruwan sanyi kawai" bata musa ba kuwa tace "to tare da shiga bangi da don d'ako masa.
Bata jima ba ta kawo, jin tace " gashi" yasa na mi'ke a zabure, ina zare ido fuska ta a had'e.
Dariya mama tayi tare da cewa "dama ai nasan kinaji na, dakin cigaba da 'kaliya ai dakin ga aiki".
Turo baki nayi tare da zuro 'kafafuna a 'kasa, shiko kamar wani ubana yana wani kauda kai ya had'e rai yace " tashi kisa uniform mu tafi" kallon sa nayi tare da hararan sa.
Zuwa can nace "ai nayi latti , sai kuma gobe".
" Baki isaba tashi kisaka uniform nace" "uhum banyi wanka bani, ba'a bu'kata wuce ni kina 'batan lokaci" yace tare da barin d'akin.
Yana daga waje yace "ina jira minti biyar na baki, kika wuce rai ya 'baci".
" Kiji fa mam, sai kace wani ubana, to wai meye ruwan shi dani".
Bugen baki mama tayi tare da cewa "karki shirya ki tsaya yau naga duka" daga haka ta fita itama.........
Comment & share pls
[11/5, 9:50 PM] Safeeya Aliyu: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*'KAUYEN 'YAR KADDE*
🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*Story & written by: Safiyya Aliyu Wakili*
💫DA BAZAR MU WRITER'S ASS💫
*We are here to make you happy, smile, educate and realized that we are best among all........ DA BAZAR MU MUKE TUN'KAHO*
*Dedicated to Safiyya A W fan's club, kuna bani nishad'i godiya mai tarin yawa*
*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*
🅿2⃣9⃣to3⃣0⃣
Bayi na shiga, wanka ta nayi sannan na fito, koda na fito ganin kayan makaranta na da school bag d'ina a gefen katifa da kayan shafa, nasan duk aikin mama ne.
Janyo kayan shafan nayi ina hararan uniform d'in kamar shine ya min laifi, shafa mai nayi kawai na d'au kayan na saka, fuka babu komai na fito, tunda na fito ya kafeni da ido.
Kauda kaina nayi daga gare sa tare da tsaki a zuciya ta, nufan hanya fita nayi ba tare da na kula mama koshi ba.
"Baki sallame taba", kamar ba dani yake ba na 'kara gaba.
Girgiza kai kawai yayi mama tayi murmushi tare da cewa " nagode yaro na, ubangiji ya taimake ka" "ameen" yace tare da bin bayan na.
Ina fito wa naga Aisha tsaye, muna had'a ido na d'auke kai na.
Cikin masifa ta nufo ni, tana cewa "ai da baki fito ba, da ya barki, kinje kin shanya mutane, kuma muje yau sai kinsha duka biyu, gana rashin zuwa gana latti".
Kamar ba dani take ba na nufi hanya, lokacin ne ya fito motar sa ya bud'e, yana mai cewa Aisha " shiga muje na kai ku" da farin ciki ta nufi motan.
Ina jin su ban ko waigo ba, tana shiga ya tada motan.
Ya fara tafiya a hankali, don garin namu hawa da sauka ne, ga wasu shegun duwatsu, har da uban ramu ka, gomnati ta'ki kawo tallafi. Koda yazo dai-dai inda nake sai ya tsaya ba tare da yayi magana ba.
Ganin haka na bud'e bayan motan na shiga tunda Aisha na gaba.
Ajiyan zuciya ya saki tare da lumshe idanun sa na wani lokaci, kafin ya nisa ya bud'e a hankali ya sauke su akan fuska ta.
Ta madubin motan, wani irin nishad'i naji yana tsarga 'kashi da 'bargo na, shima ta 'barayin sa hakan ne.
Aisha ko washe baki take ta shiga motan da bata ta'ba shiga ba.
Fara tafiya yayi, a hankali yake tu'kin mota shiru kamar kurmaye, sai aukin kallo kamar zai cinyeni.
A haka har muka fito bakin titin shiga cikin gari, yana ganin sa a kwanlta yace yana mai kallon gefen da Aisha take "inane hanyan makaranta?" .
"Nan hanyan zaka bi" ta nuna masa gefen dama, daga nan ne ya fara tu'ki cikin kwarewa, da taimakon Aisha ya kawo mu makaranta .
Yana parking muka fita, kiran Aisha yayi don yaga sai faman had'e rai nake tunda muka fito.
Dawo wa tayi tare da le'ka kanta ta gilas d'in motan, kud'i ya mi'ka mata yace "kuyi break" godiya tayi masa sa'anan ta biyo bayan na da nake ta tafiya ta ba tare da na jira ta kona waigo ba.
Yana kallon na har na shiga class sa'anan ya bar wurin cike da tsanani 'kauna ta.
"Wai besty yau Allah ya d'aga mu, kuma Allah ya cece mu, da yanzu muna can hanya muna cin kwakwa, amma gaskiya yana da kirki, kalli kud'in da ya bamu, da har inajin haushin tsaida ni da yayi", kallo d'aya nayi na d'auke kai na, " ga naki, banso" nace.
" Kai amma guy d'in nan ya had'u, idanun sa farare 'kar dasu, gashin giran sa masu tsanani kyau da tsari, inama inama besty ohhhhhh Allah na" tace tana rugune hannun ta a 'kirjin ta
Esha ke cewa bayan mun zauna, zancen ta na sufan tamin habibi yayi ba'in 'bata min rai amma ban nuna ba nabar abin a raina yana cin raina, bamu dad'e da zuwa ba aka fara tsaron latt, malami ya shigo muka fara karatu.
****************
Muna fito wa daga cikin makaranta muna tafe Aisha sai zuba take ita d'aya kamar kad'anya .
Bamu lura dashi ba sam, sai jinsa nayi dai-dai saitin kunni na yace "ku nake jira" cikin daddad'an muryan sa.
Bugawa zuciya ta tayi, na d'an juya kad'an na gansa gab dani, yana cikin kyakkyawan shiga, Aisha dajin muryan sa ta washe baki tare da cewa "sannu da zuwa yaya".
" Kutumar uban can" nace a zuciya ta, murmushi yayi mata tare da cewa "yauwa 'kanwa ta, kun tashi lafia? ya karatu dai?".
"Lafia qalu, alhamdulillah" "masha Allah, muje ko?" yace yana mai nuna mana inda motar sa take.
Tare muka jera yana ta gefen hagu na, koda muka zo shiga motan bayan ya bud'e .
Zan shiga baya kamar yadda nazo da farko ya daka tar dani, tsayawa nayi ina kallon sa har iso gareni.
"'Kanwa ta koma baya" yace da Aisha data hakince a gaba.
"To" tace tare da fita ta koma baya, "shiga" yace yana tsaye tare da kallo na, ban ce komai ba na shiga ya rufe 'kofar tare da zaga yawa ma zaunin shi na drive ya shiga muka d'au hanya.
Kamar tafiyan farko haka mukayi wannan ma.
Bai tsaya a ko ina ba sai 'kofar gidan mu, bud'e 'kofar motan mukayi a tare kowa ya fita.
Aisha na cewa "mungode yaya, Allah ya saka", " ameen" yace yana murmushi idon sa na kaina da nake ninyan shiga gida ba tare da na waigo ba.
"Tsaya 'kanwata ki kar'ba" bud'e but d'in motan yayi tare da ciro ledan shopping ya mi'ka mata.
Godiya tayi tana kallon sa cike da sha'awa a zuciyar ta tana raya "ashe yana da kirki?" tayi gida tana waigen sa.
Shiru yayi bayan shige wansu yana sosa kai da key d'in hannun sa.
Kallon kayan dake dam motar yayi, yana na zarin yadda zai kwashe su.
Ganin babu mafita yasa ya fara fidda kayan yana ajewa a zauren gidan, yana cikinyi 'kanin Aisha ya fito, kiran sa yayi tare da mi'ka masa wani leda yace "shiga min dashi kaji aboki?".
" To" yace ya shiga gidan su Joy dashi ya mara masa baya, Joy ne zaune tsakar gidan lokacin da ya shigo zaune da d'aurin 'kirji ga bokiti a gaban ta tana ta faman ya tsina fuska.
"Sannu da dawo wa Anty Joy" Muhusin yace, d'ago da kai tayi tana kallon sa tare da cewa "yauwa yaro kirki".
Aje kayan kusa da ita Auwal yayi shima Muhusin yayi hakan.
Haka Auwal ya kwaso kayan nan tasa tana zaune yana shigo wa dashi ba tace dashi ci kanka ba.
Duk da taso cewa wani abu, bakin tane yayi nauyi shiyya sa.
Sai da ya shigo dana 'karshe ya sallami Muhusin tare da zama kusa da ita.
Kallon sa tayi da mamaki domin wurin da 'kura amma ba tace komai ba.
Jan nufashi yayi murya can 'kasa yace " Joy" ido kawai ta tsira masa.
"Ina son ki" sai yayi shiru, murmushi ne ya su'buce min a take, kallo na yayi shima ya saki murmushi tare da kauda kai yace "alhamdulillah, don alamu sunnuna itama tana son sa".
Cigaba da cewa yayi " ina tsanani 'kaunar ki, kuma ina da kishi mai tsanani akan ki, ga kaya nan don Allah kirin'ka sawa kibar sa wad'an kike sawa don zuciya ta na 'kuna duk lokacin da nagan ki dasu".
"Duk da nasan addinin mu ba d'aya ba, amma zuciya ta tafi na'am da kayan mu, ki daure ki saka su".
Juyo wa yayi gaba d'aya yana kallon ta, yace " kina sona?" babu kunya na d'aga masa kai ina murmushi.
Farin ciki na ya'ki 'boyu, kallon na yake cike da 'kauna .
"Har da irin wannan zaman a dai na please" yace yana nuna d'aurin 'kiri dake jikin ta.
Rufe fuska tayi tare da cewa "wanka zanyi shiyya sa" a hankali.
"Zaman me kike to baki shiga bayin ba?" shagwa'be fuska tayi tare da cewa "na gaji ne shiyya sa" dariya yayi tare da mamakin ta.
Kafeshi da ido tayi kamar zata lasheshi, "kallon fa?" yace yana mai gintse dariyan sa .
"Kafi kyau idan kana dariya, Allah ko?" yace yana 'kale mata ido d'aya.
Kallon a gogon hannun sa yayi tare da cewa "muje na miki ankusa kiran sallah" zaro ido tayi tare da cewa "a'a, na yafe, hmmm, shikenan ai aukau lokacin da ko kince bazan bari ba. Mama fah?, tana barci" tace tana kallon cikin idanu wansa.
"Ta kyau ta, ki dai na kallo na haka idan ba haka ba akwai babban matsala" dariya nayi tare da cewa "tom, bari naje nayi wankan Allah har da yunwa nakeji, nima haka" yace yana shafo cikin sa.
Cikin tausayawa tace "bari na kawo maka kaci" tace tana mi'kewa, yamu ya had'iye kut tare da kauda kai da sauri.
Bata 'bata lokaci ba ta dawo hannun ta d'auke da tire, dire wa tayi a gaban sa tare da zama.
Bud'e kwanon tayi, shinkafa ne da miya, gaskiya bazai iya cin wannan shinka fan ba.
Don haka sai yace "kici kawai bari naje masallaci" 'bata fuska tayi ba shiri ya fasa mi'kewa.
Tura masa kwanon tayi gaban sa, kallon ta yayi ta masa nuni da yaci.
"Bani to" yace yana bud'e baki, kallon tsabtataccen bakin sa tayi, yayi matu'kar burge ta.
Babu damuwan komai ta saka cokali ta d'ebo ta nufi bakin sa dashi.
Ta bashi kusan sau biyar aka kira salla, don haka ya dakatar da ita.
"Maza kiyi wanka kafin na dawo mu cigaba da fita" yace yana gab da fita.
"Oho har da abinci kici kinji?" d'aga kai nayi ina mai jefan sa murmushi, shima ya mayar mini.
Comment & share pls
[11/5, 9:50 PM] Safeeya Aliyu: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*'KAUYEN 'YAR KADDE*
🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*Story & written by: Safiyya Aliyu Wakili*
💫DA BAZAR MU WRITER'S ASS💫
*We are here to make you happy, smile, educate and realized that we are best among all........ DA BAZAR MU MUKE TUN'KAHO*
*Tell my mistake to me, not to others. Because my mistakes are to be corrected by me, not by others.*
*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*
🅿3⃣1⃣to3⃣2⃣
Bayan fitan sa na kwashe kayan da ya sayo min na kai d'aki na aje na fito, dawo wa nayi inda na tshi na zauna, wani irin farin ciki naji yana mamayeni, kasa tashi nayi daga wurin har na tsawon wani lokaci, ina nan zaune sai faman murmushi nake Aisha ta shigo, kallo na take tunda ta shigo, nayi nisa bansan ta shigo ba.
"Besty! Besty!! Besty!!!" sau uku duk banji taba, gashi sai faman murmushi nake ina karkad'a kai.
Jin kiran sunana da tai tayi shine ya farkar da mama, fito wa tayi tana cewa "kun dawo yaushe Aisha?" .
"Tun d'azu, mama anya 'kwa'kwalwar besty lafia yake kuwa?" dariya mama tayi kad'an tare da cewa "mai kika gani?".
" Matso kiga mama, wallahi tunda na shigo take a haka, kuma nakira sunan ta bata san inayi ba".
"Joy" mama ta kira ta da 'karfi, firgit na dawo daga duniya ta nida hubby na, kallon Aisha nayi dake gaba na.
Murmushi da tunda nake da ita bata ta'ba ganin nayi wa wani ba bare ita taga na mata.
"Besty wannan fara'an fah? da murmushi fah?" rungume ta nayi ina ta faman sakin murmushi.
"Shafa min mana besty mai muka samu bayan dawo war mu?".
" Am very happy today my 'kawa" nace ina kallon ta, itama ni take kallo fuska ta d'auke da murmushi.
"Really?" d'aga mata kai nayi tare da sake rungume ta, mama na tsaye tana ganin ikon Allah.
"Burina, farin