A a Faruk a wajen Ammi za mu bar shi."
Abida kuma na ta kallon Farha itama tana ta kallonta kamar ta gane ta, kamar ba ta gane ta ba, sai ta miƙa mata hannu tana faɗin"Farha zo mu gaisa."
Ta mik'a mata hannu Farha ta tafi zuwa gare ta, ta riƙe ta ta daɗe tana kallonta kafin ta shafa kumatunta tana faɗin" Farhan Bilki ta girma!
✍️
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: *Bojuwa herbs*
*Oder your kayan mata for women of class*
*Our products are healthy and original*.
*Tested and trusted*.
*Sanyi flusher dinmu zai raba ki da dukkan nau'in infection, ya kuma sabunta Ki*.
*Ki zo ki saka order din ciccibin garari ko kazar sababi ki gode mini later domin saiwowin da nake amfani da su na yi imanin ba kowa zata iya zuba kudi ta saro masu daraja irinsu ba*.
*Duk wadda ta ciccibi sai tasan ta ci abu gangariya haka ma kazar sababi*
*Just DM for your order @08033773332*.
Na kalle ta ina mai murmusawa, duk yadda soyayyar ɗa da uwa take Abida ta yi jarumtar bar mini abin da ta haifa shi yasa nake yi mata uzziri don ta nuna mini zahirin soyayyar da ta shafe dukkan iyashegenta a zuciyata. Nan duniya na shaida Abida na cikin jerin masoyana na haƙika. Duk da tana kawaici amma yanayin yadda take kallon Farha zaka san akwai soyayya irin ta uwa a idanuwan Abida.
Ta sake tambayar Farha da 'Ina yayarku?'
Farha ta ce "Mun barsu a Zaria tare da Dady".
Ganin har biyar ta gota ya sa na mike na kwantar da jaririn a saman gado, ganin na mike yasa Farha ta saki hannun Abida ta nufo ni tana faɗin" Mahma ina za ki?"
Ina kallonta na ce" Ba inda zan je Farha salla zan yi "
Ta sake ni jin ba tafiya zan yi ba.
"Je ki zauna wajen Ammmi ku k
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Bilki ta fara dariya a zuciyanta ta ce yaushe rabon duniya da ayyaraye?
A fili kuma sai ta ce' Ai ni na gama, yanzu lokacin amarya ne ta yi ta zazzaga masa yara.".
Domin ta fahimci ya fi ɗokin haihuwar daga bangaren amarya tun da yadda yake b'arin jiki kan cikin nan ko a lokacin da ta yi cikin Amrah ba ta ga ya yi wannan ba'rin jikin ba. A yanayin da ta ke ciki bata ma fatan ta sake haihuwa to ta ina ma ta ga mijin ballanta har ta sake samun ciki? Mutumin da yanzu sun fi wata biyu bai neme ta ba tun samuwar cikin matarsa, ranar kwanan ta ma yanzu ba ta ganewa domin a sati bai wuce sau biyu yake kwana a dakinta ba shima a tafe yake kwana haurawa sama yana duba yar gwal, asuba na yi idan ya fita ba ya sake dawowa. Gabadaya ta rasa ma ina tsarin gidan yake kawia tana cigaba da binsa da ido ne Amma akwai ranar kin dillanci. Yana ta karakaina a kanta, haka ƴan'uwansa ma kullun cikin zuwa gidan suke da sunan duba amarya. Haka nan itama Hawwan k'annenta biyu sun zo daga Kaduna sun fi sati sannan suka tafi, ita dai sai dai ta ga ana shiga ana fita. Wanda ya shigo wajenta su gaisa wanda bai neme ta ba, ta yi kamar bata san ma ya zo gidan ba cikin irin rayuwar da take ciki ke nan.
Shi kan shi maigidan tamkar wanda aka yi musu farraku abin kullum hauhawa yake yi, ta kuma tabbatar ba wani farraku kawai sabbin bita yake mata cikin littafin kitabur ra'asi. Dan haka bata jin zafi domin ƴan'uwansa sun nuna rashin kulawa a kanta. Ba ta ɗorawa kanta damuwarsu a zuciyarta ba. Ta tabbatar wulak'ancin Baban Amra yafi jan kaso mai yawa na ciwon damuwar da ya kamata fiye da kason damuwar abin da ya faru cikin ahalinta.
Tunda tun kafin ya yi aure yake nausa mata bak'in ciki, yanzu da ya yi aure tozarta ta yake yi ta hanyar fifita yarinyar da bata wuce ta zo a mai yi mata hidimar gida tana biyanta ba.
Ana cikin haka semister ta yi nisa har an yi gwaji, sai ga Sahal ya zo yana yi mata magana, akan darasin da ta ke daukar su Amarya. Wai ta yi musu gwajin(test )kuma ya ga ta bata karamin maki 6 a cikin 20 me take nufi da hakan?"
Ya fada yana wurga mata takardan gwajin a jikinta. Lokacin tana cikin ɗakinta tana duba wasu takardu ne na makaranta ya shigo yana yi mata wannan jawabin.
Ko ɗagowa ma ba ta yi ba, ta cigaba da duba takardun hannunta. Idan shi ba adali ba ne to kar ya yi tunanin kowa ma irin sa ne, wato tunda tana matarsa ta bata maki 20/20 saboda shi, lalle Sahal ba shi da kunya to ai bai tsinana mata komai na abin arziki ba tun bayan auransa ballatana yarinyar ta ci darajarsa.
"Magana fa na ke yi miki kin yi mini banza?"
Ya fada a fusace Bilki ba ta son hayaniya shi ya sa ta dakata da abin da take yi ta dago tana kallon sa.
"Akan me ka ke magana?
Ta tambaya cikin nuna kamar ba ta gane in da ya dosa, duk bai sa ya fahimci ba ta da lokacinsa ba sai ma ya sunkuya k'asa ya dauko takardar yana nuna mata.
"Kin kyauta ke nan abin da kika yi Bilkisu?"
"Me na yi Baban Amrah?
Itama ta tare shi da sauri.
"Au ba ma kin san laifin da kika yi ba ko?"
Ya fada cikin harzuƙa.
"Ban sani ba, idan na sani ai ba zan tsaya ina tambaya ba."
Ya mika mata takardan yana fadin" Duba ki ga ni."
Ta karba ta duba sannan ta kalle shi tana fadin" Wannan kamar darasina a ina ka samu?"
Ta fada har tana bayyana mamakinta.
Baki ya saki yana kallon Bilki tana nufin ba ta san ko takardar wace ce ba?
"Duba sunan?
"Hawwa Hamza!
Bilki ta karanta a bayyane sannan ta mayar da fuskarta gare shi ta ce
"Wace ce ita? "
Ta tambaya cikin mamakin. Sahal ya yi wani sororo, wuyansa ya lamgwabe kafin ya ce" Kina nufin ba ki ma san ta ba?
"Ban gano wace ce ba, kasan daliban nawa suna da yawa ba zan iya rik'e sunan kowa ba."
Ta fada tana mik'a masa takardar hannunta amma ya kasa karɓa saboda mamakinta.
Ajiye masa ta yi a gefen gado ta d'au takardunta ta cigaba da dubawa.
"Kina nufin ba ki san sunan matata ba Bilki? Amma dai ai kinsan kin fara daukarsu darasi?"
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: "Don Allah fa?"
To ban ma taɓa lura ba, kuma ita ta fada maka ina daukarsu? Idan na shiga ajin bana tsayawa tantancesu abin da nake yi basu darasi da tabbatar da sun fahimcin darasin da kyau. Bayan haka bana sanin komai akansu illah zakwakuran cikinsu, Wanda hazakarsu ta wuce gigiggiwarsu. Bana ji itama ta dauke ni malamarta mai daraja don ban tab'a ganinta a aji ko a makaranta ta yi mini gaisuwar da zan shaida ina koyar da ita ba"
Ta fada tana kallon sa.
Kafin ta sake ce wa" Ka fada mata ta mai da hankali gaskiya, ta rage rawar kai a tsakanin kawaye if not , ba zata kai labari ba."
Sahal ya kai k'ololuwar fusata wato da gangan Bilki ta yi wannan muguntar?
"Ke nan da gangan kika kayar da ita a gwajin ko?
"Allah ya tsare ni, abin da ta rubuta shi ta samu."
Bilki ta amsa masa, a ɗan zafafe domin ita kam ta gaji da wannan ihun da ya ke yi mata a saman kanta.
"Ko da ba ta ci ba ai darajata sai ki bata maki mai d'an dama Bili"
Ya fada yana wani rage murya har da fadin sunan da rabon da ya ambace ta da shi ta manta.
Ta kalle shi shekeke kafin ta ce" Ai ba na haka, duk inda na ke adalci na ke yi ba zalunci ba, bana k'arawa mutum hak'kin da ba na shi ba."
Sai jikinsa ya yi sanyi domin sai ya ji kamar shagube Bilki ta yi masa.
"To ki d'an k'ara mata ko zuwa goma ne ga ta can tana kuka."
Haushi ya kama Bilki ta mike ko magana ba ta yi masa ba ta shige tiolet ta bar shi nan da ya gaji ne da tsayuwa ya fice sai da ta ji fitarsa sannan ta fito amma ta kwana cikin mamakin Baban Amrah, da ba ya jin kunyar aikata duk abin da ya ga dama. Ban da k'arfin hali har ya zo ya same ta da wannan maganar? A a ba kuka take yi ba, ta yi na jini ma, yarinyar sam bata mayar da hankali wajen karatu kwakwalwarta ba ta ja, sannan kusan kullum sai ta ga tana nunawa mutane ita suna zundenta. Bata taɓa nuna ta gane ba bare ta tanka a bata rashin gaskiya. Shine kuma ta k'i yin karatu, sai kuma ita dan tana tsoron kada ace ta yiwa kishiyarta mugunta sai ta k'ara mata makin din da bata cancance shi ba? Wato ta turo shi ne ya yi mata dole shi kuma ba tunanin komai ya zo zai yi mata tilas. Ta dade tana mamakinsa har Basma sai da ta bawa labari da suka yi waya. Basma ta buga wani zagin Katsinawa sai da Balki ta kashe waya tana dariya. Ashe zance bai k'are ba da aka yi jarabawa ma sai da ya zo ya same ta akan ta bawa yarinya sakamako mai kyau ta ce to babu musu illah iyaka ta kud'iri ajiyar ba zata taimake ta ba, haka nan ba zata danneta ba. Ai kuwa sakamako na fitowa Hawwah ta samu F a darussa biyu ciki har da wanda Bilki take daukarsu wato pharmacology. Sannan sauran ta haye ne irin da k'yar din nan dan haka gabad'aya GDP dinta ya yi k'asa matuƙa da gaske.
Ta dinga kuka sosai tun a hanya yake rararrashinta tare da cewa yasan tana da kokari lififin cikine ya hanata hayewa dan haka ta kwantar da hankalinta yana tare da ita kuma zai yi kokari komai ya daidaita mata.
Cikin rishin kuka ta ce "Ban ci na wacce kake da iko da ita ba sai na wani ne za'a gyara mini? Ni Wallahi ka bude mata k'wanji ta gyara mini sakamakona, na gane bak'inciki take yi da ni tunda ta ga ina da ciki shike nan ta daura aniyar sai ta kai ni k'asa. Duk ajin ni da kawayena kawai ta kayar har wanda muka fi su k'ok'ari duk ta ciccibasu sun haye amma ban da ni da duk wanda nake mu'amala da su."
Suna dawowa gida kaitsaye wajen Bilki ya dira yana neman ba'asin kayar da Hawwa da ta yi.
Bilki da bata son jan maganar ta mik'e ta ce "abin da ta yi ne ta ga ni".
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Rikici har wajen Hajiya, itama wai Hajiya kamar ta manta da zaman da suka yi tana goyon bayan Sahal da matarsa.
"Haba Balki abu duk na gida, ai ko don darajar Sahal kya bari ta wuce tunda kina da damar yin haka"
Mamaki ya hana ta magana sai da Hajiya ta ce wai idan ta isa da ita to ta gyarawa abokiyar zamanta jarabawarta.
"Kin ga ciki ne da ita har ya fara girma damuwa kadan zai saka a samu matsala."
Bilki ta gyara zama tana kallon Hajiya ido cikin ido kafin ta ce" Ai ba ni da wannan ikon Hajiya na riga na bawa makaranta duka sakamakon jarabawar komai na hannunsu yanzu, ita ce za ta gyara carryover ɗin ta wata shekaran amma ni ba ni da wani taimakon da zan iya yi mata."
Hajiya ba kunya tafara fadin" Haka za ki ce Bilki? Ashe ba kamar uwa kika dauke ni ba?"
"Uwa kuwa mai k'ima na d'auke ki Hajiya. Amma hakan ba zai saka na ci amanar aikina ba. Ko shi Baban Amra nake koyarwa ya kin yi karatu to ba zan ba shi makin da bai cancance shi ba. Don a lahira ni kad'ai zan kwashi zunubin son zuciyata "
Hajiya ta kasa magana Balki ta gama daure ta da maganganu da haka maganata da mutu mussaman da k'anin Sahal din ya ce wa Hajiya ba maganar suna auren miji d'aya wannan daban, bangaren malama da daliba daban idan ta yi abu mai kyau za ta ga ni.
Babu adalci a tilastawa Bilki ta ci amanar aikinta, da haka zance ya k'are ba ta san yadda ya k'are da mai kuka ba. Kan dole Hawwa ta gaji ta hakura tunda ba ta samu mafit ba wato tunda suna auren miji daya bari ta kwanta a gida ta k'i karatu, tana jiran ta wuce a banza, ba mutuncinta take ga ni ba, bare ta taimaka ta cicciba ta, tana ganin yadda take hada kai da kawayenta suna gulmarta suna zundenta.
Sai da ta zo making ta tarar duk yan group din nasu basa wani ja.
Cikin Hawwa ya fito ana gani sosai, tuni ta fara zuwa awo a bakin Alti take ji domin akwai wata rana da Sahal ya sakata ta rakata shi zai kaita sai kuma aka kira shi daga wajen aiki. Ba domin Alti ba, ba ma za ta san wattanin cikin ba ta ga dai ya girma tun da har ya fara turowa a riga sosai.
Ba ruwanta da harkar da ba a saka ta ba, shi yasa ta zauna lafiya in da ta sake godewa Allah warkewarta daga cutar damuwa yanzu ba ta shan magani, sai na hawan jini kawai domin ya kamata, shi ya sa take kiyayewa sannan tana shan mgani.
Ta riga ta kama kanta da sha'anin gidan gabadaya ba ta maida kai akan wasu abubuwan, shi yasa ko wani abu ya faru a gidan sai dai ta ji a bakin yara ko bakin Alawiyya to yau ma tana dawowa daga aiki ta yi yamma a cikin makaranta. Amrah ke faɗa mata Abban su ya siyo su dankali da doya bai kawo musu ba duk an haura da kayan zuwa saman Anty. Dama tana son ta samu damar da zata bata labarin abin da ta jiyo kwanakin baya dan haka duk Amra sai ta had'a ta faɗawa uwarta abin da ta ji Anty na faɗawa Dady, akan batun cefane da mota da kuma super wax.
Wato yanzu shine ya yo mata cefane irin nata da take ga ni tunda garar da aka kawota da ita ta k'are.
Lamarin ya daurewa Bilki kai, har yana da kudin siyan su doya da dankali da kayan miya daga Jos shi ne ita bai taɓa yi siyo mata ba! Tunda ya yi aure ya ce kowa ta yi girkinta ba zata iya tuna abin naira biyar da Baban Amrah ya siya musu na kayan amfanin gida ba. Amma tasan ya kawo mata k'aramin buhun shinkafa da katon din taliya da man gyada 5litr, wanda cikin garar Hawwa ne. Ba zata iya tuna me ya kawo mata ba bayan wannan.
Ba ta yadda da maganar Amrah ba sai da ta tambayi Alti itama ta bata tabbacin ta ga sadda yake hawa da su har da ledar kayan tea ta ga ni.
Shi yake siyawa amaryarsa ita kuma bangarenta idan ba zata siya ba sai dai su hakura da shan tea din, shi yasa ba ta jiransa sannan ba ta tambayarsa idan tana da kudi siyan abin da take so kawai take yi.
Abin ya dame ta amma ta kud'iri niyar sai ta yi masa magana, ranar ko ya shigo d'akinta zai kwana kamar yadda ya saba sai dare ya tsala ya yo shirin barcinsa daga can yake shigo mata.
Har ya kwanta ta ce ya tashi zasu yi magana ya fara faɗan sai da ta ga zai kwanta sannan za ta ce za ta yi masa magana.
Ta hakurkurtar da zuciyarta ta ce "maganar ba za ta daɗe ba sannan fa ya tashi ya zauna.
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: "Baban Amrah kana yin wasu abubuwa da ban gane musu a cikin gidan nan ba.'
A hassale ya ce" Kamar na me fa? "
"Kamar na yadda kake tafiyar da mu tsakanin ni da yaranka da amaryarka mu ba ka yi mana cefane, tunda ka yi aure sisi na dawainiyar abincin bangarena ba ka bani ba, duk ni ce nake yi, yanzu fa ba da ba ne Allah ya rufa maka asiri dama saboda ba ka da shi ne nake yi, na dauka yanzu za ka yi tunanin karbar ragamar da Ubangiji ya dora maka, amma sai na ga ba haka ba. Ita kana yi mata cefane ni kuma ko oho ni da yaran ka. Ai ya kama ta ka daidaita bisa adalci na yadda ko wanne magidanci yake yi. Kuma ni dai a sanina a farkon aurenmu kai adali ne ba abin da baka yi a gidanka na bajinta ma amma yanzu ka sauya mini gabadaya Baban Amrah!
Ta fada cikin taushin harshe ainun.
Kai tsaye ya ce" Kin taɓa ce mini baku da wani abu ne kika ga ban kawo ba Bilki?
Ya k'ura mata ido yana kallonta sosai.
"Ban gane ban taba fada maka ba. A matsayin ka na megida ai ya dace kasan duka hakkin da yake rataye a wuyanka. Ba bukatar a tunasar da kai."
Ta fada kaitsaye don ta fara harzuk'a.
Ya jinjina kai kafin ya ce" To ai ganin ba kya magana shi ya sanya na dauka kina da komai ne. Hawwa kuma tana fada mini abu kaza ya kusa k'arewa tun ma kafin ya k'are shi yasa kika ga ina siya mata, ke ma idan kin koyi yin hakan zan siya miki ai hakan ba matsala ba ne "
Baki bude Bilki take kallonsa kafin ta samu zarafin magana ya cigaba da fadin" Duk abubuwan da kike yi ke kika saka kan ki. Ni ban tab'a rokon ki alfarmar ki yi ba, saboda haka ba ki da ikon magana. Ko lokacin da ba ni da aiki, ke da kanki kika kika fara abubuwa kan ki tsaye ban roke ki ba, bayan na samu aiki na ga kin cigaba daga inda kika tsaya, kin ga ita ta tasan nine zan bata don bata da sana'ar da zata nuna mini bata buk'atar hidimata sannan ba ma'aikaciyar gwamnati ba ce. Ke kuwa fa?"
Kalamansa sun daki