Dingishin Kwado Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Salma Category :  Romance

Chapter   3 / 7

6K to 9K   out of 19.7K words

fatata da sauran abubuwan da zasu banbanta jikin mace da na namiji. Amma tabbas muna matukar kama da juna.
Na tafi lissafin shekarunsa domin shekaru shida ya bamu. A lokacin shekarunsa talatin da uku. A wanccan lokacin gani ake yi ya zama tuzuru domin dukkan sa'aninsa da ma wanda ya girma sun yi aure har sun haihu.
Tun filazal Yaya Sulaiman dan gaye ne kuma dan bokone na gaske. Amma da ya dawo na fahimci ya samu cigaba mai yawa, ya goge da ilimi da kuma wayewar rayuwa.
Sadda suka iso ni da Abida muna farfajiyar harabar wajen adana motoci, gidan Yaya Faruk zamu je yini.
Da girmamawa muka gaida Baba karami.
Ya kalli Abida ya ce "Maryam kin huce, kin daina fishin?"
Ta dauke kai i tana fishi fishi kunya kunya ba tare da tanka ba.
Ya ce "Ato gara kisan matakin dauka dan kuwa tabbas babu maganar wata makaranta kuma sai a dakinki. Ke ko sha'awar yanuwanki da kike ganinsu da yaransu ba kya ji?"
Da shagwaba ta ce "To Baba sun duk sun samu mazan ni kuwa fa?"
Ya zabura ya mata dakuwa tare da yin kanta zai kai mata bugu.
Ta yi maza ta goce ta falfaala bata tsaya ba sai da ta bada tazara, sannan ta tsaya tana dan haki.
Ya ce "Mutane nawa suna zuwa wajenmu da sunan sun gan ki suna so, kina yin tsallen albarka kina fadin ba da yawunki suka zo ba?"
Ta kasa amsa masa. Ya yi kwafa ya ce "wannan karon kam ko ni ko ke na gaji da iyashegen ki, inma jinnul ashuq ne akanki zasu ci iyayensu dan kuwa na shirya yin arangama mai zafi da su".

✏️
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Daga ni har Yaya Sulaiman muka kwashe da dariya domin yadda Baba ya furta jinnul ashuq akwai ban dariya kwarai da gaske, yayin da ita kuma ta sha mur.
Haka muka tafi gidan Yaya Faruk tana ta gungunin ita bata da mashanshani, don kuwa duk wanda ake lissafin sun zo da sunan suna sonta ba jarumai bane ba kuma mijinta a ciki. Don ta yi imani da akwai mijin da kaddara ta zaba mata a cikinsu da tuni ta yi auren ai.
Muka isa gidan Yaya Faruk muka tarar yana shirin tafiya gidan gona. Ya dinga marabtarmu cikin barkwanci.
Haka ma matarsa domin a yanzu kam gaisuwar girma da arziki muke yi ta daina tsananta mini.
Ya zauna ya ce to ku gaisa da matar gidan ku sha ruwa sai mu tafi gidan gonar mu yini a can ko sarauniyar shaiba?"
A duk sadda ya ce hakan har cikin raina nake jin sunan. Tare da tasowar al'amura masu yawa a kansa.
A sanyaye na ce "To Yaya Faruk".
Ya saka hannu ya dauki mai sunansa da ya yi barci tun a hanya. Yana fadin my name sake tashi ka ga Yaya Faruk senior."
Na murmusa ba tare da na ce komai ba.
Ya kalli Abida ya ce "Autar momi wai har yanzu ba ki huce ba ne?"
Ta sake zumbura baki amma bata tanka ba.
Ya sassauta ya ce "Indai kin san akwai wanda yake sonki ki ba shi dama mana, ba fa wacce su Baba suka daga mata kafa irin ki. Ina jiye miki kada ki yiwa kanki sanadin da zaki ji sun bada aurenki ga wanda suka ga ya dace"
Ta murmusa ta ce "Ba maganar a mini auren dole Yaya Faruk. A wannan karnin? Da ilimina?"
Ta girgiza kai tabbacin ba mai yiwuwa ba ne.
Na zuba mata ido ba tare da na furta komai ba. Wato Abida asalin feminine ce.
Ya Farook ya kalle mu ya ce "Rigunan jininku sun mini kyau. Ban cika ganin abayas irin haka ba anan".
Abida ta ce "Bilki ta siya mana a wajen Umm Aslan &Asalah. Egyptian abayas ne kasan sune original. Ya ce gaskiya sun yi kyau sosai nima zan baki ki siyowa Jamila irinsu ".
201121544627 da +2349162662750 Kawai ta tuntube ta a WhatsAp sai ta zaba da kanta idan kun tura kudin, sai na karba muku a Kano tunda anan kayanta suke sauka.
Haka muka rankaya muka nufi gonar ladi farms da kwandon abincinmu matarsa ta hado mu da shi.
Yadda muka zo a motar Abida haka muka shiga ya ja muka yi gaba yayin da ya shiga tasa ya bimu a baya.
Gabadaya gidan gonar ya sake habaka, dukiyar dabbobi kala daban daban a ciki iya ganinka. Haka nan an gyara ta gyra na mussaman domin har zuwa ake yi da sunan yawon bude ido. Sosai ake hada hadar kasuwanci a ciki. Madara da yogurt din da ake sarrafawa a ciki na manyan kudade ne masu matukar nauyin gaske. Hatta kwai a kullum ana diban sama da dubu talatin ban da wanda suka fashe, shiyasa ma'aikatan wajen suma yawane da su tamkar me, an samu cigaba ta hanyar samarwa matasa masu yawa aikin yi
Yaya Faruk ya sake zama babban mutum kudi ya zauna masa duk da shi kadai ne a Funtua cikin yayyanmu. Amma yana cikin daula don idan kana gidansa ma sai ka zaci kana Abuja ne cikin rikunin uguwanni masu daraja.
Duk yadda nasan ladi farms girmanta ya kai kurewa amma a wannan ranar da na shiga cikin shekaru na hankali, ina kuma cikin nutsuwa sosai, na tsorata da irin girmanta da tarin dabbobi da shuke shuke. Don yanzu har 'katon runbun abinci an gina ta yadda ake adana kayan amfanin da aka nomawa a ciki.
Jikin mangwarori suka yi parking muka yi shimfida muka zauna. Gabadaya wajen yabanya ce ga danshin k'asa a dalilin duk safiya da maraice sai an jona tiyo a duk inda aka yi shuke shuke ko inda koriyar ciyawa take.
Duk yadda shekarun nan suke tafiya Yaya Faruk bai canja ba. Zama yake cikinmu a rak'ashe duk mai matsala ta zano masa, shi kuma zai saurare ka da kunnen basira ya kwantar maka da hankali ya kuma baka shawara ta gaskiya.

A yau kam Abida ce ta dinga jero masa laifukan Momi. Ashe duk yadda soyayyar Abida bata boyuwa a wajen Momi yanzu zaman nasu ya fara tsami bisa dalilai guda biyu. Ita Momi aure take so Abida ta yi, dan haka ta matsa lambar sai ta fito da miji, bayan haka mafi yawa bata bari ta yi dinkuna ko saka kayan alatu bisa hujjar wai maza zasu kasa dunfararta da sunan aure tunda suna ganin matsayin aikinta da matsayin gidansu, kaya masu tsadar gaske kuma zasu sake kaita kololuwar
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: matsayi.
Ya yi dariya ya ce "Hakuri za ki kara yi, lamarin iyaye dole a bisu yadda suke so. Sannan ni kaina so nake ki yi auren Abida! Menene ya rage miki ne? Aure kuma shine suturar mace. Duk zurfin karatun da zaki yi, matukar ba ki da aure kin rasa wata kariya ta mutuntaka da aure kadai ke bawa mace shi. Ki nutsu ki sassauta burinki, ba yadda za'a yi ki samu irin teste din ki, domin no body is perfect a cikin wannan rayuwar."
Ba walwala ta ce "Aure lokaci ne fa yaya Faruk. Kuma ni ba wani dogon buri ko wani tsatssauran ra'ayin na dauka ba. Kawai wanda zuciyata ta nutsu ne ban samu ba, amma ko yanzu idan na samu wanda na aminta da shi zan gabatar da shi. Akan me za'a matsa mini har sai na je na auri wanda ba mijina ba ne?.
Muka kwashe da dariya. Na kasa ce wa komai domin yanzu zata sauke mini fishinta da take fama da shi, na sani. Yaya Faruk ne ya ce "Dama ana auren mijin da ba naka ba ne autar momi?
Da dukkan zuciyarta ta ce "sosai ma domin idan na auri wrong person ai ban auri mijina ba domin na fada cikin garari da talajaurar duniya".
Ya gintse dariyarsa ya ce "Da ikon Allah na gari za ki aura albarkacin adalcin da iyayenmu maza suke yiwa iyayenmu mata ba za ki yi aure inda za ki wulakanta ba. Fatana ki kwantar da hankalinki. Ki bude zuciyarki ki fahimci manufar iyayenmu ".
Anan muka yi sallar la'asar.
Wajen karfe biyar sai ga Yaya Sulaiman ya iso akan machine.
Yaya Faruk ya kalle shi ya ce "Baka son yin tuki ne?"
Da walwala ya ce "Da kafata na yi rabin tafiyar.
Sai kuma na hau machine domin daga bakin gate din nan ma shigowa ciki ba karamin tafiya ba ce mikakkiya".
Yaya Faruk ya ce "Ka yi kokari, ka kuma motsa jikinka.
Na kalle shi na ce "Yaya Sulaiman sannu da zuwa dama na k'osa mu hadu".
Ya zauna yana ce wa "Ga ni "Bilkisu sarauniyar shaiba in ji Yaya Faruk ".
Muka murmusa gabadayanmu ban da Abida da dama ba wani jituwa suke yi ba tun filazal.
Ya kalle!ta ya ce "Autar momi saboda Allah har yanzu ma da kika girma ba zamu shirya ba? Tunda na dawo sau uku kika bude baki kika mini magana fa".
Yana rufe baki ta ce "To ai sau ukun muka hadu."
Ya ce" yau fa?"

*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke da kyau da nagartar.*
*Gunis hijab ado cikin wayewar addini da rayuwa*
*08163761797*

Kaitsaye ta ce "Dazu bamu gaisa ba? Yanzu kuma daga zuwanka sai na ce make me?"
Ya girgiza kai tare da ce wa "Ho Abida! To sannu da yammaci ".
Ta amsa da fadin"Sannunka dai Yaya Sulaiman".
Daga haka ta tsuke bakinta yayin da ni nake ta fadin
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Baba karami kam sai da aka sare gaban motar sannan aka fito da shi sai dai Babu rai ya amsa kiran mahaliccinmu.
Wannan mutuwar na tsaya hakaito muku yadda ta yi mana mugun bugu bata lokaci ne mai yawa. Amma mutuwar Baba ya zama tamkar tafiya da dukkan nutsuwa da walwalarmune gabadaya.
Daidai nan kuka mai tsananin gaske ya k'wace mini, dama lallaba zuciyata nake yi sai kuma na zo inda duk dauriyata dole na koka, dole hankalina ya tashi domin an zo gabar da bana fatan masifar da ta sauko mana ta sauka kan kowanne ahali.
Mutuwa da ciwo da tonon silili take. Allah ka jikan makabantanmu.
Da yake dab da magariba aka yi hadarin labarin mutuwar sai bayan magariba ya riskemu. Cikin tashin hankali na isa gidan Abida.
Kuka muke yi kan kuka ita kam ta tubure a lokacin zamu tafi tunda Yaya Sulaiman na asibiti rai a hannun Allah.
Da k'yar da sudin goshi Yaya Asad ya dakatar damu akan gobe da asuba zai saka a zo a kaimu Funtua.
Barci barawo a wannan ranar bai iya satarmu ba. Gabadaya ni da Abida a rikice muka ainun ba mai bawa wani hakuri. Sai dai na yi imanin Abida ta fini rikicewa. A fili cikin kuka take ce wa "Allah ka kaddara mini na ga Yaya Sulaiman da ransa, Allah na tuba kada a yi mana biyu innalillahi wa inna ilaihir raji'un!

*Bojuwa herbs*
*Oder your kayan mata for women of class*
*Our products are healthy and original*.
*Tested and trusted*.
*Sanyi flusher n zai raba ki da dukkan nau'in infection, ya kuma sabunta Ki*.
*Ki zo ki saka order din ciccibin garari ko kazar sababi ki gode mini later domin saiwowin da nake amfani da su na yi imanin ba kowa zata iya zuba kudi ta saro masu daraja irinsu ba*.
*Duk wadda ta ciccibi sai tasan ta ci abu gangariya haka ma kazar sababi*
*Just DM for your order @08033773332*.

Kuka nake yi mai tayar da hankali sosai amma da zarar na kalli Abida sai na ji tashin hankalina na sake rub'anya mussaman idan tana gunji tana rokon Ubangiji kada ya k'addara mata yin takaba a yanzu.
K'arfe shida na asuba motar y'ansanda ta zo ta kwashe mu.
Muka isa muka tarar da kofar gidanmu tamkar zai stage da jama'a.
Haka muka kutsa muka isa. Idanuwan kowa ya yi jajur tabbacin an sha kuka an gaji. Baba Babba kuwa gabad'aya ya rikice baya um baya umum ya zama wani iri k'arfin imani ya hana shi ya shiga cikinmu ya yi ta rafsa ihu, don tabbas an masa mutuwa mai gigitarwa. Mami kuwa sosai take sowa da k'yar aka samu ta koma yin na sharb'e.
Hankalinmu bai dawo ba sai yamma aka tafi asibiti wajen Yaya Sulaiman. A can muka tarar da Abida tana zaune duk ta fige ta lalace. Kasancewarta likita kuma ta yi aiki a wajen ya sanya ba'a shata mana layi wajen shiga wajensa ba. Jikinmu ya sake yin sanyi a lokacin da muka halin da yake ciki. Yana kwance bai san inda kansa yake ba.
Yanzu haka sun tura shi asibitin
K'ashi na dala. Don ya bugu sosai.
Tashin hankalin da muke cikinsa k'warai ya tsananta.
Ranar da aka yi sadaka uku aka tafi da Yaya Sulaiman asibitinn Dala cikin Kano.
Cikin k'ankanin lokaci gabadaya aka gigita mana nutsuwa da walwalarmu gabadaya, don Baba Babba ma a kwance yake ana ta kara masa ruwa.
Dukkan ahalinmu kowa ya bar inda yake ya taho gida. Daga Funtua kuwa aka d'unguma Kano nemawa Yaya Sulaiman da har lokacin ba'a san matsayin lafiyarsa ba, tunda asibitin dala ma sun ce sai an hada masa da ganin likitan kwakwalwa don ya bugu a kai. Ganin hakan Yaya Asad ya ce Farouk da Abida su shirya zasu tafi Germany ya ga likitoci a can, tunda a can ya yi karatu ya kuma yi aiki na shekaru zai samu kulawa ta mussaman.
Wata guda yana asibitin cikin coma sannnan aka samu visar tafiyarsu. Gabadaya bama cikin nutsuwa sai dai su Yaya Asad sun koma wajen aikinsu. Kan dole muka hakura muka bi Baba
da adduar rahama, aka mayar da hankali wajen neman lafiyar Yaya Sulaiman da a yanzu muke cikin tashin hankali ganinsa tamkar gawa.

*Dafatan zaku gyra zama don yanzu ne zamu kutsa cikin danbarwar labarin. Ku nutsu sosai, ku bi sannu a hankali har zuwa inda zn karkare don kuwa yanzune abin da labarin yake tafi da shi zai fara.*
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Su Abida sun isa ƙasar Germany tare da Yaya Sulaiman, sun dai yi waya damu sun sanar damu isar su amma tun bayan nan ba mu sake ji daga gare su ba, ni kaina idan na k'ira wayar Abida ba na samu, da man Yaya Faruku ne ya kira ni a lokacin da suka sauka a k'asar. Su suna can mu kuma muna nan amma zullumi bai bar mu ba, mun san ce wa mun rasa Baba ƙarami ya tafi in da har abada ba zai dawo ba, amma zullumin da fargaban halin da Yaya Sulaiman ke ciki ke nurƙurkusan dukkanmu, kowa ka yi waya da shi jikinsa a sanyayaye ba karsaashi ba farinciki.
Mami kusan ko da yaushe muka yi waya da ita cikin kuka take, haka muke ta kwantar mata da hankalin ce wa ta cigaba da addua in sha Allahu Yaya Sulaiman zai warke. Amma ita ga ni take yi kamar shima ɗin kamar Baba karami ne rasa shi za mu yi, ni kaina karfin hali na ke yi amma a yadda aka tafi da Yaya Sulaiman bai san wanda ke kansa ba kowa ma ya sare amma saboda kar na zama raunin Mami ya sa na ke daure zuciyata ina nuna mata da ikon Allah Yaya Sulaiman zai tashi da ƙafafunsa.

"Umh Bilki, shima rasa shi zan yi, rasa shi za mu yi kamar yadda muka rasa Babanku."
Kalaman Mami ke nan a duk lokacin da muka yi waya da ita shi ya sa in muka gama waya sai na zauna na ci kukana na ƙoshi ba mai lallashina. Domin Har da tausayinta ke nuk'urk'usata, mutuwar miji da rashin sanin makomar rayuwar d'a tashi guda ba k'aramin alamari ba ne.
Baban Amra lokacin farkon faruwan lamarin ya kula da ni, ya tausaya mini,amma tunda aka fara nisa da mutuwar shike nan ya janye tausayawar. Kullum sukuku na ke, ga ciwon mutuwar mahaifi ga zullimin makomar lafiyar Yaya Sulaiman.
Amma sai ya kalle ni ya ce
"Ki k'arantawa kanki wannan damuwar fa duk ba mafita ba ce, hakuri da addu'a shi ne mafita. Allah ya jiƙan Baba shi kuma Sulaiman Allah ya tashi kafaɗun sa."
Na sani gaskiya ya fada, kuma shi zuciyarsa d'aya yake fadin hakan. Amma ni so nake ace cikin taushi da laushi tare da kulawa zai dinga fada mini, ba wai ya fada ya cigaba da uzzirinsa ba.
Tun da na dawo ba na cikin sukuni da walwala, hakan bai hana shi kallo ko charting ba, har ga Allah na ji zafin sa ko dai bai taya ni kuka ba ai ya taya ni alhinin halin da na ke ciki ni da zuciyata amma bawan Allah nan da wuri ya wartsake.
Alhalin lokacin da nasa tsohon ya kwanta dama mun shafe fiye da wata ko talabijin bamu kunna ba. Ba Shi da sukunin yin kallo dan haka nima na haramta mana ni da yara dan taya shi jimami, amma abu ya zo kaina, na ga daban. Matsanancin mamakinsa kullum k'ara ara yi mini tsamari yake yi tare da tunanin mene matsalar ne?
Basmae kullum sai ta kira Ni a waya tana sake kwantar mini da hankali. Duk bayan kwana biyu sai ta zo ta debe mini kewa tare da ba ni hakuri tabbas ita ɗin ƙawar alheri ce.
Baba Babba duk dakiyarsa wannan lamarin ya raunana shi ya gaza, ko a waya na k'ira shi yadda na ke jin sa wani sanyi sanyi ba na jin daɗi, yana gida ba ya zuwa ko'ina lalle mutuwar Baba karami ta raunana kuzarinsa sosai Momi ce ma in muka yi waya da ita na ke jin karfin gwiwa domin ƙwarin da tabbaci ta ke bamu da cewa Yaya Sulaiman zai warke, mu ma kuma muna fatan haka in sha Allahu.
Tun tafiyar su ba a sake jin su Yaya Faruƙu ba, sai bayan kwana goma sannan Yaya Asad ya kira Baba Babba ya sanar da shi halin da suke ciki, ashe shi suna magana da shi, mune suka rufe hanyar sadarwa da mu, shi kuma da ya ke da aljihunsa ake yin komai, sannan a matsayinsa na babba suna k'iransa suna kuma sanar da shi halin da ake ciki.
Alhamdulillah likitoci sun yi gwaje-gwaje akan ƙwakwalwar Yaya Sulaiman jini ne ya taru a wani gefe in da aka gode ma Allah bai taɓa ƙwaƙwalwarsa ba, tuni an yi masa aiki
sannan in da ya ke da karaya sun ɗora shi sun kuma ba da tabbacin a kowani lokaci zai iya farfaɗowa, a bakin Yaya Muneera na fara jin labarin sosai n samu sassaucin zullimin da nake ciki ba ma ni kaɗai ba dukkan mu wannan labarin ya

3 / 7