[12/10, 8:46 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A* Yabo da godiya su tabbata ga Ubangijin talikai. Tsira da aminci su kara tabbata ga shugaba Annabi Muhammadu S.A.W. Wannan littafi ban yi shi don wani ko wata ba. Kama daga sunaye gari kamanceceniya. Idan an yi katari da hakan arashi ne. Ban yarda a yi amfani da labarin nan ta kowace irin siga ba, idan aka aikata hakan ba ni da masaniya Allah Ya saka mini. *SADAUKARWA NE GA:* *NANAH ABDUL* *TUKWUCI NE GA:* *SURAYYA DEE* ( Halin Yau) *GODIYA TA MUSSAMAN GA:* Momi Fatima Musa Hajiya Babbah Autar manya Halima wada kura Prof Asabe Kabir Halimatu Amarah Basira Hamza Usaina Ibrahim Zainab Yola Zainab Fadima Sani Hairi Sakina Jumpum Rauda Abubakar Zainab Salisu Umar Ummi Labaran Maman Rahama Ummu Ulfat Rabbatul-Bait Rajkumari Maman Janan Fatima Gwaram Asiya Mu'azu. *KANO STATE* *UNGUWAR KURAWA* *Shimfid'a* 1&2 "Kyauta kina ina? fito nan, wallahi yau a gaban kowa za'a yi ta ta k'are na gaji da wannan halin na ki". Zuciyata ta harba tare da zullumin yau kuma mai aka shiryo mini ni Ummu Kulsumu" Na fita ina hirji. Gabadaya matan gidan suna tsaye sun yi cirko cirko tamkar zakaru. Ya kausasa harshe yana cewa "Kyauta wana d'amkawa ragamar kulawa da sito din abinci?" Murya babu amo na ce ni ce amma me ya fa..... Ya daga hannu a zafafe yana cewa " Sa aya kawai malama, ta ya ya za'a ce mini babu man gyad'a da indomi a gidan nan?" Zuciyata ta buga da tsananin gaske. Domin ni kaina na ka'du da furucinsa. Idan lissafina daidai ne to kuwa yau kwanaki goma kacal da bude jarkar mai 25 Lita. Taliyar yara kuwa yau kwanaki uku da ya shigo da katon biyu. Sau daya kacal na dafa domin kuwa su ban ga sun dafa ba ma. Amma ace yau babu. Lallai dole ya yi fad'a ban ga laifinsa ba a yanda rayuwar nan ta yi tsanani. A sanyaye na ce "Allah ya huci zuciyarka Yaya amma wallahi ban san komai ba akan wannan sha'anin. Kuma Dole idan iyalai suka yi yawa sai an yi hak'uri saboda hidima tana k'aruwa za'a gyara In sha Allah" Ya ja tsaki ya ce "Kina nufin dole na yi hakuri na zuba ido kina neman yi mini sanadin shiga ba'kin talauci? Nawa ake siyar da kwalbar mai ne bare jarka? wato bak'in cikin da ake cewa kina yi ne yake neman fitowa muraran ko?" Nan da nan zuciyata ta karye hawaye ya cika idona murya na rawa na ce "Yaya da bakinka kake jifana da yi maka bak'in ciki a cikin gidanka?" Maimakon ya sassauta sai kuwa ya sake fusata ya ce "Ba iya bakina kad'ai nake magana ba, har da zuciyata. Domin mugunta da bak'in ciki ya sanya kike kwashe mini kayan abinci". Kuka ya ke ce mini. Na kasa cewa uffan domin zuciyata ta yi nauyi ainun! To na kwashe kayan abinci na kai su ina? Ya ja tsaki ya ce "Kukan ki ya k'are Kulsumu je ki dauko mini mukullin sito din hannun ki. Na yi iyakacin kokarina akan na baki girmanki amma abin ya faskara dan haka idan girkinki ya zo sai ki karba a hannun Nadiya." Kafin na yi magana. Nafisa ta yi fit ta ce "Ai kuwa idan kana nufin ita zaka bawa mukullin sai dai a raba girki amma tabbas ban yarda da alwalarta ba bare ta ja mu jam'i." Aliya da ita ce amarya ta ce "Ai kuwa dai ni ma ban yarda ba. Kukana ya tsaya cak. A dalilin na fahimci dukkansu sun had'a kai ne dan su kai ni k'asa. amma kuma da za'a shugabantar da wata a cikinsu ba ni ba, to zasu koma rikici da junansu. Na yi k'asa da kaina. Ina jin sauki da jarumta na ratsa ni. Wato duk da ni kad'aice ban haihu ba a gidan ba ni da ko kaza amma na dame su, na yi musu karantsaye a zukatansu. Duk wadda ta kwaso makircinta a kaina zata sauke shi. Abin da yake d'aure mini kai shine; ba ga ni suka yi yana fifita ni ko yana tausaya mini ba. Asalima wani cin kashin suna yi mini ne dan sun ga yana yi mini kai tsaye babu d'ar. Nafisa ce kawai take sassauta mini tare da mutuntanta ni itama kuma akwai dalilin hakan ba wai tana yi ne dan na kai ta yi mini ba. ta yi ne saboda yadda nake cire Ido akan yaranta mussaman hajjaju dukda yarinyar bata mutuntani na kan saya mata kayan ado da kwalliya ganin ta fara girma idan na fita duk abinda na gani na mata sai na sayo mata, wannan dalilin ne kadai ya sa take daga mini kafa, amma duk lokacin da ta so rashin mutuncinta mancewa take yi da komai Nafisa fitinnaniya ce sosai domin duk rabin rigimar da take faruwa a gidan itace take haddasawa dan dai kawai maigidan a tsaye yake shiyasa take shakkarsa. Maganarsa ta katse mini tunanin. Domin a kausase ya ce "Nafisa ki yi duk abin da kike ganin zaki yi, ita zan bawa idan kuwa kin ga ba zaki bi hakan ba kina iya tafiya ai ba daure ki na yi ba." Yana rufe baki ta fashe da kuka ta ce "Akan me zaka dinga nuna banbanci tunda ka bawa Kulsum ka ga bata yi maka yadda kake so ba, ai yanzu ni ce nake bin ta, ba sai ka ba ni ba, amma ka tsallake ni ka tafi kan wadda ta zo daga baya dan kawai ita kana jin tsoronta, saboda babanta maigidanka ne!. Ya harzuka ainun ya ce "Ki tsarkake bakin ki Nafisa domin wallahi zaki koma gida, kin san na ce miki ba zan sake daukar iyashegen ki ba. Tabbas ba ki yi karya ba ubanta maigidana ne kamar yadda nake maigidan yayunki guda biyu." Ta sake rushewa da kuka fiye da na farko. Nadiya ta zabgata mata harara tana cije bakinta ta ce." Nafisa ki iya bakinki fa kada mu kwashi 'yan kallo a wurin nan, wace irin magance wannan ko ubana abokin wasanki ne?" Ya daka musu tsawa Yana gyara zaman babbar rigar jikansa Ya ce." Ku ka kuskura ku kayi cacar baki a gabana ba zamu wanye lafiya ba." Sai kowacce ta yi shiru. Ni dai Allah Allah nake yi ya sallame ni na koma dakina. Ko kad'an ban ji ciwon karbe mukullin rumbun abinci da ya yi a hannun ba. Asalima sauki zan samu tare da addu'ar y'ar manuniya ta nuna kanta. Ya Kalli Aliya ya ce." Saboda Nafisa ta ce ba ta yarda ba ke ma ba ki yarda ba ko? To zan ga wanda zai rusa mini tsarin gidana a cikinku." Ya ja tsaki ya wuce yana banbamin bacin rai. Wanda har cikin zuciyata nima na ji takaicin yadda aka kwashe kayan abincin. Ina matukar kaduwa da bak'ak'en taadodin da matan yau suke aikatawa da sunan kishi. Ban da haka ka samu mijin da zai ajiye maka abinci ka diba babu fargabar awo amma sabida son sai an yi makirci da mugunta sai a kwashe dan kawai ana son a kai wata k'asa. Sannan ban da abinsu ni da suke yiwa wannan makircin dan kawai suna kallon bani mukullin wata alfarma ce, bakina ne kad'ai, su kuwa fa? Nafisa da ita ce amaryar da ya fara yi mini yaranta hudu a yanzu. Babbar shekrarta sha hudu. Wacce sunan mahaifiyarsa ta ci muna kiranta Hajjaju. Sai mai biye mata sunan uwar Nafin ce Aisha sai muke kiranta da Walida. Tun kuma daga lokacin gwamnatin Nafi ta fara sanyi a wajensa a dalilin ba mata yake so a haifa masa ba. Ni ban haihu ba, sanadin haka ne k'arin auren. Ya samu haihuwar kuma sai kuma jinsin da ake haifa masa basu yafi so ba. Dan Adam da butulci da izgili yake. Ni da zan bada komai dana mallaka na haifi macen da na yi. A dalilin haka ya auro Nadiya wacce y'ar maigidansa ne. Nadiya kyakkwar yarinya ce ta gaske. Sannan tana zuwa ta haifo masa namijin da yake muradi. Shekararta bakwai yanzu a gidan yaranta hudu duk maza. Yayin da Nafisa ma ta sake haifar namiji Khalid a huzaifa yaranta hudu kenan biyu maza biyu mata Ga Nadiya da take da Baffa sunan mahaifinta, Sadik, Umar Usman. Wadannan dalilan ya sanya da wahala ya yiwa Nadiya wulakanci a gaban jama'a sai dai ko a dakinta tunda ta sha yin yaji ana dawo da ita. Amma dai yadda ake ga ni tafi mu kyallin goshin a wajensa. Y'ar babban gida kuma uwar mazaje reras. Sai Amarya Aliya da take da yara biyu Aliyu da mai sunana Ummu Kulsum. Tamkar kazar da k'wai ya fashewa haka na ja sayyadata zuwa dakina. Na fadi tamkar wadda aka ingiza ni kan kujerar falon. Tsawon lokaci na zama mutum mutumi. Ba abin da nake yi sai nazarin rayuwa. Wai menene riba ne idan mace ta sace kayan abinci sannan ta kitsawa miji da mutanan gidan watabce daban ba ita ba? A da na dauka sai tsofaffin mata ne suke irin wannan makircin ashe yaran mata ma sun iya shirya kaidi. Ko da yake ai ance kowacce mace da irin nata makircin. Hawaye ya balle mini a dalilin yadda kullum zaman gidan yake sake tsananta mini. Shi ya yi, matansa su yi, haka yaransa su yi mini. A yadda nake gani barin gidan shine yafi alheri a gare ni, tunda Wanda ya ajiye ni ba wani muhimmancina yake ga ni ba. Yana gigicewa ne idan ya kuntuka mini takaici na gudu gidanmu hankalinsa yana tashi ya dinga tura jama'a har sai an dawo da ni. Mafi yawa dangina da makusantana gani suke yi hak'urina ne ya yi karanci a dalilin ban samu haihuwa ba. Amma ai ko dakina aka shigo aka yadda yake a shirye da kayan alatu an san yana sona. Ni Kuma ni nasan me nake fuskanta a hannunsa. Ba abu mai wahala ba ne ya yi mini tijara akan y'aya'nsa tunda shi mutum ne mara kawaici da rashin ha'kuri. Yanzu duk rashin kunyar da Hajajju take yi mini da zan d'an bugeta sai kowa ya ji bare kuma ace Baffah ne shalele. Shi wannan da a ta'ba shi a gidan gwara an yi ya'ki, domin ko Uwarsa ce ta yi masa hukunci muddin Yana gidan suna kwasar 'yan kallo. Kuma nan da can ba ya aikuwa hatta na uwarsa ma baya zuwa shiyasa bana damuwa. Walida ce Allah ya had'a jinina da ita. Duk yadda uwarsu take hanasu zuwa wajena sai ta faki ido ta zo mini. Ni kuwa bana gajiya da mika mata komai nake da shi mussaman da yake Ina sana'ar kayan Kwalam da makulashe. Domin ina yin albushir na bayar akan sari, ina yin iloka a biyani lada, ina yin kuma ta siyarwa, sai dai ni da yawa nake yi sai azo a sara na bi karamar riba na karbi kudina take. Sannu a hankali na k'ara da tuwon madara da y'ar kullisuwa. Dan haka kullum bana rabuwa da kayan dad'i a dakina. A dalilin hakan sai na yi y'aya' da yawa. Ko na gidan basu zo ba, to kuwa na makwabta yini suke suna yi mini sintiri. Domin duk sadda zasu tafi islamiya sai sun shigo sun karbi alawar madara ko albishir. Hakan ta sake jawo mini iyayensu. Dan haka ban saka rashin haihuwa a raina ba domin na yi imani ba itace karshen niima ba. A duk sadda aka guma mini azanci ko bak'in ciki akan yara. Bana zama na yi kuka domin idan na tuna Nana Aisha sai ta zame mini madubin da take wanke dukkan kumburin da zuciyata ke yi. Na riga na yi imani da haihuwa dole ce, ko kuma ita ce cikar niima kad'ai da Annabi ya rokawa Aisha tunda gabadaya malamai basu samu sabanin akan itace ta yi rinjaye a zuciyarsa ba. Hakan bai zame mata nakasa ba, sai ya zame mata kususiya ce mai girma a wajenta. Ta rungumi k'addara ta yi rayuwa cikin walwala, ta yi ilimi ta kuma yad'a shi wanda har zuwa yau ana cin moriyarsa. Dama amfanin d'a ai ya cigaba da ayyukan alheri da kake yi da kuma yi maka addu'a bayan ka kwanta dama. Idan hakan bata samu ba, sai musulunci addinin adalci ya ce Idan ka yi sa'a ka yiwa kanka sadaka mai gudana ko baka nan ladan zai bika har zuwa sadda abin zai katse. Bayan haka idan ka yiwa mutane adalci, ka kyautata musu, ka ja yara k'ananu da marayu a jikinka ka tallafa musu, Ubangiji kuwa ba zai barka ka koka idan tsufa ya zo maka a dalilin rashin y'aya'ba. Tabbas ne sai ya turo maka wadanda zasu yi maka abubuwan alfarma na kyautatawa tamkar y'aya'n da ka haifa ko ma fiye da hakan. Wadannan nasiha da tunatarwar da mahaifina yake yawan yi mini ya sanya na cire bacin rai akan rashin haihuwa, na rungumi y'aya'n gidan da na makwbta da na yan'uwana nake yi musu iya abin da zan iya tare da fatan Ubangiji ya karba. Na kuma gamsu domin babu damuwa ko kad'an a raina, kullum kuma k'ara samun jama'a nake yi a kusa da kuma nesa. Tunda ina da islamiyar yara da nake koyar musu a duk ranakun lahamis da juma'a a cikin gidan nake da kebebben waje dan gudanar da karatun kullum kuma makarantan cika take yi, tunda mafi yawa duk yaran da suke zuwa mini ne ma'ana ba makwabtaka. Ni kuma ina zuwa makarantar asabar da lahadi domin dai na cigaba da daukar ilimin addin da kuma yad'a shi a tsakanin al'umma. Wani abin mamaki a gidan namu ni kad'ai ce bani da kowa sai Allah sai miji. Amma na damesu rufin asirin da nake ciki ya zama abin tattaunawa. Makarantar da nake koyar da yaran a cikin gidana tana matukar ci musu tuwo a k'warya. Hatta shi kansa mijin namu ya zama abin zargi a wajensu. Alhali shima sa'i sa'i sai ya yi barazanar zai dakatar da makarantar ana cika masa gida da hayaniya. Kawai ya ga abin ya girmama ne shiyasa ya yi mukus. Babban abin da na rik'e kuwa addu'a ne, sannan ban tab'a ayyana na cutar da su ba. Amma mafi yawa kullum sai sun yi mini sanadin bacin rai. Misali zan aiki Hajjaju ta ki zuwa, karshe ta bige da yi mini kunkuni amma uwarta ba zata tsawatar ba, idan na hassala na tsawatar a tunanina taya tarbiya na yi sai ya zame mini kalubale. Dan haka sai na hak'ura da aikenta. Sai kuma sakayya ta shigo domin sai ta koma take yiwa uwarma babu yadda za'a yi ta sarrafata, uban kawai take shakka. A maimakon hakan ya zama izna ga sauran matan kowacce ta shiga a hankalinta. Ina sai suka sake nausawa jeji. Kowacce akan d'anta babu s'auki. Wata bata isa ta mori d'an wata ba. Mata! mata muna da muguntar da take cin kanmu da kanmu Allah ya shiryemu kawai. Ana cikin haka aka fara auren kanwarsa wacce da ga ita sai autansu. Shine ya yi komai. Kuma ni ya damkawa ragamar siyayya da gudanar da komai. Dama kuma tun farko ya fara yi mini hakan akan y'aya'nsa, da abu ya k'i na ce ya d'ora ko wacce uwa akan d'anta ni ya bar ni Ubangiji ma da yake sona fiye da kowa hakan ya bar ni, ban kuma d'auki hakan a matsayin tawaya ba. Alhamdulillah da dukkan jarabawa. Kullum ba ni da sukuni ina tafe tsakanin gidansu da nawa gidan da kuma kasuwa. Zuwa yanzu na fara samun sassauci da ahalinsa tunda halin kowa ya bayyana a tsakaninmu da abokan zamana. Da ace zan biya sharrin zuciya da na shaidan da ko kulasu bazan yi ba. Tunda ba abin da ban ga ni ba a shekarun baya. A fili na furta wnada Ubangiji ya masa baiwar hak'uri da hadiye da bacin rai ya tara masa dukkan alherin duniya. Fahimtar da na yi hak'uri ne yasa na cigaba, shine yasa ban zama yadda ake son na zama wato na tozarta na zama Allah sarki. Sai na dimanci addu'ar Fasbir sabaran Jamila. Nake yawaita kula'uzai da li'ilafi, domin na gamsu dafa'i ne daga dukkan wani kaidin mai kaidi. Ta gidan kanwarsa ta uku na biya muka tafi kasuwar tare. Muna tafe muna hira tana jaddada mini abin da yake cikinta nawa ne ko ta mutu. Tunda na fad'a mata na ki karban y'aya'n yan'uwana ne saboda yadda gidan namu yake cike da rikitarikita da rashin tsarin tarbiya a wajen matan gidan. Dan haka bazan yarda na dauko d'a ayi ta tashin hankali da musgunawaa gare ni tare da gori mai ciwo ba. Ta kuwa ce "ai idan ni na baki babu mai tsinin bakin da zai tayar miki da hankali. Ni a k'asan raina ma ba so nake yi ba. Bana damuwa tunda na riga na roki Ubangiji kada ya jarrabe ni da butulce nasa dan ban haihu ba. Na gode masa da ya sanya ni cikin bayinsa musulmai, ya ba ni lafiya, ya kuma bude mini k'ofofin alherin da zan yi ta neman lahira, da kuma yiwa mutane ihisanin da zan zama ni din ta kowa ce. "Alhamdulillah" bana gajiya da furta hakan. Kafin mu kammala siyayyar tuni na yi dinkunan da zan yi hidimar biki tare da bayar da gudunmawata mai kauri. Addu'a kan addu'a na sha a wajen mahaifiyarsu wadda suke kira da Inno Amaryar kuwa da tun tana k'arama y'ar dakina ce, kayan gyara takanas na sanya Surayya HALIN YAU ta hada mata. Saiwowin sanyin da take siyarwa kyaunsu aziman ne. Bayan haka na shaida sauran kayan ma babu algus. Daga ni sai ita muka yi abinmu ba'a sani ba. Saiwowin dahuwar kaza kuwa da yake mutum biyu zasu yi amfani tare na siya na dafa mana kazar nima na sabuntawa d'an sababin nawa😅. *08032773332.* A yanzu tauraruwata ce take haskawa a wajenta. Har wanda bai sanni ba, zai yi zaton bansan bak'in ciki ko musgunawar uwar miji ba. Amma da yake kowa ya yi hak'uri za'a yi da shi, sannu a hankali ta gane nice mai rangwamen tsiya a cikin surukanta gabadaya. Tun ranar jere na fahimci Nadiya na nemana da sababi mai girma, material din da an sanya na Umm Nihla mazauniyar Malaysia ya yi matukar mintsinin ta. Ni kuma ban ga abin damuwa ba da ta tambaye ni sai na bata contact din kai tsaye ta zabi kalar da take so kafatalin kishiyoyina ba wadda take da takamarta, ba wadda take son fato ni irinta. Tabbas mun goga da Nafisa domin ita da aka aurota ta zo ne da gillin ita ce zata haifi yara magadan gida, sannan kuma ta zo da niyyar ta fitar da ni a gidan ta hanyar cusa mini takaici da bak'in ciki. Tabbas na yi kuka, na shiga garari akan aurenta, haka tsananin da na fuskanta a sadda ta samu ciki mai yawa ne, ba daga shi ba, ba daga danginsa ba. Sai dai tafiyar bata yi nisa ba alkadarinta ya karye tunda mata ta haifa ba maza ba sharri kuma dama d'an aike ne. Bata tashi ganin gayya ba sai da ya auro Nadiya. Bansan kuma dalilin da yasa nafi tsayawa Nadiya a rai fiye da Nafisa ba. Ta damu da ni. Ana cewa da ta farko da ta uku suke had'a kai su bar ta biyu to ni kam ban samu wannan tagomashin ba. Izzar Nadiya ta sake kasaita ne da ta ga ta haifi maza a jere. Sai take ganin zata take kowa tunda ita din d'iyar masu kumbar susa ce, sannan tana ganin itace mai kyallin goshi a wajen miji da danginsa hatta Inno mahaifiyarsa rarrashin zuciyarta take yi. Matan gidan masu haihuwa Nafisa da Aliya basu shak'e mata wuyan da ni na shake mata ba, na rasa dalilin wannan masifar da take yi da ni. PAID BOOK #500via 7084653262 Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. ✍🏻 *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE* [12/11, 9:30 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A* 52U/HARVERT NETWORKING BUSINESS *ALHERI NE💃💯* Ina masu sha'awar shiga shahararren kasuwancin nan wato 52U basu da hali? ga dama ta samu SZARIA tazo maku da sabon tsari domin taimakawa marasa 'karfi, wato TEAM WORK. da kud'in ki 'kalilin zaki samu abunda zaki taimaki kanki da 'ya'yanki. Tsarkakken kasuwanci ne mai ingantacin da babu asara a cikinsa sai riba mai gwa'bi. 'Yar'uwa maza ki shiga gruop din mu ga link din nan a kasa, domin mu gudu tare mu tsira tare. Domin 'karin bayani ku tutubi wanan number *08037930727* https://chat.whatsapp.com/CSQ94ZeYnPJ26ppXhBnRII 3&4 Saura sati d'aya biki ya kawo mana leshina da atamfofi. A falonsa ya tara mu. Bisa al'adarsa baya mana tufafi iri d'aya. Zai siyo ne kaloli hud'u masu kyau mabanbanta kaloli, sai dai masu daraja d'aya ma'ana kudinsu daya. Ba zabi yake bayarwa na fara zaba ba, illah iyaka shine zai bawa kowacce wacce yake ganin ta dace da kalarta. Amma idan aka dinka sai ace tawa tafi kyau ko ace ta Nadiya da sauran magaganganun gutsiri tsoma. Domin matan gidan ga ni suke yi yafi karkata a kaina da Nadiya. Ita kuwa Nadiya kullum maganarta tsorona yake ji. Ni kuma sai na ga ita yake so yake kuma shakka. Da na nutsu sai na gane har abada namiji ba zai fita daga zargi a wajen mata ba, matukar ya ajiyesu da yawa. Da yake Nadiya ce mai girki na yi godiya na tashi da kayana na barsu a hade. Na sani kuma k'orafi za su amayar domin kullum a cikin haka suke. Na sauko da akwatina na ajiye na saka a ciki na goge k'urar da ya yi na rufe, na mayar, domin tuni na tanadi din'kunan da zan saka masu kyau da tsada. Da yake da tazara a tsakanin gidansu da da nasa gidan amma ba mai tsayin ba. Sai na roki ya bar ni idan na tafi juma'a da yamma an yi kamu na kwana domin mu yi asubancin d'ora abincin d'aurin aure. Bai k'i ba, da yake hidimar tasa ce, da hidimar gidanmu ce babu nauyi zai murza gemu ya hana ni kwana. Kai idan ya ga zirga zirga zata yi yawa hanawa yake yi babu jin nauyi bare kunya. A hakan nake ta hakuri da baudadd'en halinsa har zuwa lokacin da komai zai zama tarihi kamar yadda ake yawan jaddada mini. Tsakanina da Allah ko yanzu Yaya Rabi'u ya zama yadda nake son ya zama na ci goruba a hannnusa ba kwakwa ba. Wani irin mutum ne murdad'de mai wahalar sha'anin gaske. Kawai na tattara na cire damuwarsa ne a raina tunda ban ga alamun zamu rabu ba. Auren namu ya zama tamkar na zobe. Bai cika gane muhimmancina ba sai na yi masa tutsu. Babban bak'in cikina idan ya ga wani ya tab'a ni ya hau zuba bala'i da sababi. Amma shi ya yarda ya taka ni, ya muzanta ni a gaban kowa. Yau da ace iya ni da shi yake yiwa da na ji sassauci to shi a gaban kowa ma yana iya yi mini tijara. Ranar yini na zuba leshina na yi kyau tamkar mai shekaru ashirin. Gabadaya sai walainiya nake yi cikin kwalliyar da na zuba babu karya. Nadiya da suka iso ta ganni ai gabad'aya sai ta rikice domin tana ganin ita ce yafi kamata ta dinga kwalliyar da nake yi. A dalilin tana ganin iyayena talakawa ne sannan ta sha gabana a wajen miji. Nan da nan zuciyarta ta yi bak'i. Ta yi kicin kicin tamkar ta rushe da kuka. A ni kuwa ko a kaina sai kai komo nake yi, ina bawa bak'i abinci da abin sha. Da yake ta zo da yayarta sai na mutuntata na kai abincin gabansu. Ashe hakan ma laifi ne. Ta kaikaice ta ce "Ni din ai ba bakuwa ba ce a gidan, domin ta wata fuskar ma na fiki dangantaka da su ke kawai shishshgi da shiga da fita kika kere ni". Duk yadda maganar ta buge ni. Sai na murmusa na ce "Tun kafin ayi kwaram aka yi kwandi Nadiya! domin dai Yaya Rabi'u ko ban ajiye masa komai ba ai tuni iyayenmu kinsan yan'uwan junane". A hassale ta ce "Makwabtakar kawai?" Na sake murmushi dan na tabbatar mata ta yi kad'an na nuna ta bata mini bare ta yi farinciki. Na ce "kin manta Annabi ya ce." Ya yi zaton yadda Allah ya yi ta yi masa wasiyya akan sha'anin makoci za'a saukar da ayar da makoci zai gaji makocinsa saboda yadda Allah ya ce a girmamasu." Ta dauke kai domin ta ji maganar Annabi bata da ja. Can kuma ta yi tsaki mai tsananin gaske tare da ce wa "An mayar da mazaje saunoni, idan mace ta ga tana da kalar da zata ja hankalin maza ai komai ma sai ta yi don ta dinga samun kud'ad'e tana yin bajintar neman suna tare da saka suturu dan dai ayi fariya". Ban san ya aka yi ba na juya tamkar zan fita sai kawai na d'auketa da mari irin wadda ake yiwa lakabi da 'barin makauniya. Na kuma cakumeta da dukkan k'arfin da Ubangiji ya yi mini. Da yake shammatar ta na yi, ta ji jiki a hannuna kafin ta fara ramawa, ganin hakan da yar'uwarta ta yi sai kawai ta shigar mata. Basu kai ni k'asa ba amma dukkanmu mun ji jiki. Domin na fasa mata gefen ido gabad'aya jini ya wanke mata fuska wanda hakan ne ya janyo hankali jama'a suka shigo dakin da muke ciki wanda na Inno ne. Yar'uwarta kuma na naushe ta a hanci sai ha'bo take yi. Mafi yawa da ba sa ra'ayina sai salati suke yi suna fad'in "Wannan idan ya zo da k'arar kwana ai sai ta yi kisa, ta had'a tima timan mata ta fitar musu da jini! Inno ta shigo ta kalli yadda nake huci. Ta kasa yi mini sababi yadda take yi da amma kuma jikinta na rawa ta nufi Nadiya tana fad'in "Sannu Nadiya. Sannu kin ji zuwa yanzu ya kamata ace kun saurara da wasu abubuwan. Wai har yanzu bitar da ake ta faman yi muku babu sassauci bai shiga kunnuwanku ba? Ai had'a kashi da kishiya ba abin da yake janyowa a gida sai tsiya. Ku bari haka nan. Ke ban da abin ki ma menene zai dame ki ne, kin riga da kin yi k'arfin da dole ke ce a gaba. To ba na son irin haka". Na zubawa Yaya ido ina kallonta. Idan har na fahimci karatun tana jaddadawa Nadiya cewar "Itace da gida. Dan kawai ta haifi maza hudu. Ko waya tabbatar mata da hakan, ko sai yaushe za'a gane rayuwar nan gaibu ce ba wanda yasan da me gobe zata zo da shi sai Allah. Zuciyata ta yi mini nauyi mai tsananin gaske. Karon farko da na ji na shiga rudani da damuwa akan rashin haihuwa. Na kasa daurewa hawaye masu nauyi suka tsinke mini. Inno ta juyo a sanyaye ta ce "To kukan me kuma zaki yi tunda kin kasa daukar girmanki. Yau ko wata ba'a yi ba, kika mini alkawarin ba zaki sake yarda ki yi dambe ba, ko me zasu yi miki kuwa. Sai ga shi kin sake yi din a cikin dakina kuma. Na yi mamaki Malama Kyauta". Murya na rawa na ce "Yaya hak'urina ya kai geji akan caba mini magana da yarinyar nan take yi ne. Bazan sake cewa ta bari ko na kai togaciya akan ta ba. Amma tabbas ta sake kankanbar jifana da mummunar kalma jikinta zai fad'a mata, sai na illata ta, sai na sauke mata dukkan abin da take takama da shi." Inno ta dauki ki salati mai tsananin gaske tare da ce wa "Sai kin illata ta kika ce Malama?" Yar'uwar Nadiya da take faman goge hanci da tissue ta ce "Ke ce shaida Inno domin Wallahi ba zamu bar maganar nan ta tafi a banza ba sai hukuma ta shiga, tunda ta riga da tasan me ta taka." Nadiya bata ce uffan ba illah kuka da take yi sosai tunda Inno ta shigo dakin. Da fishi suka bar gidan bikin. Yayin da nima suka rage mini walwalar da nake ciki. A zuciyata kuma sai fargabar mai zai biyo baya nake yi idan na koma gida. Nasan tana can tana gunshekin kuka tare da tsarawa mijinta karya da gaskiyar zance. Tare da Nafisa muka koma gida bayan mun raka amarya dakinta. Sai gulmar Nadiya take yi mini, ni kuwa na kame bakina domin nasan dan tasu ta hadosu ne akan mukulli amma ai ba yarda zan yi da ita ba, tunda tare suke yak'ata. A k'ofar gida muka tarar da shi duk yadda hasken wutar lantarki ya haske fuskarsa amma babu annuri ko kad'an a tare da shi. Na bude kofar falona ke nan, ya shigo a harzuke tamkar kububuwa. Da tsananin huci ya ce "Allah ya yi wadaran halin ki na tsiya Kulsum! A ce ba kya jin d'ar din keta mini alfarmata? Ki kama matar da nake aure ki daka a cikin jama'a saboda ke ce wa?" Ban ce kala ba, bare na tanka, illah iyaka ina ta maimaita RABBI INNI LIMA ANZALTA ILAIYYA MIN KHAIRUN FAQIR" Ganin ban kula shi ba, ya tuntuzura ya rik'e kafadata ya girgiza ni tare da ce wa "Mahaukaci na zama da zan yi magana ki yi mini diban karan mahaukaciya Kyauta?" Nan ma ban kula shi ba. Ya fusata ya ce "Tunda kin kore mini tauraruwata ki tabbatar ke ma baza ki ji dad'ina ba, ba dan abu d'aya da na fahimta a tare da ke ba, da na sallama ki na huta. Ace mace kullum sai ta yi maka sanadin bacin rai! Na fara gasgata Ilimin ki na son halaka ki, tunda da shi kike fakewa kike yi mini k'ulunboto ". Na yi murmushin da babu nishadi na ce "Sannu a hankali dai dab'iunka kullum k'ara rikicewa suke yi. Shikenan ni ba ni da darajar da zaka zauna ka ji abin da ya faru. Sai kawai ka ji iya abin da aka fad'a maka. Ka zo ka dirar mini saboda na zama karkatacciyar kuka?" Ya ja tsaki tare da matsowa yana nuna ni da yatsa tamkar zai doke ni. Yana fad'in "An ki aji ta bakin na ki! Ai tunda Ilimin ki bai amfana miki komai ba, to kuwa zan dinga mu'amalantar ki irin yadda ake yiwa jahilan mata." Na girgiza kai na ce "Dama can haka kake yi, rangwame na samu saboda wata ajandarka. Jahilci kuwa kasan ba ni da shi. Na yi boko, arabi kuwa sai dai na koyar da kai. Sannan ina gargadinka kada ka yi kuskuren tsole mini ido ko saka mini hannu da sunan duka." Bak'in cikinsa ya ninku. Ya shiga jifa da duk abin da hannunsa ya sauka tunda ya riga da yasan na kerewa dukansa tun rikicin da muka yi na k'arshe. Na koma gefe na zauna ina kallonsa. Cikin kwarmato ya ce "Na soke makarantar da kike zuwa, na kuma haramta miki wacce kike tara yara kina koya musu, tunda gidana ne, sannan ban ga ranar da Ilimin na ki ya yi mini ba". Na kalle shi na yi murmushi mai harshen damo. Ya ce "Ban isa ba ko Kulsum? Na riga da na fahimci sana'ar da kike yi ta sanya kina mini kallon ban isa ba, ko kuma na gaza. Wallahil azim zan baki mamaki, ba zan ce ki tafi ba, amma na rantse sai kin dandani bak'in ciki fiye da wadda kika k'unsan mini. Kuma Baban titi kika jikawa aiki domin shine zai yi mini jelen bikon Maman Baffah". Na sake murmushi na ce "Kasan zai iya tunkarar ko wanne mahaluki ne saboda shi din dattijon arziki ne, ka kuma sani baka aike shi bama yana zuwa maka bikon bare ka mutunta shi ka wakilta shi". Ya rasa inda zai tsoma ransa da takaici. Domin ya fahimci kullum rage tsoransa nake yi. Ya yun'kura zai yi magana wayarsa ta hau kuwwa. Ya duba sai da ya yi tsaki sannan ya amsa. Muryar Nafisa na ji ta ce "Yau ma zaka raba dare ne a dakinta?" "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun! Wai ke wacce irin halitta ce mai tsananin zargi haka?" Da karadi ta ce "Zargi ko kuwa gaskiya. Kana tafe fankam fankam kamar namiji nan kuwa sahorami ne. Gabadaya mace itace take jan akalarka amma ka k'i gane hakan kullum cikin buyagin iska kake yi." Ya katse wayar ya fice yana fad'in"Magana bata mutu ba, na shiryawa faruwar komai wallahi. Ba zai yiwu na zuba ido ki kore mini mace mai wuyar samu ba. Kalilan din mata ne suke haifar mazaje reras iri ne mai kyau da ba'a wasa da su." Karon farko da ya yi mini maganar mai kama da gorin haihuwa kai tsaye ba a sakaye ba. Na kifa kaina a hannun kujera hawaye ya tsinke mini domin sosai maganar ta tab'a ni. Wai sai yaushe Rabi'u zai mini adalci? Sai yaushe zai yabe ni, sai yaushe zan ji dad'in da ake ta fad'a mini zan ji, zuwa yaushe ne zan ga d'an kaina? Rashin tartibiyar amsa ya sake tsananta kukan da nake yi. Na tab'a ganin haka, babu jin ba'asi sai kawai ka hau sababi dan kawai an tab'a maka uwar mazaje. Kaina ya d'aure da al'amarinsa gabad'aya yana abubuwansa kamar bagidajen da ya rayu a jeji babu ko wanne Ilimin rayuwa tsabar gidadanci. Na tabbatar ya kasa cewa na fita na bar masa gida ne saboda abin da ya yi imani na d'amfare da ni. Abin mamaki 'bacin ran da nake ciki bai yi tasirin da ya hana ni rintsawa ba. Domin ina idar da sallar shafai da wutiri barci mai nauyi ya yi awon gaba da ni. Sai daf da ketowar alfijir na farka. Ina idar da asuba ma na sake komawa na kuma fahimci jikina ne ya yi tsami a dalilin zirgar da na sha, da hidimar biki, ga kuma y'ar k'ashin da muka gwabza. Ko da na farka ruwa na dumama na yi wanka na gasa jikina, na karya sannan na hadiyi Panadol. Ko ta kan ta'adin da ya yi mini ban bi ba. Sai dai me a zabure na farka na ganshi yana huci. Take na fahimci shine ya tashe ni. A zafafe ya ce "Barci ma kike yi ko? Na zuba masa ido gabad'aya ya jirkice ya koma azababben mutum. Murya babu amo na ce "Yaya Rabi'u ina kwana?" Tamkar ya rufe ni da duka tsabar tunzura ya ce "Kyauta na rantse miki baki isa ki tayar da zaune tsaye ke kuma ki zauna k'alau ba. Ki tashi ki tafi gidansu Nadiya ki bata hak'uri, ki dawo mini da ita". Na yi murmushi na ce ka "fasa tura tsohon nawa ne?" "Kulsumu ki shiga taitayinki, ba fa wasa nake yi da ke ba". Na dara kad'an na ce "Hak'uri kam bazan bata ba. Da ka biyo ta lallama mai zai hana na je bikon kishiya tunda ka gamsu ina da matsayi da kamalar da zan je biko a madadinka". Ya ja tsaki ya kasa magana. Can ya ce "Ki tashi ki je ki yiwa yaran wanka, tunda kin kori uwarsu." Na ce "Ubansu ai yana nan. Ga kuma sauran matanka masu y'aya' su ya kamata su had'a da su, tunda albarkacin kaza kadangare ke shan ruwa." "Tabdi ashe kuwa zan ture komai na miki rashin mutuncin da ba ki yi zaton zan miki irinsa ba Kyuata! Ya fad'a da fishi ainun. Na ce "Ba abin da zaka yi mini ya ba ni mamaki domin na tabbatar maimaine akan na baya." Ya rasa yadda zai yi domin yasan a yanzu na wuce dukansa. Ba kuma zai iya jarumtar fitar da ni a gidansa ba, saboda wata fahimtar da ya yi ammana da ita. PAID BOOK #500via 7084653262 Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE* [12/12, 9:46 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A.* *ADVERT* Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/JrVGCbG7R8SFurApPbPilB *SAMIES KITCHEN* The Best Chartering Service🥗🥘. *KANO STATE: NO4 ZOOROAD HOUSING ESTATE* *Jama'a Samies kitchen wurin fita kunya ne da kece raini. Wuri ne ingantace da ya amsa sunansa domin sharewa ma'abota karamci hawaye a yayin da wata hidima ta same su. Bari na jaddada muku SAMIES KITCHEN Ya samu sheda da lambar yabo gurin cika alkawari da karrama jama'a. Kada na cika ku da surutu bari na tafi kai tsaye domin sanar daku ainihin abinda ya sa nake kwad'aita muku 'kulla alaka da su. Wato SAMIES KITCHEN sun 'kware wajan shirya girke girke na gida dana waje. Sun yi shura wurin 'karbar order daga kowane sassa a fad'in Najeria. Suna yin abincin biki, abincin suna, abinci taro, abincin saukar al'kur'ani, order domin yin Birthday. Sun gwanance sosai wurin yin cima iri-iri da kayan ma'kulashe duk domin fita kunyar abokan hurd'arsu. Sannan ba su tsaya iya nan ba suna hada-hadar sayar da manya manyan leces 'kananu da manya kowane irin na'ui. Suna bud'e dilolin leces irin namu na gida (mama ta mutu) kala daban daban. Ana samun kayansu da inganci tare da farashi mai sau'ki. Domin neman karin bayani sai a tuntubi wannan lambobin.* *08173037544 ko 07044417448* 5&6 Kansa ya girgiza ya kama hanyar fita yana sa'be babbar riga sai kace sabon limami. Na yun'kura na tashi na fita zuciyata a 'kuntacce na shiga kicin domin lalubar abinda zan sa a bakina. Kicin din kace-kace babu gyara kudaje sai tashi suke yi ina kuma jin muryar Jummai mai yi mana wanke-wanken da shara a gurin Nafisa suna hira da dariya. Raina ne ya 'baci ainun domin na san tabbas da Yaya Rabi'u ya lura da k'azantar kicin din a kaina zai sauke bala'i duk da ya san ba ni nake da alhakin hakan ba, zai ce ai ni ce babba amanar gidansa a hannuna take. Kofar Nafisan na nufa na iske su a zaune durshen suna hira. Baffah da 'yan'uwansa suna zaune du'kun-du'kun da d'aud'a Nafisa ta yi wa Yaranta wanka tana shafa musu mai. Babu fara a fuskata muka gaisa sama-sama, na ce." Jummai kin ga kicin kuwa 'kudaje sai bi sukeyi kwanuka duk sun bushe kina zaune kina hira ga sharar tsakargida da gate duk ba ki yi balle ki wanke band'ukuna, lokacin nan fa takaitacce ne, har yaushe ki ka kammala wannan aikin ki ka d'orawa Yara abincin rana, kuma kin riga kin san islamiyarsu ba su da wasa gaskiya Jummai ki canza idan ba haka ba zan sanar da maigidan halin da ake ciki domin wannan shine karo na uku." Cikin ya'ke ta ce." Yi ha'kuri Uwar dakina bisimillahi bari na tashi na yi aikin da yake gabana. Nafisa ta dakatar da ita babu fara'a a fuskarta ta ce." Wai Ummi girki ki ne ko nawa da za ki shigar mini hurumi?" Jim na yi ina kallonta kafin na ce." Girki ki ne amma ba sai na yi miki 'karin bayani ba kin san komai. Sunkuyar da kanta ta yi tare da cewa" Ni fa ki daina yi mini katsaladan ina ganin mutuncinki, ranar girkinki bana sa miki Ido saboda haka babu ruwanki Jummai dai ni na kira ta muna magana kuma ba ke ki ke biyanta albashi ba." Murmushin takaici na yi na ce." Sai ki fad'awa Mijinki idan ya ce na zare hannuna daga kanku dama haka na fi bu'kata." Ta bugi kirji tana fad'in." Ni fa ba Nadiya ba ce wallahi, kin san ni sarai idan ki ka yi mini ba zan saurara miki ba, ya kamata ki fahimci wannan, zaman aure ki ke yi, zaman aure nake yi, na lura kawaicin da nake yi miki ba kya gani amma idan ba rashin mutuncin ba ina ruwanki da shiga abinda bai shafe ki ba." Tsaki na ja na kalli Baffah dake zaune yana had'awa 'kannansa jirgin Leda na ce." Ku ta shi Baffah mu je ayi wanka." Da sauri ta ce." A banza dama ai babban burinki ki kore mu daga gidan, kin kori uwarsa kina kinibibi, ai wallahi Kulsumu tuntuni na dawo daga rakiyarki, ki juya mana miji sannan ki juya mu to ni wallahi ba ki isa ba, kin yi tsararo! Kuma zama daram a gidan Rabi'u." Ban tanka mata ba saboda ganin yadda Yaran sukayi tsit! suna kallonmu, kawai na yi gaba ina fad'in" Baffah ku biyo bayana ayi wanka, ke kuma Jummai wata'kila shan ruwanki ne ya 'kare a gidan tunda gulma da munafurci ki ka zo yi." Ina jin hargowarta tana fad'in." Ba ki isa ba wallahi Jummai zama daram dam! sai ke ki fita ki bar mata gidan. " Takaici ya kama ni, dama ai mai hali ba zai fasa halinsa ba, lokacin muna biyu Nafisa ba irin cin mutuncin da ba ta yi mini ba, sai ta kai ni bango wani sa'in nake turmusheta na daki kayana Yaya Rabi'u yazo ya yi ta shari'a, ta kama hanya ta tafi gidansu wai ta yi ya ji saboda na doke ta, idan ya yi biko ta'ki ta dawo sai ya rabu da ita ya shiga sabgoginsa, da k'afafunta take dawowa saboda iyayenta ba su da karfi wasu daga cikin 'yan uwanta ma a k'arkashinsa suke cin abinci, kuma da yake Ubanta dattijo ne duk abinda zai shiga tsakaninmu ba ya goya mata baya, saboda sanin halinta sai dai ma ya ba ni ha'kuri ya tattaramu ya yi mana nasiha har mijin namu gabad'aya. Ina ko'karin kunna wuta Jummai ta shigo tana soki burutsu duk a 'ko'karinta na kare kanta ta kar'bi ashanar da take hannuna tana gyara bakin buhun gawayi zata zuba a korfoti take fad'in na je na zauna yanzu za ta d'umama ruwa ta yi wa yaran wanka. Kafin ma na yi magana Baffa ya yi caraf ya amshe Yana fad'in "Munafuka wallahi sai na fad'awa Babanmu maganar da na ji kuna yi akan Mama har kuna k'yalkyala dariya ai duk na ji abinda ku ke fad'a ke da Ummansu Walida." Jummai ta diririce ta fara kame-kame. Yaron ya cigaba da za'kulo zance wanda ya d'aure mini kai mutu'ka wato dama amincin da yake tsakaninsu na gaibu ne suna yin hakan ne domin su kai ni kasa wai Nafisa yau ita take farinciki da fitar Nadiya har tana addu'ar Allah ya sa ta tafi kenan ba za ta dawo ba. Na yi sauri na daka masa tsawa jin yana ko'karin zaginta saboda tana musantawa, Baffa ba k'yalle ba ne, ba shi da kunya uwarsa ma bai bari ba balle wani. Na kalleta duk ta muzanta sai zare Ido take yi na ce " Jummai kin ba ni kunya wallahi, ai idan duniya da gaskiya ba za ki zauna a ci naman Nadiya dake ba idan an yi duba da irin hidimar da take yi miki a gidan nan cikinmu babu wadda take kwatantawa, ba gori zan yi miki ba daga gidansu Nadiya duk shekara kina da Zakkah ta bayar da sunanki, sannan da Azimi kina da buhun shinkafa da gero bayan wanda maigidanmu zai ba ki, da sallah kina da turmin atamfa da kudin d'inki duk daga gidansu Nadiya, idan ban mance ba kuwa Nadiya idan ta tashi bayar da kayanta dana Yara ke take had'awa d'auri guda ki d'auka ki kai garinku amma yau dake aka zauna ana cin dunduniyarta. "Billahil-lazi 'karya yake mini Uwardakina kwarankwarsa dubu ban......Katse ta ya yi yana fad'in." Wallahi Ummi karya take yi Munafuka ce domin har ji na yi suna cewa wai kin wanke wandonki kin bawa Babanmu ya sha a ruwa kece ki ke sarrafa shi, sai umarnin da ki ka bashi." Jummai ta yi tsuru-tsuru tana zare Ido. Hakan ya tabbatar mini da gaskiyar maganar Baffah dama kuma yaron da wuya ya yi k'arya, kusan halinsu d'aya da ubansa rashin tsoro da kafiya da taurin zuciya! Na kalleta tana sinne kai na ce." Jummai yi maza ki kunna wuta zan yi wa tufkar hanci. Ido jawur ta ce." Dan zatin Allah ki rufa mini asiri kada ki sa a kore ni wallahi zan kiyaye gaba, zan kula da aikina. Tausayi ta ba ni ganin yanda take shirin fashewa da kuka, tabbas idan na fad'awa Yaya Rabi'u abinda ya faru babu makawa sai ya sallameta 'karshe ya had'a mata da cin mutunci tunda na san hali. Na ce." Jummai wannan ya zama na farko kuma ya zama na k'arshe kada ki kuskura ki sake ke'bewa da wata daga cikinmu ki yi gulma idan hakan ta sake faruwa a bakin aikinki." "Zan kiyaye wallahi ba zan 'kara ba." Cikin nadama ta yi maganar. Na ce." Ki d'ora musu ruwan wanka idan kin sauke sai ki dafa mini indomi biyu. Ta amsa da sauri ta fara ko'karin rura wuta. Yaran na ja d'akina muka zauna ina ta kwakwkwafar Baffah akan maganar kada ya fad'awa Babansu ko Mamansa, da 'kyar na shawo kansa ya yi mini al'kawarin babu wanda zai fad'awa a cikinsu. Sai hankalina ya kwanta domin ina fargabar maganar ta fita wani rikicin ya 'balle wata'kila itama Nafisan yana iya kora ta gidansu muddin ya ji murna take da fitar Nadiya a yadda hankalinsa ya tashi da faruwar hakan bai 'ki gabad'aya mu fita mu bar masa gidansa ba muddin Nadiya tana ciki. Da daddare muna tare da yaran a dakina muna karatu Ya shigo na yi sauri na yi masa sannu da zuwa ya amsa babu walwala yaran suka gaishe shi ya amsa ya nemi guri ya zauna kan kujera. Baffah Ya ja 'yan'uwansa za su fita sai ya dakatar dasu suka koma su ka zauna, ni kuma ban so Hakan ba domin tunda na ga yanayin fuskarsa nasan abin babu dad'i, wata'kila duk dabarunsa sun 'kare akan lamarin sai kawai na ji hargaginsa Yana hura hanci yake Fad'in." Kyauta kin san Allah da Annabi sai kin gyara kwa'bar da ki ka yi idan ba haka ba zamu sa kafar wando d'aya dake. YA ZA A YI Littafin Binta Umar Abbale Ya za a yi ki yi sanadin fitar Uwar Yara ki zauna kina koya musu soki burutsu, ni kin bar ni da kame-kame! Ina galantoyi kina so ki sabauta mini rayuwar yarana, shi fa d'a dole sai uwarsa, ba zaki ta'ba burge ni ba idan wannan salon ki ka d'auka, ki kyale ni da matata ya fiye mini, yanzu ga shi juyin duniya Nadiya ta yi fushi ta'ki dawowa dole sai kin taka sayyadarki kin je gidansu kin bata ha'kuri da iyayenta. Ina dalili ni da na ajiye matayena ban mika hannu na dake su ba sai ke, to ba shakka zan sayi bulala na rataye duk ranar da hannunki ya kara gangancin dukan wata da cikinsu na rama musu ba zan lamunta ba." Tunda ya fara maganar Bai tsahirta ba har sai da ya kai geji tukkuna ya ajiye Yana nishi kamar wani kumurci tsabar bala'i hular da take kansa ma ta karkace tsininta ya yi gefan kunansa, banta'ba ganin namiji da gumin hanci ba sai akan Yaya Rabi'u, idan Yana bala'i karan shancinsa dabaibayewa yake da gumi kamar an yayyafa ruwa. Shiru na yi tak ban ce ba, domin ina iya yin magana ta 'baci dalili ya Kai ni ma'kura inda nake Jin ba zan iya jurewa ba, shiyasa nake ta nanata Kiran Allah a cikin raina saboda bana so mu yi b'ataciyya a gaban Yara. Allah ya kar'bi addu'ata kuwa Yana cigaba da nanata maganar Hajjaju ta shigo tana kumbure-kumbure daga Bakin kofa ta tsaya tana fad'in aiken da akayi mata. Aikuwa ya buga mata tsawa da sauri ta zube a kasan gurin. Ya ce." Don Ubanki waye sa'anki a gurin nan ? Za ki shigo babu gaisuwa ki tsaya kerera akan mutane zan yi maganinki da Uwartaki Gabad'aya. Da rawar murya take ba shi ha'kuri tana gaishe shi, Bai amsa ba illah ta shi tsaye da ya yi, ta gaishe ni na amsa ban ko kalleta ba, domin na San gaisuwar dole ce ta yi mini dalilin Ubanta. Ya nufi bakin kofar Yana fad'in." Ta shi daga gurin nan kafin na k'araso dan ball zan yi dake na karya ki." Da sauri ta ta shi ta raku'be har ya wuce kana ta bi bayansa. Zazzafar ajiyar zuciya na sauke na d'an sa ci kallon yaran domin lura da halin da suke ciki. Wasa suke yi Amma ga dukkan alamu Baffah duk ya nad'e abinda ya faru domin na ga sauyi a tattare da shi. Na ce." Babbah anan zaku kwanta ne ko a dakinku?" Kai ya girgiza tare da cewa" Zamu kwana a nan." Na ce." To maza ka je ka d'auko muku bargo sai ku rufa da shi tunda ana sanyi. Da sauri ya amsa ya ta shi ya fita. Duk yanda na so na danne ba'kincikin da yake cikin raina kasawa na yi, na kwana ina kuka da tunanin abubuwan da Yaya yake mini. Wai ni yake wa gorin haihuwa har Yana fad'in d'a sai uwarsa wannan kalma ta tsaya mini a raina mutu'ka idan na tuna kausasan lafuzansa sai hawaye masu azaba su goce mini. Yaya Yana da manta alheri, a tunani na ni da shi mun zama d'aya 'ya'yansa nawa ne wallahi har a cikin zuciyata haka nake ji ko da na haihu ba zan iya bambamta abinda ya Haifa da wata da Wanda na haifa ba, sai ga shi da bakinsa yake munana zato a kaina yana jifana da manyan kalamai duk akan Nadiya da iyalinta to ina tsammanin zai yi biyu babu domin na rantse da girman Allah muddin ni zan je masa bikon matarsa sai da ya sake ni, tunda shi mutum ne mara adalci idonsa ya rufe saboda Yana Jin tsoron bacin ran Ubanta a matsayinsa na Ubangidansa zai d'auki lefi ya d'ora mini ni kad'ai alhalin ya san taura biyu Bata taunuwa haka kawai ba zan Kai hannuna jikinta ba sai da dalili, zahiri sai dai ya zaba Ni ko Nadiya wannan shine hukuncin da na yanke. Ina zaune a kan dadduma ina lazimi na ji maganarsa da Yara suna gaisawa. Ya shigo d'akin babu sallama ya coge daga bakin kofa. Zuciyata na danne na gaishe shi, Ya amsa Yana muzurai! sai na kawar da kaina daga barin kallonsa saboda yanda nake jin wani irin haushinsa. "Ki tashi ki shirya gari Yana yin haske zan sauke ki a gidansu Nadiya domin ki bata ha'kuri da iyayenta, mahafinta mutumin kirki ne ba za ki yi mini kasassa'ba." Uffan ban ce masa na ninke dadduma na kwanta a gado. Sai ya shigo d'akin sosai ya tsaya a kaina yana magana. A nutse na tashi zaune na ce." Idan ka yarda idan na yi maka bikonta ni zan wuce gidan tsohona wannan shine hukuncin da na yanke." Yanda na yi maganar babu wasa shine ya sanyayyar masa da guiwa, ya zauna kusa da ni yana yi mini wani irin kallo. Na ce." Ka za'ba Kulsumu ko Nadiya Yaya na gaji da zaman gidanka Allah ne sheda na yi abinda zan yi Allah ya saka mini tozarcin da ka ke yi mini." Kuka mai k'arfi ya k'wace mini. Kamo ni ya yi yana so ya rungume na kama hannunsa na gartsa masa cizo! Ya ri'ke hannuwana duk biyun Yana girgiza kafad'ata. A raunane Ya ce." Kyauta Ya zan iya rayuwa babu ke! kin san dai abinda ki ka yi ba daidai ba ne, me ya sa za ki dinga dukan iyalina? ke waye ya yi miki haka? Kuma kin fi kowa sanin matsayin Uban Nadiya a gurina, me yasa a matsayinki na wakiliyata ki ka d'aura damarar wargaza mini kan gida, duk wata 'baraka daga gurinki take fitowa ya ba zan yi zargin ki ba." Ina kuka na ce." Shiyasa kenan ka ke yi mini gorin haihuwa ko Yaya Rabi'u? Ni ban yi maka gori ba sai kai za ka yi mini, anya duniya da gaskiya Yaya, kullum rikici idan ya tashi a gidan nan baka bin ba'asi ni kake d'orawa lefi na gaji wallahi, dama ban ajiye komai ba ka sallame ni kawai ka zauna da masu cikin haihuwa, ba za ka had'a kai da matanka ku tarwasa mini zuciya ba." Kuka na ke yi mai cin rai. Na tashi da sauri na fara birkito da kayana da suke jere a cikin kwaba... PAID BOOK #500via 7084653262....Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. Masu tambayar wannan karon babu Vip ne . Zan yi amma a talgram kawai za mu kammala littafin cikin kwana goma ko 'kasa da haka da ikon Allah. Wad'anda suke bukata kuma suna yin talgram din sai su yi mini magana domin jin abinda za su biya. 'Yan Nijar kuma dala d'ari katin airtel sai ku yi magana da momina kai tsaye babbar macace don Allah a kula. *+227 88 13 77 40* *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE* [12/13, 9:16 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A* *ADVERT* *HTTPS://INCENSEREPuBLIC.NG* *KANO NAJERIA* *GIDAN 'KAMSHI DA FITA KUNYA.💯💃* *Ina masoyan kayan kamshi Ina manyan mata? mata 'yan kwalisa? wannan sanyi fah sai da turare trust me kina bukatar turaren wutan Incense republic muna da turaren wutar daki,turaren jiki,turaren kabbasa da kabbasa spray ba a iya turarukan wuta kadai muka tsaya bah muna da humrori asalin humra mai kamshin manyan Hajiyoyi irin asalin kamshin yan Maiduguri ba tsami gaye bah 😄 Ga kuma kullacha maii Tashin kai 💥wadda zaki ji dadinta a wannan yanayi na sanyi.Sannan muna da oil perfumes da zaki iya shafawa ko a jiki ko a kaya kuma wani abin burgewar a cikin oil perfumes dinmu akwai wanda har maza za su iya amfani dashi. Hajiya za ki iya sayawa mijinki ko kuma saurayin ki saboda kara dankon soyayya ♥️💃* Turaren wuta Humra Kullacha Kabbasa spray Turaren Kabbasa Turaren wanka Room Freshner Oils masu kamshi Souvenirs package mai dauke da Turaren wuta,Humra,Kaskon turare wuta da Lalle da sticker *Domin neman karin bayani sai a tuntubi wannan lambobin* Wa.me/2348137369317 0813 736 9317 ko 0904 482 2052. Na yi nisa sosai a arewa. *Binta Umar Abbale.* https://www.arewabooks.com/chapter?id=67482a18ca3a075ba0996752 7&8 Ya dabaibayeni ta baya. Na fara turjewa ina buge hannuwansa. Yana nishi yake fad'in." Kyauta ki ka fita daga gidan nan, Allah sai ranki ya 'baci wai ya kuke so na yi da rayuwata ne? Me yasa ko wane namiji yake zaune lafiya da iyalinsa, amma ni kun mayar da ni gaula kullum cikin fargaba da zullumin kaidinku." Na kalle shi hawayena na zuba na ce." Kai ka saya duk abinda yake faruwa a gidanka ba ka da adalci, dan haka ni na yi abinda zan yi a zamana da kai Allah ne sheda ban cuceka ba." Kafin ya ce wani abu kira ya shigo wayarsa ya fito da ita daga gaban aljihunsa ya rike tsintsiyar hannuna katamau! Ya sa wayar a kunnansa. Nafisa ce cikin hayaniya ta fara yi masa sababi! maganganuta duk a kaina ne tana furzar da su da tsantsar kishina da yake cikin k'okon ranta. Na d'auka zai biye mata sai naga ya kashe a jirkice ya kalle ni ." Kyauta kada ki fita daga gidan nan idan kina so mu wanye lafiya." Da sauri na ce." Idan ba na so kuma fa?" Tashin hankali muraran! Ya bayyana a cikin idonsa. Duk ranar da ya tu'ke ni na yi masa tutsu! irin wannan ya kan ransa nutsuwarsa komai nasa Yana tsayawa cak! Na ja tsaki na juya ko tausayi bai ba ni ba domin duk abinda yake yana sane ya mayar da ni karkatacciyar kuka duk jarabarsa idan da tashi a kaina zai sauke. Maganar da yake a waya ita ta dakatar da ni daga barin abinda na ke yi. "E, wallahi Baba gata nan tana had'a kaya ta 'ki jin maganata kwana biyu Kulsumu bata mutuntuni, idan zan kafa doka a gidana itace take fara rusawa. Yanzu Baba daidai ne Kyauta ta dinga zage 'kwanji akan abokanan zamanta! Har sai da ta fasawa Nadiya baki fa." Jikina ne ya yi kwata'kes jin irin sharrin da yake shirya mini a gurin mahaifina wanda nake ta jinsa yana salati da tu'ajibi. Na sake tsinkayar maganarsa yana fadin." Wallahi kuwa Baba dama yau na ce zan zo na d'auke ka domin aje a basu ha'kuri ta dawo d'akinta ko saboda Yaranta." Ban ji abinda Babanmu ya ce ba amma yanayin yanda yake magana a fusace da 'bacin rai shi ya kara tabbatar mini da cewa; Hud'ubar da Rabi'u ya yi masa ta samu gurbi a zuciyarsa. Kashe wayarsa ya yi, ya kama hanya ya fita ya barni da akwati a gaba domin ya san abinda zai yi mini kenan ya dakusar da ni. Akwatin na mayar Saman kwaba na duba agogo bakwai saura da sauri na tashi duk da ba girki na ba ne amma dole na sa Ido akan su Baffah dalili Nadiya da Aliya sun sa gilli a cikin zuciyarsu kowacce zata kimtsa Yaranta ne domin tafiya makaranta. Kicin na nufa Jummai ta kammala musu abinci ta zubawa kowa a fulas. muka gaisa na tambayeta su Baffah nan take sheda mini ta yi musu wanka tun d'azu suna can suna shiryarwa. Ina fitowa daga kicin na ji hayaniya na tashi daga gurin Nafisa. Gabana ne ya fad'i ban san ranar da zamu zauna lafiya ba a gidan nan. Nafisa 'korafi ne da ita, ita a haukanta ranar girkinta kada ya kula kowacce daga cikinmu saboda haka akace mata ana yi. Fitowa ta yi hijabin wuyanta ya karkace tana share hawaye. Da sauri na tari gabanta na ce." Nafisa menene haka da sanyin safyar nan?" Hannu ta d'aga mini a kufule ta ce." Kin ga Ummi kada ki yi mini wata magana tunda igiyar aurena a hannuki take sai ki sa almakashi ki datse d'ayar da ta yi saura dama biyun ma ke ki kayi sanadinsu." Na tausasa harshe na ce." Nafisa don girman Allah ki koma d'akinki, ki yi ha'kuri da rayuwar nan kina kallo dai Hajajju ta yi wayo shekara goma Sha hud'u ga walida idan ku ka cigaba da irin wannan wallahi Khalid da Huzaifa ma da suke da k'ananun shekaru ba za su manta ba." Yaran duk suka fito suka tsatstsaya da kayan makaranta a jikinsu. Da Ido na nuna mata su. Sai ta juya ta koma tana share fuska. Na kalli Hajjaju dake share hawaye wato duk hatsaniyar da iyayen sukeyi a gaban yaran ne, na ce." Ke Hajajju ki ja su ku wuce ku tafi Adamu direba na jiranku." Da sauri suka fita jikinsu duk a sanyaye." Har na yi nufin tafiya gurina na sake tsinkayar wata sabuwar sa'insar a tsakaninsu. Ban yi nazarin komai ba na kutsa kaina d'akin tana tsaye a kansa tana sakin kausasan kalamai tana kuka babu tauna harshe shi kuma yana zaune ya shirya tsaf Yana gyara link din hannuwan rigar dake jikinsa. Yun'kurin tashin da ya yi dukkaninmu ba mu yi tsammani ba kawai na ga ya d'auke fuskarta da wani bahagon mari! wanda sautinsa har sai da ya fita. Itama ta zabura ta matsa gefe hannunta dafe a kumatunta Da sauri na shiga tsakaninsu bakina na rawa na ce." Wai Yaya Rabi'u don Allah menene haka? wannan fa ba mutuncinka ba ne, YA ZA A YI a gaban yara ka dinga tozartamu, wallahi zaka lalata musu tarbiyar baka sa ni ba." Ba tare da ya ce mini komai ba ya ture ni ya je ya d'auki hularsa ya d'ora a kansa ya tsaya gaban mudubi yana daidaita zamanta. Ashe ba ni kad'ai lamarin ya yi wa ciwo ba. Kawai sai na ga ta zabura! za ta nufe shi hawaye na zuba share-share a kumatunta. Na ri'ke hannunta ina girgiza mata kai. Tana sheshshekar kuka ta ce ." Me yasa ba ki bari ya nakasta ni ba, ai duk abinda yake yi mana a gidan nan da sa hannunki, kin san ba girkin ki ba ne amma idan ya shiga d'akinki da asubah sai ki rike shi Allah ne kad'ai ya san abinda kuke aikatawa na shiga hakkinmu wallahil-azimin ban yafe ba." Da mamaki mai yawa a tare da ni na ce." Nafi ki dinga kyautata zato na alheri tsayin shekarun da mukayi a tare ya kamata ace ki san halina, bana fatan ranar da zan ci amanar wani daga cikinku abinda ki ke zargi Bai ta'ba faruwa ba. Ta cire hannunta daga nawa tana fad'in." Ai ga shi nan sai ki tambaye shi yaushe rabon da ya had'a shimfid'a da ni, yau kusan wata biyu kenan, Kuma na auna na lura duk ranar girkina yake shiga gurinki ya shud'e awanni bai fito ba, wallahi ba zan yarda ba sai manya sun shiga maganar nan." Shiru na yi kawai ina kallonsa domin maganar ta girmi tunanina, lallai kishi ya rufewa Nafisa Ido da har ta yi subtar Baki gurin fad'in sirrin dake tsakaninta da mijinta. Na san dabi'arsa ce yin hakan, amma ni bana lamuntar son zuciyarsa duk da a wani 'kaulin Malamai sun yi inkarin cewa; Miji zai iya kwanciya da matarsa Koda ba ranar girkinta ba ne. To ni duk lokacin da ya bijiro mini da lamarin bana aminta gudun abinda zai je ya dawo, zahiri dai duk ranar da girki ya dawo hannuna baya daga mini 'kafa cikin kwanaki biyun nan ina jin jiki a hannunsa dan dai na saba da dabi'arsa ne tuntuni shiyasa ban fiye damuwa ba. Maganarsa ce ta katse tunanin da nake yi. " Na 'ki na kwanta dake d'in, ai zuru na yi miki sakarya kawai babu abinda ki ka sa a gaba sai kishin jaraba. Ni ba soko ba ne, a gurin da na fi samun maslaha da nishad'i zan lalace, ki yi nazarin maganata." Zuru mukayi muna kallonsa yana d'aura agogo a hannunsa babu abinda ya dame shi ya cigaba da cewa" Ita Aliya ai matar rufin asiri ce Dama ku ne kuke 'kokarin lalata mini ita, tana burgeni mutu'ka babu ruwanta da sakarci irin naku, kuma tana Jin maganata saboda haka ita da na auro a bayanku ta fiye mini ku sau dubu tunda zan kafa doka ta bi, kuma ba ta yi mini rashin kunya sakarkaru kawai." Ya suri mukkulin motarsa ya kama hanyar fita 'kalau da shi sabuwar shaddar jikinsa tana ta motsi! Tsabar takaici ban iya cewa komai ba na ja jiki na fita daga dakin guiwa a sanyaye, ba yau Yaya Rabi'u ya saba tsinka ni ba, amma zahiri cin mutuncin da ya yi mana a yanzu ya sosa mini zuciya, Rabi'u wani irin ba'aboren mutum ne da duk jarabar mutum ba zai gane ha'ki'kaninsa ba. A yinin ranar na yi ta zuba ido na ga ko Nafisa za ta tafi gidansu shiru ba ta fito ba sai hankalina ya kwanta cikin zuciyata nake yi mana addu'ar samun nutsuwa da kwanciyar hankali. Nafisa ta fita da girki Aliya ta kar'ba a tsakanin kwanaki biyun wata hatsaniya ba ta tashi ba maigidan ma baya zama sosai a dalilin hidimomin da suke gabansa na harkar kasuwanci, idan ya shigo gurina da asuba a tsaitsaye muke gaisawa ya fita. Ranar da girki ya dawo hannuna ya shigo muka gaisa ya mi'ko mini mukkulin sito na ce." Me zan yi dashi kuma?" Ya ce." Tsarin na canza a gidana duk wacce take da girki zan bata da hannuna idan ta fita na bawa 'yar'uwarta." Ban ce komai ba nasa hannu na kar'ba. Ya kama hanyar fita yana gyara zaman agogon hannunsa yau kwalliya aka ca'ba da k'ananun kaya sai ya yi kyau sosai ya dawo matashi babu wanda zai ce ya ajiye 'yar shekara goma sha hud'u dalili yana da jiki mai kyau kuma yana kula da kansa. Na ce." Adawo lafiya." Ya amsa kafin ya sa kai ya fita daga d'akin. Dama tsarin gidan namu wacce take da girki ita ke bawa maigidan karin kummalo da abincin dare. Jummai kuma tana kula da hidimar abinda yara za su ci da safe da rana da wanda za su tafi dashi makaranta. Towon shinkafa na shirya yi mana da daddare. Na sa Jummai ta harhad'a mini komai. Ina idar da sallar la'asar na yi niyyar shiga kicin. Sai kira ya shigo wayata Maigidan ne, a nutse na gaishe shi ya amsa yana shan toka. Shiru na yi ina sauraransa Ya ce." Yanzu Yunusa zai kawo kaji inaso ayi farfesu dalili yau Nadiya za ta dawo sannan ki sa Jummai ta 'kara gyara gidan a kunna turaran wuta." Na ji wani gundumemen abu ya yi kakagida a ma'kogwarona. Saboda Nadiya za ta dawo shine za a yi farfesu na mussaman sannan a tsabtace gida harda su turaran wuta! Lallai Lamarin Nadiya a gurin Rabi'u azimun ne." "Kyauta ko ba kya ji ne?" Ya fad'a a kausashe! Na daure sosai ina danne zuciyata na ce." Bayan farfesu me kuma za a yi Yallabai?" "Shi kad'ai na buk'ata." Na ce." To za a yi in sha Allahu." Kashe wayar ya yi ba tare da ya sake magana ba. 'Kwalla ce ta cika kwarmin idona. Na nemi guri na zauna k'afafuna duk sun yi sanyi. Nadiya ta 'kwace mini Yayana hawayen da nake dannewa suka su'bce suka fara falfala gudu kumatuna. Nasa hannu na rufe fuskata ina ta Kiran sunan Allah kafin na samu sassaucin kishin da yake yun'kuro mini. Na tashi da rashin kuzari na fita daidai lokacin da yaronsa Yunusa ya shigo hannunsa da buhu muka gaisa sama-sama ya ajiye buhun ya fita. Na kira Jummai domin ta taimaka mini, kaji ne manya guda takwas a gyare. Na ce ta markad'a mini kayan miya kafin na zo kansu. Har na kammala aikina Nafisa da Aliya babu wacce ta fito kowace tana gurinta da yaranta. Na zubawa maigidan nasa da yawa su Baffah ma na di'bar musu, sauran kuma na bari a kicin din na san duk zulumar mace za su ci su bari, Jummai da ta taimaka mini itama na d'ibar mata rabonta. Sai da na gabatar da sallar magariba tukkuna na yi wanka na samu kaya marasa nauyi nasa a jikina. Bayan Isha'i wajan karfe takwas Nadiya da 'Yan uwanta suka dira a gidan. Baffah da 'Yan'uwansa duk suka fice daga gurina suna ihu Mamanmu ta dawo. Murmushi kawai na yi na gyara kwanciya ina ta nazarin rayuwar duniya. Hayaniyarsu har gurina duk da cewa akwai tazara a tsakaninmu. Ni da Nafisa muna daf da juna Nadiya da Aliya suna kusa haka tsarin gidan yake 'bangaran maigidan kuma yana tsakiyarmu sai babban gate wanda yake d'auke da d'akunun ba'ki da masu gadi da gurin ajiye motaci, cikin gidan kuma akwai babban tsakargida da band'akuna uku d'akin Yara hud'u da kicin mai yalwa, tsarin gidan dama can na zaman mace hud'u ne da kuma gurin da yara za su sake. Sai wajejen tara da kwata tukkuna na daina Jin hayaniyarsu tabbacin sun gama abinda suke yi sun tafi, mamaki lamarin ya dinga ba ni, sai ka ce wata sabuwar amarya harda yin zuga! gurin dawo da ita. Ashe mamakin da na ke yi lami ne domin lokacin da maigidan ya dawo kasa tsugun ya yi, ya kai ya kawo sai murmushi yake tauraruwarsa ta dawo. Ya shigo yana ta yi mini murmushi na babu gyara babu dalili, ni kuwa na sha kunu saboda yanda nake jin bala'in haushinsa kwata-kwata Rabi'u bashi da ta Ido ina tsammanin lokacin da akayi rabon kunya baya gurin. "Kyauta ki kai mini abincina gurina sannan inaso zan yi magana daku." "To." Abinda na ce kenan ban kara kallonsa ba. Ya shiga dakina ya yi minti biyu ya fito kafin ya sake maimaita mini maganar. Na sake cewa "To." Ban kalle shi ba, sai ya kama hanya ya fita, na bi shi da kallon takaici. Lokacin da na shiga falon duk sun hallara ita tauraruwar tasa tana zaune kusa da shi ta ca'ba ado da wani lece wuya da hannu gold sai walwali take yi, ga lalle ja da ba'ki a hannu da kafa abinka da farar fata ta yi kyau kamar sabuwar amarya. Na ajiye tiren hannuna a daddaumar da ya killace domin cin abinci. Na samu guri na zauna ina d'an satar kallon Nafisa sai kace mahaukaciya Ido ya kod'e da wata koriyar atamfa ajikinta duk ta zazzage ko yari babu a kunnenta balle a kai ga maganar kwalliya ita ga wacce ta yi ta fad'a da miji sai hura hanci take yi. Ita kuma Aliya an sha k'ananun kaya riga da siket da kitson gaba sai da babu wata 'kira ta matantaka gaba da baya sai shukuran. Da 'kyar na danne dariyar da take ko'karin 'kwace mini, na sunkuyar da kaina kasa ina nazarin yanayin zamantakewar gidan mata hud'u. Gyaran murya ya yi kafin ya fara da Bismillah sannan ya kira sunayenmu duk muka amsa, sai ya d'ora Ido a kaina kafin Ya ce." Kulsumu ba zan ga ji da jadadda miki ba cewa; Ke din Wakiliyata ce a ko'ina. Ba wai don bana sonki na auri Nafisa ba, haka zalika ba don kun gaza ba na auro Nadiya Aliya k'addarata ce, kowacce da matsayinta a gurina. Kulsumu ke kin fi su sanin waye Rabi'u dalili auran kuruciya mukayi ni da ke, kuma ina sonki duniya ta sheda hakan kema kin tabbatar, ba wai na furta miki hakan ne domin ki yi fuffuka ba, yanda nake sonki haka nake son duk wacce na kawo gidana babu wacce ta fi wata a cikinku sai mai kyautata mini. Kyauta ina gargadinki da babbar murya wannan ya zama na k'arshe kada sa'insa ya shiga tsakaninki da abokan zamanki ki mi'ka hannu da zummar duka, ba zan lamunta ba zan d'auki mataki a hukumance! domin babu wacce ki ka ajiye a cikinsu. Ki ri'ke girmanki sannan ki kula mini da amanar gidana. wannan shine gargadina dake. Ya numfasa kafin ya cigaba da cewa" Nafisa Nadiya Aliya ban amince ba ban kuma lamunta ba wata daga cikinku ta tozarta mini Kyauta, ita din wata baiwa ce ta mussaman wanda ni kad'ai na san hakan, kuma garkuwa ce a gare ni. Kada ku ga kun hayayyafa ku nemi wula'kanta mini ita ranku zai 'baci muddin na samu labarin faruwar haka. Itace babba a gidana Kuma mai wakiltata, duk da ba ta wani baku shekaru masu yawa ba, ya zama dole ku bata girmanta Wallahil-azimin duk wadda ta yi kuskuran cin zarafinta sai mun sa kafar wando d'aya. Saboda haka wannan shine dalilin zamana daku anan, ku zauna lafiya da junanku shine abinda nake buk'ata." Shiru falon babu wadda ta yi magana. Sai na daure zuciyata a hankali na ce ." In sha Allahu zamu kiyaye Allah ya Kori shed'an a tsakaninmu." Shi kad'ai ya amsa da Amin. Kafin ya ba mu umarnin tafiya. Na koma wurina da tunani mai yawa a tare da ni. da kyar na ci abinci na yi shirin kwanciya domin ban yi tsammanin zuwa d'akinsa ba dalilin dawowar Nadiya a shari'ance ita za ta kwana tare da shi duk da cewa; Ni na yi girki sai kuma ga shi ya shigo Yana fad'in." Kyauta na ce Ya za a yi ne gashi ke ki kayi girki kuma Nadiya ta dawo ai bai kyautu mu yi mata haka ba ko?" Ina bubbuge zanin gadona na ce." Gaskiya bai kyautu ba, kawai ka kwana a d'akinta ni ban damu ba. Ai tunda ta dawo an yi me wuyar." Jim ya yi yana kallona kafin Ya ce." Anya kyauta ko dai akwai wani 'kulli a cikin zuciyarki ne ." Na kalle shi ina jin kamar na farfasa masa hanci na ce." Wai ni Yaya Rabi'u yaushe za ka daina zargina ne? wane irin 'kulli kuma bayan yanzu na ji kana yabona a gabansu. Kuma fa shari'a ce ta ce hakan, ka je kawai ka yi kwanakinka idan basu isheka ba na baka kyautar nawa." Murmushi ya yi mai sauti kafin ya tunkaro ni, Yana so ya rungume ni. Na yi saurin gocewa band'aki na bude na shiga ina jan tsaki. Sai da na tabbatar ya fita daga d'akin tukkuna na fito. Na kwanta ina tunano abinda ya shud'e a shekarun baya.......... PAID BOOK #500via 7084653262....Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. Masu tambayar wannan karon babu Vip ne . Zan yi amma a talgram kawai za mu kammala littafin cikin kwana goma ko 'kasa da haka da ikon Allah. Wad'anda suke bukata kuma suna yin talgram din sai su yi mini magana domin jin abinda za su biya. 'Yan Nijar kuma dala d'ari katin airtel sai ku yi magana da momina kai tsaye babbar macace don Allah a kula. *+227 88 13 77 40* *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE.* [12/14, 11:04 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!* *NA* *BINTA ABBALE ABBALE 🍒* *M.W.A.* Na yi nisa sosai a arewa. *Binta Umar Abbale* https://www.arewabooks.com/chapter?id=67482a18ca3a075ba0996752 52U/HARVERT NETWORKING BUSINESS. *ALHERI NE💃💯* Ina masu sha'awar shiga shahararren kasuwancin nan wato 52U basu da hali? Ga dama ta samu SZARIA tazo maku da sabon tsari domin taimaka ma marasa 'karfi, wato TEAM WORK. da kud'in ki 'kalilin zaki samu abunda zaki taimaki kanki da 'ya'yanki, tsarkakken kasuwanci ne mai ingancin da babu asara a cikinsa sai riba mai gwa'bi. 'Yar uwa maza ki shiga gruop dinmu ga link nan a kasa, domin mu gudu tare mu tsira tare. Domin 'karin bayani ku tutubi wanan number 08037930727 https://chat.whatsapp.com/CSQ94ZeYnPJ26ppXhBnRII 9&10. Sunana Ummu Kulsum Adamu Kyauta. Na samu inkiyar Kyauta ne a wajen mahaifiyata. Saboda maza biyu da na rako. Kafin nan kuwa sai da ta yi b'ari uku kafin cikina ya tsaya mata. Akwai tazara mai yawa tsakanina da yayana da na biyo wato Yaya Ibrahim. Ina son sunan nawa na kyauta. Shiyasa ma na saka shi a cikin sunana a makaranta. A makarantar kuwa mafi yawa sun dauka inkiyar Babana ne ko ta kakana. Dan haka suke fad'in Ummu Kyauta, wasu ma kyauta kawai suke fad'a har malamai. Shi yasa sunan ya danne Ummu Kulsum tunda a gida kowa Kyauta yake fad'i. Mahaifina Malam Adamu haifaffen cikin birnin Kano ne. A unguwar Magashi. Bai yi karatun boko ba, sai ta allo. Da ya fara girma sai yake zuwa kasuwar rimi yana sayar da kayan koli, a hakan har ya yi teburinsa a maimakon da farko ya fara dauka a tire. Da wannan sana'a aka yi masa aure, ya haifomu, muka taso muka ganshi da ita. Mahaifina mai k'aramin k'arfi ne ainun amma kuma daidai gwargwado muna cin abinci, ba'a tab'a sauke tunkuya a gidanmu ba, yana kuma kokarin bamu abin da ya sauwaka na bukatar yau da kullum. Mu uku iyayenmu suka haifa. Yaya Usman sai Yaya Ibrahim. Sai ni Ummu Kulsum da na zo bayan shekaru goma da haihuwar Yaya Ibrahim Daga kaina kuma bata sake ba. Sai dai a yadda na ji labari mahaifanmu sun yi wabi, ma'ana y'aya'nsu sun yi ta rasuwa ne suna k'ananun. Kafin Yaya Usman ma sai da aka yi biyu suna komawa. Aminin mahaifinmu kut da kut tun 'kuruciyarsu Malam Saleh asalinsa shima d'an unguwar magashin ne . Tare suka yi ta fad'i tashin rayuwa. har zuwa lokacin da suka yi aure. Aka bawa kowa daki a cikin gidansu, tunda gidajen a jere ne. A haka duk suka yi haife haife. Malam Saleh ne ya fara kammala gininsa a bayan unguwa. Ya k'aura da matarsa da y'ay'a bakwai. Sun so su samu fili a jere su sake makwabtakar juna, sai dai hakan ya ci tura. Amma sun saya din sai dai akwai banbanci layi d'aya a tsakani. Mahaifina ne bai samu zarafin tashi ba sai da aka haife ni. Sannan ya yi k'aura zuwa k'aramin gidansa da ya gina cikin taimakon Allah. Na taso cikin gatan yayu da na iyaye. Domin lokacin da nake girma yayyena duk sun girma mussaman Yaya Usman. Sai na kasance ni ce k'aramar yarinya bayan haka ni kad'aice mace. Na taso da son karatun islamiya fiye da na boko. Hakan ya sake janyo mini soyayyar iyaye. A hankali ina girma ina fahimtar yadda al'amar suke gudana. Na kuma gane k'arfin amincin da yake tsakanin Babanmu da Baba mai keke. Domin kaf unguwarmu ba gidan da nake shiga ba'a biyo bayana ba sai gidan duk kuwa da y'ar tazara. Duk abin da baba mai Keke zai yiwa y'aya'nsa mata sai ya had'a da ni. Dija ce sa'a ta a gidan. Matansa biyu. Inno ce uwargida itace Kuma take da mafi yawan yara. Domin y'aya'nta tara cif. Sai da ta yi mata biyu sannan ta haifi Rabi'u, mata suka cigaba da biyo shi sai a karshe ta sake yin namiji ya zama auta. Dakin amaryarta kuwa da ake kiranta da Yadikko Kamal ne babba sai Khadija sai Asabe. Da yake akan girmanta ya aureta, ta yi haifehaifenta a gidanta na farko. Kasancewar Dija ce tsarata kuma kawata sai na fi dabdala a dakin Yadikko. Basa wani rikici a tsakaninsu sai abin da ba'a rasa ba. Tun muna yara da mun hango Yaya Rabiu muke guduwa a dalilin shi din azababben mutum ne. Bayan haka baya wasa da mu. Shekararmu goma kwatsam annobar amai da gudawa ta dira a wasu yankuna na cikin birnin kano. Mu dai bata shigo gidanmu ba, amma ta shiga gidan Baba mai Keke ta yi awon gaba da Dija da kuma mahaifiyarsu Yadikko. Tsiran kwana uku a tsakaninsu. Duk da ina karama na ji mutuwar Dija domin har cikin zuciyata nake sonta, ba ni da y'ar uwa mace, ba ni kuma da aminiya. Itace duka a wadannan matsayin a wajena. Da k'yar aka shawo kan wannan annobar da ta dinga lakume rayukan al'umma. Mutuwar Dija da Yadikko sai ya sanya gabadaya na daina zuwa gidan Baba mai keke. Inno da kanta ta zo ta dinga rarrashin na dinga zuwa ina debe mata kewar abokiyar zamanta da Dija. Cikin rarrashi ta ce "Ai da yara ku yi wasanku, ga yayyenki nan su Jummai, su Asabe ki dinga zuwa kin ji Kyuata". Na ce "To" Amma ba dan zan je ba. Shi da kansa baba mai Keke sai da ya zo bikona amma fir na k'i zuwa domin na riga da na tsorata. Domin sai nake ganin a gidan mutuwar take, tunda ta dauke mutanena idan ina zuwa ni zata sure. Yaya Rabiu da Yaya Ibrahim sa'annin juna ne, sai dai basu wani shaku ba, a dalilin kowa mai zuciya ne kamar kuturu. Bayan haka Yaya Rabiu makarantar kwana ta maza da take garin gaya ya yi, sai ya zo hutu. Da suka kammala sakandire kuwa kowa makarantarsa daban. Yaya IBRAHIM yana zuwa F.C.E KANO. Yayin da Yaya Rabiu yake zuwa polytechnic, yana yin diploma in public administration. Kafin lokacin kuwa kowa yana buga bugarsa ta neman taro da sisi. Mafi yawa wadanda suka tashi a cikin k'waryar birni yana wahala ka ga mai zaman kashe wando. Yaro da babba ana ta sana'a. Yaya Rabiu gawayi yake kullawa yana siyarwa a bakin titinmu. Shi kuwa Yaya Ibrahim Kes din caji ne da shi. A duk sadda na je siyo gawayi sai ya k'ara mini. Baya kuma hantara ta kamar yadda yake yi mana ni da marigayiya Dija. Sai kuma ya k'ara mini da wanda ya zarce na adadin kudina. Tun ina dari dari da shi har na sake. Da ya fara zuwa makaranta ma bai fasa ba, akwai mai jire masa, idan ya dawo da yamma kuwa zai cire kayansa ya saka na zaman gaban gawayi ya yi ta kullawa tunda kullum abin gaba yake yi. Da buhu d'aya ya fara amma yanzu har rabin buhu yana siyarwa. Shekarar da na kammala aji uku na sakandire a lokacin ya kammala diploma. Tunda ba daga kammala sakandire ya fara ba a dalilin rashin cikakken kudi. A duk sadda muka had'u da shi, walau a hanya ko gidansu, ko ya shigo namu gidan, ko kuwa na je siyan gawayi. Sai na tsinci kaina da jin nauyinsa. Bana iya had'a ido da shi. Shi kuwa da ya fahimci hakan sai ya fara tsokanata da ce wa "Matar! Ko kuma ya ce "Matar mai gawayi." Hakan ya sake rub'anya kunyarsa da rashin sakewa da shi. Ban fahimci ko ina sonsa ba, nasan dai ina matukar jin kunyarsa. Baya ga haka bana ganin aibun ba'kar fatarsa. Idan ka cire shi kuwa, ni bana son bak'in namiji haka siddan. Na fara zama budurwa . Domin ni din doguwa ce sambal. Sannan fara tas, ba ni da kiba, amma dukkan jikina a cike yake, mussaman a yanzu da nake shirin shiga sha biyar komai nawa daukar ido da hankali yake. Sannan ina da gashi sai dai cikarsa tafi tsayinsa yawa. Baki ne sosai amma mai k'arfi sosai. Da ace zan saka masa relaxer da har gadon baya zai sauka. Bayan haka ni din mai sanyin halice ainun, magana ma ba kasafai na cika yinta ba. Allah ya yi mini baiwar hak'uri kowa ya shaida hakan. Ba ni da girman kai ko kad'an. Har yanzu ban wuce na kai nik'a ko markade ba, sannan bana jin komai idan na tafi aike, sabanin sa'anina da suke ganin sun zama y'an mata aika sai yara. A zahirin gaskiya Yaya Rabiu bai tab'a furta mini yana sona da gaske ba, sai dai a wasa, sannan bai tab'a yunkurin yin abin da iyayenmu zasu fahimci yana sona ba. Amma ni kuma wasan da yake yi mini ya haifar mini da wani al'amarin da na kasa tantance shi a zuciyata. Ba ni da wanda zan tattauna. Tunda ni ko a makaranta bana yarda na yi doguwar hira. Ba ni da k'awaye. Sai dai Wanda za'a yi magana d'aya biyu. Gabadaya y'an ajinmu kallon local suke yi mini. Tunda suna ganin kalata ta yin yanga ce amma kuma na mayar da kaina bagidajiya. Ni kuwa na ajiye kaina a inda Ubangiji ya ajiye ni. Sannan halittata ce shiru da rashin sin kwarabniya. Sannu a hankali na fahimci banbancin Yaya IBRAHIM da Yaya Rabiu. Yaya Rabiu mutum ne d'an fafa yafi son harka da y'aya'n manya fiye da na masu k'aramin k'arfi irinsa. Bayan haka shi din yana da kifadi. A duk sadda zai ga Kyauta sai zuciyarsa ta buga. Yana jin wani irin abu ya tokare shi. Amma kuma shi gaskiya yafi son y'ar attajiri. Ba zai yiwu ya taso a gidan babu ba, sannan ya sake kwasowa kansa y'ar masu k'aramin k'arfin da zasu zuba masa na mujiya akan sana'arsa ba. Bayan haka yana son ya shiga sahun wadanda za'a musu jere na kece raini ba irin na yaku bayi ba. Sab'anin Yaya Ibrahim da shi gabad'aya bai damu da komai ba. Karatunsa da sana'ar da yake ta sayar da kayan wasa a bakin kasuwar k'ofar wambai kawai ya rik'e. Banbancin ra'ayinsu ya saka rashin shakuwa a tsakaninsu. Ba wai shiri ne basa yi ba. amma kuma babu aminci irin na kut da kut kamar na iyayenmu. Bai fasa tsokanata ba, matukar muka had'u. Wani zubin ma cewa yake yi "Saboda Allah kyauta a hakan zamu yi aure kin ki karbar cigaba da duniya ta zo da shi? Kullum kina cikin burum burin din hijabi kamar matar limami. A gida ko a dawa. Akan me idan kina gida ba zaki dinga cirewa kina shan iska ba? To gaskiya na fasa domin ni din wayayyen man ne". Ban tab'a tanka masa ba. Wani lokacin idan ya ji haushin shiruna sai ya hau ce wa "Irinku ne mata masu ganawa namiji azaba. Ba dama ku bude baki ku yi magana sai ku yi ta kunbiya kunbiya kafin a ankare mutum ya ji jiki a hannunku. Mijinki na da aiki Kulsum". A ranar da ya fara fad'a mini hakan ba k'aramar dariya na yi ba. Domin kuwa da dukkan zuciyarsa ya yi maganar. A gaban Inno mahaifiyarsa. A sanyaye na ce "Yadda kasan damo haka nake fa Yaya." Ya ce "Yabon kai dai jahilci Kulsum." A ranar dai ya ce "Wai dan Allah me yasa kika yarda ake ce miki Kyauta ki amsa? Sunanki mai dad'i da asali amma an wani k'ak'alo na gargajiya an lank'aya miki ke kuma saboda gidadanci har wani mak'ala shi kika yi jikin sunanki a makaranta. Ba ki ga yadda na dinga yak'ar masu ce mini Rabe ba, har sai da ya b'ata b'at! Da murmushi na ce "Ai kai d'an gayu ne Yaya." Ya ji dad'i domin yana son ace masa shi din ya iya wanka ko big guy ne shi. Bayan haka yana matukar jin dad'in yadda nake ce masa Yaya sak ba sai na had'a da Rabiu ba. Inno ta yi dariya ta ce "Zan ga dai ranar da zaka rage fafa. Menene abin k'i a Rabe ban da d'agawa?" Ya na gyara zaman hularsa da ta had'e da tsalelen farin yadin da ya sanya ya ce "Haba Inno. Ni din ai Ubangiji bai mini zubin y'an gargajiya ba. Ya fice ya barmu da k'amshin turarensa da ya baibaye gidan gabadaya. Na bishi da wani irin kallo ina ayyana sam sana'ar gawayi bata dace da d'an kwalisa irin Yaya Rabi'u ba. Sai dai sana'ar ta zabe shi, sai fatan Ubangiji ya sanya masa albarka a cikin nemansa. A lokacin da na kammala aji ukun na sakandire wato junior graduation sai ga memo, da key holder hadi da kuma stika irin wacce ake mannawa a bayan waya. Ya kawo mini hadi da koriyar shadda da zamu yi ankonta. Murnar da na yi ba kad'an ba ne, domin kuwa ba yi mini za'a yi ba a gida. Yaya Usman ya yi mini hidimar walimar saukar kur'anin da na yi watan jiya. Haka Yaya IBRAHIM shi ya biya kudin allo da sauran k'ananun tsarabe tsarabe. Babanmu kuwa baya irin wannan al'amarin tunda ba shi da halin yi. Abin da na sani duk abin da aka ce makaranta ce ta ce dalibai su kai, to Babanmu zai yi dukkan iyawarsa ya ba ni na kai. Amma baya d'orawa kansa tsirfar dalibai. Kayan da Yaya Rabiu ya Aiko mini fall leda ya yi matukar tasiri a wajen Babanmu. Tasirin da ba yadda za'a yi gari ya waye bai ce mini." Kyauta tunda a gida ana so ai bazai yiwu a kai dawa ba. Ki cigaba da kamewa. Kowa ya yi nufin tsayar da ke , ki ce ke an yi miki miji." Bana damuwa da kalamansa domin na gane Yaya Rabiu yake nufin had'a ni aure da shi. Ni kuma duk yadda nake shuru shuru, hayaniyar Yaya da hargaginsa burge ni suke yi k'warai da gaske. Nene kuwa fad'i take yi "Rabe ai ba da wata manufa ya yi wannan kayan ba. Ni yadda nake ganinsa ai bai ajiye kansa nan kusa ba." Sau d'aya ta fad'i hakan a gaban Baban titi ya dinga sirfa sababi. Yana fad'in "A ce d'ansa na wajen Saleh za'a yi inkari dan zai bashi aure? To ko bai ajiye kansa kusa ba, Kyauta bata da mijin da ya wuce shi a wajensa ". Daga wannan ranar ta kame bakinta bata sake cewa komai akan sha'anin ba. Ta zuba ido ta ga ta yadda al'amarin zai kasance. Ta shiga addu'ar zabin Allah. Ba dan komai Nene take ji d'ar din al'amarin ba sai dan sanin Inno mahaifiyarsa ta d'ora dukkan burinta a kansa, bayan haka shi din d'an fariya ne na gaske. Gabadaya abokansa y'aya'n manya ne. Ya kuma sha fad'in gara mutum ya auro wacce zata yi masa silar arziki idan ya zo wajen Yaya Ibrahim. Shiyasa take shakku a kansa, amma bata zafafa ba. Babban abin da yake bata mamaki shi bai ce yana sonta ba fa. Amma yadda ta ga maigidan nata ya fitititke ne yake bata mamaki ainun. A wannan lokacin Yaya Rabiu ya so jona digiri amma yadda kudin karatun jami'a ya tsefe ya sanya dole ya hak'ura domin ba shi da hanyar samun wadanan makudan kudaden. Dan haka sai ya mayar da hankalinsa a wajen sana'arsa. Yaya Ibrahim kam da ya kammala N.C.E. sai makarantar da ya yi Tp suka roki ya dinga zuwa da safe yana bawa y'an firamare darasin Integrated science. Kamar yadda ya koyar musu a lokacin da yaje koyon Tp. Bai k'i ba ,tunda zuwa karfe d'aya na tashi sai kuma y'an yamma su shiga. A haka har headmaster din ya yi masa kokari ya samu gurbin aikin koyarwa ta dindin alabashinsa. Duk da haka kuma idan ya dawo gida ya yi sallar azahar ya ci abinci zai fita kasuwa. Samun aikinsa ya yi matukar saukakawa Babanmu wasu al'amarin rikon gidan duk da dai albashin nasa ba wai yawa ne da shi na sosai ba, amma Alhamdulillah an samu sassauci. Ganin hakan Baba ya ce ya nemo yarinya ya yi aure ya gaji da zamansa haka. Yaya Usman bai kai shekarunsa da sana'arsa ba ya yi aure. A yanzu haka yana kasan unguwarmu a k'aramin gidansa a kansa da ya gina da k'yar. Sana'ar gini yake yi. Shima yana iyakacin kokarinsa akanmu sai dai da yake yana da iyalinsa shima tiritiri yake yi da nasa gidan. Matarsa d'aya da yara uku. A hankali ya ce "To Babah zan duba a kuma cigaba da yi mana addu'ar dacewa. Matan yanzun ne Mafi yawa masu dogon buri ne. Basu cika sauraren mai k'aramin k'arfi ba. Sun fi son tsalalen saurayin da ya jiku da Naira." Da murmushi Baba ya ce masa "Da sannu zaka samu irin wacce ta dace da kai mai yakana. Kada ka zarme a wajen masu kyal kyal din nan. Ka mayar da hamkalinka akan wacce ta siffantu da addinin take kuma kiyaye kaidojinsa. In Sha Allah zata zama mai godiya ka kuma samu gamsuwa da nutsuwa da ita ". Nene da take gefe ta ce "Allah yasa, Allah ya had'a shi da ta gari". ** Duk da na yi saukar kur'ani ban fasa zuwa makarantar islamiya ba. Sai na koma ajin hadda. Hazakar da nake da ita, ta sanya malamin ajinmu ya fara nuna ra'ayinsa a kaina. Sai dai ko kad'an ban ba shi fuska ba. Shi kuma bai yi k'asa a guiwa ba, bai fasa cusa kansa cikin siyasa ba. Kafin ya ce kowa ya biya sai ya ce "Ummu Kyauta. Hatta y'an ajin sun fara sansanar akwai abin da yake ransa game da ni. Ni kuwa ban san dalilin da yasa ko kad'an ban ji zuciyata ta buga a kansa ba. *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE* PAID BOOK #500via 7084653262....Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. Masu tambayar wannan karon babu Vip ne . Zan yi amma a talgram kawai za mu kammala littafin cikin kwana goma ko 'kasa da haka da ikon Allah. Wad'anda suke bukata kuma suna yin talgram din sai su yi mini magana domin jin abinda za su biya. 'Yan Nijar kuma dala d'ari katin airtel sai ku yi magana da momina kai tsaye babbar macace don Allah a kula. *+227 88 13 77 40* [12/16, 9:48 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A* *ADVERT* *HTTPS://INCENSEREPuBLIC.NG* *KANO NAJERIA* *GIDAN 'KAMSHI DA FITA KUNYA.💯💃* *Ina masoyan kayan kamshi Ina manyan mata? mata 'yan kwalisa? wannan sanyi fah sai da turare trust me kina bukatar turaren wutan Incense republic muna da turaren wutar daki,turaren jiki,turaren kabbasa da kabbasa spray ba a iya turarukan wuta kadai muka tsaya bah muna da humrori asalin humra mai kamshin manyan Hajiyoyi irin asalin kamshin yan Maiduguri ba tsami gaye bah 😄 Ga kuma kullacha maii Tashin kai 💥wadda zaki ji dadinta a wannan yanayi na sanyi.Sannan muna da oil perfumes da zaki iya shafawa ko a jiki ko a kaya kuma wani abin burgewar a cikin oil perfumes dinmu akwai wanda har maza za su iya amfani dashi. Hajiya za ki iya sayawa mijinki ko kuma saurayin ki saboda kara dankon soyayya ♥️💃* Turaren wuta Humra Kullacha Kabbasa spray Turaren Kabbasa Turaren wanka Room Freshner Oils masu kamshi Souvenirs package mai dauke da Turaren wuta,Humra,Kaskon turare wuta da Lalle da sticker *Domin neman karin bayani sai a tuntubi wannan lambobin* Wa.me/2348137369317 0813 736 9317 ko 0904 482 2052. Na yi nisa sosai a arewa books *Binta Umar Abbale* https://www.arewabooks.com/chapter?id=67482a18ca3a075ba0996752 13&14 Cikin rashin kuzari nake tafiya da zummar zuwa gidan Inna Hauwa. Zuciyata na sa'ke-sa'ke da tunanin yanayin da Yaya Rabi'u ya shiga a lokacin da Babanmu ya yi masa gwanintar bashi aurena. Gabana ya cigaba bugawa! saboda tunanin wani abu da zuciyata take raya mini. Sai nake ganin kamar hakan da akayi masa ba a burge shi ba ko ga yanayin yanda ya yi godiya kamar an tilasta shi. Idona ya dinga kawo ruwan hawaye ina dabarar mayarwa tunda a kan hanya nake gabad'aya na kasa iya danne lamarin a zuciyata ina ganin ko da Allah ya kaddara auren da wahala Yaya Rabi'u ya mutunta ni, duba da yadda ya kasa jure kutsen da akayi masa. Babanmu ya yi hakan ne da zuciya d'aya, Kuma a hasashen da yake a hannun Rabi'u kad'ai zan iya samun nutsuwa, sai dai har yanzu bai fahimci waye shi ba. Yaya Rabi'u bai ajiye kansa a kusa ba, yanda na fahimta duk tsokanar da yake mini ba ta da ala'ka da abinda Babanmu yake tunani. Ni kaina na jima ina rokon Ubangiji ya cire mini abinda nake ji a zuciyata dangane da shi. Amma duk kwanan duniya abin yana nan a mak'ale a zuciyata kamar ana tiri. Na isa gidan Inna Hauwa a gajiye ga damuwa da ta yi mini dabaibayi. Zubewa na yi akan tabarmar dake shimfid'e a rumfarta na rufe fuskata da mayafina hawayen da nake dannewa suka fara zuba. Kukan kad'ai shi zan yi na ji sassaucin abinda yake damuna. Allah ne ya jarrabe ni da san Yaya Rabi'u duk da cewa; Akwai tarin maza masu nagarta da suke 'kaunata amma ba na Jin su a raina ko kad'an zuciyata ta fi karkarta a zuciyar da ba ni da gurbi. Da zan iya cire son Rabi'u da tuni na cire na jefar na huta da damuwa. Inna Hauwa ta shigo rumfar tana fad'in." Kyauta daga zuwa kuma sai bacci, ko idonki biyu ne?" Shiru na yi mata ina ta ko'karin danne mahaukacin kukan da yake ko'karin kufce mini. Hannu tasa za ta janye mayafin dana rufe fuskata. Na ri'ke da kyau ina girgiza mata kai. Ta ce." Kuka ki ke yi Kyauta me akayi mini?" Zaune na tashi ina kare fuskata. Ta ce." 'Karya ki ke yi da dalili wannan kukan na ki, ki fad'a mini abinda akayi mini." Shiru na yi ban ce mata komai ba sai da ta sake magana tukkuna na yi mata bayani wai ko da shawarar da za ta ba ni. Kawai sai ta fara fad'a cewa; Yanzu an daina haka, auran na gani inaso ma ana samun tangard'a ballanatana na cushe! Idan tana raye ba zata bari ayi abinda za a yi kuka daga baya ba. Na so nayi mata bayani amma ta'ki saurarata dama kuma macace mai fad'an tsiya da mita. da zan tafi ta ba ni humra mai kamshi da dari biyu Humrar kawai na kar'ba ta yi ta yi dani na 'ki kar'bar kudin. Na yi mata sallama tana jadadda mini cewa; Na fad'awa Nene gobe ta tsammaci zuwanta. Na yi dakacen sanar da Inna Hauwa lamarin, domin na riga na san halinta 'yar tada zaune tsaye ce, duk da suna wasan 'kanwar mata da Babanmu hakan ba zai hana ya tsinkata ba muddin akan lamarin Rabi'u ne, ni kuma ba zan so hakan ba, wata'kila ita kanta Nene ta fuskanci 'bacin rai mai tsanani. Dan haka ko da na koma gida ban tashi maganar ba, har dare dai ba ni da kuzarin kirki. Ina kwance a rumfa na ji shigowar Yaya Ibrahim gidan. Babanmu Yana tambayarsa Yaya Usman saboda ya kwana biyu bai zo ba, Yaya Ibrahim din ya ba shi amsa da cewa; Yanzu sukayi waya yana kan hanya. minti goma sha biyar a tsakani Yaya Usman ya shigo gidan, ina jin suna gaisawa na yi shiru gabana na bugawa! kiran sunana da ya yi shi zaburar da ni, na tashi zaune ina amsawa. Tsakargidan na fita na raku'be a kusa da Nene cikin ranshin kuzari na gaishe su suka amsa Yaya Ibrahim Ya zuba mini Ido yana kallo kafin ya fara tambayata. Na ce." Lafiyata lau Yaya." Babanmu ya yi gyaran murya kafin ya fara magana akan abinda ya tarasu. Ya numfasa ya cigaba da cewa" Ko bana raye a doran duniya ban amince ku aurar da Kyauta ga wani ba face Rabi'u shi na mallakawa ita a matsayina na Ubanta wanda shari'a ta ba ni damar za'ba mata miji nagartacce! wannan shine; dalilin tara ku anan." Yaya Ibrahim shi ya fara sukar lamarin, Yana ta ko'karin nunawa Babanmu illar hakan da ya aikata, akan wane dalili zai yanke hukunci ba tare da ya saurari ra'ayin wanda akayiwa bajintar ba. Shi fa ya san waye Rabi'u tare da d'abi'unsa tunda tare suka taso, dalilin da yasa kenan kanwarsu bata ji'kuwa tunda an samu banbancin ra'ayi. Rabi'u Yana da 'kafafa da izzah uwa uba kuma rashin ha'kuri, gashi dai ubansa ba kowa bane amma bai ajiye kansa a kusa ba. Sannan duk lokacin da zaman majalisa zai had'a su yana jin irin zantunkan da yake yi akan irin macen da yake so ya aura wayaiyiya kuma 'yar manyan mutane, wannan shine kud'irin Rabi'u, Yana ganin idan a ba shi kyauta kamar an yi masa kutse ne, tunda ba shi ya ce yana sonta ba, zai ajiye a ransa ita din matar ladan noma ce. Kyauta macece mai ha'kuri da kawaici a ganinsa ba ta dace da zaman aure da Rabi'u azababbe ba wanda duk cikin abokanansu babu wanda bai san halinsa na musu da cacar baki ba, ga zahirin gaskiya Amma idan ana musu dai shi zai k'aryata mutum ya kawo k'auli da ba'adi, kuma ya tsaya kai da fata maganarsa itace daidai duk da ya san 'karya ya 'kir'kira, haka d'abi'arsa take yana da baki sosai kuma ba a kada shi a magana. Yana zuwa majalisarsu ta samari take d'aukar zafi. wasu lokotan a tashi lafiya wani sa'in kuma a tashi da hayaniya! Duk da Yaya Ibrahim ya bud'awa Babanmu asalin Rabi'u, amma sai ya take ya rufe shi da fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba. Yaya Ibrahim ya shiga ba shi ha'kuri ganin yanda ransa ya 'baci. Shi kuwa Yaya Usman fad'i yake Allah ya sanya alheri Ubangiji yasa da mu za a yi. Nene dai tashi ta yi ta shiga d'aki uffan ba tace ba, ga dukkan alamu al'amarin bai kwanta mata ba, sai ya kasance ni da Babanmu ne kawai muke son Rabi'u, domin duk sukar da Yaya Ibrahim ya kawo a kansa bata samu gurbi a zuciyata ba, abinda nake ji dangane da shi yana nan a jibge ko 'kwarzane bai yi ba. Washe gari da sassafe sai ga Inna Hauwa. Nene ta dinga tambayata lafiya domin zuwanta da safe ya bata tsoro! Ina d'aki a kwance na ji tana yi mata bayani abinda na je na fad'a mata kai tsaye kuma gurin Babanmu ta zo. Nene dai ba ta yi farinciki da zuwanta ba ko ga yanayin yanda take bata amsa. Muryar Bababmu na ji a rumfar yana tsokanar Inna Hauwa kamar yanda ya saba. Suka gaisa tana rama tsokanar da yake mata kafin ta kutso da ainihin abinda yake tafe da ita. Sai kawai na ji maganarsa a fusace ya juya lamarin kan Nene ya rufe ta da fad'a wai duk wanda zata je ta fad'awa lamarin nan bai isa ya hana shi iko da abinda ya haifa. Inna Hauwa tana fad'a yana fad'a. Kawai sai na ji Nene ta fashe da kuka tana fad'in." Hauwa ta shi ki tafi dan girman Allah ki cire kanki daga lamarin nan babu ruwanki, ki kyale shi ya yi abinda ya ga dama." Ganin tana kuka sai ya fita daga rumfar bai sake wata maganar ba. Ita kuma Inna Hauwa tana ta nanata maganar tare da fadin kuskuran da Babanmu yake ko'karin aikatawa. Nene ta ce." Yanda na bi lamarin nan da addu'a Hauwa ke ma ki bi shi da addu'a. Bana san abinda zai daga mini hankali ko kad'an. Wannan furucin shi ya sanyayyar da jikin Inna Hauwa ta bar maganar suka shiga yin wata da ta shafi zumuncinsu. Lamarin ya cigaba da tafiya cikin rashin da'di domin tunda lokacin da Babanmu ya furtawa Rabi'u abinda yake cikin ransa ya d'auke mini wuta, idan za mu had'u a hanya sai ya d'auke kansa. Hakan da yake mini ya fara sosa mini rai dan na tsani wula'kanci da a rayuwata! wasan da yake mini ya daina, ko siyan gawayi na je gurinsa sai da yasa yara su ba ni, kuma baya kar'bar kudin. Ganin abinda yake yi mini ya yi yawa yasa na kama kaina. Gabad'aya ma na daina bi ta hanyar gidansu ko makaranta zan tafi sai da na yi zagaye ta bayan layi. Na daina zuwa siyan gawayi. Sai Yaya Ibrahim ya shiga sayo mana buhu guda Yana ajiyewa. Na ji dadin hakan sosai domin dama neman hanyar da zan nesanta kaina da Rabi'u nake yi. Tunda maganar aure ya shiga tsakaninmu na daina zuwa gaisuwar Juma'a gidansu saboda ina jin tsoron na riske shi a gidan ya yi mini kallon banza. Bayan haka kuma ina jin kunyar Inno yanzu gabad'aya ba na so na had'u da 'yan gidansu ko a hanya ne saboda abinda yake shirin wanzuwa. Watanni biyu kenan ban sa Rabi'u a idona ba. Na damu sosai, domin ni kad'ai na san ciwon da zuciyata take yi mini a kansa, ina ko'karin dannewa ne kada ya fuskanci yanda nake sonsa ya samu makamin da zai ya'ke ni, shiyasa na d'auki wannan matakin. Ranar wata Alhamis misalin takawas da rabi na dare sai ga yaro ya shigo gidanmu wai Kyauta ta je Rabi'u yana kiranta. Na ji gabana ya yanke fad'i! Ko sunansa aka ambata a gabana sai na ji wani iri. Ban ta'ba tsammanin zai zo zance gurina duba da yanda ya ke nuna halin ko'in kula akan lamarin. Yaron ya kama hanya ya fita bayan Nene ta ba shi amsa kan cewa ya ce gani nan zuwa. Na jima kafin na tashi da sanyi jiki na canza tufafi na fesa turare mai kamshi a jikina sannan na zurma hijabi har 'kasa na fito da dadduma a hannuna. Nene dai ba ta ce komai ba har na fita daga gidan na same shi a tsaye a soro ya fesa kwaliyya da sabuwar shadda milk da dinkin 'yan birni hankalinsa gabad'aya yana kan wayar dake hannunsa. A sanyaye na shimfid'a daddumar ina fad'in." Yaya Rabi'u ka zauna." Gwasale ni ya yi ta hanyar fadin shi fa ba zance ya zo ba menene zan wani shimfid'a masa dadduma. raina ya 'baci na murguda baki tare da d'auke daddumar na rungume a kirjina ban sake kallonsa ba. Sai na tsinkayi maganarsa yana fadin. To in banda abinki Kyauta ai da mayafi mai raga raga ya kamata ki fito domin na duba zahirinki meye zaki zurmo hijabi sai ka ce wadda za ta je gidan gaisuwa. Shi fa lamarin aure yana buk'atar nazari da tantancewa." Na 'kulu sosai da maganarsa domin duk kawaicina kasa daurewa na yi na ce." Ai da yake bazawara ce ni. dole na fito da mayafi mai nuna tsaraici domin ka tantance ni." Murmushi ya yi, ya shafa sajen fuskarsa Ya ce." Ni ban fad'a ba, amma dai kin san ba ni ke aka yi ba ni, na gani ina so ba, dole akwai nazarin da nake so na yi a kan ki." Kasa daurewa na yi nasa masa kuka ina fad'in." To ni ma ai ba sonka nake yi ba. Nani'ka mini kai aka yi, kuma saboda farincikin mahaifina na kar'be ka." Dariya ya kama yi yana kallona kamar wanda kukan nawa yake masa d'adi! Nasa gefen hijabina na goge fuskata na yi nufin shigewa cikin gidan sai ya tari gabana da sauran dariyar a tare da shi. Ya ce." Kyauta ni abinda yake ba ni haushi dake saurin kuka yanzu fisabillahi menene abin hawaye a cikin maganata idan ba shagwa'ba ba." Hararasa na yi na murgud'a baki na ce." To ai kaine na ji kana wata magana ta daban. Shiyasa na fayyace maka abinda yake raina ni ma ba wani kwanta mini ka yi a rai ba." Ya dinga kallon fuskata yana murmushi. Sai na kasa gane abinda yake kallo Na sake murgud'a bakina na juya masa 'keya. Ya sake fuskantata yana kallon bakina. Nan na fahimci abinda ya ke kallo tuntuni! a karo na uku na sake murgud'a bakin ina hararasa. Ya dinga k'yalkyala dariya Yana fad'in." Lallai kin raina ni, yarinya daga harara sai murgud'a baki ashe haka za mu yi auran kina yi mini tsiwa!" Uffan ban ce masa na kawar da kaina. Ya cigaba da zantukansa idan na ga dama na ba shi amsa wani kuma idan na ji da rainin hankali na murgud'a masa baki! tun a nan na fahimci salon dana d'auka yana burge shi. haka mu ka yi zancen a tsaye kusan awa d'aya da rabi duk k'afafuna sun yi tsami. Yaya Ibrahim ya shigo soron sai ya tsaya Yana kallonmu. Kafin daga bisani ya mika masa hannu suka gaisa kowanne fuskarsa a d'aure gaisuwar ma dai kamar ta dole sukayi. Ban ji dadin hakan ba a cikin raina, domin ina so tun kafin tafiya ta yi nisa a tsakaninmu su daidaita kansu komai ya wuce tunda surukantaka ta shiga tsakani. Da zai tafi ya bani kyautar dari biyar sabuwar kar. 'Kin kar'ba na yi sai kawai ya lalubi hannuna ya saka mini ya fice daga soron ba tare da ya saurari maganar da nake yi masa ba. Kwanan farinciki na yi a ranar ganin yanda na fara shawo kansa cikin 'kan'kanin lokaci. Kuma na fahimci akwai 'bur'bushin sona a tare da shi kawai dai ba zai nuna ba ne saboda 'ki fad'i da kuma wane k'udiri da yake cikin zuciyarsa. Haka muka cigaba da soyayya mai tafe da rigima domin duk hak'urina a wasu lokotan idan ya kai ni bango tutsu nake masa, na daina kula shi ko ya zo zance bana fita. Dan akwai lokacin da mukayi fad'a ya zo yana fad'a mini irin kalar matar da yake so 'Yar duma-duma kuma wayaiyiya 'yar gayu mai zurfin karatun boko. raina ya soso sosai amma ban yarda na yi masa kuka ba saboda ba na so ya cigaba da ganin lagona sai dai ban kyale shi ba sai da na narka masa ba'kaken maganganu! masu zafi ban saurare shi ba kuma na buge zanina na shiga gida zuciyata kamar ta fashe saboda tsananin kishi. Fushi ya yi mai tsanani! Sai na nuna masa na fi shi Koda wasa ban kira shi a wayar da ya siya mini ba, kuma ban yi masa text na kalaman soyayya ba irin wanda na ke yi masa kullum. wata hudu ba ma kula juna har Nene ta fahimci wani abu ta dinga yi mini fad'a akan dole na koyi ha'kuri da juri'a tunda na san halin wanda Allah zai hada ni zaman aure da shi. Jinta kawai na ke yi amma bana tsammanin zan neme shi domin ya kai ni ma'kura 'kaunar da nake masa ita ta haddasa tsananin kishinsa ba na so na ji yana ambatar wata mace a gabana balle ya yabi surar jikinta. shi kuma ya kasa fahimtar hakan. Na lura mutum ne shi mai zara da k'ulafucin 'ya'ya mata. Misalin karfe takwas da minti goma na ranar wata Juma'a muna zaune a tsakargida harda Babanmu da Yaya Ibrahim Muna hira yaro ya shigo Yana fad'in ana sallama da Kyauta inji Rabi'u. Nene ta ba shi amsa ya fita. Ta shi na yi na shiga d'aki na kwanta ba ni da niyyar fita minti goma a tsakani na fara jin hayaniya tana tashi a tsakargidan tsakanin Babanmu da Nene Yaya Ibrahim Yana sa baki. Ina fitowa na fahimci akaina suke rigimar. Yaya Ibrahim ya kalle ni tare da ba ni umarnin tafiya gurin Rabi'u. Da sauri na sa hijabina na fito lokacin Nene ta d'auki zafi tana ta sakin maganganu masu kaushi! Babanmu ya yi mata shiru ya 'kyaleta! dama an ce mai ha'kuri bai iya fushi ba. Ni dai ganin yanda abin ya zama yasa da saurin gaske na fita hankalina ma duk baya jikina, ina Jin tsoro Rabi'u ya samu Babanmu ya fad'a masa rikicin da mu ke yi lamari ya 'kara dagulewa. Shiyasa koda na fita na sassauta fuskarta na gaishe shi. Aikuwa ya amshe da sauri yana ta jana da hira. Cikin raina na ce iskanci banza haka zan dinga yi maka a duk lokacin da kayi mini abinda ban gamsu da shi ba. Mun jima muna hira kamar wani abu bai ta'ba giftawa ba a tsakaninmu.Ya d'auki dari biyar ya ba ni kamar koyaushe na yi masa godiya sosai kafin na koma cikin gidan da tunanin lamarina da shi. *** Sannu a hankali na kammala sakandire lokacin na kuma yi haddar al'kur'ani mai girma tare da wasu littafan addinin musulunci. Lokacin auranmu Yana ta gabatowa daga 'bangaran mu komai an tanada lokaci kawai ake jira. Yaya Rabi'u kuwa abubuwa sun kacud'e masa, babu gurin zama sannan bai gama had'a lefe ba. Akwatina biyu ya siya masu sau'kin kud'i amma turmin bakwai kawai ya zuba a ciki 'Yan uwansa mata suka zuba masa abinda ya yi saura. Sai aka fara fafutukar gurin zama domin ya dage shi ba zai zauna a cikin gidansu ba. Kuma gashi babu kud'in kama haya. Kuma shi a ra'ayinsa ya fi so ko hayar zai kama shi kad'ai ba ya son wanda zai yi tarayyya da wani. Lokacin da Babanmu ya ji dambarwar da ake yi da shi sai ya dinga fad'a Yana cewa ai lefen ba dole ba ne. Tunda ba shi da kud'in kama hayar gurin zama sai ya rushe lefen ya je ya biya gidan da zai zauna turmi uku da takalmi da mayafi ya isa albarka ake nema a aure ba wani abu ba. saboda haka aure fa ba za a 'kara wasu wattanin ba, za a d'aura shi a lokacin da aka gindaya ba za a janye ba. Babu wanda ya sani a cikin gidanmu Babanmu ya siyar da sabon kekensa da Yaya Usman ya siya masa dan ya dinga zuwa kasuwa. Ya kira Rabi'u ya bashi dubu hamsin kyan-kyan! a hannunsa yace ya je ya kama hayar dasu. Sai da aka kwana biyu tukkuna da Yaya Ibrahim ya lura babu keke a gida ya tambayeshi bai 'boye ba ya fad'a masa abinda ya aikata. Yaya Ibrahim ya ji ciwon lamarin sosai! amma sai ya danne bai ce masa komai ba ya 'kyaleshi duk domin a zauna lafiya. Haka aka kawo lefena babu arziki sai kace na bazawara mara gata. Har kuka na yi da naga irin k'ananun atamfofi da takalman wambai da Rabi'u ya zuba mini a lefe sai wasu mayafai kamar abin tatar koko guda hud'u da wando da breziyya rabin dozin. Kayan kwaliyya masu sau'kin kudi. Na shiga d'aki na ci kukana na 'koshi kuma ko da wasa babu wadda na gayyata daga cikin 'kawayena akan ta zo ta ga lefe na. Abinda na ajiye a raina shine; Rabi'u ya yi niyyar tozarta ni ne amma idan ba haka ba shekara biyu da wata shida da sa ranar auranmu ai ya kamata ace ya tanadi duk abinda ake bu'kata gurin neman aure. Ranar d'aurin aure ya bada sadaki dubu goma sha biyar. Da shi aka saya mini zanin gado da ledar d'aki. Saitin gado da kujeru da sauran tarkace Yaya Ibrahim da Usman suka had'u suka yi cikin rufin asiri aka yi mini jeren d'aki a gidan da Rabi'u ya kama haya wanda duk 'kafafarsa bai samu wanda zai zauna shi kad'ai ba, akwai wani a gidan. Sai yasa akayi masa katangar langa-langa aka zagaye mana gurinmu.falle-falle guda biyu sai kicin da band'aki sai d'an guntun tsakargidan da ba zai isa mu yi kwanciyar zafi ba. PAID BOOK #500via 7084653262....Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. Masu tambayar wannan karon babu Vip ne . Zan yi amma a talgram kawai za mu kammala littafin cikin kwana goma ko 'kasa da haka da ikon Allah. Wad'anda suke bukata kuma suna yin talgram din sai su yi mini magana domin jin abinda za su biya. 'Yan Nijar kuma dala d'ari katin airtel sai ku yi magana da momina kai tsaye babbar macace don Allah a kula. *+227 88 13 77 40* *GARKUWAR MATA.* *BINTA ABBALE* [12/17, 8:51 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A* Na yi nisa sosai a arewa books *Binta Umar Abbale* https://www.arewabooks.com/chapter?id=67482a18ca3a075ba0996752 * *AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE* _Jama'a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau'i magungunan gargajiya masu kyau da inganci_ _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_ _nfection_ _Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯☑️*_ _Muna sayar da supplement gangariya irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._ *08089965176* *07084653262* 15&16. Cikin rufin asiri aka yi hidimar biki. Sai dai kuma azahar tana yi wani irin zazzafan zazzabi ya rufar mini. Tun ina jarumtar boyewa har ya kada ni. Hak'ora na suka dinga karo da juna. Anti Jummai Yayarsa itace ta fara lura da yanayina tunda sai kai kawo suke yi a tsakanin gidajen namu biyu. Ta saka hannu ta tab'a jikina ya had'a zafi ainun. Da azama ta fad'awa Nene aka rufu a kaina. Amma ina abu sai tsananta yake yi. Dole aka samo a daidaita sahu muka yi asabitin Murtala tare da Inna Hauwa da kuma ita anti Jummai. Kai-tsaye aka ba ni gado aka shiga ba ni taimkon gaggawa. Gabadaya jikin mutanan da suka cika gidan ya yi sanyi, ana hidimar biki amarya kuma tana gadon likita. Ganin gado aka bamu ya sanya Inna Hauwa komawa gida dan d'auko abubuwan da zamu bukata. Sai da magariba labarin ya samu Yaya Rabi'u. A sukwane ya isa asibitin. A lokacin na dan shiga hayyacina amma k'arin ruwa ake yi mini. A rikice yake fad'in "Jummai me ya sameta? Wanne irin ciwo ne da zai tashi ranar aurenta haka?" A sanyaye ta ce "Likita ya ce jininta ne ya yi k'asa. Sannan akwai zazzabin cizon sauro da ya tsananta a jikinta." Ya hura iska ya ce "Sallama ba yau ba ke nan?" Ta ce "E, to da alamu. Tunda ga wata allura da suka ce , idan an yi takwas na dare, takwas na safiya ma zasu yi mata wata". Ya saki gauron numfashi ya matso jikin gadon ya ce "Sannu Kulsum! Na kalle shi kawai. Domin yadda ya ce Kulsum din har raina na ji ya bambanta da yadda yake fad'a a baya. Ban iya bude baki na amsa ba. Domin gabadaya jikina ciwo yake yi mini ga rashin k'arfi. Ya ce "ikon Allah! Ana cikin hidimar farinciki sai kuma murna take neman komawa ciki. Idan kin san jikin da sauki kawai zan nemi sallama mu wuce gidanmu, an shirya komai abin sha'awa. Gobe da kaina zan nemo kwararriyar ma'aikaciyar jinya ta duba ki tare da saka miki ruwan da sukace za'a saka miki d'in" Ni dai da ido na bishi zuru. Ya ja kujerar gefen gadon ya zauna daf da gaban gadon. Har wajen goman dare yana tukure bai tashi ba. Tun kafin tara kuma Inna Hauwa ta dawo da shirgi kayayyaki. Ta zuba ido tana ganin rashin ta ido a wajen Yaya Rabiu. Ya kanannad'e komai. Da ta ga goma na shirin yi sai ta cire kawaicin da take yi ta ce "To tashi zan mu kwanta dare ya fara ja ". Ya mik'e ba tare da ya iya cewa komai ba. Ta kalli anti Jummai ta ce "Bi shi ku tafi ki kwana da yaranki. Idan Allah ya kaimu da safe kya zo". A sanyaye ta ce "To Inna. Allah ya bata lafiya." Ta amsa da ameen Jummai. Suka tafi na bisu da kallo ba tare da na iya ce musu k'ala kanzil ba. Domin nauyin da jikina ya yi har harshena. Yayin da Inna Hauwa ta dinga mita tana fad'in "Me za'a yi da halin wannan yaro. Allah ka rufa mana asiri kawai. Amma da ganin yadda idanuwansa suke a tsaye kyam tamkar nonon budurwar jiya, ba ta yau da duk a zube suke ba. Ba k'aramin artabu za'a yi da shi ba, ni kad'ai na gama nazarinsa kafaffe ne bayan rashin kunyar ma. Ta yi kwafa ta ja tsaki tare da cewa Malam Adamu bai kyauta mana ba, amma Allah yasa hakan ne alheri. Allah ya juyar da al'amarin zuwa kyakkywa." A zuciyata na ji babu dad'i. Domin damuwar da ya shiga ta isa tasa inna ta fahimci cewar ba cushe na aka yi yiwa Yaya Rabi'u ba. Kawai ya riga da ya saba da yin Abu a baibai. Duk naci da tambayar da Yayah yake yiwa likitoci da sauran ma'aikatan lafiya akan za'a iya kula da ni a gida bai sa sun sallame ni ba sai da na kwana uku. Sosai ka yi treatment din maleria. Na warware ina takawa tare da cin abinci. Ranar sallama kuwa shi so ya yi inna ta wuce da ni dakinsa. Yayin da ita ko kad'an hankalinta ma bai kai ga hakan ba. Har muka fito bakin asibitin yana ta dibi-dibi ganin yadda take rike da ni da tamau. Murya babu amo ya ce "Inna za ki wuce gidanki ne, ko sai mun fara zuwa can gidanmu?" Yana rufe baki ta ce "Kai Rabi'u wanne irin gabo ne kai haka? Na kwana uku da yarinyar a asibiti sannan mu fito ka yi tunanin na barta a titi nayi tafiyata, ko dai ka manta cewar cikinmu d'aya da uwatata ne? ka fitine ni, ka hana ni skaat da rashin ta ido Wallahi." Ya tumbatsa ya ce "Allahu ya huci zuciyarki Innarmu. Da wai ki wuce gida ki kintsa ki huta gajiyar zaman asibiti ne. Amma tunda baki fahimce ni ba, kin mini fahimtar da galibin jama'a suke yiwa Rabi'u to ki huce wa zai mance da matsayin surukursa ne Inna?" Ta sassauta fushin ta ce "Wa yasan maka. Ai al'amarin naka ne na ga yana nema ya zama iyashege. To bazan tafi na huta din ba domin kuwa ban gaji ba, ko cewa zasu yi mu koma sai bayan wata guda Wallahi ba zan k'osa ko na gaza ba". Da sauri ya ce "Haba Inna! Allahu ya Kyuata. Da ikon Allah ba zamu koma ba, daga nan sai d'akinta. Ai irin wannan abin ma da tausayi." Ta yi jagale ta kasa cewa komai. Kawai ta tsayar da adaidaita ta ce Magashi. Muka hau tare da wasu cikin kayanmu muka tafi, muka bar shi da wasu kayan a gabansa. A gida muka tarar da Babanmu. Ya dinga marabtarmu tare yi mana sannu gabadaya. Ni sannun ciwo ne, ita kuwa Inna sannun hidimar zama da ni ne. Cikin soyayya baba ya kalle ni ya ce "A a gawa ta ki rami. Da alamu kin fi ko wacce amarya zullimi tunda har kwanciya kika yi ranar aurenki. Allah ya baki lafiya. Sai hak'uri, gabadaya rayuwar ma hak'uri ce domin kalubalen da yake cikinta kabiran ne. Baka fita da ga wannan matsalar ba sai wata ta yanko maka. Ki tsananta addu'ar a sanya ki cikin bayi masu hak'uri domin shine jagoran dukkan arzikin duniya da lahira ". A sanyaye na ce "To Baba." Daidai lokacin Yaya Usman ya shigo hannunsa dauke da ledar lemo da ayaba. Kai tsaye gabana ya ajiye yana ce wa "Daga asibitin nake na tarar an muku sallama." Inna ta cafe da ce wa "Ai da basu sallamemu ba, da kaina zan nemi sallamar saboda azabar takura da Kwarzabar Rabi'u! Kai wannan yaro za'a yi azinanne". Baba na jin haka ya yi maza ya shuri takalmansa yana cewa "Ki gaida gida sarkin daru, yau dai ba zamu yi fad'a ba, kin yi dawainiya bai kamata bacin rai ya biyo baya ba. Amma lamarinki sai an daure. K'anina Maalam Hassan yana hak'uri kan hak'uri da ke". Ta ce "Wallahi Malam dawo mu yi fad'an, wacce hidima na yi? Dan uwa ta yi abin da ya kamata akan diyarta sai ya zama dawainiya? Dawo mu yi kawai, gara na fito na fad'a muku gaskiyar magana." Ya yi dariya ya ce "To tattara gaskiyar ki fad'awa y'arki, amma abin da nake so ki fahimta d'aya ne. Aure dai na riga na d'aura. Har zuciyata kuwa so nake ya wanzu har gidan aljanna. Idan kyauta ta ji maganta ta zauna da mijinta lafiya, ta ninka hak'urinta da kowa ya santa da shi, duk runtsi, duk wahala sai ta ga sakayyar alheri domin ta yi mini biyayya, ta kuma mutuntata aure. Amma idan ta je ta tsiro da halayen banza dan tana jin kuna kushe dab'iun mijinta, to ta sani fa itama zata ga ba daidai ba. Domin Ubangiji da kansa ya girmama sha'anin aure, ya d'aga darajar miji akan mace. Ina rok'onku, ku fad'a mata hak'uri da juriya ne kawai a cikin ko wanne aure amma dad'insa kalilan ne." Daga haka ya fice daga gidan gabadaya. Daga Nene har Inna kowa bakinsa ya mutu murus. Yaya Usman ne ya ce "Allah yasa alheri mai yawa ya biyo baya. Sannu KYAUTA". Da kai na amsa shi tare da daukar ayaba na yi Bismillah na fara ci. Ana haka Yaya Rabiu ya yi sallama ya shigo.da tarkacen kayan da muka bar masa. Ya gaida Nene cikin mutunci, ya kalli Inna ya ce "Kun iso lafiya?" Ta amsa da lafiya lau Alhamdulillah". Ya sassauta murya ya ce "Sannu Kulsum, ya k'arfin jikin dai?" Murya babu amo na ce"Da sauki". Ya mik'e yana addu'ar samun dauwamemmen sauki. Sannan ya tafi. Sai da aka yi sallar la'asar Inna Hauwa ta tafi gidanta tare da shirgin kayanta da na biki. Kwana biyu da sallamo ni, lafiya lau nake jina, amma gabad'aya jikin nawa babu k'arfi. Da na yi tafiya zan ji na gaji. Ganin hakan Baba ya jinkirta tariya. Ya hak'ura ya bar ni sai na ji k'arfin jiki. Kullum kuma sai Yaya Rabi'u ya zo ya duba ni. A kwana na uku ya sassauta murya ya ce "kyauta kina da wata matsala ne da jikinki?" A hankali na ce "kamar ya ya?" Ya gyara tsayuwar da ya yi ya ce "To me kike yi a nan gidan. Ai ke Malama ce kinsan dai babu kyau a daura auren yarinya ta cigaba da zama a gidansu. Kin wani saki jiki kina ta marairaicewa. Ki tsananta jikinki, a saka ranar tariyar nan kyauta. Bar ganina haka nima na iya jinya da rarrashi sosai fa". Na yi dariya na ce "Yayah ke nan. Ina na rufe baki sai ji na yi ya saki baki ya ce "Kin san Allah akan gadonmu zan kwantar da ke na dinga bin sashe sashe ina yi miki tausa a hankali, ina kuma dunbular abin da yake tsole mini ido." Gabadaya na ji na rikice, kunya ta ban mamaki ta yanko mini. A kidime na ja jikina na shige cikin gidan. Ya bude murya yana kirana da yake baifi taku biyar ba tsakanin zauren da tsakar gidan tunda gidan k'arami ne. "Kyauta ki dawo ban fadi abin da na zo fad'a miki ba ai". Nene da ke zaune a rumfa ta yi kamar bata fahimci yanayin da na shigo da shi na kunya na shige uwar dakin ba. Ga shi ya bude murya yana kirana babu ko kunyar gidan surukai yake. Yana tsaye Ibrahim ya shigo zauren ya same shi. Suka gaisa. Sama-sama ya ce "Ya ka tsaya, ka shiga mana". Rabiu ya dauke kai ya ce "Ban gane ba, kada ka mayar da ni wani irin mana, shikenan bazan yi kunyar surukuta ba. Kawai idan ka shiga ka turo mini ita, ban gama fad'a mata kalaman bakina ba ta tsere ta bar ni.". Yaya Ibrahim ya jijjiga kai ya nuna kansa ya ce "Ni zaka aika na kira maka Kyauta Rabe?" Ni ban zama surukinka ba ashe, wanne irin raini ka yi mini ne?" Ya dauke kai ya ce "To ina ce kai abokina ne, kuma gaskiya kada ka sake ce mini Rabe! Ka sani, bana so, nifa Wallahi zan had'aka da Baban titi ya mana iyaka, ka bala'in matsa mini, tun sadda aka fara maganar aurena da Ummu Kulsum." Ibrahim ya yi sakare yana kallonsa domin ya yi zaton auren da aka yi masa da kyauta zai sa Rabi'u ya sassauta ya rage rikice masa da gangan. Suna haka Baban titi ya shigo ya ce "Halan yau ma cece kuce kuke yi." Nan da nan Rabi'u ya ce "Yauwa Baban titi raba ni da Ibrahim ya matsa mini akan me zaice mini shu surukina ne, ba nine babba ba? Ance kwana araba'in na ba shi. To akan me zai titsiye ni wai sai na girmama shi akan shi yayan Kyauta ne. Ko Yaya Usman da ya yi mini fiko mai yawa bai mini hakan ba. Gaskiya ya rage shiga hancina". Ya fad'a da sigar damuwa. Baban kuwa ya ce "Ibrahim ka daina zungurar Muhammad Rabi'u. Ba d'an uwanka ba ne? Ai ba auren kyauta ne ya had'a ku ba. Bana son rashin gaskiya." Kan dole Ibrahim ya ce "To Baba zan kiyaye." Ya juya ya tafi yana gunagunin takaici wanda na takaici yadda ba wanda ya ce masa ga ranar tariya. Kaitsaye gidansu ya afka, babu sallama. Inno ta ganshi tamkar jifa sai huci yake yi. Ta sassauta ta ce "Menene kuma kai da har yanzu ba zaka daina fad'a irin na kumfar baki ba." Tana d'isa aya ya ce "Inno na rantse ban tab'a ganin kaskantaccen ango Irina ba. Ta yaya za'a daura mini uare a saka ni kama gida, aje kuma a shirya shi, sai kuma a barni ni kad'ai? Na tabbatar ko kema ba ki tab'a ganin hakan ba." Tsaki ta ja tare da mikewa ta bar shi tana fad'in shasha marar kunya kawai! Ya yi sak'alo yana ayyana menene abin da ya yi na rashin kunya? Ya make kafadarsa ya fito ya yi waje cikin kunci mai yawa. ** Muna zaune a tsakar gida Nene na yin kad'ai da yake tana yin lagwanin risho Babanmu da Yaya Ibrahim suna tafiya mata da shi kasuwa, suna siyarwa. Ta kalle ni ta ce "Yau dinma sai na ce ki debo maganin sanyin ki Sha? Wai ke wacce irin yarinya ce haka da ba Kya son magani? Kina dai Jin yadda innarki Hauwa ta fad'i kyawun maganin da ta yi kundubalar siyowa ta kawo miki, amma sai fama nake da ke ki sha. Shiyasa ban yi asarar kudina ba. Tunda ga wanccan hakkin dakan ma ki diba ki sha da madara amma kin k'i dad'in azanci. Na kyale ki, itama Hauwan ta ce na kyale ki, zaki nema da kanki ne." Na yi k'asa da kaina domin tunda na fahimci amfanin hakkin dakan da take dirka mini nake jin matsananciyar kunyar na sha a gabanta. Gara na sanyi na kan sha, kawai ni ina cikin jerin mutanen da basa son magani ko wanne irin ne. Amma tabbas idan na sha na sanyin ina jin dad'in marata dama jikina, tunda hatta fitsarina canjawa yake yi. Haka kazar da aka dafa da Saiwowin chadi na cinye duk da dai ba ta dad'i ba ce, amma kuma bata da bauri ko kad'an. Ku tuntubib wannan lambar 08032773332 don samun naku maganin sanyin sahihi cikin farashi mai rangwame. Ba iya maganin sanyi ba, dukkan kayan gyara akwai wanda ake kawosu daga Chad. A daren wannan ranar Baba ya ce gobe da yamma za'a raka ni dakina. Ina dakina na ji wani irin matsananciyar faduwar gaba a dalilin maganar tariyata. Haka kawai nake shiga rudu da fargabar zan kad'aice daki d'aya da Yaya. Tunda aka Shafa mana fatiha yake sakin maganganu masu kunyatarwa da sanya fargaba a zuciyar budurwa mai karancin wayewa Irina. Na kwanta na dunkunkune ko sallar isha sai tsakiyar dare na tashi na yi. Da safe haka na tashi salo salo babu kuzari. Nene ta hau sababin yau ko suma nake yi sai an kai ni dakina ta gaji da iskancina da kuma rashin kunyar Rabe. Na je na yi jinyar a dakina. Baba dai bai ce komai ba. Shi kuwa Yaya da hantsi ya bugo mini waya. Ina dauka sai cewa ya yi "Tsire za'a tanadar miki ko kaza?" Zullumin da nake ciki ya sake hauhawa. Na kasa ce masa kanzil. Ya numfasa tare da ce wa "Kyauta ki fahimce ni fa. Ni gaskiya bana son ki zo kina mini gidadanci irin haka? Na tambaye ki, kin mini shiru. Menene abin kunya a wnanan maganar fisabillahi?" Ya yi k'aramar tsaki ya kashe wayarsa. Ya bar ni da tawa a kunne. Ana yin azahar sai kawai labari ya iso mana Inno ta yanke jiki ta fad'i an tafi kaita asibiti. A gigice Nene ta shirya ta bi bayansu. Har zuciyata na ji rashin dad'in abinda ya faru. Amma kuma na samu salamar zullimin tariyar da zan yi a yammacin yau, tunda ta lafiyar Inno ake yi tukun. Ni kad'aice a gida har magariba Nene bata dawo ba. An idar da sallar Isha sai ga Yaya Rabiu ya shigo. Ya zauna a akan turmin da nake zaune. Fuska babu walwala. Murya babu amo ya ce "Anya kyauta taurarona da na ki ya had'u? Ta yaya al'amari irin haka zai dinga gittowa da zarar za'a kai ki dakinki? Jikina ya yi sanyi akan yadda ya yi maganar da take nuni yana da malamai da suke fad'a masa ililimin falaki a karkace. Wai tauraronmu bai had'u ba. Dariyarsa ta nemi kwace mini. Amma nasa k'arfin tuwo na gintseta domin idan na yi sai ta zamo wani abin daban. Tunda na sha ganin rikicinsu da Yaya Usman akan ya yi masa dariya. Kawai zuba masa ido na yi. Ina kallon sa cikin kaduwa ainun. Ya tsargu ya ce "Ki kalle ni da kyau. Na san kina mini kallon rainin ajawali ne. Ni kuwa har zuciyata na karaya da ke. Idan kinsan canka cakare haka kike zame mini. Ta Yaya za'a ce ranar daurin aure jinya ta rafke ki, sannan an saka ranar tariya uwata ta fad'i ta samu karaya a hannu. Sannan an zo har rumfata an sace mini buhun gawayi, ai kinsan ana alamta mini ba zan kwashe k'alau a cikin sabgarki ba". Idon dai na cigaba da zura masa cike da madaukakin mamaki. "Ki cigaba da bina da kallon izgili da sannu Ubangiji zai warware mini komai. Amma yadda na shaida Annabi manzon Allah ne haka na shaida taurarinmu basu jitu ba.! Ban tab'a jin labarin ango irina da ba'a tashi jarraba shi sai ranar aurensa da tariya. Idan kuwa ansan kina da jinnul ashiq a fito a fad'a mini domin ina da bulalar bugun ko wanne irin makirin jinni ke har ma da mugayen insu da suke yiwa jinni sharri a gamsu da su". A wannan karon kam dariyar k'arfi ta gwada mini ta k'wace da k'arfin gaske. Dan haka na dinga kyalkyalewa har sai da na kwanta akan tabarma da nake zaune. Yayin da ya yi suntum tamkar kububuwa. A haka Nene ta dawo ta samemu. Sai dai yadda ta ga ina dariya ga Yaya Rabiu yana cikin matsanancin fushi sai jikinta ya yi sanyi. Ta zauna tana fad'in "Bismillahi! Ta kalle ni ta ce wacce irin dariya kike yi da ta wuce ka'ida haka?" Ya sake harzuka ya ce "Da ni take Nene. Kuma Wallahi komai zai faru bazan yarda da wananan wulakanci nata ba. Sai Baban mai keke da Baban titi sun yi mana shari'a. Ba zan iya ba. Tabdi jam ni Rabi'u zata hiwa haka?" Ya fad'a yana nuna kansa. Cikin rarrashi Nene ta ce "Ban da abinka Rabiu menene na kai k'ara tun baku fara zama ba? Ai kowa ce wa zai yi baka da juriya. Sha'anin mace kuwa sai anyi hak'uri da juriya. Kada ka sake ka zama mai saurin kai k'ara. Ke kuma ba shi hak'uri ai kowa baya son dariyar shegantaka irin haka. Na yi maza na ce "Yaya Rabi'u yi hak'uri. Ka gafarce ni". PAID BOOK #500via 7084653262....Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. Masu tambayar wannan karon babu Vip ne . Zan yi amma a talgram kawai za mu kammala littafin cikin kwana goma ko 'kasa da haka da ikon Allah. Wad'anda suke bukata kuma suna yin talgram din sai su yi mini magana domin jin abinda za su biya. 'Yan Nijar kuma dala d'ari katin airtel sai ku yi magana da momina kai tsaye babbar macace don Allah a kula. *+227 88 13 77 40* *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE* [12/18, 8:57 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A* 52/HARVERT NETWORKING BUSINESS *ALHERI NE 💃💯* Ina masu sha'awar shiga shahararren kasuwancin nan wato 52U basu da hali? Ga dama ta samu SZARIA tazo maku da sabon tsari domin taimaka ma marasa 'karfi, wato TEAM WORK. da kud'in ki 'kalilin zaki samu abunda zaki taimaki kanki da 'ya'yan. Domin 'karin bayani ku tutubi wanan number 08037930727 https://chat.whatsapp.com/CSQ94ZeYnPJ26ppXhBnRII Na yi nisa sosai a arewa books. *Binta Umar Abbale.* https://www.arewabooks.com/chapter?id=67482a18ca3a075ba0996752 17&18 Ta sassauta ta ce "Menene kuma kai da har yanzu ba zaka daina fad'a irin na kumfar baki ba." Tana d'isa aya. Ya ce "Inno na rantse ban tab'a ganin 'kaskantaccen ango Irina ba. Ta yaya za'a daura mini aure a saka ni kama gida, aje kuma a shirya shi tsaf sai kuma a barni ni kad'ai? Na tabbatar ko kema ba ki tab'a ganin hakan ba." Tsaki ta ja tare da mikewa ta bar shi tana fad'in shasha marar kunya kawai! Ya yi sakato yana ayyana menene abin da ya yi na rashin kunya? Ya ma'ke kafad'arsa ya fito ya yi waje cikin kunci mai yawa. ** Muna zaune a tsakar gida Nene na yin kad'ai da yake tana yin lagwanin risho Babanmu da Yaya Ibrahim suna tafiya mata da shi kasuwa, suna siyarwa. Ta kalle ni ta ce "Yau d'inma sai na ce ki d'ebo maganin sanyin ki sha? Wai ke wacce irin yarinya ce haka da ba Kya son magani? Kina dai jin yadda innarki Hauwa ta fad'i kyawun maganin da ta yi kundubalar siyowa ta kawo miki, amma sai fama nake da ke ki sha. shiyasa ban yi asarar kud'ina ba. Tunda ga wancan hakkin dakan ma ki diba ki sha da madara amma kin k'i dad'in azanci. Na kyale ki, itama Hauwan ta ce na kyale ki, zaki nema da kanki ne." Na yi k'asa da kaina domin tunda na fahimci amfanin hakkin dakan da take dirka mini nake jin matsananciyar kunyar na sha a gabanta. Gara na sanyi na kan sha, kawai ni ina cikin jerin mutanen da basa son magani ko wanne irin ne. Amma tabbas idan na sha na sanyin ina jin dad'in marata dama jikina, tunda hatta fitsarina canjawa yake yi. Haka kazar da aka dafa da Saiwowin chadi na cinye duk da dai ba ta dad'i ba ce, amma kuma bata da bauri ko kad'an. Ku tuntube Surayya Halin Yau akan wannan lambar 08032773332 don samun naku maganin sanyin sahihi cikin farashi mai rangwame. A daren wannan ranar Baban titi ya ce gobe da yamma za'a raka ni dakina. Ina kuryar d'akin Nene na ji wani irin matsananciyar fad'uwar gaba a dalilin maganar tariyata. Haka kawai nake shiga rudu da fargabar zan kad'aice daki d'aya da Yaya Rabi'u Tunda aka shafa mana fatiha yake sakin maganganu masu kunyatarwa da sanya fargaba a zuciyar budurwa mai karancin wayewa Irina. Na kwanta na dunkunkune ko sallar isha sai tsakiyar dare na tashi na yi. Da safe haka na tashi salo salo babu kuzari. Nene ta hau sababin yau ko suma nake yi sai an kai ni dakina ta gaji da iskancina da kuma rashin kunyar Rabe. Na je na yi jinyar a dakina. Baba dai bai ce komai ba. Shi kuwa Yaya Rabi'u da hantsi ya bugo mini waya. Ina dauka sai cewa ya yi "Tsire za'a tanadar miki ko kaza?" Zullimin da nake ciki ya sake hauhawa. Na kasa ce masa kanzil. Ya numfasa tare da ce wa "Kyauta ki fahimce ni fa. Ni gaskiya bana son ki zo kina mini gidadanci irin haka? Na tambaye ki, kin mini shiru. Menene abin kunya a wannan maganar fisabillahi?" Ya yi k'aramar tsaki ya kashe wayarsa. Ya bar ni da tawa a kunne. Ana yin azahar sai kawai labari ya iso mana Inno ta yanke jiki ta fad'i an tafi kaita asibiti. A gigice Nene ta shirya ta bi bayansu. Har zuciyata na ji rashin dad'in abinda ya faru. Amma kuma na samu salamar zullimin tariyar da zan yi a yammacin yau, tunda ta lafiyar Inno ake yi tukun. Ni kad'aice a gida har magariba Nene bata dawo ba. An idar da sallar Isha sai ga Yaya Rabiu ya shigo. Ya zauna a akan turmin da nake zaune. Fuska babu walwala. Murya babu amo ya ce "Anya kyauta taurarona da na ki ya had'u? Ta yaya al'amari irin haka zai dinga gittowa da zarar za'a kai ki d'akinki? Jikina ya yi sanyi akan yadda ya yi maganar da take nuni yana da malamai da suke fad'a masa ililimin fala'ki a karkace. Wai tauraronmu bai had'u ba. Dariyarsa ta nemi kwace mini. Amma nasa k'arfin tuwo na gintseta domin idan na yi sai ta zamo wani abin daban. Tunda na sha ganin rikicinsu da Yaya Usman akan ya yi masa dariya. Kawai zuba masa ido na yi. Ina kallon sa cikin kaduwa ainun. Ya tsargu ya ce "Ki kalle ni da kyau. Nasan kina mini kallon rainin ajawali ne. Ni kuwa har zuciyata na karaya da ke. In da ki ka san canka cakare haka kike zame mini. Ta Yaya za'a ce ranar daurin aure jinya ta rafke ki, sannan an saka ranar tariya uwata ta fad'i ta samu karaya a hannu. Sannan an zo har rumfata an sace mini buhun gawayi, ai kinsan ana alamta mini ba zan kwashe k'alau a cikin sabgarki ba". Idon dai na cigaba da zura masa cike da madaukakin mamaki. "Ki cigaba da bina da kallon izgili da sannu Ubangiji zai warware mini komai. Amma yadda na shaida Annabi manzon Allah ne haka na shaida taurarinmu basu jitu ba.! Ban tab'a jin labarin ango irina da ba'a tashi jarraba shi sai ranar aurensa da tariya. Idan kuwa ansan kina da jinnul ashiq a fito a fad'a mini domin ina da bulalar bugun ko wanne irin makirin jinni ke har ma da mugayen insu da suke yiwa jinni sharri a gamsu da su". A wannan karon kam dariyar k'arfi ta gwada mini ta k'wace da k'arfin gaske. Dan haka na dinga kyalkyalewa har sai da na kwanta akan tabarma da nake zaune. Yayin da ya yi suntum tamkar kububuwa. A haka Nene ta dawo ta samemu. Sai dai yadda ta ga ina dariya ga Yaya Rabiu yana cikin matsanancin fishi sai jikinta ya yi sanyi. Ta zauna tana fad'in "Bismillahi! Ta kalle ni ta ce wace irin dariya kike yi da ta wuce ka'ida haka?" Ya sake harzuka ya ce "Da ni take Nene. Kuma Wallahi komai zai faru bazan yarda da waanan wulakanci nata ba. Sai Baba mai keke da Baban titi sun yi mana shari'a. Ba zan iya ba. Tabdi jam ni Rabi'u zata yi wa haka?" Ya fad'a da zuzutawa! Cikin rarrashi Nene ta ce "Ban da abinka Rabiu menene na kai k'ara tun baku fara zama ba? Ai kowa ce wa zai yi baka da juriya. Sha'anin mace kuwa sai anyi hak'uri da juriya. Kada ka sake ka zama mai saurin kai k'ara. Ke kuma ba shi hak'uri ai kowa baya son dariyar shegantaka irin haka. Na yi maza na ce "Yaya yi hak'uri. Ka gafarce ni". Rausayar da kansa ya yi, bai ce mini komai ba illahi bin jikina da kallo da yake yi. Kunya ta rufe ni, na kalli Nene da sauri sai na ga hankalinta ma gabad'aya ba ya kanmu. A hankali na ce." Ya Rabi'u ka tashi ka tafi don Allah." Ya nisa kafin a hankali ya furta." Balangu kike so ki tsire?" Shiru na yi masa saboda takaici. Ya sake yin kasa da murya. "Kyauta wai ba kya jin abinda nake ji, a matse fa nake." Gabana ne ya fadi, ya juya na kalleshi ya kura mini ido. Nene ta zo ta gifta mu ta shige d'aki. Ya sake kusanto ni kamar zai rungume ni. Kuka nasa na ture shi da saurin gaske. Sai ya tashi yana dariya tare da fad'in ." Yarinya yau za ki fadawa 'yan garinku." Gabana ya tsananta bugawa. Gabad'aya na kasa had'a ido dashi. Ya ce." Ni na tafi na kimtsa kaina." Ban ce masa komai ba, ya 'kwalawa Nene kira tare da yi mata sallama. Bayansa na bi da kallo jikina duk a sabule. Na zame na kwanta kan tabarmar fargaba ta ishe ni. Haka na yini sukuku jiki babu kuzari. Da yamma ciwon cikin da nake yi ya rufe ni, na dinga matagugu kafin jinin ya fara zuba. Inna Hauwa ta ce kawai a daga tariyar tunda ba ni da lafiya ga kuma wannan abu da ya yi dirar mikiya. Farincikina ya koma ciki lokacin da Baban titi ya shigo ya tabbatar da maganar tariyar babu fashi. Sai kawai na 'kunshe kaina a d'aki na dinga rizgar kuka. Da kyar inna Hauwa ta rarrasheni, na yi wanka na sanya sabuwar atamfar da Nene ta dinka mini. Muka zauna muna jiran zuwan Gwaggwo Hansatu, da Habiba wandanda suka kasance 'yan'uwan baban titi na jini. Tsabar takaici har kuka sai da na yi saboda abinda Yaya Rabi'u ya yi mini na rashin kawo mota a d'auke ni don ya ga babu nisa da kafafu na je. Sai da suka kai ni wurin matar gidan suka d'amka mata amanata sannan suka yi mini sallama suna jaddada mini kyautata ha'kuri da juriya. Na tattare jikin wuri d'aya hawaye na tsiyaya. Ya shigo da karsashi da kwarin guiwa.Na kalleshi yana cire babbar rigar jikinsa. Ya ke cewa" Wata rayuwa ce sabuwa muka tsinci kanmu Kyauta, shi fa auran nan da ki ke ganinsa rahama ne wallahi, ni'ima ne ai annabi ya yi gaskiya da ya ce ku yi aure da 'kuruciyarku domin ku more rayuwa!." PAID BOOK #500via 7084653262....Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. Masu tambayar wannan karon babu Vip ne . Zan yi amma a talgram kawai za mu kammala littafin cikin kwana goma ko 'kasa da haka da ikon Allah. Wad'anda suke bukata kuma suna yin talgram din sai su yi mini magana domin jin abinda za su biya. 'Yan Nijar kuma dala d'ari katin airtel sai ku yi magana da momina kai tsaye babbar macace don Allah a kula. *+227 88 13 77 40* *Domin jin yadda take kasancewa dari biyar ne, za ki biya a saki a guruf, kamar yadda na fad'a da farko akwai tsarin manya wato special za mu kammala littafin cikin kwana bakwai in sha Allahu rabbi. Amma a talgram za mu yi. Ga duk wadda take da buk'ata sai ta yi mini magana. Sannan ka'ida ne dama duk masu bibiyata sun san cewa Idan na gama littafi ya zama complete dubu daya ne, kada ki zo saye ki ce kin ga an sa dari biyar a jiki, lokacin da nake posting din pege by pege ne. Ubangiji Allah Ya yassare ya baku ikon saye. Na tabbata dai daga farkon shimfidar labarin kun sheda tafiyata ta wannan karon ta bambamta data sauran, dukda cewa ina ta'bo al'amura da dama na yi rubutu akai, amma dai wannan tafiya ce, mai hargitsi tare da dambarwa. Sha'anin Rabi'u ba'abore da matarsa Ummu-kulsum Kyauta, wani lamari ne mai sosa zuciya. Ku dai kasance da ni. Domin jin yadda za ta kaya. Hanyoyi biya gashi can a sama, idan kina da matsalar acct sai ki yi mini magana domin na gaya mini irin katin da nake so ki turo mini. Na gode sosai💯🙏🏻* *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE* [12/19, 9:18 AM] Bintu: *BA A BORAN NAMIJI!!* *NA* *BINTA UMAR ABBALE 🍒* *M.W.A* Na yi nisa sosai a arewa books *Binta Umar Abbale* https://www.arewabooks.com/chapter?id=67482a18ca3a075ba0996752 *ADVERT* Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/JrVGCbG7R8SFurApPbPilB *SAMIES KITCHEN* The Best Chartering Service🥗🥘. *KANO STATE: NO4 ZOOROAD HOUSING ESTATE* *Jama'a Samies kitchen wurin fita kunya ne da kece raini. Wuri ne ingantace da ya amsa sunansa domin sharewa ma'abota karamci hawaye a yayin da wata hidima ta same su. Bari na jaddada muku SAMIES KITCHEN Ya samu sheda da lambar yabo gurin cika alkawari da karrama jama'a. Kada na cika ku da surutu bari na tafi kai tsaye domin sanar daku ainihin abinda ya sa nake kwad'aita muku 'kulla alaka da su. Wato SAMIES KITCHEN sun 'kware wajan shirya girke girke na gida dana waje. Sun yi shura wurin 'karbar order daga kowane sassa a fad'in Najeria. Suna yin abincin biki, abincin suna, abinci taro, abincin saukar al'kur'ani, order domin yin Birthday. Sun gwanance sosai wurin yin cima iri-iri da kayan ma'kulashe duk domin fita kunyar abokan hurd'arsu. Sannan ba su tsaya iya nan ba suna hada-hadar sayar da manya manyan leces 'kananu da manya kowane irin na'ui. Suna bud'e dilolin leces irin namu na gida (mama ta mutu) kala daban daban. Ana samun kayansu da inganci tare da farashi mai sau'ki. Domin neman karin bayani sai a tuntubi wannan lambobin.* *08173037544 ko 07044417448* *Wannan shine 'karshen shafukan da zan ba ku kyauta. Ubangiji Allah Ya yassare ya ba ku ikon saye. Domin karanta dambarwar da take faruwa a gidan Rabi'u ba'abore! sai a duba k'asan shafin na yi bayanin yadda za a biya kudin karatu. Rabi'u ya ce ya gode da 'kaunarku a gare shi🤣😂 Ya ce a sanar da ku bai yi komai ba amma kuke masa fatan mutuwa. Ya 'kara da cewa na jadadda muku shi da abar kaunarsa Kyauta mutuwace za ta raba su, don bai ga dalilin da zai sanya ya rabu da matar rufin asirinsa ba☺️* *Masu amfani da manhajar arewa books za su iya zuwa can su karanta littafin domin na yi nisa a can din.* 19&20 Na yi bakam! Ina satar kallonsa yana sambatu, shi ko rakiyar abokai ma babu shi kad'ai ya tawo abinsa. Ya kunna wayarsa yana haska fuskata. Da sauri na juyar da kaina gabana na cigaba da tsalle. Yaya Rabi'u ne gabad'aya yau ya canza mini, tsoronsa nake ji. Zuciyata ce ta yi sanyi dana tuna cewa duk zulamarsa dole ya barni dalilin abinda nake tattare dashi. Ya kira sunana a tsanake. Kyauta." Na ce."Umm!" Sai ya sauke ajiyar zuciya da 'yar wata dariya irin ta murna yana fad'in." Yanzu nan zan sayi bakin nan, bari mu yi sallar godiya ga Allah tukkuna. Ban ce masa ba na yi ba. Na rabu dashi ya je, ya yi, alwala ya dawo ni ma na je na yi. Na bishi muka yi sallar. Na nisa na fashe da dariya duk da a cikin 'bacin rai da hawaye sha'be-sha'be nake hakaito tushen rayuwarmu sai da na murmusa. Wato a dukkan tsayin rayuwata ban yi abin da yake damuna kuma ya sanya ni dariya mai yawa irin sallar da na bi shi muka yi ba ni da tsarki ba. A wanccan lokacin tsoro da kuruciya ya sanya na yi hakan. Dariya ta sosai ta k'wace mini. Domin sababi da sakacin da muka da yi a daren farkon namu ba kad'an ba ne. Komin bacin ran da nake ciki idan na tuna wannan dare sai na murmusa ko kad'an ne. Sai da na nutsu na juya na kwanta sosai na cigaba daga inda na dakata. Na takure a gefe guda. Yayin da shi kuma ya matsu ya takura mini akan mu kwanta. Ya yi kundubalar sanya hannu ya daga ni, ya kai ni kan gadon, tare da zare mini hijabina. Nan da nan na saka hannu na rungume kirjina domin duk yadda nake da shi ba zan iya tuna yaushe ya gan ni ba tare da hijabi ba. Kullum cikin yi mini mita yake wai kamar matar limamin gari. Kan akwatinana ya dora hijabin bayan ya ninke. Duk yadda na takure hadi da kankame jikina bai fasa mannuwa da ni ba. Da na ga dai shafar da yake yi mini ta tsananta ya sanya na ture shi gefe ina 'barin jiki tare da ce wa "Ba ni da tsarki fa Yaya Rabi'u". Ya yi galala ya numfasa ya ce "Mai karya d'an wuta ne Kyauta. Ki kwantar da hankalinki ba abin tashin hankali zamu yi ba, domin dai iyayenmu ne suka hadamu daki d'aya, wannan kad'ai ya isa ki gane girman sha'anin aure. Kada ki janyowa kanki tsinuwar malaiku, ai ke Malama ce, ta ya ya zaki bini sallah bayan baki da tsarki? Kin san wanda ya yi sallah ba tare da tsarki ko alwallah ba ya kafirta." Yana rufe baki na rushe da matsanancin kuka mai sauti tare da ce wa "Ashadu Allah illahu wa ashhadu anna muhammadir rasulillahi. Allah ka karbi musuluntar da na yi"! Na tsananta kukan da nake yi. Bak'in cikin da Yaya Rabiu ya shiga ya wuce misali. A dalilin ya gamsu ba karya nake yi ko iyashege ba ne. Cikin fishi ya ce "Za ki mini shiru ko kuwa sai kin ankarar da mutanan gidan halin da muke ciki alhalin ba komai ne yake wanzuwa a tsakaninmu ba, sai tsantsar bakin ciki. Na rantse da buwayi gagara misali Kulsumu tauraronmu bai jitu ba, alamu sun gama bayyana 'kashinmu ba su daidaita ba, haba jama'a Ibtila'i da bacin rai sai rufto mini suke yi daga wannan sai wannan. Babu wani abu da na tsinta a cikin hadin auren nan sai bacin rai. haba, haba, tunda aka daura auren nan kullum da abin da zai yanko na musiba. Ban tab'a cin karo da labarin ango mara sa'a ba Irina ba." Ya numfasa ya yunkura da nufin yin magana na sake rushewa da kukan da yafi na farko. A dalilin na ji haushin maganganunsa da babu sassauci da tauhidi a cikinsu. Tsawon lokaci ina kukana kamar ba zai tanka ba, sai kuma ya nisa ya ce "Ki duba darajar Ma'aikin da alkur'ani da k'imar Baban Titi ki mini shiru." Jikina ya yi sanyi domin kuwa ya dabaibaye ni da girman kalamansa. Na sassauta kukan na gyara na cure gefe tamkar alkaki na kwanta, ina ta sakin ajiyar zuciya. Maimakon na ji ya kwanta, sai na ga yana ta zagaye a dakin tamkar dai mai yin sa'a'yi nan da ake fad'a mana yana cikin rukunan aikin hajji. Ya jima yana yi, kafin ya zauna a gefen gadon yana gunji mai kama da kuka. Na dinga satar kallonsa ta kafar mayafina, gabad'aya ya diririce sai cije bakinsa yake yi kamar dan tauri Tsorona ya sake ninkuwa! Kafafu da hannayena suka dinga rawa. Sai kawai na fara kiran wallahu galibun ala amri, a wautata Allah ya ba ni rinjaye a kansa kada ya yi mini komai. Sake makurewa na yi a can karshen gado gabana na lugudan daka. Zumbur ya yi, ya juyo. Sai ni ma na zabura da sauri na tashi tsaye tare da rungume kirjina da hannuwana. Gadon ya hayo sosai Yana fad'in." Ba zan iya ba Kyauta, ba ni da karsashi da kumaji a wannan lamarin. Dole sai kin tagaza mini, na kai na kawo ina neman d'auki. Baki na bude sosai na fara kuka ina fad'in." To ni me zan iya yi maka bayan kasan hakan haramun ne, ka dai yi ha'kuri na yi tsarki tukkuna ." Ya sake kusanto ni yana kiciniyar cire hannuwana dana rufe kirjina. "A'a kyauta ke fa Malama ce ba sai na yi miki dalla-dalla ba, akwai dabaru idan ma ba ki iya ba zan koya miki." Cikin fargaba na ce." Ni dai ka yi hakuri ka daure ai kwana hud'u nake yi zuwa sati babu yawa." Daidai lokacin dana kai k'arshen maganata na ji saukar hannunsa a kirjina. Na 'kwala ihu! Ina ko'karin dira kasa. Ya janyo ni yasa a tsakanin kafafunsa. Jikinsa Yana kyarma yake cewa." Muddin ba ki kawo d'auki ba numfashi zai yi 'kaura daga gangar jikina. Kyauta ji na yi kamar kin buga mini guduma a tsakiyar kaina da kina fad'in na yi ha'kuri, ai ko awa d'aya ba zan bari ba ballanatana sati d'aya, ki 'kyale ni na mutsike wad'annan abubuwan, idan da hali ma ki tallafi kaina ki shayar da ni kafin zuwan abinda zamu haifa." Dojewa na dinga yi ina dukan hannuwansa da yake ta cusa mini a cikin riga. Kuka nake yi sosai ina fad'in." Don Allah ka bari wallahi idan ina cikin wannan halin ciwo suke yi mini ko wanka na zo yi a hankali nake ta'ba su." "Kyauta ba fa zan bari ba, dole ne na nemo miki maganin girmansu domin ba suka kai ga cika mini hannuwana ba." Ihun! hauka na shiga yi ina ture shi. Ya yi mini rikon tsauri! yana ta cusa hannunsa a rigata har sai da zif din ya zuge! Nishi yake yi! kamar zautacce yana ta sakin zantukan da basu da tushe ballanatana makama. Na dinga kuka ina rokonsa ya bari domin har ga Allah zafi suke yi mini, amma kamar turi! jikina ya matu saboda ko-kaye-koyen da muka yi. Gashi dama ban jima da tashi daga ciwo ba. ina jinsa yana fad'in.''Kyauta ki tallafi kaina ki shayar da ni mana." Wani takaici ya tsaya mini a wuya. Na dinga mintsinsa a cinyarsa amma ko gazau! sai da ya mutsike mini kirji son ransa sannan ya cika ni. Ya sauka daga gadon. Jikina ya yi laushi bayan fitarsa na takure ina shar'bar kukan takaicin rashin imanin da ya gwadawa 'kirjina. Kuka ya shigo ya same ni ina yi. Ya kunna fitilar d'akin sannan ya zauna kusa da ni. Da sauri na juya masa baya. Birkito ni ya yi yana fad'in." Ni ne fa zan yi kuka kyauta amma ban yi ba na daure to meye a ciki don na tattaba abinda ya fi soyuwa a raina. Ni fa a Hakan ma ba wani garau na ji ba, na dai yi maleji ne. Kuma na fad'a miki zan samo miki maganin da zasu zama dumbula- dumbula, ba zan rufe ki ba abinda nake so kenan a jikin 'ya mace." Cikin kuka na ce." To ni ina ruwana, ni ba wani magani da zan sha domin su 'kara girma a haka Allah ya yi mini su." "To ni sun yi mini 'kan'kanta, domin duk a zatona sun fi haka cika Ashe beriziya ce mai koko." Cikin zubar hawaye na d'auki fillo na jefa masa ina mamakin bud'ewar idonsa. Hannunsa ya mi'ko zai ri'ke ni na goce ina cigaba da jefa masa k'ananun fillon da akayi mini kwalliyar gado. Yana 'yar dariya yake kad'an fad'in." Ke fa sokowa ce Kyauta menene abin kuka? kin ga yi shiru don Allah kin san dai ba mu kad'ai ba ne a gidan, ki yi shiru na ce miki." Yana maganar ne a lokacin da yake kare fillon da nake jefa masa na ce." Wannan ai wula'kanci ne ni wallahi Allah ba zan yarda ba sai ka ba ni hakuri." Hannu yasa ya rufe bakina. Ya rungume ni tsam! A jikinsa yana fad'in." Ai durkusawa wada ba gajiyawa ba ne, Allah Ya ba ki ha'kuri." Shiru na yi ajikinsa ina sauke ajiyar zuciya. Cikin kunnena na ji yana cewa" Da gaske nake fa Kyauta ina so kirjinki ya fi haka girma, ki yi kokari a kan hakan." Yanda ya fadi maganar cikin taushin kalami shine dalilin da ya sa na shiga nazari. Lallai tunda ya furta hakane a zuciyarsa dole kuwa na cire kunya na nemi Inna Hauwa da maganar domin itace 'yar kunga-kunga kuma tana da jama'a sosai, na san za ta nemo mini sahihin maganin gyaran nono irin na hausa *08089965176 Muna da ingantacce Kuma sahihin maganin gyaran nono irin na hausa wanda amfaninsa bai tsaya iya nan ba har matantaka yana gyarawa, a tuntu'bemu ta lambar wayarmu kai tsaye.* Kashe mini jiki ya yi da kalaminsa har na mance a kwance nake a jikinsa. Sai da ya bijiro da wani lamarin tukkuna gayyar ta watse a lokacin da ya nuna yana buk'atar mu had'a baki (kiss) na ce ban san wannan ba. Ya turza ya turza na 'ki aminta karshe ma sai nasa masa kuka. Dole ya ha'kura ya kyale ni amma bai kwanta kusa da ni ba. Ina kallonsa ya d'auki bargo da fillo ya fita daga d'akin. Lamo na yi a gadon fargaba da zullumi sun yi mini dabaibayi. Cikin nazari da tunanin rayuwar auran da za mu yi bacci mai nauyi ya d'auke ni. Da asubah na farka sakamakon motsin fitarsa da kuma kiraye kirayen sallah da massalatai suka yi. Da yake da wutar lantarki ina fitowa na ga ya jona ruwa a irin babban bokitin nan mai had'e da hita. Sai da na kashe tukkuna na zuba ruwan a babbar buta na surka ruwan na je na tsaftace jikina. Ina burushi a d'an kewayenmu na dinga Jin motsin matar gidan tana ta zurga-zurga. 'Daki na koma na takure ina jiran gari ya yi haske na je na gaisheta, domin Nene ta jadadda mini cewa; Na mutuntuna tunda a haife ta haife ni, kuma an yi mata sheda mutuniyar kirki ce. PAID BOOK #500via 7084653262....Binta Umar Opey bank ko 0542382124...Binta Umar gtbank. A tura sheda 07084653262. Masu tambayar wannan karon babu Vip ne . Zan yi amma a talgram kawai za mu kammala littafin cikin kwana goma ko 'kasa da haka da ikon Allah. Wad'anda suke bukata kuma suna yin talgram din sai su yi mini magana domin jin abinda za su biya. 'Yan Nijar kuma dala d'ari katin airtel sai ku yi magana da momina kai tsaye babbar macace don Allah a kula. *+227 88 13 77 40* *GARKUWAR MATA* *BINTA ABBALE*