💖💖RAYUWAR MU💖💖
_Written by ✍️ _
*Jagaban Jajirtattu*
_(Ta Batulu)_
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
*(J.W.A)*
_Wannan shine Whatsapp group ɗin da zaku samu cigaban wannan labarin. Ku taya ni shering Please👇._
https://chat.whatsapp.com/LSKW0PJdQ6Z2S2wltDG6oT
(Tafiyar ƙaddara kamar tafiyar ajali take, duk inda ka kai gurin guje mata sai ta risƙe ka. Komai na duniya yana da lokaci kuma yana da iyaka, Rabbi ka yi daɗin salati ga shugaban kowa da komai, manzon tsira manzon Rahama Annabi Muhammad s a w.)
*Bismilahi rahamanun Rahim.*
*Page 1-2*
Wata matashiyar budurwa ce sanye da uniform ɗin makaranta blue black sai farin hijjabi wanda ya wuce guiwa tafe take ta na ran gaji.
Kana ganin uniform ɗin ka san na islamiyya ne ba za ta wuce 20 yrs ba duk da uniform ɗin sun koɗe amman babu datti ko kaɗan ajikin shi.
Ta na tafe ta na ya mutsa fuska da dukkanin alamu akwai gajiya a jikinta.
A bakin wani ƙaramin gida mai dakali guda biyu ta tsaya.
Ta yi kusan 9 minutes a zaune a kan ɗaya daga cikin dakalin kafin ta shiga gidan bakin ta ɗauke da sallama.
Wata mata ne zaune a kan kujera a ƙofar wani ɗaki daga gani ɗakinta ne ta amsa sallamar ta ce.
"Shukrah har an dawo?"
Wannan matashiyar da aka kira da shukrah ta ce.
"Eh na dawo Umma sannu da gida"
Shukrah ta ƙarema ummanta kallo a ƙalla za tai 40 years amman ya na yin rayuwa yasa ta zama kamar mai shekara 40 da wani abu.
Kana ganin gidan ka san a kwai ya nayin rayuwa ɗakuna uku ne a gidan sai ban ɗaki a ƙarshen gidan.
Kana shigowa a kwai ɗakin farko ɗakin babansu Shukrah.
Daga ɓarayin dama kuma ɗakin umman Shukrah sai ta ɓangaren hagu ɗakin amaryan Abba.
Sai kitchen kusa da ɗakin baban su Shukrah.
Umma ta na ta magana Shukrah ba ta ce komai ba.
Umma ta tashi ta riƙo Shukrah ta ce.
" Ki rage ma kanki wannan tinanin bai da amfani"
Shukrah ba ta ce komai ba ta shiga ɗakin su ciki da parlour ne
parlourn ya na da faɗi ba laifi Amman kujeru biyu ne kawai a parlourn mai zaman mutum biyu.
Sai mai zaman mutum uku masu ruwan toka duk ya ji jiki amman tsaff suke babu datti.
Sai carpet shima mai ruwan toka da ratsin baƙi shima duk ya koɗe amman babu datti a jikinshi.
Akan kujera Shukrah ta zauna ta jingina bayanta ta lumshe danun ta kamar tana bacci.
Ba ta jima ba ta ji hayaniya na tashi a waje ta shige cikin bedroom ta na tsaki.
Ta na shiga sai ga wasu mata san ƴan mata sun shigo da sallama mata ne su biyu sai namiji ɗaya.
Su kaiwa Umma sannu da gida Umma ta amsa tana cewa "Har kun dawo?"
Suka amsa da
"Eh Umma mun je bata nan sai da muka jira ta"
Umma ta kali ƙaramin yaron ta ce.
"Mudan na ga ka yi shiru hala sun gajiyar mun da kai?"
Mudan ya rausayar da kai ya ce.
"Ehh wallahi Umma Aunty Darraini sai jana take yi"
A cikin ƴan matan da suka shigo wacce tafi girma a cikin su.
Ta taso zata dake shi ta na cewa tinda sharri zai mata.
Umma ta tare ta na faɗin ba zata dukar mata autan ta ba ai gaskiya ya faɗa.
Mudan ya kalli Darraini ya yi mata gwalo Darraini ta yi ƙwafa ba ta ce komai ba.
Umma ta kalli ɗayar yarinyar da tinda suka shigo ba ta ce komai ba ta ce.
"Manaheer lafiya ki kai shiru ba ki ce komai ba?"
Wanda aka kira da Manaheer sai ta zumɓuro baki ta ce.
"Umma ni da nake jin yunwa Ina naga bakin surutu"
Umma ta kalli Auta ta ce.
"Autan maman shi ka naj in yunwa?"
Mudan ya ce.
*Eh mana ummana ji nake kamar banda hanji"
Yana faɗin hakan suka kwashe mai da dariya.
Darraini ta kalli Umma ta ce.
"Umma har yanzu Yaya bata dawo da ga islamiyar ba?"
Umma ta ce.
"Ta dawo tana ɗaki"
Suna jin hakan suma suka shiga ciki bakinsu ɗauke da sallama .
Basu ganta a parlour ba sai suka shiga cikin bedroom su na shiga suka ganta ta kwanta rigingine fuskanta na kallon rufin ɗaki,
Idonta biyu Manaheer ta na ta magana shiru da alama tayi nisa domin tunda suka shigo bata motsa ba.
Ganin hakan sai Darraini ta je ta taɓa ta ta na taɓa ta tayi ajiyar zuciya.
Duk suka mai da idanun su kanta Shukrah ta kalli ƙanin na ta guda biyu ta kau da kai.
Ganin ba tace musu komai ba sai suka sata a tsakiya suka kewaye ta.
Ganin hakan sai Shukrah ta tashi ta zauna ta na ƙare musu kallo ba tare da ta ce musu komai ba.
Suna da sanin cewa in zasu kwana a hakan Shukrah ba za ta ce musu komai ba.
Darraini ta ce.
"Aunty Shukrah mai ke damunki ko baki da lafiya lafiya ne?"
Ita kuma Manaheer ta yi shiru tasa musu ido
ta na jiran ta ji abin da Shukrah za ta ce duk da ta san abune mai wahala ta faɗa musu damuwarta.
Babu zato ta ji muryar Shukrah na faɗin yanzu haka zamu cigaba da rayuwa kullum jiya iyau babu wani cigaba a rayuwar mu?"
Dukansu sun gane mai take nufi suka kasa bata amsa ta kalli Manaheer ta ce.
"Tunda muka taso muke shan wahalar rayuwa har yanxu bamu san wani abu wai shi farin ciki ba.
Ku duba ku gani yanda Umma take wahala akan mu kullum burinta ya za ayi mu koma school amman hakan yaƙi samuwa"
Itace cin mu da shan mu itace sutturan mu itace maganin mu komai itace kuma kuna ganin babu wani sana'ar da ta ke yi kullum faɗi tashi ta keyi a kan mu"
Ta na gama faɗin hakan kuka yaci ƙarfinta.
Suka haɗe suna ta kuka sunyi 20 minutes suna kuka kawai ji su kayi an dafa su.
Suna ɗagowa suka ga Umma tsaye a kansu ta na ƙare musu kallo ta ce.
"Nayi ta magana a fito ai sallah na ji shiru sai na shigo in ga abinda ya hana ku jin kiran sallah ashe kuna nan kuna aikin da kuka sa bayi"
Umma taci gaba da cewa "Da a ce kuka na maganin damuwa da tini baku da sauran damuwa a duniya"
"Ku tashi kuje ku fuskanci ubangiji shiɗin maji roƙon bawa ne kuma duk duniya shi kaɗai zai iya yaye muku damuwarku,
Ta na gama faɗa musu hakan ta shiga ciki ta ɗau darduma ta fita ta basu guri.
Ita kanta ƙarfin hali tayi ta rike kanta domin tunda suka fara magana take tsaye a kansu tazo tai musu magana a kan suzo su naimo abinda za suci sai taji suna wannan zancen.
Ita kanta haƙuri take da mahaifinsu ta na da gata da komai amman ta zaɓi zama dashi ko dan ƴaƴanta.
Basu motsa ba daga in da suke har sai da Auta ya shigo ya ce
"Umma ta na kira"
Sannan suka tashi kowannensu jiki a san yaye suka fita parlour suka sameta a saman darduma ta na jan casbih.
Da ido kawai ta kallesu kowa ya yi waje yaɗau buta Shukrah ta shiga toilet ta fito Darraini ta shiga ta na fitowa.
Manaheer ta tashi zata shiga har ta kai ƙofar toilet ta ji an bangajeta sai da ta faɗi ƙasa aka rufe ƙofar toilet ɗin da ƙarfi Manaheer tayi saurin janye ƙafarta.
Darraini na ganin hakan tai sauri taje ta faɗawa umma domin ta san halin Manaheer ba ta yafiya idan ka ta ɓata.
Ta na zuwa taga Umma na sallah sai ta tsaya tana jiran ta idar da sallahn.
Ita kuma Shukrah taje ta ɗaga manaheer ta ce.
"Idan kika ƙyale wannan yarinyar keba jinin umman mu bane"
Ta na gama faɗa mata hakan ta tashi ta shiga ɗaki tana leƙen Umma domin ta ga abin da take yi.
Ta na leƙawa taga Umma sallah take Darraini na gefenta a zaune.
Shukrah tai hamdala ta koma tsakar gida ta sa kujera ta zauna tana kallon Manaheer da ta kasa magana kawai toilet ɗinsu take kallo idanunta sunyi jajir kamar wanda aka zuba ma yaji.
Ita dai shukrah ta na ta kallon Manaheer domin ta san idan ta kama na cikin bayin nan sai allah.
Manaheer duk ta fisu jiki kuma tafi su cika.
Ƙaran buɗe toilet ne ya dawo da shukrah cikin tunanin da ta fara.
Allah allah take ta fito daga toilet ta ga abin da zai faru.
Bata gama tinanin da take ba ta ji wani gigitaccen ƙara sai da gidan ya amsa ta na kallon Manaheer taga abin da tayi sai da ta zaro ido ta miƙe tsaye.
Mimah ne a kwance a ƙasa Manaheer na dukan ta. Shukrah ta ce.
"Yauwa sister baki daki bakin rashin kunyar ba"
Ai Manaheer najin hakan kamar an ƙara mata ƙarfi ta dinga jibgan Mimah.
Jin ihun ya yi yawa ne yasa Umma fitowa jiki na rawa Darraini da gyangyaɗi ya fara ka mata itama ta yi waje da gudu,
Ganin abin da ke faruwa suke kamar a film duk da sun san Manaheer bata da haƙuri amman basu taɓa tunanin za tai ma Mimah wannan dukan ba.
Ganin Umma ta fito yasa Shukrah ɗaga murya ta ce.
"Sister bugun ƙarshe ga Umma nan"
Ai ko Manaheer na jin hakan ta saɓi Mimah zata buga da ƙasa Umma ta yi mata tsawa ta ce.
" Mata kull kika aikata hakan sai ranki ya ɓaci"
Manaheer ta saki Mimah ta faɗi ƙasa kamar kayan wanki ta saki wani marayan kuka.
Umma ta kalli Shukrah ganin hakan sai Shukrah tai huf ta faɗa ɗaki.
Umma ta ce.
"Manaheer tazo ta huce ɗaki"
Ba tai alwalan ba.
Cewar Darraini Umma ta kaɗa kai ta ce.
"Yi alwalan mu wuce ɗaki"
Manaheer ta tsallake Mimah dake yashe a ƙasa tana ta gunjin kuka ta shige toilet ta bugo ƙofa saura kaɗan ta bige ƙafar Mimah
Umma ta kama Mimah ta miƙar da ita ta na kakkaɓe mata ka yanta da yasha ƙura.
Umma ta ce,
"Kiya haƙuri Mimah dan allah"
Mimah ba tace mata komai ba ta fisge jikinta ta shige ɗakin su,
Darraini ta yi dariya ta ɗaga murya ta ce.
"Amman fa Mimah sai kin gasa bakinki da ruwan ɗumi"
Umma ta kalli Darraini ganin kallon da Umma take mata yasa tai wuf ta faɗa ɗaki tana ƙunshe dariya.
Ta na shiga ta samu Shukrah a saman darduma ta idar da sallah ta na jan casbih.
Darraini ta kalli Shukrah ta kwashe da dariya sister a na ta lazimi kenan Shukrah ba ta ce ma Darraini komai ba taci gaba da jan casbihn ta.
Suna cikin haka Umma ta shigo ita da Manaheer Umma na gaba Manaheer na baya.
Ganin Umma ta shigo yasa Darraini ta yi shiru Manaheer ta ɗauki hijjab ɗin Umma taje gefen Shukrah ta tayar da sallah.
Darraini na ganin hakan ta tashi da sauri ta fita taje ta ɗau buta ta sake sabon alwala.
Ta shiga ɗaki ta samu Umma zaune akan kujera Darraini na ganin Umma ta zauna sai ta kau da fuska kar Umma tai mata magana
Umma tayi kamar bata ganta ba.
Darraini ta matsa kusa da Shukrah ta ce.
"Sister ɗan matsamun in yi sallah."
Shukrah ta ɗago ta watsama Darraini harara sannan ta tashi.
Ta koma kusa da Umma ta zauna a ƙasa.
Umma ta kalli manaheer da ta idar da sallah.
Manaheer ta zo ta zauna kusa da Shukrah.
Umma tayi shiru ba ta ce komai ba.
Auta ya shigo da sallama suka amsa suka amsa mishi ya shigo ya kwanta a jikin Manaheer .
Umma ta kalli Auta ta ce.
"Daga Ina kake domin na san ba daga masallaci kake ba?"
"Bayan an idar da sallah banga Bashir a massallaci ba shine na je gidansu na duba shine na ga baida lafiya cewar Auta"
Umma najin hakan ta maida dubanta gun Darraini.
Ta na lura da ta idar da sallahn amman taƙi sallamewa Umma ta yi murmushi.
" Baki idar da sallahr bane?" cewar Umma ta na kallon Darraini.
Darraini bata ce komai ba ta zo ta zauna kusa da Manaheer.
Umma ta kalli Shukrah ta ce.
"Zan fara ta kanki saboda duk kinfi su laifi.
"Yanzu a matsayin ki na babba ya dace abin da ki kayi?"
Dukan su suka duƙar da kai ƙasa.
Umma taci gaba da cewa " Nayi tunanin ke mai tsawatarwa ne a garesu bamai sawa suyi ba"
"Idan kinga su nayin abin da bai dace ba sai ki tsawatar musu a matsayin ki na babba"
"Amman abun takaici kece mai sawa suyi kuma kece mai basu umarni"
"Kin bani kunya kuma kin bani mamaki wallahi Shukrah a kan hakan zan saɓa miki ba zaki barni da abin surutu ba ku bakwa gudun abun magana a rayuwarku?"
"Yanzu a kan abinda kuka aikata kun san abin da zai je ya dawo kuma kun san a kaina komai yake ƙarewa"
Maiyasa idan za kuyi abu bakwa tsayawa ku yi tinani maiyasa bakwa tausayin halin da muka tsinci kan mu aciki" Umma ta na magana muryanta cike da rauni?,
Manaheer ne tai ƙarfin halin cewa " Kiya haƙuri Umma in sha Allah ba za mu ƙaraba"
"Dan allah kiya haƙuri" cewar Darraini.
Auta ma ya ce.
"Umma sun ce kiya haƙuri ba zasu sake ba"
"Dan allah ki yafe mana ɓata miki ran da mu kayi in sha Allah allah hakan ba zai sake faruwa ba" cewar Shukrah fuskan ta ɗauke da hawaye.
Umma ta nu na ma kowa kuskurenshi kuma sun yi mata alƙawarin ba zasu sakeba,
Darraini ta kalli Umma ta ce.
"Nifa cikina yana ciwo"
Shukrah ta watsama Darraini harara.
Kije saman gado ta gefen pillow ɗina za kiga ɗari biyar ki ɗauko kije ki siyo garin kwaki da sugar cewar Umma.
Darraini ta je ta ɗauko ta zo zata fita Auta ya tashi ya bita suka fita tare.
Shukrah ta tashi ta je ta ɗauko bucket ta zuba ruwa ta shiga toilet ta watsa ta fito.
Ta buɗe wardrobe ɗin kayan su wardrobe ne mai ƙofa huɗu ta buɗe na farko ta ɗauko doguwar riga na yadi tasa.
Ta fito parlour tazo ta zauna kusa da Umma Manaheer ma taje ta watsa ruwan ta sanja kaya.
Umma na zaune da casbih a hannunta Auta ya shigo bayan ya yi sallama.
Ya zauna kusa da Umma
Ta Batulu ce ✍️
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LSKW0PJdQ6Z2S2wltDG6oT
RAYUWAR MU
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Written by
Jagaban Jajirtattu 🥰
(Ta Batulu)
*Page 3~4
Darraini ta yi sallama ta shigo hannunta riƙe da baƙar leda ta a'je ta fita sai ga ta da kwano mai ɗan faɗi.
Ta juye wannan garin a ciki ta ɗauka ta fita.
Ba ta jima ba ta dawo hannunta ɗauke da spoons ta zuba sugar ta sa spoon ɗin aciki ta zauna.
Duk abin da take Umma na zaune ta na kallonta.
Auta ya sauko ya zauna a ƙasa Manaheer ta zauna kusa dashi.
Darraini ta zauna kusa da Auta su kai bismillah suka fara sha.
Shukrah na hakimce a gefe ta na kallon su ko alamar tashi babu a tare da ita.
Umma ta kalli Shukrah ta ce.
"Hala kin ƙoshi ?"
Shukrah ta turo baki ni ba naci.
Gaya mun abin da kika ci tin da kika dawo?
Cewar Umma.
Shukrah tayi shiru Umma ta ce.
"Ki tashi ko kuma yanzu ranki ya ɓacci."
Shukrah ta tashi ta na turo baki ta je kusa da Darraini ta zauna.
Ta ɗau spoon dama saura ɗaya ne.
Ta naci ta na ya mutsa fuska spoon ɗaya tayi ta mayar dashi ta a'je.
Manaheer tayi waje bayan ta ɗau buta ba ta jima ba ta dawo ta zauna kusa da Umma.
Darraini ma ta tashi taje ta zauna kusa da Manaheer
Shukrah ta tashi ta ɗau buta tayi waje Umma tayi ƙwafa ta dawo da kallon ta kan Auta.
Ta ce
"Auta meke damun Bashir na ji kace bai da lafiya?"
Kafin Auta ya ba Umma amsa sukaji hayaniya na tashi a tsakar gida.
Umma ta ce.
"Allah ya kyauta"
Manaheer zata fita Umma ta hana tace su jirata ta je ta ji.
Umma ta fita Auta yabi bayanta.
Amaryan Abba ne Aisha take masifa.
Ta na zagin Shukrah dake zaune a tsakar gidan.
Ta na ganin Umma ta