Dingishin Kwado Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Salma Category :  Romance

Chapter   4 / 7

9K to 12K   out of 19.7K words

wanke kaso mafi girma daga cikin damuwarmu. Sai bayan kwana biyu na samu mgana da Abida yadda na ji muryanta cikin sukuni ya sa na samu tabbacin labarin da muka samu gaskiya ne.
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: "Maigado an gano matsalar Yaya Sulaiman na masa aiki a kansa sannan an masa na k'afa dazu!

Abin da ta fara faɗa mini ke nan ko gaisawa ma ba mu yi ba, farinciki ya cika ni na yi hamdala a fili da sarari, mun ɗan jima muna hira, tana tambayana ya su Mami da mutanen gida?
Na ce "kowa lafiya da godiyar Ubangiji, a baya dai muna cikin zullimi amma yanzu sai godiya. Ta tambayi yara, na ce su suna nan lafiya, mun ɗan jima muna hira ta ce mini za ta ɗan kwanta tun zuwan su ba ta samu barci ba.
Ranar yini na yi murna da farinciki na kira Basma na faɗa mata itama sai murnar farinciki take yi. Baban Amra ma da rawan jiki na tare shi da labarin har sai da ya ɗan rumgume ni yana faɗin" Alhamdulillah."
Nima na riƙe shi ina mai bayyana farincikina har fararen haƙorana suna bayyana tsabar murna.
Yara ranar kaf sun san Mahma na cikin farinciki saboda yadda na yini tare da su. Mutuwar Baba karami ta gigitamu k'warai da gaske mussaman da ba jinya ya yi ba. Sai kuam aka had'a mana da kila wa Kala na rayuwar Sulaiman dole dukan sai ya yi mana yawa, ace ba Baba ƙarami sannan ba Yaya Sulaiman, tabbas zukata za su raunana sai dai da ya ke Ubangiji ne mai yin abin da ya so, idan ma hakan ne ya so ya faru sai dai mu yi haƙuri ba mu isa mu ja da hukuncin Ubangijinmu ba. Labarin farfaɗowar Yaya Sulaiman ya zo mana da kwana ashirin da isar su ƙasar Germany. Yaya Faruku ne da kansa ya kira ni ya sanar da ni, bayan shi Abida ma ta sanar da Ni an kawo shi ɗakin hutu amma dai yana ta barci ne ba su samu shiga wajen nasa ba. amma tabbas ya dawo hayyacinsa. Na samu K'warin guiwar tafi ganin Mami tunda an samu cigaba sosai . Hakan ya sa na ce wa Baban Amra gobe ina son zuwa gida bai hana ni ba. Washegari na tattara yara muka zo Funtua kamar na sa ni gida cike da matansu Yaya Faruku da yara ana ta barka da arzikin da aka samu.
Baba Babba kuwa kofar gida ya fito aka tara masa almajirai ya riƙa rabon kuɗi sadaka domin godiya ga Ubangiji, mu kam mu a cikin gida kowa ka ga ni ya d'an samu k'warin jiki har Mami na ga ta d'an samu kuzari.
Yaya Asad daga can lagos ya nemi visa sai dai kawai da suka kira mu Video call suka haɗa mu da Yaya Sulaiman muka gan shi a can kwatsam ba tare da kowa ya san tafiyarsa ba. Allahu Akbar Allah mai gagara misali, sai ga Yaya Sulaimam zaune a kan gadon majinyata ga rigarsu ta asibitin kafafunsa da ya samu karaya an ɗora shi kansa da wani bandeji, amma yana zaune yana mgana kamar ba shi ne aka kai shi rai ƙwaƙwai ba, kowa ya gaishe shi kuma ya amsa sannan ya kira sunan kowa alamun dai ya dawo hayyacins sosai a Allah abin godiya.

Ni ina ganinsa sai kawai na ji kuka ya zo mini. Farha na jikina ta lafe. Abida ta leƙo da kanta tana kallona ina ta sharan ƙwalla, sai kawai ta kaɗa kai kafin ta ce" Sola ke wai me ya sa ba kya girma ne? Gaban ɗiyar ta ki, kike b'are baki kina kuka?
Ina jin ta ce haka sai na sake fashe wa da kuka don gabad'aya tausayinsa ya yi mini k'awanya Bai san mahaifinsa ya rasu ba.
Baba Babba ne ya kalle ni kafin ya ce" Bar kuka Maigado yi magana da ɗant'uwanki kin ji!
Na gyaɗa masa kai, kafin na yi magana Yaya Sulaiman ya murmusa kafin ya ce" Bilkkina ba ga ni kin ganni ba? Ki daina kuka kin j! Kar ki saka Farha ta fara gata nan idanuwanta ya kawo ruwa." Sai da ya faɗa na juya ina kallon Farha ta kusa kukan itama.
"Ya jikin ka Ya Sulaiman?
"Na ji sauƙi Bilkina. Alhamudulillah mun gode ma Allah"
Kallonsa kawai nake yi duk ya rame ya yi baƙi sai na tuna dr rasuwar Baba ƙarami kawai sai na sake fashewa da kuka kamae wata ƙaramar yarinya na ɗauka bai sani ba ashe ya sani sai ji na yi yana ce mini "Maigado ya ƙarin haƙurinmu!? Allah ya jiƙan Baba da gafara Allah ya kyautata makwancinsa"
Gabaɗaya muka amsa da Amin Yaya Usman ne na ji yana faɗa mini Yaya Asad ne ya sanar da shi bayan ya isa a jiya. Su Abida ba su samu wannan ƙarfin zuciyan sanar da shi rasuwar Baba ƙarami ba.
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Har wayar ta gama zagayawa hannun kowa ban daina kuka ba, Mami da Momi suna ƙwalla amma na farinciki ne Baba Babba faɗi yake yi" Allah na gode maka da ka karɓi ɗan'uwana, sannan ka bar mini ɗana Ubangiji na gode maka."
Muryarsa ta karye mutuwar Baba ƙarami ta sake dawo mana sabuwa dama tana jika, ba ta gama fita ba, kuma har abada ba za ta fita ba, ba za mu manta ba, don da yanzu ina tunano abubuwan da suka faru amma ina jin kamar a yau ne muka rasa Baba ƙarami. Mutuwa tana da d'açi, sannan mutuwa mai tonon asiri mutuwar Baba ƙarami ce ta yi sillar ta tarwatsewar gidanmu, kaina na saka a cikin tafukan hannayena duka biyu na sake fashe wa da kuka ina jin wani irin nauyi a samam k'irjin irin nauyin da na riƙa ji lokacin da gidanmu ya hirgitse, Ubangiji na ke fata da roƙo ya daidaita kan ahalina

Na cigaba da hakaito rayuwarmu washegari muka koma gidajenmu cikin sukuni da salama, sannan yanzu muna mgana da su sosai, barin ma Yaya Faruƙu yana yawan kirana saboda har gobe Yaya Faruƙu nawa ne, ina girmama karamcinsa a gare ni. Abida ma muna waya sosai sannan Yaya Sulaiman ma suna haɗa mu da shi, kuma jikinsa sai godiya yana ta samun sauƙi.
Ya Asad sati ɗaya ya yi ya juyo zuwa gida Nigeria. Abida da Yaya Faruƙu za su cigaba da zama tare da shi har sai an sallame shi, Abida ko an ce ta dawo ba za ta yarda ta dawo ba. Baba Babba ya ce a barta ta zauna ta samu ladan jinyar mijinta, ban ɗauka haka Abida ke son Yayana ba sai a wannan lokacin aikin ta ta ajiye ta ta tafi jinyar Yaya Sulaiman kuma da aknsa ya faɗa mini da jikinta da zuciyarta take wahala da shi, kusan ita ke yi masa komai sai na ji tausayinta ya kama ni, shi da man Yaya Faruƙu Ladi farm ne kuma ba matsala akwai masu kula da wajen shi ya sa ba shi da wata matsala.
Gabaɗayanmu mun koma bakin aikinmu tunda hankula sun kwanta ni kuma a gida na cigaba da karɓan aikin snacks sannan a bangaren aikina na W.H.O, mun cigaba da wayar waa da mata kai wajen kula da cikin da raino da kuma muhimmancin yin rigakafi ga yara bayan haihuwa.

Ba tare da shawara da kowa ba Baba Baaba ya fara tattara dukkan wata dukiyarsu shi da ɗan'uwansa idan a baya ba wanda ya san shiga da fitar dukiyarsu, yanzu mutuwa za ta yi sillar fallasar komai. Idan a baya dukiyarsu tana haɗe ne a waje ɗaya ba wanda yasan tsakaninsu yanzu dalilin mutuwa yasa dole komai ya bayyana, ya shiga har bangarenmu ya yi magana da Mami da Ansari tun da Yaya Sulaiman baya kusa.
Ya ce 'an fara tattara dukan abin da Baba ƙarami ya mutu ya bari idan an gama tattarawa lokacin su Yaya Sulaiman sun dawo za a zauna a raba gado domin a sauke masa nauyi, wannan maganar rabon gado, wannan gadon shine silar dambarwan da ta faru a gidanmu dambarwar da ta yi silar da na rasa Abida na rasa Ya Munnera.

Bansan da mganar ba Mami ta kira ni da kanta a waya tana faɗa mini abin da yake faruwa.
Sai na ji hawaye ya goce mini, yanzu shike nan mun rasa Baba ƙarami, har ga shi ana mganar rabon gado Allah sarki rayuwa Allah ya kyautata makwancinsa ranar yini na yi kamar marar lafiya. Baban Amrah yana can bangaren Hajiyarsu sai da ya shigo ne ya ganni zaune a falo na shiga zurfin tunani ban san ya shigo ba sai da na ji hannunsa a saman kafaɗata sannan na dawo hayyacina.

"Lafiyarki kuwa?

Ya faɗa yana kallona cikin kulawa, na sauke ajiyar zuciya idanuwana suka kawo ƙwallah, gidan da ma ya yi mini shuru yara sun tafi islamiya, Basma ce ta ce mini za ta shigo to ta kira ni ta ce ta fasa zuwa Baban Abdul ya yi baƙi sai dai zuwa gobe.
"Na sha faɗa miki ki daina zurfafawa kanki tunani. So kike na rasa ki na shiga uku?
Kalamansa na ƙarshe yasa sai da na yi dariya, kusa da ni ya zauna ya ɗan rumgumo ni da sigan lallashi yana ɗan buga bayana.

"Komai mai wuce wa ne, Allah ya jiƙan Baba,. Shi kuma Yaya Sulaiman da ikon Allah sun kusa dawowa"
Na gyaɗa masa kai cikin gamsuwa domin na yi lamo a jikinsa na kuma karɓi lallashinsa, ban san me yasa ba sai gani ina bashi labarin wayar mu da Mami, ina ƙoƙarin mai da hawayen da suka cika mini ƙwarmin idanuwana, amma ga mamakina sai da ya ɗago ni cikin nuna murnarsa kamar na ba shi labarin wani abin daɗi.
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: "Ma sha Allah."
Ya faɗa yana kallona, na yi kasaƙe ina kallon sa, faɗa masa fa na ke yi mutuwar mahaifina ta dawo mini sabuwa saboda an yi maganar rabon gado, amma yana kallona da farinciki a muryansa har ya bayyana a saman fuskarsa.

"Gaskiya Baba Babba ya yi tunani kuma ya cika ɗanuwa na gari, gwara a raba a bawa kowa haƙƙinsa haka addini ya tanadar"
Ni dai har ya gama magana ya tashi, ban sake wani motsi ba me ya sa yake murna? Saboda na ce za a raba mana gado, a kullum al'amuran Baban Amrah mamaki yake ba ni, ba ya gyarawa kuskuransa sai ma ƙoƙarin sake wasu yake yi, ajiyar zuciya na sauke amma abin da ya yi ya tsaya mini cak a zuciyata sai dai ban iya faɗa wa kowa ba sai washegari da Maman Abdul ta zo, ban yi mata wata magana ba, saboda na
san ko na faɗa mata sharhi da magana kawai zan jawowa kaina ita da Abida har gobe ba sa iya boye adawarsu akan Baban Amrah shi yasa na yi shuru da bakina amma dai na ji daɗin zuwan ta mun yini tare muna hira kuma ta saka ni na saki jikina har na manta damuwata.
Tun daga lokacin da na yi ma Baban Amrah maganar rabon gado ya dame ni bini-bini sai ya tambaye ni wai ya ake ciki ne har yanzu ba a kiramu ba? Tun ina mamakinsa har na daina na gama fahimtarsa kuɗin kawai yake hange, tun da ranar ma muna karyawa a gaban yara yake ce mini." Kai gaskiya za ku sha kuɗi Balki, ko gidan gonar nan kaɗai ai sai ta yi miliyan dubu da doriya."
Kawai sai na saki baki ina kallonsa, au shi da man ya kwanta ne da gidan gona yana lissafin zan samu kuɗi ya sake komawa ya naɗe hannu ni kuma na sakin masa kuɗi ina masa hidima shi da ƴaƴansa da iyayensa, tun da na riga na sabar masa, a lokacin ban ba shi amsa ba sai da ya sake yi mini zancen kai tsaye na faɗa masa gaskiya.
"Gidan gonar da kake mgana ba ta Baba ƙarami ba ce shi kaɗai, duka dukiyar tare ne da na Baba Babba. Ko mu y'ayansu bamu san yadda dukiyar su take ba."
Tun daga nan na kashe masa baki amma duk da haka bai daina tambayata har yanzu Baba Babba bai kiramu ba?Ranar da daddare har mun kwanta ya sake yi mini mganar na harzuƙa na miƙe ina faɗin" Bai kiramu ba, don Allah Baban Amrah ka ƙyaleni da wannan maganar. Mu fa ba gado ba ne a gabanmu mutuwar mahaifinmu ta fi yi mana ɗaci, sannan lafiyar Yaya Sulaiman ta fi damunmu fiye da tunanin wani gado."
Ganin na buɗe masa wuta ina masifa sai ya yi ƙasa da murya yana faɗin" Sorry ni ma ai mutuwar tafi damuna amma ina so na ga an sauke ma Baba ƙarami nauyi, ai Allah ne ya ce a raba ko Bilkis? Kuma ke matata ce duk abin da ya shafe ki ai ya shafe ni."
Saboda haushinsa da ya kama ni ko magana ban yi masa ba na koma na kwanta na juya baya ya san ya yi laifi shi ya sa ya mirgino ta gefena yana kiran sunana, ta gefen kunina da dama yana yi mini raɗa, da ya ke ya iya kalamai sanyaya zuciya Idan ya so, tuni ya shawo kaina da azama muka tallafi juna sai dai kamar ko yaushe bai wani daɗe ba, ya matsa gefe ya fara barci ni kuma ya bar ni kwance cikin hawaye, na daɗe ina kallon shi ina tunanin wai haka sauran maza suke? Ba su damu da damuwar matansu ba sai kan su? Ban gane komai ba amma ba ni da yadda zan yi haka na ja jikina na shiga tiolet na yi wanka na tsarkake jikina na zo na sauya rigar barci na raɓe ta gefensa na kwanta ina tunanin makomar rayuwata, shike nan ni a haka zan ƙare, ba zan iya ɗorar da komai akan jin daɗin aure ba, a wajen ana mini kallon mace a cikin sahun matan da suka yi dacen samun gwarzon miji, kyakkwa Kuma marar hayaniys, ni kuma a cikin gida ni kaɗai na san inda ɗakina yake yi mini yoyo, na daɗe kafin barci ya kwashe ni cikin tunani da zullumi.
Tun da muka yi haka da Baban Amrah ya kiyaye ni da maganar rabon gado, nima jin Mami ba ta sake yi mini maganar ba, sai na cire abin a raina sai kwanaki biyu tsakani Ansari ya kira ni a waya yana faɗa mini wai Baba Babba shiru har yanzu bai ce komai ba? Takaici ya kama ni amma sanin da na yi Ansari da Mami bakinsu ɗaya
[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Lokacin da Upper ɗin ta fito da kansa ya shirya ya zo gidana, na yi mamakin ganinsa amma sai murna ya danne mammakina, na yi ta rawar jiki da shi, na rasa ina zan saka shi na ji daɗi, ga shi yara ba sa gida baban Amra ma baya nan ya shiga cikin gari. Na share hawaye a ɓoye saboda shi kadai ya ke damuwa da lamarina a yanzu. Ya Hamida da gaske take ta yanke alak'a da ni, ba ta k:irana ko na k'ira ta sai ta ga dama take ɗauka. Su Saddiqa ba kasafai muke mgana da su ba, Duk ta zuge su. Ya Sulaiman ɗin ne kaɗai na ke gani na ji daɗi, lokacin da ya damƙa mini upper ɗina ta aiki bansan ya aka yi narumgume shi ina fashewa da kukan dan nake ta danne shi ba. Murna da tausayin kaina suka dabaibaye ni. Ina kuka ina faɗin" Na gode sosai Ya Sulaiman, na gode Ubangiji ya yiwa rayuwarka albarka, ya tsare ka ya sanya albarka a dukiyaka da ya'yanmu, Allah ya jiƙan iyayenmu."

Ya amsa da Amin kafin ya ce" Ba komai Bilkina ni dai fatana ki nutsu, ki yi haƙuri, ki rungumi mijinki da ƴaƴan ki, ki koyi juriya da yadda za ki iya tsayawa kanki ko da ba ki kowa a duniyar to ya zama kina da Allah kina da kanki!
Sai na ji maganganunsa masu kama da yana barin wasiyya ne.
Hankalina ya tashi kar ya zo shima mu rasa shi kamar yadda muka rasa Mami da Baba ƙarami.

"Yayw Sulaiman waɗanan mganganun fa? Ina za ka je?"
Na faɗa cikin damuwa da tashin hankali
Sai ya yi saurin ce wa" Ba komai Bilkina, wata yar tafiya zan yi amma kar ki tayar da hankalinki, idan da rabo za mu sake haɗuwa."
In jin ya ce haka na fara kuka ina faɗin" Na shiga uku Ya Sulaiman kai ma barinmu za ka yi! Don Allah kar ka tafi ka bar ni."
Hannayena ya riƙe cikin nasa kafin ya ce" Na ce ki kwantar da hankalinki ba zan daɗe ba, zan dawo, ke dai kawai ki koyi dauriya da jarumta, komai zai wuce, kina da ƴaƴa da mijin da wata rana za su iya zama garkuwa gare ki"

Duk yadda na so Ya Sulaiman ya faɗa mini k'udurinsa bai yi ba, ban dauka ganin k'arshe na yi masa idan a ce na san haka da ko za a mutu bazan bari ya bar gidan nan ba. Ganin yadda nake ta kuka yasa ya ɓata lokaci wajen lallashina har sai da ya ga hankalina ya kwanta.
Har abinci sai da na yi masa kuma ya ci mun d'ade muna hira yana ta mini nasihohi yana ce mini na kula da rayuwa, na kuma saka ido sosai akan yara. Ni kam na gama tsorata da jawabansa ya yi mini fatan alheri da fatan nasara sannan ya ce zai tafi.
Na ce ya ɗan jira su Farha sun kusa dawowa.
Ya kalleni kafin ya ce" Farha kaɗai sauran yaran fa?
Na yi shuru ban yi mgana ba.
Ya numfasa ya ce "Ki daina danganta Farha da ni Bilkina, d'aya take da su Amra a wajena, ba tawa bace ta kice tun kafin ta zo duniya kowa ya tabbatar da cewa Farha taki ce don kuwa na fi Abida cancantar na ba ki ita".
Na ba shi haƙuri ganin ransa ya ɓaci sai da na tabbatar da ya hakura sannan na sakoasa batun Abida tare da fatan ya dauke ta Su tafi inda zashi don na tabbatar hakane kadai zaisa hankalinsa ya nutsu. Ya girgiza kai ya ce "Bilkina ban saki Abida ba, amma matukar sai na nemi ta dawo gare ni

4 / 7