*TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY). NA GODE BISA KARAMCINKI GARE NI, UBANGIJI YA RAYA MIKI ZURU'A AMIN* *LABARIN TURKEN GIDA NA MUSAMMAN NE ZUWA GA ƘAWATA SURAYYA DEE(MARUBUCIYAR HALIN YAU) NA GODE DA MARTABAWA ƘAWATA. TURKEN GIDA NA GODIYA DOMIN KE KIKA SANYA MA LABARIN SUNA. A MADADIN NI DA MASOYANA MUNA YI MIKI TA'AZIYAR RASUWAR BABA YAU SHEKARU GOMA, ALLAH YA JIƘANSA DA RAHAMA ALLAH YA GAFARTA MASA AMIN. MUNA BARAR ADDU'ARKU FANMILY* *GARGAƊI* *LABARIN TURKEN GIDA HAƘƘIN MALLAKA NA JAMILA UMAR JANAFTY NE. A GUJI JUYA SHI KO SARRAFASHI TA HANYAR TAƁA SHI KO SAUYA SHI ZUWA WANI MANUFAR DA BA NI DA MASANIYA. YIN HAKAN KAMAR SAƁA MA DOKAR HAƘƘIN MALLAKATA NE A KIYAYE.* *MANUNIYA* *LABARIN TURKEN GIDA ƘIRƘIRAREN LABARI NE.  DUK ABIN DA A KA CI KARO DA SHI YA YI KAMCECENIYA NA SUNA KO HALLAYA, GARI KO DAƁI'A. TO A YI HAƘURI AN SAKA NE DOMIN ARASHIN LABARI BA DOMIN NUNIYA KO TOZARCI GA WATA ƘABILA KO AL'ADA BA* *NA GODE* _*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN ƘAI*_ https://www.wattpad.com/story/393283954?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_reading&wp_page=reading&wp_uname=JamilaUmar315 https://www.tiktok.com/@jamilaumar630?_t=ZM-8w7lOpzJaYJ&_r=1 *🅿️ 01* *SHIMFIƊA* *NIGERIA, KANO STATE* _AREA: LODGE ROAD KANO._ MONDAY, 2rd Feb. 2015. Jihar kano, jiha ce da take a arewa maso gabashin yammacin Nigeria. Tana da yawan faɗin ƙasa kimanin kilimota murabba'i 20,131 da yawan Jama'a miliyan sha ɗaya da dubu hansim da takwas da ɗari uku(a ƙiyasin 2011). ***** ENGR. YUSUF MUHAMMAD INUWA ya fito daga masallacin dake can gaba da gidan shi, lokacin misalin shida saura kaɗan ne na safe, tun da ya saba sai ya tsaya ya yi azkar da yan addu'o'in shi bayan nan kuma ya kan ɗan tsaya ya gaggaisa da mutane, duk da anguwan ta masu dashi ne amman akwai mutane masu mutumci da dattako mazauna a anguwa ko dai ba a haɗu a ko'ina ba magidanta na haɗuwa duk sallar asuba a masallacin, tunda wasu daga asuba sai asuban ake samun damar ganinsu saboda aiki, irin su injiniya Yusuf ma masu harkokin da yawa da baya ma samun zama ko yini a gida shi ko weekend ne yana fita tunda shi ba aikin gwamnati yake yi ba ma'aikaci ne mai aikin kai da kai da ya tsayu da kafafunsa tun da kuruciyarsa. A ƙiyastin shekaru Injiniya Yusuf ba zai gaza shekaru 42 a duniya ba. Kuma ba zai iya haura haka ba, yana tafiya sannu sannu bayan barowan sa daga masallaci zuwa gidansa tunda kusa ne ba nisa, sanye yake da jallabiya baƙa mai kyau har tana kyallin sabunta kansa kuma da hula wata baƙar dara sannan hannunsa ɗauke da Casbaha. Dogo ne namiji ne a tsaye mai zati da haiba, a kallo farko in ka ganshi za ka shaida bafullatani ne saboda ya na da haske sannan sumar kansa za ta iya fallasa ko shi waye, duk da ba ma'abocin tara suma ba ne. Ba doguwar fuska gare shi ba tana da ɗan faɗi amman Injiniya Yusuf yana da kyau saboda yana da dogon hanci ga kwarjini da zatin na cikakkun maza. Wani maidaidaicin gida ya nufa a anguwan Lodge road, gidan yana bakin titi ne saboda gabaɗaya anguwan tana shimfiɗe da kwalta ne. Fasalin gidan na ƴan gayu ne ko na ce ma tsarin gini ya sanu akan aikinsa. Sannan yanayin gidan daga waje zai iya shaida maka gidan ko ba sabo ba ne, to bai daɗe ba domin har a lokacin baƙin get ɗin dake gidan yana ta ƙyallin sabunta sannan fentin gidan daga waje mai ruwan ganye yana nan a sabuntar shi kamar yau aka yi shi, yana zuwa ƙofar gidan ya zura hannu a aljihun gaban jallabiyansa ya ɗauko key ya buɗe gidan ya shiga sannan ya maida kofa ya rufe, haraban shima ƙarami ne na zaman mota ɗaya zuwa biyu, sannan ga wata baƙar mota ƙiran TOYOTA C.HR. a fake a haraban gidan sannan haraban ya ƙawatu da filawoyi masu kyau da sha'awa suna fidda kamshi. Ƙofar da zai sada shi da cikin gida tana rufe ne itama sai da ya sanya key ɗin hannun shi ya buɗe sannan ya shiga kuma ya maida ƙofa ya rufe. Falon gidan na farko ya fara iskewa wanda ba wani hayaniya daga kujeru sai ƙaton tibi dake kafe sai cafet ɗin tsakar ɗaki. Falon yana da girma sosai saboda daga can gefe ta hannun dama akwai dining mai zaman mutum biyar, falon kalan shi mai ruwan golden yellow mai haske, hatta labulayen da suka zagayen falon kalarsu kenan. Daga falon ya fara cire takalmin kafarsa ya fara taka doguwar kafarsa mai cike da gargasa zuwa wata kofa dake fuskanta shi, domin falon shuru, ko'ina ya na rufe har wutan ma falon a kashe ne sai da ya yi amfani da hasken wayarsa duk da kuma akwai wutar nepa bai tsaya neman makunnin wutar falon ba, tunda ba zama zai yi a ciki ba.   Ƙofar da ya sake buɗewa bai saka mata key ba tunda ta na buɗene. Tura ta kawai ya yi ta buɗe sai ga shi ya ƙara bayyana a wani ƙaramin falo mai ɗauke da kujeru guda uku ba manya sosai ba, sannan akwai tibin bango ƙarami ba wani babba ba sai cafet da Fridge babba mai kofa biyu. Daga can gefe kuma akwai dispanser a kafe shi wannan falon kalan brown ne, hatta shima labulanyan nashi suma kalansu kenan, shima falon tsit ba motsin komai, sai da ya saka hannu ya kunna wutar falon haske ya bayyana ko'ina. Daga tsakiyar falon akwai wata kofa a rufe, daga gefe kuma korido ne dogo da zai sadaka da wata kofa amman daga gabas ɗin sa kuma akwai wata itama a rufe ita ya taka ya nufa. Sai ya ƙwankwasa lokaci ɗaya da sallama saboda daga bakin kofar kana iya jiyo sautin karatun azkar da wasu muryoyi sirara ke yi. Buɗe ɗakin ya yi lokaci ɗaya yana shiga sannan ya maida kofar ya rufe. Lokaci ɗaya mirmishi ya wanzu a saman fuskarsa lokacin da ya yi arba da kyakyawan ƴaƴan nashi dake zaune a saman karamin cafet ɗin da ya ɗan rufe tsakiyar ɗakin. Duka mata ne babban kimanin shekarunta na haihuwa 13 da kaɗan a duniya ta na sanye da Hijabi baki har kasa da littafin azkar a hannunta sai ƙaramar mai kimanin shekaru biyar itama da irin Hijabin ɗayar a jikinta itama da ƙaramin littafin azkar a hannunta. Sanda ya shigo har ƙaramar ta yi ƙokarim milƙewa da sauri ya ɗaga mata hannu lokaci ɗaya ya na faɗin. " Ku ƙarishe azkar ɗin ku Baby." Babbar ta kalleshi ta yi masa mirmishi sai shima ya maida mata, ya ɗan jima tsaye yana kallonsu kuma yana saurarensu suna rera azkar ɗinsu cikin muryoyinsu mai sanyi da karaɗi, kamar ma sun haddace a kansu ba gargada ba komai agogon wayarsa ya duba ya ga shidda ta wuce na safe sai kawai ya kaɗa kai kafin ya ce" Jidda kar ki manta yau Monday in kun gama azkar ɗin ku yi wanka ku shirya" Da kai babbar ta amsa masa wacce ya kira da suna Jidda, ya juya ya fice ya na mai rufe musu ƙofar ɗakin a hankali kada ta ba da sauti, ɗakin daman ba shi da wani girma akwai tiolet a ciki sai ƙananun gadaje guda biyu kowani gefen shi akwai ƙaramin wardrope mai ƙofa biyu, sai daga can gefe ƙaramin dirowa in ds suke tara littafansu na boko da na isalamiya. Yana fitowa ya nufi hanyar korido ya buɗe kofar ya shiga sai ga wani ɗan lungu ƙarami mai kofa na fuskantan shi, sai wasu kofofin na kallon juna. Ƙofar da ke hannun dama ya buɗe ya shiga da siririyar sallama a bakinsa daga bakinsa duk da ya san wacce ke cikin ɗakin ta na barci ba lalle ba ne in ta farko, ballatana ace ta ji shi amman tunda sallama wajibi ne ko babu kowa a ɗakin shi ya sa ya yi sallama sannan ya shiga lokaci ɗaya mai da kofar ya rufe. Akwai hasken wuta a ɗakin ya manta shi ya kunna lokacin da zai fita sallar asuba. Yanayin kwanciyar da Sadiya ta yi ne ya sa sai da ya kusa sakin dariya shi kaɗai a sannu sannu ya karisa bakin gadon dake bedroom ɗin kafafunsa suna mai nitsewa cikin ƙaramin cafet ɗin da ya yi ma bakin gadon kwalliya. Sanye take da kayan barci riga da wando, masu taushi kanta ba ɗankwali ko ma ta saka wajen barci ya cire, kuma ba ta yi kitso ba duk gashin ya birkice duk da a kallon farko za ka fahimci ma mallakiyar gashin ta na da yawan gyara. Kwance take a kan gadon amman yanayin kwanciyar ne abin dariya kafarta ɗaya ta sauka ƙasa, ɗayan kuma ta yi can gefe da ita ta buɗe kafarta kanta ya sauka daga kan filo sannan kwanciyar rigingine ta yi hannunta ɗaya ya yi yamma ɗaya ya yi gabas ne. Kai ya girgiza kafin ya saka hannu ya ɗago kafarta guda ɗaya da ta sauka ƙasa ya maida ta saman gado, sannan ya gyara mata hannuwanta ya jirkitata ta yi kwanciyar gefen dama, yana shirin rufa mata blanket ɗin da ta yi gefe dashi ne ta yarfa masa hannunta a fuska a cikin barci sannan ta yi wani juyi sai da ta ture shi ba domin yana da ƙarfi ba sai ya faɗi saboda da karfi ta yi juyin. Kai ya kara girgizawa ya ja blanket ɗin ya rufa mata daga ƙafafunta zuwa cikinta, ya san ta na fashin sallah sannan a satin da ya gabata kaf ba ta zauna ba saboda Rahila ta haihu sun sha hidima.   Wajen kanta ya koma ya tattara mata gashin kanta, rebon ɗin can ya tsince shi gefen da ya kwanta ya zura hannu ya ɗauko shi ya kama sumar kan nata duk da ba shi da cika amman akwai tsawo ya kama mata shi, sannan hular dake kanta a daran jiya mai taushi da ta yi wani gefe can ya ɗauko ya saka mata sai motsawa ta ke yi tana ƙananun kunƙuni na barci. Ba ta buɗe ido ba amman ta motsa kuma ta riƙe hannunsa mai cike da garsasa bakin ta ya motsa wajen faɗin "Yallaɓai na." Ƙayataccen mirmishi ya saki kafin ya riƙe hannun ta na dama da ta riƙe shi dashi, ya kai bakinsa ya sumbata lokaci ɗaya yana faɗin" Na'am Sadiya ta." Sai kuma ya ga ta koma barci sai ya sauke mata hannunta ya ƙara gyara mata bargo sannan ya bar bangarenta. Ya koma ɗaya bangaren ya zauna lokaci ɗaya ya cire hula kansa ya ijiye nan saman Side drower ɗin gadon, daman casbahan hannunsa na cikin aljihun bakin wando ke jikinsa a ciki ya saka, miƙewa ya yi ya cire jallabiyan ya rage daga shi sai dogon baƙin wandon dake jikinsa. Babban wardrope ɗin dake ɗakin mai kofa shidda ya buɗe ya saka jallabiyan sannan ya saka hannu a aljihun wandon dake jikinsa ya cire casbahan ya juya ya ijiye saman makeken madubin dake bedroom wanda ke shaƙe da kayan kwalliya. Laptop ɗinsa dake cikin drower ɗin gefen gadon ya buɗe ya ɗauka akwai aikin da yake so ya kamallah kafin ya fita office. Kan gadon ya koma ya zauna ya jingina da jikin gadon. Sannan lokaci ɗaya ya mikar da kafarsa ya dora yar ƙaramar laptop ɗinsa ya fara aiki, lokaci bayan lokaci yana kai kallonsa kan Sadiya da ta cigaba da barcinta cikin salama. Sannan kuma wani lokacin sai ya ɗaga kansa ya na zagayen ɗakin da idanuwansa.   Babban ɗaki ne domin bayan gado da wardrope akwai shuraf ɗin takalma mai hawa bakwai ne kuma dogo ne shaƙe da takalma na Sadiya da na Yusuf sai gefen kuma karfen sagala jakunkuna ne, ga su nan kala kala sama da goma, shi kalan ɗakin mai ruwan baƙi da fari ne ya yi kyau kwarai domin hatta zanin gadon fari ne da blanket ɗin su sannan haka labulan dake jikin window ɗin bedroom ɗin baki ne da fari. Yana cikin aiki ya shagala kawai sai ji ganin kafar Sadiya ya yi a kan hannunsa dake saman laptop ta mako masa da karfi. Sai da ya yarfe hannu ya koma yana kallonta, kai ya ƙara girgizawa sannan ya ɗauki kafarta ya maida mata kan gado ya na ƙokarin cigaba da aikinsa ta ƙara yarfa masa hannu ya rankwafa yana gyara mata hannunta guda ɗaya,ta ƙara saka ɗayan hannun ta zargo wuyansa wanda sai da ya yi sauri cewa"Sadiya.." Kamar ta ji sa sai ta sake shi, shi kuma sai ya koma yana kallonta bai san lokacin da ya kara sakin kayattacen mirmishi wanda Sadiya ce kaɗai in ya kallah ya ke iya yi ma wannan mirmishin. Fuskarta yake kallo yana jin wani farinciki daga ƙasan ransa, yar duma duman fuskarta mai ɗauke da kalan chaculate domin ba fara ba ce wankan tarwaɗa ne, mai ɗauke da doguwar fuska hancin ta ɗan madaidai ci ne da bakinta ƙarami mai ɗan tudu, ta haura talatin amman har gobe kamar yarinya yar shekara goma sha yake kallonta a kuma haka take a idanuwansa har gobe har kuma gaban abada. Hancinta ya lakuce lokaci ɗaya yana faɗin" Yar tekwando kawai." Leɓenta ya kalla har yanzu akwai danshin jan bakin da ta yi masa kwalliya jiya, hannunsa guda ɗaya ya saka ya shafi leɓenta nata lokaci ɗaya yana mirmishi da ya tuna ranar daran amarcin su ranar da shi da Sadiya suka zama Miji da mata. Tun ta na jin ɗari ɗari ta dunkule waje ɗaya, bai raina kansa ba sai da barci ya kwashi Sadiya ranar duk jikinsa a gajiye ya tashi, Kafafunta da hannayenta ta rika yarfa masa kwana ya yi yana gyara mata kwanciya, tun daga lokacin yake zolayanta da yar Tekwandon dare, Sadiya tana da nauyin barci da mugun barci ta yi ta buge wanda suke kwana tare, in kuma ya yi magana da safe ta musa har sai ya samu wata rana ya yi mata video ta gani sannan ta gasgasta. Tun tsawon shekaru goma sha da auransu har gobe Sadiyarsa da ya aura yar ashirin ta na nan ba ta sauya ba, ba ya kuma tunanin ko tsufa ta yi akwai wasu hallayar ta da ba za su taɓa sauya wa ba. Vibration ɗin waya dake saman can side drower bangaren Sadiya ya katse masa tunaninsa. Wani gur gur sautin ke ba da wa ya ɗauka ma nashi ne sai da ya waiwaya sai ya ga ba tashi ba ce, sannan ya fahimci wayar Sadiya ce. Laptop ɗin dake saman jikinsa ya sauke nan saman side drower ɗin bangarensa. Sannan ya sauka daga kan gadon ya taka zuwa wajen wayar ya duba sai ga ALHAJINMU ke kira, ya na shirin ɗauka sai wayar ta katse, ya san password ɗin wayarta saboda date ɗin auran sune, ya buɗe yana shirin bin bayan kiran Alhaji ganin ko bakwai ba ta yi ba yana tunanin kamar ba lafiya sai ga wani kiran Alhaji ya ƙara shigowa sai ya ɗaga kiran da sauri lokaci ɗaya ya na faɗin. "Alhaji barka da Safiya.." Da yake wayar tana da ƙara ana jin sautin mgana ta cikin wayar. "A.ah Yusufa ne?. Mun tashi lafiya ya kwanan iyalan naka? Kamar yana ganin shi Yusuf ya rankwafa yana amsa masa da lafiya kalau. Shima ya tambaye shi ya su Gwaggo ya ce duk suna lafiya. Alhaji Sulaiman Yashe dagacan bangaren ya ce" ina ita DUBUN take? Ko ta na can wajen yaran ne? Kai tsaye Yusuf yace"A'ah ba ta tashi ba ne Alhaji amman in ta tashi zan sanar mata da ta kira ka." Alhaji cikin gamsuwa ya ce'"To to ba laifi daman ba wani abu ba ne. Kai ma daman ina son ganinka, in ka samu dama yau bayan sallah isha'i ina son ka zo gida kai da Dubu." Cikin ladabi Yusuf ya ce"To Alhaji in sha Allahu muna nan tafe" Da haka suka yi sallama, ya maida wayar mazauninta ya juya sai ya ciro karo da idanuwan Sadiya kaifaffu a kansa, mamakin yaushe na farka ya bayyana a saman fuskarsa cikin sanyin murya ya ce"Oh daman idanuwanki biyu kike ta buguna da sunan barci ko? Mirmishi na saki kafin na miƙe zaune lokaci ɗaya ina yaye bargon jikina. Hannu guda ɗaya na miƙa masa sai ya kama na jawo sa ya zauna a gefena ni kuma sai na yada kaina saman kafaɗansa lokaci ɗaya ina faɗin" Allah yanzu na tashi, mganarka naji sama sama a saman kaina." A tare na kuma kallonsa kafin na ce"Waye ya kira hala? Yana wasa da yatsun hannuna na dama da suka shan jan lalle, ya na faɗin" Alhaji ne." Cikin zaro ido na ce"Alhajinmu? Bayan na tada kaina daga saman kafaɗansa. Dariya ya yi kafin ya miƙe lokaci ɗaya ya miƙa mini hannunsa na kama ya miƙar dani tsaye ina miƙewa ya buɗe min hannuwansa na faɗa jikinsa ina sauken numfashin salama. Murya ƙasa ƙasa yace" Muna da wani Alhaji ne bayan Alhajinmu? Shi ne ya kira ya ce yana son ganin mu ni da ke. Yau da daddare" Ina lafe a jikinsa ban wani jin mamakin jin haka ba, daman nasan za a rina ai ni daman uwar laifi ce yanzu har an samu wata ta je ta gaya ma Alhaji faɗan da ya faru tsakanina da Ma'u a gidan Rahila. Ban da Allan misuri amman ina da tabbacin dalilin kiran Alhaji kenan, ƙaramin tsaki na saki abin na cin rai na har yaushe ne yan gidammu za su gane Ma'u makira ce ita da uwarta? Tun muna yara ita ke nasara a kaina saboda macijin sari ka noƙe ce ni kuma ina da baki shi ya sa take ta samun nasara a kaina har kuma yau din nan komai ya faru tsakanimu ni ce mara gaskiya fitinanniya. Ƙara sakin tsakin na yi wannan karon mai karfin har sai da ya ji, sai ya rankwafa da kansa dai dai kunnena yana faɗin" Me ya faru matata? Sai na ƙara shigewa jikinsa kamar wani zai ƙwace min shi kafin na ce"Ina kwana Yallaɓan Sadiya" Duk da ba na kallon shi amman na ji sautin mirmishin kafin yace"Ina kwana Sadiyan yallaɓai." Atare muka saka dariya, sannan ya ɗago ni, ya sumbaci goshina ni kuma na sumbaci kumatunsa sannan na kalleshi cikin ido ina faɗin" ina sonka Yallaɓai na." Mirmiahi ya yi min sannan ya sumbaci lebunana ya ɗago ya na kallona na wani lokaci kafin ya ce" Nima ina kaunarki Sadiya ta." Komawa na yi na sake lafewa a saman kirjinsa ina faɗin"I miss u" Cikin ƴar shagwaɓa da har sai da ya yi mirmishi ya rumgumeni yana faɗin"Ba ga ni ba, ni naki ne har abada Sadiya ta." Ina jinsa ban yi mgana ba tsawon lokaci muna rumgume da juna, muna jin buguwar numfashin juna. Da sauri na ɗago kaina ina kallonshi shima kallona ya ke yi. "Yau wata rana Yallaɓai.? Gira ya ɗaga kafin ya ce" Monday mana." Da sauri na waro ido kafin nace"Monday fa ka ce? Ya na yar dariya ya ce"E, mi ye to? Gabansa na bari ina gyara zaman  kaina na ce" Yallaɓai yau fa monday ka manta su Jidda na da makaranta." Riƙo ni ya yi na dawo gabanshi lokaci ɗaya yana faɗin" Ba matsala na faɗa ma Jidda su yi wanka su shirya." Wuya na karya a shagwaɓe kafin na ce"Breakfast fa Yallaɓai? Yana shirin mgana muka ji ana knooking shi ne ma ya ce a shigo, ko ban tambaya daga ni har shi mu san su waye. Buɗe ƙofar suka yi suka shigo a tare cikin shirinsu na kayan makaranta, Jidda riga da wando ne a jikinta da ƙaramin farin hijabi, sai Baby sanye da doguwar riga zuwa gwiwa daga kaɗan amman ta saka wando baƙi dogo. Itama da ƙaramin farin hijabi ita uniform ɗinta maroon ne da fari. Da sauri na buɗe hannuwana ina faɗin"My Babys" Da sauri Baby ta nufo ni na duƙa ta faɗa jikina tana faɗin"Good morning Umma" Ina shafa kanta na ce"Morning my princess" Sannan ta ɗago ta sumbaci kuncina nima sai na sumbaceta, Yusuf ta nufa tana faɗin"Good mornig Abba." Gefe ya yi ya na make kafaɗa kafin ya ce"Naƙi sai da aka gama rumgumar Umma sannan a ka tuna da Abba." Kafafunsa ta rumgume ta na faɗin"Abba" Lokaci ɗaya ta na dariya ni kuma sai na miƙe ina faɗin"Yallaɓai kishi kake yi da Umma yau? Hararata ya yi ba tare da ya yi mgana ba, cak ya ɗaga Baby sama. Ni kuma sai na ƙarisa na rumgume Jidda wacce ke faɗin"Ina kwana Umman mu." Ina shafa kumatunta na ce"Lafiya lau Jiddan Umma " Mirmishi ta yi irin na babanta kafin ta ce"Umma mun gama shiryawa, har na ɗumama mana sauran shinkafan da kika dafa jiya mun ci ni da Baby" Baki na washe kafin na ce"Good girl to lunch box ɗin ku fa? Kai tsaye ta ce" Na soya mana doya Umma sai na haɗa mana tea za mu tafi dashi." Farinciki ya cika ni domin na gaji har daman fargaban aikin safe nake yi na sake rumgume Jidda ina faɗin" Allah ya yi ma Jiddan Umma albarka. Ta amsa da Amin Umma bayan mun gama ta ƙarisa wajen Abbansu bayan ya sauke Baby itama ya rumgumeta bayan ta gaishe su. Ina dariya na ce" Yallaɓai ni fa yau Jidda ta fanshe ni bari na koma barci." Ya na kallona ya mele baki kafin ya ce"To daman Sadiya yar laushi." Ina shirin hawa kan gadon ban san lokacin da na fasa ba, hannu na saka na daki kafaɗan Yusuf ina hararansa kaucewa ya yi yana ƴar dariya idanuwana kamar za su faɗo wajen hararan shi, shi kuma yana ta faman dariya ya rike hannun Jidda da Baby yana faɗin"Mu je daga falo kafin mai mashin ɗin ku yazo. Mu bar Sadiya yar laushi ta huta dakyau.." Filon dake kan gadon na ɗauka na wurga masa ina faɗin"Tafida bana son sunan nan fa."   Da gudu daga shi har su Jidda suka fice daga ɗakin suna min dariya, nima mirmishin na yi sannan na koma na kwanta na lulluɓa da blanket ina tuna sunan da ya kira ni da shi, ko a baya a gida in aka kirani da wannan sunan sai Alhajinmu ya yi sharia faɗan ke rabuwa, Allah ya jiƙan Mama da Rahama ita ta lanƙayamin sunan nan da har gobe bana kaunarsa. Ƙara gyara kwanciya nayi, ina tunanin me kuma wannan karon aka je aka gaya ma Alhaji akan abin da ya faru tsakanina da Ma'u? Wayata na zura hannu na ɗauko na shigar da kaina cikin blanket ina duba wayar tawa, Missed calls na Rahila ba adadi tun jiya take kirana ban ɗauka ba har Yaya Murja na ga ta kirani har da Ma'u, kai matar nan ba karamar makira ba ce, uban ta zan yi mata da ta kirani bayan sun haɗu ita da ƙawarta sun ci mini mutumci? Kwafa na yi ni kaɗai na buɗe data ina ganin saƙonni na ta tururuwan shigowa, abin da ya fi jan hankalina ganin group ɗina gidanmu na S. YASHE'S sai faman tagging ɗina ake yi ko shiga ban yi ba saboda nasan zagi nake sha wajen su Yaya Abubakar tunda an taɓo yar gwal wacce ba ta laifi a wajensu, su na ba ni mamaki ta ya ya za ka yanke ma bangare ɗaya hukunci ba tare da an ji bayani daga ɗaya bangaren ba? Na rasa gane wani irin tasiri Ma'u ke da shi a wajen yan gidanmu da suke fifita damuwarta sama da damuwar ni da nake ƙanwarsu jininsu. Na ga Yaya Murja ta min Vioce note mai tsawo ko buɗewa ban yi ba, na ga ma mganar Yaya Abubakar naga dai a farko ya ce Sadiya ke wai ba ki jin mgana ko? Sai saƙon Rahila rututu wajen ashirin na tsaki ma na kashe datan ta je ga ta ga Ma'un ta zaɓe ta sama da ni yar'uwanta da muke uba ɗaya, wulla wayar na yi can gefe na sake gyara kwanciya ina tunanin abin da zan gaya ma Alhaji, ba ni da damuwa da Yusuf saboda nasan halin mijina ɗan ba ruwan shi ne duk abinda na ce masa zai ce ya yi dai dai ne, mutum ne mai ƙoƙarin girmama duk wani abu da nake so da wanda ba na so duk da baya sanin wasu rigimgimun dake tsakanina da Ma'u amman shi shaida ne ni da ita ba ma ga maciji. Rufe idanuwana na yi ina tuna abin da ya faru a shekaranjiya asabar wajen sunan ƴar ƴar'uwata da muke uba ɗaya Rahila wacce muka taso tare tun muna yara aure ma rana ɗaya aka yi mana. Tsabar baƙin ciki sai da na ji taruwan ƙwalla na yi saurin shanyewa, daga kan gado ina jin mganar Yusuf ta haraban gidan tunda window ɗakin na ta wajen haraba kenan su Jidda ya raka Salisu mai mashin ɗin da yake kaisu makaranta ya zo, ina kuma kwancen ba jimawa ya shigo ɗakin sai na yi luf kamar ina barci ina jinsa ya zo ya ɗauki wayarsa da laptop ɗinsa sannan ya kashe min hasken ɗakin ya fice bayan ya rufo min ƙofar. Sai na koma na ƙara lafewa na lumshe ido ina wani tunani a cikin raina ban sa na furta a fili ba sai da na riga na furta cewa" Ya Allah ka ƙara bani haihiuwa ko guda ɗaya ne na ƙara haifa." Idanuwana suna yi wani luu kamar zan fashe da kuka in na tuna wautar da kuruciyar da na tafka a zamanin baya gashi yanzu abin da na aikata na neman ya zo ya dame ni. Barci ya kwashe ni sama sama ban daɗe ba na tashi saboda na ji karan ruwa a Tiolet kenan Yusuf ya shiga wanka sai na miƙe duk da ina jin kasala na saka takalma na tsakar gida mai taushi na fita daga ɗakin na buɗe kofar kitchen ɗina na shiga mai girma ne, irin kitchen ɗin zamani amman ya yi kaca kaca saboda manya sun yi aiki mirmishi nayi Jidda, ba ni ta biyo ba karsashinta irin na Babanta ne amman da ni ta biyo ba za ta iya taimakamin kamar yadda take taimakamin yanzu ba, ta yi ma Baby wanka ta shiryata sannan ta shirya kanta ta kuma yi musu abin karyawa da na tafiya makaranta sai in naga dama na ke fitowa na yi wani abun. Gyara kitchen ɗin na yi sannan na dora ruwan tea bayan na saka haɗe haɗen ganyen shayi. Nima doyar na fere na soya mana sai na yi mana yar source ɗin miya ta albasa. Na kwshe komai zuwa dining kenan Yusuf ya fito cikin shirin fita, sanye da shadda mai ruwan ƙasa dinkin riga da wando tazarce da hula a saman kansa kuɓe takalmin kafarsa mai buɗewa ne baƙi A falon muka haɗu yana ta tashin kamshi sai na tsaya ina kallonsa har sai da ya tsole min ido kafin ya ce"Kallon fa? Na koma miki saurayi ne? Mirmishi na yi kafin na ce" Ko da yaushe Saurayi ka ke a idanuwan Sadiya Injiniya Yusuf, ina kallon ka ne kamar yau ɗin ne na fara ganinka a hanyar dawowata daga BUK a wata ranar laraba." Na faɗa ranar ta na dawo mini a cikin tunanina a tare muka saki mirmishi, kujera na ja masa na dining ya zauna lokaci ɗaya ya na faɗin"Na ce ƴan mata doguwa sallamu alaikum ba, ki ka wani juyo kina min fari da ido kika juya kika cigaba da tafiyarki" Ina dariya ban yi mgana ba ina tsaye ina haɗa masa tea shi kuma yana faman kallona, basarwa na yi ina faɗin" Yau sai ka shirya ba ka jirani na zo na shirya ka ba ko? Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce"Na bar Sadiya yar laushi ta huta ne." Da gangan na ɗiga masa ruwan zafi a hannunasa dake ɗaure da agogon fata baƙi, da sauri ya cire hannunsa a wajen ya na yarfewa ni kuma sai na haɗe rai ban ma kalleshi ba, cikin kallona ya ce"Sadiya bayan Tekwondon ɗin dare kin fara na safe ne? Kafarsa na taƙa dake cikin Takalmi da sauri ya janje kafarsa ya na faɗin"Akwai matsala kam." Ina tura masa Mug ɗin tea ɗin gabansa da Doyar da na saka masa amman ban kalle shi ba. Na juya zan tafi ya riko hannuna amman sai na ƙi juyowa daman raina a jagule ya ke, amman sai ya yi tunanin mganarsa ne ya ɓata min rai, tasowa ya yi ya rumgumeni ta baya yana faɗin"Kin ji haushi ne? To Allah ya baki hakuri Sadiya ta." Mirmishi na saki ina riƙe hannunsa kafin na juyo da shi muna fuskantar juna, gemunsa na shafa zuwa sajensa kafin na ce"Ka ji ka wani haushi? Sadiya ce fa da Yusuf? Ka manta.? Sai ya duka ya sumabaci goshina tunda ya fi ni tsawo kafin ya ce"To ai na ga za ki tafi ki barni ni kaɗai ahalin ba haka muka saba ba." Da sauri na ce"Ruwa zan ɗauko kasanni da shan ruwa" Tuna haka yasa ya sakar min hannu na fice daga falon zuwa falo na biyu kitchen na koma na ɗauko karamin mug na koma wajen depenser na tsiyaya ruwa mai ɗan sanyi sannan na koma falon na ja kujera gefensa na zauna muka fara karyaawa. Amman ni ba wani ci nake yi ba sai juya cokali na ke yi yana ta min hira kan wani kwangila gina makaranta da aka ba kamfanin shi sun gina wajen shekaru biyu ba a biya su kuɗin aikinsu ba to daman an kira shi tun wancan sati ana saka ran payment ɗin shi ne ya ke ta mini surutu ba na wani fahimta gabaɗaya natsuwata ba ta tare da ni Sai da na ji ya na kiran sunana. "Sadiya." "Sadiya." Ajiyar zuciya na sauke sannan na kalleshi idanuwana sun yi laushi kamar zan yi kuka. Daƙatawa ya yi da cin abincin ya na mai ƙure ni da ido kafin ya kira sunana cikin yanayin da yakan kirani a duk lokacin da ya ga na shiga damuwa. "Sadiya." Na kalle shi amman ban amsa ba cikin ƙasa ƙasa da murya ya ce" Me ke damun ki ne? Tun fitowata na lura da yanayin ki ya sauya." Da sauri na yi mirmishi kafin na ce"Haba. Bakomai fa kawai ina tunanin kiran me Alhaji ke yi mana ni da kai? Ina ji ya sauke ajiyar zuciya kafin ya saka hannu ya rike min hannuna guda ɗaya yana faɗin"In dai kan wannan ne karki damu ba komai, ina tunanin kawai kila Alhaji na son ganin ki ne, kin san fa ke dubu ce." Ya faɗa da sigan zolaya duk dai ya sakani dariya kuma sai da na dara, ya manta ko wancan satin ni da yara acan muka yi ni sai dare ya je ya ɗauko mu. Amman ba na son na kawo masa mganar Ma'u shi ya sai na bar shi a hakan na san halin shi in har bai ga na saki ba ba zai fita gidan ba ko ya fita to cikin damuwa ne shi ya sa na saki jiki muka karya muna mganganumu na soyayya da muradi kamar yadda muka saba. Bayan mun gama tare muka koma ciki ya wanke bakinsa nima na wanke duk da ban yi wanka ba. Yana riƙe da hannuna har falo ya ɗauki laptop ɗin sa na karɓa da wayarsa na rike masa shi kuma da key ɗin motarsa a hannu na rakashi har haraban gida na saka masa kayan a gaban mota bangaren mai zaman banza shi kuma ya je ya buɗe get sannan ya dawo ya rumgumeni muka sumbaci juna sannan ya sake ni yana faɗin"Karki damu in na dawo gida da wuri sai mu je mu ga Alhajin ko? Sai na gyaɗa masa kai, na buɗe masa gaban mota ya shiga ina ɗaga masa hannu yana ɗaga mini har ya fita daga gidan ya tsaya sai da ya fito ya rufe get ɗin ya ɗaga mini hannu nima na ɗaga masa a fili na furta"Allah ya dawo mini da kai lafiya yallaɓai na." Cikin gida na koma na zauna a falo kawai rumgume da cussion ina tunanin rayuwa, na ɗan lokaci sannan na tashi na koma ɗaki na yi wanka na yi shigar doguwar rigar wani material mai maroon da baki sai na saka baƙar hula, ina cikin shiryawan na ji ana buga get daman na ce Saude ce ganin shuru ya sa sai ta kira wayata ina ɗauke da wayar na fita zuwa can haraban gidan na buɗe mata kofar, wata yar budurwa ta shigo tana a faɗin. " Anty hala barci kike yi ne ina ta bugu ba ki ji ba? Kai tsaye na ce"A'a na yi wanka ne ina kan shiri ne." Gaisheni ta yi na amsa ina faɗin" Ya su Balaraban ? Ta amsa min da lafiyan lau suna gaisheni. Ina gaba tana bin bayana har cikin gida falo na biyu na shiga bayan na kalli Saude ina faɗin"Akwai sauran abin ƙaryawa a dining ki ci sannan ki fara aikin" Da to ta amsa min sannan na shige ciki na rufe ƙofa. Saude kenan mai zuwa tana mini aikacen aikacen cikin gida. A can anguwan mu na Ɗorayi ta ke, makota suke da gidanmu. Saboda ba na son zaman shuru ya sa na kunna Tibin a tashar MBC3 ina ga Baby ta kunna sai ban sauya ba suna haska cartoon ina kallo saboda yara. Ya ɗan fara ɗaukan hankalina kiran wayata ya katse ni ina duba mai kira sai na ga RAHILANMU ce ke kirana. Karamin tsaki na ja har sai da ta katse ban ɗaga ba sai da ta ƙara kira gabda za ta katse sannan na ɗaga bayan na saka a amsa kuwwa a fusace ina faɗin" Wai me zan yi miki tun jiya kike ta faman kirana? Daga can bangaren Rahila ta ce" Kai Sadiya daman kina ganin ina kiran ki shi ne kika ki ɗauka? Kai tsaye na ce"To me zan yi miki? Rahila ba ta ji haushi ba ta ce" Yi haƙuri na ga jiya ba ki dawo ba ne Sadiya." Ƙaramin tsaki na ja kafin na ce" To na zo na yi miki mene Rahila? Ai Ma'u na nan za ta iya miki abin da ni ba zan miki ba ma." Daga can bangaren Rahila ta ce"Haba Haba Sadiya wai ke abu ba ya wucewa a wajem ki? Jiya nan fa Ma'u har da kukanta ta ce ita wallahi ba ta ji daɗin abin da ya faru a tsakanin ku da shema'u ba a gabanmu fa har da yaya Murja ta kira ki baki ɗauka ba, me kike so a yi miki Sadiya.? Karamin tsaki na ja kafin na ce" Munafuka kawai,." Rahila ta ce"Don Allah Sadiya ki daina wannan ƙiyayar ga Ma'u. Yar uwanki ce fa." Rahila ta magana kamar na kifa mata mari ta cikin wayar haka na riƙa ji. Wai Ma'u ta na kuka a gabansu Yaya Murja, takaici ya hana ni mgana ina jin Rahila na ta wa'azin ta na fama akan na manta komai na rumgumi Ma'u. A fusace na ce"Allah ya tsari Sadiya da ta rumgumi Ma'u. Kamar yadda ba na kaunarta itama ba ta ƙaunata amman kun kasa ganewa, shi ya sa har da Alhajimu kuka haɗa ni, ku kuka sani ga ku ga Ma'un nan tunda kuka zaɓe ta shikenan amman in dai ta na waje ina waje sai dai ɗaya ya hakura ya bar ma ɗaya." Rahila ta ce"Ni ban gaya ma Alhaji ba sai dai in su Yaya Murja ne." Baƙi na taɓe kafin nace"Koma waye ku kuka sani. Ai an taɓa yar gwal dole a je a kai ƙarana wajen Alhajin mu mana" Rahila ta sauke kai tana faɗin" To ki yi hakuri Sadiya don Allah." Kamar ba zan yi mgana ba sai can na ce"Uhm" Rahila ta yi dariya kafin ta ce"Sadiyar Dubu tawa, ga naman sunan ki a hannuna fa." Kai tsaye na ce" Ban so. Ki haɗa ma Ma'u duka ki aika mata." Ban ba ta ma zarafin mgana ba na yanke kiran ina ƙara jin takaicin kaina da na tsaya ma ina sauraranta alhalin nasan Rahila ta fi shaidar Ma'u sama da ni da muke jini ɗaya. Ƙwafa na yi a raina ina tunanin in muka je gaban Alhajinmu zan fito masa a mutum kawai gwara ya raba tsakani na da Ma'u kowa ya yi sabgarsa zai fi alheri. *Janafty.* *25/09/2024* *11.03am. *Wednesday 07/05/2025* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY).* *FATAN ALHERI GA AMINIYATA AISHA MUHAMMAD ALTO(SISINAH), ITA ƊIN TA DABAM CE A WAJENA. NA GAISHE KI* *NA GAISHE DA IYAYEN ƊAKINA* *ZAINAB INUWA(AUNTYSIS)* *HAJIYA LUBABATU MUSA* *KHADIJA SALISU YUSUF(UMMINA)* *HAJIYA HABIBA ABUBAKAR IMAM* *ANTY AISHA AHMAD IYA* *ANTY ZAINAB ABDULWAHAB* *HAJIYA HALIMA ƊALHA SHEHU.* *ANTY HADIZA MAHE MUHAMMAD* *ANTY HAIRI* *ANTY FADILA KABIR* *ANTY FIDDAUSI KABIR* *FATAN ALHERI NA GODE* *JINJINAN TURKEN GIDA ZUWA GARE KU* *MARYAM JUMARE.* *MARYAM(KITTY)* *HAFSAT HAFNAN(SAHIBATU)* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JMpd8nXr7TIDD3ILDXh64z *🅿️02* Ina zaune a wajen Rahila ta ƙara kirana sai na danna mata busy. Ina mai ƙara sakin tsaki ni kaɗai ƙara miƙe kafata na yi a saman kujera mai zaman mutum biyun da nake zaune akai ina mai ƙara jin wani  takaicin na ƙara cika min zuciyata. Rahila ba ta haƙura ba sai da ta ƙara kirana har wajen sau uku ina kashewa sannan daga ƙarshe sai ta turamin saƙo. Na ba ma Hubby  saƙon ki da zai fita, zai biya gidan Bulo ya ba ma Musabahu. Zai kawo miki ko kuma in ya haɗu da Yallaban na ƙi ya bashi ya kawo miki. Ki yi haƙuri."   Ba saƙon ne ya ba ni dariya ba sai Hubby da na ga Rahila ta rubuto mini shi ne ya sa ni tsintsirewa da wata dariya mai sauti wanda har sai da Saude da ke kichen ta leƙo tana faɗin"Lafiya Anty? Ina dariya na ɗaga mata hannu ina faɗin"Bakomai Saude. Ci gaba da aikin ki." Sai ta amsa min da kai ta maida ƙofar kitchen ɗin ta rufe ta bar ni nan zaune ina ta faman dariya. Wai Yaya Muntarin ne Hubby kai in na tuna da sunan ma sai na ji wata ƙarin dariya ni dai ban taɓa katarin Rahila ta kira shi da wannan sunan ba. Baban Islam na san tana kiran shi dashi ko Yaya Muktar ɗin da ta lankayamai amman yau shi ne karon farko da na taɓa jin ta kira shi da sunan Hubby.   Ina dariya ina tuna wani zamani a can baya ina jin na kasa riƙe dariyata. Har sake karanta saƙon na yi ina dariya a fili na furta" Tab! su Rahila masu Hubby manya." Saƙon Rahila shi ya tafi da kaso mafi girman ɓacin rai na, har na ji zuciyata ta yi sanyi, ban jima a falon ba na miƙe dauke da wayata ta kitchen na bi saboda daga kichen ɗin akwai ƙofar da za ta sadani da ƙofar koridin Bedrooms ɗina.   Saude na gani a rakuɓe kamar wata bakuwa tana cin doya, a tsugunne ba ta san ma na shigo ba a saman kanta ta ɗago kawai ta ganni harara na ɓalla mata kafin na ce" Wai ban hana ki wannan ɗabi'ar ba Saude? Nan gidan baƙon ki ne? Cin abinci a tsugunne kamar an hana ki zama a in da kika ga dama?   Da sauri ta ɗago tana faɗin" Yi hakuri Anty, daman na ga ina sauri ne shi ya sa ban zauna ba." Ƙaramin tsaki na ja kafin na wuce ina faɗin"Ke dai kika sani, ki kuma cire hijabin nan saura na fito na ga kina aiki dashi kamar wata yar gudun hijira ki ga yadda za mu kwashe da ke a cikin a gidan nan."   Dariya ta yi har ina jin sautin ta kafin ta ce" To Anty." Ni kuma Bedroom ɗina na koma kan Dressing ɗin mirrow ɗin da ke ɗakin na ijiye wayata na koma na kwanta har da shigewa bargo. Har ga Allah na ji ana ta kiran wayata amman ban mai da hankalina ba, na ɗauka yan gidanmu ne kan maganar ƴar gwal Ma'u shi ya sa ban ko motsa daga cikin bargon da na ke kwance ba afili ma sai da na yi ƙwafa kafin na ce"Ku ci kan ku." Na ƙara shigar da kaina cikin bargo ina ƙara gyara kwanciyata.   Barci ya fara ɗauka ta domin har na fara wani mafarki mai ɗan karan daɗi, kamar daga sama na ji muryan Saude ta na kirana. "Anty. Anty.." A firgice na tashi saboda a saman kaina a can cikin barci na ji kiran sunan.   Saude na gani a cikin Bedroom ɗina daga can baƙin kofa, tana ganin na tashi zaune da sauri ta ce"Anty kin yi baƙuwa." Yamutsa fuska na yi kafin na maimaita kalmar" Baƙuwa? Sai ta gyaɗa min kai kafin ta ce"E. ta ce na faɗa miki Bahijja ce." Shuru na yi ina tunanin wace ce kuma Bahijja, ido na ɗan waro kafin na yi saurin yaye bargon jikina na sauko daga kan gadon lokaci ɗaya ina faɗin" Tana can falo ne? Saude ta gyaɗa kanta kafin Ta ce" E. tana can falon farko." Kai na gyaɗa kafin na ce" Je ki ce mata gani nan zuwa Saude." Ta amsa min cikin ladabi sannan ta buɗe kofa ta fita ta barni ina sauke numfashi.   A gaban madubi na tsaya ina kallon fuskarta sai da na tabbatar da ba ni da wani abu da za ta kalla ta yi ƙorafi sannan na gayyato mirmishi da fara'a a saman fuskata sannan na zura takalmina mai taushi na zirga zirgan cikin gida, na zo zan gota ta jikin madubin sai da na ƙara tsayawa na kurama kaina ido ta cikin madubin ina jin gabbaina suna yin wani irin sanyi ƙalau, yanayin jikina na bi da kallo tabbas ina da son gayu da gyara ni macece da kana ganina kafin ma a faɗa maka wani abu akaina za ka sha shaida ina da son gyara, tun da ga kan gyaran fata na gashi da gyaran ƙasa na mace duka ba na wasa dasu bangaren gyaran fata kayan AISHA LAME +234 703 666 2633 na ke amfani da su, in kuma bangaren kayan ƙawa na gayu ne tun da ga kan atamfofi da abayoyi da takalma a wajen DIJA COLLECTION na kan yi siyayyata da ga ni har su Jidda shi ya sa kayana tare da na ƴaƴana muka fita dabam a cikin Dangi.   Numfashi na ja sannan na ƙara fesarwa, wayata na ɗauka sannan na fice daga ɗakin ba ta kitchen na bi ba sai ta bi ta korido tunda falon farko zan je, ina tafe ne ina latsa wayata na ji na tsorata lokacin da na ga cikin waɗanda suka kirani har da Anty Bahijja, lalle yau Allah ne kaɗai ya isa ya cece ni daga ƙorafi da ƙananun mganganu sai wanda kunnena suka iya ji,  ina tura ƙofar falon lokaci ɗaya tare da sallamata da kuma tahowa da fara'a a saman fuskata. +234 903 661 7473   Ta na hakimce kan kujera mai zaman mutum ɗaya, sanye da dogon hijabi mai ruwan kuka har da liƙabinta, kenan daga makaranta take, ta biyo ta nan ina nufarta ina washe baki lokaci ɗaya ina faɗin"Maraba da Anty Bahijja." Sai a lokacin ta ɗago kanta daga duba wayarta da take yi, sai da na kariso gabanta na zauna saman kujera mai zaman mutum ukun da take gefenta ina faɗin" Ina kwana Anty Bahijja." Sai a lokacin ta iya ɗaga likaɓin ta sama fuskarta ta bayyana. Cikin yanayin maganarta ta kalleni daga sama har ƙasa ni kuma ina ta faman yi mata mirmishi. "Barka dai ta tashi gimbiya ko na ce Sadiya yar laushi ba"   Wani abu mai ɗaci ya taho daga cikina ya tokare a saman ƙirjina. Shi ya sa har abada ba zan taɓa ƙaunar Ma'u ba, kuma ni da ita ba za mu taɓa zama a inuwa ɗaya ba. Amman ban nuna mata ba sai ma na ɓige da yin wani kayattacen mirmishi kafin na ce"Kai Anty Bahijja, ki yi haƙuri kin kirani ban ji ba. Na ɗan kwanta ne." Baki ta taɓe kafin ta ce"Ai fa aikin kenan barci, kina ciki kin kwanta yar aiki na yi miki aikace aikace" Kai tsaye nima na ce" Saude ai tana zuwa tana taimaka mini ne, kinsan aikin gida da yawa Anty Bahijja." "Ina wani yawa a aikin gidan nan Sadiya? Kawai daman kin saba da hutu shi ya sa kike kallon shi a matsayin aiki."   Ni ko sai na yi mata mirmishi duk da maganar ta na sukan zuciyata amman sai na ɓoye hakan a saman fuskata. Kai na kaɗa kafin na ce"Hutun ne ya zo Anty Bahijja  amman karki manta a baya nima na yi aikin." Ta san magana na gaya mata shi ya sa ta yi mini wani kallo, ban bari ta samu damar magana ba na cigaba da faɗin" Kuma Anty Bahijja laifi ne in mace ta samu hutu ta huta a gidan mijinta? Kema fa kina da yar aikin nan sannan ki na fatan nan gaba in su Sulaihat suka yi aure suma su samu gidan da za su huta ko ba haka ba ne? Ba fa wanda ba ya son jin daɗin nan fa."   Na faɗa ina kallonta saboda na ga kuma wata magana za ta ƙara faɗa mini, sai na ga ta juyar da kai ta na faɗin"Ba irin na ki ba Sadiya." Ban yi magana na nima sai na kauda kaina ina ɗan mirmishi, na rasa wani hutu suke hangomin a cikin wannan gidan? Sun manta a baya komai na gidana da mijina da ƴaƴana ni nake yi ma kaina? Saude ba ta fara zuwa mini aiki ba sai bayan mun tare a wannan sabon gidan amman gabaɗaya ƴan'uwan Yusuf gani suke yi da kuɗin ɗan'uwansu na ke walwali ina haskawa sannan na samu duniya ina ta jin daɗina.   Ban ƙara ce mata ƙala ba, amman ita sai faman kalle kallen falon take yi tana wani taɓe baƙi, ba yarinya ba ce tunda Yayar Yallaɓai ce, daga ita sai shi tana da manyan ƴaƴa amman ba taba aurarwa ba suna karatu ne. Can ta ga ji da zaman mulkinta ta kalleni ta na faɗin" Su Jidda suna makaranta ko? Sai na gyaɗa mata kai, kafin na yi magana ta rigani da cewa" Kuma sai satin nan ba ki kai su gidan Yaya Maimuna ba? Me ya sa ?   Daman na san rashin zuwan su gidan Anty Maimuna sai ya zame min abin magana, zama na gyara kafin na  fara faɗin" Ba su samu zuwa ba. Amman weekend ɗin nan in sha Allahu za su je."   Anty Bahijja ta ƙara faɗin" Me ya sa na ke tambaya? Kai tsaye na ce"Gidanmu muka yini ranar asabar, lahadi kuma na ce su tsaya saboda shiryen shiryem makaranta, su goge uniform da homework lokaci ya ƙure shi ya sa sai na ce bari su bari wannan satin da sun dawo makaranta ranar jumma'a zan tsa yar mai mashin ɗin su, sai ya kai su in sha Allahu."   Miƙewa ta yi, lokaci ɗaya ta na rayata jakarta, kafin ta kalleni tana faɗin"Kina  da ƙulafucin ƴa'ƴan Sadiya. To ki yi zuciya ki sake haihuwa mana. Amman ace kamar gidan Yusuf shi da ke son yara a ce ƴaƴa biyu kaɗai gare shi kamar ba shi da wani zaɓi, yanzu in muka ce ya ƙara aure sai ki ji haushin mu ko? Ƙuramin ido ta yi saboda tana so ta ga yadda zan yi, sai ni kuma na nuna mata har yanzu ba ta gama sanin wacece Sadiya ba.   Dariya na saki har ta na fidda sauti kafin na ce" Jin haushi kuma Anty Bahijja? Ai aure umarnin Allah ne shi ya ba su damar ƙarawa, wallahi tallahi na sha faɗa ma Yallaɓai in zai ƙara aure ya ƙara domin ni ba ni da matsala da ƙarin auransa tun da ba akaina za ta zauna ba, kuma ko ta zo sai dai ta zo a ta biyu kin ga kenan ko ya ya dai na ke na amsa sunan Turken gida. Haihuwa kuma ta Allah ce, in ya tsara min ƴa'ya biyu zan haifa shike nan, kuma ni ba zan yi ma Yallaɓaina baƙin cikin ya ƙara aure ya sake haihuwa ba, duk wani abu da ya fito daga tsatson Yusuf abin so ne a wajena."   Kamar ba ta yarda da magana ta ba, domin sai ta ƙara kallona take yi, tana mirmishi, kallonta na yi domin har ta mirmishinta irin na Yallaɓaina ne. Ganin ta kama hanyar barin falon ya sa na miƙe na bi bayanta dai dai lokacin da na ji ta na faɗin"Ke fa kika tsaida haihuwan da kanki Sadiya kin ga ko, ko auran Yusuf ya ƙara bai yi miki rashin adalci ba." Ina bin bayanta na yi mirmishi amman ban yi magana ba.   Ni ce har haraban gida na rakata, ina ce mata"Ba ki zo da mota ba ne Anty Bahijja? Kai tsaye ta ce" Tana waje." Sai na gyaɗa kaina fulawowin gidan ta bi da kallo kafin ta ce" Fulawowin nan sun ƙara ma gidan nan kyau fa." Na biye mata ina cewa" Sosai ni ko ma da farko ban so Yallaɓai ya saka su ba sai bayan sun fara girma sai na ga sun yi ma wajen aiki."   Wani kallo ta yi min ta cikin likabinta  da ta saki kafin ta ce"To gidan ki ne? Da sai kin zaɓi abin da zai saka ma gidan shi? Dariya na yi kafin na ce" Gidana ne mana Anty Bahijja, ko kwatance za a yi gidan Sadiya za a ce ko Maman su Jidda, kamar yadda kema a ke kwatancen gidan mijin ki da gidan Malama Bahijja." Kallona ta yi ido cikin ido ni ko sai na waske ina dariya.   Sai ta bige da yin mirmishi kafin ta ce"kin samu dai kan Yallaɓai ta bakin ki kina yadda kika ga dama, to tunda ya yi miki gida saura mota ko? Ina riƙe baki na ce"Ni Sadiya? Ai ko kuɗin ya samu kuka ji zai siya mino mota hana shi za ku yi Anty Bahijja" Kai tsaye Ta ce"Tabbas. Gwara ya yi aure shima ya tara zura'a  kar ki manta a gidasu mata huɗu cif ne da kimanin ƴaƴa 21 ban da waɗanda suka rasu." Ni ko da gayya na ce"Allah ya bashi kuɗin da zai wadatamu. Sannan sai ya yo auran miye a ciki?   Anty Bahijja ta san halina ko Hajiya Maimuna ba na raga mawa, in suka faɗa min cuta zan faɗa musu mutuwa, duk da suna yayyen mijina, saboda suna da ƙananun maganganu sannan sun sakama rayuwata ido, a wasa ne za su yi ta faɗa minI magana Nima ko a wasa na ke maida musu martani. Anty Zuwaira ce kaɗai ba haka a tsakanin mu saboda ita tana kama girmanta, da yake yar boko ce ga isa da gadara ba ta da ma lokacin tsayawa ƙananun maganganu. Har makaranta private nata na kanta gare ta, sannan ita ma ta kai matsayin Principal a wata makaranta ƴan mata ta cikin gari, sannan uwa uba mijinta a Mininsty of education reshen jihar kano ya ke aiki.   Ban bar jikin get ba sai da Anty Bahijja ta shiga motar ta ta tafi, ina ɗaga mata hannu bayan na ce ta gaida su Suhailat, sannan na rufe get ɗin na koma cikin gida a falon da muka zauna na koma na sake zama. Duk a cikin maganganun Anty Bahijja magana ɗaya ta fi tsayamin a rai. Wai da ta ce ni na tsaida haihuwa da kaina, tuni na ji kaina ya fara sarawa abin nan mai ɗaci ya tokaremin a cikin kirjina ya kasa wucewa, wani tuƙiƙi kawai na ke ji kamar zan shiɗe. Har yau na kasa aminta da ba Yusuf ba ne ya je ya kwance min zani a kasuwa a gaban ƴan'uwan shi ba, tunda ya na da wani hali na faɗi ba a tambayeka ba, sai sai Ma'u ita ce abin zargina na biyu saboda tana auran yaron mai bi ma Mijin Anty Bahijja ma'ana suna aure a dangi ɗaya duk wasu maganganu da suke samu a kaina ta bakin Anty Bahijja ne, ko sunan Sadiya yar laushi da ke bakinta ko na yi rantsuwa ba zan yi kaffara ba daga baƙin Ma'u ne.   Wannan yarinyar tun zuwanta gidanmu na san annoba ya zo cikin zuru'armu, idanuwan kowa ya rufe sun kasa gane tsabar makircin Ma'u da ta yi  gadon shi wajen uwarta Baaba Asiya ta tsotsa a nono, ban san ina hawaye ba sai da na ji danshin saman kumatuna. Baƙin ciki ya cika min zuciya,  me ya sa mutane suke kasa gane wani abu. Mace da Namiji waɗanda ke zaune ƙarkashin inuwa ɗaya ta ma'aurata tsakaninsu sai Allah, ba za ka ji bangare ɗaya ka yankema bangare ɗaya hukunci ba saboda Ubangiji ne kaɗai ya san mai ya ke faruwa tsakaninsu. Ƴan'uwan Yusuf suna ganin kamar komai na ke da shi sanadin ɗan'uwansu na samu Allah na tuba ba kyau tone tone in har da abin da nake dashi ya zauna a hannuna da yanzu na wuce matsayin da nake a yanzu, sun manta a yadda na auri ɗan'uwansu bashi da komai sai kwalin Degree da Masters sun manta gwagwarmayan da muka shafe shekaru sama da goma muna yi tare dashi rana tsaka saboda ya ɗan samu rufin asiri har ana tunanin ya ba ni duniya ina kwance a gida ina hutawa.   Hawayena na share ina jan ƙaramin tsaki, ni ba domin Yallaɓai ya hana ni aiki ba da tuni ba su ganni ina zaman gidan ba, amman in har ya biyani kuɗina da nake bin shi ina nan da tunanin buɗe shagon Saloon kamar yadda na ke buri. Suna alfahari da wannan gidan su a tunanim kamar ya gama mini komai tunda ya gina min wannan gidan sun manta tsawon shekarun da na kwashe ina zaman haya. Maganar auran sa ba ta gaba na ta lafiyata na ke, na riga na shafa faɗama Yallaɓai cewa ba zan taɓa baƙin ciki domin zai ƙara aure ba amman ya sani kafin ya yi tunanin ƙara aure ya yi tunanin mu ya wadatamu da komai na rayuwa da ni da ƴaƴansa ba kuma mu ba mu wadatatu ba, ya je ya ɗauko mata ta zo ita a wahale mu a wahale.   Jikina ya yi sanyin da na ƙasa tashi daga kan kujeran da nake zaune. Yallaɓai na kira domin na tuna masa maganar da muka yi na komawata ganin Gynea Asibitin ABU SHIKA. Ya sake kiran Uncle Abba mu ji yadda suka yi da wani abokin shi da ya ce zai kira a can Zaria zai taimaka mini. Amman ban same shi ba daman wani lokacin  wajajen office ɗin sa ba Network a yi ta neman wayarsa ba a samu. A shekarun baya wani babban asibitin kuɗi ma'ana private Hospital na yi ta wahala da jelangen zuwa ba wani cigaba sai cin uban kuɗi sai aka bani shawara na koma babban asibiti ko Aminu kano ko ABU Shika da ke Zariya. Yallaɓai ya so na zaɓi Aminu kano, ban san me ya sa tunani na ya fi karkata da gwara na fara ganin likita a Asibitin Shika ba. Shi kuma daman Yallaɓai ya na girmama ra'ayina da buƙatuna shi ya sa bai hana ni ba. Daga nan sai na sake buɗe data Group ɗin mu na BUK ya fara ɗaukan Hankalina saboda na ga ana ta massages da yawa kuma ni dai nasan tun da muka gama makaranta ba wani mgana ake yi sosai ba. In magana ta yi yawa to ɗayan biyu ne ko rasuwa ko an samu ƙaruwan aure ko na haihuwa.     Ina shiga ko sai na ga Hauwa Jamilu ce ta haihu ƴ'a mace, ƙawarta Samira Aliyu ne ma ta tura hoton Baby da sanarwan haihuwan, na ƙurama hoton Baby ido mai kyau da ita. Ina son haihuwa ina son na ƙara haihuwa har a cikin raina, ko a ina naga an yi haihuwa sai na ji dama ni ce ko da ace daga shi in na yi ba zan ƙara haihuwan ba.   Tagging na yi sai na yi mata barka a ƙasa kuma nace zan kira wayar ita Hauwan, duk da ban da wata ƙawa sanda muka yi BUK amman kuma ina gaisawa da mutane. Daga baya ma bayan mun gama makaranta na fi zumunci tun da in aka yi rashi ko ƙaruwa ko ban je na kan kira waya in kuma za a haɗa gudummuwa na kan tura nawa. Ina yin maganar Samira na Online ta yi min Reply. "Amin Amin. S Yashe ku kam dai kun gama ko?   Sai na ba ta amsa da cewa" Mun gama me Samira Aliyu? "Haihuwan mana, kin daɗe fa ba ki ƙara haihuwa ba ina jin" Emojin mirmishi na tura mata ban yi magana ba. Ina gani Maijidda Bala, ta yi tagging ɗin maganar Samira da cewa" Ƴan boko ne matar Injiniya guda ko matar Yallaɓai zan ce? Sai da na yi dariyan Sarari saboda ko username ɗina Sadiyar Yallaɓai ce a rubuce.   Kuma Maijidda Bala anguwanmu ɗaya, ta san gidanmu na san na su , duk halina na rashin son sakewa da mutane amman Maijidda na zuwa gidanmu saboda Rahila, to daman duk wanda ya zo gidanmu saboda Rahila ce ko Ma'u su ne masu jama'a. Ba zan taɓa mantawa da maganar Mama tun muna ƴan mata ta sha ce mini" Ke kam Sadiya da wuya ki ta shi aure ki ga jama'a. A yi mutum ba shi da son shiga jama' a kwata kwata." A lokacin dariya na kan yi kafin na ce"Shike nan sai ke da Gwaggo ku ci min ƙawayen amarya."   Allah Sarki Mama Allah ya sa kina aljannah. Ban biye ma mangaganunsu ba na sauka saboda kar na manta nan take na kira Hauwa na yi mata barka, har tana mini tsiyan ni na gama na ji daɗi na. Mirmishi kawai na yi ban yi magana ba. Saboda ko me zan ce ba za ta gane ba sai da na ji tana faɗin"Nima daga wannan na faɗa ma Baban Afnan na gama wallahi. Allura zan je a yi min na shekara biyar." Da sauri na ce"Kul ɗin ki Hauwa. Karki yi wannan gangancin, in kika tsaida haihuwa na shekara biyar to za ki yi ta nadama har na shekaru ashirin ba ki daina ba. Saboda lokacin da kike son ki ƙara haihuwan ba za ki samu wannan damar ba."     Na faɗa ina jin raɗadin abin a cikin raina Hauwa ko cewa ta yi" Ko Sadiya? Sai kawai na rausayar dakai kamar tana ganina kafin na ce" Ku yi na gargajiya ko na musulunci Hauwa. Saboda haka ina gargaɗin ki in ba so kike yi ki ƙare a zuwa gaban Gynea ba." Hauwa na jin haka sai ta ce to shike nan za ta yi magana da Daddyn Afnan duk yadda ta so na yi mata wata mgana ban yi ba saboda ba close na ke da ita ba, rayuwa ai darasi ne  amman da zan buɗe mata cikina sai ta ji tunanin da ke cikin ranta ya fita ba domin komai ba sai tsira daga faɗawa irin halin da ni na faɗa.   Ina nan zaune ina ɗan duba wayata amman ban shiga group ɗin gidanmu ba sannan ban shiga na ɗaiɗaikun su da suka yi min magana ta private ba saboda nasan tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi. Fita na yi zuwa Instergram ina kallon kwalliya domin  ni Allah ya yi da son abu fashion. Domin har certificate gare ni akam koyon kwalliya ba ma ɗaya ba sannan ina da na koyon saloon da gyaran jiki, shi ya sa wayata cike suke da ire iren su.  Ban san na ɗau lokaci haka ba sai da Saude ta zo ta ce mini ta gama da ciki za ta gyara falo sannan na ba ta waje, bayan na ce in ta gama ta ɗora min ruwa a gas ta dafa taliya fara tunda ina da miya a firiza.   Bedroom na koma na yi zama ma ina ta kallon Videos ɗin yadda ake kwalliya da na ɗaurin ɗan kwalli a istergram daman ni can na fi auki, kiran sallar azahar ya tada ni na ijiye wayar na je na yi sallah lokacin har Saude ta tsane taliyan da na ce ta dafa guda biyu, ni na karɓe ta na ce ta shiga ɗakin su Jidda ta yi sallah ni kuma sai na fito da miyar na ɗumama. Na saka ma kaina sauran kuma na bar shi a cooler.  Ƙaramin falo na koma na kunna kallo sai na sauya tasha zuwa Mb2 na iske a wani film mai kyau sai na barshi, filet ɗin abincin na kan jikina ni kuma na miƙe kafata saman cafet ina cin abinci ina kallo har Saude ta fito sai na ce ta ɗauko kofin ta tsiyayo mini ruwa a Dispenser.   Sai ta kawo mini sannan na kalle ta ina faɗin" Ki ɗiba abinci ki ci sai ki zo ki wuce gida kin san kina da makaranta." Da toh ta amsa min ta wuce kitchen ta diɓo taliyan ta zo ta zauna a kasa ta na ci, ba hira muke yi ba sai ni ce ma ke mata tambayoyi. "Babanku ya dawo? Sai ta ce min a'a sai na girgiza kai kawai, lagos ya ke zuwa kwadago in ya tafi sai ya yi rabin shekara bai dawo ba ya bar iyalansa da wahala. Ni na riga ta tashi, na tafi da filet ɗin hannuna da kofi zuwa kitchen na saka a sink ɗin wanke wanke. Leda na samu na buɗe drower ɗin cabinet ɗin kitchen ɗin na auna mata shinkafa tiya biyu sai taliya da maracaroni da na diɓar mata tunda nima abincin nawa ya yi ƙasa.     Bedroom na koma na ɗauko mata 2k daga cikin jakata sannan na dawo falon lokacin ta gama cin abincin sai na ce ta wanke hannu ta zo. Ina zaune ta zo ta zauna gabana ta na faɗin" Ga ni Anty" Ledan na tura mata gabanta lokaci ɗaya ina mika mata kuɗin hannuna ina faɗin"Ki kaima mamanku kin ji ko? Ta karɓa tana faɗin"An gode Allah ya saka da alheri." Na amsa da Amin ina faɗin"Ki yi sauri ki hau mashin ne biyu ta kusa." Sai ta amsa minI, tare muka fita saboda zan rufe gida tana fita na maida gidan na rufe na dawo falo ina kallo, film ɗin horror ne ya ɗauki hankalina sai da aka gama shi amman za a yi part 2 ɗin shi. Uku na rana na koma ɗaki na kwanta sai barci ban ta shi ba sai huɗu da rabi, sai na yi alwala na yi sallah na ga tunda huɗu ta wuce sai kawai na ce bari na yi azkar ɗina.   Ni kaɗai a gida kamar mayya na matsu su Jidda su dawo sai shidda suka dawo saboda biyar da rabi ake tashin su kafin ya je ya ɗauko su shidda ta yi tunda makaranta boko da isalamiya ne. Dawowarsu ne ya sa na fito falo suna bani labaran makaranta suna cin abincin, Baby ce mai surutun Jidda irin Babanta ne tana da sanyi sosai ba kamar Baby ba. Suna gama cin abinci suka sauya kaya zuwa na gida. Unform ɗin Jidda ta ce za ta wanke na ce yamma ta yi, tunda suna da guda biyu ta bari zan wanke musu gobe da safe   Tare muka yi sallar mangariba, muna idarwa a ƙaramin falo muka fara karatu. Jidda na suratul maryam ne Babby kuma tana ƙasa ƙasa sai da suka biya na jiya na ƙara musu sannan muka yi azkar tare. Muna gamawa sai muka miƙe muka yi isha'i tunda an kira. Muna idarwa na bar su a falo suna kallo ni kuma na shiga kitchen na dafa ma Yallaɓai tea daman na dafa masa farar shinkafa tunda shi taliya ba ta dame shi ba, ina gamawa na shiga wanka ina wankan ma na ji shigowar motar Yallaɓai.   A gurguje na shirya cikin riga da wando, wandon plazo ne mai buɗewa ta kasa. Rigar kuma Top ce mai wuya ta kama jikina sai na gyara gashin kaina na tufke a tsakiya na saka wata hula mai love a saman kaina kalan pick .  Tsakiya babu komai, kwalliya na yi kamar yadda na saba na saka jan baki na kamar yadda na saba. Na ji ƙaran bude ƙofa ganin bai shigo ba ya sa na san ya shiga tiolet ne. Ba jimawa sai gashi ya shigo da sallama ina zaune a gefen gado ina bin shi da mirmishi bayan na amsa sallamarsa.   Hannuwana ya buɗe minI na tashi da sauri na faɗa masa ya rumgumeni. Nima sai na ƙamƙamesa ina fadin"Barka da dawowa Yallaɓai na." Ya na shinshina ƙamshin humran dake jikina ƙasa ƙasa ya ce" Uhm. I like it."   Ɗagowa na yi muna kallon juna kafin na ce'Me? Yana mini wani kallo ya ce"ƙamshin ki mana." Far na yi masa da ido kafin na ce"All is yours" Kumatuna ya shafa kafin ya ce" Allah ya yi miki albarka." Na amsa da Amin. Ruwan wanka na ce zan haɗa masa ya yi wanka sai ya ci abinci. Shi kuma sai ya ce"E. sai mu ta fi wajen kiran Alhaji ba"   Gyaɗa masa kai na yi ba tare da na yi mgana ba. Sanda ya shiga wanka ni kuma na je haɗa masa abinci bayan ya fito ya sauya kaya zuwa wani yadi riga da wando ɗinkin zamani. Falon farko mu ka je saman dining ya ci abinci su Jidda kuma suna ƙaramin falo Bayan mun gama ba mu tsaya ɓata lokaci ba ya ce na saho hijabi mu ta fi, daman na fito da Hijabin jalbab mai ruwan ƙasa har ƙasa sai na saka takalmina iri ɗaya da wanda Yallaɓai ya saka daman tare ya siya mana.   Na ce musu Jidda su kula da gida za mu je gidansu Gwaggo mu dawo. Baby taa saka rigiman sai ta je Babanta ya tsaya yana lallashinta da zai siyo mata ice cream sannan ta yarda na ce in za su kwanta su kashe komai za mu fita da key da toh Jidda ta amsa da yi mana a dawo lafiya. Sai da muka fita da motar sannan Yusuf ya koma ya rufe get ɗin Sannan ya dawo muka kama hanya mun ɗauki hanya kenan na kalle shi kafin na ce" Na gwada kiran ka yau ban same ka ba." Hankalinsa na wajen tuƙi ya ce"Nima na kira ki ban same ki ba." Sai ya kalleni kafin ya ce"Me ya faru? Kai tsaye na ce"Kan mganar komawata Abu shika ne, Uncle Abba bai ƙara kiran ka ba? Sai a lokacin ya tuna ya ce"Kash! Ya kirani amman shaf na manta ba mu yi mganar ba. Amman bari yanzu zan kira shi."   Ni ya miƙa ma wayar ya ce na kira shi, Kawu Abba daman ya saka masa da na kira sai na saka a speaker har ta kusa katsewa sannan ya ɗauka. "Kawu barka da dare." Shuru bai yi mgana ba. "Uncle Abba barka da dare" Wata murya a dakushe ya ce"Yusuf in ma bashi kake nema na kuɗi ba ni dashi wallahi. Wanda ma nake binka EFCC ne za su ƙwatar mini haƙƙina."   Daga ni har Yusuf sai da muka kyalƙyace da dariya. Ni ce na ce"Haba Uncle Abba ba amana yanzu sai ka kai mini Yallaɓai EFCC? Jin muryata ya sa ya ɗan yi dariya kafin ya ce" Sadiya?  daman kina kusa? Na amsa masa da e, sannan muka gaisa dashi. Shi kuma sai ya bige da faɗin"Yallaɓan nan naki ya ci bashina kamar gadon ubansa yaƙi biyana. Gwara babbar hukuma ta shiga ciki, in na je gaban manya sai a saka sanayya a ciki gwara a kame shi ko amansu ne sai ya yi." Yusuf na dariya ya ce" Na ci fa halas, abin da ya yi Nene shi ya yi ka fa Kawu Abba." Kai tsye ya ce"Ko? To ai ko ita Nenen ta ci kuɗina sai ta biyani ballatana kai." Ni dai ina ta dariya ganin sun sarƙe da gaddama shi Yusuf ya na faɗin ya ci halas kawu na fadin shi ba ƙanin Uban shi ba ne na uwarsa ne bashi da gadonsa. Zungurin kafar Yallaɓai na yi sannan ya yi gyaran murya yana fadin"Sadiya ta ce a yi maka tuni ka yi mganar da Dr Fadil ɗin? Kawu Abba dagacan bangaren ya ce"Kash na manta. Amman bari na kira shi na ji yadda muka yi zan kira ka."     Sai ya kashe wayar, dai dai Yusuf na faɗin" Kina ganin komawarki can da ganin likitan ba damuwa? Sai na gyaɗa mai kai ina fadin"E, ba matsala can ma ƙwararru ne. Tunda na yi ta nan ban dace shi ne aka ban shawara na gwada can ɗin." Sai ya jinjina kai, bai yi magana ba sai ni ce na cigaba da faɗin"In ina da appoitment na ganin likita tun ana gobe zan je zariya na sauka gidan Ya Hamza bayan na gama ganin likitan sai na dawo."   Kai tsaye ya ce"E  hakan ma ya yi. Allah ya sa a dace." Na amsa masa da Amin. Mun shiga anguwan ɗorayi kawu Abba ya sake kira ya ce sun yi mgana da abokin nashi Dr Fadil shi likita ne a bangaren zuciya amman ya ce ya yi ma wata Dr Nayami mgana musulma ce amman ba bahaushiya ba ce, ya ɗan yi mata brief na matsalata ta ce zuwa sati mai zuwa za ta iya bani appiotment in har ya tabbata zai kira Kawun ya sanar dashi.   Jin haka ya sa sai na ji daɗi kamar na je ta shaida mini zan iya sake samun wani cikin haka na riƙa ji.  Daidai lokacin Yallaɓai na gyara parking a kofar gidanmu da ke anguwan Ɗorayi. *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU  #1k NE KACAL,  AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *03/10/2024* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JMpd8nXr7TIDD3ILDXh64z *🅿️03* Gidanmu na nan a farko layin shiga anguwar Ɗorayi. Yanayin fasalin gidan babba ne sannan tun daga waje za ka fahimci tsarin gidan na tsohon ɗan boko ne. Domin Alhajinmu  kafin ya yi Ritire(Ritaya) sai da ya riƙe mukamin babban darakta na kamfanin wuta na jihar kano(KEDCO). Bayan kasancewarsa manomi. Kuma gidanmu na da ga cikin rukunun gidajen da suka daɗe a anguwar tun da sama da shekara ashirin duk da ko mu kanmu muna da wayau lokacin da muka dawo gidan tun a wancan lokacin zamani na kwance. Sai dai yanzu lokaci bayan lokaci yana samun ƴan gyare gyare da kwaskwarima daga su Yaya Hamza.   Ni na fara fitowa daga Motar. Yallaɓai na kuma an kira wayarsa ya tsaya a mota ya na mgana. Kofar gidan namu tar da hasken wuta gabaɗaya ma anguwa akwai hasken ƙwakwayen da suke kofar gidajen wasu mutane dake cikin rukunin anguwan ta Ɗorayi. Gidanmu na ke kallo ina tuna wasu shuɗaɗɗun al'amura da suka faru damu a cikin gidan masu daɗi da akasin su. Yallaɓai ne ya katse min tunani da cewa" Kin ga ko na manta ɗazu musabahu ya zo offishina ya bani saƙo ya ce in ji Yaya Muntari mijin Rahila."   Sai a lokacin na ɗago ina kallonsa ya fito daga mota ya na nuna min kullin abu a baƙar leda, yadda ya ga na taɓe baki ya sa ya san tabban nasan da saƙon. "Bar shi a motan kawai."   Bai yi musu ba sai ya koma cikin motar, ina hangensa daga waje ya buɗe akwatin motar ya jefa sannan ya fito yana ƙoƙarin rufe motar hasken wata mota da ke tunkaromu ta kashe mana ido daga ni har shi sai da muka saka hannuwammu muka kare fuskokin mu dashi. "Kai. Waye wannan da ba zai rage filita tunda ya shigo cikin anguwa ba."   Na kasa magana ne saboda mamakin ganin motar ba wucewa ta yi ba, kusa damu itama ta gyara parking, tun kafin ma na ciki su fito na shaida su waye tun daga cikin motar akwai hasken fitila. "Ma'u ce.." Haka na faɗa a cikin raina dai dai san da ta buɗe murfin mota ta fito shima mijinta ya fito daga can bangaren direba. "Alhaji Mustapha ne, da Ma'u ashe."   Yusuf ya faɗa ya na sakin mirmishi, na kalle shi wani abu ya yi mini tsaye a zuciyata. Lalle Alhajinmu wato zaman yau bayan ni da Ma'u har da gayyar mazajen mu kenan?   Kara haɗe rai na yi, ganin Ma'u na nufoni shi kuma Yusuf ya nufi Alhaji Mustaphan shi adole ya ga ɗan'uwan mijin yayarsa. Ƙaramin tsaki na ja dai dai lokacin da Ma'u ta ƙariso kusa da ni ta na faɗin"Sadiya kema Alhajinmu ya kira ku ne ke da Injiniya?   Ta faɗa lokaci ɗaya ta na ɗora hannunta saman kafaɗata. Sai na ji kamar ta ɗora min cuta da sauri na kauce ina yi mata wani irin kallon ke ki kiyayeni. Ita kuma ta na bi na da wannan munafukin mirmishin nata na yaudara.   Ƙoƙarin sake matsowa kusa da ni take tana yi min mirmishinta da ba alheri a cikin sa. Tsaki na ja mai karfi na juyawa na fara tafiya zuwa ƙofar da za ta sada ni da cikin gidanmu na ji muryan Ma'u da ɗan karfi ta na faɗin"Haba Sadiya. Ke shike nan abu ba ya wucewa a wajen ki? Na yi ta ba ki haƙuri fa?   Sai da na kai kofar gidan sai na juya ina kallonta sai na ga har su Yusuf ma sun dawo da hankalunsu kan mu, dariyan gefen ba ki na yi. Ni ai sai dai na rubuta littafi guda akan maƙircin Ma'u daman ta yi ne domin hankulansu ya dawo kan mu, shigewata cikin gida na yi ina ji Yusuf na kiran sunana na yi masa banza na yi shigewata na bar su nan ƙofar gida.     Dogon korido ne mai ɗauke da ɗakuna uku na waje, biyu suna rufe ne sai guda ɗaya ne a buɗe. A raina na ce kila Datti ya zo gida ko kuma an yi baƙin maza daga Yashe ko Yan tumaki. Ban gama mamaki ba sai ga Datti ya fito daga cikin gida sai muka ci karo da juna. "Datti.." Na kira sunan shi, sai  ya kalleni domin fitowarsa daman hankalinsa na kan wayar hannunsa. Daga shi sai baƙin wando da farar singileti. "Yaya Sadiya? A daran nan? Ya faɗa yana kallona, jiyo muryoyinsu Yusuf suna ƙokarin shigowa ya sa na raɓa ta gefensa na wuce, ina jin sa ya na tambaya ta. "Ke kaɗai kika zo? Ina Yallaɓan da su Jidda?   Ko juyowa ban yi na faɗa tsakar gidanmu da sallama. Gwaggo na Madafi na kuma nasan shayi ta ke dafama Alhajinmu da tun tasowarmu nasan ba ya iya barci sai ya sha wannan ruwan zafi. Ita ta amsa min sallamata tana kuma leƙowa muka ci karo da juna tsakar gidan tar yake da hasken  gulop.   "Maraba da Hajiya Dubu."     Sai na sa ki mirmishi ina faɗin"Kai Gwaggo ni dai wannan tsohuwar ta mutu ba ta bar mini gadon komai ba sai na sunan ta." Gwaggo na dariya ta ce"Ka ji min ƴar nema. Ai ko ita ta bar miki gado tunda ta bar miki gadon suna mai daraja irin Halimatussadiya."   Ya na iya?. Domin in dai  Gwaggo ce ta riƙa sharhin sunan kenan da kawo tarihi. Gaisheta na yi cikin girmawa ta amsa ta na faɗin"Na gan ki ke kaɗai ina shi Yusufan? Na rausayar da kai kafin na ce"Ga shi nan shigowa."   "Oh. To ina yaran suke? Ko can gida kuka baro su? Ban amsa mata tambayarta ba. Sai na bige da faɗin"Alhajinmu na ciki ne Gwaggo? Na faɗa ina kallon ƙofar falon shi da na hangi hasken wuta.   "E. ya na ciki tun ɗazu ya dawo. Zaman jiran ku yake yi. Domin nima sai yanzu ya ke yi min taɗin kuna tafe ke da Ma'u"   Ta na dire maganarta sai ga sallamar Ma'un ban tsaya ba ni kuma na kara sauri zuwa falon Alhajinmu. Da nesa kaɗan dashi ɗakin Gwaggo ne shima akwai hasken wuta daga cikin ɗakin, kusa da shi kuma ɗakin Mama ce a sakaye, daman in dai ba mu ne muka zo gida ba, ɗakin Mama yana yini a sakaye ne Ɗakin na kallah ta window ya yi duhu alamun an kashe hasken ɗakin gabaɗaya ƙwallah suka taho min na yi saurin shanyewa amman a fili sai da na furta" Allah ya yi miki Rahama Mama." Lokaci ɗaya na cire takalmina akofar ɗakin Alhajinmu na shiga da sallama a bakina.   Alhaji Sulaiman Abubakar Yashe(Alhajinmu) na zaune a saman kujera mai zaman mutum biyu cikin jerin kujerun da suka yi ma falon kwanya. Falon da na girma sosai shi ya sa sai kujerun suka zama a can tsakiya.   Alhajinmu ba tsoho ba ne, ko na ce yanayin jikinsa na ɓoye shekarunsa. Ya mori jiki saboda bashi da kiɓa tun zamanin samartakansa har kuma girmansa. Dattijo ne wankan tarwaɗa,  mai matsaikacin faɗin fuska da furfura ta gama zagayewa. A shekarunsa zai iya haura 65 amman kuma ba zai ga za  67 ba.   Cikin yanayin maganarsa da zafin murya irin ta Alhajinmu ya amsa min sallamata. "Amin wa'alaikis salam. Dubu ce tafe? Sai da na ƙarisa gabansa na zauna ina faɗin"Ni ce Alhajinmu barka da dare." Yana yar dariyansu ta manya ya ce"Barkan mu dai. Yana ganki ne kaɗai ko Yusufan ya na waje ne? Ko kafin na samu zarafin magana Ma'u ta yo sallama ta shigo bayan ta kuma mijinta ne Alhaji mustapha da Yallaɓaina Injiniya Yusuf.   Itama gaban Alhajin ta zo ta zube ta na gaishe shi, ni dai na matsa can gefe na jingina da kujera suma su Yusuf nan kasan cafet ɗin da ya malale ɗakin suka samu mazaunin zama cikin girmamawa suna gaishe da Alhajinmu ya amsa cikin sakewa da dattako, sai ya karkata kansu yana tambayan su aikinsu da sauran harkoki.   Ni kuma kaina sai na dukar da kaina ina duba wayata ganin har tara na dare ta gota da kaɗan. Ita kuma Ma'u sai ta tankwashe kafa kamar mutuniyar kirki kanta na ƙasa ban san abin da ta ke yi ba.   Shigowar Gwaggo ɗakin dauke da shayin Alhaji ya katse hiran ta su, ta miƙa masa a wani ƙaramin mug ya karɓa ya na faɗin"Na gode Maimuna. Allah ya yi albarka" Ta amsa da Amin. Sannan ta juya suna gaisawa da su Yusuf tunda da suka shigo ta ce su shiga itama ga ta nan zuwa.   "Ma'u ya gida ya yara? Ina su Alhaji karami? Gwaggo ta faɗa ta na kallon Ma'u. Ita kuma sai ta ɗago ta na faɗin" Lafiyan su lau Gwaggo na baro su gida tare da Zainab"   Gwaggo ba ta yi shuru ba sai ta kara cewa" Ya gajiyan ku? Kun sha suna. ke ce kawai daman da Sadiya ba ku biyo ta nan ba ranar sunan" Gum na yi da bakina saboda daman in dai Ma'u na magana ba na saka baki, can na ji ta na ce ma Gwaggo wai mun yi dare ne shi ya sa ba mu biyo ta gidan ba.   Shi kuma Alhajinmu sai da ya yi rabin da shan shayinsa sannan ya kalli su Yusuf ya na faɗin"Ban yi muku ta yi ba, ko Maimuna ta haɗa muku shayin ne? Alhaji Mustapha ne ya yi saurin cewa" Mun gode Alhaji." Yusuf dai bai yi magana ba saboda na ji an kira wayarsa bai ɗauka ba ina jin sai ya sakata a silet.   Ficewa Gwaggo ta yi daga Falon zuwa ɗakinta. Ta bar mu daga mu sai Alhajinmu sai da ya gama shan shayinsa sannan ya kalleni yana faɗin"Dubu kai kofin can madafi"   Ya faɗa yana mika min mug ɗin hannun shi da ya gama shan tea, sai na miƙe da sauri na karɓa na fita zuwa tsakar gida na tura kofar madafin tun da har Gwaggo ta sakaya ban ijiye ba sai na diɓi ruwa a katon botoki mai murfin ɗin dake cikin madafin na tara a sink na wanke shi, tunda madafin gidanmu ya daɗe da komawa na zamani na kife kofin saman cabinet ɗin kitchen ɗin sannan na fito na sakaya shi kamar yadda na ga Gwaggo ta yi.   In da na tashi nan na koma na zauna. Sai sannan Alhajimu ya gyara zama ya na sanye da jallabiya mai ruwan madara kansa ba Hula sai furfuran da suka masa kwanya daga kansa suwa gemunsa da sajensa. "Ma sha Allah, na ji daɗin yadda bayan na kira ku kuka amsa kirana. Allah ya yi muku albarka gabaɗaya."   Muka amsa da Amin gabaɗayanmu. Alhajinmu ya kalleni sai ya kira sunana da sai irin haka mgana mai muhimmanci ya ke kiran sunana bayan Dubun da yan kirani. "Halima.." Sai na ɗago na kalle shi lokaci ɗaya ina mai amsawa. "Na'am Alhajinmu." Sai ya karkata kan Ma'u itama ya kira sunanta. "Asma'u.."   Itama ta amsa da na'am Alhajinmu Sai ya cigaba da faɗin" Kusan dalilin da ya sa na ce ina son ganin ku wannan karon tare da mazajen ku? Dukkanmu muka girgizanmu kanmu kafin mu haɗa baki wajen faɗin"A'a Alhajinmu."   Kai ya gyaɗa kai kafin ya ce"To ba saboda komai ba ne sai dalilin bayan ni kuna da wasu shugabbanin da in kuka yi ba dai dai ba, za su iya yi muku faɗa akan ku gyara kamar yadda ni zan yi muku. Mazajen ku su ne alhakin duka rayuwarku da tarbiyansu yake hannunsu bayan na aura musu ku, shi ya sa wannan karon ganin wannan rigimar da sheɗan ya ba da gudummuwa wajen gina ta a tsakaninku da ta ƙi ci ta ƙi karewa  na yi tunanin saka mazajen ku a ciki, saboda ba na so na faɗi na mutu a zaman makokina ke Sadiya da ke Asma'u a ce bakwa yi ma juna mgana akan abin da bai kai ya kawo ba."   Sai ya dakata ya na nazarin mu, dukkanmu kan mu na ƙasa ba wacce ma ta ɗago. Sai ya karkata hankalinshi zuwa ga mazajen mu. "Yusufa. Cikin ladabi ya ce"Na'am Alhaji" "Mustapha." Shima cikin ladabi ya amsa da Na'am Alhaji.   Sai Alhajnmu ya gyara zama ya na faɗin"Ban sani ba ko kun taɓa sanin tsakanin matayen ku ba a ga maciji? Ma'ana ba sa haɗuwa waje ɗaya su yi rabuwan lafiya? Wataƙila za ku iya fahimtar ba sa shiri da juna amman na san ba su taɓa zama sun warware muku lamarin yadda za ku fahimta ba.   Wannan karon Alhaji Mustapha ya fara faɗin" Haka ne Alhaji. Ban dai san me ya ke haɗa su ba amman Sadiya ba ta zuwa gidana sannan ko haɗuwa muka yi ni da ita in dai ba ni na yi mata mgana ba. Ba za ta yi mini ba, na taɓa tambayan Ma'u ko akwai wani abu a tsakaninta da Sadiya ne amman ba ta ce komai ba"   Ya karishe faɗa yana kallona, nima ko na ɗago muka kalli juna na kauda kaina domin ba ƙarya ya faɗa ba mun sha haɗuwa da shi gidan Anty Bahijja sai na yi kamar ban gan shi ba in har bashi ya yi mini mgana ba. "Kai fa Yusufa? Ka taɓa fahimtar wani abu? Cikin girmamawa ya ce"E. Na fahimci ba shiri tsakaninsu. Amman na ɗauka faɗa ne kawai na ƴan'uwa ba mai tsananin da zai haifar da matsala ba ne Alhaji."   Alhajinmu sai ya sauke numfashi kafin ya ce"Kowa ma haka ya ɗauka daga farko farko. Amman suna ƙara girma lamarin na su na ci gaba, tun suna yara har suka girma na aurar da su gare ku, suka hayayyafa suka zama iyaye sun tashi daga yara sun koma uwaye waɗanda ba zan ce ba su san ciwon kansu ba. Sun sa ni tunda Tarbiya ne ma a ƙarƙashin ikon su, daga lokacin ne na fara fahimtar lamarin ya wuce tunanin zai tsaya anan ina tsoron kada su mutu su bar ƴaƴansu cikin muguwar gaban da sheɗan ya kulla a tsakanin su."   Dalon sai ya yi shuru, Alhajinmu kuma bayan ya yi shuru na wani lokaci kafin ya cigaba da faɗin"Ba yau ne na saba sulhu tsakanin Halima da Asma'u ba, tun yan'uwansu na yi musu ban sani ba har ya fi karfinsu suka dangana da ni, na yi nasihan da ban baki sai sun ce sun bari amman ba a daɗewa sai an zo an faɗa mini sun haɗu kuma sun yi faɗa. Wannan zaman saboda dalilin faɗan ne da suka haɗu shekaranjiya a gidan sunan ƴar Rahila. Murja ta zo har gida nan ta na faɗa mini a gaban mutane ke Halima kika yi ta ma yar uwanki ɗiban albarka, ita kuma an ce Asma'u haƙuri take ba ma Sadiya amman dai sun sanar dani faɗan dalilin ita ƙawar Asma'un ce da ta je sunan ƴar Rahilan"   Yusuf ya ce"Subhanallah" Shi kuma Alhaji Mustpha ya kaɗa kai kafin ya ce"Asha. Abu bai yi daɗi ba." Ni ko kaina na ƙasa a raina ina mamakin Yaya Murja, ko miye riban ta na zuwa ta karantama Alhaji komai?   "Wannan dalilin ya sa na ce zan saka ku a ciki. Gani ga ku zan tambayesu ɗaya bayan ɗaya menene haƙikanin matsalansu da ko da yaushe suka haɗu sai sun yi faɗa? Ko sun manta su ƴan uwan juna ne dangi ɗaya? Ko ke Sadiya kin manta matsayin Asma'u a gare ki ne? Ko ke Asma'u kin manta matsayin Sadiya a gare ki ne?   Ya ƙarishe faɗa ya na bin mu da kallo, kowaccen mu ta kasa ɗagowa saboda nauyin idanuwan Alhaji a kan mu.   "Ke Sadiya ke ce Babba da ke zan fara. Ɗago ki kalle ni"   Ba ni da mafita illa ɗago kaina ina kallon Alhajinmu cikin muryansa a kaushashe da ɓacin rai ya ce"Halima na san halin ki, kina da tsiwa da mgana sannan ke ce daman ko faɗa aka yi dake ko an yi sulhu ba kya hakura ki yi ta gaba saboda daman gaba ba ta yi miki wahala. Ki faɗa mini gani ga Asma'u da mijinki wani irin abu ne Ma'u take yi da ba ki so? Ki faɗa mana sai ta ji ta ba ƙi hakuri ta kuma ɗauki alkwarin za ta daina yi miki saboda ku samu zaman lafiya"   Shuru na yi na wani lokaci kafin na ce"Alhajinmu ba fa ni kaɗai na tsani Ma'u ba. Itama ta tsane ni tun zuwanta gidan nan ba ta sona nima ba zan maka ƙarya ba ba na sonta Alhaji. In kuma ana son a samu zaman lafiya to Ma'u ta daina bin hanyata ni daman ba ta gabana domin na fi ƙarfinta Alhajinmu ka raba tsakanina da  Ma'u don girman Allah."   Na karishe faɗa har ina haɗa hannu alamun roƙo, gabaɗaya ni suke kallo har Ma'u sai kawai na ga ta fashe da kuka, ban ko razana ba domin kaɗan daga cikin makircin Ma'u kenan. Yusuf kuma ni ya ke kallona, saboda ya san halina ina da taurin kai, in na kuma ce na tsani abu to da gaske na ke yi ba na son shi. "Innalillahi ni ko Sadiya me na taɓa miki a rayuwa da kika tsane ni haka?   Kai tsaye na ce" Ban sani ba. Ke za a tambaya abin da na yi miki kika bi kika addabi rayuwata kina yi mino bita da kulli a wajen iyayena da ƴan'uwana wannan bai isheki ba kin fara yi min ta bangaren dangina mijina wannan bai isheki ba sai kin je kina yamaɗiɗi da ni cewa planning na yi shi yasa har yanzu na ke neman haihuwa ido rufe ban samu ba, har wannan matsiyaciyar ƙawar na ki ta kalli tsabar ido na tana gaya mini mgana."   Na ƙarishe faɗa cikin tsawa domin nima raina ya ɓaci. Tuna abin da ya faru da a gidan Rahila kaɗai kan haifar mini da ƙuncin zuciya.   Daga Alhajinmu har su Yusuf shuru kawai suka yi suna kallon mu. Ma'u ta na kuka ƙaryan da ta saba na yaudaran mutane ta fara rantsuwa ta na faɗin" Wallahi tallahi in kin yarda dani Sadiya ban san a ina Shema'u ta ji wannan labarin kuma, a gabanki na yi mata mganar ban ji daɗin abin da ta yi ba, saboda haka ya sa ko yau ta zo gida ta na faman bani haƙuri ban saurareta ba. Har a waya tana ta kirana ban ɗauka ba domin na faɗa mata ba ke ta tozarta ba ni ta tozarta domin abin da ya yi ki shi ya yi ni Sadiya da ni da ke bamu da bambamci" Ta ƙarishe faɗa tana shesshekan kuka sai kuma ta kalli Alhaji tana cigaba da faɗin"Alhaji wallahi Allah ɗaya kenan ba ni da wani mugun nufi kan Sadiya. Ina son ta kamar yadda na ke kaunar yar uwata Zainab, ina son ta ƙwatankwacin yadda nake son su Rahila. Amman ban san me ya sa Sadiya ta kasa fahimtata ba, Alhajinmu ko rashin fahimtar da ta faru a baya ta maganar aurena da Yaya Hamza tabbas raina ya ɓaci kuma na ji haushin Sadiya amman har ga Allah daga baya na cire abin a raina ban taɓa kallon Sadiya dashi ba. Ni ko me ya sa zan yi haka? Alhaji Sadiya ce ba ta sona ban kuma san me na yi mata ta tsane ni ba tana hulɗa da kowa Alhaji ban da ni in dai abu ya shafe ni Sadiya tsame hannunta ta ke yi a ciki ba ta zuwa gidana ni in na je wallahi ko bare Sadiya ba ta yi masu abin da ta ke yi mini, in muka haɗu a gida ko gidajen ƴan'uwa Alhaji ko na yi ma Sadiya magana ba ta yi mini ta yi ta gaba da ni. Na zauna ta yi ta tunanin abin da na yi ma Sadiya ta tsane ni amman na kasa ganewa, daga baya sai na fara tunanin ƙila saboda Alhaji ka ɗauke ni ka sanyani cikin Iyalanka ne, ita kuma Sadiya ba ta so wani daga waje ya raɓe ta, sai kuma daga baya na kwaɓi kaina da cewa ai ni ba  bare ba ce Alhajinmu ni ma ƴarka ce kamar Sadiya"   Ta faɗa har ta na riƙe kafar Alhaji, tana kuka, gabaɗaya na san ta gama cika zuciyar Alhaji da tausasa kalamanta. Ni ko a raina ban ji na yi nadama ba, kallonta na ke yi ina mamakinta har ta manta mganganun da ta gaya mini a lokacin da aka fasa auranta da Yaya Hamza? Har ta manta?   "Tashi. Tashi Asma'u. Ke kam ba bare ba ce ke ƴa ce kamar Sadiya. Ta shi daina kuka kin ji bari kuka nan"   Ya faɗa cikin sigan lallashi, Alhaji Mustapha har da mika mata wani farin hanky, ya na faɗin"Ki share hawayen ki  Ma'u" Ba wanda ya fi baƙanta min rai irin Yusuf har da shi a masu ba ma Ma'u hakuri daman halinta ne ta shirya makirci a raja'a a kanta.   Tsaki na ja mai ƙara kafin na ce" Ke dai Ma'u wallahi an yi baƙar munafuka kuma makira, ke wai kina kuka saboda ki zama abin yarda ni kuma na zama victim kamar ko yaushe ko? Har kin manta? Har kin manta maganar da kika faɗa mini lokacin  da aka rushe maganar auran ki da Yaya Hamza? Na ce kin manta? To wallahi kamar yadda baki ƙaunata nima abada ba..'   "HALIMA..." Alhajinmu ya katseni tare da kiran sunana a tsawa ce, ban kalle shi ba na cigaba da faɗin"Alhajinmu cewa ta yi fa sai ta rama abin na yi mata sai ta kun samini kwatankwacin baƙin cikin da na kunsa mata kuma.."   "Na ce ya isa ko Halima? Ko so kike yi na saɓa miki?   Alhaji ya faɗa ransa ɓace, sai na yi sansarai rai, ganin ya koma ya ba ma Ma'u haƙuri tana shessheƙan kuka. Baƙin ciki da ya tokare mini zuciya ya ta so mini ba kasafai na ke kuka kan abu ba amman daman Ma'u ta saba cin nasara a kaina akan kowa ko da yaushe ni ce victim ita kuma mai gaskiya.   Ban san nima na fashe da kuka ba, sai kawai na miƙe zan fita daga falon ina faɗin" Shike nan ai daman ita mai gaskiya ce ita ce ba ta laifi ni ce fitananniya. Alhajinmu ni fa ƴar ka ce Ma'u fa? Bai kai kamar ni da ka haifa da gudan jinin ka ba." "Ke ke Sadiya ina za ki je? Alhajinmu ya fada saboda na juya ina kuka zan fita ne.   "Wallahi zan saɓa miki in kika fita Halima."   Shi ya sa na fasa fita amman sai na coge a tsaye ina sharan kwalla. Ran Alhaji ya ɓaci ya ɗaga murya ya na kiran sunan Gwaggo. Sai gata ta shigo da sauri ta na sanye da Hijabi a jikinta. Gani na tsaye ina goge idanuwana sannan ga Ma'u na ta shesshekan kuka Alhajinmu na faman ba ta haƙuri. Cikin mamaki da damuwa a saman fuskarta har kuma ya bayanna a muryanta ta ce"Subhanallah. Alhaji lafiya? Me ya faru ne? Duk da ta san dalilin zaman amman shi dailin koken koken namu ne ba ta sani ba.   Yusuf ne ya tashi daga in da ya ke zai iso in da na ke tsaye amman Alhajinmu sai ya dakatar dashi. "Dawo ka yi zaman ka Yusufa ƙyaleni da ita."   Sai ya koma ya zauna a inda ya tashi amman gabaɗaya hankalinsa na kaina kamar yadda hankalin Alhaji Mustapha ke kan matarsa.   "Taho min da Halima nan gaba na Maimuna."   Umarnin da Alhajinmu ya ba ma Gwaggo kenan sai ta riƙo ni lokaci ɗaya ta na faɗin" Mu je Sadiya. Mu je Alhaji na kiran ki."   Ban isa na yi musu ba sai na bita har gaban Alhaji ta kuma zaunar da ni a gabansa a kuma in da na tashi, jan majina na ke yi ina ƙokarin shanye takaicina. Gwaggo ta kalli Alhajinmu kafin ta ce"Daga sulhun ne suka fara koke koke kuma Alhaji?      Bai amsa mata tambayarta ba, sai ma kallonta da ya yi kafin ya ce" Samu waje ki zama, saboda abin da zan faɗa ina so kema ki zama shaida."   Sai Gwaggo ta koma ta zauna a kujeran mai zaman mutum biyu dai dai lokacin da ta ke kallon Ma'u wacce ke ta faman tsane hawayenta da hanky ɗin da ke hannunta. Sannan lokaci ɗaya ta na cigaba da shessheƙan kukanta. "Ke ma Ma'u ki bar kukan ya isa haka nan." Ta fada cikin wani yanayi, a cikin ranta tana tunanin komai Alhaji zai yi ba za a taɓa samun daidaito ta bangaran Ma'u da Sadiya ba. "Halima.."   Kamar daga sama na ji Alhajinmu ya kira sunana a kausashe kuma da karfi jikina da zuciyata suna rawa na ɗaga kai ina kallonsa cikin ɓacin ran da ya bayyana har a saman  fuskarsa na ga ya nuna ni da yatsar sa manuniya da ya hana ni ma iya amsa masa kiran sunana da ya yi.   "Yau ce rana ta farko kuma ta karshe da zan ji ƙin ƙara kiran Ma'u da bare, yau ce rana ta ƙarshe da za ki ƙara yi mata kallon wata ba ƴar uwanki ba. Na san halin ki saboda ni na haifeki da gaske ki na da fitina da rashin haƙuri sannan ba ki da yafiya da barin abu ya wuce, sannan kina da nacin faɗa, kowa sai ya manta amman ke zuciyarki ba ta iya mantuwa. "   Ya ƙarishe faɗa da karfi, kamar zai kai mini duka daman Alhajinmu akwai faɗa in ran shi ya ɓaci. Kuma ka da ka ba ri faɗan shi ya faɗo ta kanka domin ba za ka taba jin daɗi ba.   Shi ya sa na ji zuciyata ta karye na fara kuka, kenan har a yau ma Ma'u ce za ta sake yin nasara a kaina?   "Kar na kuskura na kara jin kin danganta Ma'u da bare, ita ba bare ba ce. Jinin ki ce domin in aka tsaga jininta za a ga na ki jinin haka itama in aka tsaka na ta jinin za a ga naki, bari na tunasar da ke abin da nasan ba ki manta ba,  ni na saki nono mahaifiyar Asma'u ta kama Asiya ƙanwata ce uwa ɗaya uba ɗaya. Me ya sa kike da tunanin banza ne? Me ta yi miki? Tana bin ki amman kina ƙara nuna mata tsana? Ina ce har hakuri Murja ta ce ta yi ta ba ki kika tafi kina ta cin mutumci? Ke sheɗan ce da ba ki jin bari Halima ko so kike ki zama sheɗaniya a cikin mutane?   Kuka kawai na ke yi, wannan karon kukan da na ke yi ya fi na wanda Ma'u ta yi fidda amon sauti, falon ya yi tsit sai tashin faɗan Alhaji kawai ake ji har Gwaggo tana zaune ne amman ba ta iya dakatar da Alhaji ba.   Ma'u ce ta ɗago kanta tana kallon Alhaji kafin ta ce" Alhajinmu har a waya na kira ta bata ɗauka ba sai na yi mata saƙon murya ta WhatApps bari ma ka ji." Nan da nan ta ɗauko wayarta ta shiga ta duba sai ga shi ta kunna muryanta tarwai ta na fadin"Ki yi hakuri Sadiya da abin da Shema'u ta yi miki. Har ga Allah ban san a ina ji maganar ba. Na nuna mata ban ji daɗi ba na kuma ce sai ta ba ki hakuri saboda haka zan tura mata lambarki sai ta kira ki ta baki hakuri."   Alhajinmu ya girgiza kai kafin ya kalleni ya na faɗin"Ta yi ta ba ki hakuri akan laifin da ba ita ta yi miki ba amman kin kasa hakura. Tabbas na fahimce ke ce sheɗaniya sannan ke ce ke hassada duk abun da ke faruwa."   Ina rawan muryan kuka na kwashi rantsuwa ina faɗin"Wallahi Alhajinmu..." "Rufe min ba ki, ki kuma tsaya dakyau ki saurareni. Ga uwarki nan ta zama shaida ga mijin ki nan ya zama shaida, daga yau ina mai ba ki umarni a matsayina na mahaifinki, ki ijiye duk abin da ke cikin ranki game da Asma'u ki rumgumi ƴar uwarki. Sannan ki yi zumunci da ita ki je gidanta in abin farinciki ya same ta ki taya ta murna. Sannan ki je a lokacin jaje domin ki ta ya ta jimami. Sannan in ku ka  haɗu ke za ki fara yi mata magana, ki bi ta a inda ta ke ku gaisa cikin zumunci da ƙaunar juna. Gargaɗi na ƙarshe a gareki shine ki bi umarnina ya zama wannan shi ne zama na ƙarshe da zan yi a kan wannan mganar, na ƙara faɗa miki ki yarda makaman yaƙin ki ki bi Asma'u sannan ki yi zumunci da ita, in kika saɓa ma ko ɗaya daga cikin umarnina zan yi fushi da ke fushi mai tsananin da ba ki taɓa tsammani ba Halima. Saboda haka in kina so ki rabauta har a ranar gobe ƙiyama ki yi gaggawan bin umarnin da na ba ki."   Alhajinmu na mgana ina jin kamar zuciyata za ta faso ƙirjina ta fito tsabar baƙin ciki tuni kukana ya ɗauke. Saboda ban ga amfanin ina zauna ina kuka saboda Ma'u. Na yarda ta yi nasara a kaina kamar ko yaushe.   Muryanta na rawa na ce"Na ji Alhaji in sha Allahu zan zama mai bin Umarnin ka." Na faɗa ina sauke numfashi saboda na ji kamar numfashina na shirin kwacewa.     Alhajinmu ya gyaɗa kai kafin ya ce" Kin yi kyan kai. Ki sani ko da rana ɗaya na ji labarin kin bambanta Asma'u da Rahila ki sani kin ɓata mini sannan zan daɗe ban iya kallon ki ba, zan daɗe ina miki kallon wacce ta gagare ni."   Da sauri Gwaggo ta ce" Haka ma ba zai faru ba. Sadiya kara ba ma Alhaji haƙuri."   Kaina na ƙasa na ƙara faɗin" Allah ya huci zuciyarka Alhaji. In sha Allahu hakan ba za ta ƙara faruwa ba." Na faɗa ina ƙokarin danne abin da ke taso mini daga ƙasan zuciyata.   Sai ya saussauta fushin sa jin har Yusuf ya rankwafa ya na neman min afuwa har da Ma'un da mijinta sai Alhajinmu ya jinjina kai kafin ya ce" Bakomai. Na tsorata ne sabo da halin rayuwa. Ka da na faɗi na mutu na bar baraka daga zuru'a ta, na ji daɗin da kika hangi kuskuranki kika kuma yi aniyar gyarawa. Ki yi ma Asma'u sallama  ta amsa miki tare da musabaha yanzu a gabana Dubu."   Ban yi musu ba na juya ina miƙa ma Ma'u hannu lokaci ɗaya ina yi mata sallama. Ta miƙo min hannunta ta na yi min wani irin mirmishin da ni kaɗai nasan ma'anarshi lokaci ɗaya tana amsa sallamata tare da sarƙe hannun juna. Ni ma sai na yi mata mirmishi kwatankwancin mirmishin da ta yi mini, ai ba Ma'u kaɗai ita iya bariki ba nima na iya tunda na fahimci ta na cin nasara a kaina ne ta hanyar amfanin da makirci. "Ki yi hakuri Ma'u. Ki yafe mini sharrin sheɗan ne."   Haka na faɗa ina mai gayyato mirmishi da rahama a saman fuskata, ko ta yi mamaki ba ta nuna ba sai ta waske,  kafin ta ce"Bakomai. Na ji daɗin haka Yar'uwata."   Daga zaunen na matsa na rumgumeta, sai da ta yi wani sansarairai kafin ta rumgume bayana ta na ɗan mirmishi nima mirmishin na ke yi sannna muka saki juna bayan mun kalli juna kowaccenmu ta yi mirmishin da bai kai zuuci ba.   Gwaggo ta yi hamdala Alhajinmu ma haka ya ɗora da cewa" Na ji daɗin haka. Allah na gode maka da korar min sheɗanin da ya shigo cikin zuru'ata. Allah ya yi muku albarka gabaɗaya, ku kuma na ƙara ɗora muku nauyi ku yi musu gyara in sun yi ba dai dai ba. Sannan kuma ku gaya musu su sada zumunci a tsakaninsu saboda samun falala wajen ubangiji irin ta masu sada zumunci."   Suka amsa ma Alhaji da In sha Allahu. Ganin har sha ɗaya ta yi na dare sai ya ce mu ta shi mu ta fi gida mun bar yara su kaɗai a gida.   Dukkanmu a tare muka yi ma Alhajinmu da Gwaggo sallama muka fita, muna gaba ni da Ma'u su kuma mazajen namu suna bin bayan mu.   Ni ce na fara kallon Ma'u dai dai mun fito kofar gida, ƙasa ƙass na ce"Kin iya acting kyan shi ki faɗa harkan film za ki ci kuɗi sosai" Dariya ta yi kafin ta ce"Ko Sadiya? Ke ma ashe kin san na iya acting sosai." Sai na gimtse fuska kafin na ce"Kin sha yin nasara a kaina Ma'u kamar baya yau ma kin ci nasara. Amman ina mai ba ki tabbacin daga yau ba za ki ƙara samun nasara a kaina ba har abada."   Cikin reni ta ce"Kai don Allah? Da gaske? Ban tsaya sauraranta ba na ƙarisa jikin motar Yusuf,ganin sun kariso suma ya sa na ɗaga murya ina faɗin" Sai da safe Ma'u. Alhajin Ma'u mu kwana lafiya a gaida yaran."   Shi ya amsa min cikin sakewa, ita kuma Ma'u sai ta bige da mirmishi kafin ta ce" A gaida min da yarana Sadiya." Kai na jinjina mata a saman leɓena na amsa. Mu muka fara yin gaba sannan su, a juctiion muka rabu mu muka ɗau hanyar Lodge road, su kuma suka ɗauki hanyar Rijiyar zaki in da gidan Alhaji mustapha ya ke.   Tun da muka ɗau hanya ban yi magana ba. Hawaye na ke yi a ɓoye ina sharewa da gefen jijabina jikina. Yusuf sau ɗaya ya yi min magana na ce ya rabu da ni, sai ya maida hankalinsa kan tuƙi amman rabi da kwatan hankalinshi na kaina ganin yadda hawaye ke kwaramyamin wani na korar wani, ba wanda zai iya fahimtar yanayin baƙin cikin da na ke ciki, Ma'u ta daɗe ta na gigita duniyata ba tare da an sani ba amman komai ya zo ƙarshe. Na fahimci ni nake ba ma Ma'u daman da ta ke cin galaba a kaina to in haka ne zan dakile wannan damar zan toshe mata duk wata hanyar da za ta ƙara kuntatamin.   Sanda muka isa gida ko jiran Yusuf ban yi ba, na yi shigewata cikin ɗaki na barsa yana leƙa ɗakin yara. Bedroom ɗin mu na shiga na faɗa kan gado na saki kukan da na ke ta riƙewa tun dazu har da fitar da sauti.   Ina ji Yusuf ya shigo ganin ina kuka ya sa ya nufeni da sauri ya na faɗin"Haba Sadiyata, ina raye kike kuka? Ko za ki yi kuka ba za ki yi kuka a saman kafaɗata saboda na ji daɗin lallashin ki ba?   Ya faɗa ya na mai hawa gadon ya tarairayoni jikinsa, sai na faɗa masa muka durkushe saman gadon ina wani irin gunjin kuka shi kuma yana ta ɗan tapping ɗin bayana alamun lallashi bai hana ni kuka ba sai da na yi ya isheni sannan ya ɗago fuskata ya saka hannuwansa ya na share min hawaye lokaci ɗaya yana faɗin.   "Ya isa. Ki daina kuka ka da kanki ya fara ciwo. Shii.. is ok kin ji ko?   Haka ya ke faɗa, cikin sanyin murya, buɗe idanuwana da suke rufe ina kallonsa  da jajayen idanuwana kafin na ce" Ka yarda da cewa Ma'u makira ce? Ka ga fa ta haɗa ni da mahaifina a gabana na kasa wani abu Yusuf, ta haɗa ni da kowa nawa.' Sai na ƙara fashewa da kuka ina faɗin" Na rasa me na yi mata ta ke yi min haka? In saboda fasa auranta da Yaya Hamza ne ban yi nadama ba, saboda in da na bari da tuni ta haɗa mana yaƙi a gidanmu. "   Shi dai yana ta faman ba ni, ba ki ya na cewa na yi hakuri na daina kuka tunda Alhaji ya yi min faɗa na bi umarninsa.   Ƙura masa ido na yi kafin na ce"Haka ne zan bi umarninsa. Bakomai." Daga haka na tashi daga saman jikinsa na sauka daga kan gadon lokaci ɗaya ina cire Hijabin jikina. Fita na yi zuwa toilet ina wani tunani a cikin raina. Ba haka zan zauna Ma'u ta cigaba da cin galaba a kaina ba, tunda har ta riga ta samu magoya baya, ni kuma daman ba ki na yasa ko ina da gaskiya na ke zama mara gaskiya gwara na yi amfani da fatar bakin nawa domin ka da Alhaji ya sake yin fushi da ni gwara na cigaba da tafiyar da Ma'u kamar yadda nima ta ke tafiyar da ni. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY).* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JMpd8nXr7TIDD3ILDXh64z *🅿️4* Sanda su Ma'u suka ɗau hanyar gidansu da ke Rijiyar zaki. Zaune ta ke a bangaren mai zaman banza, kamar ba ita ce ta gama kuka wurjajan ba. Wannan karon mirmishi ne da Annuri ke fitowa daga ƙarƙashin zuciyan Ma'u kuma har ya ke iya bayyana a saman fuskarta. Mijinta Alhaji Mustapha na tuki, sai ya waiwayo da hankalinsa zuwa kanta a tunaninsa har a lokacin ba ta bar kuka ba, amman ga mamakinsa sai ya ganta zaune tana mirmishi. Cikin mamaki ya ce"Har kin huce kenan Hajiyata?   Kallonsa ta yi ta na ɗan mirmishi kafin ta ce"Me ye a ciki? Ba fa komai Alhajina. Farinciki na ke yi yau Sadiya ta kalleni a matsayin ƴar'uwa. Zuciyata na cike da farincikin da ban taɓa tsintar kaina a ciki ba."   Ta ƙarishe faɗa fararan haƙoranta na bayyana a waje. Ma'u Fara ce farinta mai irin ja ja ɗin nan ne, taNa da fadin fuska sannan ba ta da tsawo kuma tana da ɗan jiki, sai kibar ta yi mata kyau sosai. "Ni fa Sadiya ce ke ba ni mamaki har yanzu. Kina ƴar'uwanta haba. Sai ka ce bare ko bare ce ke ai wannan ƙiyayyar ta yi yawa Asma'u. Ni ko da muke haɗuwa ba ta son yi mini magana ban kawo haka ƙiyayyar nata a kan ki ya yi ƙamari ba, na fi danganta haka da halinta ne tunda ko Anty Bahijja za ki ji ta na complain da Matar Tafida ba ta son mutane, ga shi kuma ta auri ɗan dangi."   Maganarsa ya katse mata tunanin da ta ke yi, kallon shi ta yi mirmishin da ya ke so game da ita. Asma'u ba ta fushi ko an ɓata mata rai yanzu yanzu za ta huce ka ga har tana mirmishi. "Bakomai Alhajina ai komai ya wuce yanzu. Kuma da man ko lokacin muna gida ni da Rahila mun fi Sadiya son mutane, ita haka take ba ta cika son mutane ba gaskiya."   "Amman ko halinta ba mai kyau ba ne. Ina mamakin yadda Injiniya ke iya zama da ita da wannan murɗewan na ta."   Mirmishi Ma'u ta yi masa ba tare da ta ƙara magana ba. Ta gaji da bashi amsa tana Allah Allah ya yi shuru ya maida hankalinsa kan tuƙinsa amman sai da ya juyo da niyar ƙara yin wata mgana sai kuma wayarsa da ke gaban Aljihunsa ta fara ɗaukan sauti alamun ana kiran shi, shi ya katse masa mganarsa sai ya maida hankalinsa kan wayarsa. "Alhaji Garzali ne.."   Haka ya faɗa sannan ya ɗaga wayar. Mirmishin gefen kawai ta yi, ya na waya hannunsa ɗaya na saman sitiyari hankalinsa rabi na kan waya rabi na kan tuƙi, shi ya sa ma ya rage gudun motar sai aka ci kuma sa'a dare ya yi sosai ba yalwar giftawan motoci sosai.   Ƙuri Ma'u ta yi masa da ido, tana ƙare masa kallo. Alhaji Mustapha ba zaɓin ta ba ne, ba kuma shi ne muradinta da mafarkinta ba. Ba domin Sadiya ba da ƙila yanzu ita ce a gidan Yaya Hamza kuma ita ce mahaifiyarsu su Afnan ba Khaleesat ba, ba domin Sadiya ta yi mata baƙin ciki ba da yanzu ba ta auri wannan magidajen kanon ba. Shi ya sa har gobe wannan dafin da Sadiya ta bar mata ya kasa ɓacewa daga cikin zuciyarta. So ta ke yi ko da ƙwatanƙwacin irin baƙin cikin da ta ji ne, itama Sadiya ta ɗanɗani irin shi ta ji in da daɗi. "Ma'u..Ma'u.." Muryan Alhajin nata ya katse mata tunani, sai ta dawo da ƙwayan idanuwanta a kansa, daman can sunan ta na kallon shi ne amman tunaninta da hankalinta ba su a kansa kwata kwata. "Tunanin me kike yi haka? Ina ta magana kin yi shuru? Basarwa ta yi kafin ta yi mirmishin da ta san ya na sace zuciyansa.   "Tunaninka na ke yi mana My Alhaji."   Ta faɗa lokaci ɗaya ta na yi masa fari da wani kallo da shi kaɗai ta san yana kunna shi, aiko sai ga shi ya ke ce da wata dariyan nishaɗi kafin ya buga sitiyari lokaci ɗaya yana faɗin" Ma'u. Ma'u na, ba ki da dama."   Mirmishi ta sake yi tana kara narke masa, dariyan ya sake yi kafin ya ce"Alhaji Ghali na gaishe da Amarya Ma'u."   Cikin yar dariya ta ce"Ina amswa. Ya iyalan nasa? Ya amsa mata da suna lafiya kafin ya ɗora da faɗin" Kin san ko har gobe in na je gidan sai Hajiya Fati ta yi mini tsiyan ba ki zo mata Allah ya sanya alheri ba, lokacin bikin ƴa'ƴanta."   Kai tsaye Ma'u ta ce"Ayya. Ba ka gaya mata bana nan ba ne lokacin? Kuma ai Hajiya ta je ta wakilceni"   Ya na dariya ya ce"Nima haka na ce, da Hajiya da Ma'u duk abu ɗaya ne a waje na."   Taɓe baki ta yi, a farko sannan ta ɗan saki fuska kaɗan. Hira ya cigaba da yi mata, sai faman taɓe baki ta ke yi, in zai juyo sai ta sakar masa lallausan mirmishin da ta san ya na kunna sa har cikin zuciyarsa.   Kanta ta maida jikin window din motar tana kallon hanya har ga Allah ba ta son surutu, surutun ma a wajen Namiji, ba haka ta so mijin auranta ya kasance ba, ta na son namiji mai Aji da kamewa amman mai ake yi da gidahumin namiji, waiwayawa ta yi ta na ƙara kallon Mijin nata wani abu da ya daɗe da tokare mata zuciya duk sanda ta kalleshi a matsayin mijinta ya sake ta so mata. To ta san ba ta san shi me ya sa ta aure shi?   Ba saboda kowa ba ne sai Saboda da BAABA. da kuma KUƊI. Ba domin kuɗin Alhaji Mustpha ba, da ko hanya ba za ta iya haɗawa da shi ba, tunda ya yi yamma da irin zaɓin mijin da ta daɗe tana mafarkin samu. Alhaji Mustpaha irin ƙauyawan kanawan nan ne, shi bai yi boko ba sai arabi, amman fa ya san kan kasuwanci yana kasuwancin Fata sannan kuma ɗan chajin ne, yana da kuɗi sosai. Kuma mahaifinsa ma har ya mutu sana'ar fata ya ke yi, shi ya sa zuru'arsu ke da kuɗi, amman bayan nan mugun bagidajen ƙauye ne, mara lissafi. Sannan ita ba ta taɓa hango kanta a matsayin macen da za ta yi aure ta zo a mace ta biyu, ta tsani zama da kishiya a rayuwarta saboda mahaifiyarta tun auranta na fari ba ta ji daɗin kishiya ba, kafin ta zo ta auri mahaifinta mutuwa ta zo ta raba, sannan a auranta na uku ma gidan kishiyiyon ta je, da har gobe ba ta huta ba. Shi ya sa ta yi fatan samun gidanta ita kaɗai ta gina shi duk yadda ta ga dama ba wai ya kasance ita ce zata shiga gidan da wata ta gina ba.   Amman kaddara ta riga fata, ko da ya ke Sadiya ce ta sauya mata kaddaranta. Domin saura ƙiris ta cika mafarkinta ta yi sanadiyar lalata komai, shi ya sa itama ba ta da wani buri sai na ganin ta lalata ma Sadiya jin daɗin duniyarta ta gigita mata rayuwarta yadda ƙwatankwacin yadda ba ta samu abin da ta ke so ba, itama ba ta fatan Sadiya ta cigaba da samun abin da ta ke so, in ma ta samu to za ta yi sanadiyar lalata shi ya zama baƙinciki a gare ta. Tana da burika da dama akan Sadiya waɗanda ko kwatansu ba ta cika ba. Nasara a kan Sadiya yanzu ta fara yi in a baya ita ta ta yi kuskuren barin Sadiya yin nasara a kanta wannan ƙarnin baya ne da ya shuɗe. Wannan ƙarnin na yanzu ita ce za ta cigaba da samun nasara akan Sadiya daga nan har abadan.   Ba ta ma san sun iso gida ba, sai da ta ji yana hon sannan ta farga da har sun iso gida, gidan Asma'u ƙaton gida ne mai kama da Aljannar duniya, amman duk wannan daular ba ya gabanta matukar ba ta ɗanɗana ma Sadiya irin ɗacin da ta ke ji a cikin zuciyarta ba, ba za ta taɓa samun kwanciyar hankali ba.   Ita ta fara yin gaba zuwa cikin gida. Ta bar Alhajinta na magana da megadi, a falon gidan ta ci karo da ƙanwarta Zainab ƴar kimanin shekaru 16 zuwa 17, da ke hannunta tana zaune ta na kallo, abin sai ya ba ta mamaki ta na ganinta ta yi saurin miƙewa tana sosai ido, wani kallo Ma'u ta yi mata kafin ta ce"Uban me kike yi har yanzu ba ki yi barci ba?   Cikin In ina Zainab ta fara faɗin" Ina. Ina. Kallo ne." Kafin Ma'u ta samu zarafin magana Alhaji Mustapha ya shigo falon kawai sai ta fasa maganar da za ta yi sai ma ta kalleta tana faɗin" Kin tabbatar da kin saka su Baba ƙarami sun yi fitsari kafin su kwanta ko?   Da sauri ta ɗaga kanta, Alhaji Mustapha na tambayan me ya faru? Ba ta tsaya bashi amsa ba ta kama hanyar ɗakinta lokaci ɗaya ta na faɗin" Ki kashe kallon nan ki je ki kwanta." Daga haka ta shihe koridon da zai sada ta da ɗakin barcinta a ƙasan ranta ta na ji kamar ta ce Alhaji ya je gidan Hajiya yau ba ta cikin Mood ɗin da za ta iya dauriyan kwana dashi.   Shi ya sa ta na shiga ɗakin barcin na ta ta maida ƙofa ta rufe. Wayarta ta sauke nan saman gadon da mayafinta sannan ta buɗe kofar tiolet ta shiga wanka za ta yi, ta na cikin wankan ta ji Alhajin nata na ƙwanƙwasa mata kofar, tsaki ta ja a fili da ɓoye wani abu na suƙan zuciyarta dagacan ƙasa.   Ta na fitowa ɗaure da Towel, har lokacin bai tafi ba ko ya tafin ma ya sake dawowa.   "Ma'u. Ma'u ta,..'   Tsaki kawai ta ƙara ja a fili sannan ta isa ga kofar ta murza key, ta na buɗewa kawai ta juya ta dawo cikin ɗakin gaban madubin da ke shake da kayan kwalliya ta tsaya shi kuma cikin jallabiya ya shigo yana mai washe baki. "Au wanka kike yi ne?   Juyowa ta yi sannan ta gyaɗa masa kai tana mirmishi, shi kuma sai ya rumgumota ta baya fuskarsa da nata na bayyana ta cikin madubin, Asma'u ta yi mirmishi, mirmishin da a saman leɓenta kawai ya tsaya, tana kallon Alhaji Mustapha kansa har ya fara furfusa ga uban sauƙo, a fuskarta mirmishi ne, amman a ƙasan zuciyarta ƙuna ne da wani irin turiri da ya ke ta so mata.   Ita ko za ta iya yafe ma Sadiya? Kai ina sai ta gigita rayuwar Sadiya. Sai ta yi sadiyar zama sanadin da farincikin Sadiya zai yanke na har abada. Yadda ita ba ta zauna ita kaɗai ba, itama Sadiya burinta ba zai cika ba, sai ta gayyato mata damuwowi masu tarin yawa a rayuwarta wannan alƙwarin ASMA'U SULAIMAN YASHE ce. ****** *BAYAN KWANA HUƊU* LODGE ROAD. JUMMA'A. Karfe 7:40am na safe Salisu ya zo ya ɗauki su Jidda zuwa makaranta. Suna tafiya ban huta ba na shiga ɗakinsu ina haɗa musu kayansu, na zuwa gidan Anty Maimuna ko jiya sai da ta kirani a waya tana gwaɓa mini magana wai wannan satin ma hala gidanmu za su je? Ban biye mata ba na ce yau in sha Allahu za su zo. A ƙaramar jakar baya na Jidda na haɗa musu kayansu da duk abin da za su buƙata, tiolet na shiga na ɗauko musu brush na fito kenan sai na ga Yusuf zaune a gefen gadon su Jidda.   Sanye yake da jallabiya. Tun bayan dawowarsa sallar asuba ya kwanta ban ma san ya tashi ba. Tsayawa na yi sororo ina kallon shi kafin na yi mirmishi na ƙariso ina faɗin"Har ka tashi? Miƙewa ya yi ya zo gabana ya buɗe min hannuwansa na faɗa ya rumgumeni yana faɗin" Ina kwana Sadiya ta."   Na amsa ina sakin sa kafin na ce"Na ga barcin ka ya yi nisa shi ya sa na ce su Jidda kar su tashe ka, su tafi kawai."   Ya na tsaye ya harɗe hannuwansa a saman kirjinsa ni kuma sai na duka ina saka musu brush ɗin su a cikin jakan da na haɗa musu kaya. "Kayan me ye wannan? Ina duƙe na ce" Kayan su Jidda ne. "Na zuwa ina kuma? Sai da na ɗago sannan na kallesa kafin na ce"Gidan Anty Maimuna. Wancan satin kasan ba su samu zuwa ba."   Sai a lokacin ya ce"Oh. Na tuna ko jiya da na je gida Nene sai da ta yi min magana. Wai Anty Maimuna na ta faɗa." Ina kallon idanuwansa na ce"Wai faɗan me? Taɓe baki ya yi kafin ya ce"Ban sani ba, amman ta tambayeni me ya hanasu zuwa wancan satin na ce ma Nene ban sani ba."   Baki kawai na saki ina kallon shi, wai bai sani ba, Me ya sa Yusuf ya ke yi mini haka ne? Yadda ya ga ina kallonsa ne ya sa ya fara dariya, ya matso ya riƙeni na matsa baya ina haɗe rai kafin na ce"Ba ka sani ba ko? To ai ya yi kyau."   Ina gama faɗin haka na juya na bar masa ɗakin. Wai ni haka maza suke ko nawa mijin ne haka? Sau tari wasu laifuffukan da danginshi ke kallona da shi har da laifin shi, sai a yi abu kuma ya san dalilin faruwan shi amman in suka tare shi da maganar sai ya ce bai sani ba, kuma na yi masa ƙorafi har na gaji ya kasa dainawa, in na yi magana sai ya ce ai bai sani ba ne, ko game da zuwa sha'anin dangin shi, gajiya suka yi suka ƙyaleni, da suka fahimci ba ma su kaɗai ba hatta nawa dangin ba kasafai na ke shiga ba, ganewan suka yi ko gajiya suka yi da abu ɗaya suka kyaleni ban sanin musu ba.   Kitchen na koma, daman yara saboda yau jumma'a ne drink suka tafi da shi da Bicuit, sai tea da suka sha da biredi kafin su tafi, doya na fara ferewa zan soya mu sha tea da shi, ina feran doyan ya shigo kitchen ɗin yana faɗin"Fushi kika yi? Banza dashi na yi, saboda ya ba ni haushi, burin sa na yi ta laifi a idon danginsa shi kuma ya na jin daɗi.   Zuwa ya yi ya rumgumeni ta baya. Lokaci ɗaya yana ɗora kansa saman kafaɗana bayan ya rankwafa. "Sorry, kin ji ko?   Taɓe baki na yi kafin na ce"Ba dai da man so kake yi ko da yaushe na zama mai laifi a wajen ƴan'uwanka ba? To ai shikenan."   Matse cikina ya yi da hannayensa da ya saƙalo ta cikina. Sannan da ƴar murya ya ce" To ai na ce ne ban sani ba, kin sani da yawan mantuwa."   Mirmishin gefen baki kawai na yi, ba tare da na yi magana ba ya yi ta taƙalan mgana da ni na yi masa gim daga e, sai a'a kawai na ke amsa masa, sanin halina ya san in raina ya baci haka na ke yi sai ya sake ni yana faɗin" Bari na je na yi wanka. Zan je Rano." Sai da na ji ya ambaci Rano sannan na ɗago ina kallonsa kafin na ce"Uncle Abba bai kira ka ba? Kai ya girgiza kafin ya ce" Ya kirani amman bai yi mini maganar ba, amman in mun haɗu zan tuna masa."   Kai na jinjina, ba tare da na yi magana ba shi kuma ya fice daga kitchen ɗin, bayan ya rufo mini ƙofar. Na bi shi da kallo kawai, a baya ne ba na ƙaunar na ji ya ce zai je Rano duk da tushen shi ne, saboda GIMBIYA, amman tunda yanzu ta yi aure ban damu da yawan zuwan shi ba, in na yi duba da irin ayyukansa na kwangilan gine gine in an samu yana zuwa ko Uncle Abba ya yi masa hanya, tun da shi har gobe ya na garin Rano kuma a nan ya gina ƙaton gida duk da bai yi aure ba.   Gun bayan lamarin da ya faru tsakani na da Ma'u da yadda Alhajinmu ya goya mata baya. Tun da na dawo gida ban wani saki ba, ko Jidda sai da ta ce Umma ko ba ki da lafiya ne? Gabaɗaya zuciyata ba ta mini daɗi, ballatana da gabaɗaya ƴan gidanmu suka goya ma Ma'u baya, Yaya Hamza ne kaɗai bai shiga maganar ba shi daman sai a yi abu goma bai saka baki ba, mutum ne mai fahimta shi ya sa ko a baya nake ƙaunar Yaya Hamza saboda hallayarsa ɗaya ne a cikin dubu. Shi da Yaya Auwalu za a daɗe ana abu ba su maida kai ba.   Yaya Abubakar har sake kirana ya yi, bayan na ɗauka zagina ne kawai bai yi ba akan Ma'u. Su Yaya Murja kar a ji labari. Yaya Aina har cewa ta yi za ta iya yanke ni akan Ma'u. A group ɗin Gidanmu an fi kwana uku maganar kawai ake tattaunawa. Ban san ina suka samu cikakken bayanin abin da ya wakana tsakaninmu da Alhajimu ba, sai ga shi Yaya Murja na maida yarda aka yi, to har na yi mamaki Ma'u ce ta faɗa mata ta na jin daɗi haka. Yaya Aina har ta na cewa gwara da Alhajinmu ya yi min haka ƙila zan shiga tairayina.   A mganar nan mutane biyu ne suka ce nima ya kamata a duba maganata ƙawar Ma'u ta yi magana domin tozarci. Yaya Balki da Amina. Sauran kuma duk iyalan Ma'u ne, shi ya sa nima na sauya musu matsayi. Rahila dai ba ta saka baki ba wannan karon, domin ta san halina wallahi sai na yanketa. Sai na yi amfani da shawaran da na yanke a cikin zuciyata akan na shiga na yi magana na ƙara ba ma Ma'u hakuri a gaban kowa kamar yadda take yi min amman munafuki shi daman a koda yaushe yana shirye ne.   Sai kawai ta rigani shiga ta yi magana, hakuri ta ba ma kowa sannan ta ce a bar maganar daga karshe ta yi tagging ɗina kafin ta ce"Komai ya wuce, zumunci da ni da Sadiya har aljannah ko ƴar'uwata? Ban yi wani mamaki ba, sanin ba tun yau ba Ma'u ta kware a iya acting ba sai nima na fito muka yi acting ɗin a tare, kai tsaye na ce"Kowa ya yi hakuri mun daidaita barakan dake tsakaninmu da ƴar'uwata Asma'u."   Sai gashi sun fito suna murna, Yaya Murja ni kaɗai nasan haushinta da nake ji, har da cewa Allah Sarki Ma'u mai hakuri ce daman, ke kuma Sadiya a rage zafin zuciya. Ita da Yaya Abubakar Ma'u kamar ƙanwar uwarsu, ko da ya ke shi Yaya Abubakar akwai tsohuwar soyayya, ita kuma Yaya Murja har da son abin duniya, tunda Mijin Ma'u na da kuɗi ana zuwa ana maula dole ta riƙa zama mai goyon bayanta, ni fa a gidanmu na riga na san halin kowa sannan na yi ma kowa wajen zamansa wallahi.   Har na gama soya doya raina a ɓace ya ke, na kwashi komai zuwa Dinning, sannan na koma Bedroom sai na iske Yusuf suna waya da Uncle Abba sai na ce ya ba ni mu yi magana kan dai maganar fara zuwa na ganin likita asibitin Shika dake Zaria ne. Sai ya ce sun sake magana da Dr. Fadel ya ce in ta bashi lokaci zai kira mu ya sanar da mu. "Ki kwantar da hankalinki Sadiyan Yallaɓai. Da zaran ta saka lokacin ganin ki zan sanar ma Tafida kin ji ko?   Sai na gyaɗa masa kai kamar ya na ganina sannan muka yi sallama na miƙa ma Yusuf wayarsa. Tiolet na shiga nima na fara wanka ko da na fito baya falon. Sai na samu daman shiryawa a tsanake. Riga da wando na saka na material Daman ni in dai ba fita zan yi ba, ba na saka kaya masu nauyi.   Kalan kayan maroon ne, sai na yi amfani da bakar hula mai raga raga, kaina har lokacin ban yi kitso ba mai zuwa har gida ta yi mini kitso ta yi tafiya ne, ni kuma ko sake wanke shi a gida ban yi ba, tunda na iya ina da kayan wanke kan, har su Jidda ni nakan wanke musu kai na gyara musu.   Takalmin gidana mai taushi na saka bayan na fesa turare mai ƙamshi na fita zuwa falo Yusuf na jira na mu karya sannan ya fita. Ni na zuba masa doyan sannan na haɗa masa tea ɗin, sannan na haɗa ma kaina na zauna kujeran gefensa.   Ban ɗaure fuska ba amman ban kuma saki fuskar ba, ganin yanayina yasa sai ya rika takala na da magana sai dai in bishi da ido kawai.   "Ko za ki shirya yau ki je ki gaida Nene, in na dawo daga Rano sai na biya ta gida mu dawo tare."   Kai na gyaɗa kafin na ce"To shikenan sai na shirya na je ɗin."   Yana mirmishi ya shafa kumatuna kafin ya ce"To a saki fuskar, shan kunin ya isa haka." Kalamansa suka ba ni dariya, sai na murmusa, mun cigaba da karyawa mun gama kenan na kallesa ina faɗin"Wata kwangilar a ka samu a Rano kuma? Ya na miƙewa ya ce"Ban sani ba. Abba ya ce na shigo mu je mu gani."   Sai na gyaɗa kaina kafin na ce" Allah ya sa a dace? To su dai waɗancan masu payment ɗin shuru ko?   Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce"Wallahi shuru. Amman ban cire rai ba tun da sun ce ko da yaushe zan iya jin su." Fatan alheri na yi masa amman ban yi ɗoki ba domin ni nasan yanayin aikin shi, sai a yi shekara ana cewa za a biya shuru amman fa aka biya muna warkewa masha Allah tunda kuɗi ne ba kaɗan ba, kuma in aka samu aikin ana yin shi muna shiga hali tunda kuɗin shi zai ɗauka ya yi amfani dashi a karkashin kamfaninsa na HM. TAFIDA AND SON'S LIMITED. office ɗinsa na can hanyar zoo road kan titin Zaria Road.   Ni na raka shi har bakin mota kamar yadda muka saba, ya ba ni 2k ya ce na hau adaidaita zuwa gidansu da ke Gwammaja, muka rabu bayan ya rumgumeni ya sumbaceni, nima na maida masa martani, yana ɗaga min hannu nima ina ɗaga masa da fatan Allah ya kai shi lafiya ya dawo mini dashi lafiya.   Bayan tafiyarsa na koma cikin gida, falon farko na zauna saboda ka da Saude ta zo ta yi ta buga gida ina ciki ban sani ba, sai na kunna kallo tunda akwai wuta a tashar arewa 24 suna haskawa wani film hausa mai suna Ahalil kitab duk da na kalli Film din amman ina son waƙoƙin ciki sai na zauna ina kallo har na ji buga gida na je na buɗe ma Saude muka shigo tare, na zauna na cigaba da kallona ita kuma ta fara aikinta.   Kafin azahar ta gama min komai, ni har barci ma na yi a saman kujera anan falo da za ta tafi na ba ta 500 na ce ta hau abin hawa, tafiyarta ba dadewa su Jidda suka dawo daman na yi ma Salisu maganan zai kai su Alu Venue anguwan su Anty Maimuna sai ya ce mini bari ya je ya yi sallar jumma'a ya dawo kan nan sun shirya.   Sai murna suke yi tunda na ce can za su yi Weekend,tunda akwai jikokin yarta na fari Mardiya suna wajen Anty Maimunan ne sa'anin Baby ne, sannan autan ta ma sa'ar Jidda ne Afiyatu.   Ban yi musu girki ba, Coorfleck na ce su sha bayan sun sauya kaya sun yi sallah. Kayan su suka saka iri ɗaya shadda mai ruwan ƙasa da na ɗinka musu da sallah da ta wuce da mayafansu, iri ɗaya har takalminsu iri ɗaya ne, na faɗa ma Jidda su yi kitso a can saboda na san ba da wuri za su dawo ba. Ban san me ya sa Anty Maimuna ta ke kulafacin su Jidda ba, ko don Baby ita aka yi ma takwara? Ko kuma daman can ita mai son yara ce gaskiya. Ɗaya da rabi na rana Salisu ya dawo ya ɗauke su suka tafi. Suna tafiya nima na shirya na saka wata atamfata hollad mai ruwan ganye, sai na yi amfani da green ɗin mayafi jaka da takalmina kuma na saka baƙi, key ɗin gidan da na ɗauka sai da na tabbatar da na kashe komai na wuta sannan na fita na rufe get ɗin da makulli, ban samu adai daita ba sai da na taka zuwa babban titi, anguwan shuru daman haka take to ta masu kuɗi ce, kowa na gidajenshi shi ya sa ƙawa ko ɗaya ban da shi a rukunin nan sun shigomin lokacin da muka tare amman ni da ya ke halina sai ni sau ɗaya na taba shiga gidan gefen mu gidan maman muhsana, da ta haihu na yi barka. Allah ya halliceni mace mara sson shige ma mutane, ko yan gidanmu in ba wani abu ya faru ba, ba kasafai nake zuwa ba, gwara na yi zama na a gida in yi barci ya fiye minim   Drop na ɗauka zuwa Gwammaja. Muna tafe na ji wayata na ringing a jaka na ɗaukota na duba sai na ga Zaituna ce Matar Yaya Abubakar. Na yi mamakin ganin kiranta domin ni dai ban wani yi da ita na fi yi da Anty Khaleesat ɗin Yaya Hamza. Ita Zaituna akwai kwaɗayi da surutu da an ce kace kace shi ya sa ban cika sakin mata ba, sannan daman ina jin haushin mijinta shi ya sa na ɗauka a dakune ban sakar mata fuska ba. Bayan mun gaisa, sai na yi shuru ina jiran abin da za ta ce. "Kina gida ne Sadiya?   Yamutsa na yi kafin na ce"A'ah me ya faru? Kai tsaye ta ce"Ayya daman ina kusa da anguwarku ne, mun zo suna gidan wata ƴar'uwarmu ne, na ce bari in kira ki in kina gida, sai na biyo."   Daga yanayin yadda take magana kamar a wahale, na fi tunanin ƙila sun je ne ma ba abinci za ta ce ina kusa bari ta kirani ta daɓo gayyar danginta su zo min gida, na ji daɗi da ba na gida saboda ita ma Zaituna ƴar ƙashin bayan Ma'u ce. "Ai ko ba na gida, ina hanya za ni Gwammaja gidan su Yallaɓai."   Sai ta ce to shike nan, daman ta ɗauka ina gida ne, daga nan muka yi sallama. Na kashe wayata ina hararan wayar kamar ita ce a ciki, na tuna ko faɗan da muka yi da Ma'u a gidan Rahila, suna yan gaba gaban saka bakin cewa ni ce ba ni da gaskiya.   Wayata na mayar jaka, ni kaɗai ina ƙunƙuni ni fa su san halina duk wanda ya ci tuwo da ni wallahi miya ya sha, ga su ga Ma'un duk za su ci ubansu.   Mai adaidaita bai direni ko'ina ba sai ƙofar gidan Iyayen Mijina da ke Anguwan Gwamnaja. Na sauko daga adaidaitan ina miƙa mi shi kuɗin shi na ji an kira sunana. "Anty Sadiya.."   Ina juyawa sai na ga Adnan ne, sai da na sallami mai adaidaitan ya tafi sannan na nufe shi, ya na tsaye a ƙofar gidan shi da abokonsa guda biyu sun sha manya kaya ƙila daga masallacin jumma'a suke. "Adnan manyan kasa, yaushe a gari? Na faɗa ina kallonsa yana dariya ya ce"Jiya na shigo garin. Ina su Jidda?   Ina amsa masa da cewa sun tafi gidan Anty Maimuna, abokansa suka gaisheni na amsa, jakar hannuna ya karɓa muka jera zuwa get ɗin gidan.   Gidan Marigayi Alhaji Muhammad Inuwa babban gida ne, mai bene sama da ƙasa. Ko haraban gidan wargajeje ne, duk da mai gidan ya fi shekara ashirin da rasuwa, gidan bai rankwafa ba, saboda ya hayyafa, kuma ƴa'ƴa sun tasa, in wannan bai kawo ba wannan zai kawo, shi ya sa ƙyallin gidan har gobe bai daina haskawa ba.   Muna tafe ne zuwa cikin gida Adnan na yi min hira makaranta. A ABU ZARIA ya ke karatunsa na Engniaring, a tsakar gidan muka ga Jawahir na shanyan ƙananun kayanta da ta wanke.   Tana ganina ta washe baki ta na faɗin" Anty Sadiya." Na amsa ina faɗin"Au kema kin zo hutun ne? Ko guduwa kika yi? Dariya ta saka tana faɗin" Kai Anty Sadiya, da ne fa yanzu ai mun zama ƴan makaranta."   Adnan ya ce"Tunda ba ki son bokon ki yi aure mana ko Anty Sadiya? Kai na gyaɗa ban yi magana ba Jawahir ta balla ma Adnan harara lokaci ɗaya ta na faɗin" To ai sai ka zo ka yi min auran ubana." Yana ƴar dariya kafin ya ce"Ko ba ki faɗa ni ubanki ne, domin zan iya ɗaura miki aure."   Suka kacame da gaddamansu na saƙo da saƙo ni kuma ina ta dariya. Jakata na karɓa hannun Adnan ina faɗin"Bari na karisa, su Hajiya Iya ba sa nan ne na ji gidan shuru?   Jawahir ta ce" Maman Farko ba ta nan an yi musu rasuwa, Iya kuma ta kwanta ne Nene kuma ki haura sama ta na ciki."   Wuce su na yi, na bar su suna musu, ya na cewa shi ubanta ne, ita kuma ta na cewa Allah ya kyauta ya zama babanta.   Shashen ƙasa Hajiya Iya ne da Mahaifiyar su Jawahir marigiyayiya Hajiya karima Allah ya jiƙanta, sama kuma Hajiya Nene da Maman Farko suke bangaren sama, amman a ƙasa akwai ɗakunan baki daga can haraba kuma akwai ɗakunan mazan gidan.   Sama na haura, ƙofar shashen Nene ne a farko tun kafin na shiga na jiyo hayaniya, ina sallama bayan na cire takalmi na sannan na shiga babban falon na Nene. Hauwa na gani zaune a falon sai fama take yi da yara, Hauwa matar ƙanin Yusuf ne mai bi masa, Muttaƙa. Sai ƴaƴan Halima da su ban ga uwarsu ba, ina ga su kaɗai aka kawo Nene ba ta falon ma gabaɗaya.   Hauwa na ganina ta tare ni da mirmishi, karamar ƴarta, Sahla ta nufoni ta na min oyoyo na taro ta ina ƴar dariya saboda yarinyar ta gane ni, duk in da ta gani ta riƙa gwarancin mgana kenan, suna zuwa gidana sosai nima ina zuwa saboda Hauwa tawa ce, duk cikin Facalolin gidan ba ni da kamar Hauwa.   A bangaren Matan gidan ba ni ba ce Babba ba, akwai Matar Yaya Usman Zabba'u, sai ni sannan Muniran Yaya Nasir sai Hauwa da tsakanin auren mu da na su shekara shidda ne. Amman ina son Hauwa saboda muna da kamaceceniyar hallaya, ba ruwanta tana da sanyin hali duk da yar uwa ce tun da ƴar rano ce a can Mutaƙƙa ya auro ta. Gaisawa muka yi faram faram kamar yadda muka saba in mun haɗu. "Ina Nene? Sai ta ce mini ta shiga ciki ta kwanta. Yaran Halima na kallah kafin na ce"Tare da Haliman suke? Na ga ban ganta ba? Sai ta ce mini "A'a su kaɗai baban ya kawo ya ce Haliman ba ta jin daɗi" Sai na ce Allah ya sauwake, sai da na ji Hauwa na faɗin ƙila ma Haihuwa ce. Baki na saki domin ni har ga Allah ban san tana da ciki ba, har sai da na furta ma Hauwa. Ta na dariya ta ce" Kin daɗe baki ganta ba ne? Ni mun haɗu a walimar sabon gidan Anty Suwaiba, a can ne na ganta da cikin". Kai na jinjina kafin na ce" Ni kin san ban samu zuwa ba." Sai ta gyaɗa min kai, hira muka cigaba yi, amman hankalin Hauwa na ga yara, ita yayanta huɗu, sauran ta ce suna gida tare da babansu da Sahla kawai ta zo amman sai wahala take yi da yayan Halima da ba sa jin mgana. Muna zaune muna hira Walid da wayonsa ya fi shekara biyar ya yi fitsari a cafet, mamaki ya isheni ganin Hauwa ta miƙe jikinta na rawa ta na masa faɗan me ya sa ya yi fitsari a zaune bai zai yi magana ba?   Sai kawai yaron nan ya fasa kuka ya nufi bedroom ɗin Nene, na saki baki galala ina kallon abin mamaki. Ina kallo Hauwa ta je ta diɓo ruwa ta zo da towel tana tsane fitsarin ina zaune ko motsi ban yi ba, na yi wannan wahalar a baya amman ban yi wahalan ƴaƴan ƙannen miji da yayyensa ba, na yi dai na uwar mijina a baya amman a yanzu wallahi na daina, in ba a gode na baya ba a barshi.   Falon duk sun yi kaca kaca dashi sai da ta share, sannan ta dawo ta zauna Walid dai tun da ya shiga bai fito ba, Salha da Afra kuma Hauwa ta ce su sauka kasa su je wajen Anty Jawahir.   Sai da suka bar falon sannan na kalleta kafin na ce"Wai sannu da aiki." Mirmishi ta yi mini ba ta yi magana ba..ni kuma da ban iya shuru na ce"Ke wai har yanzu ba ki daina wannan wahalan ba? Uwarsu na can gida tana hutawa, ke kin baro na ki yayan wajen ubansu, kuma kin zo nan kina hidiman na wasu."   Dariya ta yi kafin ta ce"Kai Anty Sadiya ba ki da dama." Daman haka ta kan kirani, kai na girgiza kafin na ce"Tab. Wallahi Hauwa ba ƙanwar miji ko y'ar mijin da zan yi ma bauta, na yi ma mahaifiyarsa ita ce dole na, ko ita na yi a baya yanzun ma sai abin da ba a rasa ba."   Cewa ta yi" Allah ko? Na ɗaga mata gira sai muka yi dariya har da tafawa ƙasa ƙasa ta ce"Nene ce kafin ta shiga ta kwanta tace mini na kula da su, gwara ke Sadiya haɗuwan juction kuka yi da Yaya Tafida, ni fa yar uwa ce abu kaɗan zan yi a taso min shi ya sa."   Taɓe baki na yi kafin na ce"Kina da aiki. Ni fa sanin da na yi ko na yi ko ban yi ba sai an yi sururtu shi ya sa da gangan na ke ƙin yin abin,tun da ko ka yi ba godewa suke yi ba su yi ta bin ka da ƙananun maganganu. Ballatana ni da na yi ƙaurin suna."   Dariya muka saka har muna ƙara tafawa, bajewa muka yi a falon Nene muna ta hira kiran sallar la'asar ne ya tashe mu, ni ce na leka ɗakin Nene ta na barci ga Walid a gefenta sai na bubbuga gefen gado ba ta da nauyin barci ta buɗe ido, sai ta ganni. "Lokacin sallah ya yi Nene." Kafafunta ta sauko ƙasa ta na faɗin"Sadiya? Yaushe kika zo? Rankwafa na yi cikin ladabi kafin na ce"Tun dazu, Hauwa ta ce kin kwanta." Sai ta mike, ɗankwalinta ya zame kanta cike da furfura, ni na ɗauko mata ɗankwalin na bata ta ɗaura lokaci daya tana fadin"Ina su Hauwa'un na ki? Ko sun je gidan Maimunan ne yau? Da e, na amsa mata sai ta jinjina kai kafin ta ce"Tafida ya je Rano ko? Ko ya dawo ne?   "A'a Nene, sai ya dawo zai biyo ta nan mu koma gida." A sanyaye ta ce Allah ya maido su lafiya. Nene dattijuwa ce ce za ta haura 60 da huɗu haka, jikinta ya yi tubus saboda hutu da jin daɗi amman tana da hawan jini ga sugar, amman da ka ganta ka ga ƴa'ƴanta saboda da ita suke kama barin ma Mazan, matan ne su ka ɗan ɗauko kamanin mutanen Rano.   Ni na riƙeta har Tiolet sai da ta shiga sannan na fito, a ɗakin da muke sauka na falon Nene muka shiga muka yi alwala ni da Hauwa, muka yi salla, muna zaune muna ɗan taba hira haka sama sama ni da Hauwa. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. *🅿️05* Ni da Hauwa muna Gwammaja gidansu Nene har bayan sallar isha'i. Maman Farko ba ta dawo ba, Nene ta ce daman ta ce sai an yi uku za ta dawo wani kawunta ne ya rasu, sauran ƴa'ƴan nata ma da surukanta suna can gidan gaisuwan tare da ita. Hajiya Iya kuma na shiga mun gaisa bayan ta tashi. Akwai wata ƴar dattijuwa Dije mai yi musu aikace aikace da girki amman ba kwana take yi ba zuwa take yi ta tafi, ranar ma ko da na zo ba ta nan an kira ta a waya jikanta ba lafiya.   Ni da Hauwa muka gyara shashen Nene muka yi girki, saboda yara ne sannan ga Nene ga su Jawahir da daman kamar a ɗakin Nenen suke duk da ita Jawahir a bangarensu ta ke kwana in ta zo gida hutu a School of Nursing na ABU kongo take karatunta tana Aji biyu.   Sai wajen tara na dare Yusuf suka shigo gidan tare da Muttaƙa, da Musabahu, ko kafin su shigo ina ta kiran Yusuf ban samu ba, dare ya yi sannan ni na gaji da zaman hankalina ya koma gida ga yaran Halima ba sa jin mgana Hauwa ce ke ta fama da su, ni dai ina zaune nima fama na ke da kaina, girki dai na ta ya Hauwa muka yi saboda Nene.    Gaisawa kawai muka yi da su Muttaƙa, na ce ma Yallaɓai ya zo mu wuce gida sai ya ce bari ya shiga ciki su gaisa da Nene, saboda ita ta na ciki mu kaɗai ne a falon muna bidiri, sai da mangariba ne ma Jawahir ta shigo nan muna tare da ita.   Sai da muka ƙara ɓata lokaci sannan mu ka yi shirin tafiya, Hauwa Mijinta mashin gare shi, su suka fara ma tafiya mun rabu akan cewa zata shigo gidana sati na sama, bayan sun miƙa ma nima na shiga na yi ma Nene sallama sannan muka tafi. Yaran Halima aka bar Jawahir da jage jagen su tunda uwar ta su ba lafiya.   Musbahu ne ya rakomu har wajen mota ina yi masa tsiyan yaushe  rabon da ya zo gidana? Ya na dariya ya ce ayyuka ne suka yi yawa shi ya sa ba ya samun zama. Da ya ke shi ya ke zama a gidan bulo ɗin Yusuf, shima gidan bulo ɗin  duk ya yi ƙasa ya fi aiki in har an samu babban kwangila na ginin makaranta haka ko kamfani. Kuma sannan yana zama a can ma office ɗin Yallaɓai in baya nan.   Muna hanya na kalli Yallaɓai ina faɗin" Ya Ranon? An dace? Hankalinsa na kan tuƙi kafin ya ce" Alhamdulillah." Ganin ya yi shuru bai yi magana ba ya sa na gyara zama ina faɗin" Ka samu kwangilan ne? Sai ya gyaɗa kai kafin ya ce"Muna saka ran haka, wani gidan buredi za a gina shi ne ana neman enginear sai Abba ya yi musu magana. Na je na ga wajen yanzu dai har zanen ni zan yi sai in har an gama zanen sai mu ga in har kwangilan za ta faɗa." Kai na girgiza kafin na ce"To Allah ya tabbatar. Ya kuma ba da sa'a." Ya amsa da Amin. Kafin ya ce" Su Jidda na gidan Anty Maimuna ko? Kin kira su? Sai na girgiza kai kafin na ce" Ban kira ba."   Da sauri ya juyo ya na kallona cikin mamaki kafin ya ce" Me ya sa? Ba za ki kira ki ji ko sun isa lafiya ba? Ido na sakar masa ban yi magana ba. Yallaɓai na  da mantuwa ne, ya manta abin da ya taɓa faruwa a can baya? Su Jidda sun taɓa zuwa gidanta na kira na ji sun isa lafiya Anty Maimuna ta yi min kaca kaca wai saboda sun zo gidanta shi ne na kasa sukuni to kar na manta ƴaƴa ba nawa ba ne ni kaɗai balle na ƙwallafa rai da su, in ina son zama da yara na saki jiki na yi ta haihuwa ko wasu sun tafi, ba zan damu ba tunda wasu na nan. Tun daga lokacin ko sun tafi wallahi ba na kira na kama mutumcin kaina ba zan kai kaina in da za a gaya min ba daɗi ba  sannan na zo na yi ta faman da ɓacin rai ba.   Ganin yadda na yi shuru ya sa ya ƙyaleni bai ƙara mini mgana ba, har muka isa gida shi ya tsaya rufe get ni kuma shiga ciki ina buɗe ƙofar falo.   Bai ƙara tada maganar ba har sai da muka yi wanka muka yi shirin barci, har na kwanta kawai na ji sa yana faɗin"Ba ki kyauta ba, ko ma me ya faru ya kamata ki kira ki ji in sun isa lafiya, karki sake irin haka Sadiya."   Ɗagowa na yi ina kallonsa, in na ce zan yi magana ma ba zai fahimta ba sai na gyaɗa masa kai, yana zaune a gefen gado ya miƙaar da kafarsa ga laptop samansa.   "Ki yi barcin ki. Zan yi aiki ne."   Sai na ƙara jinjina masa kai. Zane zai yi, tunda Mijina Yusuf ya karanta fannin zane zane ne Archicture, sai kuma fannin da ya yi ma haye shi ne kwangilan gine gine, shi ya sa ya samu sunan injiniya, tun a sanina da Yusuf mutun ne mai neman na kansa mai fafutuka, ina ta kallonsa yana aikin sa, in muka haɗa ido,  sai ya yi min mirmishi nima na maida masa martani har barci ya sace ni ban sani ba.   Tun asuba wayar Anty Bahijja ta tashe mu, wai Halima a asibiti ta kwana naguda. C.S ma za a yi mata. Wayar ɗan'uwanta ta kira nima shi ya ke faɗa mini. Na so na huta a gida ranar amman ya na iya cewa ya yi na shirya nu fita tare ya kaini asibitin sai ya wuce Office. Ba ni da mafita haka na sake shiryawa bayan mun karya, ko da sha ɗaya ta yi muna asibiti, wani asibitin kuɗi ne sanda muka isa an shiga da ita tiyatar ma. Mun iske su Anty Maimuna da Anty Bahijja, Anty Zuwaira ta zo amman ta wuce makaranta suna da taro.   Muna nan Mutaƙƙa ya zo, bayan mu ga mijinta da yayarsa. Mutaƙƙa tare suka fita da Yallaɓai., ya ce zai kira Hauwa ta yi girki ta taho zuwa anjuma. Zaman jugum jugum muka yi duk na gaji har aka fito da ita daga Tiyata an samu nasaran ciro mata namiji, an kawo mana jaririn ita kuma sun kaita ɗakin hutu ba ta farfaɗo ba.   Ranar dai a asibitin nan na yini, gajiya na yi da la'asar na ce ma Anty Bahijja zan ta fi, tunda ita Anty Maimuna ta koma gida, Badawiyya ce ɗiyarta ta biyu ta zo, Hauwa sai wajen biyu na rana ta zo da abinci, ni ban ma iya ci ba, saboda ba na iya cin wani abu in dai a acikin asibiti ne sallah ne da ya zame min dole na fita can haraban asibitin in da masallaci ya ke na yi sallah.   "Za ki tafi kuma? Ba ki jira ta farfaɗo. Kuma ai na ɗauka sai dare in Tafida ya dawo sai ya ɗauke ki, ku koma gida tare."   Mamakinta ya kamani, ita wai ba ta da tausayi ne, ko mijin Haliman ya ta fi gida yayar tasa ma tace bari ta je ta dawo. Ni fa na yi iya abin da zan iya yi ko ƙanwata ce ai sai haka, kuma ba zan zauna domin na faranta musu ni na ƙuntata ma kaina ba. Sai na buɗe baki na ce. "A'a ba mu yi haka dashi ba, gida zan koma na takura da zaman waje ɗaya. Zan dawo gobe da safe in sha Allahu."   Wani kallo ta yi min kafin ta ce" Uhm! Ni ban ma tsaya bi ta kanta ba na ce ma su Hauwa zan ta fi gida, lamgwabar da kai ta yi kafin ta ce"Na ɗauka sai dare"   "Wallahi ko Yallaɓai ya ce na zauna sai dare zan faɗa masa na gaji haba. Gida za ni da safe sai na dawo."   Tana min dariya ni kuma na sha kuni, mun yi nesa da su Badawiyya, ta rakani har haraba asibiti sannan ta koma ita kan zama daram tun da sai Mutaƙƙa ya dawo zai biyo ya ɗauketa su koma gida  yara ma gidan Nene ta kai su wajen Jawahir.   Ko da na isa gida na gaji, wanka na fara yi sannan na nemi abin da zan ci indomie na dafa na ci sannan na dawo dai dai. Sai a lokacin na samu daman duba wayata na ga ashe Yaya Auwal ya kirani har sau biyu ban gani ba sai na bi bayan kiran na shi. Bai ɗauka ba sai na kyaleshi, Dan Abuja ne masu aiki a gidan kuɗi ba sa ɗaga kira sai dai su kira, ba daɗewa sai ga shi ya sake kirana. Bayan na ɗauka mun gaisa da tambayan iyalai.   "Ke wai me ya faru ne? Na ga ana ta cewa kun samu matsala da Ma'u a can group na gida? Baki na taɓe kafin na ce"Rashin Fahimta ne. Amman Alhajimu ya daidaita mu." Sai kawai ya ce"Oh. Ku ma dai kamar wasu yara. Sadiya kin girma fa ya kamata ki daina wasu abubuwan.".   Da toh na amsa shi sanin halin shi, busy shi baya bashi daman zama ya gane abin da ke faruwa na kuma san sai yanzu ne hankalinshi ya kai kan abin da ya faru, daga nan muka sauya wata hirar. "Yaya Auwalu me zan samu ne?   Ya na yar dariya ya ce"Me zan samu dai Matar injiniya? Baki na rufe ina yar dariya kamar ya na ganina kafin na ce"Ku ne masu kuɗin a hannun ku fa, ni dai faka faka ko yar wata ashirin ne ina jira."   "Allah ya kawo."   Daga haka muka yi sallama, bayan na ce ya gaida Aneesa da yara, nima ya ce in gaida su Jidda, mun gama waya ba daɗewa sai ga alert ɗin 10k ya turamin na yi mirmishi, shi ya sa fa nake son Yaya Auwal ba ya kiran banza, irin Yaya Hamza ne, ba su ba ka ɓacin rai amman kuma za su saka ka farinciki. Ba irin su Yaya Abubakar ba, shi ai wani lokacin kamar wani mace haka ya ke jin kansa.   Sau ɗaya na kira Alhajinmu muka gaisa bayan ya yi mana Sulhu da Ma'u. A raina na yi niyyar sai an yi wata ban je gida ba, Ma'u ta cigaba da zuwa a madadina. Yaya Murja, har yau ban buɗe sakon ta ba ni fa ba na son munafurci,  Rahila daman ita ban saka ta a lissafi ba ta da matsaya. In na ce ta na tsoron Ma'u sai ta ce ba haka ba ne, amman dai na san cewa tana ƙaunata, takaici na ɗaya tafi kaunar Ma'u sama da ni.   Sai can mangariba Yallaɓai ya kirani wai ina asibiti ne? Na ce na dawo gida sai ya ce shi zai biya sun yi waya da Anty Bahijja ta ce Halima ta farfaɗo na ce to ya gaishe ta.   Sai can dare ya dawo,  bayan ya yi wanka muka zauna a dinining ya ci abinci, muna hira sama sama akan dai wani aikin kwangilan makaranta da ya yi sama da wattani goma shuru ba a biya su ba sun gama processing komai suna ta saka rai shuru, ni har na saba saboda na san yanayin aikin na su, kafin kuɗin su zo duk sai na hannun ya gama ƙarewa an jigata. Ko da zamu kwanta hirar da muke yi kenan, ina faɗa masa ko kayan abinci sun yi ƙasa ga haihuwan Halima ma, Allah dai ya rufa mana asiri.   Ko a baya in ƙannensa ko yayyensa cikin ƴaƴansu sun samu karuwa in bashi da shi, ni na ke yi wani lokacin ma ba na jiransa in akwai kuɗi a hannuna, tsakaninshi da su dabam nima haka, in ban yi ba sai surutu ya tashi ko ba yawa ina zuwa na miƙa, ban damu da a gode ko kar a gode ba abin da na san zan iya shi na ke yi ba ruwana  da yin abu don wani ya gani ko ya yaba, kai tsaye na ke yin al'amarina ka zauna da ni domin Allah ko akasinsa ruwanka ni ba ruwana harkan gabana kawai na ke yi.   Da safe ma da ya shirya zai fita cewa ya yi ko zai ijiyeni a asibitin ne, na ce a'a ya je kawai in na shirya an juma zan je da kaina  ina zan bi shi na je saman jumgum kamar ni ce na haihun. Sai azahar na fita bayan na ci na ƙoshi na je na iske asibitin cike duk da fa an ce a bar ta ta huta, dangin mijin ma kaɗan ne duk iyalan marigayi inuwa ne.    Na iske Anty Zuwaira da  Anty Maimuna. Anty Bahijja ne ba ta zo ba sai dai su Suhailat. Hauwa ma can na isketa amman ba ta daɗe da zuwa ba. Ban daɗe da zuwa ba Sai ga Hajiya Iya,  tare da Suwaiba. Muna asibitin Maman farko ta zo tare da su Zulaihat, daga gidan gaisuwan suke, anan na yi ma Mama gaisuwan ma, Anty Zuwaira ce ta ce min wai ta daɗe ba ta ganni ba, ina yar dariya na ce"Mimisco ba ki zaman gida ko an je bakya nan." Mirmishi ta yi kafin ta ce" In na dawo ai za a faɗa min kin zo ko? Har su Jidda ma ana yi min rowan su?   Hakuri na ba ta na ce suna gidan Anty Maimuna amman za su zo mata in sha Allahu, Anty Maimuna na kusa ta na ji ta fara faɗin itama da ya ya na aikasu sai da ta yi ta mita ban takan ta ba, itama Mimisco ɗin da ya ke yar ba ruwanta ne ba ta wani maida kai kan mganar Anty Maimuna ba.   Ni dai na ga mun yi yawaa a asibitin ana la'asar na yi musu sallama, na ce zan biya na gaida Nene an ce ta kwana da zazzaɓi, tare koma da Hajiya Iya, a gidan Nene na yi sallar mangariba sai na kira Yusuf na ce ina Gwammaja, in ya ta so daga Office ya biyo mu ta fi gida.   Nenen ma ta ji sauƙi, tunda Anty Zuwaira ashe ta zo da safe sun je asibiti an duba ta an bata mganguna. Ni dai na ce har da hayaniya saboda yaran Halima suna nan kuma ba sa jin magana sun cika ƙiriniya.   Har goman dare muna gidan Nene mun shiga gida sha ɗaya na dare, a gajiye nake ko wanka ban yi ba na yi shirin kwanciya. Tunda na ci Tuwo a gidan Nene, dije ta yi shi da rana da miyar taushe. Na bar Yusuf na ta aiki a bisa laptop ɗinsa ni dai na yi barci na barshi ban san lokacin da ya gama ya zo bayana ya kwanta ba sai dai farkawa na yi kawai na ganshi kwance ni kuma duk na rufa masa kafafuna bawan Allah ya na shan bugun dare.   Da safe da Inna Mariya ta kirani ƙanwar Mama ce tana gaya mini rasuwar, Yayar babansu Baaba Atu, Allah Sarki na ji mutuwarta ko kwanaki da muka je Gandun albasa mun shiga mun gaisheta ashe jinya ba na tashi ba ne. Ni na kira Amina na faɗa mata rasuwan ita tunda ta na nesa a kaduna take aure sai dai ni na shirya, kuma mu daman a gidanmu duk abin da ya faru a bangaren Gwaggo gabaɗaya ake zuwa haka bangaren Mama, tun Mama na da rai har ta rasu haka muke yi, Aminar ce ta shiga group ɗin gidanmu ta faɗa rasuwar sai na ji Anty Balki suna faɗi a haɗu a gida sai a tafi gabaɗaya a raina na kunsa sai dai mu haɗu a can. Yaya Auwal kawai na kira na sanar mawa ya ce Yanzu suka gama waya da Alhajinmu ya ce ya gashi ma a hanya zai tafi jana'iza mun gama wayar da cewa ya ce karshen wata zai shigo kanon in sha Allahu.   Ina faɗa ma Yallaɓai rasuwan yace na shirya mu tafi Allah ya sa ya samu jana'iza. Tea kawai muka sha muka fita sai Gandun albasa, can ne asalin gidan su Mama, itama Baaba Atu ɗin da jinya ta yi tsanani ne, su kawu su ka ɗaukota zuwa gida anan aka yi jinyarta. Ta yi aure a kura mijinta ya rasu amman yayanta duka mata ne duk suna can, ko da muka je dai duk sun iso, tun da rasuwar ta asuba ce can muka iske Alhajinmu da Datti, har da Yaya Abubakar.   Ni kuma sai na shiga cikin gida. Inna Mariya ce kaɗai mace a yan'uwan Mama da suka rage uban su ɗaya, sai su Kawu Nafi'u da suma uba suka haɗa, Inna Madiyana ta riga ma Mama rasuwa itace suke uwa ɗaya uba ɗaya, namijin ma tun kafin a haifemu ya rasu. Duka iyayensu sun mutu, daman ko da muka taso ba mu san kakkaninmu na bangaren uwa ba, mun dai san ta bangaren Uba. Allah ya jiƙan ki Hajiya Dubu.   Sai bayan an yi jana'iza an tafi kaita sannan sai ga su Yaya Balki, Yaya Aina, Yaya Murja. Sai Zaitunan Matar Yaya Abubakar. Sun shigo kenan ana gaggaisawa sai ga Ma'u itama ta iso, Gwaggo daman tare da su Alhajinmu suka zo.     Saboda gidan gaisuwa ne ya sa ba su yi min wata mgana ba mun dai gaisa. Sai can bayan an dawo daga kaita maza sun shigo sun yi gaisuwa masu tafiya sun tafi masu tsayawa suna ƙofar gida suna karban gaisuwa. Yallaɓai mun yi sallama ya ce zai leka Office zuwa anjuma zai zo ya ɗaukeni, Alhaji mustpha ya zo, Alhajimu dai da Datti suna kofar gida Yaya Abubakar kuma ya tafi.   A waya Yaya Auwal ya kirani na ba ma Inna Mariya ya yi mata gaisuwa  ya ce ya yi ma su Kawu Nafi'u ta wayar Alhaji, wasu ƴan uwan namu ma na daɗe ban gansu ba sai nuna ni ake yi ana faɗin diyar Rukayya ce marigayiya, muna gidan har dare, Ma'u da la'asar ta tafi, mun gaisa da fara'a kamar yadda nima ta yi min.  Anty Aina ma ta tafi ta ce za ta yi girki ita da Anty Balki, Anty Murja ce kawai sai ni da Gwaggo.   Muna ɗakin matar Kawu Ali tare da su in da ake karɓan gaisuwa  Yaya Murja ta kalleni bayan mun idar da sallar mangariba. "Kin kyauta Sadiya  har ni na kiraki kiƙi ɗauka na yi miki magana ta wasop nan ma shuru, ni fa yar gaskiya da gaskiya ce, daga kuma ƙin ta sai ɓata."   Kallonta kawai na yi ban yi magana ba. Ta yi ta faɗa har ta na ce min"Ma'un da kika tsana ga ta nan da ita wajen gaisuwan nan in ba masoyinka ba waye zai yi maka haka? In ta biye ta naki ai da ba za ta zo ba."     Kamar in yi tsaki sai kuma dai na fasa na kyaleta, Gwaggo ce  ta tsawatar  mata ta ce ta bar maganar Alhaji ya riga ya kashe ta. Ni dai ƙala ban ce mata ba na fahimci gwara na riƙa yin shuru zai fi mini alheri. A lokacin Rahila ta kirani ta yi min gaisuwa bayan mun gama waya Anty Maimuna ta kirani ta ce Tafida ya ce an yi mana rasuwa. Su Jidda suna gidan Nene in mun taso mu biya mu ɗauke su. Ta yi min gaisuwa na tambayi jikin Halima ta ce da sauki suna saka ran gobe su sallamesu su maida ta gidanta.   Sai Taran na dare muka bar gidan, nan na bar Gwaggo tare da Alhaji za su koma gida, Yaya Murja ma ta na nan mijinta ɗan gareji ne in ya taso zai biyo ya ɗauke ta. Sai da muka biya Gwamnaja muka ɗauko su Jidda, Baby ta makalemun tana faɗin"I miss u Umma." Ina dariya na ce"Miss u more my Princess."   Sun yi kitson su, sannan an siya musu sabbin lunch box da sock da sandal ɗin makaranta suna nuna min nace sun gode. Nene na falo zaune ta ji sauƙi ta yi min gaisuwa ta ce Maimuna ta faɗa mata da ta kawo su Jidda. Har Hajiya Iya sun yi min gaisuwa, sun ce in suka samu lokaci za su leƙa tunda Nene ba ta jin daɗi.   Washegari Litini ma ban zauna ba. Amina ta iso daga kaduna ni kuma na tsaya a gida na yi girki sannan na tafi dashi. Ko da na je Ma'u ta yo abinci ta aiko da shi alale. Yaya Aina ma ta yo awara ta kawo hatta Gwaggo ta dafo abinci ta zo da shi, Rahila ma ta zo gaisuwa a ranar, haka muka yi ta jigilan zuwa har ranar uku, Hauwa ta zo mini gaisuwa ita da Mutaƙƙa. Muniran Nasir ta zo min gaisuwa, Anty Zabba'u kuma a waya muka yi magana tun da mijinta soja ne, Yaya Usman suna parthercourt ne su Yaya Hamza ma duk ta waya suka yi mana gaisuwa.   Sai da aka yi uku na samu hutu a gida wannan zirga zirgan ya sa na ji duk jikina ba daɗi  sannan sai na yi ta ganin juwwa ban kawo tunanin komai ba sai rashin zama waje ɗaya. An sallami Halima tana gidanta ni ban ma je ba, Amina ranar huɗu ta koma kaduna ni dai ban sake komawa ba sai ranar biyar daga nan sai ranar da za a yi bakwai. Da la'asar kuma na wuce gidan Halima domin na ƙara duba ta. Tun da tun bayan da ta koma gida ban samu zuwa ba. Sun ɗaga suna sai sati biyu sannan za a yi.   Ban yi mamakin ganin Ma'u ba, saboda tana shiga dangin mijina da sunan ta na yi ma Anty Bahijja kara, ni kuma na san  ba haka ba ne, tana ganina ta taso ta tare ni, na saki fara'an da ke faman fuskata. Wacce itama nata iya saman fuskarta ne. Tare da ƙawarta Shema'u suke, wacce haɗuwa ce ta tun muna makaranta. Shema'u na ganina ta tare ni da fara'a tana fadin" Hajiyar Injiniya Afuwan. Ban ɗauka maganata ta ranar za ta yi miki zafi ba. Don Allah ki yi hakuri." Mirmishi na yi mata kafin na ce"Ayya rashin fahimta ne. Ya wuce."   Ban zauna wajensu ba na shiga cikin ɗakin mejego muka gaisa, na ɗauki Baby, ina kallo ta na gefe ta ce"Anty Sadiya ya haƙuri? Yaya Tafida ya ce an yi miki rasuwa" Sai na amsa mata, muna ɗan taba hira su Sulahait ne a gidan sai Hauwa da Jamila, Hauwa ce ke ta aiki, kallonta kawai na ke yi ina dariya a raina. Ba aikin da zan yi nima na gyara zama can falo kuma su Ma'u ne, ban son haɗa inuwa ɗaya da ita shi  yasa ban fita ba.   Ina zaune na ji marata ta karta daman tun jiya da daddare ciwon mara kaɗan kaɗan ya matsamin ba na tunanin al'ada tunda na yi shi a wannan watan. Ban taɓa tunanin in na shiga makewayi zan ga jini ba, jini sosai na gani na zubar mini hankalina ya tashi na wanke jikina na fito, da sauri na ce ma Halima zan ta fi, ko tsayawa ma in bi ta kanta tana cewa lafiya ta ganni cikin gaggawa?   Na fita falo ina kiran wayar Yusuf ta shiga amman bai ɗauka ba, su Ma'u ba sa falon ƙila sun shiga sallah ne. Hankalina tashe na fita na samu abin hawa zuwa gida ina shiga gidan sai ga wayar Yallaɓai. "Yallaɓai jini na gani, na bani al'adata ta dawo da mini wasa kamar baya." Cikin damuwa ya ce"Topha. Yanzu kuma? To da yawa? Ina cire mayafin jikina na ce"Ina jin sa yanzu haka yana bin kafata. " "Subhanallah, ko za ki tura mini mganin da suke rubuta miki a asibiti lokacin nan? Na ga kina amfani da shi zubar jinin ya ke dakatawa."   Kamar in yi kuka na ce"Na daɗe ban je na ga likita ba. Ba zai yuyi na sha mgani ba tare da na je an sake dubani an ga in da matsalar take ba. Ka taimaka mini ka sake kira mini Uncle Abba ina bukatar ganin likita a cikin satin nan."   Sai ya ce na kwantar da hankalina bari ya kira shi, muna gama wayar a daddafe na tafi tiolet ɗin falo ma ba na ciki ba, kayana duk sun baci ina ma turarradin ban bata ma mai Napep kujera ba, kayan jikina sun lalace na tube na yi wanka kayan kuma na jika su a bucket, haka na fito ina hawaye, ina ta murna side effect ɗin planining ya daina taɓa ni, tunda duk a asibitocin da na riƙa zuwa a baya sun tabatar mini da komai lafiya zan iya samun ciki ko yaushe ne. Mun kashe kudaɗe a asibitocin kuɗin dake garin kano ba a dace ba, shi ya sa na yi amfani da shawaran mutane na ga gwara na je babban asibiti. A baya na yi ta fama da ciwon mara da zubar  jini a can wani babban private hospital sun ɗorani kan wani mgani na yi amfani dashi kuma cikin ikon Allah komai ya daidaita. Ina cike da yaƙinin komai zai zama tarihi sai ga shi al'amarin ya dawo sabo.   Zubar jini nake yi sosai sai da na saka Pampers  daman ina da shi, saboda ina bleeding in ina period shi na ke amfani dashi.   Ina zaune kawai ina hawaye, abin duniya ya isheni Yusuf ya sake kirana labarin da ya ke faɗa mini ya saka ina hawaye ina dariya. Likitan da zan gani a Shika ta ba ni dama ranar monday sha ɗaya na safe, in na je zan kira wayar Dr Fadil wanda Uncle Abba ya tura masa lambar.   Ina mirmishi na share hawayena ina faɗin"Alhamdulillah." Me na ke tunani. Ina tunanin kamar ina da wata matsalan anan ba a gano ba ne,tun da ba babba asibiti ba ne. Ina hashashen in na sauya waje da asibiti mai kyau da ke da ƙwararru kila za a iya gano wani abun har na nemi magani domin na samu waraka. "Ki kwantar da hankalinki, sai mu je tare in sha Allahu "   Ajiyar zuciya na sauke kafin na ce" Shi ke nan,  Allah ya kaimu nan da kwana shidda kenan ko?   Sai ya amsa mini ganin duk na damu sai ya shiga lallashina, da cewa in sha Allahu ba wata matsala. Cikin yaƙinin da na ke dashi na ce" In sha Allahu." Bai kashe wayar ba sai da ya ga na sake har muna hira da dariya sannan ya kyaleni. Amman bayan mun gama wayar tagumi kawai na yi ina tunanin makomar rayuwata. Ina kwaɗayin na ƙara haihuwa, an ce komai na mahaifata lafiya kalau zan iya samun ciki kowani lokaci amman sai yaushe? Sama da shekaru uku tun ina saka rai har na fara gajiyawa? Ni kaɗai na yi ta kukana ina sharan hawaye kasa komai na yi kafin su Jidda su dawo makaranta jinin ya ɗan tsagaida sau ɗaya na sauya pampers, ban yi musu ko abinci ba cewa na yi su sha goldenmorn sannan in sun huta Jidda ta dafa musu ko farar taliya ne su ci da mai, ɗakina na koma kawai na kwanta  ina jin kasala na rufe ni. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:JamilaUmar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. *🅿️06* Har bayan mangariba ina cikin ɗaki ban iya fitowa ba, na ci kukana har na ƙoshi na lallashi kaina. Baby ta zo za ta dameni da surutu na ce ta je Yaya Jidda ta kunna mata Cartoon. Ita kanta yarinyar ta lura da yanayina har yadda ƙasan idanuwana suka kumbura.   "Umma ba ki da lafiya shi ne kike yin kuka?   Sai da ta saka ni mirmishi, kanta na shafa kafin na ce" Lafiya ta ƙalau. Je ki wajen Jidda, kun yi sallah ko? Sai ta gyaɗa mini kai.   Jin abin da na ce ya sa sai ta juya ta fice daga bedroom ɗin na bita da kallo tana fita na ƙara fashewa da kuka, ƴaƴa biyu gare ni su Allah ya ba ni, yanzu in ban ƙara haihuwa ba suka zo suka mutu fa? Tuna haka kaɗai sai da ya sa na ji kamar jinina ya yi sama, domin ji na yi numfashina na barazanan barin jikina gabaɗaya tsabar tashin hankali da damuwa.   Daga ƙarshe suma sun gaji da zama a falo su kaɗai sun saba in ina gida tare muke yi salolli da azkar mu yi karatun Qur'ani sannan na duba littafansu na makaranta muna yi muna hira, su kaɗai gare ni domin a wannan rayuwar ƴan'uwanka ma suna gudunka, Mijin ma ba lalle ya zama mai amana ba, su ko ƴaƴa ko akan bola uwa ke kwana ba su isa su sauya ma tuwo suna ba.   Ganin har an yi sallar isha'i takwas ta gota ban fito ba sai ga Jidda ta kwaso mini Baby sun shigo har Bedroom ɗina, ina cikin bargo na dunkule suka hawo har saman gadon suna kiran sunana. '"Sannu Umma? Kan ki ke ciwo?   Haka Jidda ta tambaya, sai na yi ƙoƙarin goge idanuwana na miƙe zaune ina faɗin"Na ji sauƙi, kun yi sallar isha'i? Jidda ta ɗaga min kai kafin ta ce"Har karatun Qur'ani mun yi na ƙara ma Baby na ta karatun" Kanta na shafa kafin na ce"Allah ya yi miki albarka Jiddan Umma." Baby ta ɓata rai tana faɗin"Ban da ni Umma? Sai itama na shafa kanta ina saka mata albarka, kantowa ta yi saman jikina, ni kuma sai na koma ina wasa da jelan kitsonta na 2step da akayi mata, da ya ke suna da tsawon gashi ni suka ɗauko duk da shima babansu da dangin shi gabaɗaya suna da cikar suma.   Jidda ta yi ta yi ta zubo mini abinci na ce ta bari in na tashi zan sha Tea. Wanka na ke so na yi ga kaya can da na ɓata ma ban wanke ba, Baby har ta yi barci a jikina sai na ce Jidda ta ɗauketa zan ta shi.   Tashin ta ta yi, domin ba ta iya ɗaukanta Baby akwai jiki a cure,  bayan ta tashi ta kama hannunta zuwa ɗakinsu na ce ta tabbatar ta kaita tiolet ta yi fitsari, na ɗan ƙara samun natsuwa ganin jinin ya ɗan tsagaita amman bai ɗauke gabaɗaya ba. Wanka na yi, na fito kenan na ji buɗe get na san Yallaɓai ne.   Ba ni da wani ƙarsashi sai kawai na zura wata rigar barcina doguwa, kaina buzu buzu ko ta kan shi ban bi ba, haka na koma gefen gado na zauna ina tunanin abin yi? Sai na ji kamar ina rasa tunanina na wani lokaci saboda halin damuwar da na ke ciki.   Ina jin sa sai da ya shiga ɗakin yara ya gansu sannan ya ƙariso Bedroom ɗin mu, yanayin yadda ya ganni kamar ƙanwar mahaukaciya shi ya san ya yau ɗin fa ba lafiya.   Hannuwansa ya buɗe mini alamun in ta so amman na kasa tashi, kallonsa kawai na ke yi hawaye suna cika mini kwarmin idanuwana. Shi ko ganin naƙi tasowa ya sa ya tako gabana, hannunsa akwai brief case ɗinsa sai wasu takardu, sai da ya sauke su saman madubi sannan ya ƙariso gabana ya durkusa lokaci ɗaya ya na rike mini duka hannuwana.   Ina jin ya riƙe ni sai kawai hawayen da na ke ta riƙewa suka kwaranyomin a saman fuskata, marairaice fuska ya yi kafin ya ce"Haba Sadiya ta, ba na ce ki bar damuwa ba? Kin kuma ce min kin bari? To me ya sa kike kuka kuma? Kalle ki fa Yallaɓanki ya dawo amman kin kasa taran shi da irin mirmishinki da kika san ya na kwantar masa da hankali, sai ki tare shi da kuka? Alhalin kin san kukan ki dai dai yake da yi ma kwanciyar hankalinsa barazana?   Ya ƙarishe faɗa, ya na kallona ni kuma sai na ji raunina ya bayyaana share mini hawaye ya ke yi da tattausan hannayensa duka biyu, faɗi ya ke yi" Ki daina kuka, ki bar wannan kukan? Kina so na shiga damuwa ne?ko so kike yi nima na fara kukan? Uhm Sadiya ta?   Sai kawai na riƙe masa hannunwansa da duka hannayena guda biyu, ban san ma lokacin da na barƙe da kuka ba, kuka wiwi kamar Jidda. Daman a jikin Yusuf kawai na ke samun daman wannan kukan, ba ni da uwa da ace Mama na raye ita zan yi ma wannan kukan. Gwaggo kuma ba na zuwa gaya mata matsalolina ita da Alhajinmu ba na so su shiga damuwa, sannan duka ƴan'uwana ba ni da sakewa da kowa sai Rahila, itama ta na da ji da na ta auran ba zan ta zuwa ina damunta, a ɗakin mu Yaya Auwal ne kuma shi Namiji ne sannan ya yi nesa da mu, Amina kuma ƙanwata ce itama kaduna ta ke aure, Datti kuma yana makaranta sai in ya zo gida hutu.   Dole dai kafaɗan Yusuf ne abin jingina na in yi kukana shi kuma ya lalace wajen lallashina, har a raina ina jin ƙila watarana wannan kafaɗan da na ke kwanciya na yi kuka za ta iya yi min nesa da wat rana sai dai na yi kuka na a saman gwiwoyoyina ba zan iya samunsa a duk lokacin da na ke bukata ba, tunda ƙila ba lalle ya ƙare rayuwarsa da ni kaɗai ƴaƴa biyu kacal ba, ahalin ya na da yadda zai yi ya samu abin da ya ke so na mallakan yara da yawa.   Lallashina yake yi da duka iya kalamansa bakinsa, amman sai da na ji zuciyata ta rage kunci sannan na daina kuka na koma shassheka, rumgumeni ya tashi ya yi bayan ya zauna gefen gado, yana ɗan tapping ɗin bayana alamun lallashi.   Ɗagowa na yi ina kallonsa fuskata jage jage da hawaye, shi kuma sai ya saka haɓan hannun rigansa zai share mini hawaye da sauri na kauda kaina na saka hannu ina sharewa da kaina cikin muryan damuwa ya ce"Me ya sa kika hanani na share miki hawaye Sadiya?   Cikin dakushewar murya na ce" Saboda kar ka ɓata kayan ka." Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce"Kaya? Me nene kaya? Ban so kar ki sake hana ni share miki hawaye, domin ina fatan har ƙarshen rayuwata na zame majinginar in za ki yi kuka, sannan na zama mai share miki hawayen ki, ba na so na ji kamar na gaza miki ne Sadiyata."   Kai na girgiza kafin na ce"Ko ɗaya. Ba ka gaza mini ba Yallaɓai. Sai ma ni ce na gaza maka, na kasa ba ka farincikin da ka ke so, na kasa sake Haihuwa Yusuf, wallahi ina so na ƙara haihuwa ko ɗaya ne? Ko ɗaya ne ko? Ai kana so ko?   Haka na ke faɗa da sauri da sauri  sai ya lura kamar ma na fara fita hayyacina sai ya yi ƙokarin rike mini hannu lokaci ɗaya yana faɗin"Shii. Kin manta muna da ƴaƴa? Ƴaƴan mu biyu Sadiya muna da Jidda muna da Baby? Me ya sa za ki yi ta damuwa bayan muma muna da ƴaƴa ba wai ba ki taɓa haihuwa ba ne"   "Ba za mu rayu da ƴaƴa biyu ba Yusuf, in suka zo suka mutu fa?   Haka na faɗa, ina jin har hannuna da ke cikin na Yusuf na rawa. Kallona kawai ya tsaya yana yi cikin mamaki kafin ma ya samu zarafin mgana na cigaba da faɗin.   "Ina ta tunanin me ya sa lokacin da na kawo shawaran zan yi planning saboda makaranta ba ka hana ni ba? Me ya sa ka biye mini? Me ya sa ka amince, da ka hana ni da ka bar ni, na yi ta haihuwa ai wahala ba ta kisa, ba zan mutu ba sai lokacina ya yi, me ya sa ba ka hana ni ba?   Haka na faɗa da ƙarfi sannan lokaci ɗaya ina jijjiga hannayensa, Kasa motsi ya yi sai kallona ya ke yi, yasan na fita hayyacina kuma ko ya yi magana ba zan saurare shi ba, sai kawai ya kamani ya yi mini wata irin rumguma da ƙarfi sai da na ji numfashina ya na barazana ɗaukewa dole na yi shuru amman fa na fashe masa da kuka.   Ƙamƙam ya riƙeni yana faɗin"Ba na so, me ya sa kike irin wannan tunanin? Ba za su mutu ba in sha Allahu ba yanzu ba."   "Yara suna mutuwa fa Yusuf? Ko Baby in ta mutu fa? "Na ce ki bar cewa haka ko? Ya yi min tsawa bayan ya ɗago ni yana mai ƙureni da ido. Sai na sadda kaina kasa ina kuka. "Kin yi nadama ne? Ko ba ki yi planining ba. In abin da Allah ya kaddaromana kenan Sadiya ba fa mu isa mu tsallake wannan kaddaran ba, kuma planning ba laifi ba ne domin kin nemi tazara saboda karatun ki, ko malamai ai suna mgana kan a yi tazaran haihuwa, me ya sa yanzu kike nadama? Ko an ce kina da wata matsala ne? Kin je asibitin nan an yi duk gwaje gwajen an tabbatar da lafiya lau mahaifanki. Side effect ne, kawai ya taɓa ki, kuma kusan daman komai na rayuwan yana da nashi amfanin da rashin shi, me ya sa za ki zauna ki rasa hankalinki? Har kina yi ma ƴaƴan mu fatan mutuwa?   Kafaɗata ya rike duka biyu, sannan ya kira sunana har sau biyu na amsa sannan na ɗago ina kallonshi.   "Kar na kara jin mganar mutuwa a bakin ki kin ji ko? Sai na gyaɗa masa kai kawai ba tare da na yi magana ba, shi kuma sai ya koma ya na sharemin hawaye yana faɗin"In Allah ya so za ki kara haihuwa, in bai so ba duk som mu da haka ba za ki ƙara ba. Ubangiji ne ke iya tsara ma bawa rayuwarsa tun daga ranar haihuwarsa har ranar mutuwansa."   Jikina ya yi sanyi, shi na ke kallo kafin na ce" Kai fa? Haka za ka zauna. Na san kana son yara a kallah dai ko ba da yawa ba kamar biyar haka." Bai yi min mgana ba sai da ya gama gogemin fuska tas da haɓan rigan shi, ya na kauce ma mganar ne, ya mikar da ni yana faɗin"Mu je ki yi wanka"   Kai tsaye na ce"Na yi wanka fa" muryata a shake, shima kai tsayen ya ce"Ba irin wannan ba, irin wankan da kika saba mini" Ban san lokacin da na yi mirmishi ba, har cikin tiolet ya kaini, ya duka ya sumbaci bakina sannan ya fice ya barni, na ɗan samu natsuwa shi ya sa na ƙara tuɓewa na sake yin wanka lokacin da na fito ya na ɗakin shi ya taya ni na shafa mai na shirya, kwalliya ya ce yana so na yi masa ina shagwaɓewa na ce"Wani kwalliya kuma da daren nan Yallaɓai na? Hararana ya yi kafin ya ce"Bashi za ki biya,  ki yi mini abin da kika saba na more kallon ki kafin na kwanta,." Ganin na yi shuru ya sa ya marairaice ya na faɗin"Ko ba ki so na samu natsuwa daga kallon ki ne?   Ina jin haka na yi saurin girgiza kaina. Kwalliyar na yi masa na saka riga da wando. Wandon mai ɗamewa ne, rigar ma haka shi ya tayani na gyara gashina na saka rebon zan saka hula ya ce na bar mai kayansa ahaka, to kayansa ne shi ya sa bar masa kayansa.   Na faɗa masa ban yi girki ba, taliya ne Jidda ta dafa, sai ya ce kar na damu ya siyo mana kaza. Falon farko muka fita ya ɗauko mana kazan muka baje a saman cafet muna ci, ya na bani a baki ina bashi muna hira haka sama sama sannan jefi jefi muna kallo.   Na leƙa su Jidda har sun yi barci daman guda biyu ce muka ci ɗaya muka saka musu ɗaya a fridge, bayan mun gama ci muka ɗora da sanyayar maltina Yusuf ya kwashe komai da muka gama ya gyara wajen, ya kawo mini tissue ya goge mini hannuna da bakina shima ya goge na shi, kujeran mai zaman mutum ɗaya muka zauna ni na kwanta saman jikinsa,   shi kuma ya saka hannu ya rumgumeni yana wasa da gashin kaina, muna hira sannan muna kallo a tashar Mb2 ne ana wani film ɗin Horror ina ta cewa ina jin tsoro amman Yusuf ya ƙi sauyawa wai ba wani tsoro.   Mu ne har 12 na dare sai da film ɗin ya ƙare, sannan muka kashe komai muka koma ɗaki. Yusuf ya yi wanka sannan muka kwanta muna rumgume da juna, dukkanmu mun yi shuru muna jin bugun zuciyan juna. "Yallaɓai na" "Uhmm"   Sai na gyara kwanciya a saman ƙirjinsa ina faɗin" Ka yi hakuri, na gaza ba ka dukkan farinciki ta bangaren ƴa'ƴa. Na san kana son yara domin tun kafin mu yi aure in ka zancen wajena sai ka yi ta faɗin Sadiya ko ƴaya goma kika haifa min ba za su isheni ba, na daɗe da sanin kai mai so ka ga gidanka cike da yara ne, bayan haka kuma ƴan'uwanka ma son ka haihu da yawa Nene ma haka, uwa uba ƙannenka da suka yi aure bayanmu duk sun fika yawan ƴaƴa na san ko yaya ne kana jin ba daɗi a ƙasan ranka, ka yi hakuri ba ni da wata mafitar ne."   Na faɗa muryata na yin ƙasa,. Kamar ba zai yi magana ba na ma ɗauka yana barci ne. Sai da na ɗago ta cikin duhun ɗakin akwai ɗan hasken dake shigowa ta window, na ganshi idanuwansa a lumshe, na fahimci ba barci ya ke yi ba da ya ƙara rumgumeni ƙam a samam kirjinsa. Ajiyar zuciya ya saki kafin ya ce" Ni ba ki taɓa gazamin ba,kin ba ni dukkan wani farincikin da ko wani namiji ya ke bukata. Kin zame min matar rufin asiri, da me kika rage ni? Ba ki rageni da komai ba mganar ƴaƴa na faɗa miki in biyun Allah ya bar mana mun gode in ya ƙara mana mun gode, mganar ƴan uwana kuma wannan na su ra'ayin ne, ba wanda ba ya son ya tara kyakyawan zuru'a Sadiya. Ita kuma Nene ki daina maganarta jikokinta nawa? Me ya sa sai nawa ne za ta damu domin ban haifa da yawa ba?   Idanuwana suka kawo kwallah kafin na ce"Saboda kai ne Tafida. Kowa ya shaida kai ɗan gatan Nene, ne ta sha yi maka addu'an ka gaji mahaifinka wajen tara  zuru'a mai yawa. Sannan ka manta burin ka na sake haihuwata domin na yi ma Alhajinku takwara?   Numfashi ya saki ya fesar kafin ya ce"Ban manta ba. In kin sake haihuwan zan yi ma Allah godiya in ma ba ki sake ba duka godiyar zan yi masa, ai bar ni haka ba ya bani biyu, ina waɗanda suke nema har yau ko ɗaya ba su samu ba? Ko ban yi ma Alhajinmu takwara ba, ƴaƴan sa nawa ne suka yi masa? Masu sunan Alhaji ai ba su da adadi  ballatana in sha Allahu za ki sake haihuwa bayan Alhajinn Gwammaja har Alhajinmu za mu yi ma takwara in sha Allahu."   Kansa na ɗago na sumbata kafin na ce" Allah ya amsa" ya amsa min da Amin, ƙara shiga jikin juna muka yi, ya na so ya yi barci ni kuma ba na jin barci.   "Sadiya ta"   "Yallaɓai na."   "Barci na ke ji,"   Haka ya faɗa mini a saitin kunnena, sai na yi mirmishi kafin na ce"Saura magana ɗaya ta rage, in muka gama sai mu yi barcin ko? "Umh" Kawai ya ce ba tare da ya yi magana ba, ni kuma sai na yi shuru saboda ina ƙoƙarin iya faɗin abun da ke cikin raina. "Yallaɓai." "Ina jin ki"   Haka ya faɗa ya na tusa hannunsa a cikin rigata, wani sanyi na ji a cikin raina nima sai na kai hannuna saman kirjinsa ina shafawa kafin na ce.   "Yallaɓai na, kana son ka ƙara aure ko? Ya ji ni, amman bai yi mgana ba ina wasa da gashin ƙirjinsa cikin wani salo, mirginawa ya yi kaina ya kama bakina ya na kissing, nima sai na tallafi kanshi, daga nan mu ɗan birkita juna da salon wassani kafin mu koma muna maida nunfashi, tunda mai jan mota ya yi bakare a ƙofar boda ba halin shiga kuma ba halin fita.   "Ƙarin aure hukunci ne na ubangiji. In Allah ya kaddaromin zan iya ƙarawa, amman ni a yanzu ba ni da ra'ayi domin duk abinda namijin kwarai ke nema a wajen mace ina samu a wajen ki, me zan nema kuma a wajen wata macen? Raɗa na yi masa a kunne sai ya zille ya na dariya kafin ya mirgina ni na dawo saman shi ya ɗaga ni na zauna a saman cikinsa yana kallona ya ce" Ina samun natsuwa a tare da ke, har ina jin ba Namijin da ya kai ni morewa ma aure. Ko wata na aura an ya za ta kai ki a wajena? Ina dariya na ce"Oho. Amman dai ni nasan halin maza ne, kun ce ba kwa ta cin shinkafa ba sirki ba, gwara ku sirka da taliya ko macaroni"   Dariya ya fashe dashi ina taya shi. "To ni ke ce komai na, Taliyar macaronin tuwon duka kowani nau'in" Kafaɗa na noƙe ina faɗin"Ba na son yaudara da daɗin baki" "Sadiya ni zan yaudare ki? Yusuf ɗin ki ne fa?   Sukuwa na yi a kansa ina faɗin"Daɗin bakin maza ba, shi ne yaudaran" Nishi ya yi kafin ya ce"Ba dadin baki fa a tsakanin Yusuf da Sadiyarsa. Allah da gaske na ke yi  ke ce duka kayan daɗi na."   Ya faɗa ya na saka duka hannuwansa cikin rigata ta ƙasa, ya fara matsa min ciki da karfi, ina bige hannunsa ina cewa ya bari yaƙi, sai da na mirgina ya bina ya hau kaina yana ta matse mini ciki ina ta dariya har da hawaye sai da ya ga zan shiɗe sannan ya ɗagani yana faɗin"Ba daɗin baki Yusuf ke yi ba ko? Ina dariya na ce"Yallaɓaina ba ya daɗin baki."   Sai ya koma gefe ya na faɗin"Good. Girl." Kafa na saka na shure sa ina faɗin" Sai na rama" Yana dariyan keta ya ce"To taho mana, zo ki rama."   Ya faɗa yana ƙokarin kamoni na matsa baya ina dariya na san halinshi, yanzu sai ya yi min mugunta, bi na ya yi yana faɗin taho ki rama mana Allah ba komai,   Na haura ƙarshen gado ina faɗin" Ina ga na yafe maka." Dariya saka irin ta nishaɗin nan, sai da na tabbatar da ya ce ba zai min komai ba sannan na dawo jikinsa muka kwanta muna maida numfashi. "Ka matse min ciki, in ka kashemin ƙwayayon haihuwata fa? Ya na ƙokarin mikewa ya ce" Mu ga ni?  Ni fa na san in da na matse."   Hannunsa na bige ina faɗin" Wato su ƙarishe mutuwa ka samu hujjar ƙara aure ko? Na faɗa ina yar dariya shi kuma ya daina dariyan ya koma ya kwanta kawai na fahimci baya son maganar yasa na koma na lafe saman kirjinsa ina faɗin. "Ka sa ni ko aure ka ƙara ba zan taɓa juya maka baya ba. Saboda duk abin da ka kake so nima ina so, sannan ina son ka tara zuru'a kaima, amman abu ɗaya na ke so, don Allah kar ka yi hakuri ka ji a ranka saboda ban cike maka wani gurbi ba, mun kusa cika adadin shekaru sha biyar da auran mu, har ga Allah ban sa a raina zamu dauwama mu kaɗai ba, amman ina fatan lokacin da za ka yi auran ka wadatamu ka wadata kanka kada ka ɗauko aure ba tare da ka shirya ma hakan ba ka ji ko Yallabai na? "Na ji."   Haka kawai ya ce, na san halin kayana sai na fara shafa fuskarsa zuwa gemunsa ina faɗin" Ka yi fushi da ni ne? Hannuna ya riƙe kafin ya ce"Ko ɗaya. Na ji maganarki amman ina so ki sani ko mata nawa zan aura a bayanki ne, kin zama Turken gidana ke ce tsanin duk matakin da na taka arayuwata. Ki bar ni da maganar auren nan."   "Mu kwanta mu yi barci"   Haka ya faɗa ganin ina shirin yin magana, dare ya yi domin ɗaya ma ta gota. Lafewa na yi saman kirjinsa shima haka tun muna jin bugun zuciyar juna, har barci ya kwashe mu gabaɗaya.   Sanin halin da na ke ciki ya sa Yusuf bai ma tashe ni ba, ko da na tashi har su Jidda sun tafi makaranta. Yusuf ya yi musu abin karyawa da na lunch box, sannan muma ya dafa mana Tea ya soya mana ƙwai, ina ta shi ya ta sani tiolet ya ce na yi wanka ko da na fito ya zubomin tea a mug ya ce na sha sannan shima ya shiga wanka,  ban yi mamakin Yusuf ba sanin halin shi, ba shi da ƙiyuwar aiki, ya kuma iya komai yanzu ne ma aiki ya yi masa yawa amman zamanin farko farkon auran mu ai na mori Yusuf sosai. Shi ya yi zaman Bording School, shi ya sa aiki ba ya gagaran shi na tuna haihuwan Jidda na farko a gida na haihu kafin Gwaggo ta zo har ya gama wanke duka kayan jinin nan, haka zan tafi makaranta ban gyara gida ba sai dai na dawo na ga ya gyara gidan ya yi mana abinci, lokacin nan har makaranta ya ke rakani ya ɗaukar min Jidda,  kafin ya samu aikin nan na shi ya kankama mun gina wata rayuwa ne mai wuyar mantawa.   Har ya bar gidan nan bai barni na ɗauki ko kofi ba. Sai da na raka shi ya tafi sannan na je na wanke kayana na jiya  da na ɓata na fita haraba na shanya, na ɗaga waya na kira wayar Saude na ce yau ta zo da wuri, kasala na ke ji na kasa komai gashi har lokacin jinin bai tsaya ba amman dai ba ya zuba sosai. Da wuri Saude ta zo ta yi mini aikace aikace ta yi girki, sai wajen ukun rana na ba ta kuɗin mota ta koma gida, sukuku sukuku dai na yini Hauwa ma ta kira ni wai jiya ba ta san tafiya na ba, na ce ban jin daɗi ne, ta yi min sannu har ta na cewa ko zan leƙo can gidan Haliman? Na ce gaskiya a'a saboda ba na jin ƙarfin jikina ta yi min sannu sannan muka yi sallama. Ni fa ko lafiyata ƙalau ba zan koma ba ko Rahila da ta haihu sau ɗaya na je sai ana gobe suna da ranar suna na koma.   Saboda yanayina tun ranar ban ƙara fita ba ina gida ina shirin tafiya Zariya. Na gama haɗa duka takardun gwaje gwajen da aka yi min a asibitocin kano da tests da sauransu waje ɗaya saboda kar na manta. Na ma kira Anty Khaleesat na faɗa mata ina nan zuwa, Yaya Hamzan dai na kira shi ban samu ba. Ranar asabar da yamma muka je gidanmu tare da Yara na sanar da Gwaggo tafiyata Zariya ta ce Allah ya sa a dace. Na jira har Alhajinmu ya dawo shima na faɗa masa. "Allah ya sa ki je a sa'a. Allah ya sa a samu abin da ake nema."   Na amsa masa da Amin Amin, mun daɗe a gidan sai wajen goman dare Yallaɓai ya zo ya ɗauke mu, shima baya samun zama a Rano ya ke yini, saboda ya samu kwangilan gina wannan gidan biredin, gabaɗaya ya kwashe kuɗin hannunsa ya zura a ciki. Sai da muka dawo gida mun yi shirin kwanciya na ji suna waya da Uncle Abba, na ji kuma ya na faɗin bashi da kuɗi.   Sai da suka gama waya, ina gaban madubi ina saka Humra, yau ni amarya ce domin jinin ya ɗauke min yau da safe,shi kuma ya na zaune gefen gado daga shi sai ƙaramin wando. "Wai an ya za ka samu rakani asibitin nan kuwa?   Na faɗa ina kallon bayansa ta cikin madubi, bai juyo ba na ji ya ce"Ina tunanin haka nima, saboda aikin nan kuma kin ga ana buƙata ta a wajen"     Sai da na gama fesa turaren na gyara gashina da na kasa kitso har yau, kuma na kasa wanke shi a gida na kuma kasa zuwa a sake wanke mini.   Gabansa na zagayo ina faɗin"In ba ka da lokaci ka bari gobe kawai na tafi, in na ga likitan zuwa jibi sai na dawo in sha Allahu."   Kallona ya yi kafin ya ijiye wayarsa a gefe, ya saka hannu ya jawo ni na zauna a saman cinyarsa ya zagaye hannayensa a kuguna muna kallon juna. "Kin tabbatar da ba matsala in kika tafi ke kaɗai?   Ina yar dariya na ce"Haba! Kamar wata yarinya? Ba matsala Allah tunda aiki ne ya hana ka rakani." Sai ya jinjina kai kafin ya ce"Ga lambar Dr Fadil Abba ya turamin ya ce sun yi mgana in kika je asibitin shi za ki fara nema."   Sai na gyaɗa masa kaina gudun mantuwa sai ya ce na ɗauko wayata na kwashe lambar, tashi na yi na ɗauko ya faɗamin na saka na yi saving ina so na yi masa maganar kuɗi amman kuma sai na fasa na san Yusuf game da lafiyata in dai yana da shi ba abin da ba zai yi min ba, ni ina da kudi a hannuna 40k, na so na siya ma Halima turmi atamfa da rigan yaro amman sai na ga Yusuf ba shi da kuɗi ya saka a wannan aikin sai na dakata, in har bai ba ni da yawa ba sai na ɗauka na ƙara dashi.   A daran mun raba dare muna farantama juna rai. Muna ƙamƙame juna, cikin shauƙi da kauna. "I miss you Sadiya ta." Mirmishi na yi ban yi magana ba. Shi ya ta shi ya fara yin wanka sannan ya tasheni nima na yi wankan Sannan muka dawo muka sake kwanciya sai asuba muka tashi, Saboda ina da tafiya a gaba na da wuri na tashi.   Lahadi ne yara suna gida, shima Yusuf din ya ce mini sai azahar zai tafi Rano. Ni na yi mana Breakfast muka karya gabaɗaya sannan na yi wanka na shirya Yallaɓai ya ce na tafi da wuri baya son na yi yammah a hanya.. Kaya kala biyu na haɗa a karamar akwatina Baby na ganin na haɗa kaya ta fara rigiman sai ta je, Babanta ne ya zauna ya na lallashinta.   Na kira wayar Saude ban samu ba sai na kira na Balaraba mamanta, na faɗa mata zan yi tafiya Saude ta zo da wuri ta gyara gida ta yi ma yara abinci sannan in ba damuwa ta kwana da su kafin na dawo duk da nasan Yallabai zai kula da su ga jidda amman gwara dai na barsu tare da Sauden tun da shi sai dare yake dawowa Balaraba ta yi min fatan dawowa lafiya tace Saude ta je islamiya in ta dawo za ta zo in sha Allahu.   Yallaɓai ya saka mini duka Report ɗina na asibitin da na ta zuwa a baya a cikin ƙaramar jakata ya turamin 30k a acct ɗina lokacin muna hanya shi da yara za su kaini  tasha misalin sha ɗaya na safe. "Na ga 30k Yallaɓaina. Ina godiya."   Duk na san kuɗin sun yi kaɗan amman ban iya masa ƙorafi ba, ba halina ba ne.   Ya na tuki su Jidda na bayan mota ya waiwaya yana kallona ina sanye da hijabi, na saka abaya da mayafi ya ce na cire na saka hijabi sai na sauya kaya zuwa atamfa doguwar riga. "Ki yi hakuri Sadiya ba kuɗi a hannuna in akwai kuɗi a hannunki ki cika duk abin da kika kashe ki rubuta, in an biya mu zan biya ki duka kudaɗenki in sha Allahu." "To."   Kawai na ce masa, domin na saba jin in aka biyamu zan biyaki duka kuɗinki kuma an sha biyan shi ɗin amman sai ya manta da ni in na yi mgana sai ya ce kuɗin sun ƙare na yi hakuri a gaba zai biyani. Ba su bar tasha ba sai da motar mu ta tashi, sit ɗin mutum biyu Yallaɓai ya biya min kada na takura, sannan ya biya kuɗin mota muka rumgume juna ni da shi, yaran ma haka suna ɗaga min hannu ina ɗaga musu motar mu ta bar tashan, sai bayam mun tashi ina ga shima ya tuka motar zuwa gida.   Muna hanya ma na sake kiran Anty Khaleesat, tunda da safe ta kirani ta ce yaushe zan ta so,  na ce mata zuwa sha ɗaya na rana lokacin da na ce mata mun taso Yaya Hamza na gida har ya karɓi wayar ya na faɗin" Na ɗauka Yallaɓan na ki ne zai kawo ki?   Ina dariya na ce"Haka ya so, amman ya fara wani aiki kuma ka san ana bukatarsa sai na ce kawai ya yi zamansa ni na je na dawo"   Sai ya ce ai shikenan Allah ya kawo mu lafiiya. Na amsa musu da Amin sannan muka yi sallama.     Kafin mu sauka Zariya ban san sau nawa Yallaɓai ya kirani ba, na sauka ma a kwangila Zariya ya sake kirana na ce yanzu zan samu Adaidaita zuwa anguwan da Gidan Yaya Hamza ya ke. Gra kusa da bankin Gt Bank in da yake aiki. ****   Ina zaune a falon gidan Yaya Hamza rashe rashe ina cin abinci shinkafa da miyar Naman rago da Anty Khalesat ta yi min, ita ta na zaune a saman kujera ta ba ma Amna nono muna hira sai ga kiran wayata da ke saman kujera a cikin jakata tun da na iso na watsar da su saman kujera ban bi ta kai ba. Na iske Yaya Hamza a gida amman ban daɗe da zuwa ba ya fita ya ce wani abokin aikinsa mahaifinshi ya rasu za su je Ta'aziyya. Khaleesat ta fi kusa da jakar ita ta matsa ta ɗauko jakar ta, bude ta ɗauko wayar. "Waye? " Wata wai Sameena Tafida Rano." Mirmishi na saki kafin na ce Allah Sarki  da hannuna na hagu na miƙa hannu na karɓi wayar. "Wace ce? Ƙanwar Yallaɓai ce? Sai na girgiza mata kai, kafin na ce"E, a'a. Ɗiyar marigayi Tafidan Rano ce."   Ɗaga kiran na yi da fara'arta kamar yadda muka saba mace ƙwara ɗaya da muke mutumci sosai daga gidan Marigayi Alhaji Yusuf Tafidan rano, duk cikin su da ita kaɗai na saba kuma na ke zumunci ko Gimbiya  da muke da lambar juna ba ma waya iyaka ta dai in mun haɗu a gidan Nene ko Rano gaisuwan fatar baki ce. "Matar Baba." Haka ta faɗa daga bangarenta ina dariya na amsa mata mu ka gaisa da tambayan yara. Da ta ce min ta zo sunan Halima na gobe ba ta ganni ba an ce ina Zaria. Daman na san za ta zo tunda Halimar ƙawar ta ce.   "E. wallahi na zo gidan Yayana zan kwana. Gobe ina da ganin likita a asibitin Shika in sha Allahu."   "Lafiya kuwa? Ko ba lafiya ne? Da sauri na ce"Lafiya ƙalau zan dai ga likita ne kawai. Kin  shigo garin kenan? Sai ta amsa min ina ma jin hayaniya, daga karshe ta ce yaushe zan dawo na ce mata gobe in sha Allahu sai ta ce za mu haɗu ita sai jibi za ta koma Rano. Sai da muka yi sallama na ijiye wayar a gefena.   "Ban ga ne wata Sameena ba. " "Da wuya ki santa. Rahila ce ta san ta, ɗiyar wannan aminin mahaifin su Yallaɓai? Wanda ya rike tafidan rano lokacin ya na raye, amman bayan ya rasu an ɗora ƙaninsa, ita wannan da muka yi wayar autan su ce Sameena, kin ga kamar ƙanwa take a wajen su Yallaɓai." "Oh na gane su, lokacin haihuwan Baby na ga duk sun zo na ji ana cewa iyalan gidan marigayi Tafida ne." Ina gyaɗa kai na ce" Su fa, ai Yallaɓai na ya zauna gidan sosai tun yana matashi, kuma uwargidan Marigayi ɗin Hajiyar Tafida ƙawar Nene ce tare suka yi yarinta ƙawaye ne sosai. Yadda Yallabai ya faɗa min a bikin Nene marigayi Tafida ya ga Hajiyar ya ce yana so har ta kai su ga aure suka tara zuru'a. " "Allah Sarki.." In ji Khaleesat, ni kuma ina cin abinci na ce" To ita wannan da muka yi waya ɗiyar Amaryansa  ce, Hajiya Kaltume."   Ita dai Khaleesat da ba wani sanin su ta yi ba sai dai ta bi ni da Allah Sarki kawai. Sai da na ci na koshi sannan na shiga ɗakin da aka sauke ni na yi alwala na yi sallar azahar da la'asar sannan na kira Yallaɓai bai ɗauka ba sai na kira Saude ta ba ni su Jidda muka yi mgana.   Daga nan sai na kira Dr Fadil, shima bai ɗauka ba sai na ƙyaleshi, ina duba wayar sai na ga ashe ma Hauwa ta kirani sai na kirata daga baya.   Daman na san za ta ce ba ta ganni gidan Halima ba na ce mata ina Zariya ba da ni za a ci wannan sunan ba, sai ta yi min fatan dacewa muna ma waya Dr Fadil na kirana sai na katse nata na ɗaiuki nashi. Mun gaisa ko da na faɗa masa sunana sai ya ce ai ya gane ni Abba ya tura masa lambata. Na faɗa maaa na shigo Zariya ina gidan Yayana sai ya ce gobe da safe ƙarfe goma zai shigo asibitin na tabbatar da na shigo a wannan lokacin sai na kira shi, da haka muka yi sallama.   Ba gaji saboda zaman mota, gado na haye ina jin kamar ba zan iya tashi ba. Khaleesat ta leƙo ni ta ganni kwance sai ta ce na huta kawai itama tana ciki tana gyara kaya ne.   Gidan Yaya Hamza flat ne daidai na zaman mutum ɗaya haya suke yi amman yana gina nashi. Yayansu biyu duka mata, tana goyon na biyun mai sunan Mama Ruƙayya Amna(Tasleem) ta na gidansu Jawahir ɗin ta je hutu.   Har na fara barci na ji kiran wayata na ɗauka cikin muryan gajiya, da barci. Jin na isa lafiya ya sa Yallaɓai ya ce na huta sai mun yi magana anjuma.   Ban tashi ba sai gabda mangariba, na yi wanka na saka riga da wando, ni daman kaya irin atamfa damuna suke yi, plazo na saka da T.shirt.   Daman na ɗauro alwala ina shiryawa na tada sallar mangariba, tun ina sallar ake kiran wayata sai da na sallame na ga wai Ma'u ne. Tsaki na ja na ƙi ɗauka kira biyu sannan ta ƙyaleni, amman da na kunna data sai na ga saƙon ta. "Ban gan ki a gidan Halima ba. Ina fatan lafiya ko? Daƙyar na iya ce mata lafiya lau, daga haka ban ƙara ba sanin da na yi gulma ce ai na san ta ji labarin na je Zariya, tunda Yallaɓai ya ce ya faɗa ma Anty Bahijja ba zan je sunan Halima ba zan je Zariya ganin likita kuma ina da tabbacin Ma'u ta ji labari. Ni da kaina na kira Rahila a waya muka sha hira  na ce mata ga ni a gidan Yaya Hamza. " Kai Sadiya, ko ki jirani mu zo tare in na yi arba'in" Kamar tana ganina na harareta kafin na ce"A'a sai dai na tsaya ki yi hamsin" Sai ta kwashe da dariya, zolayata take yi tasan ai abin da ya kawo ni. "In sha Allahu Sadiya za ki ƙara haihuwa da ikon Allah."   Kamar zan yi kuka na ce"To Amin. Amman kin ji daɗin ki Rahila. Da ba ki yi planning ba, ba ki haɗu da side effect ba gashi nan kina ta haihuwanki yayanki huɗu bayan ma kin yi ɓari sau ɗaya."   Rahila ta yi saurin cewa"Ki daina cewa haka ko ba wannan dalilin in Allah ya kaddaro fa, ki dai kawai ki ce ya zama sanadi, mu yi fatan kuma ya zo karshe." Ganin na damu ta yi ta lallashina sannan muka yi sallama. Ina nan zaune har aka kira isha'i na tashi na yi salla. Ban fito daga ɗakin ba sai da na ji muryan Yaya Hamza sannan na fita muka gaisa. "Ke lafiya na gan ki wani iri?   Sai na ce masa bakomai, Khalesart ta ce"Bai wuce damuwanta na haihuwan nan"   Ya na zaune gefen matarsa ya ce"Mi ye to abin damuwa? Ba ga su Jidda ba, ke ba na son damuwan nan ba wani abu in ma ba ki ƙara haihuwa ba ko? Shuru na yi masa ban yi magana ba, shi daman ɗan kai tsaye ne.   Kifin hausa ya siyo mana mai daɗi, sannan ga shi akwai wuta ana kwana chasa'in sai na zauna afalon Yaya Hamza bayan ya gama cin kifinsa ciki ya shiga ya bar mu muna kallo muna hira. Muma ɗina wajen goma muka yi sallama na shige ciki na yi shirin kwanciya sai da na kwanta sai na ɗau waya na kira Yallaɓai ya ce min yanzu ya shiga gida yara duk sun yi barci. "Har Sauden??. Sai ya amsa min da e, hira muka yi kaɗan tun da shima ya gaji na dai sanar dashi yadda muka yi da Dr Fadil. Ya ce na kwanta da wuri saboda na tashi akan lokaci, mun yi sallama tare da kalaman soyayya sannan na yi addu'ar barci na kwanta. *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU #1k NE KACAL, AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:JamilaUmarJanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. *🅿️7* Tun da na kwanta ban farka ba sai da na ji kiran sallar asuba daga can masallacin da ke baya kaɗan da gidan Yaya Hamza.   Na tashi da ƙarfin jiki, sannan ina jin wani karsashi a tare da ni, ina idar da sallar asuba ina zaune ina azkar sai ga Khaleesat ta leƙo ni, bayan mun gaida juna da kwana ina tambayan Amna ta ce min ba ta tashi ba, ita ta saka min ruwan zafi a kittle ya na tafasa ta ce na juye na yi wanka.   "Yaya Hamza fa? Sai ta ce min kar in damu dashi, akwai wani Kittle ɗin a Tiolet ɗin cikin ɗakin barcin su zai yi amfani dashi.   Ko kafin ƙarfe bakwai na safe na yi wanka na shirya, tunda goma Dr Fadil ya ce za mu haɗu a cikin asibitin akwai sauran lokaci, sai na zauna gefen gado na jawo wayata da niyyar in kira Yallaɓai.   Sai ma na ga ya kirani har sau biyu, ƙila lokacin ina wanka ne sai na kira shi, bai ɗauka ba sai da ta gama ringing ta katse sannan ya biyo bayan kiran nawa. "Ina kwana Yallaɓan Sadiya." Cikin yanayin maganarsa ya ce"Yallaɓan na ki na nan ya yi kewarki? Kin tashi lafiya Sadiya ta?   Na amsa masa da lafiya lau, ina tambayan su jidda, cikin ɗan sauya murya ya ce"Kya bari mu gama gaisawa. Amman hankalin ki na wajen yara, suna lafiya suma Saude na taimaƙa musu da abin karyawa sun shirya lokaci kaɗan zan kai su makaranta in sha Allahu."   Sai da na yi dariya kafin na ce"Afuwan Yallaɓai na. I miss u jiya fa dakyar na yi barci saboda rashin ka." Na ƙarishe faɗa ina masa shagwaɓa dariya ya yi kafin ya ce"Jiya na kira wata, tana ta mgana cikin magagi kamar dai Sadiya ta ko?   Baki na rufe ina ƴar dariya shima yana ta ya ni.   "Allah da gaske na yi kewarka, duk in da na juya domin in laluɓoka sai na ji wayam."   Kai ya kaɗa kamar ina ganinsa amman saboda ni na san Yallaɓan nawa shi ya sa na fahimci abin da ya yi ɗin kafin ya yi maganar. "Uhm ko dai kina kewar jikina, ba ki samu kin buga tekwondon ɗin dare ba ko? Kin ta buga kafa shuru ko?   Dariya na kwashe masa da shi ina faɗin"Laa Tafida kai ko? Shima dariyan ya yi, sannan muka cigaba da hira ya na ce mini na tabbatar da na fita da wuri, kar kuma na makara a samu matsala, sai na faɗa masa ai har na yi wanka ma ƙaryawa kawai zan yi na wuce in sha Allahu.   Kafin mu gama waya sai da ya ba ma su Jidda wayar muka gaisa. Jidda faɗi ta ke yi" Umma gidan duk ba daɗi da baki nan? Ina dariya na ce"To ga babanku nan? Ko duk da haka gidan ba daɗi?   Sai ta yi dariya ina jin sa daga gefe yana faɗin" Wato mamanku ce, Turken gida in ba ta nan ku ce gidan ba daɗi, ni kuma in ba na nan gidan da daɗi ko?   Jidda ta ce"Abba kai ma in ba ka nan gidan ba daɗi." Uhm kawai ya ce ya karɓe wayarsa ya na faɗin" Ku ba ni wayata."   Baby ce ta saka rigiman ita ba ta yi magana ba dole ya ba ta muka gaisa ita har da neman yin min kuka. "Umma yaushe za ki dawo? Nima ina so ki je da ni." Saboda ina son na tsokani Yallaɓai sai na ce"Ga Babanku nan, sai na yi sati zan dawo" kawai sai ta fashe da kuka ta na faɗin" Umma ni na fi son ki dawo. Abba fa ba ya zama a gida." Ina ta dariya san da na ji yana faɗin"Baby ki ji tsoron Allah, yaushe ne ba na zama a gidan? Wayarsa ya karɓe ya na faɗin"Yau ba zan siya miki ice. Cream ba, ki bari in Umman ta ki ta dawo sai ta siya miki."   Ni diramansu ke ba ni dariya, domin ina jin sanda ta bishi ta na faɗin Abba ka yi hakuri to Umma kar ta dawo zamu zauna da kai  ya ce daga baya kenan.   Sai da ya koma ɗaki a cunkushe ya ce"Ki dawo mai ƴa'ƴa kina ji sun zaɓe ki sama da ni." Ya faɗa har ya na wani ƙwafa, ina danne dariya na ce"Sorry Yallaɓai Uwa uwa ce fa."   "Uba ma ai Uba ne ko?   Ganin in na yi dariya zan ƙara kunna sa sai na ƙyaleshi, ba mu jima muna waya ba ya ce bari ya yi wanka ya fita kai su makaranta zai wuce cikin gari akwai in da aka kira shi zai ga waje saboda zane, bayan mun yi sallama ina zaune ina mirmishi, ina son Iyalaina, na sha wahala kafin na gina gidana, yanzu kawai sai wata rana wata ta shigo a matsayin matar Yallaɓai ko? Gabana ya faɗi, da sauri na kauda tunanin haka a raina saboda ban isa na hana shi aure ba in ya yi niyya, amman ina fargaban yadda wannan ginin da na yi shekaru ina gina shi, shin zai iya ɗorewa a haka? Ko zai rushe gabaɗaya? Yusuf mutum ne na jama'a mai harkoki da yawa, shi ya sa ya na yawan samun ayyuka,  a da sai na yi ta kallon ya na da son mutane da yawa, kowa na shi ne sai daga baya na fahimci sanin mutane ya na yi masa amfani saboda duk in da ake neman aiki irin nashi ya na zaune za a yi masa waya su ce wane ne ya ba mu lambarka muna son aiki kaza, tun a sanin da na yi masa mutun ne mai zafin nema da fafutuka.   Ina cikin wannan tunanin Khaleesat ta leko ta ce na zo mu yi breakfast, daman na riga da na shirya cikin wata doguwar rigar atamfata wata mai ja haka.   A dining muka haɗu gabaɗaya har da Yaya Hamza shima cikin suit ɗin sa na zuwa aiki. "Ina kwana Yaya Hamza" "Mun tashi lafiya Sadiya?   Na amsa masa da lafiya lau sannan na zauna muka fara karyawa, Tea ne da soyayyan biredi sai doya da miya. Tea ɗin kawai na sha da biredin. Yaya Hamza ya riga mu tashi 5k ya ijiye min a gabana ya na faɗin"Ki yi transport. Ina tunanin ko Khalee ta raka ki ne? Da sauri na ce"Laa ba komai fa zan iya zuwa ni kaɗai. Ni fa ba yarinya ba ce Yaya Hamza."   Kai ya kaɗa kafin ya ce"Ke yarinya ce mana. Saurin aure kika yi, ki daina ganin kanki a babba domin kin haifi Jidda ta yi tsawon kafa." Ni dariya Khaleesat ma dariya, shi dai ko a jikinsa ya ce mini ya wuce wajen aiki in ina bukatar wani abu zan iya kirashi, na yi masa godiya da fatan Allah ya ba da sa'a.   Matarsa ta tafi rakashi ni kuma na zauna na ƙarisa karyawa, bayan na gama na kwashi kuɗin da ya ba ni na koma ciki na kuskure baki, sannan na zo na saka mayafina takwas ta gota da kaɗan da ɗan nisa gwara na fita da wuri saboda na isa a kan lokaci.   Mayafi na ja na saka, sai na haɗa da bakar jaka da takalmi mai saukaƙƙen tudu. Atm ɗina daman yana tare da ni da duka takarduna. Sai na saka 5k ɗin da Yaya Hamza ya ba ni a cikin jaka, ina shirin fitowa Khaleesat ta sanyo kanta ɗakin sai muka haɗu a kofar ɗakin..   "Har kin shirya wai?   Ina nuna mata jakata na ce" Ga shi ma kin gani. Gwara na tafi da wuri tun da kin san da ɗan tafiya."   "Haka ne. Amman a ina kika san asibitin? Mun fita falo tare da ita lokaci ɗaya ina faɗin" Kin manta can Tasleem ta kwanta lokacin da kika haife ta?   "Oh! Kin ga har na manta kuwa."   Ta rakani har ƙofar gida ta na jaddadamin na samu Adaidaita zuwa pizzet daga nan sai na hau na Shika ɗin. Sai na amsa mata da toh, ta in ban gane wani abu ba na kira ta, ina dariya nan ma na ce mata in sha Allahu.   Haka ko aka yi na samu Adaidaita zuwa pizzet, daga can akwai ƴan sahun da suke yi lodin samaru har Shika ita na hau, ta cika da wuri, mu uku ma duk shikan za mu je, sauran ne za su tsaya a samaru.   Muna hanya Yallaɓai ya sake kirana na ce masa ina hanya in mun isa zan kira shi. Na sauka Main get na asibitin Shika na duba agogon da ke ɗaure a tsitsiyan hannuna tara da mintina sha biyar, bayan na sallami mai adaidaita na shiga ta babban get ɗin.   Ban kira Yallaɓai ba sai da na kira lambar Dr Fadil kamar yadda muka yi alkwari sai dai bai ɗaga kiran ba, sai na wuce ta can babban falon da ke kusa da main get, na samu waje na zauna asibitin ta cika da zirga zirgan mutane ballatana yau ɗin monday ne, ga marasa lafiya nan birjit ana ciwo Allah dai ya bamu lafiya.   Na sake kiran Yallaɓai na ce masa na sauka ina cikin asibitin amman na kira Dr Fadil bai ɗauka ba, sai ya ce na ƙara kiran shi tun da ma ya ga da sauran lokaci ƙila bai shigo asibitin ba ne.   Mun gama waya da Yallabai kenan Uncle Abba shima ya kirani bayan mun gaisa ya tambayeni ko ina cikin asibitin ne? Sai na amsa masa sannan na gaya masa na kira wayar shi ta shiga amman bai ɗauka ba sai ya ce bari ya kira shi.   Na ɗan yi zaman sama da mintina ashirin, data na buɗe ina duba istergram na wata Hamida makeup , ina following ɗin ta sosai saboda ta iya kwalliya so na ke yi ma na shiga class ɗin ta za ta fara farkon wata gaba anan kano ne na wata ɗaya akan kwalliya, na rage Volume ina ta kallon Videos ɗin kwalliya daman ni duk sune na ke following a wayata,  ina cikin duba dube na sai ga kiran Dr Fadil da sauri na ɗaga kiran gaisawa muka yi sai ya ce yana hanya yanzu zai ƙariso ina ina ne? Sai na gaya masa sai ya ce na jira sa ga shi nan zuwa.   Bayan nan kuma na sake wani zama na tsawon mintina goma sha biyar sai ga kiran shi Again ina ɗauka ya ce" Ga ni a babban falon, ko za ki iya miƙewa ko zan gane ki? Ina jin haka na mike na juya daman a kujerun baya na zauna duk an ma cika na gaba gaba, waige waige nake yi saboda akwai mutane sosai kuma na ga masu waya sama da mutane goma.   "Wani kalan kaya ki ka saka?   Sai na amsa da ina sanye da jan mayafi, sai ya ce kawai ya ganni daga nan ya kashe wayarsa, har ga Allah ni ban gan shi ba sai da na ga wani baki dogo sanye da suit da rigan likitoci a hannunsa tare da briefcase, fuskarsa sanye da wani siririn gilashin, ganin ya na min mirmishi ya sa na fahimci wannan ne Dr Fadil.   "Sadiya Right?   Haka ya faɗa bayan ya tsaya a gabana da sauri na amsa masa sai ya yi gaba yana faɗin"Biyo ni, sunana Dr Fadil. Ni ne Abdulmu'iz ya ce zan taimaka miki.'"   Ina bin sa a baya na ce"Ina kwana" Ya na yar dariya ya ce ai mun gaisa a waya, sai ya dan tsaya har na karoso mu ka jera yana min bayani zan siya domin na buɗe fayel, agogon hannunsa ya duba kafin ya ce"Da fari na so ki ga Dr Nayama ne amman ta ɗauki Annual leave ɗinta last week amman na samo miki appoitment da Dr Fatima Tasiu, ba ki da matsala na ce ke ƙanwata ce saboda haka mu je a siya katin sai na raka ki can in da za ki gan ta."   Muna tafe ina yi masa godiya, Ban sha wahala ba muna zuwa wajen biyan kudin kati bai ma karɓi kuɗina ba ya siya mini sannan muka je ya nuna recip ya karɓo mini kati aka buɗe min fayel, kuma ya ce a bashi Fayel ɗin da ƙaramin katin a hannunsa shi zai kai ma Dr Fatima, daga nan mu ka fara tafiya zuwa bangaren Gyea ɗin ni kuma ina tambayansa nawa ne aka kashe da niyyar na bashi kuɗin sa?   Sai ya kalleni ya na dariya kafin ya ce"Haba, ke ba ƙanwar Abdulmu'iz ba ne? Kallonsa na yi saboda ina so na tuna da sunan da ya ambata. Sai na tuna da Uncle Abba ya ke mgana. Sai na rausayar da kai kafin na ce" E. Amman ina auran yaron Yayarsa ne. Sannan aminaine tare suka tashi da mijina."   Sai ya ɗan juyo yana kallona kafin ya ce"Oh. Nima Babana ɗan Rano ne, amman kaduna muka tashi mun haɗu da Abdulmu'iz a BUK ne kafin na samu scholarship zuwa Singpore."     Sai na jinjina kai alamun gamsuwa, muna tafe yana gaiswa da mutane sannan jefi jefi ana kiransa a waya, mun isa shashen Gyea ɗin akwai likitoci da mutane suna ta layi, amman da ya tambayi Dr Fatima sai a ka ce ba ta riga ta iso ba, sai ya ce na zauna na jirata bayan ya ba ni fayel dina ya ce na riƙe zai mata waya ya faɗa mata in ta iso ni za ta fara gani, na yi ta masa godiya ya ce in akwai wata matsala na kira shi, shima zai wuce bangarensa ne akwai patient na jiran sa.   Aka ce mai nema baya fushi, mun yi zama sama da awa ɗaya, wasu ana ta kiran sunan su suna shiga wasu offices ɗin. Ni dai ina zaune mun yi magana da Yallabai na faɗa masa yadda ake ciki gani dai ina jiranta, ban gaji saboda na saba sama da shekaru bakwai ina zuwa ganin likita zaman bai wani dame ni ba  tun da ga waya a hannuna ina ta latsawa.   Hankalina ya tafi kan waya har ga Allah ban san ta ina likitan nan ta zo ta wuce ba, ni dai kawai na ga wata mace da fararen kaya ta fito tana kiran sunana. "Wacece Sadiya anan? Ina shirin na ce ni ce, sai na ga wajen mutane uku sun ɗaga hannu, sai ta tsaya tana kallonsu kafin ta yi tsam sai kuma ta ce" Wacce Dr Fadil ya kawo?   Sai na yi saurin miƙewa ina faɗin" Yes Ma.". Sai ta kalleni akwai fayels a hannunta, kafin ta ce na biyo ta, da sauri na ɗauki jakata da Fayel ɗina na bi bayanta har zuwa wani office dake gefenta tana gaba ina bin ta a baya.   Likitar na zaune a saman kujeranta, kanta na kasa tana rubuce rubuce akan wata takarda. Wacce ta shigo dani ta bani izinin zama sannan ta fice ba tare da ta yi magana ba, zama na yi a kan kujera na zaman marasa lafiya, Office ɗan daidai akwai wani kato a ciki sai wata kofa ina tunanin kamar Tiolet ne.   "Fayel na ki."   Haka kawai ta ce mini har lokacin ba ta ɗago ba, sai na miƙa ma ta ta saka hannu ta karɓa lokaci ɗaya tana gyara zaman gilashin da ke idanuwanta.   Ta duba sannan ta fara rubutu a jikin Fayel ɗin kafin ta ce"Kin zo da Report ɗin ki na baya? Kaina na gyaɗa kafin na yi saurin buɗe jakata na ɗauko su na tura mata gabanta ta ɗauka ta fara dubawa ɗaya bayan ɗaya sama da mintina goma. "HalimatusSadiya Sulaiman Yashe" Na amsa mata da Yes Mah."   "Ke ƴar Yashe ce?   Sai na amsa da eh kafin na ce"Alhajinmu ɗan can ne." Na faɗa ina kallonta sai a lokacin ta ɗago na ganta da kyau fara ce tar, a shekaru sai dai mu zo tsara ko za ta girmeni da kaɗan ne, tana sanye da rigar likitoci ta yane kanta da mayafi baki sai siririn gilashin da ke saman fuskarta.   Sai na ji gabaɗaya ta burgeni. Har na shagala da kallonta. "Haihuwanki nawa kafin ki yi planning? "Ɗaya." Da hausa take yi mini magana nima ina maida mata da hausa, kanta na ƙasa tana ta rubuce rubuce. "Na how many month kika yi alluran? "Five years" "Amma na 6 months na riƙa yi" Sai ta ɗago ta kalleni kafin ta maida kanta ta cigaba da rubutu a saman fayel ɗina. "Bayan haka, kin sake haihuwa? Na amsa da E. Sai ta ce When, sai na ce bayan first born ɗina ta shekara tara. "Wani symptoms ki ka samu kafin ki sami ciki da kuma bayan kin samu? "Na samu matsalan zubar jini, sannan ga juwwa da ciwom mara, daga baya na fara ramewa sannan bayan nan na daɗe ban samu ciki ba sai bayan shekara tara ga rikicewar al'adata." "Bayan kin samu cikin fa?   "Bayan na samu ciki na wahala, domin har lokacin ban daina zubar jini, sai da na je asibiti aka ɗora a kan mgani. Na sha wahala da ban ma iya haihuwa da kaina ba sai da aka yi min C.S." "Na gani a rubuce an ɗora ki kan magani domin tsaida jinin ko? Sai na gyaɗa mata kai kafin na ce"E. Kuma in na sha jinin na tsayawa gaskiya." Sai ta jinjina min kai, ta ɗan daɗe tana rubutu kafin ta ɗago ta na kiran sunana. "Miss Sadiya." Na amsa mata da Mah. "Da kika fara zuwa ganin likita bayan kin fuskanci canje canje a jikin ki, an faɗa miki kin samu Secondary Infertility ne?   Sai na gyaɗa kaina, ba ta damu ba ta cigaba da faɗin" Daman in kuka zo za ku yi planining, ana yi muku bayanin cewa akwai disadventage da advantage na yin shi ko? Kuma sai da amincewar miji da mata ko? Sai na amsa mata da Yes. Sai ta ƙara kiran sunana. "Miss Sadiya." Sai na amsa mata. "Me ya sa kika zaɓi ki zo wannan asibitin? Na ga a fayel ɗinki ya nuna daga kano kike? Me ya sa ba ki tsaya a asibitin Aminu kano ba? Kai tsaye na ce"E. Daman zaɓi biyu a ka bani ko can ɗin ko nan ɗin. Na ji hankalina ya fi kwanciya da nan ɗin ne."   Sai ta jinjina kai kafin ta ɗago ta na kallona lokaci ɗaya kafin ta ce" Za ki iya jin haka. Amman a matsayina ta likita zan iya ba ki wata ƴar shawara? Sai na gyaɗa mata kai. Ba ta damu ba ta cigaba da faɗin" Zai zame miki wahala a ce duk wata ki rika tasowa daga kano zuwa Zariya ganin likita. Kar mu fara saka maganar kashe kuɗe da walwalahu mu fara duba yanayin tsaron ƙasarmu da ya ke ƙara tabarɓarewa."   Ba ta damu da na yi mgana ba ta sake kallona kafin ta ce" Zan yi transfer ɗin ki zuwa Aminu kano.  Zan haɗa ki da wata consultan Dr Aisha Bukar ita za ki cigaba da gani a kan matsalan ki. Karki damu duk ƙwarewarmu a nan suma acan akwai ƙwararru kuma duk ɗaya ne abin da za mu yi miki a nan a can ma shi ɗin za su yi miki."   Na yi shuru ina tunanin maganarta. Kuma gaskiya ts faɗa. Ban yi tunanin haka ba Yallaɓai kuma bai yi magana ba saboda ya ga nan ɗin na ke son zuwa. "Miss Sadiya ta amince na yi mata Transfer zuwa Aminu kano? Ajiyar zuciya na sauke kafin na ce"Shike nan." Mirmishi ta yi kafin ta ɗauki wayarta da ke kan Tebur ta danna. Zuwa can ta  saka ta a speaker ta ɗora saman tebur ɗin gabanta. Ita kuma sai ta cigaba da rubutu saman wata takardan da ta yaga daga wani littafi da ke gabanta. "Hello. Dr Fatima." Aka faɗa daga cikin wayar cikin harshen Turanci suka gaisa sannan ta ce"Dr Aisha zan yo miki transfer ɗin wata patient ta bangarenki ce gynea. A kano ta ke ta zo ganin likita anan asibitin saboda nisa na ga gwara ta koma tana ganinki a can." "Ohk.." "Zan tura miki bayanan ta in brief ta email ɗin ki. Yaushe za ki ba ta appoitment? "Mu bar shi next week. Gobe zan je semina lagos sai after 3days zan dawo. Mu bar shi coming monday sai ta zo ta same ni a asibiti in sha Allahu." "Thank You Dr. Aisha." "Always Welcome Dr. Fatima. Daga haka suka katse kiran, ni dai ina zaune bayan ta gama rubutun ta miƙa mini takardan da report ɗin na wancan asibitin sai da na karɓa sannan ta ce" Na yi mata mgana Consultan ce. Ranar monday za ki je Aminu kano ki ganta. Ki je mata da wannan takardan" Na rusunar da kai ina yi mata godiya. Jinjina kai ta kafin ta ce"Miss Sadiya mun fito daga Jiha ɗaya nima Granfa ɗina ɗan Yashe ne. Wacce na haɗa ki da ita za ki samu dukkan abin da kike nema daga gare ta. Zan ba ki lambarta ana gobe za ki shiga asibitin ki kira ta, itama zan tura mata lambar ki in sha Allahu matsala. " Sai na ji kamar ma na samu waraka daga matsalolina ina ta yi mata godiya. Ta karanto min lambarta na kwafe a waya na yi saving. Itama ta ce za ta tura mata lambata. Na fito daga office ɗin ina yi mata godiya.   "Thank You Doctor." "My pleasure." Ta faɗa tana mirmishi.   Sai da na fito haraban asibitin sannan na kira Dr. Fadil na faɗa masa Dr Fatima ta sallame ni. Ya tambayeni ko ba matsala na? Sai na sanar dashi ta yi mini Transfer zuwa Aminu kano ta haɗa ni da wata consultan. Shima ya nuna hakan ya yi dai dai saboda zirga zirga can zai fi sauƙi kuma duk ɗaya ne Shika da Aminu kano duk manyan asibitoci ne a afurka. sallama na yi masa tare godiya ya ce bakomai.   Na dawo gidan Yaya Hamza bayan sallar azahar ne, ina ma hanya ne azahar ɗin ta same ni. Itama kanta Khaleesat ɗin ta yi mamakin dawowata da wuri. Ina sauke jakar hannuna ina faɗin" Ke kam don ma na tsaya motar da na hau zuwa pizzet ba ta cika da wuri ba da tun ɗazu ina gida.."   Khaleesat ta sake riƙe baki kafin ta ce"Ikon Allah. " Sai da na kai zaune domin na ji kafafuwana sun gaji, sannan na cire mayafin jikina ina faɗin" Ke kam komai fa yanzu a Nigerian nan in kana da hanya ba ka ba baƙin ciki. Ƙarin abin ma likitan musulma ce kuma yar garin mu ce itama ƴar yashe, sosai ta karɓe ni, ni ta fara gani bayan ta iso da taimakon Dr Fadil." "Ai fa. Na ga alama. Fatan dai an da ce? Ba wata matsala ko?   Ta faɗa lokaci ɗaya ta na zama a gefena. Kora ma jawabin yadda mu ka yi na yi sannan na ƙarishe da faɗin" Ta ce a duka ɗaya ne. Ta yi Transfer ɗina zuwa Aminu kano ta haɗa ni da wata consultan ɗin" "Allah ya sa a dace. Maganarta gaskiya ce. Ko don zirga zirga. Nima kuma sai da na yi tunanin haka ban dai yi mgana ba ne." Na amsa mata ina hammar gajiya da yunwa kafin na ce" Ni idona ne ya rufe, gani na ke yi in na je nesa zan fi dacewa.". Dariya ta yi min kafin ta ce. "Ki yi sallah ga abinci nan na gama tun ɗazu" Da toh na amsa mata sai da na mike sannan na kwashi jakata da mayafina. Ita kuma sai ta juya ta nufi kitchen daman a ciki take lokacin da na shigo gidan. "Ina Amna? Ban ji motsinta ba ne? "Ta yi barci yanzu ba daɗewa ba."   Ina shiga ɗakin da na sauka ina faɗin" Wannan yarinyar kamar kasa? Sai barcin tsiya." Ina jin dariya Khaleesat. Nima dariyan na yi nifa tun da aka haifeta duk lokacin da zan ganta tana barci ne, jiya ma da na zo ana gama bata nono sai barci da safe har na fita tana barci, yanzu ma haka.   Tiolet na shiga na ɗauro alwala na zo na yi sallah. Na idar kenan ina addu'a na ji wayata a cikin jaka na ringing da sauri na miƙa hannu na ɗauko jakar daga saman gado kafin na fito da wayar ta tsinke. Ina dubawa sai na ga Yallaɓai ne kaina na dafe na manta shaf ban kira shi ba, ina dafe da kaina ya sake kirana ina ɗagawa na ce bayan na sassauta murya. "Yallaɓai na."   Daga can bangaren ya ce"Ba wani Yallaɓan ki, ina ta especting kiran ki shuru ni da na damu na kira. Ya ake ciki ne? Ina ta jin hayaniya a wajen da ya ke, ban ma samu zarafin mgana ba na ji ya na sake faɗin" Ga Kawun ki nan ya damu sai cewa ya ke akira ki a ji me ake ciki" Karya wuya na yi kamar ya na ganina kafin na ce"Ayya Afuwan Yallaɓai na. Ina shirin kiranka ne sai ga kiran ka" "Na ji. Yanzu ya ake ciki? Bayani na yi masa duk yadda muka yi da likitan na ƙarishe da faɗin" Ta ma haɗa ni da likitan rana ita yau in sha Allahu zan je na ganta a Aminu kano in sha Allahu. Kai tsaye ya ce" Nima na yi miki wannan tunanin amman ganin kin dage sai can ɗin shi ya sa na ƙyale ki? Ba dai wata matsala ko?na amsa masa da ba matsala. Mun cigaba da tattaunawa har na ce ya ce ma kawu ya yi ma Dr Fadil Godiya ya yi min ƙokari. "Injiniya muna buƙatar ka anan wajen fa" Na ji ana faɗa daga cikin wayar. "Yau ma kana Rano ne? Sai ya amsa min da E. Sallama muka yi tunda ana ta aiki ne, muka rabu akan sai anjuma in mun sake yin waya. ina wayar ma Khaleesat ta yi ta leƙowa, na san maganar abinci ne, ina sauke wayar nan saman gado na zare hijabin jikina na fita falo. Ta na zaune akan kujeran Dinning ta na jirana tare muka ci abinci doya da miya muna ci muna hira bayan mun gama muka dawo falo, ta kunna kallo amman rabin kallon duk hirar duniya ce muke yi da ita.   "Ni fa lamarin ki ya bani tsoro. Kin san Allah ina son nima na yi tsarin iyali na huta ko na shekara uku ne."   Ina ƴar dariya na ce" Zan faɗa in dai magana ta zo akan family planning ba na sauya magana ta. Ba tsarin iyali ne ba a so ba, ba kuma cewa na yi bashi da amfani ba, ammam ki sani bayan amfaninahi akwai rashin amfaninshi, ya na da kyau a yi ɗin tun da malamai ma suna faɗin a yi amman ba zan ba ma kowacce mace shawaran ta yi tsarin iyali ba ta haihu kamar biyar ba, saboda tarin ƙalubalen da ke cikin haka, in kika haihu kamar sau biyar ko da ya ninka adadin shekarunsa sau uku ne ba za ki damu ki ji kina son ƙarin haihuwan ba, sannan wani matsawar dangin miji duk ba za ki fuskanta ba. Ko kafin a farga Ƙila Allah ya ƙara ba ki wata haihuwar shikenan amman a irin yadda na yi nawa, akwai hatsari ba zan goya miki bayan ki yi ba. Ki yi ta haihuwanki zuwa gaba sai ki yi domin ki huta amman in kin aminta da shawarata fa kenan."   Na ƙarishe faɗa ina kallon ta, sai na ga ta yi shuru kamar ta na nazari da sauri na ce" Ban fa hana ki ba. Ki yi in kina da ra'ayi amman ki sani ki shirya karɓan abin da nima na ke karɓa duk da bana yi miki fatan haka sannan kowacce  mace da yanayin yadda abin ya ke karɓanta da kuma illar da ya kan nuna a jikinta. Ba lalle abin da ya faru da ni ya faru da ke ba, watakila ke ki fuskanci ƙalubalen ta wanni fannin dabam. Amman shawaran da zan ba ki shi ne, ki bari ki ƙara haihuwa kamar sau biyu zuwa uku sai ki huta."   Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce"Shikenan bari na bari ko zuwa gaba. Shima fa Yayan na ki cewa ya yi bashi da matsala duk lokacin da na ji ina buƙata zai yi supporting ɗina."   Mirmishi na yi kafin na ce"To wai daman su Maza ina ruwan su? Zai ba ki goyon baya mana. In matsala ta faru yana da zaɓi zai iya ƙara aure ke kuma fa? Kin cutu har abada in kuma danginsa sun matsa ya ce ai tsarin iyali kika yi kamar yadda  Yallaɓai ya yi mini a wajen dangin sa. Da suka damu da rashin haihuwata bayan Jidda shi ya faɗa ma Anty Maimuna wai tsarin iyali na yi ya zo ya ba ni matsala ba shikenan ya gogamin baƙin fenti ba, da sun tashi gwaɓamin mgana sai su ce ai ba Allah ne ya tsaida min haihuwan ba ni na tsaida ma kaina. "   Khaleesat ta yi dariya kafin ta ce" Ke da Yallaɓan na ki kuma? Baki na tura kafin na ce" Yallaɓan fa nawa. Wani lokacin ya cika abin haushi ne." Dariya ta yi mini nima ina tayata. Nan muka lalace muna ta tattaunawa. Sai sallar la'asar muka tashi daga falo ita ta wuce ɗakinta ni kuma na nufi in da na sauka. Bayan na idar da sallah na kira Saude mu ka gaisa. "Saude ya gidan ne? Fata komai lafiya ko? Sai ta amsa mini da lafiya lau kafin ta ce"Anty yaushe za ki dawo? Kai tsaye na ce" Gobe in sha Allahu." Fatan dawowa lafiya ta yi mini ni kuma na ce zan ƙara kiranta in su Jidda sun dawo daga makaranta. Daga nan sai na kunna Data saƙonni na ta shigowa. Maganar Yaya Auwal na fara gani na yi saurin buɗewa. "Zan shigo wannan weekend ɗin fa."   Cikin jin daɗi na rubuta masa Allah ya kawo shi lafiya. "Kai da Laila da yara ne? Yana online amman sanin halin shi da sai ka yi saƙo sai ya ga dama zai buɗe sai na fita, ina duba sauran saƙonnin sunan MA'U da na gani ta yi mini magana ya sa na yi tsaki na wuce ta, na ga an yi mgana a group ɗin gidanmu ban shiga ba domin ban ga an yi tagging ɗina ba kenan mganar ba ta shafe ni ba. Amina ce ta yi min mgana da cewa ta kira waya ta ba ta samu ba na ce mata network ne.   Sai na fita na je bangaren Status ina ta dubawa. Rahilarmu na ga ta saka status har ina rawan jikin dubawa. Ya Muntari na gani ya na riƙe da jaririyar(Zainab Nihad) ba hoton ne ya ba ni dariya ba, sai rubutun da ta yi a ƙasa. "Hubby na. Abu Zainab I love u."   Dariyan da na saka har a sarari, na danna Viocenot ina ƙyaƙyata ma ta dariya kafin na ce"Rahila ma su Hubby, wai Ya Muntarin ne kuma ya koma Hubby? Daga Yaya Muktar ya koma Hubby." Bayan nan na sakin mata VN ɗin. Sannan na riƙa jere mata sticker na shaƙiyanci. A yammacin nan dai status ɗin Rahila ne ya nishaɗantar da ni. Ba ta online, abin mamaki shima Ya Muntarin na ga ya yi sreenshoot ya saka a jikin sunanta My Baby. Haka na ke ta dariya shima sai da na yi tagging ɗin shi. "Su Ya Muntari Hubby manyan ƙasa." Ya na online ya turo mini Emojin dariya kafin ya ce"Ke ko? Sadiya dai ta raina Yayan nan na ta ko? Emojin dariya na tura masa sai na jin kunya sannan na ce"Wace Sadiya ta raina Ya Muntari. Allah ya bar Ƙauna Hubbyn Rahila ta."   Ni kaɗai a ɗaki ina ta dariya ina tuna wani zamani a can baya har gobe ban manta lokacin da Ya Muntari ya zo gidanmu ba. Mama Allah ya jiƙan rai ta ce" Ya sunan ka ɗan samari." "Muntari. Muntari sunana Hajiya." Sai na ji wata dariya ta ƙara kamani har ina buga hannuna a saman cinyata, lokacin da Rahila suka fara soyayya da Ya Muntari ba wanda ya sani, wata rana kawai ya shigo gidan kowa na gaishe shi, da kuma sunan da muke kiran shi kenan  Ya Muntari. "Barka da dawowa Ya Muktar." "Yauwa Sannu Rahilatu." Sake baki na yi ganin yadda Rahila ta wani sunne kai tana dariya, shi ma ya na mata wani kallo. Ba zan manta ranar ba ina bakin famfo ina wanke wanke ita kuma tana bakin madafi ita da Ma'u suna gyaran wake.   Ga mamakin sunan da ta kira shi. Ga wani kallo da suke ma juna. Tun daga ranar fa Rahila, ta daina kiran shi Ya Muntari sai dai Ya Muktar har faɗa mun sha yi da ita, in na ce Ya Muntari. "Kai Sadiya. Ba fa Muntari sunan shi ba. Ba ki iya cewa Ya Muktar, muktar ne fa sunan kuke ɓata masa da sunan tsoffi wai Muntari."   In ta ce haka sai na balla mata harara sannan na ce"Ke kika san Muktar. To da bakin sa ma ya ce sunan shi Muntari ko Gwaggo?   A lokacin Rahila ta riƙa tura baki kenan ta na ƙunƙuni. Ta yi ƙokarin sauya sunan Muntari zuwa Muktar amman bai sauyu daga bakina ba, da gayya ma ma ke faɗa Ma'u dai da ya ke makira ce har wani ƙalƙala take yi wajen faɗin sunan. "Ya MUKTARR." Makircin Ma'u fa haifaffan ne, ta tsotsa a nono ne shi ya sa in ta buga acting ke yi mata kyau.   Haka Khaleesat ta zo ta same ni ina ta dariya. Domin mun yi dogon charting da Ya Muntari yana tamnbaya ta laifin me suka yi tun ranar suna Rahila ta ce ban dawo ba, na fa san Rahila ta faɗa masa dalili zai yi min wayau su na maza ne ni ko na ce ya tambayi matarsa ta san dalili.   "Ke da waye kike ta dariya haka? Ko Yallaɓan ne?   Ina mirmishi na ce"Wani Yallaɓan? Wai wannan Hubby na Rahila ne." Ina faɗa ina dariya Khaleesat ta kwashe da dariya kafin ta ce"Au kema kin gani? Nima yanzu na gani ina ta dariya a raina na ce Rahila manya ta Muntarin ta."   Miƙewa na yi daga kishigiɗen da na ke ina faɗin" Ta fa kashe wannan sunan. Muktar ko Hubby." Na faɗa ina kwaikwayon bakinta ni da Khaleesat har muna tafawa saboda dariya, Ita kuma faɗi ta ke yi" Ni ya na burgeni ba shi da damuwa. Ga barkwanci kuma ya na son Rahilatun nan ta bakin shi ba."   Jinjina kai na yi kafin na ce"Ai Muntari na ƙaunar Rahilatu." "Sadiya ba ki da dama, na shigar ma Rahila. A bar yankan mana Hubby ahto.'"   Ni dai ina ta dariya. Sai kuma mu ka cigaba da hiran Rahila da Ya Muntari muna cin dariya. Kukan Amna daga bedroom ɗinsu ya sa Khaleesat ta bar ɗakin da sauri ta fita ba daɗewa mijinta ya dawo sai ban ƙara ganinta ba sai dare wajen dinner. "Sadiya Ya ya? Fatan dai ba matsala ko? Yaya Hamza ke tambayata. Bayan mun haɗu a Dinining muna cin abinci. "Ba wata matsala. Yanzu dai ta yi min transfer zuwa Aminu kano ta haɗa ni da wata consultan." Da kai ya amsa kafin ya ce" Tunani mai kyau.'" Daga nan bai sake mgana ba. Shi ya fara tashi kafin ya goge bakin shi da Tissue sannan ya kalleni ya na faɗin" Yaushe za ki wuce? Ina kallonsa na ce" Gobe in sha Allahu" "Ba ki bari weekend mu shiga kanon tare" Kai na girgiza kafin na ce"Ya Hamza. Yara su kaɗai a gida Yallabai kuma ba ya zama in ya fita tun safe sai dare."   Ya na wucewa falo ya ce"Wasu yara? Yallaɓan dai amman Jidda yarinya ce? Shekaranta nawa? "13 in to 14 fa Ya Hamza. " "Ehem.."   Ya ce kawai alamun maganarsa ta farko dai itace Yallaɓai dai ina dariya khaeesat na faɗin" E, mana Yallaɓai dai take yi ma kewa kar ta ƙara kwana ta barshi shi kaɗai."   Mirmishi na yi kafin na rage murya ina faɗin"Da shi ɗin ma, mata ba ta yi kewar mijinta ba? Miji mai kama da dubu irin Yallaɓai na." Harara ta zuba min kafin ta ce"Mu kuma na mu mazajen masu kama da bolar sharar ki ko? Ina dariya na ɗaga hannu ina faɗin" Ba ruwana.".   Ba ta biye min ba, nan ta bar ni ina ƙarisa cin abinci ta bi mijinta falo suna hira nima ina gamawa ganin mata da miji na buƙatar privacy sai na ce musu zan shiga na kwanta. Ina shiga na yi shirin barci Yallaɓai na kira an ci sa'a yau ɗin ya koma gida da wuri.   "Yaushe za ki dawo? Yallaɓan Sadiya ya yi kewarta sosai."   Ina jin kewata a muryansa nima cikin muryan kewan na ce"Gobe gobe nan Yallaɓai. Kwana biyu ban ji ɗumin ka ba kamar ban da lafiya Am baby na." Kalamai na ƙarshe suka bashi dariya har sai da ya dara, hira muka yi sama sama na ce ya haɗa ni da su Jidda ya ce suna falo suna kallo tare da Saude. "Ki dawo gobe Sadiya ta. Da gaske Yusuf ya yi kewar HalimatuSaddiya." Ina mirmishi kamar ya na ganina na ce"In sha Allahu Yallaɓai na." Mun ɗan dade muna waya ina ta bashi labarin Ya Muntari fa ya koma Hubby ina dariyan shaƙiyanci ya ce"In kika dawo za ki haɗu da Rahila kun fi kusa."   Hiran sa ya ɗauke min hankali na tsawon lokaci sai da ya ce min zai yi wanka sannan muka yi sallama. Nima daga nan na ijiye wayar na yi addu'an barci ba daɗewa sai barci. Yallaɓai na baya son tafiyan dare ya sa da wuri na shirya. Kafin Yaya Hamza ya fita sai da ya sake ba ni 10k ya ce na yi na mota sai na yi kawaici na ce"Yallaɓai fa ya ba ni na mota ina ta saka ka ɗawainiya Ya Hamza"   Wani kallo ya yi min ban san lokacin da na karɓi kuɗin ina cewa" Allah ya ƙara ma nema albarka." Kai tsaye ya ce"Amin. Yallaɓai mijin ki ne, ni kuma Yayanki ne kin ga ne? Sai na ɗaga masa kai ina danne dariyata. Mun rabu ya ce shima suna tafe karshen Sati na ce gida zai yi albarka Zaratan Alhajinmu za su yi hutun karshen mako a gida.   Ƙarfe goma mu ka yi sallama da Khaleesat daga nan na hau adaidaita zuwa tasha ina zuwa motar kano saura mutum huɗu na shiga ba daɗewa ta cika muka tashi. Ban samu Yallaɓai a waya ba sai na yi masa saƙo. Mun shiga kano ɗaya da wani abu ne. Daga tasha na samu abin hawa sai gida. Ba key a hannuna sai na buga get ɗin Saude ta zo ta buɗe mini tana ganina ta washe baki ta na faɗin"Sannu da zuwa Anty Sadiya." Ina shiga gidan na ce"Yauwa Saude ya gidan" Ta biyo ni tana karɓan ƙaramin akwatina. A falon farko na jaɓe ta kawo mini ruwa na sha na huta sannan na iya tashi na ƙarisa ciki na ɗauro alwala na gabatar da sallar Azahr da ta suɓumu ce mini a hanya. *Janafty" *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. *🅿️08* Ina idar da Salla Saude ta kawo mini abinci shinkafa da miya ce, daman na yi miyata tun kafin na tafi Zariya. Ban iya fita ba a cikin ɗaki ta kawo mini komai na ci ta kuma zo ta ɗauke filet ɗin da kofin ruwa. Ni na ce ta jira su Jidda su dawo daga makaranta sai ta tafi saboda yau ɗin ba su da islamiya. Saude ba ta karatun boko amman tana allo tana kuma islamiya. Khaleesat kawai na iya kira na faɗa mata na isa gida lafiya sai Yallaɓai da na kira bai ɗauka ba sai na tura masa saƙon na sauka lafiya. Daga nan na haye gado na kwanta sai barci daman na gaji bayana har wani sagewa ya yi. Barci na sha sai la'asar na iya tashi da na ji kiran salla daga masallacin gefen mu. Daƙyar na iya tashi na shiga tiolet na ɗauro alwala na yi salla. Sai bayan na yi sallah sanna na samu daman rage kayan jikina saboda ɗazu gajiya ya sa ban iya sauya kaya ba kawai na kwanta.   Daga ni sai siket na ciki under. Sai bra na zauna a gefen gado ina duba wayata. Sai na ga Rahila ma ta kira ita da Datti. Kiran Datti na fara bi bayan mun gaisa sai ya ce. "Yaya Sadiya kin dawo ko kina can Zariyan ne? Kai tsaye na ce"Na dawo ɗazu. Ya aka yi ne? Su Alhajinmu dai lafiya ko? "Kowa lafiya. Zan koma makaranta gobe ne ina so na shigo yau da daddare." Kai tsaye na ce" To sai ka zo." Daga haka muka yi sallama. Sai na bi bayan kiran Rahila kamar ta na jira ta yi zaraf ta ɗauka. "Sadiya Allah ba na son wulaƙanci."   Ina danne dariyata na ce"To Sadiya yar laifi. Me kuma na yi? Cikin jin haushi ta ce"Ban sani ba. Sunan mijin nawa ne abin shakiyancin ki? Ina dariya na ce"Allah ya huci ran gimbiya Rahila a gidan Hubby." Ƙaramin tsaki ta ja kafin ta ce"Shegiya Allah zan rama ne." "Ba a kira mu sunan sabon sunan Ya Muntari ba? Ko ba a riga an yi taron ba ne? Na san ta buɗe baki ne ta kasa mgana saboda yadda na ji ta yi shuru. Fahimtar haka ya sa da sauri na ce"Allah ya huci zuciyar My Baby" Tsaki ta yi mai ƙarfi ta ƙatse wayar ta barni ina ta dariya. Sake kiranta na yi ba ta ɗauka ba sai na kyaleta. Ijiye wayar na yi na tashi na saka wata rigata ta zaman gida yar doguwa mai sauƙin kwari sannan na fita falon farko na iske Saude zaune ita kaɗai ta na kallo.   Zama na yi nima ina ta ya ta. Kallonta na yi kafin na ce"Ko za ki bari in Yallaɓai ya dawo ne mu kai ki gida Saude? Kanta na ƙasa ta ce"To Anty" Saboda in samu in yi ma Balaraba godiya sannan mu ƙarisa gida in gaida su Alhajinmu.   Muna nan a falo biyar na yi na ce ta mayar mini Tauraruwa an fara Indiyan hausa sai ta sauya mana tasha ana wani film mai kyau, har su Jidda suka dawo daga makaranta suna ganina gabaɗayansu suka faɗa jikina suna murnan ganina nima da fara'ata na tare su Jidda da ta yi girma ban iya ɗaga ta ba, amman na ɗaga Baby sama ina mata dariya.   Faɗi take yi" Umma mun yi kewarki." Ina shafa kumatunta na ce"Nima na yi kewarku ƴa'ƴan Umma."   Ni na cire ma Baby Uniform na kuma zauna tare da su suka ci abinci suna ta bani labarin makaranta ina sauraransu. Bayan sun gama cin abinci na ce Saude ta taya Jidda su wanke Uniform ɗin su da safuna. Suka bar mu ni da Baby a falo tana ta min labarai ina sauraranta zuciyata kamar farar takarda saboda farincikin na dawo gida na ga iyalaina cikin koshin lafiya.   Har aka kira mangariba lokacin su Saude sun dawo cikin gida sun gama wankin na ce su yi awala su yi salla. Ni ma na shiga ciki na ɗauro alwala na yi sallah ina kan darduma ina azkar na ɗauki wayata abin ya ba ni mamaki na ganin Yallaɓai bai kirani ba kuma na san ya ga kirana kuma ya ga saƙo na. Ban yi fushi ba sai na sake kiran shi sai da ta kusa katsewa ya ɗaga kirana. "Yallaɓai na."   Dagacan bangaren na ɗan ji hayaniya ban kawo komai ba sai na yi tunanin ƙila yana wani waje na mutane sosai. " Ina Rano. Amman yanzu zan taso." Haka kawai ya ce mini. Cikin mamaki na ce"Rano kuma? Aikin ne ya yi dare haka? "A'a. Tun dazu muka tashi na biya gidan su Nene ne. Yanzu dai ina gidan Baba ne."   Kai na gyaɗa kafin na ce"Allah Sarki. Ka gaishe su." Sai ya ce mini za su ji, naji ana mgana a kusa dashi ban gane da muryan ba amman ta mace ce. Ina shirin mgana na ji ya na ce min" Ga Sameena ta dawo daga kano yau." Bai bani damar mgana ba kawai na ji muryan Sameena.   "Matar Baba ɗazu da rana na dawo gida. Ashe sai yau kika dawo? Sai na amsa mata. Mun gaisa sannan tace za ta sake dawowa in sha Allahu. "Ko kafin ki dawo ni na zo ba." Tana dariya ta ce"Allah ya sa' Daganan muka yi sallama sai ta miƙa ma Yallaɓai wayarsa. "Yallaɓai ka dawo da wuri. Ka siyo min kaza a hanya saboda yau za mu sabunta amarci ne." Na faɗa cikin wani salo. yar dariya ya yi kafin ya ce"Amarya ko? To shikenan ango zai taho kazar amarci.' Ya faɗa kamar cikin raɗa domin na ji ya rage murya.   Mirmishi na saki kamar yana ganina na buɗe baki da niyyar mgana kenan na ji muryanta. Muryan da ba zan manta da ita ba saboda daban take. Ko mgana za ta yi cikin isa da gadara da salo. Kuma kamar ta fi yin salo matuƙar da za ta yi mgana da Yallaɓai. "DADDY. Ba ka ji ba." Yaushe ta zo garin? Haka na ke tambayan kaina a cikin raina. Baki na saki lokacin da na ga kawai Yallaɓai ya katse wayar ba tare da ma mun yi sallama ba. Gabana ya faɗi Ras!. Amman sai na lallashina kaina da cewa duk tsiyanta dai ita yanzu matar wani ce. Ba ta isa ta bibiyan min miji da auranta ba ko ita ta yi Yallabai na aminattace ne ba zai taɓa biye mata ba.   Kauda tunanin komai na yi a cikin raina na tashi na cire hijabin da na yi sallah. Gyaran ɗakin na fara duk bai da datti na san Yallaɓai na gyarawa. Sai da na share na gyara gado na goge komai na saka turaren wuta a ɗaƙin ya ɗau kamshi sannan na shiga wanka. Daga can na ɗauro alwala na fito bayan na shafa mai na yi kwalliyata kamar yadda na saba domin Tarban Yallaɓai na cikin zumuɗi da muradi mai girma. Da gaske ne na yi kewarsa sosai.   Ina sallar isha'i Jidda ta shigo ta na faɗa mini Uncle Datti ya zo. Shi ya sa ina idarwar na ɗauko wayata zuwa falo ina sanye da riga da wando na wani material na saka mayafi abaya baƙi a saman kaina ina tashin kamshi. Kaina ba kitso har lokacin amman ina tunanin zuwa gobe zan je a wanke mini na yi kitso.   Mun gaisa da Datti da tambayan su Gwaggo ya ce duk suna lafiya. Saude na ce ta zuba masa abinci. Bayan ta kawo masa na ce ta ja su Jidda ɗakin su ta zauna kafin Yallaɓai ya shigo. Datti na cin abinci muna hira sama sama. "Na ɗauka sai wani satin za ka koma. Ya Auwal na tafe wannan weekend ɗin fa."   Sai da ya sha ruwa sannan ya ce min" Na so haka amman ranar Friday an saka mana wani test ne, ina bukatar komawa na yi karatu"   Kai na jinjina kafin na ce"Haka ne. Allah ya bada sa'a. " Da ya ke yana karatu ne A kaduna state University KASU" Ko bai faɗamin ba na san abin da ya kawo shi. Alhajinmu yanzu ba kuɗi duk suna gona daman karatun na su shi Ya Auwal  da su Ya Hamza ne ke taimakawa sai ni da Amina da ɗan abin da ba a rasa ba nan take na tura masa 20k cikin kuɗin da ke acct ɗina. "Ga 20k nan ka lallaɓa zuwa karshen wata in sha Allahu." Godiya ya yi mini kafin ya ce" Yaya Auwal ma turamin 20k zan ɗan yi siyayya kafin goben na wuce." "Allah ya kai mu." "Ma'u ta zo gida jiya muka haɗu na ce mata yau zan koma. Shi ne yau da safe ta kirani ta ce na je tana son ganina ta bani kayan tea da sabulun wanka da na wanki."   Ya na mgana ina masa wani kallo sai da ya gama maganar sannan ya fahimta da sauri ya ce"Wallahi ba ni na roƙeta ba Yaya Sadiya."   Ƙaramin tsaki na ja kafin na ce"Allah ya ba da lada." Da na so na yi wata mgana sai kuma na fasa tuna nima na sauya taku akan Ma'u.   Mun saki wannan hiran sai kuma muka kama na Yaya Abubakar a bakin Datti na ke jin shekaranjiya Zaituna ta kwaso rigima har da yan sanda aka kira mata. Ita wai uwar adashe ta cinye kuɗin jama'a. An ce dakyar suka ba da belinta sai dare da ta yi kwana cell.   Mamaki ya kamani na riƙe haba ina faɗin"Kai matar nan wai har yanzu ba ta daina saka Yaya Abubakar a uku ba! Shegiya ka rasa abin da take yi da kuɗin jama'a sai ta jawo rigima ta bar ɗan'uwanmu da biyan bashin ta"   Datti ya ce"Wallahi nima har mamaki na ke yi. Kuma shi Yaya Abubakar ɗin bai iya ɗaukan mataki a kanta ba." Tsaki na ja kafin na ce"Yaushe wannan zai iya? Tun fa muna gida ni nasan Yaya Abubakar sai mace ta bautar dashi. Da dai irin su Ya Hamza ne kai kasan Zaituna ba ta isa ba. Shi fa yana jin sa kamar ba namiji ba"   Datti na yar dariya ya ce"Sanyi gare shi ne." Cikin jin haushi na ce"Sanyin me?  ya dai auro wacce ba ta san ciwon kanta ba. In bai tashi tsaye ba sai ta kashe sa lokacinsa bai yi ba"   Datti dai ta na dariya. Ban san adadin awannin da muka ɗauka muna hira dashi ba. Ni a bakinsa na ji wai Alhajinmu ma ba shi da lafiya jiya ya yini da ciwon kai nace ni ba wanda ya faɗa min ya ce su Yaya Bahijja duk sun sani sun je sun duba shi har da Ma'u."   Takaici ma ya hana ni mgana. Sai shi ne ganin raina ya ɓaci ya ce" Ƙila saboda sun ga bakya nan ne." Uhm kawai na ce ina duba agogon wayata tara da rabi na dare sai na zaro ido Yallaɓai bai dawo ba har yanzu.   Wayarsa na kira ta na ringing amman bai ɗaga ba har sau biyu tuni zuciyata ta harba ina hashashen ko har yanzu yana can Ranon ne tare da ita? Ga Saude ta na jiran mu mu kaita gida ganin har goma ta yi Datti ya ce min zai tafi sai kawai na ce ya tsaya ya tafin mu da Saude gida. "Ba nan take kwana ba daman?   Ina miƙewa na ce"Ba a nan ba ne. ta zo ta kwana da yara. Yallaɓai bai dawo da wuri ba shi ya sa na ce ka wuce da ita."   Sai ya amsa mini, ɗaki na koma na ɗauko 2k cikin jakata na wanda Yaya Hamza ya bani na fito. Sai na iske su afalo Datti ya ba ma su Jidda Chaculate din da ya zo musu dashi ya ce har ma zai tafi ya manta bai ba su ba.   Na ba ma Saude 2k ɗin ina cewa"Yallaɓai bai dawo ba sai gobe zan shigo anguwan. Ki gaida mamanku sai na zo." Ta karɓa tana min godiya Baby ta makale mata sai ta je dakyar na riƙe ta na ce ta bari ranar da ba makaranta sai su je can Ɗorayin su kwana.   Har haraba na rakasu. Suna fita na rufe get ɗin muka dawo cikin gida. Ganin dare ya yi sai na rakasu ɗakin su suka yi shirin barci sai da na tabbatar sun yi addu'an barci sun kwanta sannan na rage musu hasken ɗaki na rufe musu ƙofa na dawo falon farko na kame kan kujera. Ga TV a kunne amman ba na fahimta duba lokaci kawai na ke yi a wayata har goma da rabi har sha ɗaya na dare Yallabai bai dawo ba. Bai kirani ba sannan na ƙara kiran shi amman bai ɗauka ba again.   Na yi ta ƙokarin boye yanayina. Na zauna ina jiransa a falo ni kaɗai duk kwalliyan da na yi ta gama susucewa. Lallashin kaina kawai na ke yi ina zaune. Sha ɗaya da mintina sha ɗaya sannan na ji ana buɗe get da ƙaran shigowan mota.   Ajiyar na sauke ina zaune har ya shigo falon. Muka haɗa ido dashi ya na shigowa da leda a hannunsa mirmishi ya ke yi min irin na shi mai sanyaya mini zuciya. Amman sai na ji na kasa maida masa martanin mirmishin na shi, ya ƙariso har gabana ya na sauke ledan hannun shi ya ɗago kawai ni kuma na miƙe na wuce ma mukunnin wuta na kashe hasken falon na fice a falon na bar shi tsaye sake da baki yana bina da kallo. Na sake kashe hasken falon na biyu daga nan na shiga tiolet na kama ruwa ko da na fito na same shi a cikin ɗaki yana tsaye kawai ya harɗe hannu a kirjinsa yana kallona.   Yi na yi kamar ban gan shi ba. Na isa gaban wardrope na laluɓo rigar barcina. Ina shirin tuɓewa na ji ya rumgumeni ta baya ƙamƙam bayan ya sagalo hannunsa ya riƙe rigar barcin dake hannuna.   Na ja shima ya ja kawai sai na sakar masa. Numfashi ya fesar min ta saman wuyana. Duk ina jinsa sai na yi masa bakam mugun haushin sa na ke ji da wani abu mai zafi da ya tokare mini a ƙirji. "Sadiya ta. Fushin kike yi da ni? Haka ya faɗa ya na mai zuro da kansa wajen fuska. Kauda kai na yi kafin na ƙwace jikina ya juyo muna fuskantar juna ni da shi cikin basarwa na ce"Fushin me? Ka yi wani abu ne?   Haka na faɗa kai tsaye kuma na miƙa hannu ina faɗin"Ba ni rigar barcina. Ina so na yi shirin kwanciya ne " Sai ya maƙe kafaɗa alamun ba zai bayar ba. Ni kuma kawai sai na juya na sake buɗe wardrope ɗin na ɗauko wata itama yasake ƙwacewa na bar masa na sake ɗauko wata itama ya sake ƙwacewa a ƙufule na kalle shi kafin na kira sunan shi. "Yusuf.." Haka na faɗa ina tsare shi da ido. sai ya yi wani iri da fuska kafin ya ce" Yallaɓan naki ne kuma yau ya dawo Yusuf? "Ai sunan ka ne ko ba sunan ka ba ne Yusuf?   Na faɗa cikin gatse ina hararan shi. Sai ya yi dariya ni kuma sai na juya ina ƙara laluban wata rigar barcin kai tsaye ya ce" Ko sau dubu za ki ɗauko sai na ƙara ƙwacewa gwara ma ki tsaya mu yi mgana."   Ni na san halin ɗan kayana. Shi ya sa na dakata na juyo ina kallonsa kafin na ce" Ni fa ba ka yi min komai ba. Kawai dai ina so na kwanta ne." Takowa ya yi gabana ya saka hannunsa guda ɗaya ya riƙe min hannuna guda ɗaya ya zaunar da ni a gefen gado sai ya durƙusa a gabana lokaci ɗaya ya na riƙe duka hannuwana cikin tafin hannunsa. "Am Sorry. Na yi dare. A gidan Baba Hajiya ta matsa mini sai na tsaya na ci abinci sannan kuma Tariq ya zo gida shi da iyalansa shi ya tsaida ni muna hira ban san dare ya yi ba. Na ga kiran ki ina hanya shi ya sa ban ɗauka ba."   Har ya gama mganarsa ina kallonsa. Zuciyata ta ɗan yi sanyin jin ba abin da na yi tunani ba ne amman ban nuna masa ba sai na ƙara hade rai har ina kauda kaina gefe. "Ki yi haƙuri kin ji ko?  Ya faɗa ya na matse min yan yatsuna. Zare hannuwana na yi daga cikin na shi sannan na miƙe ina faɗin" Na ji."   Daga haka kawai na fara ƙokarin tuɓe kaya da sauri ya taso ya rike ni lokaci ɗaya ya na faɗin"Ban riga na natsu na ga kwalliyar ba. Ballantana har na yaba na biya tukwaici shi ne kuma za ki hana ni samun wannan ladan?   Ya faɗa ya na tsare da ido. A idanuwansa na fahimci ya gaji kuma ya na bukatar wanka ya huta. Sai kawai na ƙwace hannuna ina faɗin" Na yau dai ka makara. Amman ƙila gobe in ba ka makara ba ka  rabauta"   Da sauri ya riko ni na faɗo jikinsa sai ya rumgumeni ya na faɗin" kin manta kin ce yau zamu sabunta amarci? Na taho mana da kazar amarcin mu part 2" "Shima ka Makara. Amarci kuma ka gama shan romonsa shekaru goma sha a baya."   Na faɗa ina ƙokarin kwace kaina kai sai ya juyo da ni muna fuskantar juna na buɗe baki zan yi mgana ya haɗe bakin mu waje ɗaya yana kissing ɗina ni kuma na ƙi bashi haɗin kai sai kawai ya matse min cikina da ɗayan hannunsa ɗayan kuma ya riƙe wuyana dashi tamau yadda ya matse bakin mu waje ɗaya in na ce zan ƙwace kaina da karfi zan wahala sai kawai na saki na miƙa masa kaina tare da ragamar rayuwata bayan nima na saka duka hannunawa na zagaye ƙugun shi.   Mun daɗe muna sumbatar juna har sai da ya gaji sannan ya sake ni. Ya na maida numfashi ina maidawa. A tare muka kalli juna gira ya ɗagamin kafin ya ce" Amarya ta." Hararan shi na yi kafin na ce" Haka ake Ango kai duk ya fara furfura? Ni jarumi ne angona."   Na faɗa ina gyara zaman rigata da ya zame min. Wata dariya ya yi kafin ya ce"Bari in yi wanka yau ƙila da rabon har Gwaggo sai ta zo jinya ina ga."   Ina jin haka na ɗaga hannu ina faɗin" Yallaɓai na." Rigarsa ya cire yana yar ɗariya ya ce"Sadiya ta." Na san halin shi wallahi in ya so mugunta in na shiga hannu har sai na dawo ina magiya. Har mamaki na ke yi Yallabaina kullum kamar ƙara masa ƙarfi ake yi. Duk da mun yi aure yana tashen samartaka.  Amman yanayinsa na yanzu ya na ninka yanayinsa a baya ne.   Bin sa a baya na yi ina faɗin" Yallaɓai gajiyan tafiya ba ta sake ni ba. Ko na kwanta ne?   Tiolet ya shige ya na faɗin"Ki kwanta mana na hana ki ne? Gwara dai ki yi ma kanki faɗa ki ɗauko kazar amarcinki a fridge ki fara ci kafin na fito. Zan karɓi maiƙon kazata a daran nan in sha Allahu."   Nakwa nakwa na yi da fuska har lekoni ya yi yana dariya. Ba ni da mafita kitchen na fita na bude fridge ɗin na ga kazan dankwaleliya ce a faranti na sako mana kazar dai ta bakin shi ta sha maiƙo ga albasa da kabeji.   Ruwa na ɗauko mana da lemu bedroom ɗin na kawo mana ba daɗewa sai gashi ya fito daga wanka ɗauro da Babban Towel a ƙugunsa ya ganni zaune saman cafet da farantin kaza a gabana.   Ya kalleni sai ya saka dariya ni kuma sai na gimtse fuska cikin nishaɗi ya ce" Ke fa kika ce na taho da kazar amarci yau za mu tuna amarcin mu. Kin ga fa ke kika saka mini rai da kwaɗayi."   Shuru na yi kawai na fara gutsiran kazan ina ci, shima sai da ya shafa mai ya saka gajeren wando sannan ya zo ya zauna ya na tayani cin kazan tun ina share sa har na saki yana bani a baki ina bashi mun ci kaɗan ba da yawa ba. Sannan na kwashe komai na maida kitchen sauran kazan kuma na saka a fridge.   Wanka na shiga na gyara jikina. Bayan na fito na shafa mai na saka humra sai na saka wata rigar barcina ƙarama mai buɗewar gaba Yallabai na saman gado ya na jirana da na tsaya masa yanga ma tasowa ya yi yana faɗin" Kin san dai ina da karfin iya ɗaukan ki ko? Cak ko ya ɗaga ni sama amman sai da ya yi nishi. "Wai wai. A gaishe da Yusuf." Ya faɗa ya na jinjina nauyina ni kuma sai na kwashe masa da dariya na ƙara hantsila kafata da ya sa na gagari karfinsa mu ka faɗa kan gado. Bin sa na yi na danne ina faɗin" Wayyo karfin Yallaɓaina ya fara ƙarewa." Ya na jin haka ya mirgina ni na dawo kasan sa ya kalleni sai kawai ya girgiza kai ya sauka daga kaina. Gadon ma ya sauka gabaɗaya ya je ya kashe hasken ɗakin sanɗa ya fara yi in ganin duhunsa na yi gefe ina dariya ina faɗin" Yallaɓai wasa fa nake yi" Ban tsira ba sai da ya yi sufa ya dira kaina a saman gado. Ya turmusheni yana faɗin" Ƙarfin Yallaɓai ya ƙare ko? Ina ta dariya. Haka muka dinga mirgina daga kudu zuwa yamma kafin dai mu natsa sai da muka yi wassanin da muka saba. Ni da Yallaɓai muna da wasu abubuwan da in ba mu yi ba ba ma jin daɗi. Yallaɓai ya ɗauke ni a komai na shi haka nima, za mu yi ta wassani muna dariya kafin mu faɗa farantama juna, cakulckuli ya rika yi mini kamar zan shiɗe sannan ya bi ni ya danne ya haɗe bakin mu waje ɗaya.   Baki shi ke yanka wuya. Domin da gaske amarcin aka sake maimaitawa. Ni fa har da su Mama na ke kira da asuba Yallaɓai na ta yi min dariya ko kallon shi ban yi ba. Dirza na sha a hannun shi har sai da na gane ba ni da wayau ta bakin shi ya ce ya goge reni ne ina tunanin ƙarfin sa ya kare har ce min ya yi ko mata goma ne budare zai iya da su a dare ɗaya ai sai na saki baki ina kallon shi. Domin ai Yallaɓai ya fi ƙarfina.   Ranar bai fita ba a gida muka yini tare. Kuma ta bakin shi maiƙon jikina duk sai da ya gama siɗe shi. Sai dare muka samu fita zuwa ɗorayi muka je na duba Alhajinmu daga nan na shiga gidan su Saude na yi ma Balaraba godiya.   Washegari na shirya ya sauke ni gidan Halima na ƙara gaishe ta. Tunda ban samu suna ba na kuma ɗan jima tun da har girki na yi mata ita kaɗai a gidan ga jego. Jawahir ce ke zuwa mata kuma ta koma makaranta sai ƙanwar mijinta itama kuma yau ɗin ba ta samu zuwa ba. Muna ta hira a bakin ta ma na ke jin wai Yaya Usman zai ƙara aure mijin Zabba'u. Na girgiza da jin zai ƙara aure. In na duba yadda Anty Zabba ta ke son mijin nan na ta bata iya haɗa shi da kowa ga ta da kishin tsiya. Halima na faɗa min saboda maganar auren bai faɗa mata har sai da aka saka rana ta yi ta tashe tashen hankula daga karshe ma ta yi yaji a mganar da ta ke gaya min ma tana gidansu anan kano.   Sai uku na rana na koma gida saboda girki. Saude suna da walima sauka a islamiyarsu ba ta zo ba. Ni dai na yini ina mamakin auran Yaya Usman ko alama Yallaɓai bai faɗa mini ba Hauwa ma ina ga ba ta sani ba. Munnira mun kwana biyu ba mu waya ba. Ita kuma daman Anty Zabba ɗin ba ma yi sosai iyaka in an haɗu a gaisa ne kawai tunda ba ma garin suke ba in ba wani sha'ani ko rashi ba sai mu shekara ba mu ga juna ba. Daman mutuniyata Hauwa ce sai Munniran da ba kamar yadda muke da Hauwa ba.   Mu da ɗan yawa mu surukan a gidan marigayi Alhaji inuwa. Mu shidda ne har da Amaryan muhammad Kabir da bai daɗe da yin auran ba. Shi likitan jini ne yana katsina yana aiki da medical center can ya ke zaune da matarsa. Ni da yake kowa ya san halina ba ni da shisshigi kuma in ma ka shige min ba lalle na iya mu'amala dakai ba sai in Allah ya haɗa jininmu to ballatana ma mai hali irin na Anty Zabba da shigen takama da ji da kai. Ko don ta na taƙamar mijinta na ta kuɗi sannan iyayenta ma wasu ne babanta tsohon alƙali ne a jihar kano mahaifiyarta kuma daga masarautar zazzau ta ke. Ni iyakata da ita in an yi wani abu da ya kamata na kira ina kiranta itama an aka yi min rasuwa ko rashin lafiya ta kan kirani ta gaishe ni. Ba sanayyar da zan iya kiran ta na ji labarin abin da ya faru ko Halima saboda ta na yar gida ce shi ya sa ta ji labarin.   Har wajen biyar na yamma ina ta tunane tunane na kasa ma tashi na ɗora girki. Na kira wayar Hauwa ba ta shiga na ji kanun labari in ta sani sai kuma ban same ta ba. Ni kuma ba na son kiran Munnira ko yaya ne ina ɗan rike girma na, ganin har su Jidda sun kusa dawowa makaranta ban yi girki ba ya sa na tube na shiga kitchen store na fara dubawa sai na ga gabaɗaya kayan abinci sun yi ƙasa shinkafa ba ta wuce tiya daman shine buhun ƙarshe sannan taliya kwara biyu macaroni ma ya ƙare indomie ma ina ga tun ina Zariya ta ƙare tun da daman ko da zan tafi ƙawayanni na bari.   Shinkafa tuwo ce kawai ta rage da ɗan yawa. Na yi tagumi ina kallon store ɗin ko kayan su maggi robobin sun yi ƙasa na tuna suma tun watan can da ya gabata ba a siye su ba. Kayan abinci kuma daman in Yusuf ya samu kuɗi ya kan siya da yawa haka in shinkafa ne buhu biyu uku haka taliya da macaroni katan uku ko biyu da yawa dai yadda za mu daɗe ba mu nema ba. Ina tunanin gashi kayan abinci ya ƙare kuma Yallaɓai bashi da kuɗi. Ajiyar zuciya na sauke kawai a raina ina fatan kafin komai ya ƙare Allah ya kawo wata mafitar. Tunanin yin Tuwo ya kawo mini acikin raina sai na duba naga ina da kuɓewa ɗanya da Gwaggo ta ba ni wacce ta taho da ita daga Yashe ne sau ɗaya na yi amfani da ita tunda Yallabaina ba ma'abocin cin tuwo ba ne sai bayan lokaci lokaci haka.   Ban yi kai tsaye ba sai da na koma ɗaki na kira Yallaɓai na na ce masa yau Tuwo na ke so na yi ko yana so na dafa masa wani abincin ne?   "Sadiya na daɗe ban ci tuwo ba. Ina marmarin shi." Amsar da ya bani kenan. Sai na yi mirmishi kafin na ce"To zan ɗora tuwon yanzu. Ka taho min da ƙashi ko Nama wanda zan yi miyan dashi." Sai ya amsa min da toh, tunda yau ba Rano ya je ba Office ya je.   Da ƙarsashina na koma kitchen na ɗora ruwan Tuwo a saman Gas. Yara kuma na yi tunanin su sha wani abun kafin na gama girkin, ina cikin tunanin su sai na ji buga get na san sune tunda shidda saura a lokacin. Ni na je na buɗe musu kofa har Salisu ya tafi bayan ya sauke su. Tare muka shigo cikin gida da su ina tafe riƙe da jakar Baby da lunch box ɗin ta.   Bayan sun sauya kaya na ce su zo su sha ko goldemorn ne tunda corflex ya ƙare shima sai kwali kafin in gama abinci Baby ce ta biyo ni kitchen ɗin ta na faɗin" Umma me kike dafawa? Kai tsaye na ce"Tuwo." "Tuwo?   Ta faɗa ta na kwabe fuska. Sai ta bar ni ina ta mata dariya daman na san ba ta son tuwo sai na lallasheta na cewa ina da sauran miya zan ce ma Yallaɓai ya taho da buredi sai ta ci dashi jin haka yasa  ta yi tsallen murna. Ko kafin mangariba na gama Tuwo tunda na shinkafa ne har na mulmule a leda Jidda ce ma ta taya ni ɗaurewa a ledan muna yi ina nuna mata in da ba ta yi dai dai ba ta na gyarawa.   Miyan na ɗora daman na yi greting ɗin kayan miya daddawa daman ina da dakakkiya ban mantawa Inna Mariya ta aiko mini dashi. Sai na ɗan zuba ruwan da yawa saboda ban san lokacin da saƙon Yallabai da zai iso ba. Tare da yarana muka yi sallah a ɗakinsu na zauna muna karanta azkar tare sakamakon na daɗe ban yi musu karatu ba ya sa na ce kowacce ta ɗauko Qur'ani mu yi karatu.   Na biya ma Jidda na ta Baby ne muke yi lokacin da Yallaɓai ya shigo ɗakin na yi mamakin ganinsa yau da wuri haka. Ya na tsaye bakin kofa sanye da wani farin yadi kansa da hula ta zanna mai kalan aikin jikin yadin. Mirmishi a saman fuskarsa ga leda a hannunsa ɗayan hannun kuma key ɗin mota da sai wayarsa. "Sannu da zuwa."   Na faɗa ina kallon shi lokaci ɗaya nima ina maida masa martanin mirmishin. Baby ce ta tsshi ta isa wajensa ta na masa oyoyo Jidda kuma daga zaunen ta ce"Sannu da zuwa Abba." Ya amsa lokaci ɗaya yana ce ma Baby" Kar ki ɓata jikin ki." Ya faɗa ya na nuna mata ledan hannun shi. Miƙewa na yi na isa wajen shi ina faɗin" Ban ɗauka za ka dawo yanzu ba. Na ma za ta Musabahu za ka aiko."   Kai ya girgizamin kafin ya ce"Kawai na ga ba wani aiki ne shi ya sa na ce bari na dawo gidan kawai.' Ya faɗa ya na miƙamin ledan na karɓa lokaci ɗaya ina kallon Baby da ke riƙe da hannun babanta."   "Je ku gama karatun Baby."   Kumatunta ya shafa kafin ya ce"Je ki. In an gama karatu ki zo ki karɓi tsarabanki." Jin haka yasa ta wuce da gudu ta na dariya muka bita da kallo gabaɗayanmu cikin ƙauna gaban Jidda ta koma ta zauna ta ɗauki Qur'aninta ta na karantawa da karfi. Ni da Yallaɓai muka fita ina gaba ya na bin bayana shi ya rufe musu ƙofar.   Tare muka shiga har kitchen ina buɗe naman. "Ko da na je duk sun gasa sai wannan na samu na 3k ne zai isa? Yallaɓai ya faɗa ya na sunkuyo da kansa ta ɓarayin wuyana. Kai na jinjina kafin na ce" Zai yi mana. Miya ce ba yawa sosai."   Sai da na saka naman duka a cikin miyan ina juyowa Yallaɓai ya rumgumeni ta baya lokaci ɗaya ya na faɗin" Yau ko ɗan hug ɗin oyoyo ba a yi min ba ko? Ina mirmishi na ce"To ka jira ka ga ban yi maka ba ne? Na faɗa ina wucewa wajen sink in da na buɗe famfo na tara hannuna ina wankewa shima sai ya sunkunyo da kansa ta wajen wuyana lokaci ɗaya ya zuro hannayensa duka biyu ya kama nawa yana murzawa a tare ruwa na zubar mana. "Nima a wanke min hannun mana Sadiya ta."   Ya faɗa cikin raɗa sai na yi yar dariya na karɓi hannun ina murza masa na wani lokaci kafin na kashe famfon ƙaramin Towel ɗin da ke kitchen na ɗauka ina goge masa hannunsa. Nima na goge nawa hannun sannan na yi masa rumgumar da ya yi min ƙorafi shi kuma ya ɗago ya sumbaci goshina.    Ta falo muka fita na ɗauko masa wayarsa da key ɗin mota muka wuce cikin ɗaki. Wanka ya ce zai yi amman da ruwan sanyi saboda garin akwai zafi zafi mun fita damina an fara zafin nan na fiddan dawa. Shi ya shiga wanka ni kuma sai na koma kitchen ina duba miyata da na saka mata kalolin maggi. An kira isha'i Yallaɓai bayan ya fito wanka ya saka Jallabiya ya tafi masallaci ni kuma da yara muka yi a gida. Da zai shigo ne ya shigo da ice cream ɗin da ya siyo ma Baby ita kuma Jidda wani bickit mai madara mai ɗan karan daɗi lokacin har na kaɗa miyata na gyara kitchen ɗin ina jin shigowarsa na faɗa wanka.   Har na gama shiryawa yana falo tare da yara. Ni kuma sai na tsuke cikin riga da wando. Wando ya kamani ta sama amman ya na da buɗewa ta ƙasa rigar ma tana buɗewa ta ƙasa. Wandon baki ne rigar fara sai na yi amfani da bakar hula a kaina ban fesa turare jiki kuma na shafa humra har da jan baki na saka na yi ɗas da ni ina fitowa falo wajen ya ɗauka da kamshi. Jidda na kira ta tayani ɗaukan kaya zuwa Dinning. Baby ta samu ice cream tuni ta manta da mganar Biredi ni kaina na manta ban kira Yallaɓai ban ba a lokacin.   Gabaɗayanmu muka haɗu a saman dining ɗin ban da Baby da ke can falo ta na kallo. Da kaina na saka ma Yallabai guda biyu na zuba masa miyar da ta ji naman rago Jidda ma ta saka ɗaya ta ce ya isheta nima dai ɗayan na saka saboda na ci abinci a gidan Halima. "Sadiya ta. Kin yi kyau.'' Haka Yallaɓai ya faɗa yana kallona da mirmishi a saman fuskarsa. Fari na yi masa da ido kafin na ce"Thank you Yallaɓan Sadiya." Jidda na cin tuwon ta ba ta ɗago ba amman ta yi mirmishi. Yallaɓai ya kalleta kafin ya ce"Hajiya Nene ko Umma ba ta yi kyau ba? Da sauri ta ce" Ta yi kyau sosai Abba." Ya na ƴar dariya ya ce"To ai shi ne na yaba kuma sai na ga kamar ta cancanci tuƙwaici ko?   Jai ta gyaɗa masa ta na mirmishi ina jin su ban ce komai ba sai da na ji ya ce"Kar ki damu zan ba ta kyakyawan tuƙwaici" Ɗagowa na yi ina hararanshi kafin na saka kafata na taka masa kafa sai ya janye yana dariya. Jidda dai ta gama cin tuwonta ta ɗauki filet ɗin ta bar mana Falon sai da ta fita na kalle shi kafin na ce" A gaban Jiddan ka ke mganar tuƙwaici? Kai ya gyaɗa kafin ya ce"To miye a ciki? Ai ba ta san irin tuƙwaicin da kike karɓa ba madam" Wani kallo na yi masa da ya sa sai da ya ƙware yana shan ruwa na yi masa gwalo ina dariya amman sai da na saka hannuna ta bayansa ina shafawa ganin ya sarƙe da yawa. Wani ruwan na sake zuba masa na bashi ya sha sannan ya ɗan lafa masa.   Kallona ya yi kafin ya ce" Ki riƙa bari sai mun shiga ɗaki sai ki yi mini wannan kallon kin ji ko? Ina dariya ban yi mgana ba shi kuma ya ce" Saboda tsaro ba."   Murguɗa masa baki na yi shi kuma sai ya kaɗa kai kafin ya ce"Murgaɗa da kyau za ki yi bayani ne yarinya in na fara gyara miki service ɗinki har da garambahul." Marairaicewa na yi ina faɗin" Mai jan mota ya tokare boda yau Yallaɓai." Kai tsaye ya ce"ko jan jirgi ne yau sai na gyara miki service ɗin ki." Dariya na yi shi kuma yana faɗin" Yi dariya da kyau." Ni ko na ce to kuka zan yi? Ya na min wani kallo ya ce" A'a shi wannan ki bari sai anjuma."   Kafarsa na taka ina faɗin" Yallaɓai cikin shagwaɓa " Da sauri ya miƙe yana faɗin" Yau wannan shagwaɓar taki ba amfanin da za ta yi miki " Tiolet ɗin falon ya shiga ya wanke bakin shi da hannunshi bayan ya fito ya wuce kan kujera ya zauna ya dauki remot ya kunna TV ni kuma sai na tattara komai na maida kitchen ɗin ina gyara wajen daga can zaune Yallaɓai ya ce. "Ki zo mu yi hira. Hiran saurayi da budurwansa." Ina mirmishi na ce"Sadiya da Yusuf ɗin ta ba." Kai ya jinjina kafin ya ce" ko dai Yallaɓai da Sadiyarsa? Na ce ai duk ɗaya. Sai da nima na wanke hannuna da bakina sannan na leƙa su Jidda na ce tara ta yi su kashe kallon nan su je su kwanta in suna da aikin makaranta su ɗauko su yi kafin su kwanta. Jidda ta amsa min da toh sai na rufe musu kofar na dawo wajen Yallaɓai shi kuma sai ya miƙa min hannu na taho ya yi min mazauni saman cinyarsa ina zama ya kishingiɗa nima sai na lafe kaina saman ƙirjinsa ina wasa da tsillin gashin wajen tunda ya cire jallabiyar daga shi sai dogon wando shi kuma sai ya cire min hula yana wasa da gashina gefe ɗaya kuma yana min susan kunni dukkanmu mun yi shuru muna jin bugawar zuciyan juna ga ƙaran tibi da iskar fanka na ƙaɗawa. Wani farinciki na ke ji. Zuciyata na bugawa da sauri da sauri kamar yadda shima na shi ke bugawa. "Yallaɓai na." Na kira sunan shi cikin wani salon da na san ya na kunna shi. "Uhm." A saman leɓensa ya amsa min. "Ina son ka." "Ina ƙaunarki Halimatuna." Haka Yallaɓai ya faɗa lokaci ɗaya yana ɗago kaina. Bakinsa na nufa shima sai ya sunkuyomin a tare muka tarbi juna muna sumbatar juna cikin wani shauƙi da muradin junan mu. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKWRWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA (MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. *🅿️09* Mun daɗe muna sumbatar junanmu cikin wani shauƙin da a cikin zukatanmu kawai muke jin tasirin yanayin. Mu ka saki juna lokaci ɗaya kuma muka bi juna da kallo muna sauke numfashi a jejjere.   Mirmishi ya yi mini nima na mayar masa da martanin mirmishinsa. Tallafo kuguna ya yi ni kuma sai na ƙara maƙale hannuwana a a saman wuyansa jawo ni ya yi na sake lafewa a saman ƙirjinsa ina jin yadda ya ke ɗan sauke numfashi kaɗan kaɗan kamar wanda ya yu gudun tsare.   "Yallaɓai.." Na kira sunan shi bai amsa ba sai ya kalleni kafin ya lakace min hanci da hannunsa guda ɗaya yana faɗin" Uhm" Hannuna na kai saman Sajensa ina shafawa har zuwa ƙasa wajen gemunsa da ya fara fitowa domin yana yawan askewa yana dai barin kaɗan haka ina shafa gemunsa zuwa sajensa ina faɗin. "Ka san kai ne namiji na farko da ka ruguza dukkan tunanina. Kowa ya san burina na sai na gama jami'a na samu aiki zan yi aure. Amman tashin farko ina haɗuwa da kai ina yar aji ɗaya a jami'a ka susuta tunanina da ya sa na amince da kalamanka na aure ka bayan na yi fatali da mafarkina da burina gabaɗaya."   Na ƙarishe faɗa ina kallon shi. Shima ni yake kallo kafin ya yi mirmishi ya ce" To ni ɗin wasa ne? Kin ga zangaɗeɗen saurayi jikan mutanen Rano. Kin san in kika bari na suɓuce miki samun kamata ai da wahala shi ya sa kika yi amfani da maganar hausawa da suke cewa in dama ta zo maka ka yi amfani da ita saboda wataƙila in ta suɓuce maka har abada ba lalle ka ƙara samun damar ba" "Allah ko?    Na faɗa ina kallonsa da ƴar dariya. Shi kuma sai ya ɗaga min gira kafin ya ce"Kema kin san gaskiya. Samun jarumi kamata a cikin maza ai da wahala shi ya sa kika yi wuf da ni da sauri kafin ki makara. Ko wata ta yi miki ƴar kafa ba."   Ina dariya ina jan gashin sajensa ya yi shii alamun zafi ya na ƙokarin riƙe min hannu na ce" To me ya sa ka yi ta mini na ci sai da na yi maka kwatancen gidanmu? Kai ma ai kasan in ka bari na subuce maka samun kamata da wahala." Na faɗa ina masa fari, bakina ya sunkuyo ya sumbata lokaci ɗaya ya na faɗin" Ɗan bakin nan na daga cikin abin da ya fara jan hankalina a kanki. Da yanayin mganarki da takun ki. Kai kin iya jan Aji kin ba ma bawan Allah wahala ranar da na koma gida daƙyar na iya barci. A time ɗin bani da burin aure har sai na samu aiki na gina gida na gina kaina amman tun ranar da na fara ganinki kika ruguza mini wannan tunanin. Ke ce silan da ya sa na yi fito na fito da kowa akan aure saboda ai suna ganin ban kai ba me na tara me na ke da shi sannan a tunaninsu na yi yaro a lokacin ba su san a halin da na ke kwana ba ne shi ya sa.'   Ya ƙarishe faɗa yana wani sauke nunfashi ni kuma sai na ƙyalƙyace dariya taya ni ya fara yi yana cewa" Allah. Azumi fa na ke yi duk litini da al'amis ai ya kamata su gane ina son aure. Daga karshe dai na fito musu a Mutum na ce ina son na yi aure saboda ina da karfin sha'awa kuma ina tsoron faɗawa halaka. Nene na jin haka tace ku bar Tafida ya yi auran nan Zuwaira shi ne alherin mu gabaɗaya."   Shi ke tuna labarin a bakinsa amman ni kuma ina hasaso lokacin a cikin idanuwana. Tabbas lokacin an sha gwagwarmaya sosai kafin auran mu amman gashi komai ya zama tarihi. Mun yi aure har da albarkar ƴa'ƴa biyu kuma shekarun sun haura goma sai dai tunawa da abin ya faru kawai a yi dariya ko nishaɗi.   Mun cigaba da hirar baya a tsakanin muna yi muna dariya cikin nishaɗi wata magana da Yallaɓai ya faɗa sai da na sauka ƙasan cafet ina dariya.   "Lokacin da kika samu cikin Jidda na faɗa ma kawu Abba da Tariq? Kin san me Abba ya ce? Bai ba ni zarafin mgana ba ya cigaba da faɗin" Cewa ya yi wai ashe dai da gaske ina son aure ashe ƙwan haihuwa ne kunshe a cikina da ba a barni na yi auran nan ba da Allah kaɗai ya san in da za kai wannan ƙwan haihuwan."   Ia riƙe da cikina ina dariya na ce"To sai ka ce musu me? Domin ni a baya bai taɓa faɗa mini sun yi haka da su ba. Shima ƙasan cafet ɗin ya sauko kusa da ni yana faɗin" Me kuwa? Na ce wallahi ai kun kyauta ma kanku da kuka yimin yaƙi kan aurena da Sadiya. Tariq kuma ya ce Allah ya shiryeka Yusuf ban san yaushe ka lalace haka ba."   Ina kallonsa na ce" Gaskiya nima na san ka lalace ni ba haka na aure ka ba." Kansa ya saukar mini a saman kafaɗata yana faɗin" Ke kika lalatani Sadiya. Kika koyar da ni abin da ban sani ba kika buɗe mini baki. Kin san an ce da Namiji ya san mace bakinsa ke buɗewa." Mintsinin hannunsa na yi ina faɗin" Ni kar ka mini sharri. Na koyar dakai ko ka koyar da ni? Na faɗa ina kallonsa sai ya ɗago shima ya na kallona kafin ya riƙe mini hannuna guda ɗaya ya matse cikin hannunsa ya na faɗin" To shike nan na ji mun koyar da juna shike nan? Sai na gyaɗa kai matsowa na yi kusa dashi na matse shi rabin jikina na kan jikinsa ina faɗin" Wai Tarig ɗin sun koma ne? Yana shafa bayana zuwa ƙuguna ya ce" Ina jin kamar sai cikin Weekend ɗin nan za su koma. Faridarsa ma ta ce na gaisheki ranar na sha'afa ne." Kai na jinjina ina gyara zaman kaina a saman ƙirjinsa lokaci ɗaya ina faɗin" Yallabai. Kayan abinci fa sun ƙare." Shuru ya yi na wani lokaci kafin ya ce"Bari mu gani zuwa a shiga wannan satin. Sauran da ya rage zai kai mu lokacin? "A'a gaskiya. Ko su indomie duk sun kare lemun su Jidda na makaranta ba ko rabin katan bai kai ba."   Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce"Allah zai rufa asiri. Amman duk kudaɗen hannuna na saka su cikin aikin nan kuma ba a ma gama ba ballatana su yi mana payment amman dai na yi magana da su za su fara ba mu half ɗin in angama aikin sai su cika mana."   Ɗago kaina na yi ina kallon shi kafin na ce"To wancan payment ɗin na ku da suka ce tun wancan watan fa? Shuru har yanzu? Ɗan girgiza kai ya yi kafin ya ce"Wallahi kuwa. Kin san yanayin aikin namu ace yau a ce kuma gobe. Sai dai kawai ranar da muka gani ko jiya mun yi mgana da P.A ɗin kwamishina ya dai ƙara bani hakuri kin san sha'anin gwamnati sai haƙuri kawai."   Gyara zama na yi ina kallon shi kafin na ce" Allah ya sa su biya ku a wannan watan" ya amsa min da Amin Amin domin muna cikin bukatar kuɗi mganar asibiti na yi masa sai ya kalleni kafin ya ce" Ranar monday ne ko? Sai na shirya mu je taren ko? Sai na jinjina kai kafin na ce"Allah ya kaimu." Dukkanmu sai muka yi shuru hankalin mu kuma sai  ya koma kan TV ɗin da ya ke shi kaɗai tunda hankalimu ba shi a wajen gabaɗaya.   Har na sha'afa da mganar sai na tuna da sauri na kalleshi ina kiran sunan shi. "Yallaɓai na" "Uhm" "Ashe kuma Yaya Usman aure zai ƙara? "E. " Haka kawai ya ce mini ba tare da ya kalleni ba. Hankalinsa na kan kallo ni kuma sai na ƙara gyara zama ina faɗin" Shi ne ba labari kuma? "Labarin me? "Auran mana. Ko kai ban ji a bakin ka ba." Sai a lokacin ya juyo ya kalleni kafin ya ce"Bikin ya zo ne ba ki ji ba? Sai na girgiza masa kai jinjina kai ya yi kafin ya maida hankalinsa kan kallon shi lokaci ɗaya yana faɗin" Ba ma yanzu ba ne. Ina jin sai nan da wattani huɗu sai yarinyar ta gama karatun ta ta dawo tukunna za a yi bikin." "Au daman yarinyar ba anan take ba? "E. Ɗiyar ogansa ce a wajen aiki. Tana london ta na karatun masters ɗin ta amman ta kusa dawowa in ta dawo ne za a yi bikin." Ƙara matsan Yallaɓai na yi domin ina son na ji labari kai tsaye na ce" Ikon Allah. Kuma ya na sonta? Wannan karon wani kallo Yallaɓai ya yi mini da ya sa na yi shuru ina yar dariya kai ya girgiza kafin ya ce"Ban san wannan ba. Shi kaɗai zai iya amsa miki wannan tambayar.".   Ina dariya na ce"Kai ma za ka iya." Bai ƙara mgana ba sai na kwantar da kaina saman kafaɗarsa ina faɗin" Na yi mamkin da na ji zai ƙara aure. Duk irin yadda suke son juna shi da Anty Zabba'u.'' Yallaɓai dai ya lura da mgana a bakina sai bai biye mini ba sai kawai ya kallleni kafin ya ce" Uhm" Ina shafa kirjinsa na ce"Wallahi. An ce fa ta yi yaji ta na kano yanzu haka. Gaskiya ban ji daɗi ba. Kuma har yau shi Yaya Usman bai zo biko ba ya kyauta kenan?   Yallaɓai ya muskuta kafin ya cire ni daga jikinsa yana kallona cikin buɗe ido ya ce" Sadiya a ina kika ji wannan maganar? Kai tsaye na ce" Yau da na je gidan Halima ta ke faɗa mini fa. Ko ba a yi ba ne? Kai ya girgiza kafin ya ce"Ban sani ba. Domin ni a bakin ki ma na ji wannan mganar." Da sauri na ce"Au wai ba ka sani ba? An ce ko ba ta a fatakol. Ta dawo kano domin Halima ta faɗa mini bai faɗa mata mganar auran ba sai da aka saka rana da ta ji shi ne ta tada hankalinta ina ga dalilin yajin kenan." Ƙura mini ido ya yi yana kallona nima ko ina kallonsa ban damu ba na cigaba da faɗin" Gaskiya Yaya Usman bai kyauta ba. Bai kamata ya yi ma Anty Zabba haka ba an zama ɗaya an tara iyalai yayansu biyar fa aurensu sama da shekaru ashirin a ji Anty Zabba ta yi yaji saboda zai ƙara aure ai wallahi sai an zage shi duk da ban sani ba ai na san ba ta rage shi da komai ba. Wani lokacin ku Maza ba ku da adalci in za ku ƙara aure a ƙokarin ku sai duniya ta fahimci mace ta gaza ne ya sa kuke son ƙara aure" "Shi ya ce miki saboda Zabba'u ta gaza ne ya sa ya ke son ƙara aure? Ya katse mini mgana nima ko na taso masa da cewa" E mana saboda ya yi munafunci miye a ciki in ya na son ƙara aure da ba zai faɗa mata ba sai da mgana ta kamkama bayan ma an saka rana? A hankali ya ce" To ai Ogansa ne ya bashi yarinyar kuma akwai girmamawa a tsakaninsu shi ya sa ya karɓa". Mamakin Yallaɓai ya kamani yadda ya zauna ya na kare ma ɗan'uwansa..   "Duk da haka dai ai yana so ne ya karɓa shi fa namiji ba a yi masa dole Yallaɓai na. Kuma tun da har ya amsa me ya sa bai zo gida  sun tattaunawa da matarsa ba? Tsakani ga Allah bai kyauta ba a ce sai da aka saka rana ya ke gaya mata ko ni ce zan yi abin da yafi nata. Yanzu ta koma gida in an zauna ana mgana sai a ce saboda mijinta zai yi aure ta tada hankalinta ta kasa zaman gidanta ahalin abin ba haka ba ne shi ne bai kyauta mata ya yi mata rashin adalci bai kuma kalli zaman auren su na tsawon shekaru ba"   Yadda na ɗau zafi kamar ƙanwar Zabba'un abin ne ya ɓata mini rai ganin Yallaɓai na nuna abinda ya yi ɗin dai dai ne. Kallona kawai ya ke yi ya ina ta faɗa sai kawai ya juya ya jingina da kujera ya harɗe hannayensa a ƙirjinsa amman bai yi mgana ba sai ni ne da na gaji na kalle shi ina faɗin" Yallaɓai ba ka ce komai ba? Kai tsaye ya ce" Me zan ce! In yi mgana ki ce ina kare masa saboda yana ɗan'uwana ko in ce ita ba ta kyauta ba ki ce sabo da ni Namiji ne ko? Baki kawai na saki ina kallon Yallaɓai ganin kamar ya ɗau lamarin da zafi. Ban gama mamaki ba na ji ya na faɗin" Ke ba ki san abin da ya faru ba kin bi kin zauna akai har kina zargin wani bai kyauta ba a mata da miji ba ka jin bangare ɗaya ka yanke hukunci shin shi kin ji na shi ne! Kin san me ya faru tsakaninsu da ya sa ta yi yajin? Kuma ban yarda Yaya Usman bai faɗa mata ba sai dai in ita ce ta ƙi amincewa tun farko daga baya da ta ga abin da gaske ne sai kuma ta sauya labarin. Mganar yaji kuma ita ce ta ji kunya miye na ta na yin yaji? Auransu shekara ashirin ko sakin ta Yaya Usman ya yi gidan nan ya zama nata. Hakan da ta yi ta nuna cewa ba za ta iya rufa ma mijinta asiri ba ta gwamace ta koma gida ta fallasa komai domin a san halin da suke ciki a yi musu dariya kuma wallahi kanta ta rage ma ƙima in ma tana tunanin ta yi ne domin samun wata daraja ko ɗaukaka in ta yi hakuri wallahi tallahi wata ba za ta zo ta fita ba ba kuma ina kare masa domin yana ɗan uwana ba sai domin na san halin shi adali ne kuma jajircettace ai yana sonta ya aureta ba zai zama domin ta gaza ba ne zai ƙara aure sai domin auran na cikin kaddaran Rayuwansa"   Idona a kan Yallaɓai ganin yana ta rattabo mgana. "Hmm " Kawai na ce kafin na yi shuru shima shurun kawai ya yi yana cigaba da kallon shi ban sake mgana ba ina auna mganarsa a zuciyata ba wani saboda yana ɗan'uwansa sai kuma domin ya na Namiji amman ko Anty Zabba na da laifi shima Yaya Usman ɗin ya na da laifi ni ko kwana za mu yi anan wajen maganganun Yallaɓai ba za su sa na daina ganin laifin Yayansa ba. Haɗe rai na yi har ina matsawa can nesa da shi kallona ya yi kafin ya yi ɗan mirmishi ya na faɗin" Ni ban kare masa ba. Gaskiya na faɗa miki. Sannan ki cire wannan tunanin na in namiji zai kara aure wai gazawar ta gida ce ba haka ba ne saboda shi aure da mutuwa duk ɗaya ne ba ka sanin lokacin in Allah ya kaddaro maka ne ba yarda za ka yi amman ba nufin ta gida ta gaza ba."   Taɓe baki na yi kafin na ce" Haka kuke nunawa shi ya sa muka ɗauka haka ɗin ne." Na faɗa har ina hararan shi sai kawai ya yi yar dariya kafin ya ce"To ke miye naki a ciki! Tun da ba ni ne zan ƙara auren ba." Ina mele baki na ce" Da nawa a ciki tunda mace ce ƴar uwata kuma muna aure a zuru'a ɗaya." Kawai sai ya fara mini dariya na kalle shi ina faɗin" Na zama abar dariya ne? Hannu ya ɗaga sama kafin ya ce"Ko ɗaya gani na yi har matsawa kika yi daga kusa da ni. Ni ne Yaya Usman ɗin? Tabe masa baki na yi sai ya fara matsowa kusa da ni yana faɗin" Yanzu dai Yaya Usman bai yi ma Zabba'u adalci ba ko? Mata ban san me namiji zai yi ya iya muku ba. Auran su sama da shekaru ashirin bai yi tunanin ƙara aure ba sai yanzu. Da ace ya ce zai yi a farkon auren su sai a ce daga yin aure zai ƙara mata kishiya in ya bari sai ta ɗan sha miya sai a ce sai da ya ga ya sun gama wahala tare ya yi kuɗi zai saka mata da kishiya in kuma ya bari ta manyanta sai a ce ya ga ya gama moran ƙuruciyanta zai ƙara mata kishiya. Mara adalci butulu duk kalaman ku ne. Na rasa ko wani yanayi ne na kishiya zai taɓa zama dai dai a wajen ku.' Kafin ma ya ƙariso na yi saurin miƙewa ina faɗin"Ba wannan yanayin domin ba macen da ke son zama da kishiya. Ko a gidan Annabin Rahama matansa sun yi kishi ballatana mu."   Shima miƙewan ya yi yana yar dariya kafin ya ce" To wai an ya ni za ki bari na ƙara auran nan? Wata uwar harara na wurga masa kafin na ce" Ai na san ka na da ra'ayi. Allah ya ba da sa'a. Ta zo mana tunda ba kaina za ta zauna ba "    Na yi wucewata na barsa nan tsaye sai ya biyo ni yana dafani kamar irin yadda ƙawaye ko abokai suke yi "Ba yanzu ba. Sai na zama mai kuɗi lokacin kin zama Gwaggo sai na auro yar shilla mu ƙarishe rayuwarmu tare ko? Da gwiwan hannuna na tokare masa ciki ya yi gefe yana dafe cikinsa fita na yi daga falo ina mai buga masa ƙofa. Bai biyo ni ba sai da ya tsaya ya kashe kayan wuta gabaɗaya ni daman ɗakin yara kawai na leka na ga sun yi barci sun bar wuta akunne Jidda ta bar littafanta nan ƙasa barci ya ɗauke ta. Ta shin ta na yi ta koma saman gado ni kuma sai na kwashe littafanta na ɗora mata saman drower ɗin su na tashi Baby ta je tiolet ta yi fitsari sannan ta dawo na kwantar da ita na sake tofa musu addu'a na kashe musu wuta na rufo ƙofar ina fitowa muka haɗe da Yallaɓai na dauƙe kai na ƙarisa wajen makashin wuta na kashe duhu ya bayyana. Na ji takunsa ta baya na ban anƙara ba na ga ya ɗagani sama yana nishi nishi. Wuntsila kafa na fara ina faɗin" Ni ka sauke ni"   Na faɗa ina tura masa baki,  shi kuma ya na faɗin" An ki ɗin" Wuntsila kafa na yi da sauri muka yi baya kamar zamu faɗi shi ya sa ya sake ni yana dafa bango. Dariya na saka masa saboda akwai duhu har bayansa na bige bango. "Wassh.." Haka ya faɗa, ni kuma sai na kwashi gudu ina jin sa ya na faɗin" Sadiya ki tsaya anan wajen." Ƙofa na buɗe na gudu bedroom ɗin mu ina faɗin" In kana da karfi ka kamani.".   Ina shiga na kashe hasken ɗakin duhu ya bayyana ya na shigowa ya fara kiran sunana ni kuma ina danne dariyata. "Yarinya in na kama ki za ki sha wuya fa." Motsina ya ji ya fara laluɓata ina gudu muna zagayen gado daga karshe mune har saman gado. A ƙarshe dai Yallaɓai ya yi nasaran kamani ina ta dariya gabaɗayanmu muka baje kan gado muna sauke numfashi. Muna kuma kallon juna acikin duhun ɗaki ni ce na ganganra na hau jikinsa na rike masa duka hannuwansa biyu na duka ina sumbatar bakinsa. Shima ya na tayani daga karshe. Da ya ke ya fini karfi tuni ya ƙarbi ragamar lamarin ya mirgina da ni na dawo ƙasan sa shi kuma ya kama ni a hannu tuni muka lula cikin irin ta mu kyakyawan duniya ta ma'aurata irin mu masu marmarin juna da muradi a kullum.    ***** Washegari ta kama jumma'a ne. Yara sun tafi makaranta Yallaɓai kuma an kira shi ya fita office tun safe sai ni kaɗai a gida. Tara na safe Saude ta zo yau gyaran kitchen na ke jin yi sai na ce ma Saude ta gyara sauran ɗaku nan ni kuma sai na gyara kitchen. Ina can ina gyaran wayata na ɗaki ana ta kira ban sani ba. Da ya ke Saude iyakarta gyaran falon farko da na biyu sai ɗakin yara da kitchen sai wanke tiolet ni na ke gyara ɗaki na da kaina sai haraban gidan bayan kwana biyu ko uku haka. Ni na ce ta shiga ɗakin da na ke sauke baki da ke kallon Bedroom ɗina ta gyara mini sai ta ji kamar ana ta kiran wayata sai ta ruga kitchen ta na cewa" Anty na ji kamar ana kiran wayarki a ɗakin ki." Sai na sauke Towel din da nake goge gogen na nufi cikin ɗakina sanye na ke da riga doguwa amman iyakarta gwiwata da kaɗan kwalliyar safen da na yi ma Yallaɓai ne kafin ya fita. Ina zuwa na ɗau wayata da ke saman gado na yi mamakin ganin kiran Ya Auwal har sau uku shi da kira ɗaya ya ke yi shi da Yaya Hamza in kin zo kin ganni sai ki kira su daga baya ganin kiran sa har uku sai na ji tsoro ina shirin bin bayan kiran shi sai kuma ga kiran shi ya sake shigowa da hanzarin na ɗaga.   "Yaya Auwal" Haka na faɗa cikin fargaba daga can bangaren da sauri na ji ya ce"Sadiya kina asibitin ne? Ya jikin Alhajinmu na mu? Cikin mamaki da rawan baki na ce" Wani asibiti ku. Kuma? Alhajinmu ba shi da lafiya ne? Cikin mamaki ya ce"Ba ki sani ba! Dazun nan Yaya Abubakar ya kirani ya ce Gwaggo ta kira shi a ruɗe Alhajinmu ya faɗi. To mun sake mgana ya ce ga shi sun isa asibitin mun rabu kan zai sake kirana amman shuru kuma na yi ta neman layin sa ban samu ba." Cikin tashin hankali na ce"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un. Wallahi ban sani ba. Ba wanda ya kirani Ya Auwal." "To ki yi maza ki shirya. Ki kira ki wayar Gwaggo ki ji asibitin da suke kin ji ko? Sai na amsa masa shima ya ce daman suna shirin tahowa ne da ya bari sai gobe asabar amman tunda ga wannan matsalan suna nan tafe in sha Allahu. Muna gama mgana hankalina tashe na kira wayar Gwaggo ba ta ɗauka ba sai na kira ta Yaya Abubakar amman ba ta shiga ba sai na kira Rahila ita na sameta abin mamaki suna asibitin tare da Ya Muntari shi ta ba ma wayar ma ya faɗa min asibitin da suke. Hankalina duk ya tashi Alhajinmu na da hawan jini amman ya daɗe bai tashin masa ba sama da shekaru biyar. Bayan rasuwan Mama ne ya kamu da hawan jinin. A gaggauce na yi wanka na shirya na kira Yallaɓai ina faɗa masa ya ce gashi a hanyar Rano amman zai dawo da wuri mu haɗu a asibitin. Saude na bar ma gidan na ce ta dafa musu sauran taliyan da ta rage ita da su Jidda. Ta kuma tsare min gida har in dawo Alhajinmu ke asibiti ba lafiya. Cikin yar damuwa ta ce" Sai kin dawo Anty. Allah ya bashi lafiya" na amsa mata da Amin tsabar sauri sai da na fita na tuna jakar da na ɗauka ba kuɗi a ciki sai da na koma na sauya wata jakar fitar ta sauri ce kayan jikina doguwar rigar atamfa ce sai na saka dogon hijabi Jalbab. Adaidaita na tara zuwa asibitin na kuɗi ne ban ƙara razana ba sai da na kira Rahila ta ce suna Emergency a firgice na tambaya aka kwanta ta mini Duk da ina cikin firgici na yi mamakin ganin kaf ƴan gidanmu a wajen kowacce da mijinta har da Ma'u Alhajinta da su ake shiga ana fita. Yaya Aina ce kawai ba mijinta a wajen amman har da Mijin Yaya Balki da na Yaya Murja. Yaya Abubakar da zaituna suna wajen. Ga Rahila ga Ya Muntari. A ƴan ɗakin mu ba kowa tunda Amina na kaduna ƙila ba ta sani ba ni ce kuma a cikin su ba wanda ya kirani amman sun iya kiran Ma'u saboda tsabar munafunci.    Raina ya ɓaci da haushi shi ya sa daga su har mazajen na su ba wanda na ce ma sannu. Ina ji Rahila na kiran sunana na wuce zuwa in da Gwaggo ke zaune na duka ina gaisheta ta amsa min cikin kulawa da casabaha a hannunta. "Ya jikin Alhajinmu Gwaggo? Kai tsaye ta ce" Da sauƙi sun ce jininsa ne ya yi sama sosai nunfashin dakyar ya ke fita amman sun saka masa Oxygen yanzu ba daɗewa." Ido na zaro ina faɗin" Innalillahi." Sai tadafa kafaɗata kafin ta ce"Ki kwantar da hankalin ki in sha Allahu Alhaji zai tashi."   Sai na jinjina mata kai ina maida kwallar da ta kawo mini mutuwar Mama kawai na ke tunawa. "Gwaggo shi ne ba a samu wanda zai kirani ya faɗa,mini ba? Yanzu ɗin ma ba domin Yaya Auwal ba da ba zan sani ba kenan? Cikin lallashi da damuwa ta ce" Ki yi hakuri hankula a tashe suke. Abubakar kawai na kiran suma yan'uwan na ki ki yi musu usuri sun shiga ɗimuwa" Sai ban ce komai ba amman a raina na ce a dimuwan aka kira wanda ake so.   Ba bari a shiga in da Alhajinmu ya ke Yaya Abubakar ne kaɗai da su Ya Muntari ke zirga zirga. Zama na yi kusa da Gwaggo ba wacce ma na kallah balle in yi mata sannu har Yaya Abubakar ban gaisar ba sabida ya bani haushi har da ya ganni ya na ce min" Ke sai yanzu kika iso? Cikin gatse na ce" E. Sai yanzu aka faɗa mini" Hankalinsa ya yi can bai ma jini ba Rahila ce ta zo ta zauna kusa da ni muka gaisa Yadda ta ga na haɗe rai ne ya sa ba ta jani da magana ba. "Hala Yallabai baya nan ne? Kai tsaye na ce"Lokacin da na ji labarin abin da ke faruwa ya fita" Sai ta yi shuru kafin can ta ce"Ki yi hankuri ni kaina hankalina ya tashi na manta da kiran ki." Wani kallo na yi mata amman ban iya mgana ba. Muna nan zaune jugum jugun har wajen azahar sai da aka cire ma Alhajimmu iskar Numfashi tun da sun ce numfashinsa ya daidai ta. Sannan suka maida shi ɗaki na musamman da Mijin Ma'u ya biya duk na ji Yaya Abubakar na faɗin Yaya Hamza ya turo kuɗi shi da Yaya Auwal amman kuma mijin Ma'u ya biya komai. Ina kallo suna ta yi masa godiya su Yaya Murja har tana faɗin" Allah ya saka masa da alheri ba domin alherin Ma'u a gare shi ba yaushe har zai riƙa yi mana Hidima haka? Ma'u ƙi kara yi masa godiya kin ji ko" Sai ta amsa da toh kawai. Ban yi wani mamaki ba sanin halin su balle Yaya Murja akwai son abin duniya ita kuma Ma'u in ta fahimceka ta san yadda za ta riƙe sosai. Sai bayan an kai shi ɗaki na musamman ne aka bar mu muka shiga yana barci amman Alhajinmu duk ya rame ya faɗa. Daga gani ya daɗe da ciwo a jiki bai faɗa ba an ce mu bar shi ya samu hutu sosai sai muka fito dukkanmu zuwa kofar ɗakin muka zauna saman kujerun wajen. Mijin Ma'u ya yi ma Gwaggo sallama zai tafi ita kuma ta tafi raka shi. Sai bayan sun wuce ne Ya Balki ta kalleni taba faɗin" Sadiya ya gida? Ɗazu kin zo hankula ba a kwance suke ba ba a gaisa ba." Sai na ɗan saki fuska muka gaisa buɗe bakin Yaya Murja sai cewa ta yi" Duk da haka ta ganmu amman ta fi ƙarfin ta ce mana sannu." Nima sai na kalleta kafin na ce"Saboda me zan ce muku sannu? Kun ware ni a cikin dangi ba wacce ta iya kirana ta faɗa mini halin da ake ciki sai Ya Auwal dake Abuja ne ya kirani ya faɗa mini. " Yaya Balki ta ce"E ba a kyauta ba to ki yi hakuri. Nima Ma'u ce ta kirani ta faɗa mini ta ce itama Yaya Murja ce ta faɗa mata.'   Shekeƙe na kalle su kafin na taɓe ba ki na ce"Ai da ya ke Ma'u ce ake son ta sani an kirata an faɗa mata ba shikenan ba." Rahila na taka min kafa wai in yi shuru cikin masifa na ce"Sai kin ƙi faɗan gaskiya! Wa na ke tsoro? Gwaggo ba ta nan ta na ciki wajen Alhajinmu. Ya Muntari ne a wajen ya kirana sunana ya na faɗin" Asibiti ne fa nan ba gidan biki ba. Ku bari ku koma gida mana." Yaya Murja kuma sai ta taɓe baki ta ce"To daman ai mun san baki tsoron kowa mara kunya. Hassada ce da kishi saboda ta ga Ma'u ta riga ta zuwa. An ce ki yi hakuri kuma sai ki na neman gaya mana mgana" Anty Aina ta tsawatar ta ce a bar mganar ni ko ba na barin ta kwana na ce"Allah ya tsari Sadiya me Ma'u ta mallaka a duniya nan da ni ban da shi sai na yi mata Hassada! Ai ba ta kai ba tukunna dai."   "Zan fa ci ubanki Sadiya ni ba tsaran ki ba ne wallahi." Zan sake mgana Anty Aina ta daka min tsawa ta na faɗa min" Wai ba na ce ki yi shuru ba ne Sadiya? Kaina na kawar gefe ina kaɗa kafata cikin bacin rai. Yaya Balki ta ce"Ita Yaya Murja saurun fusata  ita kuma Sadiya rashin kunya. Alhajinmu na kwance ba lafiya ma ba za su fasa ba." "Ba za su fasa ? Me ya faru? Yaya Abubakar ya faɗa yana ƙariso wajen tare da Ma'u sun jero Ba wanda ya yi mgana sai Zaituna.   "Sadiya ce da Anty Murja suke cacan baki." Yaya Abubakar ya kalleni ya kalleta kafin ya ce" Me ya faru? Anty Balki ce ta maida masa yadda aka yi kawai sai ya juyo yana kallona kafin ya ce" Ni ne nan na kira Murja na faɗa mata na kuma ce ta kira Ma'u da sauran ta faɗa musu. Tun da sun ce ki yi hakuri sun yi kuskure ba shike nan ba? Ko ke shikenan ba a baki hakuri ki hakura? Ko kallonshi ban yi ba sai da na ji ya ce"To kar ma ki fasa. Ke daman ba ki son zaman lafiya ko da yaushe cikin ƙananun mganganu kike." Ɗagowa na yi ina kallonsa cikin ɓacin ran dake cikin idanuwana shi kuma sai ya juya yana ma Ya Muntari mgana.   "Ka na ji suna hayaniya ba ka tsawarta musu ba? Kai tsaye ya ce" Na yi mgana sun ki ji shi ya sa na kyale su. " Kawai sai ya juya ya na kallona kafin ya ce" Duk wacce ta san hayaniya ya kawota ta tashi ta ƙara gaba. Mu lafiyan mahaifimmu muke nema ba tashin hankali ba." "Ka yi hakuri ya Abubakar. Sadiya kema don Allah ki yi hakuri. Har ni na kira wayarki ba ta shiga." Ma'u ta katse surutun na shi. "To kin ji ma." Ya faɗa ya na kallona dakyar na iya danne ɓacin raina na kalli Ma'u ina faɗin" Ya wuce." Sai ta yi mini mirmishi na mayar mata da yake. Kusa damu ta zauna amman gefen Rahila. Shuru kawai na yi ina danne yanayina ni fa daman da Yaya Murja da Yaya Abubakar haushin su na ke ji tun kan abin da ya faru. Kuma har gobe na san suna bayan Ma'u ne. In da suka ijiyeni nima nan na ijiye su.   Kiran wayar Yallaɓai ya sa na tashi na bar wajen. Yana tambayanta ya jikin Alhajinmu na faɗa masa da sauki da yadda ake ciki. "Allah ya ƙara sauki muna idar da sallar  jumma'a zan taso kin ji ko? Ban da damuwa ok? Sai na gyaɗa masa kai kafin ya cigaba da faɗin" Yara fa! Ina kika kai su? "Suna gida tare da Saude." Sai ya sauke numfashi kafin ya ce"Sai na dawo." Da haka muka yi sallama. Ganin har azahar ta yi sai na fita haraban asibitin na tambayi wata nurse masallaci sai ta nuna mini. ga mata nan suna alwala mazan dai ina ga waje za su fita su samu sallar jumma'a nima sai na bi bayansu na yi alwala muka shiga masallaci na yi sallah na zauna ina addu'o'i bayan na shafa sai na kira wayar Amina sai ta ce minI ita Yaya Aina ta kira ta faɗa mata mijinta baya nan amman in ya dawo in sha Allahu suna tafe gobe na ce Allah ya kaimu. Muna waya Khaleesat na kirana bayan na katse sai na kirata jikin Alhaji ta tambaya na ce da sauƙi ya na barci ita ke faɗa min suna hanya na yi musu fatan isowa lafiya. Na daɗe a masallaci sai da Rahila ta kirani ta ce ko na tafi ne? Na ce a" a ina masallaci. "Oh mu ai nan muka yi tamu sallar. Ki zo ga su Baba Aminu  nan sun iso." Sai na ce mata gani nan zuwa. Ji fa har mutanen jihar katsina sun ji labari sun iso amman ni ana raina min wayau. Kuna ina da tabbacin cikin su ne wata ta kira su ta faɗa musu. Na fito daga masallacin zan wuce bangaren dakin da Alhajimmu ya ke na ci karo da Baaba Asiya ta na ta neman ɗakin kamar ma ta na kiran waya ne ƙila Ma'u take kira sai na ƙarisa wajenta ina faɗin" Baaba." Sai ta juyo ta na kallona fuskarta kadaha kadahan kamar yadda muka saba karɓan juna tun bayan faruwan rushewar auran Ma'u da Yaya Hamza da na zama ni ce sila." "Yauwa. Ma'u bari ma ga Sadiya na gani." Daga haka ta katse wayarta. Da yar jaka a hannunta da kayanta a ciki. "Sannu da zuwa Baaba" "Yauwa dai." Sai na mika hannu zan karɓi jakar sai ta hanani ta wuce gaba tana faɗin" Ina ne ɗakin da aka kwantar da Yaya Sulen? Ban damu ba na wuce ina faɗin" Ciki ne." Ba tun yau ba ni na san ta tsane ni ita da yarta. To nima dai ɗin ba wani son su nake yi ba shi ya sa ban taɓa damuwa ba matar da na san ba ta ƙaunar uwata ina zan taɓa ganin farinta. Ta bakin Hajiya Dubu da ke yawan faɗin" Asiya ki daina wannan dabi'un naki karki tsufa kuma tsufar ta zo ta yi miki gardama." Allah ya jiƙan Hajiya Dubu da gafara. Mutuwarta da mutuwar Mama sai nima na mutu  zan iya mantawa da su.     Muna tafe ina gaba ta na baya har zuwa ɗakin da Alhajinmu ya ke. Baba Aminu ne ashe da Baba Sani suka zo. Ma'u na ganin uwarta ta yi wajenta tana mata barka da zuwa. Ban ƙara ta kan su ba na isa wajen su Baba Aminu ina gaishe su. "Lafiya lau! Dubu ce? Sai na ansa musu domin kaf gidan su Alhajinmu ba mai kiran sunansa sai dai Dubu saboda na ci sunan Hajiya Dubu ce kuma ita ɗin mai Daraja ce ta matsayin uwa a wajen su.   Da ɗaya da ɗaya likita ya ba su izinin shiga su ga Alhaji. Da suka fitio ne na ji Baaba na faɗin Yaya Sule ya ya ɗan farka yana ta mganganu har yana kiran sunan Ruƙayya Gabana ya faɗi Mama kenan fa. Kar shima dai Alhaji tafiya zai yi ya bar mu? Likita ne ya ce daga yanzu ba wanda zai sake ganinsa sai dare a barshi ya huta.   Kowa ya ji labari amman ban da Datti na ce aƙyale shi saboda suna da test kar mu ɗaga masa hankali. Ma'u ta kira gida yar aikinta ta yo abinci direba ya kawo tare da Zainab. Dukkanmu ba wacce ta koma gida sai Zaituna da mijinta ya ce ta koma gida Gwaggo ma sai bayan la'asar da su Baba Aminu suka matsa sannan ta yarda Yaya Abubakar ya ɗauketa a mashin ɗinsa ta koma gida ta yi wanka sannan ta ɗauko ma Alhaji wasu kaya ruwan zafi da kayan Tea Ma'u ta saka an kawo. Abincin da ta kawo shi kowa ya ci amman ban da ni. Har su Baba Aminu shi suka ci Rahila ta ce ba zan ci ba na ce ta san ban iya cin wani abu a asibiti.   Wajajen biyar Yaya Hamza suka iso tare da Khaleesat da yayansu Amna da Tasleem. Ba daɗewa tsakani sai ga Yaya Auwal da Anty Laila suma sun iso asibtin diret ko gida ba su je ba sai da suka leƙa Alhajinmu suka ganshi sannan hankalinsu ya kwanta. Yaya Auwal yana zuwa ya ba da kuɗi aka siyo kata  katan ɗin ruwa da lemuka. Ya yi kuma oder abinci na dare tunda muna nan ba wacce ta iya koma gida sai Gwaggo. Ita kuma a can gida Yaya Abubakar ya siya anta ya kai mata za ta dafa ma Alhaji tunda sun ce yana bukatar cin wani abu mai ruwa ruwa haka. Yallaɓai na ji sa shuru har bayan mangariba sai da na kira sa ya ce bai dawo da wuri ba ne.  Zai je gida ya yi wanka sai na ce ya taho da su Jidda tare da Saude asibitin ya amsa min da toh. Gabaɗayanmu muna asibitin har sai da likita ya yi mana tsiyar Alhaji ba zai mutu ba zai ta shi mu je gida hakanan saboda sun ga zugan ne da yawa.   Tare da Alhaji Mustapha Yallabai suka shigo wajen da muka zazzaune. Kowanne da leda su Jidda na baya Yallaɓai dai kayan lambu ya siyo shi kuma mijin Ma'u ban sanin masa ba. Su dai an bar su sun shiga duba Alhaji ya farfaɗo da sauki wannan karon har sun gaisa ya ce ina yan matansa Yallaɓai ya ce suna waje suma sun zo duba megidansu.   Ganin ya farfaɗo da sauki sai likita ya ce mu shiga gabaɗaya mu duba shi amman da sharaɗin ban da hayaniya kuma muna dubashi mu fito mu tafi gida. Haka ko aka yi ɗaya bayan ɗaya muna ƙarisa gaban gadon shi muna gaishe shi yana amsawa ga jikokinshi kusa dashi Jidda har ta na bare masa ayaba ta nufi bakin shi tana cewa" Alhaji ga ayaba." Aka saka dariya Baba Aminu na cewa" Ka ji min ja'ira tun ɗazu ta ganni amnan ba ta bare min ayaba sai Yaya Sule dake kwance rai ga hannun Allah."   Su dariya mu ma muna ta dariya Alhajinmu ya buɗe baki ta saka mai sai da ya haɗiye sannan ya ce"To ai ta ga duk yinii yau ina kwance ban ci abinci ba. duk ta fi min sauran matan nawa ita maimuna ban ma ganta ba " Yana mgana sai ga Gwaggo ta shigo ta na faɗin" Gani nan na zo. Wace ce ta zo za ta yi min fashi miji." "Gani nan. Tunda kin yi tafiyarki kin bar shi."   Jidda ta faɗa ta na mirmishi gabaɗaya aka kwashe da dariya ban da Baaba da ke wani taɓe baki kamar ta ga kashi. Yaya Hamza ya ce" Ai sai ba ɗiyar Sadiya ba." Anty Aina ta karɓe da faɗin" Ai Baby ce Sadiya sak. Jidda kuma Yallaɓai ce ba ta da hayaniya"   Likita ne ya zo ya ce dubiyar ta isa haka kowa ya fita shi ya sa muka yi ma Alhaji sallama muka fito. Khaleesat na haɗa da Saude tunda can gida za su kwana na ce su wuce mini da ita. Ina jin Ma'u na neman yan kwana a gidanta ba ta samu ba Anty laila yar kano ce amman nan gida ta ce min zata kwana Baaba dai ban sanin mata ba na dai ganta da yarta suna ƙuskus.  Baba Aminu daman gida ne Baba Sani ne aka bari zai kwana da Alhajinmu Yaya Abubakar ya so ya je gida ya Huta ya ce miye amfanin shi? Shi zai zauna ya kwana har a sallami Alhaji.   Wajajen tara muka bar asibitin Gwaggo a motar Ya Auwal. Shi Yaya Abubakar ya ɗauki matarsa a mashin dinsa ita kuma Rahila ya Muntari shima yana da mashin Baaba kuma a motar mijin yarta ni kuma a motar Yallabai ni da Ya'yana. Mun yi sallama gabaɗaya Yaya Murja ta riga tafiya daman da megidanta ya dawo suka tafi tare Anty Aina ma mijinta na da wata tsohuwar benz shi ya zo ya ɗauketa.   Sai goma saura muka shiga gida yunwa na ke ji ya sa Yallaɓai ya siya mini tsire a hanya da lemu sai ya siya biredin da zamu ƙarya da shi da safe in Allah ya kaimu. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SSADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* *🅿️10* Tun da na tashi da safe na fara tunanin wani abinci zan dafa na kai ma Alhajinmu. Gashi kayan abincin mu duk sun ƙare kuma Yallaɓai har yanzu bai ce mini komai ba. Da safe ma Tea muka sha shima kayan tea ɗin saboda ya na yawan siyan shi ne ba sai ya ƙare ba shi ya sa shi ya kan zama na ƙarshen ƙarewa.   Na daɗe ina tunanin abin da zan yi. Kafin na tsaida shawara yin tuwon shinkafa miyar agushi tunda shinkafar tuwon kaɗai gare ni. Sannan ina da kayan miya nikaƙƙe a frizer sauran kayan cefanen ba zai gagara ba. Tun safe na kira wayar Ya Auwal mun yi mgana ya ce sun je ma asibitin sun duba Alhaji da safe jikin sa da sauƙi ya na ta barci sun ɗan dawo gida su karya ne sannan su koma  ni ma na ce in na gama abin da na ke yi zamu zo asibiti tare da Yallaɓai in sha Allahu. Yana falon farko ya na aiki na je na same shi na faɗa masa ina so zan yi ma Alhajinmu girki in za mu je mu tafin mai dashi. "Me za ki dafa masa? Ya faɗa ya na ture takardan gabansa lokaci ɗaya yana kallona. Kai na rausaya kafin na ce" Tuwo zan yi masa miyar agushi. ". Kai ya jinjina mini kafin ya ce" Kina buƙatar wani abu ne? Kai na gyaɗa kafin na ce"E. Ina son Nama da ganda. Sai ganyen Ogun ina da sauran stock fish da agushi ɗin."    Sai ya gyaɗa min kai kafin ya ce" Shike nan. Zan yi ma Musbahu waya sai ya siyo ya taho dashi." Duƙawa na yi na sumbaci bakinsa kafin na miƙe ina faɗin" A huta lafiya Yallaɓai na." Kai ya jinjina min yana ɗan mirmishi fita na yi daga falon bayan na rufe masa ƙofar saboda zane ya ke yi ba ya son hayaniya ɗakin su jidda na shiga ba hasken sai da na kunna dukkansu suna kwance suna barci ga darduman da suka yi salla nan da azkar din su ko kwashewa Jidda ba su yi ba ban tashe su ganin yau asabar kuma suna hutun Tahfeez ya kamata su huta tattara kayan na yi na maida shi a muhallin shi sannan na gyara ma Baby kwanciya ita kuma Jidda na zare mata Hijabin jikinta ganin da shi ta kwanta. Sake kashe musu hasken ɗakin na yi bayan na rage musu iskar fankar a hankali na rufe ƙofar kar ƙara ya tashe su.   Tuwon na kunna gas na fara ɗorawa. Saboda ina so mu fita da wuri duk da za mu fara biyawa ta Gwammaja mu kai su Jidda sannan mu wuce asibitin. Ɗaki na koma ina gyarawa saboda Yallaɓai ya ce na haɗa kayanmu waje ɗaya mai wanki zai zo ya ɗauka sai na firfito da kayan ina haɗawa. Ni kaya ba su da yawa atamfofi ne da lesuna ƙananun kayana ni na ke wanke su da kaina in na samu lokaci tare da unders ɗin Yallaɓai na na yara kuma ba su taru ba ko sati biyu ba a yi da kawo musu wanki ba. Bayan na gama haɗa kayan na saka su cikin ghana must go ɗin da daman saboda kai wanki ne in kuma za a dawo dasu a ciki ne a goge. Gyara ɗakin na fara saboda ya ɗan yi ƙura, sai na fara tunanin unders ɗin Yallaɓai duk sun yi datti ya kamata na wanke masa. Amman sai na duba ya na da sauran wankakku zan bari in Alhajinmu ya koma gida ya samu natsuwa sai na yi mana wankin. Allah ya sa ma ya na da su da yawa tun da in na samu kuɗi ina siyan masa da turaruruka in yi masa kyauta a matsayinsa na mijina.    Ban ma gama gyaran ɗakin ba na koma kitchen na wanke shinkafar na saka kafin ma ya tafasa saboda in ya jiƙu ya fi danƙo. Ƙara komawa ɗakin na yi na gama gyaran na ɗauko abin shara na share sannan na ɗauko towel ɗin goge na gege madubi da jikin wardrope ɗina tunda ya na da glass. Sai kawai na ji yau gwara na yi aikin gidan tunda ba ma nan kar na ba ma Saude wahala tuna haka ya sa na ɗau waya na kira Sauden tun da ni na siya mata wayar saboda matsala irin haka bayan mun gaisa na ce yau ta yi zamanta ba sai ta zo ba sai ta ce mini toh.   Ina tuwona ina aikina. Ban share falon farko ba saboda Yallaɓai na aiki amman gabaɗaya na share gidan na yi mopping sannan na turare gidan da turaren wuta na kajiji a burner. Kitchen kuma ma bari sai na gama girki gabaɗaya. Sai da na tuƙa tuwon sannan Jidda ta taso ta na murza ido ta ganni ina fito da sabbin kolilina in da zan saka abincin. "Ina kwana Umma." Na waiwayo ina faɗin" Lafiya lau jidda. Ina Baby ba ta tashi ba ne? Ta na murza ido ta ce" Ta na wajen Abba" Sai na gyaɗa kai ina faɗin" Akwai ruwan zafi a flasks a saman dining ni da Abbanku mun ƙarya. " Ta na kallona ta ce" Umma ba ki tashe mu ba to? Ina kai kololin wajen sink ina faɗin" Na ga yau weekend sai na barku ku huta. In kun gama karyawan ki yi ma Baby wanka tare za mu fita. Gwammaja za mu kai ku ku zauna har dare." "Umma ya jikin Alhaji? Na ce mata da sauƙi ina ƙokarin fara wanke kololin sai ta ce in kawo kallonta na yi ina faɗin" Ki je ku karya. In gama aikin sai ki wanke sauran ki gyara mini kitchen ɗin" sai ta amsa da toh sannan ta wuce. Ni kuma bayan na wanke su na saka Towel na goge su tas sannan na kwashe tuwon a leda na ƙulla. Wajen guda goma na saka a kula sauran kuma guda huɗu na bar mana a gida in mun dawo mu ci ban ɗora miyan ba tunda har lokacin musabahu bai zo ba.   Ban ko kai ga barin kitchen ɗin ba sai ga Jidda da leda ta kawo min ina karɓa na kalle ta ina faɗin" Uncle Musbahu ya zo ne? Sai ta gyaɗa min kai. Ijiye ledan na yi na koma ɗaki na sako hijabin na fito falo in da suke da Yallaɓai muka gaisa. "Anty Sadiya ya jikin Alhaji? Yallabai ke faɗa min bai ji daɗi ba? Sai na amsa masa shi kuma sai ya yi masa fatan samun sauƙi na amsa da Amin Amin nan falon na bar su na koma ciki Ina ce ma Jidda in sun gama karyawan ta gyara ɗakin su kafin ta yi ma Baby wanka.    Da ya ke miyar ba ta da yawa sosai ba ta ɗau lokaci ba tunda agushin ma soya shi kawai na yi. Naman kuma na rago ne akwai ƙashi ƙashi a jiki sai da na tafasa sannan na yi amfani dashi kafin ka ce me gida ya ɗau kamshi miya. Na gama ɗiban ma Alhajinmu miya na saka a kula har na haɗa shi cikin kwandon da za mu tafi dashi sai ga Yallaɓai ya shigo kitchen ɗin. "Ni fa an gama cika mini ciki da ƙamshi. Me muka samu ne? Ya faɗa ya na tsaye a ƙofar kitchen ɗin. Kallonsa na yi kafin na juya ina goge jikin gas ɗin da miya ya ɗan ɓata.  Mirmishi na yi kafin na ce"Sai anjuma za ka ci na ka fa Yallaɓai." Koƙarin shigowa ya ke yi na wurgar da abin hannuna na nufe shi ina turashi waje lokaci ɗaya ina faɗin" Mu je ka yi wanka lokaci na tafiya."   Ba shi da mafita haka na riƙa tura shi har cikin bedroom ɗin mu. Takardun hannunsa na karɓe ina faɗin" Mai wankin bai zo ba? Ya na saɓule dogon wandom jikinsa ya ce"Sakarai ne. Na fa kira shi ya riƙa ce mini yana hanya amman sama da awa ɗaya bai zo ba" Ina dariya na ce"Kai da Sabitu ba" saboda suna shan dirama shi Sabitu karya da saɓa alƙwari shi kuma Yallaɓai ba ya son mutum mai ƙarya da saɓa alƙwari. Su yi ta samun matsala kuma ko ya ce ba zai ƙara bashi wanki ba sai Sabitu ya yi ta magiya domin ya na samun alheri a wajen Yallaɓai. Cikin side drower na ijiye masa takardunsa ina juyowa muka ci karo da Yallaɓai fuska na kwabe kafin in yi mgana ya rumgumeni ni kuma ina ture sa na ce"Ban yi wanka ba Yallaɓai."   "Nima ai ban yi ba. Kawai yau mu bar ta ranar tsami na duniya ne."   Ina dariya na rumgume shi ta baya ina ɗan dukan bayan shi mun daɗe a haka kafin mu saki juna hammatar shi na ɗaga tunda bashi da riga ina rufe baki kafin na ce"Yallaɓai na na bukatar shaving gaskiya."   Hannuwansa ya ijiye saman kafaɗata yana faɗin" Sadiya ta sangarta Yallaɓanta. Ki zo kawai ki yi aikin ki Madame.'" Dafa kafaɗansa na yi shima ya dafani muka fara tafiya ina faɗin" Muje Tiolet na gyara mijina." Kallona ya yi ƙasa ƙasa kafin ya ce"To wai da na ce ko ni na fara gyara ki anan ne a ciki kuma ke sai ki gyara ni? Ina jin haka na sake shi na yi gaba ina faɗin" bar shi kawai. Na gode Cafinter"   Sai ya biyo ni yana dariya har ya na cewa" Wai kada mu yi ta asaran ruwa. Gwara mu haɗa aikin." Ko juyawa ban yi ba na buɗe kofar tiolet na shiga bayan na yi addu'a shima sai ya biyo bayana zai shigo na ce" Yallaɓai addu'ar fa" Sai ya koma da sauri ya yi sannan ya shigo ya maida ƙofa ya rufe zai yi mgana na masa alama da bakina na ja zif alamun ya yi shuru sai shima ya yi haka alamun ya kama bakin shi mirmishi na yi masa kawai Towel na zaro daga hanger dake sama na mika masa sai ya karɓa ya juya yazare gajeren wandon da ke jikinsa ya ɗaura towel ni kuma sai na ciro veet din a saman wajen ɗan dirowan ajiye su kayan wanka a cikin sink na ce ya shiga ya zauna kamar dai yadda muka saba.   Ni na shafa masa a ƙasan sa da hammatarsa sannan bayan minti biyar ya yi na kwashe na goge wajen sannan na wanke masa. Tare muka yi wanka ranar bayan na chuɗasa nima sai ya chuɗani muna yi muna ɗan wasannin mu da muka saba cike da so da ƙauna muka fito dukkanmu ɗaure towel shi a kugunsa ni kuma asaman ƙirjina.   Yallaɓai na fara tayawa ya shirya cikin shadda mai ruwan ƙasa domin ya ce min suna da ɗaure aure na wani abokinsu da suka yi secondary tare zai ƙara aure. Ina saka masa link ina faɗin" Har da Uncle Abba zai zo daurin auran? "E. Har da ma Tariq. Muhammad Bello ai ajin su ɗaya ma da Tariq lokacin muna makaranta."   Sai na jinjina kai kafin na ce"Abokan ku sun fara biyu kuma kuna hanya kenan" Ya na yar dariya ya ce"Wasu ma ko ɗayan ba su ijiye ba. Irin su kawu ba. Da wani Salihu bala wallahi sun zame mana tazuran kawai. Yau ina ga yau sai sun sha caccaka tun da kaf mate ɗin mu za su zo wajen ɗaurin auran nan " Ina dariya na ce"Kar a taɓa min kawunaa. Ina nan ina nema masa mata." Yallaɓai na kallona ya ce"Allah ya sa kar kawun naki ya baki kunya. Tun da kika har Nene ta ƙyale Abba da mganar aure kin san lamarin ya fi karfin kowa" "Bai fi ƙarfin Allah ba. Muna addu'a in sha Allahu in lokaci ya yi zai yi." Sai ya amsa min da cewa" Allah ya sa muna da rabon gani." Agogo na ɗauko masa wani ɓaki na fatar damisa na saka masa. Turare na fesa masa sannan ya ce na zaba masa takalmin da zai saka. Wani baƙin takalmi na zaɓar masa ni na siya masa kwanki lokacin ina da ɗan kuɗina na ga wata mate ɗina a BUK na tallarsu suka yi mini kyau na ce ina so 18k na siye shi Yallaɓai na son takalmin nan fiye da sauran takalmansa duk da ya na ma cikin masu saukin kuɗi amman saboda ni ce na yi masa kyautarsa ya sa ya ke ji da shi. Sai da na gama shirya shi tsaɓ sannan nima na ce ya ta ya ni zaɓan kayan da zan saka. Mun daɗe gaban wardrop duk wanda na nuna sai ya ce a'a. Daga karshe dai ya tsaya kan wata super shi ya siya mini ita mai kalan green na ciro ta ina faɗin" Amman Yallaɓai mayafi zan saka ko? Hararata ya yi kafin ya ce" Asibiti gidan biki ne? Na marairaice ina faɗin" Don Allah fa. Atamfar nan ba ta kyau da Hijabi."   Jan gefen hannun rigansa na ke yi sai ya kalleni sai na marairaice ina faɗin" Haba My Yallaɓai na. " Wani kallo ya yi mini kafin ya duƙa ya na faɗin" In kin yarda mu sabunta wanka." Da sauri na ce" Bar shi na saka Hijabin." Na faɗa ina tura baki shi kuma yana mini dariya. Haɗe rai na yi ina faɗin" Ni ko? Ni ko ai shike nan." Sai ya ce to na saka mayafin amman sai na yi alƙwarin amjuna akwai ɓarnan ruwa ya na iya sai na ce na yarda sannan ya bari na ɗauko mayafin kayan takalmi ma shi ya zaɓa min wani flat mai ruwan ƙasa irin kayan shi ya na da jaka sai na ɗauki jakar ina jin Yallaɓai na faɗin" Wai ko dai ba Alhaji za ki je gaisarwa ba. Biki za ki je?   Ina dariya na ce" Kai Yallaɓai na. Wani biki kuma! Jinya zan je." "To ma su jinya." Share shi kawai na yi domin na san yanzu in na yi magana sai ya iya ɓata mini shiri shi ya sa na yi shuru ina bin sa da mirmishi. Muna nan sai ga Sabitu ya kira ya ce ya na waje sai ya ɗau kayan ya fita dashi ni kuma fita zuwa ɗakin su Jidda na ga sun shirya dogayen riguna suka saka na Abaya saboda halin Yallaɓai na ce su cire mayafan su saka Hijabi yanzu nan zai ce yara ma ƙanana ina koya musu saka mayafi. Yallaɓai ba wai yana da tsanani ba ne amman fa ya na da saka ido kan iyalansa. Wani lokaci zai yi mini tsanani wani lokacin kuma sauƙin kanshi har ya na yi mini yawa.   Jidda na ce ta ɗau kwandon abinci zuwa mota ni kuma na koma ciki ina fesa turare. Har na ɗan fesa kaɗan sai na tuna da Yallaɓai yanzu raina zai ɓaci. Da sauri na ijiye na koma ina shinshina kaina in ƙamshin ya fito na shiga uku da faɗan Yallaɓai. Hon kawai ya yi ta mini daga haraba ni kuma sai da na kashe duka wutar gidan sannan na fito na kulle ƙofar falo. Su Jidda na gidan baya ya na hira da su ina buɗe gaban mota na shiga ya juya ya na kallona kafin ya ce" Alhaji ki ka fesa ma turare ko likitocin ? Ya faɗa cikin haɗe rai. Da sauri na ce" A'a. Turaren kayan ne ina ga." Ƙura mini ido ya yi da sauri na ce" Da gaske ban fesa turare ba." Bai ce mini komai ba ya yi ma motar key sai na koma na jingina da kujeren mota ina maida numfashi. Mun ɗau hanya na ji ya na faɗin" Mu fara zuwa asibiti in na duba Alhaji sai na kai su gwammaja ɗin" Ni dai na amsa masa domin na ga ya wani haɗe rai ne. Mun isa asibitin wajen sha ɗaya saura ne. Amman na iske har Ma'u ta zo ni da Rahila ne kawai ba mu iso ba amman har su Yaya Auwal da matansu da Amina ma ta iso daga kaduna. Mun gaggaisa da su har da Yaya Murja Baaba ta na nan ita da Gwaggo suma na gaishe su Baaba a dakune ta amsa ban damu ba. Yallaɓai kuma ya fara musabaha da mazan matan ma suka gaisa ga duka har ƙasa ya gaida Gwaggo da Baaba. Ma'u har da cewa" Yallaɓai barka da safiya.' Ya juya suna gaisawa su Jidda ma suka bi kowa ɗaya ɗaya suka gaishe su. Suna waje Alhaji na ciki ya na barci Yallaɓai ne ya shiga tare da su Jidda. Ba daɗewa ya fito ya ce za su tafi ni na raka shi har bakin mota muka rabu akan cewa sai anjuma za su zo tare da su kawu ina ɗaga musu hannu suka bar haraban asibitin Baby sarkin rigima jin wajen Nene za a kaita sai ta fara murna. Abincin da na zo da shi Gwaggo na ba ta karɓa ta na ta saka albarka. "Ba wacce ta zo hannu rabbana. Yadda kuke jin ƙan mu kuma Allah ya jiƙan ku wata rana." Aka amsa da Amin Amin Baaba ta na ta wani taɓe ba ki ni ko ba ta isheni kallo ba Mun gaisa da Ma'u da tambaya ya jiki daga nan na karisa saman darduman da Amina ke zaune ita da Laila da Khaleesat suna hira.  Sai bayan na natsa ne na tambayi Baba Aminu aka ce ya koma tun safe Baba Sani kuma ya koma gida ya huta sai anjuma zai dawo. Na kira wayar Rahila ta ce min ga su nan a kan hanya ba daɗewa ta iso itama da kwandon abincin ta. Kowa da wanda ya saba dashi ya zauna su Yaya Murja yan wajen Ma'u suna zaune waje ɗaya har da Zaitunan Yaya Abubakar. Yaya Aina ce ma ta ɗan zauna a wajen Rahila kuma daman kowa ya san kaf gidanmu na fi shaƙuwa da ita shi ya sa ko an gamu tare muna hira ba wanda zai bi ta kai.     Muna nan har bayan azahar Laila Yaya Auwal ya ɗauke ta zuwa gidan su. Alhaji ya farka wajajen biyu duk mun shiga mun gaishe shi da jiki ya ce ya ji sauƙi yau ma ya ce likita ya sallame shi.   Yaya Hamza ya ce ya bari ko zuwa gobe in ya ƙara jin sauƙi. Baaba na gefe ta ce"Gaskiyar Hamza ka ƙara kwana ka samu hutu sosai Yaya Sule." Shi dai Alhaji an fi ƙarfinsa kawai ne kawai shi ya sa ya yi shuru. Sai ya koma ya kishigiɗa bayan Gwaggo ta kara mai filo "Yara nan fa duk sun taho maka da abinci me za ka ci? Gwaggo ta faɗa ta na kallon shi. "Allah ya saka muku da alheri. Allah ya yi musu albarka na gode." Dukkanmu muka amsa da Amin Amin Abincin ya ce sai anjuma amma ya sha ruwa. Ni ya kallah kafin ya ce"Dubu yau ke kaɗai kika zo? Ina kika baro min uwargidana Hauwa'u? Ina dariya na ce"Ta zo ka na barci Alhajinmu. Yallaɓai ma ya zo amma anjuma zai dawo in sha Allahu." Sai ya jinjina kai kafin ya kalli Ma'u ya na faɗin" Asma'u ki yi ma megidanki godiya maimuna ta faɗa mini bai bar yaran nan sun kashe komai ba. Allah ya ƙara ma arziƙin sa albarka Amin." Ma'u ta amsa da Amin Baaba har ta amsawa da Amin Amin da karfi na kalle ta lokaci ɗaya ina taɓe baki. Ba mu daɗe a dakin ba muka fita waje saboda dokar likita. Muna asibitin nan har la'asar sai ga kiran Hauwa ta na ce min ga su a asibitin ita da Mutaƙƙa ina ne barayin ɗakin da aka kwantar da Alhajin? Ina jin haka ni na fita haraban asibitin na taho da su.    Shi ya sa na ke son Hauwa in dai abu ya same ni ita ke fara zuwa ta yi mini jaje ko murna ita da mijinta. Mutaƙƙa ya shiga ya gaida Alhaji duk da ba lokacin dubiya ba ne na faɗa ma Alhaji ƙanin mijina ne ya na ta saka albarka. Mutaƙƙa ya zo da kayan marmari Hauwa kuma har abinci ta zo dashi kuma nan ya bar min ita karfe shidda ya ce ta koma gida. Na ji daɗi matuka ko da ganin sauran yan'uwana dangin mazajensu na ta zuwa gaida Alhaji. Ma'u har uwargidanta Hajiya Zainab ta zo da sauran ƙanensa.   Hauwa ta zo ba daɗewa sai ga Anty Bahijja ni na yi mamakin ganinta har a cikin zuciyata na san ba domin ni ta zo ba illai Ma'u ce ta je ta taro ta. Hauwa ta saki baki ta na kallon su har da rumgume juna muna ji ta na faɗa ma Baaba matar Yayan mahaifiyar Alhaji Mustspha ne. Sai ta ɗago ta ga ina kallonta sannan ta ce"Kuma Yayar mijin Sadiya ne.".   Gwaggo na ta saka albarka da godiya ina ji Ma'u ta nuna Baaba ta na faɗin ga mahaifiyarta. Anty Bahijja har ƙasa ta duka suna gaisawa Rahila na in da muke Khaleesat ta shiga cikin gari gidan ƙanwarta Anty Aina ma ta koma gida Amina ma ta je gida ta huta. Yaya Murja ma dazu ta koma mu da Yaya Balki ne kawai mu ke asibitin. Daga zaunen da na ke na gaisar da Anty Bahijja sai lokacin ta kallemu ni da Hauwa. "To su Hauwa ashe a nan nan? Cikin rawan jiki ta ce" E. Ban daɗe da zuwa ba. Tare da Baban Sahla mu ke ya kawo ni sai ya wuce." Sai kawai ta wuce tana faɗin" Hakan na da kyau." Shiga ciki ta yi Ma'u na gefenta domin ta duba Alhaji. Sai da ta shige ne sannan Hauwa ta kalleni nima sai na kalleta amman ba mu yi mgana ba muna nan zaune ta fito har ta na ba ma Gwaggo 10k. Wai sai ga Ma'u ta juyo ta na ce min" Sadiya kalli Anty  Bahijja da ɗawaniya."   Mirmishi na yi kafin na ce" Allah ya ba da lada." Ma'u ce za ta rakata ni dai ko kafata ban ɗaga daga daga na ke zaune ba. Sai ta juya ta na kallon Hauwa kafin ta ce" Yanzu za ki tafi gida na yi miki lift? Da sauri na ce"Mutaƙƙa karfe shidda ya ce ta koma gidan" Sai ta wani kalleni kafin ta ce" Ya yi. Allah ya ƙara lafiya." Na amsa mata da Amin Amin har da Baaba a masu rako. Sai da suka bar wajen Rahila ta kalleni kafin ta ce" Ku ba ku yi rakon ba Sadiya" Kai tsaye na ce" Saboda mene! Ai ni ba na neman suna. Wacce ta zo domin ta ba ki ga har da uwarta arakon ba? Sai Rahila ta kasa mgana. Saboda ta san halina ta na ƙara mgana zan saki wata mgana kuma ga Hauwa a wajen sai ta tashi tsam da goyon yarta ta wuce wajen Gwaggo itama na rakata da harara.   Hauwa ce ta kalleni cikin mamaki kafin ta ce" Wai ya kuke da Ma'un nan ne Anty Sadiya?. Kai tsaye na ce" Ina wanan tsohuwar da kika ga sun fita tare? Sai ta ɗaga mini kai. Kau tsaye na ce" Ita ce mamanta. Ita ɗin Baabar mu ce ƙanwar Alhajinmu ce da suka haɗa uwa ɗaya uba ɗaya."   Sai ta jinjina kai ni kuma sai na ƙara mata da cewa" Baban Ma'u ya rasu tun tana ƙarama sai da Baaba ta yi wani auran Alhajinmu ya ɗauketa shi ya sa ta tashi a gidanmu." Hauwa ta yi sakate kafin ta ce" Ikon Allah." Sai na kalli Hauwa domin na san akwai mgana a bakinta. Cikin sauri na ce"Me kika gani hala! Ko na ce kin ji wani abu ne a kaina daga bakin ta? Shuru ta yi ni kuma da sauri na ce" Don Allah ki faɗa mini Hauwa. Ba lalle kin san ba shiri tsakanina da Ma'u ba kina gani da idon ki yadda take shigema Anty Bahijja kuma dalilina ne tunda ai ba Musbahu ta ke aure ba. Balle kusan ta yi musu yawa haka."   Ƙasa ƙasa Hauwa ta ce" Ranar sunan Halima na ji suna mganarki." Sai na yi kwafa kafin na ce" Ai ba za ta sauya ba. Munafuka ce makira." Sai Hauwa ta riƙe min hannu tana faɗin" Ta so mu je ki ji wata mgana" Barayin muka bari gabaɗaya mun haɗu da su Ma'u a hanya za su dawo. Har ta na ce mini Hauwa za ta tafi ne na ce mata a'a da gayya na ce mata za mu yi mgana ne ina gani ta yi tsam daga ita har uwarta ni ko na ja Hauwa muka wuce abin mu.   Can haraba muka fita a babban falo muka samu kujeru muka zauna ina mai kallon Hauwa na ce"Me kika ji munafukar ta ce akaina? Hauwa ta ce" Ni fa ina ta mamaki na san ƴar uwanki ce amman me ya sa za ta biye ma su Anty Bahijja suna kushe ki?   Raina har ya fara ɓaci da sauri na ce"Me ta ce wai? Hauwa tasauke numfashi kafin ta ce" ita da Anty Bahijja da wata ban san ta ba tare da Ma'un suka zo." Kai tsaye na ce" Shema' u ce ƙawarta ce." Hauwa ta cigaba da faɗin" da Anty Maimuna ma awajen ana mganar haihuwa Anty Bahijja na ta faɗan wai kamar Tafida zai ƙare rayuwa da ƴaƴa biyu. "Buɗe bakinta sai cewa ta yi" wai daman tun farko ke ba ki da burin tara ƴa'ƴa da yawa. "   Ido na har wani ƙyalli bala'i ya haska a fusace na ce" Ita Ma'un ta ce haka don ubanta? Da sauri Hauwa ta ce" Ni fa ba na faɗa miki saboda na haɗa faɗa ba ne. Na gaya miki ne saboda ki sani ne"   Ina sassauta fushina kafin na ce" Ba zan yi ba Hauwa." Kallona ta yi kafin ta ce" Kin tabbatar? Sai na gyaɗa mata kai sai ita kuma ta gyara zama ta cigaba da faɗin" Ita fa Ma'un ta ce haka aiko Anty Maimuna ta ce ba ki isa ba kin auri ɗan dangi saboda haka in ke baki son haihuwa za su aura masa wacce za ta zo ta cika masa gida da ƴa'ƴa." Idanuwana har sun tara ƙwallah zuciyata na zafi. Na kalli Hauwa kafin na ce" Ban yi mamaki ba. Tun zuwan Ma'u gidanmu na san ita din ba alheri ba ce. Na kuna san watan wata rana sai ta zame mini matsala da damuwa. Amman ta je Allah ya fita ni dai ban taɓa bin ta da sharri ba in tana tunanin abin da ya faru na fasa auranta da Yaya Hamza take rike da ni a cikin ranta ta makara har gobe ban yi nadama ba. Da na bari ta auri Yaya Hamza da tuni ta haɗa mana yaƙi a cikin gidanmu."   Cikin mamaki Hauwa ta ce"To daman da jiƙaƙƙiya a tsakaninku? Kai tsaye na ɗaga kaina kafin na ce"Akwai kam. To sai aka yi yaya? Hauwa ta cigaba da faɗin" Kawai sai wacce suka zo tare da kika ce ƙawarta ce ta na cewa shi ya sa kika yi tsarin iyali kenan ga shi ya ja za miki matsala kina son haihuwan kuma  ta ƙi samuwa. Nan take Anty Maimuna ta ce sai dai ke matsala ta ƙare a kan ki Tafida aure zai ƙara in sha Allahu."   Mirmishi kawai na yi a cikin raina ina jin kamar in na ga Ma'u na shaƙe mata wuya. Sannan ido na idon shema'u wallahi tallahi sai ta raina kanta Hauwa na faɗin wai na kwantar da hankalina ba su isa su saka Yaya Tafida ya yi aure ba. Kallonta na yi kafin na ce" Sun isa mana tunda ƴan'uwan shi ne kuma suna gaba dashi. Ni bare ce ko yau ya sake ni gidanmu za ni su kuma ai ba shi da kamar su. Hauwa na rantse da Allah ba zan hana Yallaɓai ya ƙara aure ba, ya ƙara ta zo ta ci duk abinda suke tunanin ina ci ƴaƴa kuma ta tara masa duniya ni kuma biyun da Allah ya bani Allah ya raya min su." Na faɗa ina ƙokarin maida kwallar da ta kawo min. Hauwa ta dafa kafaɗata ta na faɗin" Ki yi haƙuri. In sha Allahu ke ma za ki ƙara haihuwa. Ba kin je asibiti ya kuka yi da likitan? Ina sauke numfashi na ce" Ta dawo da ni nan asibitin Aminu kano. Jibi zan fara zuwa in sha Allahu."   Hauwa ta yi ta mini fatan dacewa na kalleta ina ƙaƙaro mirmishi. "Na gode Hauwa." Mun daɗe a wajen ta na ba ni baki na dai nuna mata bakomai ne amman ni kaɗai na san halin da zuciyata ta ke ciki. Amman na yi ƙoƙarin nuna ma Hauwa ba komai. Saboda haka ne na kalle ta ina faɗin" Kin ji Yaya Usman zai ƙara aure?   Sai ta gyaɗa min kai kafin ta ce" Na ji fa. Duk ranar sunan na ji ana tattaunawa. Shi kuma can bakin ƙannen shi na ji su Nasara suna ta zagin Anty Zabba wai so ta ke yi shi Yaya Usman ɗin ya zauna da ita kaɗai? Ko ya yi ma Ogan shi gaddama yaƙi karɓan auran. Sai zaginta suke yi suna faɗin kar Allah ya sa ta koma ɗin." Cikin mamaki na ce"Ikon Allah. Mutane sai Allah yau kuma ita Anty Zabban suke zagi? To Maman farko ba ta yi mgana ba?   Hauwa ta ce" Oh na ji dai kamar an ce ta kira shi a waya ta ce ya bar komai ya ke yi ya zo ta na son ganin shi " Sai na gyaɗa kai kafin na ce"Uhm. Allah dai ya kyauta.". Ta amsa da Amin ni na cigaba da faɗa mata yarda muka yi da Yallaɓai ya haƙinƙan ce. Ta na dariya ta ce" Ni ai ban yi ma Muttaƙa mgana ba. Kar ya ce ina son jin gulma amman na san shima bayan ɗan uwansa zai bi" Dariya muka ɗan yi gabaɗayanmu. Muna wajen Munira ta kira waya ta. Ta na tambayata jikin Alhaji? Na ce da saúƙi a ina ta ji ta ce Nasir ya faɗa mata ya ce Tafida ya saka a group ɗin su na gida. Ta tambaye ni wani asibiti ne na faɗa mata sai ta ce min ƙila gobe ta shigo. Ina dariya na ce ma ai ga Hauwa ta zo tun ɗazu. "Kai Hauwa sannu da ɗanwaken zagaye ko ki kirani mu taho tare." A speaker na saka Hauwa ta maida mata da amsa da cewa" Ke ni fa mijina ya kawo ni. Goben ki saka mijin ki kema ya kawo ki." Munira na dariya tace" Au gorin miji da kin ga Habibi ba ya gari? To na san hanya kin ji ta Yallaɓai gobe ina nan tafe." Na ce Allah ya kawo ta lafiya daga nan muka yi sallama. Ganin shidda har ta gota yasa Hauwa ta ce bari ta je ta yi ma su Gwaggo sallama ta wuce gida. Muna zuwa na ga Shema'u ta zo har ga Allah na so na daure amman na ƙasa ta kalleni ta na mini mirmishin munafunci irin na ƙawarta amman ni ta ga irin kallon da na yi mata. Ba domin muna asibiti ba ne. Kuma da ba uba na ne ta zo dubawa ba wallahi sai Shema'u ta raina kanta baƙar munafuka. Tana min magana na yi kamar ban ji ba sai da Ma'un ta ce" Sadiya ba ki ji Shema na mgana ba ne. Ba ta gari ne ɗazu ta dawo ta na zuwa, ke ta fara tambaya." "Oh." Haka kawai na ce na juyar da fuska ta domin na kasa iya ɓoye abin da ke zuciyata. Hauwa ta yi musu sallama kularta kuma aka juye abincin na riƙa mata har bakin asibiti ta samu adaidaita muka yi sallama. Ba domin Yallaɓai ya kirani ya ce bayan mangariba suna tafe tare da su Uncle Abba  da har na gaji na ce tafiya ta gida zan yi. Rahila ma ta koma gida wai za ta yi abinci da ga ni sai Ma'u da kawarta Gwaggo ma Yaya Hamza ya maida ta gida kiri ƙiri Baaba taƙi bin ta wai ta je za ta zo. Can suka keɓe da yarta suna da ƙuskus ni ko dagani sai Yaya Balki itama mijinta take jira Zaituna kuma ta koma gida saboda yara a cikin raina ina fatan Allah ya sa a sallani Alhajinmu gobe na gaji da zaman asibitin nan Waya ta na ɗauko na kunna Data na kwana biyu ban hau ba. Sai na ga an yi min mgana har da Yaya Maimuna ta na tambayan jikin Alhaji. Hindatu kuma ta ce ta kira waya ta ba ta samu ba.  Har da matar Muhammad kabir ma na ga maganarta. Kuma na ji daɗi na amsa su sama sama saboda an fara kiran sallar mangariba. Yaya Balki kawai na faɗa ma zan je sallah sai ta ce na tsaya mu tafi tare. Muna masallacin kafin mu fito Yallaɓai ya ce ga su sun iso asibitin. A haraban wajen muka haɗu suka gaisa da Yaya Balki ta yi gaba ta bar mu ina gaisawa da Aminan mijina guda biyu. Uncle Abba da Tariq. Sun yi min ya mai jiki na ce da sauki muna gaba ni da Yallabai suna baya zuwa in da ɗakin da Alhaji ya ke ciki. "Me ya faru na ga kamar ranki a ɓace? Yamutsa fuska na yi kafin na ce" Na gaji ina son na koma gida." Sai ya kalleni da saurin na ce" Zan bika yanzu ko za ku je wani waje ne? Kai ya girgiza kafin ya ce" A'a Gwammaja muka yi. Sai mu wuce taren su ma daga can za su wuce."   Tun da Gwaggo ba ta nan da Baaba suka gaisa sai su Ma'u sannan na raka su ciki suka duba Alhajinmu ya ma tashi Baba Sani ya ƙariso zai taimaka masa ya yi alwala ya yi sallah. Ya ji daɗi ya na ta saka musu albarka da godiya ba dadewa suka yi masa sallama dukkansu kuma sun aje masa kuɗi ya na ta saka albarka. "Alhajinmu Allah ya ƙara lafiya zan bi Yallaɓai zuwa gida sai gobe." Alhaji ya jinjina kai kafin ya ce" Shi kenan mu kwana lafiya Dubu! A gaida min da Hauwa kuluta." Na amsa masa ina mirmishi,  sun rigani yin gaba ina fitowa na ce ma Yaya Balki zan bi Yallaɓai sai gobe ta ce ai ya kamata na je gida tun safe fa. Daƙyar na iya yi ma Baaba sallama ta amsa sama sama. "Sadiya Gwammaja za ku je? Na juya ina kallonta Shema' u ce. Kamar na ce a' a sai kuma na ce mata eh. Sai kawai na ji Ma'u na faɗin" To ki je mana Shema. Sadiya itama Gwammaja za ta je gidan kawunta."   Juyawa kawai na yi ban ko yi mgana ba ina ji ta na yi ma Baaba sallama. Ina zuwa na ce ma Yallaɓai za mu rage ma kawar Ma'u hanya. Ya ce to ba matsala Ma'un ce ta rakota abin mamaki tana ganin motar su Tariq dabam sai kawai Ma'u ta kalli Yallaɓai ta na faɗin" Yallabai bari ta bi wancan motar ko ba waje ɗaya za ku je ba? "Can za mu je gabaɗaya. Ta je ta shiga." "Tariq..." Ya ƙwalama sa kira ya na waya ne tsaye a bakin mota Uncle Abba ya riga ya shiga bangaren direba tunda motarsa ce. ''Ga ƙari na samo muku itama Gwammaja za ta je" Ya faɗa ya na nuna Shema'u dake tsaye ita da Ma'u. Sai ya ɗan ɗaga masa hannu alamun toh sai ya ce ta je ta shiga. Ni dai tuni na shige gaban mota na zauna Ma'u ta leƙo ta na fadin sai da safe na ce mu kwana lafiya. Muna tafe amman acikin raina ina tunanin me ya sa shema'u ta ke son bin motar su Uncle Abba? Tabbas da wani abu a ƙasa. Kafin ma a kai gidan su Yallaɓai ta sauka domin suna bayanmu ne mu dai muka yi gaba. Har ma mun shiga mun gaisa da Nene ta na tambayata Tafida ya ce Alhajinmu ba lafiya ya jikinsa? Na ce da sauƙi ta yi masa fatan samun lafiya.   Tariq ne na ji ya na yi ma Uncle Abba tsiya yau ko ya shafa kwalli ne ƴan mata sai kawo hari suke yi. Shi kuma bai ce komai ba Nene ce ta ce"Me ya faru? Tariq ya ce"Nene ɗazu fa a gidan su amaryan abokin mu yan mata shi kawai suke kawo ma hari. Yanzu ma da muka ɗauko wata yar uwan Sadiyan Tafida daga asibiti har lambar wayarsa sai da ta tambaya."   Ya faɗa cikin dariya. Ina zaune a cikin raina na ce a biri ya yi kama da mutum daman kawu ta gani kenan ta ƙyasa. Mirmishi na yi na ce lalle za ta sha wahala wallahi ko  ya na sonta ba zan taɓa bari ya aure ta ba. Ba wai ina dariya da daɗewan da ta yi ba ta yi aure ba ne. A 'a ba ta da hali mai kyau ne. Sai kawai na shiga hirar da cewa" Ba ƴar'uwanmu ba ce ƙawar Ma'u ce kawai." Nene ce ke faɗin" To Allah ya sa dai ya ga wacce ta yi masa a ciki? Yallaɓai ne ya yi dariya kafin ya ce"Ai Nene wannan ƙanin naki sai dai in yana da rabon samun Hurul aini ma'ana in ya mutu ya samu rabauta a shiga aljannah." Nene ta aika masa da dakuwa ta na faɗin" Kawun na ka ne ka ke yi ma mugun fata? To bakin Tafida ya sari ɗanyen kashi Abba" Sai lokacin ya yi mgana ya na zaune kusa da yayarsa yana danna waya. "Na ƙyale su Nene. In cikin su akwai wanda ya isa gobe ya ɗaura mini aure " Nene ta yi saurin cewa"Ba su ma isa ba. Amman dai mu mun isa Abba ka fara furfura fa" " Lokacin ta ne Nene ban tsufa ba da saura na. Aure kuma zan yi in sha Allahu." Nene ta amsa da Allahu ya sha kafin ta ce"To yau duka ba ka ga wacce ta yi maka ba? Ko yar uwan Sadiya? Gabana har ya na faɗi na ji me zai ce kawai sai ya ce"Duka fa ba su da kamun kai. Nene wacce mace ce ta gari ce mai kunya za ta yi shigar bayyana sura ta na nuna ma namiji alamun tana son shi? Ni ba irin matan da na ke son aura ba ne Nene ki bar mganar nan." "To ita wacce kuka ɗauko daga asibiti fa? An ce ka ba ta lambarka? Kai tsaye ya muskuta kafin ya ce" Ita ma ta na cikin jerin su. Ita ta fara mini mgana kin ga kenan itama kunyar ta yi ma ta ƙaranci sannan kuma ni ba lambata na ba ta na Tariq na saka mata." Me za mu yi in ba dariya ba sai aka bar Tariq da buɗe baki sai yanzu ya tuna domin da ya saka mata lambar sai ya ce wayar ba ta tare da shi tana gida a kashe. Sai ta ce ta hannun ka fa? Sai ya ce ta aiki  ne ashe shi ya gama ma aikin. Ni da Yallaɓai muna ta dariya Nene ma sai da ta dara. Tariq dai ya ce zai rama ganin dare ya yi suka ce za su koma Nene ta ce su kwana Abba ya ce kamar wasu mata. Sanin halin su ya sa ta ce Abba ya gaida Innayi. Shi kuma Tariq ya gaida da Hajiya. Tare muka fita har baby ta yi barci sai ɗaukan ta Babanta ya yi Jidda ce kawai idanuwanta biyu ta ga babaninta ta maƙale musu suna mata tambayoyin makaramta tana ba su amsa. 10k Kawu Abba ya ba ta shi kuma Tariq 5k ya ce ita da Baby su siya chaculate  sai ta ki karɓa ta na kallon Babanta.   Uncle Abba ya kalli Yallaɓai kafin ya ce" Kai Tafida ko ba ka yi ma yar namu bayanin ko kana raye muna da iko a kanka da su gabaɗaya ba." Yana dariya ya ce"Sai ku jira na mutu tukunna" Ni dai ina jinsu ina ta dariya Sai da yace Jidda ta karɓa sannan ta karba ta wuto wajena ta ba ni na karba ina musu godiya. Tariq ke faɗin" Abba mun kusa zama surukai fa. Ka ga Jidda da tsawon kafa." Abba ya jinjina kai kafin ya ce"Zan fara neman aure ko domin kar azo neman aure tarihi ya zo uban jidda ya ji kunya." Daga Tariq har Yallaɓai na suka fashe da dariya nima na dara sanin halin su in sun haɗu. Na shige mota ina ce ma Tariq ya gaida Farida  ya ce za ta ji.   Uncle Abba kuma ya ce" Ni kuma wa zan gaisar miki Sadiya? Ina dariya na ce"Amarya mai jiran gado." Yallaɓai ke faɗin" Su kawu Sa'adu ko matansu ba."   Keyarsa ya tallaba ya na faɗin" Mara ɗa' a." Tariq na gefe ya ce zai rama masa. Ni dai mun fi minti talatin a waje kafin su yi sallama su suka shiga mota suka ɗau hanyar Rano mu ma muka ɗau hanyar gida. Muna hanya na kalli Yallaɓai ina faɗin" Dare bai yi ma su Kawu ba?" Ya na tuƙi ya ce"To wallahi Abba har sha biyun dare ya kama hanyar rano." Sai kawai na yi fatan Allah ya kai su lafiya. Mun isa gida lafiya Yallaɓai ya dauki Baby zuwa ɗakin su na ce Jidda ta yi mata shirin kwanciya su sun ci abinci a gidan Nene, ni da Yallaɓai na zuba mana sauran tuwon da na yi muka ci muka ƙoshi. Sai da muka yi brush muka yi shirin kwanciya duk mun gaji sai barci sai da asuba ne Yallaɓai ya ja mu ka yi ta ɓarnan ruwa.   Da safen daman ban yi niyyar zuwa asibiti da wuri ba sai ga ma wayar Amina ta ce an sallami Alhaji sai na ce shike nan sai zuwa anjuma zan leƙo gidan. Zan tsaya saude ta zo ta kama ma Jidda ta wanke Unfiorm ɗin su nima Yallaɓai na gida ba zai fita ba ƙila sai zuwa anjuma. *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU #1k NE KACAL, AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* I just published "Page 12" of my story "TURKEN GIDA."::https://www.arewabooks.com/chapter?id=68237857847ebcbfe6d205fe *🅿️11* *1994.* *KATSINA. Ƙauyen Yashe dake ƙaramar Hukumar Kusada.* Hajiya Dubu na zaune a dandamalin ƙofar ɗakin ta, ta na ɓanɓaran masara. Masaran gonar Aminu ce an kawo ta gida yar sauran da ta rage ba ta bushe ba ne aka shanya bayan ta bushe shi ne take ɓanɓarewa.   Daga ƙofar gida ta ji kamar hayaniya ba jimawa sai ga wani magidanci ya shigo riƙe da jaka a hannunsa bakinsa kamar gonar auduga saboda farin ciki. "Hajiya Yaya Sule ne ya zo." Haka ya faɗa. Itama sai ta washe baki lokaci ɗaya tana miƙewa kakkabe hannunta ta yi a jikin zanin jikinta kafin ta kalli yar yarinyar dake gefenta a zaune a rakuɓe wacce a shekaru iyakarta sha uku sannan ba za ta haura sha huɗu ba. "Ke Asma'u kwashe mini masara ki kai cikin ɗakin can" Haka ta faɗa kafin ta maida hankalinta ƙofar shigowa dai dai lokacin da aka yo sallama kamar wanda ya fara shigowa haka ya ke shima  sai dai a akwai bambamci shi daga ganin shigarsa za ka fahimci daga birni ya ke. Shadda ce mai duhuwa ya saka da takalminsa sahu ciki kansa da hula amman fuskarsa duk ta yi ƙura saboda kuran hanya tunda shekarun da yawa ba titina a lokacin kuma akuri kura ce za ka samu in ka sauka a bakin hanya ta shigo da kai cikin Ƙauyen. "Maraba. Lale da zuwan Sule. Kai ne tafe." Safiya ce domin lokacin ba zai gaza sha ɗaya da wani abu na safe ba. Kuma da karfi ta ke yi masa maraba da ya sa matan gidan da ƴa'ƴansu fitowa daga ɗakunan su. Har ƙasa ya duka ya na faɗin" Mun same ku lafiya Hajiya? Da sauri ta ce"Haba dai. Tashi tashi maza Sule. Kai Sani shigar masa da jakarsa ciki ka yi masa shimfiɗa ka zauna anan ai sai ka ɓata jikinka"   Sai da ya shiga ciki ƙaninsa Muhammad Sani ya yi masa shimfiɗa ya zauna sannan Hajiya Dubu ta shigo ita ma ta zauna a gefe suka gaisa. Sannan matar Sani ta shigo suka gaisa har yana karɓan yarinyar da ta ke goyo mardiya. Sannan yaran ma duk sun shigo sun gaishe shi ga su nan ɓutu ɓutu. Ba karatun boko suke yi ba saboda lokacin karatun bai yawaita har ƙauyuka ba sai dai  in namiji ne  a tura shi gona in mace ce kuma a yi musu aure masu rabo ne ma iyayensu kan tura su wani gari karatun allo.   Matar Aminu ma ta zo ta gaishe shi kafin ka ce me an cika gabansa da ruwa da fura. Har da abinci ma tun da su ƙauye ba ruwansu da wani lokaci ko da yaushe ka zo suna da abinci sannan sun iya karrama baƙo. Baƙon ma irin Sule da ba ko yaushe ya ke zuwa ba sai in ya samu sarari. Yaran gidan sun zagaye shi sai da Hajiya ta fattatake su amma ba su tafi ba sai da ya buɗe jakarsa ya ɗauko alewan da ya siya musu na tsaraba ya ba ma Babban cikin su Nura ɗan wajen Sani ya ce ya je su raba sannan suka fita suna murna. Shima Sanin fitan ya yi ya ce zai gangara gona ya faɗa ma Yaya Aminu zuwan shi.   "Ya wajen iyalan naka? Ina takwarata Dubu ina fatan duk kuna nan lafiya ko? Hajiya Dubu ta faɗa tana gyara zama. Sai da ya kurɓi ruwa da cikin kwanon sha mai murfi da aka kawo masa sannan ya ce" Duk suna nan lafiya Hajiya. Rukayya da Maimuna duk suna gaishe ki. Takwaran ki kuma ta so ta biyo ni to sun fara zango karatun sakandiri na farko shi ya sa ban zo da ita ba. Sai dai ta yi jadadda mini saƙon gaisuwarta zuwa gare ki."   Hajiya Duhu ta yi mirmishin farin ciki kafin ta ce" Duka ina amsawa. Allah sarki ashe takawara an sake zama ƴan makaranta. Ina jiranta in suka samu hutu." "In sha Allahu." Sun fara taɓa hira sama sama ta na faɗa mai gidan su Maimuna ma an yi rasuwa jiya ƙanin mahaifinta ya rasu sakamakon ba wayar hannu a lokacin sai dai a tada ɗan aike ya je ya faɗa. Daman tana shirin aika Sani ne sai kuma gashi ya zo. "Allah Sarki. Allah ya jiƙansa. Daman tana ta zencen sa ashe jinya ba na tashi ba ne. Allah ya yi masa rahama." Ta amsa da Amin Amin. Shi kuma ya ce zai je ya yi musu gaisuwa kafin ya tafi gobe in Allah ya kaimu. "Gobe gobe nan za ka koma Sule? Kai ya gyaɗa kafin ya ce"Saboda wajen aiki Hajiya. dama na ga kwana biyu ban leƙo ba shi ya sa na ce bari na zo na duba ku". Ya faɗa lokaci ɗaya yana buɗe jakarsa ya fiddo da ledojin guda biyu duk ya tura gabanta ya na faɗin" Sabulai ne da sai siga Hajiya. A yi hakuri ba kamar yadda na saba zuwa ba ne. Tsakiyar wata ne ba a yi albashi ba." Ta jawo ledojin gabanta ta na faɗin" An gode. Allah ya yi albarka Allah ya raya maka zuru'a. Allah ya ba ka masu jiƙan ka kamar yadda kake jin ƙanmu. Allah ya ba ka aljanna sanadin wannan zumuncin naka." Yana ta amsa mata da Amin Amin cikin jin daɗi. "Hasiya dai na can lafiya ko? Hajiya Dubu ta gyara zama za  ta yi mgana kenan sai kawai ta ga inuwa daga saman kanta ta na ɗago kanta sai ta ga Asma'u tsaye ta na leƙen su. Shima Sulen sai ya kallo ƙofar ɗakin ya ga ana leƙe. "Ke Asma'u zo nan.." Sai ga ta ta shigo ta na laɓe laɓe hannunta  ta jawo ta zaunar da ita a gabanta lokaci ɗaya tana faɗin" Ke kowa ya zo ya gaida babanku ke ba ki da hausan zuwa ki gaishe shi? Sai ta kalle shi cikin yarinta kafin ta ce" Ina yini" Cikin sanyin murya kamar za ta yi Sule ya yi mirmishi kafin ya ce"Ina kwana dai ko?   Ya faɗa ya na kallonta. Hajiya Dubu ta taɓe baki kafin ta ce"Haka ta ke. Tunda Hasiyar ta kawo ta wajen wata ɗaya kenan ta kasa sakin jikinta. Ga yara ƴan'uwanta ta kasa sakin jiki a cikin su sai ƙulafacin uwa." Sai ya kalli Hajiya Dubu kafin ya juya ya na kallon ƴar yarinyar cikin mamaki ya ce " Ƴar waye wannan Hajiya? "Yarinyar wajen Hasiya ce fa. Wacce ta haifa da marigayi Hashimu." Cikin buɗe ido ya ce"Dama ba tana hannun dangin babanta ba ne? Hajiya Dubu ta ce"Uhm' kafin ta cigaba da faɗin" To Hasiya da ƙulafaci mana. Wai can Asma'u ba sa'aninta ba ta jin daɗin zaman gidan. Bayan ta yi auren nan ta amso ta ta tafi da ita to ashe dai zama bai yi daɗi ba sai gashi ta dawo mini da ita wai ta zauna a hannuna." "Me ya sa?. Ya faɗa cikin mamaki Hajiya Dubu ta amsa shi da cewa" To ta dai ce min yaran mijinta na ta sun ƙi karɓan Asma'u sai megidan ya ce ta maida ta dangin ubanta. Su kuma kasan duk mata ne ƙannen Hashimu wata ma ƙanwarsa da yake can ƙauyen gaba damu ta so ɗaukan Asma'u Hasiya ta hana shi ne ta bar ta a wajena ni zan riƙeta in har Allah ya aramin rayuwar." Sai ya jinjina kai kafin ya kira Asma'u da hannun alamun ta zo. Hajiya ta tura ta gabanshi. Riketa ya yi ya ɗora ta a saman cinyarta ya na faɗin" Me sunan ki? "Asma'u." Sai ya jinjina kai kafin ya ce"Ma'u ce"  Sai ya ƙara kallonta kafin ya ce" Za ki bi ni can birni kano? Akwai abokan wasa kamar ki Rahilatu da Sadiya. " Sai ta kalle shi kamar yadda Hajiya Dubu ke kallon shi sai Asma'u ta kalle shi kafin ta kalli Hajiya ita kuma sai ta yi mirmishi kafin ta ce" Ba ruwana. Kawun ki ne in  za ki bishi shike nan nima na huta.". Sai ta ɗaga masa kai alamun za ta bishi. Sai ya dawo da kallonsa kan Hajiya ya na faɗin" Hajiya zan ta fi da Asma'u na je na haɗa ta da su Sadiya na sakata a makaranta. Ba zan bari a kaita ƙauye a gurgurta mata rayuwa ba" "Allah ya ba ka lada Sule. Daman Hasiya burinta Asma'u ta samu rayuwa mai inganci. Allah ya taya ka riƙo" Ya amsa mata da Amin Amin sai ta ce to Asma'u ta tashi ta haɗo kayanta a wanke saboda gobe Sule zai wuce zai tafi da ita. Sai ta fice tana murna. Hajiya ta yi mirmishi kafin ta ce" Ja'ira itama tana son bin ka ashe."   Sun cigaba da hira har aka kira sallah ya yi alwala ya fita masallaci domin ya yi salla bayan ya idar ya daɗe a waje yana gaisuwa da mutane da aka kwana biyu ba a haɗu ba. Ya na wajen Aminu da babban ɗansa Muntari da Sani suka dawo daga gona rumgume ɗan uwansa Aminu ya yi yana murna da ganinsa Muntari ya duƙa har ƙasa yana faɗin. "Sannu da zuwa Baba Sule." Kansa ya shafa kafin ya ta da shi tsaye yana faɗin" Muntari ka ƙi zuwa dai na saka ka a makaranta tare da su Hamza ko? Ka gwammace ka yi ta zuwa gona da babanka ko? Kansa na ƙasa ya na shafa ƙeya ya ce" Zan zo Baba in sha Allahu."   Sani ne faɗin ai yana yin makaranta gwammati na cikin garin kusada. Sai Sule ya ce hakan da na kyau in ya gama ya zo ya same shi a kano domin ya nema masa ta gaba da sakandiri saboda ilimi na da amfani sun ga misali a kan shi da ilimin da ya yi ya zama abin ya zama yanzu. Cikin gida suka shiga gabaɗayansu kamar yadda suka saba in dai Sule ya zo a ɗakin Hajiya Dubu suke haɗuwa su ci abinci. To yau ma haka suka yi bayan sun gama cin abinci suka sake fita suka raka shi gidan su Maimuna ya yi gaisuwa da alƙwarin in ya koma ita za ta zo in sha Allahu. Ranar dai ya yini cikin ƴan'uwansa har dare suna tare  Hajiya ta faɗa musu zai tafi da Asma'u Aminu ya ce gwara haka ƙila za ta fi sakin jiki sannan can za ta yi karatu nan kuwa sai dai ta ta ƙara tasawa a yi mata aure.   A tsohon ɗakin su na zaure ya kwana gidan da ya ke ginin mutanen da ne na ƙasa ne da yaɓe. Da safe bayan sun karya ya yi wanka ya yi shirin tafiya  kuɗi ya ba ma Hajiya Duhu ta yi ta saka albarka Asma'u an haɗa mata kayanta a kullen ɗan kwalli itama ta ci gayunta da takalminta ɗan madina da hijabinta da ya yi mata yawa. Lokacin da Sule da Hajiya Dube suke sallama ya ce mata" Hajiya don Allah ki bari na zo na ɗauke ki in na gama gina gidana ki koma can da zama." Hajiya Dubu ta ce"To Sule in na bika su na nan ai sai su ce na fi sonka ne ko? Su Sani na wajen su ka saka dariya domin su san ba ta son barin garin kwata kwata.   Aminu ne ya ce" Hajiya da mu da Yaya Sule duk ɗaya ne. Mu ma za mu so ki samu rayuwa mai inganci da jin daɗi kafin wa'adi ya yi. Mu kuma ki bar mu anan mu ai ba yara ba ne muna da iyalai da yara. sai mu riƙa zuwa muna duba ki in sha Allahu."   Ba ta dai ce komai ba sai ta wani rausayar da kanta alamun ba ta amince ba shi kuma Sule ya shuru ne ya dai gama gina gidan na shi tabbas sai ya ɗauke Hajiya zuwa Kano domin itama ta samu chanjin rayuwa. Har ƙofar gida Hajiya ta raka shi da zugan yara duk ya sallamesu da kuɗi sulalla ya ce su je raba a tsakaninsu Muntari ne ya ɗaukan masa jaka yana gaba tare da Asma'u shi kuma ya na baya tare da ƴan'uwansa suna tattauna mganar gonar shi da ake noma masa tana hannunsu ne tun da sune suke cikin garin. Sune har zuwa in da ya samu akori kuran da zai ɗauke su zuwa babban hanya da za su samu motar kusada daga can su hau ta zuwa garin Kano. ***** *KANO. Fagge.* Ba zan manta ranar da Alhajinmu ya zo da Ma'u gidanmu ba. A wata ranar lahadi ne da yamma domin sanda suka iso ba ma gida muna isalamiya ni da Rahilaa mun dawo makaranta ne muka ga wata baƙuwar yarinya mai kallon mutane da idanuwanta a tsaye a cikin ɗakin mu. A lokacin Yaya Aina ce kawai ta yi aure. Amman su Yaya Murja sune ƴan mata a lokacin ita da Yaya Balki tun da ba su da tsareyan haihuwa. Ita Yaya Murja ta na ajin kusa da ƙarshe a babban sakandiri ita kuma Yaya Balki tana ajin farko. Ni da Rahila ne muke tasawa a lokacin sai Amina da ke bin bayan mu a lokacin da Datti da ya ke namiji.   Lokacin da na shiga ɗakin mu na ga baƙuwa. Kallon juna muka yi cikin ido tun a wannan lokacin Ma'u ba ta kwanta mini arai ba idanuwanta kir suke a kan mutane. Rahila ce ta tsaya ta na tambayanta ita wacece, ni ina ko hijabin isalamiyata ban cire ba na fita tsakar gidaa in da Gwaggo da ke shanya kaya a igiya sai Mama dake cikin ƙaramin madafin da ke tsakar gida suna kuma hira jefi jefi da juna. " Gwaggo Alhajimu ya dawo ne? Na faɗa ina kallonta. Ba ita ta bani amsa ba Mama ce ta amsa min da E. Lokacin muna gidan Haya ne kafin mu koma gidanmu na Ɗorayi Alhajimu ba shi da bangare sai dai yana zama a ɗakin duk wacce ke da girki ne.   Ina so na tambayi wace ce na gani amman na kasa na wuce zuwa ƙofar ɗakin Mama na tsinkayi muryan Rahila ta na faɗin" La Gwagggo wannan wace ce? Alhajimu ya zo da ita daga Yashe? Ta faɗa bakinta kamar kunne saboda na juya na kalleta. Sai na ji raina ya ɓaci ganinta rike da hannun yarinyar da na ji Gwaggo na faɗin" E sunanta Asma'u. Yarinyar Baabarku Hasiya ce. Anjuma dai Alhaji zai yi muku bayani sosai."   "Asma'u" Na maimaita sunan a ƙasan raina. Kai na kauda ganin Rahila na tsallen murna to miye abin murna. Tana da ni to kuma miye na jin daɗi domin an kawo wata. Duk da akiyasin shekaru ba za mu girmi Asma'u ba tabbas sai dai mu zo tsara. Ni da Rahila tare iyayenmu suka yi goyon cikin mu kwana arba'in ne cif a tsakaninmu. Lokacin da su Yaya Murja suka yo sallama suka shigo gidan suma da Kayan islamiyansu ni kuma na yi sallama a ɗakin Mama Alhajinmu ya amsa sannan na shiga. Sannu da zuwa na yi masa ya amsa ya na kishiɗen kan kujera ganina ya sa ya ɗan miƙe zaune ya na faɗin" Dubu. An dawo? Na amsa ina gurfanawa a gabansa. "Alhajinmu ina tsaraba ta? Ko Hajiya ba ta baka wani abu ka kawo mini ba? Abin da na fara faɗi kenan kuma kamar ba haka ya dace na ce ba. Ƙila ya dace na ce ne" Alhajinmu wace ce ka zo da ita? Amman ban ce ba. Shi kuma bai damu ba yana yar dariya ya ce"Tsaraban ki ta gyaɗa ta nan. Sai da Hajiya ta jadadda mini ke kaɗai ce mai gyaɗar nan."   Ina jin haka na washe baki na zauna ina tambayan ya ya baro su Baba Aminu ya amsa da duk suna gaishe mu. "Alhajinmu yaushe to mu za mu ce? Saboda ina son garin Yashe ina jin daɗi in na je garin Hajiya ta na ji dani saboda sunanta aka sakamin shi ya sa ma Alhajinmu da su Gwaggo ke kirana Dubu. Sauran ƴan uwana kuma Sadiya.   "Sai kun samu hutun makaranta. Tun ga ma Asma'u in za ta je ganin gida ke da Rahila za ku riƙa rakata."   Kallonsa na yi kamar zan yi mgana sai na fasa. Sai kawai na bige da faɗin" Yaushe Hajiya za ta dawo gidanmu da zama? Alhajinmu ya muskuta kafin ya ce"Sai na gama ginin gidana Dubu. Akwai ɗakin Hajiya sai na ɗauko ta zauna damu? Hakan ya yi ko? Sai na gyaɗa masa kai ina mirmishi. Labarin makaranta ya tambayeni na gyara zama ina bashi labari sai da aka kira sallar mangariba sannan hiran mu ta katse.   Kowa ya yi alwala domin gabatar da Sallah. Alhajinmu shi da Yaya Abubakar da Yaya Auwal sai Datti suka tafi masallaci Yaya Hamza baya nan ya na Niger can ya ke karatun babban sakandirinsa. Shi Yaya Abubakar je ka ka dawo ya ke yi anan cikin garin kano.   Ina zaune a gefe ina ganin yadda ƴan gidanmu ke kara kaina akan Asma'u da Yaya Murja ta fara laƙaba mata sunan Ma'u da ya kashe Asma'un ma gabaɗaya. Kowa na rawan jikin tambayata abin da take so ta ci Rahila har tana ɗaukan kayanta ta na saka shi cikin jakar kayan mu na sawa tun da kayanmu na waje ɗaya ne. Ni dai ko magana ta fatar baki ba ta haɗa mu ba kusa da ita ma ban je ba. Har da Gwaggo da Mama a masu kai da kawo akan Ma'u. Sai da aka yi isha'i su Alhajinmu suka dawo. Kowa ya ci tuwon da Mama ta yi amman ban da ni ba kuma ba na jin yunwa ba ne ina ji amman Rahila ce ta baƙan ta mini rai.   "Mama ki haɗa mana Tuwon mu tare da Ma'u ko Sadiya? Tsabar haushi sai kawai na ce"Ni ban ci.". Saboda na ga daga zuwan yarinya amman Rahila ta fifita ta sama da ni kawai sai na ce na ƙoshi. Gwaggo ta kalle ni kafin ta ce"Me kika ci? Sai na rausayar da kai kafin na ce"Bakomai." Sanin halina na tsirfa wani lokacin sai Mama tace a rabu dani. Ranar na sha mamaki domin Ma'u kasa cin tuwo ta yi tana ta jagwalgwalawa har su Alhajinmu suka shigo a ka shimfiɗa babban tabarma a tsakar gida ana zazzaune ana cin tuwo ni kuma ina daga gefe ina kallon kowa ɗaya bayan ɗaya. "Bakuwar nan fa kamar ba ta cin Tuwo" Yaya Abubakar ya faɗa duk sai suka kalleta. Haka ne ko ba ta ci sai wasa take yi da shi a hannunta. "Ko ba ta cin Tuwo ne Alhaji? Cewar Gwaggo. Mama ke ce tambayan Ma'u ko ba ta cin tuwo dai dai lokacin da Alhajinmu ya ce"Anya. Ban sani ba. Asma'u a siyo miki wani abun ne? Sai ta kalle shi amman ba ta yi mgana ba. "Za ki sha shayi? Yaya Abubakar ya faɗa sai ta kalle shi sannan ta ɗaga kai alamun eh. Na sandare a zaune lokacin da Alhajinmu ya ciro kuɗi daga aljihunsa ya ce Yaya Abubakar ya je ya haɗo kayan haɗa shayi a haɗa ma Asma'u tunda ba ta cin tuwo. Da fitansa da sauri da tashin da Rahila ta yi ta ce bari ta sa ruwan zafi sai Mama ta ce akwai ma a saman tukunya a madafi. A daran nan dai Ma'u shayi ta sha da buredinta. Ahalin har Alhajinmu tuwo ya ci. Gabaɗaya hankalin yan gidanmu na kanta kamar sun ga wata sabuwar hallitta. Ina ji Alhajinmu na kora bayanin wace ce Ma'u a garemu gabaɗaya. "Ɗiyar ƙanwata ce Hasiya. Mahaifinta ya rasu ɗan nan garin Yashe ne. Ta dawo hannun Hajiya da zama shi ne da na je na ganta na taho da ita za ta zauna da mu har abada." "Allah ya taya mu riƙo Alhaji." Gwaggo da Mama har suna haɗa baki wajen faɗa. "ƴar uwan ku ce Ina fata za ku kalleta a matsayin jini ɗaya." Yaya Abubakar ya amsa da in sha Allahu.   Yaya Murja ta yi karaf ta ce"Muna son ta Alhaji. Ga ƙawa ma na yi mata Rahila." A lokacin ƙankance ido na yi ganin ta haɗa hannun Rahila da Ma'u waje ɗaya. Saboda sun zauna daman a kusa da juna ne. Ita kuma Rahila sai mirmishi take yi a yayin da Ma'u ke kallon kowa da idanuwanta. Tun kafin zuwan Ma'u daman ni da Yaya Murja ba ma zama a waje ɗaya saboda ta na da faɗa ni kuna ina da baki ta bakin ta ta ce ba ni da kunya manya na mgana ina saka musu baki. "Har da Dubu ma. Saboda na ga za su yi tsara ya sa na samu karfin gwiwan ɗauko Asma'u." Alhajinmu ya faɗa sannan idanuwansa suka fara laluɓena sai ya ganni a can baya ina zaune. "Dubu..'     Ya kirani kamar yadda ya saba kirana sai na amsa. Sai ya ya fito ni da hannu na taso na zo gaban shi. "Dubu ba ki ga yar'uwan ki Asma'u ba ne? Na juya muka kalli juna ni da ita sai na kauda kaina kafin na ce" Na ganta." Ya na mirmishi kafin ya ce"To ga ta nan ke da Rahila na bar ma Amanan Asma'u. Ku yi ƙawa da ita kun ji ko? Ni dai kai na ɗaga Rahila  ce ta amsa har ta na cewa" Alhajinmu a saka ta a makarantar mu don Allah" Sai kawai na ji Alhaji na faɗin "In sha Allahu tun da daman Hajiya ta ce ta gama firamari sai na saka ta a tare daku har islamiya ma" Sai kawai Rahila  ta rumgume Ma'u tana murna. A lokacin Yaya Abubakar ya kalleni ya ga na haɗe rai sai kawai ya kalli Ma'u yana faɗin" In Sadiya ta yi miki wani abu kar ki raga mata ki rama kin ji ko? Ya faɗa yana kallonta lokaci ɗaya yana nuna ni. Ana ta dariya har Alhajinmu. Amman ni ban yi dariya saboda ni ban ɗau abin da wasa ba. Mun ƙara kallon juna ni da Ma'u na wani lokaci sannan kowa ya ɗauke kansa. Yaya Murja har tana faɗin" Wallahi kuwa. In Sadiya ta ga sakenta ai ta shiga uku." Mutane biyu da suka fara bin bayan Ma'u tun kafin tafiya ta yi nisa. Suna faɗa mata abu mara kyau game dani.   A wajen kwanciya ma na ga abu. Mu uku muke kwana a karamar katifa a ƙasa ni da Rahila da Amina. Amman sai Rahila ta jajibo mana Ma'u ban iya shuru ba sai da na ce" Rahila a ina za ta kwanta? Ko ke za ki kwana a ƙasa ki bar mata wajen ki? Daga mgana sai aka ga laifina. Kawai sai Yaya Murja ta fara zagina su suna babban gado ita da Yaya Balki. Gwaggo sai da ta shigo ta raba faɗan da har Yaya Murja ta ce Ma'u ta dawo gadon su ta bar mun katifar sai Gwaggo ta ce Amina ta koma wajen su Yaya Murja mu kuma mu kwanta mu uku ban ji daɗin hukunci Gwaggo ba amman ba ni da mafita ni ta kafafunsu na kwanta Rahila na bari da kwanciya filo ɗaya da Ma'u.   Tun daga wannan ranar Ma'u ta zama yar gida ko na ce tafi ma wasu yan gidan sakewa tun da tama da masu tsaya mata. Da ya ke Rahila tafi mu girman jiki ni kuna siririya ce ina da tsawo ba can can ba amman yanayin fasalin jikin mu ɗaya da Ma'u. Mama ta saka na tsinta kayana na ba ma Ma'u saboda sune za su yi mata kafin Alhajimu ya siya mata wasu kayan saboda wanda ta zo da su duk sun yage an zubar. Sannan Yaya Murja ta yi mata tsifa suka rakata gidan kitso. Komai fa nuna mata suke yi ga shi ba ta cin Tuwo sai dai in tuwon shinkafa ne miyar ganye. Ba ta cin dambu ba ta shan fate tsirfa dai kala kala kuma an ɗaure mata gindi. Duk ranar da aka yi ɗaya daga cikin su sai dai a siya mata wani abun ko kuma a dafa mata wani abun ta ci ita yar gata. Islamiyarmu aka fara saka ta. Sai da aka yi albashi Alhajinmu ya saka ta a makarantar mu ta Goverment Girls Junior Secondary School Diso. Kuma abin mamaki da irin sunan da muke amfani da shi. ASMA'U SULAIMAN YASHE. lokacin da Yaya Abubakar ya kai ta makaranta za a saka sunan Babanta mahaifi sai ta kalli Yaya Abubakar ta na faɗin"Ba sunan Alhajinmu za a saka mini ba? Shi kuma Yaya Abubakar bai yi shawara da kowa ba ya sanya mata sunan Alhajinmu wanda dashi ta ke alfahari har gobe kuma har abada.   Sai da ya dawo gida ya faɗa Alhajinmu kuma bai ce don menene ba. Ba aji ɗaya aka sanya mu ba mu muna A ita kuma ta na B. Anan ne ta haɗu da Shema'u da daman halinsu yazo ɗaya. Rahila ce ke wani rawan jiki akan Ma'u amman ni sai na iya kirga ma maganarmu yadda ba ta mini mgana nima ba na yi mata kowa harkan gabansa kawai ya ke yi. Tun kafin kowa ya lura ni na fara lura da makircin Ma'u saboda ni ke kula da duka motsinta a gaban mutane saliha ce sai a makaranta in ka ganta tare da ƙawarta ba ka ce ita ce ba. Ban taɓa nuna ta a makaranta na ce ƴar uwata ba ce saboda ni ba ni ma da ƙawaye Rahila ce kaɗai na ke tare da ita. Amman ita Rahila mai jama'a ce kowa nata ne ni kuma ko ana son ƙawancen dani ba na ba da fuska ki gaji da naci ki haƙura ba islamiyan ba bakon ba.   Sai ya zamanto komai za a yi mana a gida guda uku ne tare da Ma'u. Ta zama yar gaban goshin Yaya Abubakaar shi ke koya mata karatu baya shigowa hannun rabbana sai ya yo mata tsaraba. Sannan Yaya Murja yadda take ƙaunar Ma'u ko ni yar uwanta ba ta sona haka. Alhajinmu ma gata yake nuna mata shi da su Gwaggo. Tun ina mamaki har na daina na sadakar da Ma'u ta samu tasiri mai yawa a zukatan yan gidanmu. Baaba Hasiya ta zo ta duba Ma'u bayan ta yi wattani huɗu a tare da mu. Lokacin tun ba mu gama zama cikakkun mata ba na ji Baaba na yi ma ƴarta huɗuba da cewa" Kin samu rayuwa mai inganci Asma'u. Ki kwantar da kanki ki yi ma Yaya Sule da Gwaggo biyayya domin ita ce matar Fari. Wancan Rukayyar ba ta gabana. Sannan ki samu cikin yaran nan na Yaya Sule  Maza wani ya yaba dake sai ki yi auran ki kin ji ko?   Ina laɓe ina jin su kuma ba niyyata na yi laɓe ba na zo shiga ɗakin ne na ji suna mgana na tsaya. Ban ankaraa ba sai ga sun fito. Baaba Hasiya daman in dai ta zo a ɗakin Gwaggo ta ke sauka ba ta sauka a ɗakin Mama na taɓa jin tana faɗa ma Alhajinmu a wani zuwa da ta taɓa yi wai Mama mai farar ƙafa ce tun da ya aure ta al'amarinsa ya ja baya tun da ga Lokacin na san ba ta ƙaunar Mama kuma mun taɓa zuwa Yashe a ɗakin Hajiya ta yi ma Mama rashin kunya har Hajiya Dubu na yi mata faɗa ina ƙarama a lokacin amman na ƙasa mantawa da abin. "Ke lafiya? Ko laɓe kike yi mana" Baaba ta katse ni tana hararata. Sai na kalleta kafin na kalli Ma'u sai kawai na ga ta yi mini wani kallo kafin ta ce" Daman Baaba ba ta sona. tun da na zo gidan nan." Sai kawai na saki baki ina kallon Ma'u Baaba kuma ta fara tafa hannu ta na faɗin" To ai sai ta kore ki. Shegiya mai mugun hali to Asma'u zama daram in ji mai naguda."   Maganarta ya jawo hankalin su Mama da Gwaggo Ranar Lahadi kowa na gida. Baaba sai ta fara kuka tana faɗin labe ta kama ni ina yi musu ta na fitowa ta ganni shine ta fara min faɗa na yi mata rashin kunya har ina zagin Ma'u ina cewa ta zo cin arziƙi ba gidan ubanta ba ne"   Ban mantawa maganar har sai da ta kai kunnen Alhajinmu. Yaya Murja har ta na marina saboda ta dunguremin kai na ce Allah ya isa ta mare ni. Yaya Abubakar ya saka ni kneel down ban ji ba ban gani ba. Ni kuma ban ƙaryata su ba amman na yi ma Ma'u wani kallo ganin tana yi mini dariya. Alhajinmu ya yi min faɗa fata fata abin da bai taɓa yi min ba yana ƙara jadadda mini Asma'u ba bare ba ce ƴ'a take kamar kowa.   Ina ji ina gani Ma'u ta zo gidanmu tana mini iko. Sai ta takale ni da faɗa ni kuma ban gane makircinta ba sai na tanka ta shikenan in aka zo jin ba'asi sai ta marairaice ta fara kuka tana faɗin na ce mata in ta gaji ta koma gidan ubanta kafin Ma'u ta rufe shekara a gidanmu har gwammatina a wajen Alhaji ta hambarar da shi da makircinta kowa ba ya faɗin abu mai kyau akaina ko abu ya haɗamu sai ace Ma'u ce mai gaskiya ni ce mara gaskiya. Har Rahila ce mini ta ke yi" Don Allah Sadiya ki daina takurama Ma'u a cikin gidan nan. Ban ga abun da ta tare ki miki ba." Itama goyon bayan Ma'un take yi kenan daga lokacin na fahimci gwara na miƙe na kwaci kaina domin ba ni da mai goyon bayana ko Mama ce na je na faɗa mata sai ta ce ni ce ba ni da gaskiya ba mai cewa a tsaya a bincika. Mutum ɗaya ne bai taɓa goyin bayan Ma'u ba shi ne Yaya Hamza lokacin da ya dawo hutu mun taɓa wani dambe da Ma'u akan ina zaune a ƙofar ɗakin mu ina gyaran jakar makaranta ita kuma ta fito wanka. Ga hanya na bata amman da ya ke makira ce sai da ta ga ba kowa a tsakar gidan sai ta takani za ta wuce ni kuma na miƙe na jawota ta baya wajen ta tsaya sai kafartaa ta turguɗe sai ga ta a ƙasa amman yarinyar nan sai ta fasa ihu ana taruwa ta ce ni na saka mata kafa ta faɗi. Lokacin an saka ranar auran Yaya Murja ita ta saka mini hannu Yaya Hamza ya tsawatar   ashe ya na daga can ƙofar ɗakinsu ya na ganin abin da faruwa.   "Yaya Hamza Sadiya ta ɗora ma  Ma'u karan tsana tun daga ranar da Alhajinmu ya kawo ta gidan nan saboda ta ganta ba ta son tashin hankali."   Kai tsaye ya kalleta kafin ya ce"Ita ta ce miki ta tsane ta? Ya za a yi ta tsane ta sai dai in akwai abin da take yi mata ne wanda ba ta so." Yaya Murja za ta yi mgana ya ɗaga mata hannu kafin ya ce"Ki daina ɗaukan bangare ɗaya a matsayinki na babba ki zama adala. Ina  can daga ƙofar ɗaki na ga abin da ya faru. Ke ce ba ki da gaskiya ta ba ki hanya amman saboda tonon faɗa kika takata ta miƙe ta jawo ki sai aka yi rashin sa'a kafarki ta turguɗe kika faɗi ko ba haka aka yi ba? Ya faɗa ya na tsare ta da ido. Duk rashin kunyarta sai ta sadda kai ƙasa ta kasa mgana shi Yaya Hamza akwai tsare gida ba irin Yaya Abubakar ba ne shi kamar wani mace yake jin kansa. Kai tsaye ya ce Ma'u sai ta bani hakuri dolenta kuma ta bani a kausashe ya kalleta kafin ya ce" Kar ƙi kara takalanta. Ni na san Sadiya ba ta faɗa ba a taɓa ta ba. Ku zauna lafiya da junan ku.'   Sai ta gyaɗa kai. Ni kuma sai ya riƙe hannuna zuwa ɗakinsa yana lallashina. Tun daman akwai fahimtar juna a tsakanimu. Ina kuka ina faɗa masa makircin Ma'u sai abin ma ya bashi dariya cikin dariyan ya ce" To ke ma ki riƙa ramawa mana. Ki daina bari ta na samun galaba a kan ki." Shi mamaki ya ke yi ƴar Ma'u ta iya makirci tunda ya ganin ma idanuwansa.   Zaman Yaya Hamza a gida sai na samu lafiyan Ma'u. Tsoron shi take ji ko maganarsa ta ji yanzu za ta shiga taitayinta. In ya na waje ba ta iya wani motsin kirki har sai ya gama hutun shi ya koma tun kuma daga lokacin nima na gane in ta yi mini abu na rama kafin ta kai ga  haɗa min makircin ni Na haɗa mata amman ba ya tasiri tun da ni daman na yi ƙaurin suna sai ya kasance Ma'u ta riƙa cin nasara akaina ko a makaranta in na ganta tare da ƙawayenta suna nuna ni suna dariya barin ma wannan shegiyar ƙawar tata mai kama da biri Shema'u na tsane ta har acikin raina.   Mun je Yashe sau ɗaya bayan zuwan Ma'u gidanmu. Mun yi sati ɗaya har gidan Babanta mun je sai na ƙara raina mata kamar ma ba sa son ta. Domin ba a wani tarbe mu ba shi ya sa ita kanta ba ta zauna ba. Sai da muka dawo kano sai ita da Rahila suka shirya suka tafi kura in da Baaba ke aure ni kuma na ce ba zan je ba. Daga kuma lokacin in faɗa ya haɗa mu da Ma'u sai na yi mata gori da cewa in ta ji na dame ta Za ta iya komawa gidan tsoho a ƙauye nan dai gidan Ubana ne kuma ba ta isa ta hanani sakewa ba saboda na daina tsoro ko a gaban waye za ta kai ni ta fahimci makircinta ba ya yi mini aiki sai ta koma itama ramawa. Na samu sauƙi Yaya Murja ta yi aure a shekaran 1996. Yaya Balki kuma ba ta kai Yaya Murja zafi ba.    Sai da bikin Yaya Murja sannan na fahimci Ma'u ta ɗau huɗubar Baaba saboda Yaya Hamza ya dawo gida ya gama babban sakandiri shi da Yaya Abubakar duk suna gida jarabarwarsu ba ta yi kyau ba sai sun sake yi. A lokacin na fahimci in dai ta gan shi yanzu za ta fara gyare gyare lokacin muna Ajin biyun ƙaramar sakandiri ne amma har Ma'u ta san ta yi ma namiji karairaiya. Abin da na fahimta kamar tunaninta na kan Yaya Hamza shi kuma Yaya Abubakar tunaninsa na kan Ma'u ni ce na fara lura da ita da kuma abin da ke faruwa saboda ni ce daman idona ke kan duka motsinta.   Shi Yaya Hamza bai ma san ta na yi ba. Namiji ne mai tsare gida ba ya ɗaukan reni ba shi kuma da yawan sakewa mutane shi kuma Yaya Abubakar yana da sanyi ga arhan dariya shi fa kowa na magana dashi ga surutu ba kamar Yaya Hamza ba. Ga aji ga tsare gida mgana ɗaya bayan ɗaya cikin wayewa shi ya sa na ke ƙaunar Yaya Hamza na kuma saka acikin tunanin irin mijin da zan aura mai hali irin na Yaya Hamza ne sannan na ji a raina ba zan iya auran mai hali irin na Yaya Abubakar ba. Shi daman Yaya Auwal da shi da babu a gidan duk ɗaya. Sai a yi abu goma bai sani ba yana da ƙokari ko yau she yana ɗaki yana karatu in ba na boko ba na arabi. Kuma shi yana da ƙyaluwa ba kasafai ya ke saka baki a wasu abubuwan ba. Shi sai a shekaran ma ya zana jarabawar shiga babban sakandiri. *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU #1k NE KACAL, AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* I just published "Page 12" of my story "TURKEN GIDA."::https://www.arewabooks.com/chapter?id=68237857847ebcbfe6d205fe *🅿️12* Sulaiman Abubakar Yashe. Shi ne cikakken sunan Alhajinmu. Inkiyan Alhaji da ya samu ba yana nufin ya je ya sauke farali ba ne.   A zamanin baya in mutum ya baro ƙayensu zuwa garin Kano a matsayin jihar ta cibiyar kasuwanci sai a riƙa tunanin ai ka zama Alhaji ballatana in ka samu rufin asiri to mutane da yawa kan iya sakaya sunanka da Alhaji. Sunan Alhaji ya bi sa har matansa da haka suke kiran shi har muma ƴaƴansa muka wayi gari da sunan a bakin mu. Alhajinmu haifaffan ƙauyen Yashe ne. Ita kuma ƙauyen Yashe tana cikin ƙaramar hukumar kusada. Ita kuma ƙaramar hukumar kusada tana cikin yankin Jihar katsina ce. Garin kusada manoma ne da makiyaya shi ne sa'arsu da shi suka yi kuɗi har suka arzuta wasu ma. Mallam Abubakar ya kasance kafin rasuwarsa matan auransa biyu Halima(Hajiya Dubu) da Balkisu. Kuma ya rasu bayan Balkisu ta riga su gidan gaskiya. Sai ɗawaniya da nauyin komai ya koma kan Hajiya Dubu. Kafin rasuwar Balkisu ƴa'ƴanta biyu ne kacal ta haifa sauran duk sun koma Sule da Hasiya. Sai riƙon su ya dawo hannun Hajiya Dubu da ta riƙe su tun suna kañana ba nuna bambamci. Ita Hajiya Dubu ƴaƴanta uku ne biyu maza mace ɗaya. Akwai Aminu sai Muhammad sani sai ƙaramar su Aina'u wacce ta yi aure sai ta rasu wajen haihuwa. Sulaiman a cikin garin kusada ya gama sakandirinsa daga nan ya yi tunanin haurawa garin kano domin ya cigaba da karatunsa na boko. tun da ya samu na addinin har matsayin sauka. Lokacin ba kowa ke saka ɗan sa a karatun boko ba amman shi Sule da kansa ya kai kansa makaranta saboda ya na sha'awar karatun sosai. Ya tafi kano neman ilimi bayan ya saida gonar da ya gada a wajen mahaifiyarsu. Ashe dalilin haka Kano za ta zame masa mafaka da sillar zama abin da ya zama. Diploma ya fara yi a can kano cikin ikon Allah kuma sai ya samu aiki a NEPA hukumar wutar lantarki na jihar Kano tun da lokacin ana iya ɗaukan masu takardan sakandiri aiki tun da tana da daraja. Samun aikin shi a wajen shi ya inganta masa rayuwa sannan gefe ɗaya ya na kiwo a gida ga Noma Aminu da Sani duk ba su yi karatu ba suna noma sannan suna kiwo.  Ya auri matarsa ta farko Maimuna yar nan garin Yashe ne maƙota suke ma. Sun yi aure tun shekarunsa ba su rufe talatin ba itama ta ƴar yarinya a lokacin ta fara zama a yashe kafin ya kama mata haya a anguwa uku ya ɗauketa suka koma can suka fara gina rayuwarsu. Farkon rayuwar ya fara ta ne da Maimuna(Gwaggo) sai dai kamar auran naTa ya zo masa da tarin buɗi. A shekarun biyun da suka yi aure ya yi noma kuma ya samu amfanin gona sannan ya saida kiwon shi ya siya wasu alherai sai bin sa suke yi da buɗe. Sannan ga albarka samun ƙaruwa ta ɗa Namiji wanda ya ci sunan kakanshi Abubakar. Bayan shi ba daɗewa ta sake haihuwan wani namiji aka sanya ma sa suna Hamza. Maimuna na da cikin Aina'u Sulaiman ya ƙara aure da Rukayyatu yar kano ce. Sun haɗu kuma Allah ya haɗa zukatansu waje ɗaya. Ya aure ta kuma Maimuna ta karɓeta hannu bibbiyu a matsayin abokiyar zama ba kishiya ba. A ƴan'uwansa ba wanda ya yi mgana kan ƙarin auransa sai Ƙanwarsa Hasiya balle da ta ga tun bayan auran shi kenan abubuwa suka fara lalacewa ko Sulaiman ya yi noma baya samun komai sai kiwon sa da ɗaya da ɗaya suna ta kasawa wasu ma sai dai a tashi a ga gawa shi kenan Hasiya ta ce Rukayya ce da ya auro mai farar ƙafa sai da Hajiya Dubu ta tsawarta mata. Lokacin Hasiya ta yi aure anan garin Yashe amman dai Allah bai bata haihuwa da wuri ba. Ana ta raɗe raɗen wanda ta aura ne baya haihuwa kwata kwata sai da aka raba auran ta sake auran wani saurayi Hashimu shima dai kusan shekaru huɗu shuru ba wani labari. Cikin wannan halin  sai kuma a ka fara rasa wasu abubuwan na dukiya. Sai kuma aka yi ta samun ƙaruwa Gwaggo ta haifi Murja ita kuma Mama ta haifi namiji an saka masa suna Auwalu. Sai dai bai yi sati biyu ba Allah ya yi masa rasuwa. Sun tashi daga gidansu na anguwa uku ya kama wani a gandun albasa. A can aka haifi Balki da ta ci sunan kakarmu. Sannan Mama ma ta sake haihuwan Namiji sai aka maida mishi sunan wanda ya rasu Auwal. A yadda Gwaggo ta faɗa mana sun samu cikin mu a Gandun albasa ita da Mama amman kuma ba su haife mu a wannan gidan ba sai a gidan da Alhajinmu ya sake kama musu da ke Fagge shi ya fi girma ne sannan ga iyalai sun fara yawa. Kuma su Baba Aminu suna kawo masa ziyara ba shi da wajen safkarsu.   A yadda labari ya zo mana a bakin Gwaggo. Tsakani na da Rahila kwana arba'in ne. Rahila aka fara haifa, ni kuma sai ranar da Rahila ke cika kwana arba'in sannan aka haife ni. Ni na ci sunan Hajiya Dubu ita kuma Rahila ta ci sunan marigayiya mahaifiyar Gwaggo da ta rasu ba daɗewa a lokacin. Tsakani na da Amina ko shekara biyu bai kai ba shekara ɗaya ne da wattani daga kuma kan Rahila Haihuwa ta tsaya ma Gwaggo. Amman Mama ta yo auta Abdulsalam ana kiran shi Datti. A ƙiyasu mu goma ne cif a gidanmu. Ta bangaren Mama mu huɗu ne ta bangaren Gwaggo kuma su shidda ne sau zuwan Ma'u da muka zama mu goma sha ɗaya. Mun ta so cikin gata saboda Alhajinmu ya na ta samun ƙarin girma a wajen aiki sannan kuma har gobe bai daina noma da kiwo ba. A gidanmu kowa da halin shi misali kamar ni ina da tsiwa sannan ga taurin kai ina da nacin magana. Za ka ganni kamar ban san me na ke yi ba nan kuwa ina ankare da motsin kowa tun taso wata Allah ya yi ni da son jiki har suna Mama ta saka min Sadiya yar laushi. ina da sakin jiki amma ga ƴan'uwana ba ni da sakewa da mutane ba kuma tsoro ba ne kawai ni haka Allah ya halliceni ban cika son mutane ba sosai shi ya sa bayan Rahila da muka yi damben kuruciya tare ban taɓa wata ƙawa ba. Sabanin ita Rahila mai sanyi ce ga hakuri sannan tana da faram faram da mutane kuma kowa na ta ne shi ya sa in yara sun zo gidanmu tabbaci wajen Rahila suka zo ni ko mutm ya so mu saba ba na barin haka ta faru sai na janye jikina. Kamar ta bangaren Yaya Abubakar da Yaya Hamza ne. Shi Yaya Abubakar ba shi da zafi shima dai akwai sakewa da mutane ga surutu saɓanin Yaya Hamza da bashi da wasa ƙwata ƙwata. kamar misalin Yaya Auwal ne shi kuma wannan ɗan i dont care ne. Abu goma za a yi a cikin gida bai ma san an yi ba shi fa rayuwarsa kawai yasani sai ko in ya ji yunwa ya ci abinci. Yaya Aina itama ba ruwanta ba ta da faɗa amman Yaya Murja ta fi kowa shegen shisshigi da shiga abin da ba ruwanta ga sa ido sannan ba ta da haƙuri kamar zawo ta ke. Shi ya sa ba mu taɓa shan inuwa ɗaya da ita ba ita faɗa ni kuma rashin kunya. In aka duba Amina da Datti. Gwara ma Datti ita Amina miskila ce irin Auwalu sha'ani ko an saka su aciki ma ɓata lokaci ne abu nawa zai faru a cikin gidan suna nan amman ba dai ka ji bakin su ba. Shi ya sa na ce a gidanmu kowa da irin halin da ubangiji ya yi masa dai dai gwargwado da zai zauna da mutane. ****** *2000* *Ɗorayi* Hajiya Dubu ce ta ƙure Radiyo ɗin ta a tsakar gida tana sauraran gidan radiyon jihar kano ana karanto labaran yammaci. Zaune take saman tabarma daga can ƙofar ɗakinta. Gwaggo na gefen ta suna jin labaran jefi jefi Mama ma dake  can gefe tana tankaɗen garin masara a cikin farantani. Tana ɗan saka musu baki jefi jefi. Ina kwance a kan gadon Hajiya Dubu har wani ƙara nitsewa ne ke yi. Ba wanda ya san ina ciki saboda gadon mai rumfa ne. Kuma san da na shigo har Hajiya Dubun ba ta sani ba. Yau alhamis ba islamiya kuma ni ce ke da girki gabaɗaya na gaji. Da rana alkubus ɗin alkama na yi gabaɗaya a gajiye na ke daman kun sani yar laushi ba na son aiki kawai ina kwance bayan na idar da sallar la'asar ina hutawa Mama ta leƙo ta ce min na fito na ɗora miya a lokacin tura baki na yi kafin na ce. "Mama Tuwo kuma? "E." Haka ta faɗa tana kallona idanuwana har ya ciko da ƙwallah. Gaskiya dai na gaji kuma a ƙasa ƙasa sai da na ce na gaji Mama ta yi tsaki ta na sakin labule kafin ta ce"Ke daman ai ko kina kwance ne sai kin ce kin gaji. Malama ki taso kar dare ya yi kin kuma san Alhaji ya hana ku tuwon dare." Na fi mintina talatin kafin na taso sai da Mama ta ƙara leƙowa tama faɗin za ta make ni. Ni kaɗai ne a ɗakin Amina ta bi su Rahila yau wata yar islamiyan mu na aure ni daman ba na zuwa biki ban je ba ina gida amman daga baya na fara nadama da na sani na bisu sai na ga wanda zai tsaya har a ce ya yi tuwon dare. Shekaru wajen biyu kenan Alhajinmu ya ce aikin gidan da ya dawo kanmu ni da Rahila da Ma'u tun da alokacin mu ne ƴan matan gidan muna cikin shekaru na sha tara ne kuma muna zangon karatu na ƙarshe a matakin babban sakandiri a makarantar GGSS ƘAWAJI dake kwanar dakata a jihar kano.    Yaya Balki ma ta yi aure shekaru wajen huɗu da suka gabata. Yanzu a gidan daga mu sai Datti da ke ajin ƙarshe a ƙaramar sakandiri sai Amina dake ƙokarin shiga matakin farko a babban sakandiri. Sai Yaya Muntari da ya dawo gidanmu da zama shekaru uku yana karatu anan FEC KANO. Sai Hajiya Dubu da Alhajinmu ya ɗauko ta bayan mun tare a sabon gidanmu dake Ɗorayi. Domin Alhajinmu tuni likafa ta cigaba ya koma aiki da Hukumar KEDCO na jihar Kano. Sai Yaya Abubakar da ke karatu a jami'ar Bayero yana karantar Vitnary ya na shekara ta uku ne. Sun ɗaɗe a gida shi da Yaya Hamza kafim su samu su ci jarabawar babbar sakandiri a lokacin samun jami'ar ba ta wahala cin jarabawar sakandiri ne mai wahala wajen sau uku suna sake rubutawa sannan suka ci. Shi sai ya zauna a gida nan kano shi kuma Yaya Hamza sai ya lula Sokoto Usman ɗanFodiyo University Udus. Acan ya ke karantar accounting shima yana shekara ta huɗu ne. Yaya Auwal kuma yana Nasara state University  Keffi. A shekaran nan ya tafi shima. Mun zama ƴan mata duk wani tantanin budurci ya gama bayyana mana. Alhajinmu yana da burin in mun gama sakandiri mu yi aure. Ban san dai tunanin sauran ba amman ni ba ni da burin aure yanzu sai na gama jami'a na samu aiki saboda a lokacin Alhajinmu ya samu ƙarin girma manaja ne a hukumar wutar lantarki ta jihar kaduna kuma ya samu daman ƙaro karatu tun a zamanin baya. Ni ma sai na ji ina sha'awar haka. Rahila dai na san cewa ba ta da ra'ayi mai zurfi kamar nawa, Ma'u kuma har gobe ba jituwa a tsakanimu shi ya sa ni ban san me take ciki ba. Amman shekarun sun tura da ya sa na ƙara aminta da zargina na cewa Tana son Yaya Hamza shi kuma ba ta gabansa duka ɗaya ya ke ɗaukan mu. Shi kuma Yaya Abubakar a yanayin yadda ya ke kafa kafa da Ma'u son ta yake yi ita kuma baya gabanta ni dai ina gefe ina kallon komai ina tunanin ta yadda Ma'u za ta ɓullo ma lamarin ƴan'uwa guda biyu. Amman na ci alwashin ba zan bari ta zo gidanmu ta raba mana kan yan'uwa ba na san halinta ba ta da kirki kanta kawai ta sani. A yadda muka taso a haka muka girma. Ni da Rahila mune masu tsawon. Sai dai muna da bambamcin jiki ita Rahila ta fi ni kiɓa. Ma'u kuma muna da yanayin jiki bamu da kiɓa amman ita ba ta kai mu tsawo ba ta ɗauko tsawon mahaifiyarta ne Baaba dake can kura ta hayyaffa da wasu ƴaƴan bayan Ma'u. Amman kuma duk wanda ya ganmu ya san mu ɗin jini ɗaya ne. Ballatana ni ban cika yawo da Ma'u ba sai dai makaranta in ya zama dole a gida kuma ta shafa mini lafiya saboda ba na ƙyaleta. Sannan dawowar Hajiya Dubu gidanmu ya sa ba ma wanda ya isa ya taɓa ita da Yaya Abubakar sun sha artabu a kaina. Tun kuma da Hajiya ta dawo gidanmu na tattara kayana na koma ɗakin ta can na ke kwana sai in har na ga dama ne nake shiga ɗakin mu duk saboda kar na haɗu da Ma'u za mu kwana gida ɗaya mu tashi amman ba za mu yi ma juna mgana ba. In ko faɗa ya haɗa mu in na fara gaba da ita sai mu yi wata ba mu yi mgana ba sai in Rahila ta gaji ta kai ƙarar mu wajen Alhajinmu in ya yi mgana sai Ma'u ta ce in ta yi mini mgana ba na tanka ta. Sai a ɗora laifin a kaina amman thank god Hajiya na nan ita ce ke zama justice ɗina in dai akan Ma'u ne.   Bangaren Yaya Murja ma ba ta sauya zani ba. Ko bayan auran ta in dai za ta zo gidan da abun arziƙin da za ta kawo ma Ma'u da Rahila har da Amina ni kuma sai ta ce ba ni da kunya. Ni ma da na gane ko gidan zan iya kirga zuwana, na fi zuwa gidan Yaya Aina ko Yaya Balki in ma fitan ya kamani kenan. Har a lokacin ba ni da wata kawa da zan iya nunawa amman Rahila da Ma'u suna da ƙawayen su. Barin ma Ma'u ƙawarta din nan Shema'u har lokacin suna tare su Gwaggo duk sun santa ta na zuwa nan gida itama Ma'un ta na zuwa gidan su saboda su haɗu da Ma'u su yi ta munafunci  har can dakata tare suke a makaranta. Ni dai kamar yadda ban son Ma'u itama Shema'u ban ƙaunarta domin gabaɗaya halin su ɗaya. Za mu haɗu sau goma a makaranta sannu ba ta haɗamu da Shema'u amman in ta zo gida tana mini fara'a kamar ta Allah. Na daɗe da yarda da mganar hausawa da suka ce sai hali yazo ɗaya ake abota. To akwai mugayen hallayar Shema'u da Ma'u da suke kamamceceniya.   ****   Mama  ta shiga madafi ta ga na ɗora miya tana tafasa ko ƙashin miyan ma da Muntari ya shigo da shi ban saka ba sannan ban ko ɗora tuwo ba. Ba ta yi mamaki ba sanin halina sai ta fito tana faɗin" Sadiya me take son zama ne ni Rukayya? Gwaggo na zaune ta ce"Me ya faru hala? Sai ta kaɗa kai tana nufar ɗakin mu kafin ta ce" Ba ta ko ɗora tuwo ba. Kuma miya na ta dahuwa ko ƙashin da muntari ya shigo da shi ba ta saka ba." Lokacin ta ɗaga labulen ɗakin tana kwala min kira ina daga ɗakin Hajiya har na fara barci. "Ba ta fa a ɗakin" Hajiya hankalinta na wajen jin radiyonta ba ta ma jin su.  Gwaggo ce ta leƙo dakin Hajiya ta na kiran sunana na ji har gyara kwanciya na yi. Ban ankara ba sai ji na yi an ɗaka  mini duka a cinyata da sauri na miƙe ina sosa wajen sai na ga Mama tsaye a kaina tana huci. Cikin tura baki na ce"Kai Mama a cinya fa kika dake ni." "In ba ki tashi ba sai na mare ki a fuska yanzu." Ina jin haka na yi saurin saukowa daga gadon saboda na san halinta tana da saurin hannu. Ina fitowa na ga har mangriba ta yi Gwaggo ta kalleni ta na faɗin" Sadiya ho. Ke ko koyi da ƴan'uwanki ba kya yi. Su in dai suna da aiki akan lokaci suke gamawa." Haushin aikin dake gabana ya sa ban ko yi ma Gwaggo magana Hajiya ce ta kashe radiyon ta na faɗin" Me ya faru ne? Ke Dubu ina kallabin ki? Sai a lokacin na taɓa kaina ba ɗankwali ina tura baki na koma na ɗauko a saman gadonta da ya saɓule na ɗaura na fito dai dai Hajiya na faɗin" Dare ya yi ina su Asma'u ne? Su kama mata su yi girkin tare.' Jin haka sai na washe baki amman sai Mama ta ce" ƙyalata ta Hajiya. In na su aikin ne tana ɗaki kwance kauda kara ba za yi musu ba. Sai su ne za a ce su yi mata na ta aikin? Sai murnata ta koma ciki sai dai Hajiya ta sake ƙwatana da ta ce"Ita ai ba yanayin su ɗaya ba. Tun da sun fita zafin nama ai ba a zauna a zama ɗaya ba." Jin haka yasa na miƙe da karsashina saboda na san in su Rahila suka dawo sai Hajiya ta yi musu mgana sun tayani. Icce na haɗa na ɗora Tuwo Mama na ta faɗan in ina girki har jajjage ita ke yi mini kawai na fito na ɗora ina jin ƙyashi na duba har wanke wanke da sharan tsakar gida da Amina ce ke yi sai da ta yi kafin ta fita sai ni da in dai ina da aiki sai ran kowa ya ɓaci ina cikin madafi ina tura baki amman raina fes domin na samu raran kuɗin cefane Alhajimu 2k ya ba ni kayan Miya kawai na siya kashi daman yaya Muntari ya kan tura ma kuɗi in dai za a yi miya ya siyo. Kuɗin cefane ke saka ni farinciki in ranar aikina ya zagayo amman bayan haka yini na ke yi cikin baƙin ciki sai na ji gabaɗaya duk na gaji kamar mahaukaciya haka nake komawa a irin yanayin ana takata sai na yi sati ina gaba da mutum.   Ana kiran sallar mangariba su Rahila suka shigo. Gwaggo sai da ta yi musu faɗan da Alhaji ya shigo fa. Ma'u ce da yanayin mganarta ta ce" Mun taso da wuri Gwaggo rashin abun hawa ne." Ina madafi ina talge da fitila a hannuna ba wuta. Na gama kenan na rufe na fito nepa suka kawo wuta. Miya ta isa kaɗi har na kwashe ƙashin ina fitowa Rahila ta kalleni yadda na yi kaca kaca kafin ta ce" Wai ke ba ki gama tuwon ba daman?   Wani kallon tara saura kwata na yi mata na wuce ta. Ba domin ta matsa ba sai na bangajeta. Ma'u  wajen rijiya ta nufa bayan ta miƙa ma Amina Hijabinta ta kai mata cikin ɗaki wajen Hajiya na nufa ta miƙe tana kwashe tabarma tun da an kira mangariba raɗa na yi mata a kunne. "Hajiya ga su Rahila nan." Sai ta kalleni kafin ta juya ta na kallon Rahila wacce ke mgana da Ma'u. "Rahila da Asma'u in kun yi sallah ku kama ma Dubu aikin nan ta gama kafin Sule ya shigo." Rahila ta amsa da to amman Ma'u sai da ta kalleni nima na kalleta gwalo ta yi minibni kuma na ɗauke mata kai na koma kitchen. Gwara na kaɗa miyar da kaina na bar musu su ƙarisa tuwon. Sai da na kaɗa miyar na sauke sai na saka ruwan wanka ni kuma na je na yi alwala saboda ma ba na son mgana a ɗakin Hajiya na yi sallar mangariba na kuma yi zama na ƙarshenta dai Rahila da Ma'u suka ƙarisa tuwon Alhajinmu ya shigo gida bayan isha'i lokacin ina wanka a bayi daman ina ta Allah Allah na gama na fito kar ya dawo.   Ina fitowa yana tsakar gida an baza masa tabarma. Na so na yi saɗaf na shige ɗaki amman hakan bai samu ba sai da ya ganni.   "Dubu" Dole na amsa ina kallon shi faɗa ya fara min na wankan dare wannan karon ma Hajiya ce ta fito ta ƙwace ni.   "Sule ka ƙyale yarinyar nan. Yau fa a tsaye ta yini tana aiki har daren nan gwara ta yi wanka ko ta ji daɗin barci."   Alhajinmu ya yi shuru amma Mama sai da ta ce" To ta riƙa yin aikin ta da wuri mana. Sadiya son jikinta har bani tsoro ya ke in ta yi aure ban san ya za ta yi ba " Alhajinmu sai da ya yi dariya kafin ya ce" In ta ga ta samu ɗakin kanta za ta yi ne Rukayya. Nan saboda ta ga akwai su Asma'u ne in ba ta yi ba su za su yi." Ni dai na samu na shige ɗakinmu tunda nan ya fi kusa ina shiga na ga Rahila da Ma'u ana ta hiran bikin da suka je. Na yi kamar ban gan su ba mai na ɗauka na shafa ina da sauran kaya a ɗakin na buɗe jakar Rahila na ɗauko wata rigata na saka kafar Ma'u na wajen da gangan na taka ta saboda na ga ita ba makauniya ba ce ta na ganina a wajen ba ta janye ba. "Dutse kika taka hala? A sakarce na kalleta kafin na ce"Wataƙila." Ta yunƙuro za ta yi mgana Rahila ta hana ta da cewa" Kyale ta Ma'u. Ke kuma Sadiya don Allah ki koyi zaman lafiya." Na kalli Rahila kafin na taɓe baki ina faɗin" Sannu yar koran gimbiya." Haka na ke ce mata in na ga tana haƙiƙancewa akan lamarin Ma'u. Wani lokacin Rahila ba ta cika ban mamaki ba irin Yaya Abubakar bai ɗaukan lamarin Ma'u da sauƙi amman ina masa uzuri makauniyar soyayya ce ke damun shi.    Tun bayan dawowar Hajiya kano rabon mu da garin Yashe amman dai su Baba Aminu suna zuwa duba Hajiya in kuma wani sha'ani ya tashi ƙwansu da ƙwarƙwatan su. Ma'u dai ta manta da gidan tsoho ba zuwa take yi ba. Kuma ni dai ban taɓa ganin wani daga cikin dangin babanta ya zo nemanta ba. Amman tana zuwa kura wajen Baaba itama Baban na yawan zuwa kuma duk saboda Ma'un ne. In ta tashi zuwa tare da Rahila suke zuwa ni ko in yi zamana a gida ban taɓa marmarin zuwa ba. Tun da na fahimci Baaba ba ta ƙaunar uwata nima daga ita har yarta ba na som su tun ballatana da na fahimci Baaba na da son abin duniya.   Ko irin a makaranta ƙawaye an sha zama kowa na faɗin irin ra'ayin mijin da zai aura ni ba na mgana saboda ra'ayi na ya bambamta da na kowa. A lokacin maza ba sa gabana duk da an sha tare ni a hanya ban taɓa maida kai ba saboda har a lokacin ban sami irin zaɓina ba. Rahila kuma daman na fara zargin suna soyayya da Yaya Muntari. Na daɗe ina mamakin shi so daman haka yake? Saboda Ya Muntari gajeren namiji ne kuma baki sannan yana da barkwanci ni dai ban ga abin so a wajen shi ba anawa tunanin kenan Ma'u ko an taɓa tare ta a hanya muna tare ta ce ita ta na da miji. Buɗe bakin Rahila tana dariya sai ta ce. "Yaya Abubakar ba. Na sani kun dace kwarai Ma'u." A lokacin Ma'u ta kasa yin gaddama amman yanayinta ya sauya ni kuma ina gefe ban ce komai ba a raina na ce maji ma gani an tura uwar amarya biko. Kuma gashi Ma'u da jinin masu kuɗi amman ba ta sauraran kowa ni dai masu cewa suna sona daga malaman islamiyamu sai na boko ita kuma Rahila gajerun maza kamar Yaya Muntari da ta sauya ma suna zuwa Yaya Muktar. Shekara ɗaya ta shafe tuni har mun zana jarabawar fita babban sakandiri a ƙarshen shekaran  2000 sai dai dukkanmu ba wacce ta ci sai mu ka dawo zaman gida. Lokacin Yaya Abubakar da Yaya Hamza sun gama karatun su suna hidimar ƙasa. Shi Yaya Hamza can sokoto ya yi zamansa yana hidimar ƙasarsa. shi kuma Yaya Abubakar nan kano wani ƙaramin asibiti na dabbobi kuma ya gamawa suka riƙe shi duk da yana ta cewa zai ƙaro karatu shi kuma Yaya Hamza bai tsaya ba tuni ya nemi gurbin masters a University of Ibadan. Sai dai in ya zo gida hutu bai ma cika zuwa ba bai wuce a shekara sau uku haka ba. Mun sake zana jarabawa a 2001 shima dai ba a dace ba. Ga shi su Baba Aminu sun fara mganar ya kamata Alhaji ya aurar damu. Tun da lokacin 15 16 ake aurarwa mu gamu sha tara muna shirin shi ga ta ashirin amman ba mgana ƙwaƙƙwara gwara ma Rahila mganarta da Ya Muntari ya kai gaban Alhajinmu kuma ya yi murna ƙwarai. Kowa kuma ya yaba da haɗin tunda su suka haɗa kansu. Ni ce dai haɗin ke ban dariya in ta yi ma Rahila dariya in na ga ta na rawan jiki akan Ya Muntari. To gwara shi ana son shi. Shi fa Yaya Abubakar yana yi ne amman kwata kwata kamar ba a son yana yi ba.   In da ma su Gwaggo suka fahimci yana son Ma'u bini bini sai ya je Kura gaida Baaba da ɗan siyayyan shi itama kuma ta fahimta. Magana dai ta yaɗu a tsakanimmu amman ba ta je wajen Alhaji ba. Su Yaya Murja kar a ji labari tana faɗin tuwona maina ne za'ayi ita ƙanwar ango sannan yayar Amarya. Ban taɓa tunanin Ma'u da Baaba za su iya tunanin abin da suka aikata ba. Domin Yaya Abubakar kafin ya kai mganar Ma'u wajen Alhaji ya yi magana da Gwaggo sai ta tambaye shi ko ita Ma'un tana son shi sai ya ce a'a bai bayyana mata ba sai ta ce ya nemi yardan Ma'u.     Abin da ya sa na san haka ya faru. Ranar wata asabar da daddare Yaya Abubakar ya kira Ma'u zuwa zaure na fito daga ɗakin Hajiya na gansu sun wuce shi ya sa na bi bayansu a lokacin ne na ji yana faɗa mata yana sonta ya faɗa ma Gwaggo ga abin da ta ce. Ma'u ba kunya ba tsoron Allah ta buɗe baki ta ce ma Yaya Abubakar ya yi haƙuri ita a matsayin yaya ta ɗauke shi ba da wani manufa ba tun da aka kawo ta gidan nan Yaya Hamza ta ke so. Ina laɓe ina ganin har duƙa mata ya yi amman Ma'u ta fara kukan munafunci sai ya ce shikenan saboda ita muguwa ce sai ta ce wai ya taimaka ya rufe mganar ba ta so Alhajinmu ya ji shi kuma ya ɗau alƙwarin ba wanda zai ji Gwaggo ma zai san abin da zai faɗa mata. Kafin ta taho na shige ɗakin Hajiya ina maida numfashi ta na kwace sai da ta ce" Dubu lafiya? Ina sauke numfashi na ce" Ba komai Hajiya." Ranar ko barci ban yi ba ina tunanin mafita ko da ba shiri tsakanina da Yaya Abubakar jinina ne. Na ji tausayin shi da ya sa na fara tunanin yadda zan ɓullo ma lamarin. Washegari na je gaida Alhaji sai ga Ma'u bayan sun gaisa ta ce wai in Alhaji ya bar ta za ta je kura wajen Baaba. Ina jin haka na ji a raina akan Yaya Abubakar ne. Saboda lokacin wayar hannu ba ta daɗe da shigowa ba sai wane da wane Alhajinmu kaɗai ya mallaketa. Ina jin sanda ya ce shikenan sai ta shirya cikin ni ko Rahila wata ta rakata ina jin haka na yi karaf na ce" Alhajinmu ni zan rakata."    Ba Ma'u ba har Alhajinmu sai da ya yi mamaki. Ma'u kam sake baki tayi kawai tana kallona. "Lalle Hasiya na da babbar baƙuwa." Haka Alhajinmu ya faɗa ni ai ban tsaya ba na koma ɗakin Hajiya ina haɗa kayana Hajiya ta ce lafiya na ke haɗa kayana.? "Ma'u zan raka kura wajen Baaba." Da mamaki Hajiya ta kalleni ba ta da wani karfi kwana biyun nan ba ta da lafiya ta na fama da zazzaɓi sai da aka kaita ma asibiti. Maida kanta ta yi ta kwanta lokaci ɗaya ta na faɗin" Yau kuma? To Allah ya tsare." Kowa ya ji zan raka Ma'u sai ya yi mamaki har Rahila sai da ta ce"Allah ya sa Sadiya kin sauya kenan." Ni ba na ta kanta ni na san abin da zai kai ni. Ma'u ba ta da yarda za ta yi ta na ji ta na gani na shirya kayana Alhajinmu ya bamu kuɗin mota mun bar gidan ba ma mu haɗu da Yaya Abubakar bawan Allah shi kaɗai ya san abin da ke damunsa. Har muka isa kura sannu ba ta haɗamu da Ma'u ba. Mun isa gidan Baaba ita kanta ta yi mamakin ganin mu tana da abokiyar zama. Zaman dai ba wani daɗi ita kanta ta yi mamakin ganina tare da Ma'u cikin mamaki ta ce" Yau kuma wannan ce ina Rahilan? Ma'u ce ta amsa da cewa ni ce na rakota wannan karon. Duk da ban samu tarban da ya kamata ba ban damu ba Zainab ce kawai ƙanwarta ta kulani duk da ta na ƙarana ne sai sauran ƙannenta maza. Bayan mun yi salla mun ci abinci Ma'u na son keɓewa da Baaba amman ba hali tun da na hana ina wajen. Sai daddare sun ɗauka na yi barci suka ƙule cikin ɗaki ba su san ina kwance laɓo ina dakon su ba. Ina ganin sun shige ciki nima na tashi saɗaf saɗaf na laɓe ta jikin labule a daga nan na ke jiyo muryan Baaba ƙasa ƙasa. "Shi wai Abubakar ɗin ya ce ya na sonki? Ma'u ta ɗaga kai cikin damuwa saboda ina hangosu ta jikin labulen ƙurwan ɗakin Sai kawai Baaba tayi tsaki kafin ta ce" Shi ma dai da rigima ya ke. Ai ke matar manya ce duk da ban raina Abubakar ba. Sai dai tunda Hamza kike so shi ne zaɓina kuma ba kin ce yana can yana cigaba da karatu ba? Nan gaba Allah kaɗai ya san abin da zai zama." Ma'u ta kalli Baaba kafin ya ce" Baaba ya zan yi? Har fa ya faɗa ma Gwaggo. Kuma su ma yan gidan sun fara gane yana so na ba na so Alhaji ya ji labari Yaya Abubakar ya yi min katanga da abin da na ke so.' Baaba ta kama hannun ta lokaci ɗaya tana faɗin" Kwantar da hankalin ki. Gobe da safe ku koma gida ni kuma cikin satin nan zan shigo. Da ikon Allah ke rabon Hamza ce." Sauri na yi na koma wajen kwanciya a falo a saman katifa na yi kamar mai barci sai can bayan wani lokaci Ma'u ta fito ta dawo ta kwanta a gefena. Ta kwana mutsu mutsu nima haka a cikin raina ina tunanin ta wata hanya zan hana Baaba aiwatar da kudirinta? Har muka koma kano ban samu mafita ba. mun koma mun iske Yaya Abubakar na kwance ba lafiya daga ni sai Ma'u muka san dalilin ciwon shi. Zazzabi da ciwon kai har dai da Yaya Muntari ya raka shi asibiti ya ga likita.  Na ɗauka Ma'u za ta tausaya masa amman sai na ga kamar ba ta da tausayi ban samu mafita ba har Baaba ta zo gida ta kuma tara su Alhajinmu ta kawo mganar Ma'u tana son Hamza tun tuni ganin abin na gida ne yasa ta zo da mganar Alhajinmu na jin haka ya fara murna ya ce kuma zai aurama Ma'u wanda ta ke so. Gwaggo ta na so ta yi mgana amman Baaba ta san me za ta ce sai ta datse ta. Bayan an gama zaman a ɗaki Hajiya Dubu ke faɗa mini abin da ke tafe da Baaba. Daman na san za a rina. Ma'u na so ta haɗa mana yaƙi a gida Yaya na sonta ita kuma tana son ƙani. Cikin lokaci kawai na ji ana mganar haɗa auran Yaya Hamza da Ma'u da kuma Rahila da Muntari. Yaya Abubukar kuma Alhajinmu ya ce fito da matar aure. Ba shi da mafita illah ya amsa Gwaggo ta so ta yi magana sai na ji sa yana roƙonta ta bar mganar shi da Hamza duk abu ɗaya ne. Kowa ya ji ba Yaya Abubakar ba ne sai ya yi mamaki saboda shi dai Yaya Hamza kowa ya san halin shi. Shi kuma Umarni kawai Alhaji ya bashi, shi kuma bashi da mafita. Amman kwata kwata bai taɓa hasaso da ya auri Ma'u ba. Da farko da aka sanya lokaci na yarda makaman yaƙina ganin har Alhajinmu ya ba ma Yaya Hamza umarnin dawowa gida ya ga Ma'u ya kuma dawo sun gana Ma'u ta yi ta rawan jiki ita a dole burinta ya cika.  Sai dai me Yaya Abubakar ya kasa ɗaukan takwallalin ya haƙura da Ma'u ya fara rama a tsaye ga yawan ciwo ina tsoro kar rashin tausayin Ma'u ya kashe min ɗan uwan na yi ta kulla yadda zan yi na rasa mafita. A wannan halin an saka ranar auran su da zaran mun ƙara zana jarabawar sakandiri a karo na uku. Yaya Muntari ya samu aiki da wani kamfanin sarrafa leda. Shi kuma Yaya Hamza ya fara aiki da bankin first bank a can ibadan ɗin. Ni ba kaina na damu dashi ba saboda ban samu miji ba daman kuma ni burina sai na gama jami'a zan yi aure. Muna gabda gama zana jarabawarmu kawai Yaya Abubakar ya fara wani ciwo har da kwanciya a gadon asibiti ganin haka yasa na ce ba zan bari Ma'u ta kashe mini ɗan'uwa. Ni na je na samu Hajiya Dubu na faɗa mata duk abin da na sani. Ita kuma ta samu Alhajinmu ta faɗa masa abinda ke faruwa ni na ba da shaidar Gwaggo ma ta sani da aka kirata sai ta amsa amman ta ce Abubakar ɗin ya ce a bar mganar kar kowa ya sani kuma itama tana ta tabbacin ciwon nan saboda Ma'u ne. Alhajinmu bai yanke hukunci ba sai aka sallamo Yaya Abubakar daga asibiti Alhajinmu ya taramu a gaban kowa da kowa har da masu auran da Yaya Hamza da Alhaji ya sa ya dawo garin. A gaban kowa da kowa ya tsitsiye Yaya Abubakar sai da ya faɗi gaskiyan yana son Ma'u duk yadda ta yi ta masa inkiya da ido kar ya faɗa. Har Baaba an kirata tana wajen jin haka shima Yaya Hamza ya ce ya bar ma ɗan uwansa shi daman baya sonta. Hankalin Ma'u da Baba ya tashi saboda Alhajinmu ya ce an maida auran Ma'u akan Yaya Abubakar kuma ya yi ta faɗan cewa ba domin na zo na faɗa ba da an yi auren kuma azo ana neman mafita. Ban manta kallon da Ma'u ta yi mini a wannan lokacin ita da Baaba. A kuma nan take ta fashe da kuka ta ce ba ta son Yaya Abubakar Yaya Hamza take so shi kuma ya ce a ƙanwa ya ɗauketa. Alhaji ya rasa mafita yace zai yi mgana da sauran yan uwanshi. Har sai da su Baba Aminu su ka zo garin. A ɗakin Hajiya suka zazzauna suka tattauna Hajiya Dubu saboda samar da masahala sai ta kalli Alhaji kafin ta ce "Sule a shawarata kar ka matsa ma Ma'u ko Hamza. Tun da Hamza ya ce baya so. Abubakar ma yace ya hakura da ita to mu fasa wannan al'amarin kowanensu ya nemo mata itama ta nemo nata mijin mu aura musu sai na ke ganin kamar in muka yi haka za a samu mafita." Su Baba Aminu ma sun aminta da shawaran Hajiya kuma ita Alhaji ya ɗauka aka warware mganar auran Ma'u da Yaya Hamza har da Yaya Abubakar ɗin bayan an ce kowannen su ya zaɓo na shi matar daga waje. Wannan lamarin shi ya ƙara rura wutar kiyayya tsakani da Asma'u.    Kwana biyu da faruwan lamarin na samu salama saboda ko banza itama ba ta samu abin da take so ba. Sannan Yaya Abubakar ba zai ga laifin Yaya Hamza ba. Ina kwance a saman gadon Hajiya ba ta ɗakin tana makewayi Ma'u ta shigo har ɗakin ta tsaya a kaina. "Lafiya Ma'u? Idanuwanta jajir ta kalleni kafin ta fara mgana cikin zafi." "Wallahi na tsane ki Sadiya. Na tsane ki." Nima kai tsaye na ce" To ai nima ba sonki nake yi ba Ma'u." Sai kawai ta nuna ni da yatsa kafin ta ce" Tun da kika zama silan rasa burina Sadiya ina so ki rubuta ki ijiye na rantse da sarkin da ke busamin numfashi sai na kuntata ma rayuwarki sai na saka ki a uku fiye da yadda kika sakani ko kin samu farinciki sai na yi sanadiyar lalatashi zuwa baƙin ciki. Kamar yadda na saba cin nasara akanki haka zan cigaba da nasara akanki har ƙarshen rayuwarki.". Kai tsaye nima na kalleta kafin na ce"To in kin fasa. Ta Allah ba ta ki ba. Aniyar ki sai dai ta biki. Kuma ban yi nadaman abin da na yi ba. Da ki ɓata mana zuru'a gwara ke ki rasa na ki burin na zalunci." Sai kawai ta yi kwafa ta fice a ƙofar ɗaki suka haɗu da Hajiya tana kiran sunanta ta yi banza ta wuce da ta shigo sai ta tambaye ni ko mun yi faɗa da Ma'u ne? Ina komawa na kwanta na ce" Ni ina ruwana da ita." Hajiya na faɗin" Sai hakuri ki rika kyaleta yanzu kin san ga abin da ya faru.' Ina jinta ban tanka ba. Tun faruwan lamarin bayan wani lokaci Ma'u ta warware Yaya Abubakar ɗin ma da sauƙi. Ta nuna ma kowa ba komai amman ni nasan ba ta hakura ba. Tsakanina da ita sai ya ƙara lalacewa.  Ko da yaushe in ta fakaici idon mutane sai ta gaya min mgana nima sai na rama haka dai muka yi rayu cikin bata sona nima bana sonta. Jarabawar mu ta fito cikin ikon Allah ni da Ma'u muka samu ban da Rahila ba ta damu ba tunda aure za ta yi ni kuma ina ta murna zan fara jami' a. Alhajinmu ya so ya hana Yaya Hamza ya matsa masa aka nema min gurbin karatu a jami'ar bayero a shashen tsumi da tattalin kasa economics. Ma'u kuma ta ce bording za ta yi sai aka nema mata Federal University Minna  ko na ce ita ta nuna tana bukatar can ɗin.   Saboda lamarin da ya faru bikin Rahila da Yaya Muntari ba a ma ƙara mganar shi ba sai zuwa gaba in zukata sun huta. Yaya Auwal kuma yana can keffi sai salla sallah ma ya ke zuwa ganin gida wani abun ma sai dai ya ji labari bai san faruwan shi ba. Na fara zuwa jami' a farkon shekaran 2002. Ma'u ma a shekaran ta tattara ta tafi Rahila kuma tana gida amman auran su da yaya Muntari ana tunanin karshen shekara tun da shima ya cigaba da karatunsa.   A kuma lokacin ne Allah ya yi ma Hajiya Dubu rasuwa. Rasuwan da ta gigitani matuka.  Na yi kuka domin har daren da za ta rasu mun kusa raba dare muna hira sai dai mun wayi gari ba ta raye tabbas ni aka yi ma mutuwa. Rasuwar Hajiya dubu da wattani uku lokacin muna jarabawar semester farko a makaranta na haɗu da Yusuf Muhammad Inuwa(Tafida) kuma mun yi aure da shi a ƙarshen shekaran 2002 rana ɗaya aka yi bikin mu tare da Rahila da Yaya Muntari. Kuma ana saura kwana talatin da biyar auran mu Allah ya yi ma Mama rasuwa daga kwanciya barcu ciwon ciki dare zuwa asuba ta ce ga garin ku nan. *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU #1k NE KACAL, AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. *🅿️13* Tun ranar farko da na fara ganin Yusuf na ji a raina tabbas na haɗu da namijin da ya gama cika zaɓina.  Sannan na san tabbas zai iya yin katanga da cikar burina na sai na gama Jami'a na samu aiki zan yi aure. Saboda in na bari ya suɓuce mini samun kamarsa zai yi mini wahala Tun da gashi tuntuni ina tsumayen shi. Shi wanda ya dace ɗin amman ban samu nasaran haɗuwa dashi ba sai a wata ranar laraba. Daga cikin BUK na ke mun gama lacture tun safe har yamma na sha wahala ina tafe kamar zan faɗi, ba zan mata da kayan da ke jikina a ranar ba. Wata atamfa ce mai ruwan ganye hijabin jikina fari ne sai takalmin dake kafata mai saukaƙƙen tudu.   Daga bakin get ɗin jami'ar da na fito ni kaɗai ce. Ko anan ɗin ma ban yi wata ƙawa da na saki jiki da ita ba a dai gaisa kawai. Ina tsaye ina neman abin hawa ba ni da masaniyar tun a lokacin Yusuf ya ganni kuma Allah ya haɗa zuciyarsa da tawa a waje ɗaya. Hauwa'u Jamilu ta fito tare da ƙawarta da tare na gansu Samira. Na gansu amman sai na ɗauke kaina kamar ban gan su ba, lokacin duniya na kwance sannan abubuwa duk ba su zama gari kamar yanzu ba. Ko wayar hannu nan sai wane da wane ke riƙe shi ko a ajinmu akwai ma su ita handset amman sai ɗaya ɗaya nima dai ina cikin mara shi. "S. Yashe sai gobe." Haka Hauwa'u ta faɗa sai na kalle su kafin na ɗan gyaɗa kaina. Ganin ina ta tsaye ban samu abun hawa ba sai na fara tafiya zuwa bangaren yamma su kuma su Hauwa sun yi gabas. Ina tafe ina sauri saboda yamma ta fara sauka biyar za ta iya gotawa a lokacin. Ban san ya na bina ba. Saboda ban ji takun tafiya ba sai da na ji sallamarsa cikin muryansa mai zaƙi da haiba ta maza masu kyau da Aji. " ƴan mata doguwa Salamu Alaikum." Haka ya faɗa da farko ban yi niyyar na juya ba amman yanayin muryansa da salon da ya yi magana su suka rinjayi tunanina da zuciya na ɗan waiwaya na kalle shi yana daga bayana kaɗan ina juyowa sai kawai ya yi mini mirmishi irin mirmishinsa da na ke matuƙar so a tare dashi. Na yi saurin ɗauke kaina na cigaba da tafiya amman na sauya takuna. Gaba na ta faɗuwa ban san so ba amman ina tunanin nima na fara son Yusuf a wannan ɗan kallon da na yi masa. Lokacin da na yi gaba ina ta fargaban Allah ya sa ya cigaba da bina ya yi mini magiya sai na yi masa kwatancen gidanmu. Har ɗan rage sauri na yi ina jinsa ya na cigaba da bina lokaci ɗaya yana sake faɗin. "Haba ƴan mata. Ina ta mgana shuru" Ɗan sake kallon shi na yi. Kai ya haɗu! Haka na faɗa a cikin raina ban wani saki fuskar da zai fahimci yanayina ba amman tabbas Yusuf ya shiga cikin zuciyata a karon farko da muka haɗu. Cigaba da bina ya yi yana min mgana amman ban tanka shi ba sai dai kuma tuni na gama haddace kamaninshi da kayan dake jikinsa. Tun a wannan ganin farko ni na san Yusuf ɗan gayu ne kuma yana da ilimi kuma shi ɗin daga ganin ɗan manyan mutane. Yana sanye da ƙananun kaya. Jeans  baki ne sai T. Shirt fara ta na da zanen baki a jiki amman ban iya ganin me aka rubuta ba. Takalmin ƙafarsa mai rufi ne sannan akwai wasu takardu a hannunsa. Ta gefen ido na gama ƙare masa kallo a cikin zuciyata kamar in yi ta tsalle saboda murna. Tsayawa na yi ina taran abun hawa shi kuma sai ya ƙara marairaicewa yana faɗin. "Tafiya za ki yi ko muryan ki ba ki bari na ji ba? Sai na kalle shi kafin na ɗan ɗauke kaina ina faɗin" Ya dace ka tari budurwa a hanya kana yi mata mgana? Da sauri ya ce"Afuwan. to ki faɗa min sunan ki sai ki bani lambar wayarki sai na samu lokaci na zo gida mu yi mgana." Kallonsa na yi sai ya yi wani sanyi kafin ya ce"Please." Sai kawai na rausayar da kai kafin na ce"Sunana Halima. Amman ana kirana da Sadiya." "Wow.! Nice name Sadiya ta." A karon farko da ya fa kirana da Sadiyarsa. Sai na yi mirmishi ina so na tambaye shi sunan shi amman na kasa. "Ba ni da waya. Gidanmu kuma na Ɗorayi in ka ce gidan Alhaji Sulaiman Yashe za a nuna maka." Ƙuramin ido ya yi kafin ya ce" Sadiya kin tabbata zan same ki in naje? Sai na samu kaina da ɗaga masa kai kafin na ce" In sha Allahu." Mirmishi ya yi mini nima sai na maida masa martanin mirmishi. Shi ya taran min motar  haya na hau sannan ya ɗaga mini hannu kafin ya ce"Bye. See you " Ina so na ɗaga masa hannu amman sai na fasa sai dai na gyaɗa masa kai ina ɗan mirmishi. Na koma gida a ranar cikin farinciki har sai da Rahila ta fahimci yanayina. "Sadiya karatun yau hala ya fi miki daɗi ne? Sai na kalleta lokacin ina tsaye ne a tsakar ɗakin mu ina mirmishi ni kaɗai ban sani ba har Rahila ta shigo ta kama ni ina ta mirmishi ni kaɗai. "Me kika gani? Na faɗa ina kallonta sai ta ƙara matsowa kusa da ni cikin raɗa ta ce"Ko dai? Da sauri na matsa baya ina faɗin" Ko dai me! Ni matsa ki ban waje." Na faɗa ina tureta ina mata dariya. Daga tsakar muka ji Gwaggo na gaisawa da Ya Muntari. Sai na ga Rahila na mirmishi a raina na ce daman haka ake ji in ka haɗu da wanda kake so. Sai na daina ganin laifin Rahila akan Yaya Muntari saboda na fahimci haɗuwar jini ce. "Uhm kin ji muryan Yaya Muntari kin kasa sukuni." Sai ta harareni tana faɗin" Ya Muktar dai ko Sadiya? Ta faɗa ƙasa ƙasa. Ni ko ina ta dariya da gayya na fita tsakar gida dai dai zai koma can waje in da ɗakunsa suke da sauri na ce" Ya Muntari ina yini." Sai ya juyo yana amsawa kafin ya ce" Sadiya yan makaranta an dawo." Sai na amsa masa ina kallon Rahila ta cikin ɗakin mu tana faman harara ta. Ni kuma ina dariya. Yanzu saboda makaranta an ɗauke mini aikin gida sai in ranar weekend ne. Rahila ce da Amina ke yi tun da Ma'u na Minna sai an yi hutu ta ke zuwa ganin gida. Haɗuwata da saurayin da ban san sunan shi ba sama da sati ɗaya bai zo ba kuma ban ƙara ganin shi ba. Har in na fito daga cikin Jami'a. Na yi ta tsayawa ko da yaushe ina hasashen zan ƙara ganinsa amman shuru sai na fara damuwa. Ko ya zo ne bai gane gidan ba? Ko kuma dai! Na kasa iya fassara yanayin da na ke ji amman na rage walwala da fara'a kamar dai ina so na bayyana damuwar haka. In na kwanta sai na riƙa mafarkin shi tabbacin dai ya samu matsugunni a cikin zuciyata.   Har na fara fidda rai domin an fi kwana goma da haɗuwarmu . Kamar  wasa ranar da ya fara zuwa kofar gidanmu muka san juna sosai ranar laraba ne da yamma da wuri na dawo daga makaranta bayan na yi sallar la'asar na ci abinci sai na ɗan kwanta amma ba barci na ke yi ba. Na ji dai yaro ya yi sallama amman ban maida hankalina a wajen ba. "Wai Sadiya ta zo in ji wani a waje" Haka na ji an faɗa. Kamar an jeho ne sai gani a tsakar gida ina faɗin" Waye? Haka na faɗa ina kallon yaron Rahila na kan kujeran tsakar gida tana gyaran wake Gwaggo da Mama suna can ƙofar shashen Alhajinmu suna hira Amina na bakin ma zubar ruwa ta na wanke wanke. Gabaɗaya suka juyo suna kallona cikin mamaki. "Ni ma ban san shi ba." Sai da na juya ina kallon su Gwaggo sannan na dawo hayyacina. Sai kuma na yi sanyi na kasa motsi. "Je ka ce tana zuwa." Mama ta faɗa tana kallon yaron. Ya juya ya fita amman ni na kasa motsi daga in da na ke tsaye.. Rahila na dariya ta kalleni ta na faɗin" ki koma ciki ki ɗan gyara mana! Ko haka za ki fita? Sai na dawo hayyacina na koma ɗaki da sauri na sauya hijabina na duba madubi na gyara fuskata duk ina tunanin shi ne ko ba shi ba ne? Sai dai zuciyata na ta rawa. Na saka takalmina na fito tsakar gida bakina na rawa na ce" Zan je waje." Gwaggo ce ta tanka ni Mama ba ta ma a wajen ta shiga ɗaki. "To Sadiya. Amma kar ki daɗe saboda Alhaji." Sai na amsa mata na juya na fita Rahila na yi mini dariya ganin yadda na yi wani sanyi ina tafe kamar ba na son tafiyar. Lokacin da na fita na ci karo da shi a tsaye a ƙofar gidanmu yau ya yi shigar manyan kaya ne. Yana tsaye ya na fuskantar ƙofar gidanmu hannayensa harɗe ƙirjinsa. Na ji lokacin da zuciyata ta ta yi tsalle ta dawo waje ɗaya lokacin da na ganshi. Sannan farinciki ya bayyana a saman fuskata lokacin da muka haɗa ido ya sakar min mirmishi nima na maida masa martanin mirmishinsa lokacin da na ke tafiya zuwa in da ya ke tsaye ya na kallona. Bayan mun gaisa ina noƙewa kai tsaye ya fara faɗin" Sunana Yusuf Muhammad Inuwa. Ni anan garin aka haife ni amman mahaifina da mahaifiyata mutanen Rano ne. Na yi karatuna har matakin Masters ranar da kika ganni ma a Buk na je ganin supervisor ɗina ne akan project ɗina. Sadiya da gaske na ganki kuma sonki sannan ina son in mun gama fahimtar juna iyaye su shiga ciki domin maganar aure." Bayan takaitaccen bayanin da ya yi min ban ja aji ba na bashi dama mun ɗan jima muna hira har Yaya Abubakar ya dawo ya ganmu suka gaisa da juna. Daga wannan lokacin ba a ɗauki wata biyu ba hatta Alhajinmu ya san da Yusuf sannan in ya zo zence a wajena a cikin gida muke yi. Zuwa lokacin kuma ni da shi mun gama shaida muna son juna sannan mun aminta mu zauna kan inuwa ɗaya ta aure. Na gama mutuwa a kansa kamar yadda shima ya gama mutuwa a kaina, kowa dake gidanmu na gidajen auran su da mazan gabaɗaya su san labarin YALLAƁAI da tun a lokacin na laƙaba masa wannan sunann tuni na watsar da tunanin sai na gama Jami'a zan yi aure ba zan iya jira ba gwara na yi auren sai na cigaba da karatuna a ɗakin miji. Ban taba sanin daga ɓarayin Yusuf zamu fuskanci barazana daga dangin sa ba. Duk da ya sha bani labarin gidansu da yan uwan shi na san suna da yawa tunda mata huɗu babanshi ya yi kafin rasuwarsa. Lokacin da muka haɗu da Yusuf a shekaru iyakarsa 27 to 28 ni kuma ina cikin shekarata ta ashirin na kuma san ya karanta Architecture ne masanin zane zane bai samu aiki ba amma yana buga buga. Mutum ne mai sabgogi da yawa da kuma ƙoƙarin neman na kansa. Yusuf ya turo magabatansa daga Rano. Ya ce mini ƙanin mahaifiyarsa ne da ƙanin mahaifinsa sun zo sun gana da su Baba Aminu an ba su damar dawowata ta gaba za a tsaida mgana. A wannan gabar ne Alhajinmu ya gudanar da bincike a hakan Yusuf har na samu cikakken bayanin waye shi da asalin shi. ***** Marigayi Alhaji Muhammad Inuwa kafin rasuwarsa ya yi aiki a Ministry of Agriculture and natural resources. Ya rasu a shekaran 1999. Ya bar mata huɗu da tarin ya'ya guda 21. A kimanin ƴaƴan da haifa ashirin da takwas ne bakwai sun rasu. Sannan bayan rasuwarsa da wattani matarsa ta huɗu ta bi bayan shi Hajiya karima. Ɗan boko ne da ya yi shura tun a zamanin baya da boko bai yawaita ba. Sannan sun shiga gwamnati an dama da su sosai ta sanadin wani amininsa Alhaji Yusuf wanda ke riƙe da sarautar Tafidan Rano. Shima ya rasu tsakanin shi da abokin nashi shekara ɗaya ne shima ya rasu ya bar mata biyu da yaya maza da mata. Alhaji Muhammad Inuwa da Alhaji Yusuf Tafidan Rano sun fito daga jiha ɗaya ne. Wato Rano sai kuma suka haɗu a makarantar kwana ta Barewa collage dake zariya. Ajin su ɗaya sannan ɗakin  kwanan sy ma ɗaya ne. Daga lokacin suka fara aminta bayan sun gama sun nemi jami'a ɗaya ta Usman ɗan fodiyo University. Kowanne ya karanta bangaren da ya zaɓa shi Alhaji Inuwa sai ya yi karatunsa kan harkan Noma da tattalin ƙasa shi kuma Alhaji Yusuf Tafida sai ya kan harkan sanin Siyasa. Bayan sun gama karatun su sun samu manya ayyuka. Shi Yusuf a matsayinsa na jinin sarauta na Tafidan Rano yana da hanyoyin isa ga Gwammatin kano a lokacin. Dukkansu kowanen su ya je ya ƙaro karatu kuma dalilin Alhaji Yusuf Tafida rano Alhaji Inuwa ya tsinci kansa a Ministry of Agriculture na gwammatin Jihar kano a wancan zamanin. Alhaji Muhammad Inuwa ya fara aure da Hauwa'u(Nene) wacce haifaffiyar Rano ce kuma duk an san juna. Kuma a sha'anin bikin ne Alhaji Yusuf Tafida ya haɗu da ƙawar Nene Aminiyarta Fatima Binta(Hajiyar Tafida) Sai Aminan junan suka aure ƙawayen junan. Dalilin haka sai zumumcin su ya ƙullu a tsakaninsu mai ƙarfi. Kuma ya samu kafuwa har zamanin ƴaƴan su. Shi dai Alhaji Yusuf Tafida kafin rasuwar ya ƙara mace ɗaya Hajiya kaltume. Ita ce ke da jibi da masautar kano kuma har ya rasu ƙaton gidan shi na nan a Rano. Amman dai yana da gida a cikin garin kano shi kuma Alhaji Inuwa a cikin garin kano ya gina ƙaton gida a gwammaja mai shashe da yawa daga nan Nene ta fahimci Mijin nata yana da ra'ayin zama da mace sama da ɗaya. Ya kuma tabbatar mata tun da sai da ya yi mata huɗu jeras sannan kuma dukkansu matan sun haifa masa zuru'a.   A bangaren ɗakin Nene Zuwaira ce Babba sai Maimuna.  Sannan ta yi Bahijja. Sai da ta yi mata uku sannan ta samu namiji sai Alhaji Inuwa ya cika burinsa ya sanya masa sunan Amininsa Yusuf suna kiran shi( Tafida) a kuma a tsukin Hajiyar tafida itama ta sauka an samu namiji itama sai kawai shima Alhaji Yusuf ya saka masa sunan Amininsa Inuwa suna kiran shi(,Tariq) a kuma lokacin a gidan su Nene mahaifinta matan shi biyu mahaifiyar su Nene Innayi ta daina haihuwa amman abokiyar zamanta Hannatu( Inna) ta haifi ɗan ta Namiji sai ya ci sunan mahaifinsu Abdulmu'iz sai suna kiran shi da Abba shi ne kuma auta a gidan su Nene sai ya kasance waɗanan mazan guda uku sun tashi tare sun girma tare sun kuma ba da misalin kyakyawan zumunci juna a tsakanin su. Bayan Yusuf sai  Muttaƙa sai auta Halimatu. Sai Maman Farko(Hajiya Saliha) ita yar kano ce  ita ta ɗan fi Nene yawan ƴa'ƴa domin ƴaƴanta bakwai ne. Usman shine Babba wanda Zuwaira da Maimuna ne ke gaban shi a tsarin manyan gidan sai shi. Bayan shi sai Nasaratu ita sa'ar Tafida ne sai Nasir sai Jafar sai Suwaiba da Jamila autar ta mai suna Hindatu. Daga ita sai Hajiya Zaliha(Hajiya iya) ita ƴaƴanta huɗu ne. Hafsat ce babba sai Saffiya sai Muhammad kabir sai Musbahu. Sai ta huɗun da  ta rasu Hajiya karima ita ƴaƴanta uku ne. Ummu Salama sai Adnan Jawahir ce ƙaramar su. Kuma bayan rasuwarta riƙon su Jawahir ya koma ya koma ƙarkashin kulawar Nene. Kaf ƴaƴan Marigayi Alhaji Inuwa kamar shi sun yi ilimi sun kuma tsaya da kafafun su. Ba matan ba sannan ba mazan ba wasu sai sun gama karatun suke auren wasu kuma suna cikin yi suke auren sai su ƙarisa a gidan mazajen su. Yusuf dai ya yi karatunsa na fimari kaf a garin Rano ne a gidan Alhaji Yusuf Tafida tare da Tariq da kuma Abba. Sannan bayan sun gama ya nema musu makarantar kwana a kaduna mai suna. Federal  Sceince and tecnical collage (FSTC) Kafacan Kaduna. Su uku tare suka yi makaranta tun daga matakin fimari har matakin gama babban sakandiri daga nan sai Yusuf ya tafi Abu zaria. Tariq ya tafi jami'ar Ibadan shi kuma Abba ya tsaya anan BUK ya yi karatun shi.   Sun gama degree farko kuma kowanne ya zaɓi in da ya ke so ya cigaba da karatunsa. Shi Tariq Jami'ar lagos ya koma ya yi masters ɗinsa shi kuma Yusuf ya dawo kano ya yin da Abba bai cigaba ba ya koma Rano ya fara kasuwanci da noma tunda abin da ya karanta kenan.  Yawancin zaman Yusuf ba a kano ba ne ya fi zaman Rano shi ya sa akwai sabo na musamman tsakaninsa da yaran gidan Marigayi Tafida, kuma a gidan ba a kiran sunan shi sai dai Baaba. Ita kuma Hajiyar Tafida ta ce Tafida mutun ɗaya ce ke kiran shi da Daddy Saudatu(Gimbiya) ƙanwar Tariq ce. Kuma ta ci sunan gimbiya ce matar sarkin Rano a wancan lokacin. Mganar aurena da Yusuf ta yi barazana domin yan'uwansa sun ce ba zai yi ba ya yi gaggawa sannan bai gama karatu ba kuma ba shi da sana'a mai ƙarfi sai buge buge. Kuma shi Yusuf Mutun ne da ba ya son zama a ƙarkashin wani ya fi son ya zauna in his on. Ban taɓa ganin mutun mai tsari irin Yusuf ba ya karanta abin da ya shafi zane zane amman kuma ya na da sani kan abin da ya shafi gini da sauran su. Tun kafin mu yi aure ya sha  faɗa mini so ya ke yi ya buɗe kamfanin shi na kan shi ba ya ƙaunar aiki a ƙarkashin wani ya fi so ya cika burinsa na yadda zai gina kansa domin ƙara ma matasa karfin gwiwan kan dogaro da kansu. Bai taɓa faɗa mini yan'uwansa sun ƙi auran mu da farko ba sai daga baya saboda lokacin da suka ƙi sai ya kai su ƙara wajen kawun nan na su sna bangaren babansu da ke Rano su suka shige masa gaba akan mganar auran mu. Daga karshe da suka ga ya dage sai suka hakura suka bar shi ya yi. An saka rana ba lokaci mai tsawo ba sai aka sanya shi lokaci ɗaya da na su Rahila. Abu kamar wasa kamar mafarki sai ga shi abu ya tabbata kowa ya ji zan yi aure sai ya yi mamaki kamar irin su Ma'u da ba haka ta so ba sannan da ta ga Yusuf sai ta fahimci na tsere mata ko ba ta fada mini ba a fuskarta na ga hassada da kishina. Duk da rasuwar Mama ta saka an ƙara wata ɗaya kafin auran mu mutuwar da ta gigitamu har Alhajinmu da har gobe ya kasa manta rashin Mama. Da Gwaggo da ta daɗe cikin jimami shi ya sa a sha'anin bikin ba a yi wani taro sosai ba. Amma dai kayan ɗaki komai iri ɗaya ni da Rahila babu in da aka bambamta mu ni a anguwar Dakata muka fara zama ita kuma Rahila nan cikin anguwan Ɗorayi ne tana kusa da gida. A tsarina ban taɓa tsara ma kaina fara rayuwa a gidan Haya ba. Amman sai gashi nan ne muka fara shimfiɗa rayuwarmu ni da Yusuf. Ya san ina karatu kuma ya yi alƙwarin barina har na gama karatuna. Mun sha amarcin mu sosai na ke jin daɗin zama da Yusuf in zan je makaranta wani lokacin har rakani yake yi in bai da wajen zuwa in shima yana da shiga makaranta sai mu jira juna mu koma tare. Yana samun kira haka in ana son zane sannan tun lokacin yana karambanin karɓan kwangila gini sai ya nemo ma'ikata da injiniya. In na ce a zamana da Yusuf bai gatanta ni ba na yi ƙarya. Ya yi mini hidima da jikinsa da Aljuhunsa. Nene ta karɓe ni a matsayin surukarta. Amman ban da yayyen Yusuf da suke uwa ɗaya barin ma Anty Bahijjan sai bayan auran na ke sanin sun so hana auran mu a cewar su ya bari zuwa gaba sai ya auri Gimbiya. Sai daga baya na fahimci Gimbiya na son Yusuf soyayyar da ba ta iya ɓoye shi. Shi kuma ba ta gan shi a ƙanwa ma ya ɗauke ta. Suna son haɗa auren ne saboda amincin iyayensu amman kuma hakan bai yuyu ba. Farkon auran na yi musu biyayya kamar zan bauta musu saboda dai ina auran ɗan'uwansu. Kuskurena na farko shi ne na yi tunanin yin tsarin iyali saboda karatuna sai dai cikin Jidda shi ya zo ya shammace ni. Watanni tara da kwana huɗu da aurenmu na haifi Jidda da ta ci sunan Nene Hauwa'u. lokacin ina aji biyu ne zan shiga uku na sha matukar wahala ga ciki ga karatu ga aure shi ya sa ina yaye ta na nemi shawaran Yusuf akan ina son in yi tsarin iyali shi kuma sai ya ba ni goyon baya muka je wani asibitin kuɗi na fara karɓan allura duk bayan 6 months  har na shekara biyar. Daga wannan alluran sai ta zame mini matsala. Na gama karatun kuma ina son na ƙara haihuwa amman shuru ko domin goron su Anty Bahijja tunda suna ganin na daɗe ban ƙara haihuwa ba bayan Jidda sun ta zargin ko planning na ke yi amman ban faɗa musu ba tunda kamar na tona asirin kaina ne.   A kuma lokacin muka shiga rayuwa na halin babu. Yusuf ba aiki yake yi ba. Sannan aikin da ya kan samu ya ragu sai jifa jifa. Duk wani abin da na ke dashi sai da ya kare na zo da ɗan kunnen gold wanda na siya da sadakina amman sai dai na siyar da shi. Da cewar Yusuf in ya samu anam gaba zai siya mini. Saboda haka ya sa na nemi aiki a makaranta kuɗi anan kusa damu na fara koyarwa saboda mu rufa kan mu asiri. Ba zan raina ba in Yusuf ya samu na samu to amman yanayin aikinsa kafin ya samu fa? Kuma na yi na yi ya nemi aiki shi yaƙi a dole sai ya tsaya da kafafunsa. Ta ina za ka iya samar da kamfani baka da kuɗi? Zan iya cewa renon jidda ma tare muka yi tun lokacin ina makaranta tare muke zuwa ya rike mini Jidda har mu fito daga karatu ko ya kai ta gida wajen Nene. Da na fara Koyarwa shi na ke barin ma a gida kafin na dawo ya gama duka aikin gida har girki ma ya yi. Kuma albashina ba na iya cin komai dashi ɓukatunmu na ke yi mana dashi. Sai dai yan'uwan shi duk ba su ga haka ba a tunaninsu na tsaida haihuwa ne saboda Yusuf bai dashi ni ma na fara damuwa sai na fara yawon private hospital ana ce mini ba matsala zan ƙara haihuwa sai da Jidda ta kai shekara Takwas da wattani na ƙara haihuwan y'a mace sai ta ci sunan Anty Maimuna muna kiran ta Baby zuwa lokacin kuma Yusuf ya samu buɗi tunda har ya siya fili ya fara gini muma kuma Alhamdulillah muna cikin ni'imarsa. Na sha wahala a haihuwan Baby C.S ma aka yi mini daga nan kuma sai na yi ta samu matsaloli na zubar jini da kasala  sai juwwa. Daga baya sai na fara ramewa sannan haihuwa ta zo ta tsaya mini cak sai na fara jelen gen zuwa ganin likitoci a asibitocin kuɗi suna cin kuɗina suna gaya mini ba matsala in sha Allahu zan ƙara haihuwa. Tun ina ɓoye lamarin har ya fallasa ga dangin Yusuf tsarin iyali na yi ya ba ni matsala shi dai ya ce bashi ba ne ya faɗa sai na yi tunanin Ma'u tunda itama bayan ta gama karatu ta dawo gida ba daɗewa ta haɗu da Alhaji Mustapha cikin wattani kaɗan suka yi aure sai wayan gari na yi na ga Ma'u tsudum a cikin dangin mijina. Saboda sanin Yusuf a harkan kwangilan gine gine sunan shi ya ɓace daga Yusuf zuwa Injiniyan da ya yi ma haye. Sannan da tsarina da shawarata mu ka samar da sunan kamfanin shi. HM TAFIDA AND SON LIMITED." Hauwa' u and Maimuna kenan da sunana ya so ya saka saboda gudun mgana na ce mu saka na ƴaƴanmu. A can zariya road ya kama office ɗin kuma ya yi ma kamfanin sa rigister. Ya taimaka kwarai wajen samun kwangiloli masu tarin yawa. Kuma balle ya san jama'a connenction ɗin shi da mutane yasa har Gwamnati na bashi aikin kwangila. Akwai kwangilan da ya samu na gina wata makarantan koyon aikin Jinya ta ƙanin marigayi Alhaji Yusuf Tafida. Wanda shi ne yanzu a matsayin Tafidan rano yana aiki a ministry of education. Yusuf ya samu alheri sosai da shi ya ƙarisa mana gini sannan na bashi shawaran ya buɗe gidan buɗo saboda yanayin aikin shi. kuma ya yi na'am cikin lokaci kaɗan ya buɗe gidan Buɗo. Mun tare a sabon gida bayan ɗaukan shekaru sama da biyar ana ginin shi. Tsarin gidan da komai tsarina ne Yusuf kuma ya yi zanen sanan yan kwangilanshi suka gina gidan da jagorancin. Tarewarmu a anguwan lodge road. Yusuf ya hana ni aiki ya ce na zauna a gida na huta. Duk da ina da ra'ayin fashion na shiga makarantar koyon kwalliya da gyaran kai. Har zanen shagon da Yusuf zai buɗe mini ya zana amman har yau bai tabbata ba. Amman hidimdimu ba za su bari hakan ya samu ba. Tun da muka koma wannan gidan ƴan'uwansa suke tunanin ina can na samu daula kuma ban haihuwa sai kwanciya ina cin daula sun manta irin gwagwarmayan da muka sha a baya komai Yusuf ya samu ko ya mallaka tare da ni aka mallake shi. Ko bayan tarewarmu a sabon gida sun so ya ƙara aure domin Gimbiya ba ta yi aure ba har Masters ta yi. Da ta ga dai Yallaɓai na Sadiya ne ita kaɗai sai ta hakura ta auri wani tsohon sanata matansa uku ita ce ta huɗu. Ta na can Abuja kuma har ta samu aiki da NGO. A shekaru sama da goma sha huɗu da wattani da aurena da Yusuf na san me ake kira aure da gwagwamarya. Ba zan ce ba mu taba samun matsala ba mun sha samu tun da ni ina da saurin fushi ga baki shi kuma yana da sanyi wani lokacin amma in ya yi fushi ba shi da kyau. Mun sha samun matsala akan ƴan uwan shi mussaman Anty Bahijja da Anty Maimuna. Daga karshe shi sai ya bi bayan ƴan uwan shi ya bani rashin gaskiya. Nene dai ba na ce ta taɓa nuna mini kiyayya ba. Ban taɓa samun matsala da ita ba shi ya sa na ke yi mata biyayya iya iyawata. Sannan akan zamantakewa ma muna samun matsala amma sai mu shirya kan mu a tsakaninmu. Amman matsalan da muka sha samu da ya yi ƙamari shi ne akan Gimbiya. Ban samu salama ba sai da ta yi aure. Yusuf ya samu kusanci sosai da Gimbiya itama kuma ba ta sakin jiki da kowa sai shi in na nuna fushi ko kishi sai ya ce ina da matsala ina da zargi. Kuma sai ta zo gidan Nene shi kuma in ya je ya biye mata ya kai dare har kwalliyan da na yi sai ya lalace  in na yi mgana sai ya ce bai san lokaci ya tafi ba suna can suna hira da Gimbiya. Ban samu salama ba sai da ta yi aure sannan na ji hankalina ya kwanta amman fa da in na ji zai je Rano yini na ke yi zullumi. Da shekaru suka gangara haka sai nima na fahimci an gogi jigida. Na daina matsa ma kaina kan wasu abubuwan tun da na fahimci ni ba zan ga karshen su ba nima ba za su ga karshe na ba. Sannan irin wannan matsalolin ana samun su a kowani dangi. Sai dai na wata ta fi wata. Nene ce dole ne ita ne kawai ban daina yi ma biyayya ba amman sauran duk abin da na ga zan yi shi na ke yi. Na daina tsoron a ce na yi ko ban yi ba saboda shekaru sun gungura nima wuyana ya isa kaurin da na isa ga kaina. Shi ya sa na ke tafiyar da rayuwata da ga ni sai mijina sai ƴaƴa na. Sauran abin da ya fi ƙarfina na bar ma Allah ni yanzu abu ɗaya ne a gaba na. Ina son na ƙara haihuwa ko domin Yallaɓai mai son yara sosai. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWAR GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. *🅿️14* Present. Da safen tea muka sha gabaɗayan mu amman ban da Yallaɓai saboda kamar  akwai gajiya a tare dashi. Tun bayan da ya dawo daga sallar asuba ya kwanta yana ta barci sai na ƙyale shi tun da  na ga har wayarsa ma sai da ya kashe. Da wuri Saude ta zo na saka Jidda ta fito da kayan na su. Daga kitchen ɗina akwai wata kofa dake fidda mutum ta can baya in da muke yin wanki ko shanya. Ko tara ruwan sama can na ce su je su yi wankin har da Baby da ta saka rigiman sai ta yi na ce a ƙyaleta ta yi. "Umma ba fa wanki ta iya ba. Ɓata jikinta kawai za ta yi da ruwa." Ina ɗakin na su ne a lokacin ina gyarawa saboda Saude ba za ta samu lokaci ba gwara ni na gyara gidan. Kallon jidda na yi da ta shigo kawo min karan Baby. "Bar ta yi. In ta jiƙa jikinta ai shike nan ta huta." Haka na faɗa ina mirmishi saboda ni dai na san ina kamar ta ban so aiki ba amman tunda tana so ai ba zan hana ta ba. Wucewa Jidda ta yi amman ranta bai so ba sai na bi ta da kallo ina dariya. Jidda akwai son aiki da karambani in da ta biyo ni da na shiga uku. Har yanzu da shekaru suka tura ba na son aiki barin ma girki, ko anan domin ya zame mini dole ne na ga ba mai yi mini. Saude daman in ta zo sai dai na saka ta yi ma yara. In da Allah ya so ni da Rahama Yallaɓaina bai da tsirfan cewa ga abin da zai ci duk abin da na kwaɓa na bashi yana maraba. A baya kafin na samu Saude na wahala sai dai in Marwa ta zo mini hutu. Marwa babbar ɗiyar Yaya Aina ce. Lokacin da ta ke gida kafin ta samu makarantar koyin aikin jinya a garin tsafe na more ta saboda yarinyar tana matuƙar sona. Shi ya sa nima na ke son ta ina kuma kyautata mata. Ba ta zuwa gidan kowa hutu sai gidana in ta zo ba na komai sai dai na ci na kwanta Yallaɓai ya yi ta mini tsiyan daman haka na ke so na kwanta na yi ta laushi ni kuma na ce na ji ba komai. Marwa ba ta da ƙiyuwa. In ta zo har wankin kayana da guguna tana yi min kayan su Jidda sai dai na fito na ga ta wanke ta shanya, budurwa ce mai kimanin shekaru 20 zuwa da ɗaya. Duk da ni da uwarta ba sosai muke yi ba amman kuma Allah ya haɗa jinina da Marwa kuma ina daraja haka saboda yaran Yaya Murja ba sa zuwa gida na amman gidan Ma'u kam suna zuwa mata hutu. Har gwarama Firdausi ta wajen Yaya Balki ta kan zo wajena ban da su Anti. (Aina) sunan Yaya Aina a ka sanya mata sai ake kiran ta da Anti ita ce babba a ɗakin Yaya Murja ƙannenta huɗu duk maza ne. Ni bai dame ni ba domin kowa ya san halina ka yi da ni, ya ka ƙare ballantana ma ba ka yi da ni ma gabaɗaya. Allah na tuba gari da yawa ai maye ba ya ci kansa ba shi ya sa ina yi ma Marwa abin alheri har ɗinkuna ina yi mata lokacin da ta samu makaranta tsafe siyayya na yi mata mai yawa kuma har da ni a masu rakata, sannan in dai ta zo gida hutu ko da ba za ta daɗe ba sai ta zo gidana ba ta daɗe ba ta yi mini sati ɗaya. Sau tari in zan siya abin mata na kwalliya uku na kan siya saboda Marwa. Ita tunda ta fara amfani da su bra da pad in dai na fita kasuwa siyayya ina siya mata na ijiye in ta zo hutu ko ba ta zo gidana ba ina aika mata dashi na ce Yaya Aina ta iijiye mata. Ban taɓa jin na damu da ta gode mini ba koma me na yi nima ai uwar Marwa na ke, kuma abin da ke tsakanina da mahaifiyarta ba zai taɓa shafanta ba. Ko kafin in gama gyara gidan har sun gama wankin duk da bai da wani yawa daga uniforms ɗin su sai kayan barcin su. Ko daman ita Saude akwai ƙokari a shekaru iyakarta 17 ko ta gota da kaɗan ne. Na ɗan taya su shanya wajen sharce kayan. Bayan mun gama na ce Saude ta yi ma Baby tsifa ita ma Jidda ta kwance kan ta in wanke musu. Tun da ba su samu zuwa kitso ba sai in yi musu da kaina. In kana da ƴa'ƴa mata koyon kitso ba zai zama wani abu mai wahala ba. Kuma daman ina da  mai kitson  tun ta can anguwan dakata da muka ta so bayan mun dawo nan tana zuwa gida ta yi mana ina biyanta ranar da kuma ba ta samu zuwa ba na kan kira Salisu ne ya zo ya ɗauki su Jidda ya kai su. wani lokacin in ta gama yi musu kitson yarta ke dawomin da su ranar da ba su samu zuwa ba na yi musu da kaina tun ban ƙware ba har ba ƙware kaɗan kaɗan.   Da na so sai la'asar zan je gida amman sai Amina ta sake kirana tana faɗa mini duk yau Yaya Hamza da Yaya Auwal za su koma sai na yi tunanin na tafi bayan azahar. Yallaɓai bai tashi ba sai da na gaji har wajen sha ɗaya saura bayan na wanke tiolet na jiƙo hannuna na zo na tura masa a cikin ƙirjinsa da sauri ya buɗe ido sai a cikin idanuwana. Ɗan ɓata rai ya yi irin na masu barci ni kuma sai na yi masa mirmishi. "Yallaɓai a tashi haka nan. Kalli fa rana ta yi." Na faɗa ina buɗe masa labulen window ɗin bedroom din. Ai sai ya kauda kai har ya na juyawa zai cigaba da kwanciya. "Yallabai. Haba mana" Na faɗa cikin yar shagwaɓa amman sai ƙara shigewa da kansa ya yi cikin bargo lokaci ɗaya cikin shaƙewar murya cike da barci ya ce. "Sai azahar za ki tashe ni. Kin ji". Ya faɗa ya wani ƙara sakin numfashi sai na saki baki kawai ina kallon shi na buɗe baki in yi mgana wayata dake kan dressing mirro ta ɗau kiɗa alamun kira sai na bar wajensa na isa wajen wayar. "FaridaAisha." Faridan Tariq ce. Haka na faɗa a fili kafin na juya ina kallon Yallaɓai lokaci ɗaya ina faɗin" Ka gani ko? Ƙila ma Tariq ke neman ka ka kama ka kashe waya kamar wanda ya kwana aikin gajiya." Na san ya na jina amman bai yi motsi ba sai ni ce na taka zuwa gefen gado na zauna sannan na ɗaga kiran "Maman biyu." Daga can bangaren ta ce"Matar injiniya." Da fara'a muka gaisa sai ta ke ga ya min sun shigo garin ita da Tariq suna Gwammaja suna son ƙarisowa gidanmu amma an kira wayar Yallaɓan nawa a kashe Da sauri na ce"Yau hutu ya ke ji tun da ya dawo sallar asuba ya kashe wayarsa. Amman ai yanzu yana jin mu. Za ku samu ƙariwan kuwa? "E. Amman a tsaye gaskiya saboda daga nan sai kaduna in sha Allahu " Ina buɗe baki kamar ta na ganina na ce"Kai. Yau kuma! Ba ku bari zuwa gobe? Tana yar dariya ta ce"Mai gayya ne ya ce yau za mu tafi" Ina dariya na ce"kuma an gama mgana ba." Sallama muka yi ta ce suna tafe. Muna gama wayar na juya ina kallon Yallaɓai amman bai tashi ba sai na miƙe ina faɗin" Yallaɓai ga su Tariq nan da iyalansa don Allah ka tashi ka yi wanka ka ƙarya kafin su kariso" Dakyar da soɗin goshi na samu Yallaɓai ya tashi. Hararan shi na yi lokacin da na ga ya miƙe ya na miƙa. "Gajiyar duk ta mene ne? Sai da ya sargafo hannayensa ta saman wuyana muna kallon juna kafin ya ce"  To kuma me ye na tambaya? Duk tsawon gajiyar da kika tara min ne na wannan watan na ke safkewa" Ya ƙarishe yana ɗage mini gira. Ture hannun shi na yi daga kafaɗata na wuce ina faɗin" Ni ban ce ka tara min gajiya ba sai kai? "To ke wani ƙokari kike yi ban da abin ki. Ni ke fa aikin." Ya faɗa yana biyo bayana. Juyawa na yi muka haɗa ido kafin na yi masa wani kallo sai kawai ya fara dariya ni kuma sai na rausayar da kai lokaci ɗaya ina faɗin" "Au! Haka ka ce ko? Na nuna shi da yatsa kafin na cigaba da faɗin" Kai nan har wani ƙokari gare ka? Ba domin ni ba Yallaɓai uhmm." Na faɗa ina cije baki. Yana dariya ya ce" Sadiya ki ji tsoron Allah." Na juya zan fita ina faɗin" Za mu haɗu ne anjuma zamu ga mai ƙokari da mara ƙokari " Ta baya ya rumgumeni yana faɗin" Just a good morning Hug." Dakyar na tura shi Tiolet ya yi wanka kafin ya fito na soya masa yar sauran doyan da ta rage sannan na dafa masa ruwan tea mai haɗin kayan shayi. Ƙananun kaya ya saka tunda yau ya na gida a saman dining na zauna har sai da ya gama karyawa. "Yallaɓai daga yau in dafa sauran shinkafar nan komai namu ya ƙare na kayan abinci." Na faɗa ina kokarin tattara kayan da ya yi amfani da shi. "Kafin Anjuma ɗin Allah zai kawo mafita. In sha Allahu." "Allah ya sa." Haka na amsa ina mai fita daga falon zuwa kitchen. Na leka su Saude na ga Baby tana hawaye ana mata tsifa daman ita akwai zafin kai ita dai Jidda har ta tsife nata. Ina dariya na ce"Baby ki bari a yi tsifa an juma Babanki ya ce zai si yo miki ice cream kin ji? Jin haka yasa ta washe baki. Sai na ce to a daina kuka in ta na son shan Ice cream. Fita na yi daga ɗakin na rufo musu kofa duk da na yi wanka ina bukatar na ƙara tun da tun safe ne. Ina wanka su Farida suka iso domin na ji lokacin da Yallaɓai ya fita ya buɗe musu get Tariq ya shigo da motarsa shi ya sa a gurguje na gama wanka na fito na shirya na saka riga da sikat na wani material sai ga Yallaɓai ya shigo. "Ke sun fa ce suna kan hanya ne." "Ga ni nan zuwa Sorry." Sai ya juya ya fita ya na faɗn" Ki taho musu da ruwa." Sai na amsa da to. Mayafi na saka na rufe jikina sannan na biya ta kitchen na ɗauko musu ruwan gora a fridge da kofuna guda biyu bayan na saka a faranti. Ina shiga falon Farida ta zo ta tarbeni. Falon ya yi albarka Baby  ta ga yan biyu  sai wasa suke yi, ƙila babansu ya kira su su gaida baban na su, Jidda ba ta falon tabbacin ta koma ciki. "Sannun ku da zuwa." Na faɗa ina sauke ruwan saman center table ɗin da ke gaban Yallaɓai da Tariq. "Yauwa Sadiyar Yallaɓai. Ai ina nan ina masa tsiyan yau ko ba ya so mu ganki ne ya ɓoye ki? Ina dariya na zauna a kujeran kusa da Farida. "Haba dai ko ɗaya. Ina wanka ne lokacin da kuka shigo." Tariq ya jinjina kai kafin ya ce" yan hutu. Shi ma ai yanzu ya ke faɗa mini bai daɗe da tashi barci ba." "Shi ne ɗan hutu. Amman ni tun asuba ban koma ba." Farida na hararan mijinta ta ce" Shima ɗin ya na fin haka ma yana barci." Yallaɓai ya ce" to daman mana. Ni da suka raina ne suka saka mini ido shi da kawunsa Abba." Tariq na dariya ya ce" Tafida yarinyar  nan fa ta kirani. Ni dai kawun ka ya kusa kashe min aure. Madam fa ta ƙi yarda da rantsuwata shi ya sa na matsa mu zo ga ka ga Sadiya ƙila tafi yarda da mganar ku." Ina dariya Yallaɓai na dariya Farida ce ta haɗe rai kafin ta ce" To na sani ko sabuwar budurwa ya yi. Kira kan kira" Ina dariya ne amman ina auna wawancin Shema'u kina mace ki zama mai arha haka! Amman tuna wacece ita sai ban yi mamaki ba. "Maman biyu kar ki yarda. Tabbas ni ma kwanaki nan ban gane masa ba duk yadda aka yi ya fara neman aure a boye." Yallaɓai ya faɗa ya na haɗe ai sai Tariq ya kasa magana amman ya buɗe baki. "Uhm. To Allah ya ba shi sa'a." Farida ta faɗa kai tsaye ganin ta ɗan shaka sai na karɓi mganar ina faɗin" ƙyale Yallabai.' Nan na faɗa mata abin da ya faru a jiya duk da ta na nuna ba ta damu ni na san ta damu. "Ku kam ba abokan rufin asiri ba ne. Daga kai har tazurin kawun ka." Tariq ya faɗa yana ture hannun Yusuf dake saman kafaɗansa. Farida na dariya tana bamu labarin sun je gaida innayi sun haɗu da Uncle Abba shima dai tuburewa ya yi da bai san zencen ba shima Yusuf ga abin da ya ce. "Ai gaskiya ne. Mu ba mu san yadda aka haihu a ragaya  ba." Yallaɓai ya faɗa yana dariya sai Tariq ya miƙe ya na fadin" Madam lokacin mu ya ƙare anan fa." Itama sai ta miƙe tana rataya jakarta. Dukkanmu sai muka miƙe gabaɗaya ina faɗin daga zuwa sai tafiya. "To ai zuwan daman na a gaisa ne. Muna nan muna jiran ku ke da Yallaban na ki dai." "In sha Allahu." Na faɗa, muka bi su har waje ina yi ma yan biyu wasa. Kamar na sani na sako yar dubu ɗaya daga ɗaki shi na bama yaran ganin Farida ta zo ma da su Jidda bickit mai yawa. Sun shiga mota ina bangaren Farida ina yi mata sallama. Yallaɓai kuma suna bakin motar shi da Tariq suna mgana. "Man sai yaushe kenan? Tariq ya buɗe mota ya shiga lokaci ɗaya ya na faɗin" Ai ni ƙila sai ranar da tuzurin kawun ka ya samu matar aure in za mu je tambaya sai na shigo." Dariya suka yi har suna tafawa. Ni ko sai na ce" Kawun ku ke ma haka? To ai ba ku za ku yi masa tambaya ba." Tariq na dariyan mugunta ya ce" har auran ma za mu karɓa masa. Gaya min su wa za su je? To iyayen duk sun tsufa sun kare mu ɗin dai mune rufin asirin sa. Tafida ka bar gemun ka ya taru nima haka saboda na ga kamar kawun na ka ya fara maganar aure. Ko wani lokaci zai iya neman mu." Dariyan su suka sha suna tafawa nima ni da Farida muna ta ɗan dariya. "Sai mun yi waya. Allah ya kiyaye hanya." Yallaɓai ya faɗa bayan sun ƙara musabaha da Tariq. Shi ya bude musu get suka fita muna ɗaga musu hannu Allah ya sa baby ta samu biskit da ta yi rigiman sai ta je. Mun dawo cikin falo na kalli Yallabai ina faɗin" Duk abin da kuka faɗa akan Uncle Abba sai na faɗa masa." Yana ƴar dariya ya ce" To wai shi ne me? In ba ki da kati ki yi mini mgana sai na saka  miki." Kafaɗansa na kai ma duka ina dariya shima yana tayani. Mun zauna kan kujera ɗaya muna hira nan ne na ke gaya masa zan je Ɗorayi da wuri saboda yau su Yaya Auwal za su koma wajen aikin su. "Ok. Zan kai ki ne da kaina? "No. Ka bari dai sai ka je ka ɗauko ni" Sai ya gyaɗa mini kai sai na mike na wuce da farantin ruwan da na kawo ina faɗin. " Bari na je na wanke ma su jidda kan su." Da kai ya amsa min, sai na bar masa falon gabaɗaya. Kitchen na biya na sauke kayan hannuna sannan na shiga dakin su Jidda na ga sun gama tsifan har Saude ta ƙara share ɗaki. "Saude je ki wanke min sauran kofunan da suka ɓaci bari na wanke musu kai tare za mu tafi ɗorayi." "Umma ba kin ce za ki yi mana kitso ba? Jidda ta tambaya ne, sai na kalle ta kafin na ce" Sai na dawo ko zuwa dare ne." Mayafin jikina na cire na shiga tiolet ɗin akwai mayukan wanke kansu a ciki tunda daman rabi na kan raba na su da nawa. Kuma daman na iya ni nake yi ma kaina wankin kai ni da yayana a gida tunda ina da handrayer. Ruwa na tara mai ɗumi sannan na kira Baby na fara wanke mata sannan jidda a karshe, bayan na gama na fito na jona handrayer na busar musu da gashin gabaɗaya na shafa musu man kitso Jidda ita ta ƙara taje kanta ta daure da band ni kuma na yi ma Baby duk da ana yi ta na kuka har sai da Yallabai ya leƙo yana faɗin" To a kyaleta mana tun da an gama" Ina kallon shi kafin na ce" Za a dai gama amma ba a gama ba." Sai da na matse na samu na daure mata gashin. Yallaɓai ya ɗauke ta yana lallashinta lokaci ɗaya yana share mata hawaye, domin har da majina saboda kukan. "Ba ki son gashin ne? Yallaɓai ya faɗa duk cikin sigan lallashi sai ta gyaɗa masa kai, da sauri ya kalle ni kafin ya ce" Sadiya to a yi ma Baby aski ba ta son gashi balle ta rika kuka ko? Sai ya kalleta kawai sai ta fashe da kuka tana faɗin" Ba na son aski." Yallaɓai sai ya kalleni kafin ya ce" To a bar mata gashin ta shi ke nan? Ya sake kallonta sai ta gyaɗa masa kai, rumgumeta ya yi, ni kuma me zan yi in ba dariya ba. Jidda ma ta na ta dariya Yallabai ya sunkunci Baby ya fice ya na faɗin" Tunda kun yi faɗa da Umma sai a ji da Abba ko? Bin bayan su na yi bayan na ce jidda ta ƙara share ɗakin saboda gashi. Ganin har an kusa azahar sai na bi Saude kitchen na ce bari kawai na dora farar shinkafa ina da sauran miya sai a ci da shi kafin mu tafi. Ni da na so fita tun bayan azahar sai gani har karfe uku sai da muka ci abinci na sauya kaya sannan na bar ma Yallaɓai amanar gidana da yarana ina ta ƙara jadadda masa. Sai kawau ya ce" Na ji mai gida. Kina ta mini kashedi megadi ne ni? Ina dariya na ce" Kamar haka! Tun da ko a ina aka je gida na Sadi baby ne." Na ƙarishe faɗa ina masa fari sai kawai ya yi mirmishi kafin ya ce" Hausawa suna cutar mu. Kai da guminka sai ka ji ana gidan Sadiya." "Ko gidan Maman jidda ba." Na faɗa ina yi masa dariya. "To ba a cewa na Baban jidda." Yadda ya yi mganar ne yasa har ina riƙe ciki wajen dariya. Mun rabu sai mangariba zai zo ya dauke ni bayan ya sake duba Alhaji. A daidaita muka samu zuwa Ɗorayi a kofar gida muka yi sallama da Saude bayan na ce  ta gaida mamanta. **** Ɗorayi. Ko da na je gida cike da ƴaƴa da jikoki. Domin kaf su Yaya Murja da yaransu suka zo tun da yau lahadi ba makaranta. Na iske har Ma'u tare da Zainab da su Alhaji ƙarami. Rahila ce kawai ba ta zo ba wai ba ta jin daɗi Mutanen Abuja dai sun riga sun tafi saboda nisa. Sai Yaya Hamza ne shi ma lokacin da na zo suna sallama ne za su ɗau hanya. Amina kuma za ta bi su su rage mata hanya daga zariya sai ta hau motar kaduna. Da ta ce sai gobe megidanta zai zo su koma tare to shima sai daga baya ya kirata ya ce suna da taro a wajen aiki da wahala ya samu zuwa. Ya dai yi ma Alhajinmu sannu ta waya. Tunda mijin Amina lacara ne a jami'ar kaduna. Kallon ta na yi lokacin da muka samu keɓewa a ɗakin Mama ina faɗin" Ke yanzu da sai ki tafi ba mu yi sallama ba? Ta na yar dariya ta ce" Ai na san kina hanya." Gyara zama na yi kafin na ce" Tun da Datti ya koma ya zo gidanki weekend kuwa? "A'a ya ce suna ta test ne. Zai zauna a cikin makaranta ya yi karatu. Ƙila sai sun gama zai taho.' Sai na jinjina kaina. Saboda Datti a farkon shigarsa jami'ar a gidan Amina ya fara zama amman sai aka samu matsala tun da akwai wani ƙanin mijinta a gidan da suka yi ta samun matsala da Datti har lamarin na neman shafan auren Amina tunda kowa kanshi ya sani. Sai Yallaɓai ya ba da shawaran gwara ya samu hostel ya koma can da zama, Allah ya sa ma akwai wani abokin shi ɗan nan kanon ne shi ya bashi waje a ɗakinsa suka yi sukwatin. Sai dai ya na ɗan zuwa wani lokacin ya yi ma Aminar weekend. "Mubarak ɗin ma ba ya nan yanzu. " Ita ta katse min tunani Mubarak sunan kanin mijin na ta. "Me ya faru? Har ya gama karatun? "Ban sani ba. Amma ina kyautata zaton kamar ya samu matsala ne duk da yayan na shi baya son faɗa mini. na san ya na Aji uku ne sai ya tafi can zuntu sama da wata biyu bai dawo ba gashi ana ta karatu sai na yi zargin wataƙila ya samu matsala ne a can makarantar." Sai na gyaɗa kai kafin na ce" Za ta iya yuyuwa. Ke dai tunda ba a faɗa miki ba. To ba ruwan ki." Tana dariya ta ce" Haba. Kamar ba ki sanni ba' Aiko na san Amina miskila ce kafi mahaukaci ban haushi, mun ɗan yi hira sama sama kafin Khaleesat ta leƙo ta na fadin ta fito su wuce ni na riƙe mata karamin akwatin ta muka fito suna falon Alhajinmu muma sai muka shiga can. "Na gode ƙwarai. Allah ya kai ku lafiya." Alhajinmu ya faɗa ya na ɗan kishigiɗe a saman kujera. Ya na riƙe da Amna Tasleem na kusa dashi. Khaleesat ta duka a kusa da Mijinta ta na faɗin" Allah ya ƙara lafiya Alhaji sai mun ƙara dawowa." "Allah ya sa. Na gode Allah ya yi muku albarka gabaɗaya." Muka taya su amsawa da Amin mune rakiyar har waje bakin mota gabaɗayanmu ba mu iyayen ba, sannan ba yaran ba. Sai da suka ɗaga muna ɗaga musu hannu suna ɗaga mana. Har sai da motar su ta ɓace ma ganin mu sannan muka koma cikin gida. Aneesa ɗiyar Anty Balki ce ta tambayi su Jidda na ce suna gida, a ɗakin Mama muka yada zango gabaɗayan mu tun da an ce a bar Alhaji ya huta ɗakin Gwaggo kuma ta ce Baaba na ciki tana barci kar a dame ta.   A kusa da Yaya Aina na zauna ina faɗin" Wai su Marwa ba su samu hutu ba ne? Kai tsaye ta ce mini" Sun kusa fara jarabawa. In ta dawo za su fara pratical a asibiti to babanta ya ce ta dawo gida ta yi kawai." "E. Gaskiya ai yafi. Ni ko wai ba ta da waya ne kwanaki ina ta kiranta a kashe " "Ta lalace tana saka layinta a wayar wata ƙawarta ce." Sai na kaɗa kai kafin na ce" Haba shi ya sa ba na samunta. Ta dawo sai a gyara in ba ta yi sai a siya wata amman ba ta zauna ba waya ba." Yaya Balki ta yi karaf ta ce" Tun da tana da uwa Sadiya ba" Sai na fashe da dariya kafin na ce" Kwarai kuma matar Injiniya ba." Yaya Aina na dariya amman ba ta yi mgana ba. Yaya Murja na zaune waje ɗaya da Ma'u sai da suka jiyo suna kallon mu, sai na yi kamar ban gansu ba muka cigaba da hiranmu da su Yaya Aina. Muna nan zaune sai ga Zaituna ta shigo fakam fakam kamar an jeho ta. Yaya Balki ce ta yi mata mgana da cewa" Daga ina? Ɗazu mijin ki ya fita ya na cewa ba ki zo ba? Ruwa ta ce a bata sai da Aneesa ta kawo mata pure water biyu ta shanyen su tana maida numfashi. "Wallahi na ɗan je barka ne. Wata yayarmu ce ta haihu." Daga ji ƙarya take yi saboda sai wani faman kifta ido ta ke yi kamar wacce ta yi ma sarki karya. "Za ki ci abinci ne? In ji Yaya Murja ai da sauri ta ce" Wallahi kamar kin san ina jin yunwa. Can anguwa uku ne ba mu samu abin hawa ba sai da muka ci uban tafiya duk abincin da na ci ya gama zazzagewa." Su Ma'u na dariyanta ni ko ban yi dariya ba saboda ban ga abin dariya ba. Kallonta na ke yi kamar wata mahaukaciya ta hana kanta zaman lafiya saboda shegen shige shigenta ta kuma hana ɗan uwan mu ya huta. Firdausi a ka kira ta zubo mata jallop ɗin shinkafa da wake ta zauna ta na ci hannu baka hannu ƙwarya da Yaya Aina ta ce ta ci a hankali sai ta fake da cikin goyo tunda a lokacin ta na da goyon mai sunan Yaya Hamza. Ba ta lura da ni ba sai da ta ci ta koshi sannan ta ganni. "Sadiya daman kin zo? Yanayin maganarta sai ya yi kama da ta renin wayau. Amman ta juya ta na yi ma Ma'u magana. Sai na ji ya kamata na rama na nuna mata matsayinta, sai kawai na kalleta kafin na ce" To daman ina za ki ganni kin shigo kamar an koro ki" Na faɗa ina kallonta. A raina ina faɗin Yaya Abubakar ya haɗu da jarabawa na auran wannan matar, iyayenta talakawa ne ba su da komai Yaya Abubakar ne ke tallafe da su, yayanta namiji sai shaye shaye ƙannenta sai bin yan iskan anguwa amman ba ta duba haka ba ita ce yau cin bashi ita ce kafa adashe ta cinye ta sha shiga rigima Yaya Abubakar na fidda ta ina tsoron wata rana kar ta ɗauko abin da zai gagare shi ta saka a ɗaure shi. "E na shigo ban ko gani na shawo tafiya" Kai tsaye ina kallonta na ce" Wata tafiya? Ko dai yunwa domin daga ganin ki yunwar ce ke ɗawainiya dake daman." Yaya Balki na yar dariya ta  ce" Da alama kam." Ita kuma sai ta wayance da cewa" Ban tsaya a gida na yi abinci ba ne, kuma can ɗin na kaɗan na ci kuma ga tafiya cikina duk sai ya zazzage" "Ke kam Zaituna me zai hana ki tsayawa a gida ki yi abinci? Shi ya sa Yaya Abubakar da ya shigo ɗazu ya ce a zuba masa abinci ashe da yunwa kike barin shi." Yaya Balki ta faɗa tana kallon ta kafin ta samu zarafin mgana Yaya Aina ta karɓe da cewa" To ta ina ma mace na da miji da ƴaya  za ta fita ba ta yi girki ba? Ai ko fitar sassafe ce ka yi dai ko fara ba mai ne kafin ka fita." Ina gyara zama na ce" Ta saba ne. Ita fa Zaituna ba ta son komai ba sai shigen yawo da shige shige. Ko mu nan da kika ganmu sai mun yi abinci muke fitowa daga gidajenmu ballatana ke." Na faɗa ina kallonta sai tafara kame kamen wai ita ina ta ke zuwa karaf ko Yaya Murja ta ce" A a Zaituna. Kina da shigen yawo kullum ba ki iya zaman gidan ki. Na rasa gidan wa kike zuwa da ya fi gidan mijin ki? Har ta na rantsuwan wai ita ba in da ta ke zuwa ko da yaushe tana gida ba domin rashin lafiya Alhaji ai ta fi sati ba ta fita ba, Ma'u na dariya ta ce" Ko ana gobe rashin lafiya Alhaji kin biyo gidana kika ce daga anguwa kike hanya ta biyo da ke? Ko ba a yi haka ba? Ta faɗa tana kallonta ganin an ƙure ta sai ta wayance da cewa ta tuna sun je gaisuwa can ɓarayin su Ma'u shi ya sa ta biya ta gidanta. Ganin ta na neman sauya hirar ya sa na kalleta ina mai kiran sunanta. "Zaituna kenan. Ki daina ma karya kowa ya san halin ki nan kwanaki na ji an ce kin cinye kuɗin adashen mutane har da yan sanda suka dauko miki, to ni dai ba zan ce ki bari ba amman in kika ɗauko rigimarki ki riƙa tsayar da ita a kan ki ko akan dangin ki, ki bar ɗan uwana ya huta duk kin tsufar da shi kin saka shi a uku, kar ki kashe mini ɗan'uwa gwara ma ki daina abin da kike yi." Sai ta kasa mgana Yaya Balki ta ce gaskiya ne Yaya Abubakar duk ya fara tsufa saboda wahala da rashin kwanciyar hankali. Yaya Murja sai ta taɓe baki kafin ta ce" Ai Allah ya bashi wasu kudaɗen sai na ce ya kara aure ita kuma ta je can ta ƙarata, ka rasa abin da take siya da kuɗin da ta ke rigima komai dai dai gwargwado ya na yi miki zaituna me kika nema kika rasa? Ganin mun yi mata taron dangi ya sa ta fara kuka tana murza idanuwana. Yaya Balki ke faɗin" Me ye na kuka? Domin fa muna sonki ne ya sa muke gaya miki gaskiya da wasu dangin ne wallahi sai dai  ki ji wata maganar, to ki ɗauka mu muna sonki ne shi ya sa muke faɗa miki gaskiya domin ki gyara." Yaya Aina ta karɓe da faɗin" Kwarai da gaske in wasu dangin mijin ne ita kanta ta san ba za su ɗauka ba. Faɗan ke so kan ki muke yi miki ki gyara saboda ke ba yarinya ba ce kin san abu mai kyau da mara kyau, in kika bari ya yi zuciya ya ɗau wani mataki akan ki ba za mu saka baki ba to kafin akai ga haka ki sauya rayuwar nan da kike yi, ki zauna a gidanki ki fita daga shiga rigima tunda ba abin da mijin ki ya rage ki da shi' Kowa na ta tofa albarkacin bakin shi, Yaya Murja dai ta ƙare mganar da cewa" Ke ko koyi ba za ki yi da su khaleesat  da Laila ba? Dube su kowacce tsaf ita da ƴaƴanta, kuma suna rawan jiki akam mazajensu suna tattalin su amman ke ba wannan a gabanki sai shirme, to ki fara gyara kanki da gidanki in kuma ba haka wata rana za ki yi nadama."   Ma'u ta saka baki tana faɗin" Ki rika kwalliya Zaituna. Haba kamar ba mace ba, ba ki gyara balle ki gyara ƴayan ki? Namiji fa na son gyara kuma in kika gyara wallahi sai ya ji daɗi" Nima na yi mata nasihan ta daina zama kaca kaca ta zauna a gidan ta gyara kanta tana kuka tana mana godiya tare da alƙwarin ta daina muna mata fatan haka daga nan sai muka saki maganar muka shiga wata hira ana mganar Baba Sani zai tafi gobe su Yaya Hamza sun bar kuɗi a ba su Yaya Aina ta ce in muna da wani abu mu haɗa masa ko in akwai mai sabulai da omo mu kawo ni dai na ce ina da sabulai zan aiko da safe Ma'u ta ce za ta ga abin da za ta aiko, har da kaya ma Yaya Balki ta ce tunda wancan zuwan da suka yi Matar Baba Sani ta mata zencen kayan yara haka suna so. Yau dai zaman gwanin daɗi ba faɗa ba bakar magana kowa ya binne abin da ke ran shi, Yaya Aina ce ta kalli Ma'u lokaci ɗaya tana faɗin" Ke ko Ma'u dangin babanki na neman ki yanzu? Sai ta yi shuru kafin ta ce" E. Muna waya da wasu daga ciki can kwanaki ma wata wacce da mamanta da babana uwar su ɗaya uba ɗaya ta zo wajena har ta yi kwanaki. Ni dai na daɗe ban je ba amman Alhaji ya ce in ya samu lokaci za mu je mu gan su." Yaya Murja ta yi karaf ta ce" Ba dole su neme ta ba. Sun ji labarin ba ta wulakanta ba. Ta na da abin duniya." Yaya Balki ke faɗin" To daman ai sai an san kana da amfani ake nemnka. Lokacin da suka san su za su wahala da ita ai ba su damu ba. Sai yanzu da suka san za su more ta. Ba komai abin da ta ke dashi ta yi musu ba shike nan ba." Ni ko ina gefe na ce shiken nan kuwa. In kana da shi ka yi in baka dashi ne in baka yin ba matsala. Ita dai sai gyaɗa kai ta yi tana faɗin in sha Allahu. Sallar la'asar ya tashe mu a wajen, bayan mun idar da sallah na shiga ɗakin Gwaggo na gaida Baaba ta amsa kamar yadda ta saba amsa mini. Daga nan ɗakin Mama na yi shigewata ina duba wayata su Firdausi ne a tsakar gida suna shara wasu na wanke wanke su Yaya Murja na baro su ɗakin Gwaggo. Tun da su sun rigani zuwa karfe biyar Yaya Aina ta yi sallama ta wuce gida bayanta Yaya Balki tare suka fita da Zaituna ni ma sai na yi shirin tafiya har Ma'u na fadin ta ɗauka sai dare zan tafi, da haka na so amman sai na tuna zan yi ma su Jidda kitso ba zan zauna jiran Yallabai ba. "Tafiya zan yi. Na yi ma su jidda tsifa zan kama musu kai gobe makaranta." Yaya Murja na gefe ta ce" Da kin zo da su Firdausi ta yi musu." Sai na ce mata ban yi tunanin Firdausin za ta zo ba ne, ina shirin tafiya Munirra ta kirani a waya ta na tambayan muna asibitin ne ko gida? Sai na ce mata muna gida sai ta ce mini gata nan zuwa ita ta tsayar da ni na jirata har sai da ta zo na rakata falon Alhaji ta gaishe shi. "Matar ƙanin Yallabai ne Alhaji" "Allah ya yi mata albarka. Na gode.". Har da kankana ta kawo masa Gwaggo na ta godiya,  mun dawo ɗakin Mama sai ga su inna Mariya sun zo duba Alhaji ta ce Amina ce ta faɗa mata jiya shi ne ta ce bari ta zo ta duba shi, dalilin haka yasa na daɗe a gidan tun da sai bayan sun tafi tare ta ke da matan su Kawu Tasi'u, sannan ita Munnira ta ce min ba daɗewa za ta yi ba na fito rakata har bakin gida bayan ta yi sallama da su Gwaggo ta ke ce min. "Ke na taɓa ki da alheri matar Yallaɓai. Kin ji Yaya Usman zai kara aure? Ban samu zarafin mgana ba ta cigaba da faɗin" To yanzu ma mganar da ake yi Anty Zabba na gidan su. " Cikin nuna mamakin na ce"Wai har yanzu ba ta koma ba? Munnira ta ce" Ina fa ta koma, a bakin Nasir na ji wannan satin mai shiga Yaya Usman ɗin zai zo, na so kiran Anty Zabba sai na fasa kar ta ce ina da son jin gulma" Ina mata dariya na ce" Wallahi haka za ta ce." Munnira ta kama haɓa kafin ta ce" Shi ya sa ban kira ba. " Na ce gwara hakan itama Munira ta na faɗin ba ta ji daɗi ba, koma mene da ta yi hakura ta zauna tunda matar na shi ba akanta za ta zauna ba. "Uhm ke dai Munira Allah dai ya kyauta ya dai dai ta su." Ta amsa min da Amin Amin daga nan muka yi sallama na koma cikin gida sai na ga Aneesa da wayata wai ana ta kirana ina dubawa sai na ga Yallaɓai ne da sauri na ɗaga kiran. "Yallaɓai ka taho ne? Cikin wani irin murya ya ce min" Sadiya ta congratulation." Ina yar dariya na ce" Yallaɓai ka biya mini makka ne? Shima dariyan ya yi kafin ya ce" In sha Allahu ina saka ran haka, amman dai yanzu ina so na faɗa miki ne an biya ni half payment na aikin nan namu na Rano." Cikin murna na ce" Don Allah fa Yallaɓai" "Allah Sadiya ta. Yanzu kuɗin suka shigo sun kuma kirani sun faɗa mini." Ɗakin Mama na faɗa ina faɗin" Alhamdulillah mun yi kuɗi" Ya na yar dariya ya ce" In an yi mangariba zan fito sai na zo mu dawo tare" Da haka muka yi sallama, muna gama wayar na yi hamdala ina jin daɗi Allah ma ji roƙon bayin shi. Na ƙosa mangariba ta yi ma saboda murna, ina idar da sallar mangariba na shirya lokacin har Yaya Murja ta tara yayanta sun tafi gida ni da Ma'u kawai ne a gidan ita kuma tana tare da Baaba. Yallaɓai sai bayan isha'i ya zo, ya ƙara duba Alhaji sannan na yi musu sallama  muka tafi gida. Muna hanya ya kalle ni kafin ya ce" Yanzu da me zamu fara Hajiya ta? Ina dariya na ce" Mu je gida mana Alhajina." Sai muka kalli juna kafin mu kwashe da dariya, ni ko har ina dukan kafaɗansa kafin na ce" Ranka ya daɗe  mai girma Tafida." Shi dai ya na ta dariya ni kuma ina masa kirari "Angon Sadiya Ɗan gatan Nene, uban Jidda da Maimuna. Allah ya ƙara ja zamanin Tafida mai girma Injiniyan gine gine, mai muƙamin zane zane takawar ka lafiya" Ya na dariya ya ce" Me kike so Sadiya? Ina masa dariya na ce" Me kuwa na ke so? Yallaɓaina kaɗai na ke so." Gira ya ɗaga min kafin ya ce" Kin yi kyakyawan zaɓi kuwa." Muna tafe muna hira, har muka isa gida. Baby har ta yi barci, dole na tashe ta tana kuka tana komai na yi mata kitso, Yallaɓai na ta faɗan wai ban iya kitso ba ne na saka yarinya tana kuka. Baki sake na kalle shi kafin na ce" Au ban iya ba ko? Ya na kallona ya ce" To ni dai ban san lokacin da kika koyi kitso ki ka iya ba" Sai kawai na yi banza da shi Jidda dai lafiyan lau muka yi kitson mu, sai bayan na gama mu su ne na ce su yi shirin kwanciya Baby daman Babanta ya lallasheta har ta yi barci. Wanka na sake yi na yi shirin kwanciya Tea na haɗa mana muka sha sannan muka zauna kassafa kuɗi, abu na farko kayan abinci na yi masa mgana sai kuma na ce ya ijiye kuɗin makaranta yara tun da sun kusa fara jarabaawa. "A'a ki bari sai zuwa lokacin ai da sauran lokaci." Kamar zan yi mgana sai kuma na fasa saboda na san wataƙila zuwa lokacin ya zo babu, mun yi mgana ya cire wasu kuɗi saboda Gidan bulo da office sai na yi masa mganar Halima ta haihu ba a yi mata komai ba sai ya ce zai turamin 20k ya ce a siyi abin da ya kamata ina so na ce ya rage min ko kaɗan a cikin kuɗina amman ban yi ba kamar ya san me na ke tunani sai ya ce "Zan ba ki 50k ki rike a hannunki. Kuɗin ki kuma in gwammati ta biya mu sai na baki duka in sha Allahu." Ina yar shagwaɓa na ce" Yallaɓai buɗe saloon ɗin fa? Da sauri ya ce" Wannan ni na ce zan buɗe miki, kuɗin ki kuma haƙƙn ki ne zan biya ki in sha Allahu." Sai ya ga na yi shuru sai ya shafa kumatuna kafin ya ce" Kar ki damu. In sha Allahu duk za a yi." Sai na gyaɗa masa kaina. Mun cigaba da lissafi ya ce 30k na kayan maggi da kayan tea, sai na ce ai ya haɗa gabaɗaya cikin na kayan abinci tunda tare muke siya a kasuwa a wani babban shago yana da lambar wayarsa list ɗin kawai zan rubuta ya tura masa da ƙudin har gida za a kawo mana kayan abinci. Har da sabule da omo, ni kuma sai ya ce zai ƙara mini 30k saboda siyayyarmu ni da yara su Unders da sauran kayan kwalliyan mata. Kuɗin asibiti kuma ya ce zai ware mini 50k saboda bamu san nawa za a nema ba sai dai goben in mun je mun gani. Sauran kuma ya ce zai yi amfani zai sallami sauran ma'aikata da shi ko da rabi rabi ne, ni na san har da kyatttuka sai ya yi in dai Yallaɓai ya samu kudi kamar suna masa kwaiƙwayi ni na yi masa mganar Nene, daman in za mu yi siyayya kayan abinci har da ita da kayan tea sai sabulan wanka sai ya ce na rubuta list ɗin gabaɗaya sai ya tura babban shago za a kawo kayan zuwa gobe in sha Allahu. Sai na ce to a daran na rubuta abin da na manta na ce zuwa da safe zan tuna. Saboda zuwana asibiti tun asuba na tashi na yi ma yara shirin makaranta Yallaɓai jiya ya siyo indomie da kwai , sai buredi sai na soya musu buredin da tea ɗin suka tafi da shi makaranta, ni kuma muka shirya daman tun safe na tura ma Dr Fatima saƙo sai ta dawo min da amsar za ta ƙara kiran Dr Aisha ɗin amman na je asibitin na siya kati za a kai ni gynea unit ɗin in ce dai Dr. Aisha na zo gani a shigar mata da Fayel ɗina za ta duba ni in sha Allahu. Tare muka fita da su Jidda muka kai su makaranta daga nan muka wuce Aminu kano. Da taimakon Yallaɓai nan da nan muka siya kati har aka yi mana hanya zuwa Gyea Unit da taimako  irin masu zirga zirga rarraba katina Yallaɓai ya yi ma ihsani, ya faɗa mai mun zo ganin wata Dr Aisha bukar ne. Wajen ta zai kai mini Fayel ɗina sai ya ce ba matsala ba ta ƙariso ba amman tana hanya. Sai wajen tara da wani abu likitocin suka fara zuwa. Muna zaune da Yallaɓai bangaren yan jira aka shigar da Fayel ɗin mu, Saboda ihsanin da Yallaɓai ya yi mishi sai ya shiga ciki ya yi ma Dr Aishan bayani sai ta ce eh ta na sane fayel ɗina daman a sama ya saka min ni ce ta farkon da aka fara kira na shiga ganin Dr Aisha Bukar kamar yadda ke rubuce jikin Office ɗinta. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. Eaman ScholarSphere. Where ideas Take Shape. WHAT WE DO. ASSIGNMENT PRESENTATIONS. ARTICLES PROJECTS. BOOK AND MANY MORE. CANTACT US THROUGH. 02347067793152 MOTTO: "Pathways of Knowlodge Academy, Nurturing minds, illuminating Futures" *🅿️15* Aminu kano Teaching Hospital. Gynecologist Unit. Ina zaune a kan kujeran da ke fuskarta wajen zaman likita. Idanuwana kir a kan Dr Aisha Bukar ina ƙare mata kallo. Ta fi Dr Fatima shekaru ita babbar mace ce gaskiya a kallah in ba ta haura 40 ba za ta tsaya a hakan ta na da kaurin jiki, ga tsawo ga kiba sannan ba ta da wani haske sosai. Tana zaune tana duba fayel ɗin gabanta gefe ɗaya kuma hankalinta na kan system ɗin dake gabanta da alama dai akwai abin da ta ke dubawa a ciki. Fuskarta da gilashi siriri sannan sanye take da rigan likitoci kanta kuma ta sanya ƙaramin breziya Hijab fari. "Sadiya Sulaiman Yashe" "Maa." Ba ta kalle ni ba hankalinta na kan system ɗin gabanta ta ce" Ke ce wacce Dr Fatima ta yi transfer ɗin ki daga ABU KO? Sai na gyaɗa mata kai lokaci ɗaya da cewa" Yes"  Saboda da turanci ta yi maganar. Tsayin mintina goma sannan ta ce" Ga Report ɗin ki da ta tura mini  ina kan dubawa." Da hausa ta yi mganar wannan karon kafin ta dawo da hankalinta kaina. "Sunana Dr Aisha Bukar. Zan cigaba da jagorantar matsalarki har zuwa lokacin da za ki samu waraka in sha Allahu." Ba ta jira jin ta bakina ba kawai ta cigaba ta faɗin. " A yadda na ga ɗan brief na matslar ki, kafin mu je kan matakan da muke ɗauka ga masu irin laluran ki, kin san abin da ke damun ki? Ko dalilin da ya sa ba ki sake haihuwa ba? Na ɗaga mata kai zan yi mgana kawai cikin zaƙin muryanta ta ce. "SECONDARY INFERTILITY"   Kai tsaye kuma ta cigaba da bayanin ta. "Kuma shi  Secondary infertility ( rashin samun ciki bayan mace ta haihu ko hayayyafa) yana faruwa ne lokacin da mace ta haihu sai kuma haihuwa ta zo ta ɗauke kwata kwata ayi ta nemanta ruwa a jallo amma bata samuwa wani lokacin har sai an dangana da asibiti. Mace a haihuwar farko ta san lafiyarta lau saboda ta samu ciki ba tare da neman taimakon likita ko shan magani ba, amma kuma daga nan sai haihuwar tayi ɓatan dabo." Nan ma sai ta ɗan dakata kafin ta cigaba da faɗin. "Yawancin abubuwan da ke haifar da secondary infertility sun haɗa da low egg quality(wato kwan haihuwar mace ya kasance baida karfin haihuwar) matsalar mahaifa, matsalar rashin karfin maniyyi, yanayin abinci da wasu abubuwan wanda suka danganci rayuwar mace kama daga yanayin cututtuka da uwa uba Family Planning" Ta ɗan ɗago ta kalleni ganin ina kallonta sannan hankalina na kanta ya sa ta ɗan gyara zama gilashin ta sannan ta sake cigaba da faɗin.   "Babban abunda ke kawo secondary infertility musamman a kasar hausa shine family planning wato tsarin iyali. Yawancin mata idan sunyi tsarin iyali yana haifar masu da matsaloli wanda cikin matsalolin nan babbansu shine sanadin family planning. Family planning na haifar da jinkirin rashin samu ciki da wuri saboda karfinshi da kuma aikin da yake a productive system na mace Kama daga hormones har zuwa Reproductive organs "Kuma kowani abu ya na da Siide effect, kuma shi planning yana ninka adadin shekarunsa sau ɗaya ma'ana zai iya haurawa da kashi ɗaya, wani lokacin har biyu, kamar ke ɗin nan kin yi na shekaru biyar amman ya haura ki har shekara tara ba ki haihu ba, sannan kafin ki samu ciki side effect ya taɓa ki kin ta samun matsaloli ko? Ba ta damu da na amsa ba ta cigaba da faɗin. "Secondary infertility kuma mace ta taɓa haihuwa sai ta zo ta hanyar planning ko kuma haihuwar ta tsaya mata chak, shine za ta je asibiti ayi aune aune sai a bata maganin da zai dakile karfin planning din nan da kuma wanda zai taimaka mata wajen buɗe mahaifar ta da hormones ɗin don a samu cikin, kamar irin problem ɗin ki kin gane? Sai na gyaɗa mata kaina alamun gamsuwa. Tana mgana da hausa ta na haɗawa da turanci a maganarta kawai na fahimci ita ɗin kanuri ce saboda ba ta da hausa sosai. Fayel ɗina ta jawo ta fara rubutu kafin ta ce" Kafin mu kai ga ɗora ki kan mgani Akwai bukatar sai kin yi wasu gwaje gwaje kamar yadda tsarin mu ya ke." Mintina sama da biyu sannan ta sake ɗagowa tana kallona kafin ta ce" "Muna da gwaje gwaje a kallah guda tara waɗanda sai kin yi su gabaɗaya ne za mu iya gano ta in da matsalar ki take, da kuma hanyar da zamu ɗora ki kan mgani." Gwaje Gwajen da ake sun haɗa da 1.A semen analysis (mace da namiji zasu tara, sai a tara sterile container a debi sperm din daidai lokaci  da namiji ke kawowa, da gaggawa ake yin awon sbd kada sperm cells din su mutu kafin ayi awon wanda hakan zai iya lalata sakamakon da ake bukata a wannan awon ne ake gane cewa sperm din namiji na active zai iya haihuwa ko aa. 2.Blood tests to look at hormone levels (zai nuna level din hormones, suna over secreting ne ko under secreting) 3.A transvaginal ultrasound  4.A hysterosalpingogram, a type of X-ray that allows your provider to see your uterus and fallopian tubes( wannan da x-ray machine ake yin shi,zai nuna cikin mahaifa da kyallemun mahaifa duka honestly speaking its painful) 5.Blood tests. Samples of your blood can be tested for a hormone called progesterone to check whether you're ovulating. ... 6.Chlamydia test. Chlamydia is an STI that can affect fertility 7.Pap smears 8.FSH follicle Stimulatiing Hormone 9.LH Luteinizing Hormones All these are the most common primary and secondary fertility tests for women." Ta na gama yi min bayanan ta miƙo mini takardan mai tambarin sunan asibitin a jiki, hannuna biyu na saka na karɓa ita kuma sai ta maida hankalinta a wajen system ɗin gabanta. "Ki je lab ki kai musu, za su yi miki cikakken bayanin a can" A sanyaye na ce" Yanzu Dr? "Yes. Ki je yanzu a can za su ƙara miki ƙarin bayani da yadda za a yi." Sai na miƙe ina mata godiya. "Sai an baki result sai ki dawo mun da shi , on Monday ranar da zai ma ranar clinic ɗin ki." Na yi mata godiya sai kawai ta gyaɗa kanta. Ina fita na nufi Yallaɓai ya na ganina ya taso, sai na bashi takardan ina faɗa masa yadda muka yi da ita sai ya ce mu je lab ɗin. Tare muka je lap ɗin amman shi bai shiga ba ni ce na shiga na ba su takardan, laboratory ɗin da ya karɓa ya duba takardan sai ya ce. "Muna bukatar ki zo da mijin ki " Haka ya ce mini wani ɗan baki ne, kai tsaye na ce" Tare mu ke yana waje." Sai ya ce na je na shigo da shi, bayan mun dawo tare sun bamu wajen zama, sai wani lap tecnicial ɗin ya fara mana bayanin gwajin da za mu fara yi a matakin farko wato Semi analysis na sperm ɗina da na Yallaɓai." "Ya za mu iya kawo muku samples ɗin? Yallaɓai ya tambaya sai ya kora mana jawabi a tsanake, yanzu dai ya ce za mu fara yin bucking ko gobe ko jibi za mu iya kawowa amman mu kawo shi cikin gaggawa.  Kafin mu tafi sai da ya bamu sterile container  ya ce mu yi amfani da shi, kafin mu baro asibitin har kuɗin test ɗin sai da muka biya suka samu takardan da cewar sai jibi in sha Allahu za mu kawo ya yi ta jadaddamana da kar mu ɓata lokaci ana son a yi awon da gaggawa ne. Mun fito daga asibitin muna hanya sai kawai na yi tunanin bari na tsaya a kasuwa na ƴan siyayya ta daga nan na tsaya in yi saloon kafin na koma gida. Nan take Yallaɓai ya tura mini 50k kuma ya ijiye ni a kasuwar Wambai. "Yanzu sai ina? Na faɗa ina ƙoƙarin buɗe motar na sauka bayan mun iso shagon da na ke zuwa gyaran kai kusa da kasuwar Wambai. "Office zan fara zuwa akwai mutanen da zan gani." Sai da na fita sannan na leƙa ta window motar ina faɗin" Ka tura list ɗin ga babban shago saboda su kawo mana da wuri" Sai ya gyaɗa min kai kafin ya ce" Kin tabbata ba abin da za a buƙata daga baya? Jin abin da ya ce ne ya sa sai na buɗe motar na sake shiga na karɓi wayarsa na dubo list ɗin da na tura masa. Kallonsa na yi kafin na ce" Ina jin su kenan. Amman za ka iya ce ko zai duba wancan list ɗin? "In ya na da shi ba" Ina ƴar dariya na ce" Ya na da shi mana. Ai suna ijiye rocord saboda babban shago ne." Sai ya jinjina min kai kafin ya ce" ƙarfe nawa za ki koma gida? Ina gyara zaman mayafin jikina zuwa saman kaina na ce" Da na gama siyayya zan koma gida in sha Allahu" Hannuna ya riƙe ya sumbata kafin ya ce" Take care. Ki koma gida da wuri." Ni kuma sai na sunkunya na sumbaci ƙuncinsa ina faɗin" Allah ya ba da sa'a." Daga nan muka yi sallama ya sauke ni ya wuce, shagon wata Amesty ne anan na ke zuwa gyaran kai tun da daɗewa.  Ina shiga ta na ganina ta tarɓeni saboda mun saba da juna har lambar  wayar juna gare mu. "Hajiya zuwa ba waya? Ina zama kan ɗaya daga cikin kujerun dake cikin shagon na ce" Ba da niyyar zuwa na fito ba. Daga asibiti na muke sai kawai na ce Yallaɓai ya sauke ni anan, daman ina ta wa ƙen zuwa." Yaran shagon na ta gaisheni, ina amsawa ita kuma sai ta je ta ɗauko min ruwa. Ba musulma ba ce amman in ka ganta sai ka rantse musulma ce hausa a bakinta kamar jakar Kano dressing ɗinta irin na hausawa ne. "Na gode." Na faɗa lokacin da ta ba ni ruwa na karɓa na sha kaɗan saboda ina jin kishi. Amesty na zaune gefe na tana faɗin" Ina su Jidda kwana biyu? Ina Baby mai kuka." Ina dariya na ce" Duk suna makaranta." Saboda ba ko yaushe na ke yi musu gyaran kan ba, amma na fi kawo su lokacin salla ko biki saboda ba ni da lokaci tsayawa na yi musu. "Me za mu yi? Wankin kai ko Saloon? Sai na zare mayafina na tuɓe ɗankwalina na zame ina nuna mata kaina. "Saloon ko? Kamar wata biyu kenan ban yi ba." Ta na dubawa sannan ta kalleni ta na faɗin" Gaskiya. Bari mu yi Saloon ɗin" Daman in dai na zo da kanta ta ke yi mini saɓanin sauran da yaran ta ke yi musu, ni kuma muna yi duk abin da na gani ina mata tambaya saboda ɓarayina ne, na iya wankin kai Saloon ɗin ma na iya, Amesty na dariya ta ce" Hajiya wannan shagon na Saloon sai yaushe za a buɗe shi? Nima ina mata dariyan na ce" Yallaɓai ya ce Soon in sha Allahu.". Sai ta ce Allah ya nuna mana. Na yi awa ɗaya da wani abu a shagon Amesty, kafin a gama min Saloon kaina ya yi kyau. Ba ni da kuɗi a hannuna sai na ce zan tura mata ta banki in na koma gida da haka muka yi sallama ta rako ni har waje. Daga nan na samu Adaidaita zuwa cikin kasuwar Wambai akwai shagon da na ke siyan su bra da pant da kananun gajerun wanduna na yara nan na fara tsayawa na siya ma su Jidda pant da vest sai sikat na yara da ƙananun wanduna sai na siya ma Jidda da Baby dogayen wanduna baƙaƙe saboda makaranta. Har da safuna na siya musu farare da baƙake, nima na siya ma kaina pant da bra sannan na siya ma Marwa, daga nan na wuce shagon Musa mai kayan costimetic na siya irin su shampoo sai sabulin da su Jidda ke wanka, sannan na siya Veet da kayan wankin tiolet sai Moneyfresh saboda Mopping, na yi siyayya sosai na amfanin gidana har man kitso na siya mana. Saboda siyayya shago biyu ne kawai shi ya sa ban wani daɗe ba na dauki drop ɗin Adaidaita zuwa gida a ƙofar gida na ga Saude ta na jirana. "Shi ne ba za ki kirani ba?! In ban dawo da wuri ba fa." Kanta na ƙasa ta ce" Na kira ki ba ki ɗauka ba. Yanzu na zo fa daman." Sai da ta ce ta kirani sannan na tuna wayata na can cikin jaka, key na saka na buɗe gidan Saude ta taya ni ɗaukan kayan zuwa cikin gida duk na ji na gaji, ga cikina kamar an yi yasa kamar ban karya ba kafin na fita sai da na haɗa tea na sake sha sannan na dawo dai dai. Sai da na natsu sannan na kira Farida na yi mata ban gajiya da yadda suka koma gida. Sannan sai na kira Amina ba ta ɗauka ba sai na kira Khaleesat itama na yi mata ya hanya. Lailan ma Yaya Auwal mun yi mgana da ita. Da rana tuwo na yi tun da shinkar tuwon kaɗai ya rage mana. Saude sai wajen uku na rana na bata kuɗin mota ta tafi gida, ni kaɗai a gidan jin an kira sallar la'asar sai na yi sallah sannan na kira Yallaɓai nan ya ke faɗa mini ya na Rano ya je duba aiki. Ni kuma daman na manta ne ban faɗa masa mganar a saka drinks ɗin yara na makaranta ba da kayan kamshin girki tun da shagon babba ne a can kasuwar Singer ba abin ba sa saidawa. "Ai na tura masa na ce kuma ya saka duk abin da ya kamata." Sai na ce ya dai sake kiran shi ya faɗa masa sai a manta wani abun sai ya ce to. Sai shidda saura su Jidda su ka dawo, na so na yi wanki gajiya ya sa sai na ce bari na bari zuwa gobe sai na yi wankin. Sai wajen tara na dare Yallaɓai ya dawo gidan yana tambaya ta ba a kawo kayan abinci ba? Na ce ba su kawo ba nan ta ke ya sake kiran shi manager ɗin sai ya ce a ba' a gama haɗa kayan ba ne sai zuwa da safe in sha Allahu. Da wuri muka kwanta su Jidda daman ko da Yallaɓai ya dawo sun kwanta. Ina kwance a saman ƙirjinsa sai na kira sunan shi. "Yallaɓai." "Uhm" "Ba ka ga Saloon ɗina ba ne" "Na gani mana"   Ya faɗa ya na ƴar dariya duk da ba na ganin fuskar shi amman ina jin sautin dariyan shi. Baki na tura kafin na ce" Shi ne ko ka ce ya yi kyau? Hannunsa ya kai ya zare mini hulan kaina ya na mai tura hannun shi a cikin gashin sannan ya kai hancinsa ya shinshina ya kuma sumbata da baki kafin ya ce" Kina da gajen hakuri. So na ke yi daman na baki kyakyawan tuƙwaici." Na ga ko kyakyawan tuƙwaici a daran nan sai da Yallaɓai ya saka ni jiƙa kai gabaɗaya kamshin Saloon ya bi ruwa ina tura baki na ce" Yallaɓai wannan tuƙwaicin naka ban yi maraba da shi ba." Yana min dariya ya ce" Saboda mene? Hararan shi kawai, na haye gado na shige cikin bargo ina tura baki, sai da ya tsane kanshi da danshin ruwa sannan ya hayo gadon ya na min dariya ni ko ko busar da kan ban samu na yi ba na dai tsane shi da towel. Har da asuba sai da ya ƙara jiƙa mini kai, lamarin yallaɓai ya ishe ni har sai da na tsare shi ina masa tambayoyi. "Yallaɓai ka faɗa mini gaskiya me kake sha ne a bayan ido na? Na faɗa ina mai tsare sa da ido. Muna dining ne bayan mun gama karyawa su jidda sun tafi makaranta. Wani kallo ya yi mini na bangane ba kafin ya ce" Kamar na me fa? Ina haɗe rai na ce" Ko ka siya manpower ne ka fara sha a ɓoye ban sani ba? Sai ya buɗe baki yana kallona kafin ya rufe ya na dariya. Ni ko ban yi dariya na tsare shi da ido ina faɗin" To Yallaɓai gwara na sani. Kana samu ɓarnan ruwa da yawa yanzu." Haɓa ya riƙe kafin ya ce" Fisabillahi Sadiya kamar ni na yi lalacewan da sai na sha wani abu za mu yi barnan ruwa? Kai na kaɗa kafin na ce" shi ne na ke tambaya." Miƙewa ya yi a kaina sai da ya yi mika sannan ya sunkuya dai dai kunnina na dama kafin ya ce." "Ke ba ki san muna girma  ba ne muna ƙara sanin daɗin abin da darajarsa ba" Kallonsa na yi sai ya dage mini gira kafin na samu zarafin mgana ya sumbaci wuyana da sauri na ture shi na miƙe ina hararanshi. "Miye haka? Saboda na ga ya na ƙokarin riƙo ni kuma yana min wani kallon ƙasa ƙasa. "Allah zan busar miki da gashin da kaina." Ya faɗa ya na ƙokarin jawo ni ai da sauri na warce na fara zagayen dining ɗin ina faɗin" Bar shi kawai na yafe. Ina da hannu" Shima sai ya fara bi na ya na faɗin" Kai Sadiya ta. Guduna kike yi yau kuma? Ya faɗa har yana marairaicewa. Na san halin shi cikin sauri na ce" E wallahi yau na guje ka." Dariya ya yi min ni ko na haɗe rai, haka muka dinga zagayen falon nan daga karshe na fice da gudu zuwa bedroom ɗin ina shiga kafin na rufe ƙofa ya cimmin karfi ba daya ba turani ya yi kan gado ya biyo bayana ya na faɗin" Duk wayon Amarya dai." Ina ture shi ko gizau sai ya fara min cakulkuli ina ta dariya kamar zan mutu ina faɗin" Yallaɓai cikina don Allah ka bari." Sai da ya ga numfashina na sama sannan ya kyaleni ya na faɗin" Gobe dai dole ki bari na yi shagalina tunda kin ga asibiti na bukatar samples." Ko mgana ban yi mishi ba ina maida numfashi shima sai ya yi rigingine ya na nishi, ina ganin haka na lallaba na haye kanshi na fara masa cakulkuli da ƙarfi tun yana daurewa har ya fara dariya yana hantsila kafa, karshenta dai muka yi biji biji da gadon fililluka duk a kasa in ya yi min cakulkuli nima na yi masa daga haraba ma za a iya jiyo dariyan mu. Har sai da muka gaji sannan muka koma muka kwanta muna hutawa. Karfe sha ɗaya Yallabai ya yi wanka ya fita ya ce zai je Gwammaja ne daga can zai ta fi office ya fita ba daɗewa Saude ta zo ita na bari da gyaran gida na kwaso under ɗin yallabai da nawa sai kayan barcin mu na fita can in da muke wanki na kafa kujera kayan ba su da yawa kuma ba su yi wani datti ba cikin lokaci na gama na shanya na saka abin matse shanya na kama dasu. Bayana sai da ya riƙe ina gamawa na yi wanka da ruwa mai zafi, sannan na gyara bedroom ɗin da muka yi kaca kaca dashi ni da Yallaɓai. Ina da sauran fulawa sai na tura Saude kasuwar ƴan kaba ta siyo min kayan miya har da kabeji, ƙuli kuma daman ina da sauran shi sai dai bai da yawa ne. Da ya ke ina son gurasa to ina yi da kaina lokaci bayan lokaci. Gurasa na yi mana. Ita kuma Saude ta niƙa min sauran kayan miyan a blander na saka su a cikin fridge bayan ta ci na saka mata guda uku a leda na ce ta tafi da shi gida. Da safen daman Yallaɓai ya yi mganar albashinta daman mu da kan mu mun kan je gidansu hannu da hannu mu ba ma mahaifiyarta haka tsarin ya ke,  sai na ce mata ƙila mu shigo zuwa dare. Su Jidda suna dawowa su ka ga gurasa na yi suna ta tsallen murna. Kayan abinci ko sai bayan mangariba suka kawo mana. Yallaɓai baya nan dole su suka kwaso su zuwa cikin gida. Ma sha Allah na furta a raina komai an kawo har da su maclean da kayan maggi, ni da Jidda muka gyara komai a muhallinsa na Nene kuma na cire mata nata kayan Tea ne sai sabulan wanka da na wanki sai katan ɗin taliya da maracroni sai coouscous, tun da ta na so, shi ma saboda ya saba siya mata duk wata ne a matsayinsa na Namiji amman abincin gidan gabaɗaya yana Wuyan Yaya Usman ne gaskiya duk da sauran duk suna yi, matan ma kowacce tana iya bakin ƙokarinta. Kayan tea ɗin ma gida uku ne Nene da Hajiya Iya sai Maman farko. Da Yallaɓai ya dawo sai na nuna masa ya kalleni kafin ya ce" Ba matsala dai ko? Sai na rumgumeshi ina faɗin" Ba matsala mun gode Yallaɓai Allah ya ƙara buɗi da wadata." Sai shima ya riƙe ni yana amswa da Amin Amin. Ni nasan na yi dacen miji, in dai Yallaɓai ya na dashi ba zan taɓa neman wani abu na rasa ba. A daran muka fita mu ka je Gwammaja mu ka kaima Nene nata ya ƙara mata da 20k tana ta saka albarka farko ma ta ce ba za ta amsa ba ni na ce ta karɓa. Sai ta saka hannu ta karɓa tana faɗin" Komai fa suna yi min Sadiya to kuɗin kuma na mene ne? Ina mirmishi na ce" ki rike a hannun ki Nene kina yin baki da ga Rano ko na sallamansu kya samu." "Haka ne. Na gode Allah ya yi albarka" Muka amsa da Amin Amin muna gidan sai ga Mimisco(Anty Zuwaira) ita da mijinta itama kayan abincin ta zo da shi da kayan tea, sai mganar zuwa ganin likita ga Nene, tunda nauyin asibitin na ta Mimisco ce ta ce a bar mata za ta iya. Mun gaisa  da ita kamar yadda muka saba ni dai ban taɓa samun matsala da ita ba. Tana da ilmi ta kuma san yadda za ta zauna da jama'a. Saboda zuwanta ya sa muka ɓata lokaci tunda Yallaɓai suna ta hira da mijinta. Sai wajen tara da rabi muka baro gidan bayan Yallaɓai duk ya shiga ɗakunan su Hajiya Iya ya ba su 10k kowacce suka karɓa suna godiya a hanya ne ma da za mu je Ɗorayi Yallabai ke faɗa, min Yaya Usman ya shigo garin  jiya amman bai kwana ba ya koma a ranar. "To. Ya zo biko ne? Hankalinsa na wajen tuƙi ya ce" Ban sani ba. Na san dai ba zai rasa zuwa gidan su ba." Sai na jinjina kai kafin na ce" Hmm. Allah ya kyauta.". Saboda ina so na yi magana ina tsoron  kar Yallaɓai ya taso min shi mai ɗan uwa. Mun fara zuwa gidanmu muka sake duba Alhaji 20k Yallaɓai ya ba ma Alhajinmu. Gwaggo kuma 10k suna ta saka albarka. A bakin Gwaggo na ji labarin yau da safe Baaba ta koma na ce Allah ya tsare. Daganan mun shiga gidan su Saude 50k Yallabai ya ba ma Balaraba daman a wata 30k kuɗin aikinta amman Yallaɓai na yi musu ihsani kuma kafim mu baro gidan sai da ya yi mganar ya na so ya saka Saude a makaranta bai da ce a barta haka ba karatun boko ba, ta gama firamari ba ta cigaba ba. Mahaifiyarta har da hawaye tana ta godiya zaman amana ne da maƙotaka ya haɗamu har na ga Saude na ce ta riƙa zuwa tana kama min aiki saboda na taimaka musu. Daga gidan su Saude gida muka dawo tun da daman mun yi sallama da su Gwaggo muna hanya Yallaɓai ya ce na tura mai acct number Datti zai saka masa wani abu ina ta masa godiya. "Tsakanin mu ba Godiya Sadiya ta." Haka ya faɗa ya na kallona ni kuma sai na yi masa mirnishi kafin na ce" Duk da haka dai zan gode maka. Yallaɓaina Allah ya sa a fi haka." Sai ya amsa min da Amin muna yi ma juna mirmishi. ***** Washegari da sasaafe, bayan Yallaɓai ya ja mun yi ta barnar ruwa ni dai ai nace dole zan kira mai kitso kafin Yallaɓai ya sa gashina ya sauke ƙasa saboda jiƙashi da na ke da ruwa. Sai bayan su Jidda sun tafi makaranta a gurguje muka yi abin da aka umarcemu mu kawo daga Lab. Saboda yadda ya jadaddamana cikin sauri muka yi wanka Yallaɓai ya kai ni asibitin na kai musu da sauri suka karɓa bayan na haɗa musu da takardan da suka ba ni shekaranjiya. Suna karɓa suka ce mu jira a waje za su ba mu result ɗin. Tare da Yallaɓai muka yi zaman jira ana ta kiran shi ma a office bai tafi ba sai da aka gama test ɗin suka kuma bamu result ɗin da cewa zan kaima likita ranar clinic ɗina. Daga nan Yallaɓai ya dawo da  ni gida ya ijiye shi kuma ya wuce office domin ya faɗa mini akwai kwangilan da ya samu na zanen wani kamfani da za a buɗe a kaduna ne. Na bishi da Allah ya ba da sa'a shi ya wuce ni kuma na buɗe gida na shiga. Ban san me result ɗin ya nuna ba tunda rubutun likitoci sai su sai na adata kafin ranar Monday. Ranar yini na yi gugan kayan under ɗin mu da na wanke mana na goge su tas na feshe da turare, na jera mana a cikin wardrope, ganin na samu natsuwa ya sa na ɗau wayata na kira Aisha lame na yi mata mganar ina son Body lotion, sau Face soap sai Fade cream sai showergel na wanka Sai ta ce mini za a kawo mini sai na ce kamar yadda muka saba zan tura mata kuɗin ta, Aisha Lame ba abin da ba ta saidawa na gyaran jikin mata. Kuma kayan ta suna da kyau da inganci su na ke amfani dashi shi ya sa kullum Yallaɓai sai ya ce ya na son taɓa fuskata saboda taushi da santsi sannan ba guraje, jikina kuma ya yi fresh ya yi taushi domin Showe gel ɗin ta ba baya ba yana bala'in gyara fata. Cantact Aisha lame. +234 703 666 2633 Tana aikawa da kayanta ko'ina a faɗin Nigeria Daga ita sai na kira Surayya Dee mai kayan gyara na BOJUWA ta dalilin Aisha lame na san Surayya. Kuma na yi amfani da kayanta na yaɓa da ingancinsu. Ni duk bayan wata uku na ke shan mganin sanyi sannan na ɗora da na gyara Ni macece da ta yarda da gyara shi ne har gobe ya sa na ke da matsayi a zuciyar Yallaɓai. Duk da har kayan marmari ba na wasa da su da duk abin da zai kawo mini Ni'ima amman kuma ban zauna ba ina gyaran jikina tare da can ainihin majalisar ɗinkin duniyan gabaɗaya. Maganin infection na ce ina so Surayya ta aiko minibda shi in na gama zan siya kazan uwargida tana ta dariya ta ce" Hajiyar Injiniya ba a dai gajiya da gyara." Nima ina dariyan na ce" Ba a gajiya Hajiya Surayya. Gyara shi ne mace da gyaran ya sa har gobe muke ƙyalli a idanuwan mazajen mu." Tana ta dariya mun rabu akan yau ɗin nan mai kawo mata kaya zai kawo mini tun da ya san gidana, tun da ba yau muke tare ba, sama da shekara ɗaya tun da na gwada kayanta na san ingancin su. Domin ke ma ki dace da ingantattun kayan gyara contact Surayya Halin yau on +234 803 277 3332. Kano Nigeria tana aikawa da kayanta ko'ina. Zuwa yamma sai ga saƙon Surayya Halin yau, a daran kuma na tura mata har kudin kazar da zan siya. Mayuka na bangaren Aisha lame kuma sai washegari da safe ta aiko mini dashi. Ranar jumma'a gidan Rahila muka yini  ni da su Jidda, Rahilar ba ta da lafiya zazzaɓi daga ita har Bbyn na ta sai dare Yallabai ya je ya dauko mu, mun sha hira mun yi tsiya mun yi daɗi ta ji sauƙi tun da har kitso sai da ta yi mini daman ta iya ta rufa mini asiri kafin Yallaɓai ya saka ruwa ya sauke mini gashi. mun rabu da Rahila ta roƙe ni ƙanwar mijin Ma'u za ta yi aure za ta biyo mini mu je tare kai tsaye na ce" In ta gayyace ni ba? In ba ta gayyace ni ba wallahi ba zan je gayyar soɗi ba." Rahila na dariya ta ce" Ki ji tsoron Allah Sadiya. Ke yanzu sai kin jira Ma'u ta gayyace ki." Ina hararanta na ce"Kwarai kuwa. Kawai tusa kai ba kwarjini in ta gaya min zan iya zuwa amman ba ta gaya mini ba sai dai na ce a sha biki lafiya." Washegarin asabar kamar ta san mun yi maaganar da Rahila sai ga shi ta tura mini katin biki sannan daga baya ta kirani. "Ina fatan za ki zo dai zo ko Sadiya? Sai na ce mata in sha Allahu tun da sati na sama ne. ****** Ranar Monday, na koma asibiti na ga Dr Aisha bayan na ba ta sakamakon ta duba cikin ikon Allah ta ce da ga ni har Yallaɓai sperm din mu suna active matsalan ba daga nan ba ne yanzu tun da an yi wannan an tabbatar da ba matsala za su yi focusing a kaina ne. Sai ta rubuta mini blood tests to look hormone levels. Na je na kai lap aka ɗibi jinina suka ce na dawo nan da kwana biyu domin karɓan result. Tun ina hanya na kira Yallabai na faɗa masa likita tace matakin farko ba matsala yanzu dai sauran gwaje gwajen akai na ne. "Alhamdulillah. Suma sauran in sha Allahu ba matsala." "In sha Allahu." Na amsa masa cike da yaƙinin hakan A satin Hauwa ta zo gida na ta yini ita da yara a bakin ta na ke jin Anty Zabba ta koma amman sai bayan Yaya Usman ya koma ni ko sai na ce" Ya fi mata. Amma ba ta gina gidanta ta bar ma wata shi saboda kishi ba." Sai dare Muttaƙa ya zo ya dauke su. Washegari gidan Halima na je na kai mata Atamfar da na da siya mata a Dija collection+234 903 661 7473 Domin kayanta ta na ba da su ne akan farashi sari mai sauƙi. Sai na siya rigar yaro ssi pampers da na je sai na ɗora mata 5k na ce nawa ne kuɗin kayan kuma daga Yallaɓai ne tana ta godiya a gabana ma ta kira shi tana yi masa godiya ya ce ba komai. Ina shirin tafiya sai ga Anty Bahijja wai sun zo nan kusa ne ganin gidan da ƙanwar mijin Ma'u za ta zauna shi ne ta biyo wajen Halima. Da gangan na yi ma Anty Bahijja taɗin bikin ina dariya na ce. "Anty Bahijja ashe biki gare ku ba gayyata." Sai ta kalleni kafin ta ce" Ba ni ya kamata na gayyace ki ba Ma'u ce." Ina mirmishi na ce" Ai fa ta gayyace mu muna nan zuwa." Na ga ta kalleni da mamaki amman sai ta shanye ta ce sai mun zo ni dai anan na barta na koma gida da wuri saboda yara. Ranar asabar da wuri na shirya daman na faɗa ma Yallabai tun kwanaki ya ce ya ba ni izini. Shi na bar ma yara a gida na ce in zai fita ya kai su Gwammaja wajen Nene, ni kuma Rahila ta kirani ta ce wai mu a haɗu a Ɗorayi ni kuma na ce ba zan koma baya ba tun da na san gida yayar mijin Ma'un ta taɓa rasuwa muka je gaisuwa na san iyayin Yaya Murja ce za ta ce a haɗu a gida a tafi gabaɗaya tun safe Rahila ke kirana nace ina dalili su yi gaba sai azahar zan taho.   Ban ma samu zuwa ba sai bayan azahar ganin na yi rana kawai Yallaɓai ya ce na jira mu fita tare shima Alhaji Mustapha ya gayyace shi ɗaurin aure sai da muka kai su Jidda Gwammaja sannan muka wuce Maitama in da gidan iyayen mijin Ma'u suke, ko da na je su Rahila sun jima da tsufa da zuwa Ma'u har da rumgumeni can na ga su Anty Bahijja Hajiya sama Hajiya ƙasa tun da mijinta shine babba a ɗakin ita mahaifiyar Alhaji Mustapha kuma suna ji da shi, shi ya sa ita ke faɗa aji, ina ta mamakin yadda take ba da umarni a dangin mijinta an ce so so ne amman son kai yafi ita ta samu dama tana yadda ta ga dama amman idanuwanta na kan wasu kar su ji daɗi a gidan mijinsu sannan kar su zama masu faɗi a cika a dangi amman ita gashi tana yarda ta ga dama. Ma'u ta karrama mu ba zan raina mata ba. Shema'u sune yan gaba gaba Ma'u mijinta ne babba a maza duk da ya na da yaya mace, amman itama Anty Ma'u sama Anty Ma'u ƙasa sai abin da ta ce. Ina ta mamakin ina abokiyar zamanta Hajiya Zainab? Sai can na ganta ta ci kwalliyarta da kin ganta kin ga wacce ta gaji arziƙi ba haye ba. Ita ba ruwanta gaskiya ba ta son hayaniya ma Ma'u kuma da ya ke yar bariki ne duk ta siye dangin Alhajin da siyasar ta. Yaya Murja sai da ta yada mini mganar wai sai yanzu na zo biki da rana. Ni ko na ce Yallabai na gida tare muka zo dashi shima ya zo ɗaurin aure. Shema'u kuma ba ta mini magana ba ta yi wani ɗan iskan ɗinki duk ya kama jikinta fuska da jiki sun sha mai ta yi wani fayau saboda in rama wulakancin da ta mini sai da na bari ta shigo ɗakin da aka saukemu sannan na kalleta ina faɗin "Shema'u ranar da muka sauke ki a gidan Nene Tariq ke faɗin wai kin karɓi lambar wayar Uncle Abba." Ba ita kaɗai ba gabaɗaya waɗanda ke wajen sai da suka kalleni daman na yi alƙwarin yadda ta yi min cin mutumci a gidan Rahila sai na rama. Ina mirmishi na ce" Wai kin roɗa ne? To gwara ma ki bi wani sarki shi Uncle Abba mata har ƴayan sarakuna daga Rano an yi masa talla bai ɗaga kai ba ballanta ke, na san dai zuwa yanzu kin ma san ya fi karfinki tunda lambar wayar ma ba tashi ya baki ta Tariq ne." Ƙur ta yi min da ido, ni kuma sai na gauraye fuskata da mirmishi Rahila na ta mini sigina na yi kamar ban gani ba har Yaya Murja mai baki ta kasa mgana. Shema'u kuma dakyar ta iya yaƙe kafin ta ce" Oh. Wannan daman na karɓi lambarsa ne saboda na ga ya yi min kama da wani sai daga baya na gane bashi ba ne, ni fa Sadiya ɗan'uwan mijinki ya yi mini tsufa kaf ma a dangin sa ba wanda zai iya dai dai da Shema'u.' Ta faɗa cikin danne yanayinta ina dage mata gira na ce"Da gaske? Cikin renin wayau Anty Aina ce ta yi mgana. "Sadiya ki bar mganar don Allah." Sai na yi dariya kafin na ce" An barta." Shema'u na yaƙe ta fice amman ni kaina  na san ta ji abin da ake ji in ka tozarta wani  a cikin jama'a sai da ta fita Yaya Balki ta ce ya aka yi ne na gyara zama  ina faɗa musu yadda aka ƙare. Yaya Balki na dariya ta ce" Wannan akwai ɗan jaka da rabi. Zai haɗa fada." Ina dariya na ce" Kaɗan daga aikin Uncle Abba kenan." Rahila ta ce ta gane shi ta taɓa ganin shi a gidana Yaya Murja ba ta ce komai ba sai daga baya ta ce" Ko ma dai menene ba kyau cin fuska a cikin jama'a." Kai tsaye na ce" Ba cin fuska ba ne. Ai naga nan duk ɗayan ne ko? Ta kalleni na kalleta sai kuma ba ta ƙara mgana ba. Ma'u ba ta ɗakin amman na san za ta ji labari Zaituna kam duk muna tare da ita amman ta ci abinci har da guzurin alale, ni da mangariba muka tafi ni da Rahila da Zaituna Yaya Murja ta ce sai ta kai Amarya amma Yaya Aina da Yaya Balki ban ji suna zencen ba amman dai can muka bar su. Na dawo gida da Waina da sinasir Ma'u ta matsa dukkanmu sai da muka taho dashi Shi na ci na sha ruwa tunda mai siga ne sai dare Yallaɓai ya je ya ɗauko su Jidda suka dawo gida. Su sun ci abinci Yallaɓai ne na dafa ma Indomie da ruwan tea ya ci kafin ya kwanta. Washegari Lahadi da asuban fari sai ga wayar Tariq Allah ya yi ma mijin Gimbiya rasuwa. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC No 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supliments wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba. Eaman ScholarSphere. Where ideas Take Shape. WHAT WE DO. ASSIGNMENT PRESENTATIONS. ARTICLES PROJECTS. BOOK AND MANY MORE. CANTACT US THROUGH. 02347067793152 MOTTO: "Pathways of Knowlodge Academy, Nurturing minds, illuminating Futures" *🅿️16* Mutuwa ɗaya ce haƙiƙa na tausaya mata ganin ko shekara biyu ba ta rufe da auran ba. Yallaɓai a ranar suka tafi Abuja tare da Uncle Abba da Nene, da Anty Maimuna Anty Bahijja za ta taho daga baya. Sai Hajiya iya Maman farko kaɗai aka bari a gida. Can suka kwana Tariq da Farida daga kaduna suka tafi. Ni kuma ranar litini na je ganin likita sai ranar na je lab na karɓo sakamakon test ɗina na kai mata shima ta ce lafiya lau ba wata matsala. Sai muka je matakin gaba na A transvaginal ultrasound. Ta ba ni nan da kwana shidda na dawo. A ranar su Yallaɓai suka dawo daga Abuja kwanan su ɗaya amman an bar Anty Maimuna acan tare da Nene da Hajiya Kaltume sai an yi uku za ta dawo. Ranar talata muka je Abuja gaisuwa. Ni da Hauwa da Munnira sai Jamila da Hindatu, Hafsat daman ta na can Abujan ne, sai Mimisco da direbanta ne ma ya tuƙa mu. Mun iske gidan Gimbiya cike da yan uwa da abokan arziƙi. Kaf yayyenta mata da matan mazan suna nan, Hajiya kaltume da Nene ne tare da ita a matsayinsu na manya. Har Sameena a can na ganta ta ce tun ranar da da aka yi rasuwar ta zo sai an yi bakwai za ta koma. Tariq ma na nan shi da Farida da yara. Amman dai shi ya ce min da zaran an yi sadakar uku zai koma gida. Ba Gimbiya ke bin Tariq ba akwai wata mace sannan ita a shekaru ba za ta gaza 33 ba ko na girmeta bai wuce da shekara ɗaya ba. Lokacin da nake yi mata gaisuwa ta yi matuƙar ba ni tausauyi ta yi kuka idanuwanta sun shige ciki, ba ta mgana sai dai ɗaga kai ba ta ci ba ta sha sai an yi da gaske ta ke tsakura da kuma ta ci sai ta amayar dashi. Ta rame sai farin fata da dogon hanci gabaɗaya sai ta bani tausayi har araina ina yi mata addu'an Allah ya ba ta dangana. A bakin Sameena na ke jin Alhajin na gidanta ne lokacin da ciwon shi ya tashi. Ashe yana da ciwon hanta a Egypt ya ke ganin likita a daran su ka kai shi babba asibiti a nan Abuja da niyyar kafin a fita dashi waje, da asuban ranar Allah ya yi masa rasuwa. Allahu akbar. Allah ka sa mu yi kyakyawan karshe. Mun je gidajen duka matan shi mun yi musu gaisuwa tun da dukkansu suna anguwa ɗaya ne asokoro. Kuma gidajen su ba nisa bai wuce ka ga gida uku a tsakani ba. Yana da manyan ƴaƴa ba shi da ƙananu da Gimbiya ta haihu ne zai iya samun yara. Ba kuma yaro ba ne don ko da ta aure shi ya yi shekara 60 Allah na tuba a lokacin har ina ma Hauwa gulma me za ta yi da tsoho mai mata da ƴaƴa haka? Ashe zaman ma ba mai tsaho ba ne. Duk da na zo garin da Yaya Auwal ya ke ban je ba. Saboda gaisuwa muka zo kar a ce daga zuwa ina yawo. Sai dai na kira Lailan na faɗa mata mun shigo garin, sai ta ce in da sarari za ta shigo ta yi musu gaisuwa. Yallaɓai na bari, a gida shi da yara amma mun yi mgana ya ce gobe ranar uku za su dawo sai na ce kawai in sun dawo daga makaranta ya faɗa ma Salisu ya kai su gidan Rahila tunda ya ce za su kwana washegari sai a haɗu gabaɗaya a koma kano. Shi ya sa na kira Rahila na ce, za a kawo mata su Jidda su kwana a wajenta kafin mu dawo tun da Salisu ya san gidanta. Saude kuma Yallaɓai baya nan ban taɓa kwatantan barin ta ita kaɗai da yara a gida ba. Duk anan gidan Gimbiyar muka kwana. Abinci sai dai a kawo shi a dafen shi komai ga shi. Saboda ya na da kuɗi dan kwangila ne ya tara abin duniya kuma a baya ya yi siyasa. Washegari ranar da aka yi sadakar uku da wuri su Yallaɓai suka iso shi da Uncle Abba da su Kawu Sa'adu sai Anty Bahijja. har cikin gida kuma sun shigo an yi ma juna gaisuwa. Ni ina can ɗakin da muka kwana ba mu haɗu ba sai can yamma ma. Mun dai yi mgana ta waya da daddare kuma sun ƙara shigowa, a bakin Munnira na ji ta na faɗin wai Tafida ne ma ya matsa ma Gimbiya da lallashi har ta amince ta sha tee ɗin da yawa kuma sannan sai yau aka ji ta taɓa buɗe baki ta yi mgana amman ga Tafida kaɗai. Ban yi mamaki ba sanin shaƙuwarsu kuma a lokacin ai abar tausayi ce. Washegari muka dawo kano amma mun bar Nene a can ita da Hajiya Kaltume da sauran ƴan uwanta. Mota ɗaya muka shiga da Anty Bahijja na ji suna mgana da Mimisco da cewa wai Gimbiya ba ta mgana da kowa sai Tafida sannan shi kaɗai ke ba ta abu ta karɓa ta sha. Su Nene haka suke yi kamar za su ari baki amman ba ta cin komai ba ta mgana sai kuka. Anty Bahijja ta ƙare maganar ta da cewa" Ga shi kuma kin ga ba gari ɗaya ba. Balle a ce ko da yaushe ya riƙa zuwa ya na matsa mata ta ci abinci" Ina kujeran zama ta tsakiya saboda motar irin babba ce ta yara ta mijin Mimisco ne. Ni da Hauwa muna zaune waje ɗaya har muna haɗa ido muka kalli juna amman ba mu yi mgana ba. "Ba matsala ba ne. Jiya mun yi mgana Hajiya ana tunanin da an yi arba'in Gimbiya za ta koma Rano." In ji Mimisco sai Anty Bahijja ta ce" Ai ya ma fi sauƙi. Allah dai ya ba ta dangana baiwar Allah." Mimisco ta amsa da Amin.sai ita Anty Bahijja ta ƙara da cewa" To Nene fa? Ko itama tare da Hajiya Kaltumen za su zauna har arba'in ɗin? Sai ta yi shuru kafin ta ce" In za ta iya sai ta zauna.  Tunda na taho mata da magungunanta da ta manta. Gida daman ba wani abu take yi ba." Muna jin su suna ta tattaunawarsu har muka iso kano. Da ya ke mun iso da wuri Yallaɓai suna baya mun riga su yo gaba gaskiya. A bakin hanya na ce su sauke ni na samu adaidaita zuwa gida. Sai da na isa gidana na yi salla na dafa indomie na ci sannan na dawo hayyacina. Sannan na kira Yallaɓai sai ya ce min suma sun kusa ƙarisowa, sai na ce ya kira Salisu ya faɗa masa in ya dauko su Jidda daga makaranta gida zai kawo su na dawo sai ya ce to. Ni kuma sai na kira Rahila na ce mata na dawo sai ta ƙara min gaisuwa ni kuma na yi mata godiya har ta na cewa" Uban godiya ke fa ba ki da hali wani lokaci." Daga nan ta kashe wayarta ta bar ni ina dariya. Bayan Rahila da Laila ba wanda na faɗa ma an yi ma su Yallaɓai rasuwa sai gashi kwana ɗaya tsakani da dawowarmu daga Abuja a group gidanmu na ga Yaya Balki na yi min gaisuwa da na tamnbayi in da suka ji sai ta ce Yaya Murja ta faɗa mata da ta je gidanta itama ta ce Ma'u ce ta faɗa mata. Abin sai ya bani mamaki na ga ni dai ba tamin gaisuwa ba. Amman ta je tana faɗa, ban yi mamaki ba tunda tana tare da Anty Bahijja ta kuma yarda da ita shi ya sa wasu labaran na dangin mijina kafin ni na kai ga furta ma wani Ma'u ta yaɗa shi a gari. Tsaki na yi a fili kafin na ce" Wannan ai gwara ta kashe auran nata ta auri Nasir ko Musabahu da wannan bin diddigin na ta." A daren kuma sai ga ta ita da Alhajinta wai sun zo ma Yallaɓai gaisuwa. Kuma abin da ya ɓata mini rai shi Alhajin ya kira Yallaɓai ya faɗa masa za su zo amman Ma'u ba ta kirani ba, shima Yallaban ya kira wayata bai samu ba ƙwatsam na gansu lokacin shi bai ma riga ya dawo gidan ba. Da ɗan fara'ata na karɓe su. Bayan mun gaisa sun yi mini gaisuwa sai na ce ai Yallaɓan bai dawo ba sai ya ce ai sun yi mgana dashi ya na kan hanya. Kafin ya ƙariso na kawo muusu ruwa da lemu na yi shinkafa da miya na kawo musu suka ce sun ƙoshi sai da suka ci abinci sannan suka fito daga gida. Ba ko daɗewa sai ga shi ya iso. Saboda mu ba su waje sai na ja Ma'u zuwa falon na biyu na kora su Jidda ɗakin su bayan sun gaida Ma'u ta amsa cikin fara'anta har tana faɗin" Jidda idon ki kenan? Ina nan dai ina jiran ki a wannan hutun." Sai Jidda ta fara kallo na, sai na yi saurin cewa" A'a ni ba ruwana ki tambayi babanki in ya barki in an yi hutu sai ki je." Da sauri Ma'u ta ce" Ai ni dai na san Yallaɓai ba zai hana ba." Sai kawai na ɗan yi yake. Muna zaune ba mgana sai baɓatun talabijin. "Ashe kin je Abujan kema? "Uhm" Na faɗa ina kauda kaina ba na son kallon Ma'u saboda kallonta ba alheri a cikin yanayin kallon ta. "Allah ya jikan sa." Na amsa da Amin shuru na wani lokaci sannan ta ce" Allah sarki ta ba ni tausayi rashin miji ba daɗi." "Ai fa kam." Na faɗa ban bama mganar muhimmamci ba. "Allah ya kawo mata kyakyawan zaɓi." Na amsa da Amin na ɗauka daga nan maaganar za ta tsaya sai kawai na ji tana faɗin. "Anty Bahijja na gaya mini halin da ta ke ciki kamar in yi mata kuka ta ce mini ba ta cin abinci sai kuka ba ta kuma mgana da kowa sai Yallaɓan ki" Kure ta da ido na yi domin na san daman sai ta zo wannan gabar." "Ta ce min shi kaɗai ke iya cewa ta ci abinci ta ci kuma shi kaɗai take yi ma mgana. Abun mamaki ko da ya ke na ji labarin an ce daman sun shaku da juna." Ta fada tana mini mirmishi. "Haka na ji." Nima sai na ba ta amsa amman ban nuna wani abu daga saman fuskata ba." "Allah sarki. To bakomai tunda na ji Anty Bahijja na faɗin ana arba'in za a dawo da ita Rano  Sai na ce ai ko ga shi kusa ina Rano ina Kano? Yallaɓai sai ya riƙa zuwa yana kula da ita baiwar Allah abin tausayi.' Ta gama faɗa har tana bayyana jimamin a saman fuskarta. Ni na san da biyu ta yi wannan maganar sai kawai na yi mata mirmishi kafin na ce" Gaskiya ne. " Sai na datse bakina ban kara yin mgana ba amman ina kallonta ta gefen ido tana mirmishi kafa ɗaya ta ɗora kan ɗaya kamar falon gidan Alhajin na ta ne. Yadda ta ga na haɗe rai ina duba wayata ya sa ba ta ƙara mgana ba. Ba daɗewa ma sai ga shi Yallaɓai ya leƙo ya ce Ma'u ta fito za su wuce tsabar haushi iyakata a bakin kofa ban fita haraba ba Yallaɓai ne ya fita ba su shigo da mota ba sun yi parking daga waje ne. Kamar maganar Ma'u ba za ta dame ni ba, sai gashi kuma tana sukan raina ace wai komai ya faru a dangin mijina sai  Ma'u ta sani in na ji haushinta ta wani fannin kuma ban ganin laifinta ba kowa ya ba ta dama ba sai yayar Mijina. Ta kuma wani bangaren itama Anty Bahijja sai na ke yi mata uzuri saboda in dai Ma'un da na sani ne makircinta zai iya siya mata kowa da kuma wannan makircin ta siye Anty Bahijja. Renin na ta har ya yi yawan da za ta zo har gidana tana gaya min mgana na ci ji yatsa da na ƙyaleta amman dai na san za ta ƙara wata rana dole za mu haɗu. Washegari na koma asibitin domin ganin likita. Wannan karon ma Dr Aisha ta ce vaginal ɗina komai lafiya lau sai matakin gaba na A hysterosalpingogram a type of X RAY, that allows your provider to see your uterus and follopian tubes. Dr Aisha ta faɗa mini scan ɗin is very painfull  tunda na cikin mahaifa ne. Ta gaya mini zan iya bucking anan asibitin ko mu fita waje, da na kira Yallaɓai sai ya ce kawai na yi bucking anan asibitin, ban dawo gida ba sai da na yi bucking sun ba ni sati ɗaya na dawo su yi min scan ɗin. Ban damu da wahala ko wani abu ba babban burina na kai ga matakin nasarata shine a gabana. ****** BAYAN SATI UKU. Bayan sati da huɗu rasuwar mijin Gimbiya a lissafi kuma bai fi saura kwana biyu ya yi arba'in da rasuwa ba. Kuma har alokacin Nene da Hajiya Kaltume ke zaune da ita sai dai yan'uwa da ba su samu zuwa ba sukan je domin yi mata gaisuwa. Har na ji Yallaɓai suna mgana da Mimisco akan a cikin satin su Nene za su dawo da Gimbiya gida. A cikin sati ukun da suka gabata lamarin Gimbiya ya fara ba ni mamaki har na fara tunanin ko ba ta da tawakalli ne kuma har sai da na furta ma Yallaɓai har ya ji haushina. Haba abun nata ya yi yawa ba kanta farau rashin miji ba Allah na tuba sauran matan shi da suka yi shekaru aru  aru da shi ma sun ɗau dangana haka ma ƴa'ƴan shi da suka rasa uba suma sun dangana amman ita ba alamun dangana a lamarinta. Na tuna ni kaina fa uwata ba ta a duniya nan na ɗau tawakalli Yallaɓai ba shi da uba shima ya ɗau dangana. Har wani lokacin in na jin masa shaƙiyanci ko ina son ya yi min wani abu ya ce ba zai yi ba sai na marairai ce ina faɗin." Yallaɓai ka tausaya mini ka ga ni fa marainiya ce.' In na ce haka a lokacin sai ya yi dariyan nishaɗi kafin ya ce" Au ke sai yanzu kika san ke marainiya ce? Mu ai mun daɗe cikin maraici kuma ba mu mutu ba." Ko kuma ya ce" Ke ba marainiya ba ce Alhaji ai bai mutu ba ko kin kashe shi ne? In ya faɗi haka daga ni har shi sai mun ƙyalƙyace da dariya. Saboda mun yi shaida babu abun bautawa da gaskiya sai Allah. Kuma Annabi muhammdu manzonsa ne, sannan rayuwa da mutuwa duk ta na hannun shi ne. Sai dai ta bangaren Gimbiya ba ta san wannan ba, tun da a ka yi rasuwar nan saboda ba ta jin mganar kowa sai na Yallabai a rana ban san adadin sai nawa ya ke kiran waya a ba ta ba, yana lallashinta ta samu ta ci wani abu. Ko in ta fara kuka sai su kira shi su ba ta ya yi ta mata nasiha, duk wannan ƙokarin da ya ke yi mata ba ta dangana ba. Bayan wanda yan'uwa ke yi mata shima duk bai sa ta dangana ba. Tun ina tausayinta har ta koma ba ni haushi. Na yi ta tunanin ita ko wani irin so ta ke yi masa haka. ko dai garken yaya ta tara da shi sai haka amman aure duka duka wata ashirin ba ciki ba goyo haba lamarin nata ya yi yawa har na fara gajiya da jin labarin halin da ta ke ciki a bakin Yallaɓai in yana faɗa min Daughter ta zama abin tausayi, tun in yana faɗa ina nuna jimami har na daina saboda lamarinta ya wuce na musulma mai tawakalli ya koma hauka da jayayya da ubangiji. Nan  ko sati ba a yi ba sai da Yallaɓai ya koma Abuja ya kwana ɗaya sannan ya dawo. Wai ta shige ɗaki tun safe ta rufe kanta tana kuka kuma tun daren jiya ba ta ci komai ba su Nene sun yi sun yi da ita ta buɗe ta ƙi har azahar shi ne Nene ta kira Yallaɓai a waya ta ce ya bar duk abin da ya ke yi ya zo Abuja. Shi ne fa ya na ma office ya dawo gida ya na faɗa min tare da cewa na haɗa masa kayan tafiya na kwana ɗaya tun da ba zai yuyu ya je a yau ya kuma dawo ba. A lokacin ne na furta masa abin da ke zuciya ta. "Haba kamar dai ba ta da tawakkalli. Wai kanta farau mutuwar miji? Na faɗa ina mai sakin  tsaki tun da shima yana kan aikinsa ne amman an wani ta da shi zuwa Abuja. Ni ina ganin gulma ne ace duk cikin yan'uwanta da suke uwa daya uba ɗaya mata da maza ba ta ga wanda za ta riƙa jin mganarsa ba sai Yallaɓai da zaman da ya yi a gidansu na ɗan lokaci ne, za a ce ya fi mata yan'uwanta da suka fito ciki ɗaya ne? Tsawa Yallaɓai ya daka mini kafin cikin ɓacin rai ya kalleni ya na faɗin" Sadiya wannan wani irin mgana ne? Kallonsa na tsaya yi saboda sai na ga kamar ban faɗi wani abu mara kyau ba. "Me na ce? Gasikiya na faɗa hakuri ake yi. In ta na wannan abun kamar tana faɗa da Allah ne." Kawai sai Yallaɓai ya fara faɗa ta in da ya ke shiga ba ta nan ya ke fita ba. Wai na san zafin mutuwan miji kuwa.? Ni ko kai tsaye na ce" Ban san na miji ba. Amman ai na san zafin mutuwar uwa ko? Na faɗa ina kallon shi saboda na ga zai wani hau kaina daga faɗin gaskiya saboda ma na ƙara kunsa ma sa kai tsaye na sake faɗin" Kuma na tabbata ba yau aka saba mata rashi ba. Ai ta rasa uba da yan'uwata me ya sa ba ta yi haka ba sai yanzu? Gaskiya ku yi mata faɗan ta zama mai tawakkalli kuka ko rufe kai a ɗaki ba shi zai kawo mafita ba." Ni kaina tsaye na ke mgana kuma shi kan shi Yallaɓan ya san ni. Amman a mamakina kai tsaye ya kalleni kafin ya girgiza kai ya na faɗin" Na yi miki uziru saboda ba ki san zafin mutuwar miji ba. Amman ba shi zai hana na ce ba ki da tausayi ba Sadiya." Baki buɗe na kalli Yallaɓai ya na sauya kaya cikin nuna kaina na ce" Ni ce ba ni da tausayi Yallaɓai? Kai tsaye ya ce" Ƙwarai da gaske. Domin duk mai tausayi tausaya ma halin da Daughter ta ke ciki zai yi ba maganganun banza marasa tushe ballantana makama ba. Shirme kawai." "Daga faɗin gaskiya? "Ki riƙe gaskiyan ta ki ba a so." Haka ya maida mini amsa a fusace. Ajiyar zuciya kawai na sauke domiin na ji raina na tafarfasa zan iya maida masa martani amman sai na ƙyale shi, ɗakin na bar mishi kayan na shi ma ban gama haɗawa ba na ce ya haɗa da kan shi tun da da ga faɗin gaskiya sai na yi laifi ya je can ya tare saboda kula da ita. Da zai tafi ko sallaman da muka saba ba mu yi ba, shima fuska a haɗe nima na haɗe nawa ko haraba ban raka shi ba, daga falo na yi masa fatan Allah ya kiyaye hanya. Amman Yallaɓai ya ba ni mamaki, yadda ya wani ɗau zafi daga fafin gaskiya. Wani abu ke tsaya min a maƙogwaro in na ji yana ambaton ta da Daughter ƙatuwar mace shima ya na namiji  magidanci da wani sanabe da iyayi. Har ya je ya yi kwanan ɗayansa ya dawo ba mu yi waya ba. Ya san halina yadda bai kirani ba nima ban neme shi ba su Jidda suna ta tambayan Abba na ce ya ta fi Abuja. Da ya dawo ban yi masa tarban da na saba ba. Ni ban haɗe rai ba sannan ban sakar masa ba, sai dai lokacin da ya dawo sai bai dawo da fushin ba. Shi ya fara saki sai nima na saki amman na so ya cigaba ya sanni ni sai na iya gaba dashi ba wani abu mai wahala ba ne a wajena. Amman kalmar ba ni da tausayi da ya kirani da shi ya taɓa ni kuma sai da na yi masa mgana sai ya ce na yi hakuri amman nima ai bai dace na ce haka ba, kenan har a lokacin bai ga gaskiyan abin da na faɗa ba to ai shike nan ni kuma na saka a raina ba zan kara mgana ba. Abin da ma ya faru a can ɗin ban tambaye shi ba shi da bakin shi ya ke faɗa mini Ulcer ta kama Gimbiya sannan kuma jininta ya hau sai da likita ya zo gida ya duba ta. Bakina ƙanin kafata na ce Allah ya ba ta lafiya domin na fahimci Yallaɓai kiris ya ke jira da ni ya yaɓa mini mgana. Bayan arba'in da kwana uku Gimbiya ta dawo Rano. Mimisco ta je tare da ita ma aka maida ta rano. Sai yayyenta maza da suka je saboda sun gana da yan uwan marigayin da yaran shi. Farko sun nuna ba su so tafiyar ta ba sun nuna gwara ta zauna a gidanta ta gama takaba sai su kuma ƴan uwanta su kawo dalilin halin da ta ke ciki in ta koma gida ta na ganin mutane za ta samu ta dawo dai dai ba kamar zamanta anan ba, da haka suka amince ta koma gida amman sai da aka kai ta duka gidajen matan ta yi sallama da su. Suna kuka tana kuka  an kwashe mata duka kayanta a ka rufe gidan aka mika makullin ga iyalanshi tunda sun ce suna kan tatrara abin da ya bari ne bayan an gama za a bincika in da baahi a biya in babu kuma in lokaci ya yi za su nemesu domin rabon gado. Gimbiya ta yi sallama da garin Abuja, aikin nata ba mganar shi daman tun da aka yi rasuwar ba ta je ba. Ana tunanin in komai ya lafa a yi mata transfer ko zuwa cikin garin kano ne. Kwana biyu tsakani da dawowarta na je yi ma Nene bangajiya tun da sai da ta ƙara kwana a Reno sanman ta dawo gida ita ce ma ta ke bani labarin abin da ya faru kafin ta tahowar su. "Allah sarki. Allah ya yi mishi Rahama ita kuma Allah ya ba ta dangana." Nene ta amsa da Amin kafin t ce" Ai an fara karɓa mata rubutu wajen wani malami a can rano. Da safen nan mun yi mgana da Hajiya ta ce ta fara sha da safe. To Saudatu ta rame ta lalace ta fita hayyacinta. Rayuwarta akwai tausayi sosai." Nene ta ke faɗa cikin rawan murya.   Ni kuma sai na ce" Har yanzu ba ta fara dangana ba Nene? Sai ta ce a hankali dai amma in na ga Saudatu sai na tausaya mata. A gidan na yini ina nan Hauwa da Munirra suka zo da su Suwaiba domin yi ma Nene gaisuwa da barka da zuwa kaf ahalin gidan nan Yaya Usman ne kawai bai zo ba da Anty Zabba amman dai sun yi gaisuwa ta waya, har Muhammad Kabir da Nafisa sun zo gaisuwa daga katsina. Sati ɗaya da dawowarta Yallaɓai ya ce na shirya muje Rano domin na ƙara yi musu gaisuwa ban yi musu ba na shirya ashe tare da Mutakƙa ne da Hauwa sai na ji daɗi a motar Yallaɓai muka je ranar weekend yara kuma wajen Nene muka bar su gabaɗaya. Mun je mun iske mutane cike a gidan a kallah dai ba za ta yi kaɗaici ba. Sannan ga babbar Aminiyarta babbar ɗiyar Anty Zuwaira Naja'atu duk da ita Gimbiya ta girmi Naja'atu amman kuma Allah ya haɗa wannan kawancen lokacin da aka yi rasuwar ita da mijinta ba sa ƙasar suna Italy. Kuma lokacin da aka yi rasuwar ta so dawowa sai matslan visa ya hana ta sai dai su yi mgana a waya to faa sai cikin satin nan ta dawo.  Amman a kano take aure da yaron wani mashuririn ɗan kasuwa a garin kano mai suna Buhari manga. Ba su cika ma zama a Nigeria ba yawancin kuma duka yayan da Naja'atu ta haifa guda uku a kasar waje ta ke zuwa ta yi renon cikin ta ta haihu. Ita muka iske tare da Gimbiya wacce ta faɗe ta rame sai dogon fuska da hanci bakinta duk ya bushe idanuwanta duk sun zurma. Tana sanye da hijabi da caabaha. Mun gaisa da Naja'atu duk ba wani damuwa da mutane ta yi ba, irina ce shi ya sa na ke yi mata uzuri ban cika damuwa da halinta ba ammam duk in da muka haɗu za ta gaisheni da tambayan su Jidda. A ɗakin Hajiyar Tafida muka zauna ita kuma Gimbiya da ƙawayenta suna ɗakin Hajiya Kaltume kamar  acan aka sauke ta tana takabar nata. Muna Rano har bayan la'asar na yo alwala daga bayin waje Hauwa  ta rigani yin na  ta shiga ɗakin Hajiya ni kuma lokacin da na yo tawa sai na ga maza sun shigo yan gaisuwa sun shiga ɗakin sai na wuce ɗakin da Gimbiya ke ciki Naja'atu ma ta bani darduma na shimfiɗa na ta da salla. Na kai raka'a ta biyu na miƙe a raka'a ta uku Yallaɓai ya shigo na ji muryan Mutaƙka da na Uncle Abba sai na wasu mazan amman tun da ina salla ba zan iya sanin su ba. Ina ji Mutaƙka na yi ma Gimbiya sallama daman kuma Yallaɓai ya ce bayan la'asar za mu tafi. Daga nan sai kowa ya fita har Naja'atu aka bar Yallaɓai da Gimbiya. Ban sani ba ko shi ya gane ni ce ke sallah ko kuma bai gane ni ba amman ita ta san nice na ke yin salla a wajen Suna ta gefen damana ne, ina kai sujjadar ƙarshe na ga Yallaɓai ya duƙa a gaban Gimbiya yana mai kiran ta da sunan da ya saba kiran ta dashi. "Daughter." Sai ta ɗago ta kalle shi a marairaice kafin ta amsa murya shaƙe. "Daddy." Dai dai lokacin da na ce" Assalamu alakum waramatullah Hagu da dama da kuma ƙarfi, ina juyawa bangaren dama muka haɗa ido da Yallaɓai har da ita Gimbiyan Ina salla ne amman kirjina na wani irin suya ne. Kallon yadda ya gurfana na yi a gaban Gimbiya har gwiwar kafarsa na gugan kafafunta da ke tankwashe sai kawai na kauda kaina na miƙe ina na ɗe darduman da na yi sallah da shi. Ko kunya ya ji da ya ganni sai ya yi saurin matsawa baya ya na mai miƙewa tsaye. "Da man ke ce ke salla? Ya faɗa ya na kallona sai kawai na kalle shi kafin na ce" E" Sannan na ijiye darduman a saman hannun kujera kafin na kama hanyar barin ɗakin ina faɗin" Ku cigaba da mganar ku." Ban san ko sun bi ni da kallo ba saboda ni ban juyawa ba har na fice daga ɗakin. Ba dota ba doya ba daddy ba Dada.  Tun daga lokacin na rage fara'a har Hauwa sai da ta tambayeni ko lafiya na ce lafiya lau kila Yallaɓai ya tsargu ne ya sa bai daɗe a ɗakin ba ya fito ya leƙo nan ya na cewa mu fito za mu biya gidan su Nene kafin mu wuce. Sallama muka yi musu, sannan mun kara shiga wajen Gimbiya muka ƙara yi mata Allah ya jikan rai ya ba da danganta ta amsa a hankali. Daganan sai gidan su Nene muka je muka gaida Innayi ko minti talatin ba mu yi ba muka kamo hanyar gida. A cikin zuciya na ga to damuwar ta mace ce, namiji fa sunan shi Namiji ba abin da ba zai yi ba sai kawai na watsar da abin na ɗan saki fuska Yallabai daman suna hira da Mutaƙƙa ya nna ta faman sako ni a ciki da a shake na ke amsa masa sai daga baya na saki jiki muna ta hira. Sai da muka biya Gwammaja muka ɗau yara sannan muka kai su Hauwa gida muka wuce namu gidan Yallaɓai dai kamar ya kama kan shi ni dai ƙala ban ce masa ba sai shi ne da za mu kwanta ya ɗauko mganar. "Dazu Allah ban san ke ce ke sallah ba." Na yi kamar ban ji sa ba sai ya ƙara cewa" Kin san da ya ke sai a hankali. Na shiga yi mata sallama na ke ƙoƙarin lallashinta ta riƙa cin abinci." "Haka fa. Ai ka kyauta." Daga nan na juya masa baya na ja bargo. Ban sani ba ko yabi ni da kallo amman ina da tabbacin ya yi haka. Bai takuramin ba amman ya raɓo ta bayana mun kwanta. ***** Haka rayuwar ta cigaba da tafiya. Wattani wajen biyu sun zo sun shuɗe kamar tafiyar iska. Har su Jidda sun yi jarabawa 3rd tearm sun yi hutu. Jidda Gidan Mimisco ta tafi hutu ita kuma Baby gidan Yaya Maimuna gida tsit daga ni sai Yallaɓai sai Saude da ke zuwa yi min aikace aikace. Bangaren asibitina kuwa tuni na yi nisa a  gwaje gwajen da ake yi minib wanda na yi na ƙarshe shi ne Pap smears ne kuma har na karɓi result ɗin wannan satin da ya wuce na kai ma Dr Aisha cikin ikon Allah ta ce mini shima ba wata matsala. In da na ke ɗan samu salama kenan kuma ta na bani hop ɗin duk da saura gwaje gwajen ba mu gama ba, ba ni da watsala lokaci ne bai yi ba in ya yi zan ƙara haihuwa. Zuwa lokacin shiryen shiryen bikin Yaya Usman ake yi domin cikin watan da za mu shiga kafin azumi za a yi bikin na shi. Anan Gwammaja za a yi bikin tunda ɗaurin auran ma a kaduna ne. Yadda Yallaɓai ya faɗa mini gabaɗaya da Anty Zabba da yaran za su zo kamo sai an gama biki za su koma fatakot har da amaryan. Har anko ƙannensa su Nasara sun fidda Atamfa ce mu ma duk mazajen mu sun yi mana mu da yara. Aure dai ya tabbata ba fashi amarya na dawowa daga london aka tsaida date ɗin biki. A kuma tsuƙin ne na kirga za mu yi 15 years Anniversery da aure ni da Yallaɓai zuwa bayan sallan azumi da kwana shidda kenan. Ni kaɗai a raina na shirya za mu yi walima tun da tun na 10years ba mu kara ba lokacin Baby ta cika shekara ɗaya sai muka haɗe da birthady ɗin ta. Ba mu kara yi ba sai wanman karon na ke fatan mu sake yi. Daman a gida ne daga ni sai shi sai yara muka yanka cake ɗin mu sha hotunan mu da ciye ciye washegari kuma Yallaɓai ya fita damu mu wajen wassani da sauran su. Tun tuni na so na yi masa mganar amman bai samun lokaci Alhamdulillah yana ta samu kwangila bayan gama gina gidan  buredi a Rano dalilin haka ya samu kwangilan gina bayuka na wasu makaratun sakandiri a garin na Rano sai ya kasance zamansa a nan office ba sosai ba sai dai Musabahu ya zauna wani lokacin gidan bulo kuma daman sun ɗauki yara ma su kula da shi, shi dai Musabahu manaja ne kawai. Abin da na fara lura da shi shi ne Gimbiya ta fara ƙoƙarin takura ma rayuwar aurena ta na daga can gidansu tana takaba. Ni na san cewa Yallaɓai na zuwa ganinta tun da yana yawan zuwa Rano. Ban kuma taɓa nuna damuwata ba ko na nuna  fuska ban ji daɗi. Sai dai na ga ba ta  da hankali in ya dawo gida sai ta kira shi a waya ta ji wai yadda ya koma gida. Da safe kuma ta iya kiran sassafe tsirfa kala kala daga ta ce Anty Bahijja za ta ba da saƙo a kawo mata sai ta ce Nene sai ta ce Anty Maimuna wani lokacin ita ce ma za ta ce ya siya mata abu kaza ya taho mata dashi tsirfa kala kala ranar da bai je Rano ba ta riƙa kira kenan ta na korafin me ya sa bai zo ba? Abin da ke ba ni mamaki shi kuma sai ya na biye mata sau ɗaya na yi masa mgana da cewa wani lokacin ta na kiran shi a waya ba ta da abin faɗa sai kawai ya ce min abar tausayi ce kuma ga shi ta samu hawan jini dalilin rasuwar nan shi ya sa ba a son ana ɓata mata rai. Na ga ƙoƙarin Yallaɓai da ya iya faɗa min haka amman kuma ta wanni fannin ban yi mamaki ba mun taɓa samun matsala da shi a baya tun ban haifi Baby ba akan Gimbiya muka yi faɗa da Yallaɓai na ce in son Gimbiya ya ke yi me ya sa ya aure ni bai aure ta ba saboda na ga bin binin ya yi yawa amman sai buɗe baki ya yi ya ce mini" In da bai haɗu da ni har Allah ya haɗa zukatanmu ba to ya ba ni tabbacin bashi da mata sai Saudatu." Har Gimbiya ta yi aure ban daina fargaban wata rana zan ta shi na ga Yallaɓai ya auro min ita ba na huta da ta yi aure amman yanzu kam bayan ta zama bazawara ta sake dawo mini cikin rayuwata ta na yi min barazana. Akwai wata rana baƙin ciki kamar na kama Yallaɓai da duka da asuban fari fa, ya je sallar asuba bai dawo ba ta yi ta kiran wayarsa ina ganin an saka Daughter na san ita se sai ban ɗauka ba. Sau uku ta na kiran sa har wata zuciya ta ce na ɗauka sai wata ta kwabe ni sai da ya dawo na ce an kira shi a gabana ya ɗaga waya ya kirata bayan sun gaisa shi ya ma ɗauko ko wani abu ne ya faru ya na tambayanta ko akwai matsala ne ina jin muryanta ta cikin wayar tun da wayar da ɗan kara ta na faɗin. "Daddy yau za ka shigo? Sai ya ce ya na sa ran yau sai kawai ta ce" Ka taho mini da tsaraba." Shi kuma ya ce me take so ta ce duk abin da ya ke so. Tsabar takaici na kasa mgana. Sai na shanye takaicina na kalle shi ina faɗin" Wai ta gama takaba ne? Kai tsaye ya ce min" Cikin wata nan za ta fita in sha Allahu." Sai kawai na girgiza kaina, ina so na yi mgana amman kuma sai na fasa saboda maganar ba ta da amfani sai kawai na yi masa shuru kuma ya je Ranon a ranar kuma ina da tabbacin ya yi mata tsaraba tunda bayan ya dawo gida muna tare ta kira tana yi masa godiya. Ƙarin abin haushin ma wani lokacin in dai ya kai dare a can abincina sai dai ya zama kwantai sai ya ce Hajiya ta matsa masa ya tsaya ya ci abinci. Kuma Yallaɓai na ganin ina nuna damuwar hakan a saman fuskata bai taɓa damuwa da ya ba ni haƙuri ba shi a wajen shi ba a yi komai ba sai kawai na koma gefe na na zura masa ido ina ganin gudun ruwan shi amman dai ni na san ko na ƙi ko na so ai ƙarshen alewa daman ƙasa ne. *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU  #1k NE KACAL,  AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/FAtGNQc8Y8pB008TuxFJVo Eaman ScholarSphere. Where ideas Take Shape. WHAT WE DO. ASSIGNMENT PRESENTATIONS. ARTICLES PROJECTS. BOOK AND MANY MORE. CANTACT US THROUGH. 02347067793152 MOTTO: "Pathways of Knowlodge Academy, Nurturing minds, illuminating Futures" *🅿️17* Shirye shiryen biki Yaya Usman kawai ke kan layi yanzu saboda bikin ya rage saura kwana takwas. Kuma da ya ke bikin anan Gwammaja za a yi ita kuma Amarya a Kaduna gidan kakkaninta wanda ya haifi mahaifinta. Shima tsohon Soja ne mai ritaya amman ya rasu. To nan za a ɗaura aure ranar asabar amma taron biki ranar jumma'a ne asabar da an gama ɗaura aure amarya da tawaganta za su sauka a Kano sai ranar litini ango zai ɗau amaryansa da iyalansa su hau jirgi zuwa fortacol Kuma auran daman na yan boko ne lefe ma kuɗi kawai ya tura ma Amaryan aka ce ita ma uwargidan an ce ya ba ta kuɗi bayan ya biya mata Hajji shi da ita da Amarya bayan sallah da an fara tafiya za su ɗaga zuwa ƙasa mai tsarki. Zuwa lokacin hatta abincin da za a dafa Yaya Usman ya saka an kawo. Biki dai za a yi na masu da shi, ba talauci a ciki ba kuma ɓarnan dukiya dai dai ruwa dai dai tsaki.   Gimbiya ta gama Takaba tsakanin bikin Yaya Usman saura kwana goma ne. An yi walima da taro a can Rano amman ni dai ban je ba. Na ga dai su Anty Bahijja sun ta ɗora ta a status suna mata addu'an Allah ya kawo wani mijin na alheri ya kuma ƙara mata dangana. A cikin hotunan akwai wanda aka ɗauke ta a ranar da ta fita takaban ta yi kwalliya amman ta yi rama duk da dai haka a raina na ce dangana ai ta riga da ta samu ko Yallaɓai bai mini mganar ba nima ban yi masa ba. Na kuma ƙara ganin ƴan'uwan suna yi mata addu'a a group ɗin iyalan Marigayi Muhammad Inuwa 02 wanda muke ciki gabaɗayanmu har mu surukan gidan da a can Ranon gabaɗaya amman kuma suna da wani wanda ba ma ciki shi kawai na iyalan gidan ne gabaɗaya shima na sani ne saboda ina gani a wayar Yallaɓai. Kuma shi wannan da muke ciki daga baya aka saka mu, sannan ba a cika ma mgana ba sai ta kama ina ga sun fi yin ɗan sirrin su a can ne saboda ire iren mu da suke gani kamar bare.   Yallaɓai kuma daman shi harkan chart ba wani damun shi ya yi ba. Yana yi ba wai ya yi ba ne, saboda harkokin shi da jama'a amman sai ya yi wata biyar bai saka status ba. In ma ya saka sai mutuwa ko in ya  nishaɗu ranar Jumma'a ya saka salatin Annabi. Amman ni na san yana kiran Gimbiya a waya tun da ina yawan ganin sunanta a call long ɗin shi ba da kuma Niyyar bincike ba sai saboda wayarsa ba ta da shamaki a hannuna kamar yadda nima tawa ba ta da shamaki a hannunsa.   To a irin haka ne ranar da ta yi fitar Takaban wayar na hannuna da daddare Yallaɓai ya shiga Tiolet saƙon ta ya faɗo Allah na gani ban buɗe ba amman daga sama na hango godiya zuwa ga Daddy na,  na gode bi sa ɗawainiyar da ka yi ta yi da ni. Daga nan saƙon ya yanke gudun shiga hurumin da ba na wa ba sai na kauda kaina ban buɗe masa saƙo ba saboda ba ni aka tura mawa ba da ya fito kamar in faɗa masa an tura masa saƙo sai kuma na fasa na ajiye masa wayarsa a raina na ce ai zai gani. Yadda na gani ban nuna na gani ba, nima kuma bai nuna mini komai ba, sai kuma da safe kafin ya fita na ji suna waya lokacin muna dining ina haɗa masa abun kari, alƙwarin da na yi ma kaina shi ne zan zura masa ido na ga iya gudun ruwan shi daga shi Gimbiyar. Amman abin na sukan raina ganin gabaɗaya idon ta na kan mijina kamar shi kaɗai ne a dangi? Sai wata zuciyar ta tunasar da ni a lokacin." Kin manta ba namijin da ta yi ma so irin mijin ki? To ko dai angulu ne ke marmarin son ta koma gidanta na tsamiya? ****** LARABA." Yau mun wayi gari ranar laraba. Kimanin jibi Jumma'a taron bikin a can Kaduna, mu kuma nan sai ranar asabar tunda mu za mu tarbi amarya. Ita kuma Anty Zabba ta iso kano ita da ya'yanta amma a gidansu ta sauka ta ce ita a can za ta yi nata taron biki. Mijin ta kuma ya amince shi ya sa ma kowa bai damu ba. Sai dai wanda ya ga zai iya bin ta can sai ya je, ni tun da na ji haka na ce me zai kai ka? Ai sai a ce ka je ganin gulma ne gwara mu tsaya nan Gwammaja in ta zo ma haɗu a gaisa. Tun safe na tashi ina aikace aikace saboda mun yi da su Hauwa a Gwammaja za mu yi ni saboda aiki. Tun asuba da na tashi ban koma ba, tun watan da ya gabata hutu ya ƙare mini Yallaɓai ya cika alkwari ya saka Saude a makaranta wata private school ce mai ɗan sauki sauki a nan kusa da anguwar Ɗorayin ta ke da kafa ma Saude ke zuwa shi ya yi mata komai har uniform da jaka da takalmi an saka ta Jss2 saboda ta yi girma a jss1. Tun da ta fara zuwa makaranta shikenan aikin gidana ya dawo kaina saboda ba ta samun lokaci sai biyu suke ta shi in kuma ta dawo da la'asar ta na zuwa islamiya. Sai alhamis da jumma take zuwamin in ta dawo daga makaranta tun da ba islamiya weekend kuma sai ta je Allo ta dawo.   Aiki duk ya yi min yawa rabo na da barcin safe har na manta da su Jidda sun tafi makaranta zan fara gyaran gida ina gamawa na je na tada Yallaɓai ya yi wanka ya zo mu karya to sai ya fita ne nake samun daman kwanciya na huta bayan azahar irin uku saura na miƙe na shiga kitchen na ɗora girki saboda yan makaranta. Kibar da na fara yi saboda hutu duk ta zazzage ga shi daman ni ba gwanar aiki ba. Ina yi ina jin na gaji kai har gobe ba zan kaunaci aiki ba. Ga shi yanzu Yallaɓai ya lalace ba iya taya ni da komai ko da ya na gida ne sai dai ma ya yi ta mini dariya in ya ganni na yi shigar aiki na tsuke cikin Boom short da ƙaramar riga sai ya hau tsokanata.   "Sadiya ƴar laushi barka da aiki."   Ranar haka ya ke shan harara ba na ma tanka shi domin na biye masa sai ya ɓata mini lokaci shi kuma bai tayani ba, ballatana  ya rage min wani aikin Ahalin na san ba abin da bai iya ba shima kuma ya san na san ya iya komai. Yau dai aiki ya kacame mini ga wanke wanke jiya ban yi da yamma ba. Jidda ta so ta yi lokacin an kusan mangariba sai na ce ta barshi sannan ga shara na gama sai na yi mopping tunda na ɗan kwana biyu ban yi ba sannan na saka turaren wuta a burner gidan ya ɗau kamshi. Na riga na wanke tiolet ɗin su Jidda saura na mu shi na shiga na wanke ban gyara Bedroom ɗin mu ba Yallabai na kwance ya na barci har da minshari.   Falon yara na koma na zauna ina maida numfashi. Na huta kafin na tashi na yi wanke wanke. Amman na so Yallaɓai ya ta shi ya yi wanka ya karya sai na haɗa komai na wanke domin da na fara shara na fara jin jiri tuni na je na karya cikina ya cika to ina zan zauna shi ya na can kwance ni kuma ina aiki yunwa ta far min a ciki na faɗi a sume tuni na nema ma kaina mafita na karya na barshi. Na yi hutun sama da minti talatin domin kallo ma ne ya ɗau hankalina wani film ɗin hausa da suke haskawa tashar Arewa24 na ga ya fara mini kyau sai na zauna ina kallo tuna ina hutun jaki da kaya a saman kaina ne ya sa na miƙe. Har na fara wanke wanke kuma sai na tsame hannuna a cikin ruwan omo na wanke da ruwa na fita zuwa cikin bedroom ɗinmu. Tsaye na yi kawai a gaban gado ina kallon Yallaɓai ina sanye da wando baki plazo rigar jikina vest ce ta lame min jiki kaina ɗankwalin doguwar riga ne na yi gammo da shi a saman kaina. Zuwa na yi kusa dashi, na fara jan bargon ina kiran sunan shi amman sai ya juya ya na jan bargon ina ja, alamun dai ba zai iya ta shi ba. "Yallaɓai.." Na faɗa ina dai dai ta saitin kunnuwan shi. A hankali ya buɗe idanuwansa da suka shige ciki saboda barci. "Mene ne kuma? Ya faɗa da muryan barci har ya na wani yamutsa fusaka ina ganin haka na saka hannuna na shafa kumatunsa sai ya ji sanyi da sauri ya ware ido yana kallona ni kuma sai na koma na riƙe kugu ina kallonshi rabi harara harara. Ɗan tashi ya yi kaɗan ya na jingina da jikin gado kafin ya kalleni daga sama har ƙasa sai kawai na ga ya yi mirmishi kafin ya ce" Me kuma na yi! ? Baki buɗe na ce" Me ka yi fa ka ke tambayata Yallaɓai? Ya na kallona ya ce" To ba dole na tambaya ba, kin ta da ni kamar yaƙi. Ga shi ke kuma kin riƙe kugu kamar mai shirin dambe." Yana cewa mai shirin dambe na dunkule hannu na ware kafa ina masa gusha gusha sai na kai masa hannu kamar zan naushe shi. Dariya ya ke ta yi kafin ya ce"Oh yau tekwando rana za mu yi kenan! To ai na iya irin wannan ba ri ki gani" Kawai sai na ga ya sauko ƙafafunsa ƙasa ya janye bargon sanin halin shi ya sa na yi saurin dawowa dai dai na riƙe masa hannu ya koma ya zauna na zauna a gefen shi na mararaice ina faɗin" Yallaɓai na."   Na faɗa har ina masa fari, ina zan yarda ya yi wasan chinese da ni. Lokacin ina amarya sai ya ce mu yi daga karshe dai na gane ni ce ke shan wuya ya fi ni karfi awasa duk ya naushe ni in na yi shagwaɓa na ce da zafi sai ya ce wai saboda kashina ya yi ƙwari kuma nan gaba ya koya min faɗan kare kai. Daga baya na ce ni wallahi ba na so shi ya sa muka daina amman ina amarya ba wasannin da ba mu sha yi ba. Ko dawowarmu nan gida in ya na da lokaci muna yar gudu ni da shi da yara ranar weekend muna da kayan jugging. Daga baya na daina fita saboda na gaji ban iyawa shi kuma ya ce wai na tara kitse ne shi ya sa. Sai dai ranar da ya so ya na fita tare da jidda da Baby ya na kuma gaya musu motsa jiki na ƙara lafiya a jikin ɗan adam. Yadda na yi masa farin ne da yanayin maganata ya sa ya san akwai abinda na ke so. Cikin mirmishi ya ce" Me kike so ne Sadiya? Domin in za ki cuce ni haka kike yi." Hannuwansa na riƙe cikin nawa na marairaice ina faɗin" Haba Yallaɓai na wani rin cuta kuma? In miji ya taimaki matarsa sai a kira shi cuta?   "Kamar wani taimako kenan?   Ya faɗa ya na mai tsare ni da ido da sauri na marairaice kafin na ce" Yallaɓai na yi shara na yi mopping na wanke Tiolets baya na duk ya kage to kuma  ga  wanke wanke can ba a yi ba."   "To shi me? Wai na je na yi wanke wanken? Ya faɗa yana kallona da sauri na ce" Ni ban ce ba." Sai kuma na saki hannun shi na miƙe ina tafiya daƙyar kafin na ce" Ka tausaya mini Yallaɓai Allah bayana ke ciwo." "Kina da ciwon baya ne ban sani ba? Ban juyo ba na ce" To ni dai ina tunanin tun lokacin haihuwan jidda na goce. Kasan kuma sai a hankali a hankali ya ke tashi." Da iya gaskiya na faɗa domin wani lokacin in na yi aiki bayana sai ya rike amman sai Yallaɓai ya ce" Ba shakka. To sannu." Yanayin mganar na shi ya sa na san bai yarda ba sai na juya ina faɗin" Fisabillahi Yallabai yanzu ka lalace sam ba ka son aiki." Me Yallaɓai zai yi ba dariya ba, ni ko sai na tsaya ina kallon shi da gaske fa haushi ya ke ba ni, ya na gida ace ba zan more shi ba. Sai kawai na tura baki kafin na ce" Ko a da ka fi tausayina ne! Yanzu kuma ka daina tausayina ko?   Ganin yana kallona yana dariya yasa na fara matsan kwallar karya ina faɗin" Ko dai ka daina sona ne Yallabai? Na tsare shi da ido har lokacin fa bai daina dariya ba. Sai kawai na fashe da kukan da ba hawaye ina faɗin" Na shiga uku Yallaɓai na ya daina so na" Ya na dariyan ya ƙariso ya rumgumeni yana faɗin" Mamaki na ke yi da har yanzu ba ki san aikin da nake yi mai muhimmanci a cikin gidan nan ba? Sai na ɗago ina kallon shi kafin na ce" Wani aiki ne? Barci ko?   Sai kawai ya kai hannun shi saman ƙirjina ya na shafawa ina kallon shi na ga ya dage min gira ai da sauri na kwace jikina ina faɗin" Ai daman anan kafi auki ba za ka zo ka tayani aiki ka motsa jikin ka ba." Na faɗa ina tura masa baki. Yana dariya ya ce" Ai abin da nake yi shi ne babban misalin motsa jiki." Sai kawai na jinjina kai kafin na ce" Kuma kana taimakon kanka ba." Sai ya daga hannu saama kafin ya ce" In ji wa? Taimakon kai da kai dai ko? Balla masa harara na yi na kama hanyar fita ina faɗin" Kai dai ka sani." Ina jin sa ya biyo bayana yana faɗin" Ciwon bayan ya warke ne? Sai na tuna da sauri na riƙe kugu na sauya tafiya ina cije baki. Yallaɓai dariya har tana sauti na yi masa banza na fice ina faɗin ai sai ya yi ta kwanciya.   Har na dawo zan cigaba da wanke wanke ya leƙo ya ce na zo na bashi abin karyawa. Dole na koma falo na haɗa masa tea na zuba masa ɗumamen tuwon da na yi jiya da daddare miyan allayu zama na yi sai da ya gama ci muna yi muna hira bayan ya gama na tattara komai zuwa kitchen sai ya biyo ni ya na faɗin" Je ki huta bari na yi " Ina jin haka na daka tsalle na rumgume shi na bashi sumba a baki kafin na ce" Yaron kirki Yallaɓan Sadiya." Kaina ya dankwanfar ya na faɗin" Sai na fasa." Da sauri na ce" Na tuba ranka ya daɗe ka yi mini rai." Yana dariya ina dariya ban kuma iya zuwa na huta ba saman cabinet ɗin kitchen ɗin na haye na zauna yana wankewa ina karba ina jera su a muhallinsu.   Anan ne ma ya ke ce mini yanzu ya girma iyalai sun fara taruwa ba girman shi ba ne a ka ga yana aiki Ni ko sai na buɗe baki na ce" To mi ye a ciki? Ko ƴayan ka sun gan kana aiki ba abin kunya ka yi ba ka na koyi da sunnar ma'aikin mu ne kuma daman da shi muke koyi " "Uhm daɗin baki ko? Ya faɗa ya na kallona da sauri na ce" Haba Yallabai ai tsakanimu ba daɗin baki sai dai gaskiya da gaskiya." Na faɗa ina masa yar dariya sai kawai ya kalleni ya girgiza kai kafin ya ce" To ke ina wani aikin da kike ta zuzutawa? Tun auran mu tare muke aikin nan ban daɗe da daina yi miki girki kina kwance ba." Sai na buɗe baki ina kallon shi, ban rufe ba ya cigaba da faɗin" Kuma hatta renon su Jidda tare muka yi shi to ina aikin da kike ta kira? Sai na rufe bakina na kasa mgana sai da ya yarfa min ruwan wanke wanken da ke hannun shi yana faɗin" kin kasa mgana ne? Sai na kauda kai ina faɗin" To na ga abin ya koma gori ne gwara a bar mganar." Dariya ya yi yana ƙokarin sake mgana na yi saurin cewa" Yallabai yau ba za ka fita ba ne? "Zan fita mana. Zan je office akan mganar aikin nan na kaduna ki yi min addu'an Allah ya sa ta faɗa za mu samu alheri in sha Allahu.'" Da sauri na ce" In alheri ne Allah ya tabbatar in babu Allah ya kawo na alherin." "Amin Amin Abar ƙauna ta." Ya faɗa ya na min wani kallo sai nima na tsume ina masa kallon soyayya. Sai kawai Yallaɓai ya ce a hankali" Ko mu je mu yi ɓarnan ruwa ne mu dawo? Da sauri na ce" A'a. Fita fa za ka yi nima zan je Gwammaja." "To mu haɗa wankan mana ba shikenan ba." "Ba ko shiken nan ba.' Na faɗa ina haran shi, dariya ya fara yi min kafin ya ce" Me ke damun ki ne? Allah kin fara zama raguwa." Ko magana ban yi masa duk irin ƙokarin da nake yi wai na fara zama raguwa. "Na ƙosa ki sami ciki irin na Baby. Ko banza ki yi ta nema na ni kuma da sunan taimako ina shan Shagalina." Kafaɗansa na kaima duka ina faɗin" Ba Amin ba." Shi kuma ya na min dariya har ya na maƙale murya yana tsokanata. "Yallaɓai na. Uhm Uhm.." Kunya ta kamani na saka tafukan hannuna ina rufe fuska shi kuma ya na mini dariya. In na tuna lokacin har kunyar kaina na ke ji abu kamar cin tuwo na maida shi, ba na gajiya ni dai kawai a yi kuma da an gama sai na ji a lokacin nake son abin gaskiya ba zan so na samu ciki irin na Baby ba. Haka dai Yallaɓai ya gama wanke wanke sai na ce ya cika ladanshi ya wanke wajen ya goge mini kitchen ɗin harara ta ya yi ya ce" Shi wannan ɗin ba ni da lada ne ko ba ki gode ba ne? Da sauri na ce" Na gode. Allah ya ƙara girma mai girma Tafidan Rano." Kaina ya shafa ya na faɗin" Rayuwarki ta yi albarka ɗiyar ga." Ni da shi muka saka dariya gabaɗaya. Haka nan ya haƙura ya tayani muka gyara kitchen ɗin muka goge sannan muka koma ɗaki Yallabai  dai sai da ya aikata abin da ya ce wato mu ka haɗa wanka Musbahu na ta kiran shi baƙi sun iso amman shi ya na gida yana shagali.   Tare muka fita bayan mun shirya na rufe gida bayan na ɗaukan ma Baby dogon wando kawai suna da kayan sawa a gidan Nene domin wani lokacin in sun je sun kwana ba duka kayansu suke dawowa da shi ba, ni kuma ba na damuwa saboda irin haka suna wucewa daga makaranta ba ni da haufin kayan da za su sauya. Yallaɓai na sauke ni a Gwammaja ko shiga bai yi ba ya wuce office ya ce mini sai ya dawo A can na samu Hauwa Munnira ce ba ta kariso ba. Gida cike da dangin Maman Farko sannan a bangaren ƴaƴa kuma su Anty Zulaihat da Nasara sune kan gaba su da su Anty Bahijja. Anty Zuwaira kuma da ya ke yar sabga ce ba ta zo ba ƙila sai yamma. Suwaiba, Jamila  da Hindatu duk suna nan  Safiya ma haka Hafsat ce tana Abuja ba ta ƙariso ba matar Muhammad Sani an ce sai Jumma'a za su taho tare da mijin nata. Ummu Salma ma da ke aure a Bauchi da wuri ta zo, na zo ba daɗewa Jawahir ta dawo daga makaranta sun samu hutun sati biyu. A ɗakin Nene na sauka. Tunda nan ne ɗakin Uwar mijina. Ana mganar abincin da za a yi su Anty Bahijja suka ce a yi tuwo da shinkafa sai alale sannan za a yi zoɓo duk da akwai lemuka da ruwa da aka sauke sai Nama da aka ce za a kawo naman sa da na rago za a gyara a soya domin a yi amfani da shi ga baƙi masu zuwa. Sai can bayan azahar sai ga Muninira Halima ma sai bayan la'asar ta zo. Mu surukan gidan muka gyara wake tunda an farke shi ya fara ƙwari bayan mun gama an kawo kayan miya da yawa ni dai daman yar laushi ce su Hauwa na bari da gyaran kayan miya ni dai na gyara albasa Munira na yi min tsiya gyaran albasa kaɗai ne aiki a wajen? Na ce shi ne na ga zan iya. Hauwa dai an yi dama dama cikin gyaran kayan miya ina zan iya. Ba zan yi ba ada dai kam na yi amman ban da yanzu. Sai wajen tara na dare Yallaɓai ya zo muka koma gida washegari ma Alhamis mun koma ranar nama aka gyara aka soya sai kum an tafasa kayan miyan da aka nuƙo. A ranar baƙin Rano suka iso har da Gimbiya a ciki ban ɗauka ma za ta zo bikin ba amman sai na ji ana mganar har da cuku cukun transfer ɗinta ya kawo ta bikin. Sai can da mangariba ne ma muka haɗu muka gaisa. Baby dai ta kawo mini chaculate ta ce Anty Gimbiya ta ba ta, ba tun yau ba tana son su Jidda ba kyauttukan da ba ta yi musu tun tana gida ko bayan auranta da suka je honeymoon da mijinta Paris ta siyo musu kaya masu kyau da yarari. Can da dare ma tare na ganta da su Jidda da yaran Naja'atu. Sai ranar jumma'a Ango ya iso gida. Sai ihun ango ƴan uwa ke yi masa yana kamewa kusan Soja da tsare gida a ranar ma Tariq ya zo shi da Faridarsa. Muhammad Sani da Nafisa tun da safe suka iso shi Jafar ma da matar shi Nauwara ma sun iso ranar duk da Kaduna za a ɗaura auran amma dai ya zo gida shima. zuwa kuma yamma komai an kammale shi. Za a yi waina amma an ba da ne a yi sai dai Tuwon da miyan anan gidan za a yi shi kuma Alalen Anty Bahijja ta ce namu ne mu surukai mu za mu yi tsakani ga Allah ta na son ɗora mana wahala. Hauwa da Muniira na bar ma jagoracin su da ya ke a nan gidan suka kwana ni kuma gidana na koma na kwana na ce musu in sun ga ban zo da wuri ba kar su jira ni su fara aikin daman sun san halina ba da wurin zan zo ba. Jidda nan ta kwana tare da yara sa'aninta ita kuma baby ta na tare da Gimbiya Yallaɓai ke faɗa mini ta kira shi a waya ta faɗa masa ta tafi da Baby gidan Naja acan za ta kwana. Da safe sai da na sha barcina na gajiya. Yallaɓai ma a gida ya barni na dai shirya shi cikin wata dakakkiyar shadda mai ruwan ƙasa har da babban riga hula da takalminsa bakaƙe haka ma agogon fatan dake hannun shi na fesa masa turare na bishi da Allah ya kiyaye ba da motarsa ya je ba shi. Da shi da Tariq motar Uncle Abba za su bi zuwa Kaduna. Motar shi kuma Muttaƙƙa zai tukata zuwa Kadunan shima ɗaurin aure 11 ne na safe tun takwas suka ɗau hanya. Ni ina gida ma sai wajen goma da rabi na fita. Rahila ta kira ni ta ce za ta zo na ce sai ta zo domin ni ban gayyaci kowa ba Yaya Balki ma da ta yi mini mganar muna da biki ba gayya na ce ni ban yi gayya ba. Sai dai in sun zo domin Allah Gwaggo daman ta ce sai bayan biki za ta je Allah ya sanya alheri. Ma'u daman na san za ta zo balle Uwar ɗakin nata ne yan gaba gaba. Ko da na je su Hauwa sun gama alale Munnira na ta harara ta na ce su yi haƙuri na tsaya shirya Yallaɓai ne. "Au to me Yallaɓai? Mu ma ai muna da mazajen da za mu shirya amman ba mu je ba sai ke mai Yallaɓai a 'a yallaɓiya" Munira ta faɗa ta na mai ƙara ɓalla minibharara. Ina dariya na ce" To ai ban hanaku ba. Da kun tafi kuma" Hauwa ta ce" Mu tafi Anty Bahijja ta tsire mu ko? Daman da ba ki zo ba ta ce Munirra ta ɗau girman tun da ke ba ki daraja girman da Allah ya ba ki." Ina dariya na ce" Ran Munirra ya daɗe. Zan zama mai yi miki biyayya." Kafaɗata ta daka tana dariya. Hauwa ke faɗa mini Nafisa ba ta da lafiya ta na ta amai ba ta yin komai ba na ce yanzu haka ciki gare ta. Nauwara kuwa gidansu ta gudu har na zo ba ta dawo ba.   Shashen Marigayi Hajiya Karima muka gyara muka zauna tunda sauran duk ya na cike da jama'a Shashen Nene duk mutanen Rano ne Hajiyar Tafida ma da safe ta iso. Ni daman na yi wanka na a gida Jidda na nema na bata kayan da za ta saka da takalmi da mayafi saura na Baby ne an ce ba su dawo ba. Faridan Tariq kuma suna da ƴan uwa acikin gari can ta je ta kwana bayan ta dawo itama muna tare. Sameena ma sai a ranar ta so ashe ba ta nan ta je can Niger wajen dangin mijinta duk muna tare da su anan ɗakin.   Karfe sha ɗaya da mintina goma Nasir ya kira Munnira ya ce an ɗaura aure acan ma cikin gida an kira su Anty Bahijja sai suka fara guɗa suna ta iface ifacen murna. Sai wajen sha biyu muka sake wanka muka saka ankom mu. Ni na yi kitso amman ban yi ƙunshi ba saboda wacce ke yi min kunshi ta yi tafiya kuma wacce ta yi ma su Hauwa na ga kunshinta bai yi min ba sai ban yi ba. Mu aka bari da wahalan raba abinci shi dai na yi saboda Mimisco ce ta kirani da kanta ta yi mini mgana shi ya sa na yi abin da ta ce. Kafin bayan azahar kowa ka gani ya ci kwalliya sannan wasu sun ci sun sha ko na ce ana kan cin da sha ɗin. Sai a lokacin su Baby suka dawo an saka mata wani leshi mai duwatsu dogowar riga sai da na natsu na fahinci anko ne irin shi ne a jikin Gimbiya da Naja'atu da ƴayanta sun kuma saka musu ƙananun hijabi a saman kansu har takalmin su baki mai igiya iri ɗaya ne.  Baby na ta murna ta nuna mini na ce kaya sun yi kyau na kuma yi ma Gimbiyar godiya ta na mirmishi ta ce mini bakomai.   A she ban sani ba har da Jidda sai can wajajen La'aaar na ga Jidda ta sauya atamfa ta saka kayan itama tana murna ta ce mini Anty Gimbiya ta yi mata na ce ta gode.   Rahila da Yaya Balki ne suka zo min biki domin ba zan saka Ma'u da ƙawarta a lissafina ba. Ni fa ban ma san ta zo ba sai da Yaya Balki ta ce kafin su fito sun yi waya ta ce musu ta na gidan tun ɗazu na ce ni kam ban san ta zo ba sai da suka ci abinci na raka su ɗakin Maman Farko suka yi mata Allah ya sanya alheri daganan muka shiga ɗakin Nene nan na ga abin mamaki Ma'u da ƙawarta shema'u filet ɗin abincin su cike da kaji da nama sannan suna tare da su Gimbiya da Anty Bahijja ana ta hira ana shewa.   Tana ganin mu ta tsargu ni ko da gangan na kalleta kafin na ce" Su Ma'u manya maso bare kiƙi dangi. Kin zo amman ba ki iya nema na ba? Sai ta fara kame kamen ta nemi ni ba ta ganni ba sai tana taɓe baki kafin na ce" Muna shashen su Jawahir tare da su Hauwa." Nan dai muka gaisa ni dai na kai su ciki su ka gaida Nene da Hajiyar Tafida bayan mun fito na ga sun tsaya suna mgana da Ma'u da shirina na yi tafiya ta. Allah ya so mu ma Mimisco ta ce mu ɗiba komai saboda namu baƙin kuma daman ina nemanta saboda ba a diɓar mana na mazajen mu ba, mun yi waya da Yallaɓai duk da sun yi reception a can akwai bukatar mu ijiye musu abinci.   Anty Maimuna na tare da baƙin ta dangin mijinta. Sulaihat na gani na ce ina Mimisco sai ta ce mini tana bangaren Hajiya iya sai na kalli Anty Bahijja ina faɗin. " Anty Bahijja muna bukatar nama sannan da waina." Kai tsaye ta ce" Duk wanda aka ba ku fa? Nima kai tsayen na ce" To na mutane ne wannan, shi wannan da na ke magana na mazajen mu ne da suka tafi ɗaurin aure ne na yi ma Mimisco ma mgana." Sai gabaɗaya suka kalleni har da Gimbiya. Sai Anty Bahijja ta riƙe baki tana faɗin" To ma su miji. Mu namu mazajen da suka tafi fa? Ba su da rai ne ? Ina dariya na ce" Kowa na shi ya sani Anty Bahijja. Ba zan hanaki ki ijiye ma Baban Sulaihat ba. Amma ni kam sai na ijiye ma Yallaɓai duk abin da na ci." Naja'atu ta buga guɗa kafin ta ce" Kin burgeni Anty Sadiya. Shi ya sa Kawu dai ya fara ajiyan tumbi." Ina mata dariya na ce" Ai na iya kiwo ne." Ta ce kwarai kam. Sai aka maida mganar dariya Anty Bahijja ta miƙe ta na faɗin. "Muje mai Yallabai." Ta faɗa tana riƙo hannuna sai aka kara saka dariya ni ko sai na rike ta muka fita daga falon muna tafe tana ce mini wai shi Yallaɓan nan ba zai ci abinci acan ba ne? Na marairai ce na ce zai ci amman akwai tafiya kar ya dawo ya na jin yunwa. A can shashen Hajiya iya muka je ta diɓar min waina da naman na je na kawo kula ta saka mini tana ta min tsiya Mimisco ta kare min da cewa abin da na yi mai kyau ne mata da dama in ana sha'ani sai su manta da mazajen su.   Ni dai na wuce na barsu ina zuwa na ce su Hauwa sun ci sun ƙoshi suna sakin tusa sun manta da mazajensu to ni na yunƙura na samo ma mazajen namu abinci sai suka fara min dariya nace su gode minibko na fasa ba su Munnira ne wajen gaba gaban gode mini.  Su Rahila da wuri suka tafi kafin mangariba Ma'u kam tana gidan tawagan masu ɗaurin aure da amarya suka dawo. A shashen Hajiya Iya aka safki amarya da tawaganta. Ana yin mamgariba na kira Yallaɓai na tambaye shi ko yana ina? Ya ce min suna cikin gida a ɗakin Musbahu da kaina na yi lulluɓi na kai masa abinci da ruwa da lemu na san daman shi da Tariq da Uncle Abba ne nama daman da yawa na diɓar musu sauran na bar ma su Munirra domin na ga su ba su damu da cikin mazajen su ba. Yallaɓai sai da ya rumgumeni ya ba ni sumbata a baki kafin ya ce" Allah ga baiwarr ka nan Halima Allah ka jiɓanci lamuranta kamar yadda take jiblɓanta nawa." Daman sun ce yunwa suke ji.  Suna ma shirin tashi su fita su je su ci abinci a cikin gari ne sai ga ni, Tariq dai ba baka sai kunni ya fara cin nama Uncle Abba kuma sai ya kalleni kafin ya ce" Sadiya na ce wai ba ki da yar ƙanwa ne a gida? Gabaɗaya suka saka masa dariya nima sai da na dara kafin na ce" Babu Uncle Abba kana so ne sai a duba maka a dangi? Sai ya ɗau naman kaza ya saka a baki yana tauna kafin ya ce" Ina tunanin haka na gaji da wulaƙancin da yaran nan suke yi mini. Yusuf a gabana bai ji kunyar kama mace ba ina kawun sa."   Yallaɓai na cin waina ya ce" Ba fa Mace ba. Matata na kama. Kawu kuma ai ban hana shi aure ba ko?. In ka ji haushi gobe a ɗaura ko Tariq? Ya faɗa ya na kallonshi Tariq ya gyaɗa kai sannan ya ɗaga hannu Abba ya zungure shi da ƙafa yana faɗin" Shege sarkin cin abinci."   Ni dai gajiya na yi na fita na bar su domin ba za su fasa ba sai dai idan ba su haɗu ba. Farida dai na faɗa mata ba ta damuwa Tariq na tare da Yallaɓai. Su kuma su Hauwa suka ce wai na yi musu wayau na kwashe tsokoki na bar ma mazajensu kashi ina dariya na ce" To wai na hana ku diɓar musu ne da farko? Bana son son zuciya fa. Ku dai cigaba da zama."   Ranar ma ban kwana ba gida na koma amman tare da Farida da Sameena su Munnira ma gida za ta koma ta kwanta Hauwa ce na ga tana shirin ƙara kwana na ce ta je gida ta kula da mijinta tun da ban ga abin da za ta yi ba in ta kwanan Uncle Abba da Tariq Rano suka koma suka kwana Yallaɓai kan gida ya dawo su Farida a ɗakin su Jidda na sauke su da safe bayan mun karya mun yi wanka muka koma Gwammaja. Sai a ranar muka shiga muka ga Amarya. Doguwa ce baka mai jiki. A shashen da muka zauna ajiya yau ma nan muka zauna da farko ba mu yi niyyar zuwa gidan su Anty Zabba ba sai da ta kira Munnira ta ce tun da mun zama yan amarya ta yafe mu shi ne yasa muka shirya bayan azahar muka tafi can anguwarsu ta Rijiyar zaƙi.   Da muka ce ga in da zamu a gidan kafin mu tafi, sai da Anty Bahijja ta yi ƙorafin ne zai kai mu? Ita da Anty Zulaihat wai ai da gangan ta ki sauka anan a yi biki gabaɗaya Mimisco ta kashe bakin su da cewa" Ku bar su je yana da kyau haka a matsayin su na surukan gidan nan" Dole suka yi shuru.  Mun je ma Anty Zabba biki da muka je har tana cewa ta yi fushi nima ta ce ko waya ban kira ba na bata hakuri. Anty Zabba har ta ɗan rame amman kuma ta yi gayunta tsab da ita itama ta yi taro gidansu cike da mutane yaran nata sai a ranar da za mu taho suka biyo mu zuwa gidan kakaninsu a daran kuma aka zagaya da amarya duka ɗakunan gida mu ma aka tara mu aka yi mata bayanimmu ɗaya bayan ɗaya.   Washegari litini da wuri Ango ya ɗau amaryansa da Rakiyan ƙannensa mata su Anty Nasara suka raka su gidan su Anty Zabba suka haɗa su suka yi musu nasiha daga nan sai filin jirgi suka ɗaga sai garin fatacol sai fatan Allah ya ba su zaman lafiya ya kaɗe fitina.   Shikenan gida ya watse baƙi da nesa da na kusa zuwa talata duk sun koma gidajensu Gimbiya dai ta na nan amman na ji Hauwa na faɗin daga nan Abuja za ta wuce an kira su kan mganar rabon gado. Mganar aikin ta kuma Yallaɓai ya faɗa mini an dawo da ita nan office ɗin NGO da ke reshen Jihar kano. Amman sai ta dawo daga Abuja za ta fara zuwa aikin. A lokacin da ya ke gaya minibsai da na tambaye shi. "A wajen Nene za ta zauna kenan? Sai ya gyaɗa min kai har yana ce min" Nene ma ta karɓe ta. Ta ce sai kuma aure zai raba su." "Uhm!   Kawai na ce a lokacin amman ban iya sake mgana ba. Sai bayan bikin Yaya Usman na samu damar yi ma Yallaɓai tuni kan Anniversery ɗin mu ya ce wallahi ya manta gwara da na tuna mishi. To shima zai ba ni kyakyawan surpise a lokacin in sha Allahu ina ta murna ina cewa ko Hajji za ka biya mini? Ya ce Allah ya sa haka. ****** Bayan wata ɗaya da bikin Yaya Usman. Kuma a yanzu dai muna cikin watan ramadan ne har mun yi azumi takwas. Da azumi ya gabato Yallaɓai bashi da kuɗi a hannu ya samu kwangilan aikin nan na kaduna akwai kuɗin shi da ya saka a ciki, to kuma ya saba duk shekara ana yi masa kunin sadaka Maman Saude sannan yana rabama yaran dake ƙarkashin sa kuɗi ko kayan abinci.   Wannan karon ma da bai da kuɗi kayan abinci mu a ciki ya ce. A ɗibar ma Mutakka da gidan su Saude. Yaran shi na Office kuma kuɗi ya ba su, sannan gidanmu kuma 30k ya ba ni na kai musu da ƙwai da yawa da dankalin turawa wanda Uncle Abba ya kawo mana an cire ƙwai a gidan gonan shi Dankalin ma shi ya kawo mana buhu a ciki na dibar ma gidanmu da Muttaƙa. Nene ma Uncle Abba ya kawo mata kwai da kayan gona muma ma mun shaida su kwaiba da mangaro har muna kyauta. Muttaƙa ma Hauwa ta ce ya samu alheri tunda shi kaɗai ne bai kai su karfi ba. Geron da Mijin Mimisco ya raba ma su Yallabai a ciki ya ce na diɓar ma su Gwaggo sauran kuma a ka kaima Balaraba na kunun Sadaka. Duk da daman a gidanmu ba mu da matsala komai akwai Yaya Hamza da Yaya Auwalu da suke da ƙarfi sun wadata su da komai, sai dai ihsani da kyauttawa namu amatsayin su na iyayenmu. Mijin Amina ma ya aiko da kuɗi sauran alherin da aka samu ta bangaren su Yaya Balki an tura shi can Yashe wajen su Baba Sani. Ko Mijin Ma'u mota guda ya kawo na kayan abinci Baaba ai tana cikin alheri shi ya sa Yaya Aina ta ce a can kura Baaba ce yar gaban goshi to tana da ƴa tana auren mai kuɗi kuma ana aika musu da alheri. Ni Rahila ke faɗa,mini har dangin Babanta da azumin nan ta kai musu alheri. Gimbiya ta dawo wajen Nene da zama saboda aikinta. Sun je Abuja tare da ƙanin mahaifinta Tafidan Rano an raba gadon dukiya ta samu gida biyi anan Abuja da kuɗi masu yawa na tumanin takaba  dukkansu huɗun rabon su kenan. Su gwara su da ƴaya ita bayan tumin takaba ba ta samu komai ba. Yallabai na ji suna waya kan tana son a saida gida guda ɗaya a siya mata a fili anan kano kuɗin ta kuma Mota ta ke son siya. Da ya ke komai sai ta yi shawara da shi abin da ya ce kar a yi ta bar shi kenan wanda ya ce a yi kuma shi take yi. Ta ɗan yi facaka da ƙudin bayan Mota ta siya manyan suturu da gwala gwalai, har su Jidda ta siya ma Takalma da dogayen riguna daga Dubai oder ma ta yi, sai yan uwa suka yi mata faɗa suka ce ta fara tunanin kasuwancin da za ta fara tunda kuɗin gado kamar ruwa su ke za su ƙare ba tare da ta yi komai da su ba. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* https://chat.whatsapp.com/FAtGNQc8Y8pB008TuxFJVo Eaman ScholarSphere. Where ideas Take Shape. WHAT WE DO. ASSIGNMENT PRESENTATIONS. ARTICLES PROJECTS. BOOK AND MANY MORE. CANTACT US THROUGH. 02347067793152 MOTTO: "Pathways of Knowlodge Academy, Nurturing minds, illuminating Futures" *🅿️18* Azumi ya raba tsakiya, mun gama goma na marmari mun shiga goma na wuya kamar yadda hausawa ke faɗi. Yau in muka kai azumi mun kai sha biyar kenan, a duka shekarun da muka kwashe da aure ni da Yallaɓai na saba duk watan ramadana Yallaɓai ba ya kaiwa dare a waje a gida ya ke yin buɗe baki tare damu haka ya sabar mana kuma nima haka na saba.   Amma wannan azumin sai al'amarin ya ɗan sauya. Saboda ya samu kwangila gina ma'aikatan nan na kaduna gabaɗaya ma'aikatan shi suna can kaduna shima yana zuwa har ya kwana ma kafin ya dawo sai ya zama na in baya gari sai dai mu yi buɗe baki tare da yara. Ranar da muka kai azumi na sha uku ya dawo daga Kaduna na yi masa har kunin tsamiya da ya ke matuƙar so, amman bai shigo gidan ba sai wajen tara na dare. Na kira shi a waya na ji ko bai dawo daga kadunan ba ne? Sai ya ce mini ya dawo ya na Gwammaja da ya faɗa mini haka har a cikin raina ban yi zargin wani abu ba, sai da ya dawo na kawo masa abin buɗe baki bai ci abinci ba,kunin ma kaɗan ya sha ya ce mini cikin shi ya cika a lokacin sai da na yi mamaki sanin Yallaɓai ba ya iya cin komai a waje sai ya dawo gida barin ma da azumi saboda ya san ina gida na shirya masa abin buɗe baki kamar yadda na saba. "Ka ci wani abu ne a can Gwammaja? Tambayar da na yi masa a lokacin kenan. Shi kuma kai tsaye ya ce mini Nene ce ta matsa masa sai da ya tsaya ya yi buɗe baki. Na ɗan yi mamaki saboda hakan bai taɓa faruwa ba ai Nene ta san ya na da mata me ya sa za ta ce sai ya yi buɗe baki a wajenta? Amma sai wata zuciya ta kitsa min kyakyawan Niyya cewa ita ɗin uwa ce a gare shi ta na da wannan damar kuma abu na rana ɗaya. Sai ko a fuska ban nuna masa damuwata ba na basar da komai ya wuce sannan ya faran tamin rai da ya ce da Asuba na ɗumama masa kuninshi ya na so ya yi sahur da shi.   Haka ko aka yi da asuba bai ci komai ba kunin na ɗumama masa ya sha da buredi ni kuma da yara muka sha tea sai na soya mana ƙwai muka haɗa da shi. Ranar kuma da wuri ya dawo gida muka yi buɗe baki tare ana kiran sallar isha'i ya yi alwala ya tafi masallaci bai dawo ba sai da ya tsaya ya yi sallar tarawihi kamar yadda ya saba ni kuma ni da yara daman muke yin namu a gida. Sannan da rana kuma da ba na komai sai na yi ta karatun Qur'ani tunda duk watan Ramadan in ya zagayo sai na yi sauka kamar yadda na saba. ***** Saude tana zuwa da safe ta yi min yan aikace aikace sannan ta ɗan rage mini aikin yamma tunda kafin la'asar ta ke komawa gida sauran aikin kuma ni na ke yi Jidda na kama min ɗan abin da ba a rasa ba. Yau alale na yi mana mai kifi da ƙwai sai na yi mana zoɓo, Yallaɓai ya aiko da kayan ciki sai na yi ferfesu shi kuma sai na dafa masa ruwan tea da ya ji kayan ganyen shayi na citta saboda ya na so duk dare Yallaɓai zai sha kafin ya kwanta.  Muna da kayan marmari sai na ce Jidda ta raba biyu sauran kuma su yi fruit salat ni da Yallaɓai kuma sai na yayyaka mana tunda shi ya fi son cin su a haka. Bayan mun gama haɗa komai na bar ma Jidda gyara Kitchen ɗin amma bayan na haɗa duka kayan buɗe baki a falon su Jidda in da muke zama gabaɗayan mu a saman cafet mu yi buɗe bakin tare. Wanka na je na yi, saboda na gaji kuma yau ɗin nan ina ɗan jin azumin nan kaɗan ina fitowa wanka ana kiran salla daman ina da Dabino a ɗaki na yi buɗe baki Jidda ma na san ta yi na ta Baby dai daman azuminta rabi da rabi ne in ta ɗauka da ta yi rabi sai ta fara kukan yunwa Babanta kuma ya ce ta ci abincinta da cewa ta yi rabi gobe ma in ta yi rabi ɗaya kenan. Sai da na saka wata doguwar rigata na Atamfa sannan na ta da salla daman na ɗauro alwala ina cikin sallar na ji ana kiran wayata sai da na idar na jawo na duba sai na ga Amina ce sai da na shafa salatin da fara sannan na kira ta daga baya.   Mun gaisa ne ta yi mini barka da shan ruwa. Mu ɗan tambayi lafiyan juna kafin mu yi sallama Amina akwai ƙokari tunda aka shiga watan Ramadan duk bayan kwana biyu sai ta kirani ta yi mini barka da shan ruwa ita da Rahila suna da wannan ƙoƙarin a gidanmu.  Ni ma dai farkon watan na kira duka yan gidanmu na yi musu barka da shigowa watan Ramadana wata mai albarka har Ma'u sai da na kira ban wareta ba wannan karon sannan Alhajinmu ma mun yi waya dashi sau uku kenan shi da Gwaggo saboda tun ranar da muka kai azumi na uku da na je gidan kai musu saƙon Yallaɓai ban ƙara komawa ba washegari kuma na je Gwammaja na gaishe da Nene tun daga kuma ranar ne  ban ƙara fita ba.   Wayar ta ɗan dauke min hankali na buɗe data ina ganin masu turamin saƙon Happy iftar group ɗin Gidanmu na shiga na ga Ya Abubakar ya turo addu'a daman shi ke da wannan ƙoƙarin Ya Hamza ya yi tagging ya ce Allah ya ba da lada. Sai ni ma na yi Tagging na ce Amin tare de cewa fatan mun sha ruwa lafiya? duk ba sa kusa da wayarsu tun da  an sha ruwa ana can ana hada hadar buɗe baki sai nima na fita daga nan na ɗan duba saƙonnin private sai na ga Munnira ta yi min mgana da cewa Matar Yallaɓai sai na tura mata da amsa da cewa matar ƙanin Yallaɓai sannan na saka mata emojin dariya na fita. Datar na kashe na ijiye wayar saman gado sannan na cire hijabin jikina na ninke ina mamakin me ya tsaida Yallaɓai har yanzu  bai dawo ba? Tunda Office ya je bai ma fita da wuri ba sai bayan da a ka yi sallar azahar.   Falo na fita dai dai Jidda ma ta fito da Hijabinta alamun ta idar da sallah ne. "Barka da shan ruwa Umma." Ina kallonta na ce" Yauwa barkan mu dai Jiddan Umma. Ina Baby? Sai ta ce min ta na ciki ta na sallah, ganin ta juya za ta koma ɗaki ya sa na ce" Taho ki yi buɗe baki mana Jidda.' Cikin mamaki a fuskarta ta ce" Umma Abba bai dawo ba? Kai na kaɗa kafin na ce" Yana hanya in sha Allahu. Taho ko kunin ki zuba ki sha cikin ki ya warware." Sai ta amsa da toh hijabin jikinta ta cire ta zauna nima sai na zauna ta zuba mini kunun na ce kaɗan itama sai ta zuba nata sai ga Baby ta fito jikina ta faɗa tana faɗin" Umma azumi na goma.' Ina dariya na ce" Lalle Baby mai himma ce kai kai har azumin ki ya kai goma? Ta na washe baki ta ce" Umma ke guda nawa kika yi? Ina kallonta na ce" Ai muna tare da ke nima azumina goma." "Yaa Jidda fa? Ta faɗa tana kallonta ina dariya na ce" itama dai dai da naki." Sai ta miƙe ta na tsallen murna Jidda ta kalleta amma dai ba ta yi mgana ba saboda ba ta da hayaniya sosai. Har muka gama shan kunu ba Yallaɓai ba dalilin shi Baby sai cewa ta ke yi Umma ina Abba? Sai na tashi na shiga ciki na ɗauko wayata na kira shi bai ma ɗauka ba a lokacin sai da na ƙara kira sannan ya ɗaga wayar na ji hayaniya a in da yake amma ba sosai ba. "Yallaɓai na barka da shan ruwa." "Barka da shan ruwa Sadiya ta." Shima ya maida min martani. Mirmishi na yi mai sauti kafin na ce" Kana ina ne? Na ga an sha ruwa ba ka dawo gida ba." Sai kawai ya ce" Ina nan zuwa na ɗan shiga Gwammaja ne duba Nene Daughter ta kirani ta ce da zazzaɓi ta yi ni" Cikin jimami na ce" Ayya. Allah ya ba ta lafiya ka gaishe ta." Ya amsa mini da Amin sai kawai ya ce mu yi buɗe bakin mu kar mu jira shi in ya dawo sai shi ya yi na shi ban kawo komai ba na yi fatan Allah ya ƙara sauki mu ka yi sallama. Tare da yara muka yi buɗe baki ba mu ci abinci ba kawai kayan marmari muka sha sai ferfesu. Sai da muka yi sallar isha'i da tarawehi sannan muka ci abinci ni alale ɗaya na ci ma na ji cikina ya cika Jidda ta gaji da wuri ta kwanta Baby ne ma ta ɗan daɗe ba ta yi barci ba tana kallon cartoon sai da na kora ta na ce ta je ta kwanta saboda makaranta. Duk da ma yanzu 12pm suke tashi saboda azumi. Tun ina saran dawowar Yallaɓai da wuri har na fidda rai sai na fara tunanin ko Jikin Nenen ne ya yi tsanani har sake kiran shi na yi ban same shi ba duk na damu. Ina ta tunanin Allah ya sa ba jikin Nenen ya yi tsanani ba ne kamar zan kira Gimbiya sai na fasa tunda ni dai ba waya muke yi ba sai wani abu na jaje ko barka ni ba ma zan iya tuna last muka yi waya da ita ba gaskiya amma ina da lambarta kuma nima na san ta na da nawa tunda muna ganin status ɗin juna.   Har na fara gyangyaɗi na ji ƙaran buɗe get sannan da shigowar motar Yallaɓai sannan na mike ina duba agogon wayata goma da rabi har ta gota sha ɗaya saura na dare. Ajiyar zuciya na sauke na fita zuwa falon farko dai dai ya buɗe kofar falon ya shigo muka ci karo da juna ni da shi.   "Ya jikin Nenen? Da haka na tare shi domin a zato na jikin nata ne ya yi tsanani ya sa bai shigo gida da wuri ba. Lumshe idanuwansa ya yi daga gani a gajiye ya ke saboda ya na ƙarosowa gabana ya rumgumeni yana mai sauke ajiyar zuciya nima sai na rumgumeshi ta baya ina faɗin" Nenen na lafiya ko? Cikin muryan gajiya ya ce" Lafiya lau. Na gaji Sadiya ta ko'ina na jikina ciwo ya ke yi min." Ko bai faɗa ba na ga hakan a muryan shi da yanayin shi sai kawai na ce mu je na haɗa masa ruwan wanka ya yi wanka sai ya ji daɗin jikin shi. Muna riƙe da hannun juna har bedroom ɗim mu ina tambayan shi ya jikin Nene ya ce min da sauƙi likita ya zo gida ya dubata.  Maleria ce ta kamata cikin tausayinta na ce" Allah sarki. Allah ya ba ta lafiya. Amma dai ta ijiye azumin ko? Sai da ya gyaɗa min kafin ya ce" Yau ɗin ma ta ɗauka da jikin ya zafi sai ta ajiye"   Ina taya shi tuɓe kayan jikinsa ya ke tambayata su Jidda na ce sun kwanta. Kai ya kaɗa kafin ya ce" Na yo ma Baby tsaraba ya na mota na manta dashi." Ban maida masa martanin mganar shi na tura shi zuwa kofa ina faɗin" Ka yo wanka." Domin ni kaina na gaji barci na ke ji idanuwana har rufewa suke yi amma ban kwanta ba sai da na kwashe kayan da ya cire na zuba cikin kwandon kayan wanki na fito masa da wasu riga da wando masu taushi na barci. Lokacin da ya fito har na fara gangyaɗi sai da ya yarfamin ruwan hannunsa sannan na farka. "Ki kwanta mana. Kina barci a zaune? Ya faɗa ya na nufar gaban madubin ɗakin. Sai da na yi Hamma sannan na ce" Zan baka abinci ne shi ya sa ban kwanta ba." Bai juyo ba amma ya ɗau mai ya na ɗan shafawa ya ce" Yi kwanciyarki kawai na yi buɗe baki a gidan Nene amma zan duba na gani ko zan iya cin wani abu kafin na kwanta."   Ban damu ba na ce to sai kawai na kwanta ina jin sa ya na faɗin" Haka za ki kwaanta? Tsabar barci umh kawai na ce masa. Daga nan ban san yadda aka ƙare ba sai dai can ina jin sa ya na cire mini rigan jikina ina ta masa magagi sai da asuba da muka tashi sahur ne na fahimci rigar barci ya sakamin kuma wani ikon Allah duk gajiya da zan ji da mugun barcina ta bakin Yallaɓai huɗu na yi na asuba na ke tashi wani lokacin ma kafin huɗun na tashi Yallaɓai ne sai na yi ta fama dashi kafin ya ta shi har mamaki na ke yi ina faɗin haka maza suke? Ni dai Yallaɓai sai na yi da gaske ya ke iya tashi Sahur in na tashe sa tun lokacin da na tashi sai ya koma barci da cewa in na gama haɗa abin buɗe bakin sai ya tashi, to fa in na gama sai na haɗa da jan hannun shi ya ke iya tashi in kuma zan kyaleshi sai an fara kiran salla zai tashi lokacin an gama ma Sahur ɗin.   Kamar haka ne yau ma uku da rabi na farka barcin da gajiya duk sun sake ni na ganni na nannaɗe jikin Yallaɓai duk na yaɓa masa kafa. Sai da na yi mirmishi bayan na sauko daga kan gado na gyara masa bargo sannan na fita zuwa tiolet na ɗauro alwala na zo na shimfiɗa darduma na yi salla raka'a biyu na ɗan zauna na yi addu'o'ina sannan na miƙe na cire hijabin na nannaɗe tare da darduma na mayar  ajiyar su ban ta da Yallaɓai ba sai na buɗe kofar bedroom ɗin na fita na bi ta cikin kitchen sai na ga Yallaɓai ya kwaso kololin da na bari a falo zuwa kitchen sai na bubbuɗe na gani bai ci alelen ba amma dai ya sha zoɓo kuma ya sha kayan marmari, ban damu ba tunda Baby ba ta azumi sannan nima zan ci alalen tunda jiya ban ci ba.   Gas na kunna na ɗora ruwan tea kawai. Muna da sauran buredi tunda jiya ya shigo da shi. Bayan na juye a fulas sai na ɗumama alalen sannan na soya ƙwai saboda Jidda da Babanta  sai da na gama komai na kai falo sannan na shiga ɗakin su Jidda na tashe ta, ina tashin ta Baby na ji ta yi zaraf ta miƙe tana faɗin" Umma nima zan yi azumin." Kai tssye na ce" To ku wanke baki ku fito mu yi sahur."   Daga nan na fice tiolet  na shiga na yi brush ina fitowa hannuna da danshin ruwa na lallaɓa domin na shafa ma Yallaɓai ruwa a fuska saboda ya tashi sai dai ina zuwa dai dai saitin kan shi wayarsa ta kawo haske alamun ana kira ban saka hannu ba sai na leƙa sai na ga Daughter na kira. Mamaki ya kamani me ya sa ta ke kiran shi yanzu? Sai wata zuciyar ta ce min ko dai jikin Nene ne?   Tunanin haka ya sa sai na yi niyyar amsa kiran sai na saka hannu na ɗauki wayar na buɗe bayan wayar ta yanke. Tunda na san password ɗin wayarsa ina shirin kiranta ne kawai sai ga saƙon ta ya shigo wayar har ga Allah ba halina ba ne duba wayar miji duk da wayar Yallaɓai ba ta da shamaki a wajena ban taɓa tunanin bin diddiginsa ba. Kuma har ga Allah lokacin da saƙon ya shigo hannuna ne ya faɗa kan saƙo sai ya buɗe kuma ban isa a lokacin na hana idanuwana karanta abin da ta rubuta ba.   "Daddy na a tashi a yi sahur. Ko duk santin girkin nawa ne yasa ka kasa tashi? Na ga tuƙwaici na gode. Amma ka yi min laifi domin na ce ba zan karɓa ba yanzu haka ma za su dawo wajenka domin zan siya ma ƴaƴana kayan kwalliyar salla da su. Thank you so much for been their for me Daddy."   Na yi ƙoƙarin bayan na gama karanta wannan na fita amma sai zuciya ta rinjaye ni na srolling sama ina ganin saƙonnin da ta ke tura masa. Tun da aka fara azumi  ta ke tura masa saƙo da asuba a tashi a yi sahur sannan sai ta tura masa sakon barka da shan ruwa wani lokacin ya ba ta amsa wani lokacin ya yi shuru. Na duba saƙonin har wanda ta na Abuja lokacin da mijinta ya rasu. Wani saƙo da ya ba ni mamaki ya sa na ji kirjina sai da ya buga dam! Shine ta tura masa" Na yi kewarka Daddy yaushe za ka zo? Shi kuma sai ya ba ta amsa da Gobe in sha Allahu.   Kirjina ne na ji ya fara suya, har ina ganin duhu duhu da ya sa ban ƙara gaba ba na ijiye masa wayar a nan saman side drower ɗin da ya ke kwance. Kallonsa na ke yi ina mamakin Yallaɓai ashe shima ya iya munafuncin maza? Ashe jiya ba Nene ba ce ta tsaida shi ba ashe Gimbiya ce ta tsaida shi, bayan ta yi masa girki ya ci har ya na santi daga karshe har ya na ba ta tuƙwaici ni kuma ko oho. Wani ƙululin abu ya tokaremin a kirji da wani haushin Yallaɓai don Allah menene na ƙarya tsakani ga Allah? Sai kawai na juya da na so na fita ne ba zan tashe shi ba sai dai yau ya yi ɗaure amma sai na danne zuciyata da na yi wani tunani sai kawai na dawo na fara buga gefen gadon yau ko sunan shi ban kira ba. Sannan ban taɓa shi kamar yadda na saba ba. Bai da wani nauyin barci sai gashi ya buɗe idanuwansa da suka yi nauyi yana kallona sai kawai na juya ina faɗin. "Ka tashi lokacin Sahur ya yi."   Da ga haka na yi ficewata na bar shi a raina kuma na kudiri niyyar ko bai tashi ba na gama tashin shi. Daga yau sai ita wacce ke tashin sa sai ta cigaba da tashin shi. Ban da munafunci ta san ya na da mata amma wai ta ce duk asuba sai ta kira shi ya ta shi ya yi sahur? Ban taɓa lura ba saboda da na tashi na ke zuwa kitchen domin samar da abin buɗe baki ban taɓa cin karo da kiran nata ba sai yau.   Tun da na zauna a wajen nan ban yi dariya ba. Tun kafin ya fito na ce ma Jidda ta zuba ma kanta da Baby sai ta kalleni kafin ta ce" Umma Abba fa? Wani kallo na yi mata kafin na ce" Kar ki ci ki tsaya jiran wani Abba." Ita kanta na san ta yi mamaki domin sai da ta kalleni ni kuma na kauda kaina ina cin alalen da ma ɗumama sai ruwan tea wanda ban saka madara ba na ke sha dashi Baby dai sai cin ƙwanta ta ke yi ba ta damu ba Jidda kuma jikinta a sanyaye ta ke kurɓan tea ɗin ta ke sha tare da buredi ni kuma a raina ina ta roƙon Allah ya sa kar Yallaɓai ya tashi yau sai dai ya yi ɗaure sai dai addu'ata ba ta karɓu ba sai ga shi ya fito ya na sanye da jallabiya mai ruwan ƙasa Baby na ganin shi tana ƙoƙarin miƙewa ban san lokacin da na daka mata tsawa ba. "Ke koma ki zauna ko na saɓa miki." Haka na faɗa cikin zare mata ido. Daga Yallaɓai har Jidda da kallo suka bini, ita kuma sai ta kalleni ta ruɗe har ba ta san kafarta ya ture tea ɗin gabanta ba. Sai ga shi ya malale min a saman cafet kallon tea ɗin na yi yana gangarowa wani abu na tokaremin zuciya. Ganin irin kallon da na ke yi ma Baby ne ya sa Jidda ta yi sauri miƙewa ta na faɗin" Ki yi hakuri Umma bari na gyara wajen."   Yallaɓai na tsaye hannunsa harɗe a kirjinsa yana bin mu da kallo barin ma ni.  Kawai sai na yi kyafci ina kallon Baby da ta yi kamar za ta yi kuka na kaɗa kai kafin na ce" Lalle ko za ki ci ubanki Maimuna"   Ta na jin abin da na ce ta barke min da kuka, tsawa na ƙara daka mata kafin na ce" Za ki yi min shuru ko sai na zo na tattaki a nan wajen?   Na faɗa ina mata wani kallo, Sai kawai Yallaɓai ya kira ta sai ta kalleni ta kasa tashi shi kuma sai ya ce ta zo mana ya na kiranta ganin na kauda kai ne ya sa ta tashi ta nufe shi ta na kuka ta faɗa jikinsa ya rumgumeta yana faɗin" Shii Umma ce! Kyaleta kun kwance da ita ko?   Kukan Baby ma ƙara harzuƙani ya ke yi amman ban yi mgana ba sannan ban ɗago kaina ba. Ina jin su yana ta lallashinta har sai da ta daina kuka sannan ya ce ta koma ɗaki ta kwanta ita kuma Jidda ta dawo da tsumma ta goge wajen tas ta gyara da na ce ta zauna ta ƙarishe shan tea ɗin ta sai ta ce mini ta ƙoshi. Uban gayyar kuma na tsaye ban kuma ce ya zauna ba sai da ya gaji sannan ya zauna a ƙasa kusa dani yana faɗin. "Zuba min tea." Da na so na ce ya kira Gimbiya sai kuma na fasa na haɗa masa tea ɗin na tura masa gabanshi da ƙwan da buredin ganin yadda na ƙi kallon shi ya sa cikin mamaki ya kira sunana. "Sadiya." Ban ɗago ba amma na amsa sai kawai na ji yana faɗin" Me ke faruwa ne? Sai a lokacin na yi masa kallon ƙasa ƙasa kafin na ce" Me ka gani? "Abubuwa da ya wa. Na ga kamar ranki yana ɓace ne me ya faru? Ke da yara ne? Ya faɗa yana kallona nima sai a lokacin na kalle shi sai kawai na kauda kai kafin na yi mirmishi gefen baki na miƙe ina faɗin" Bakomai." Abin ya bashi mamaki ganin na bar shi a falon na yi shigewata ciki kuma na san ya bi ni da kallo ban kuma ko waigo ba. Ban ƙara ganin Yallaɓai ba sai da ya zo daukan hula da carbi ina kan darduma ya ce mini ya tafi masallaci sai na gyaɗa masa kai kawai ba tare da na yi masa mgana ba. Da safe ma haka na tashi gim da raina ko fara'a ban yi masa ba daga shi har ƴayan shi Jidda dai ta ga har da safen ban huce ba sai ta sameni a falo ina zaune domin ɗakin na bar ma Yallaɓai gabaɗaya. "Umma ki yi hakuri don Allah." Har da Baby ma kamar ta yi kuka ta ce" Ki yi hakuri Umma." Sai suka ba ni tausayi laifin Ubansu ne ya shafe su sai na ɗan saki fuska na ce musu zo su wajena na haɗa su na rumgume na saki fuskata shi ya sa suka tafi makaranta suma sun warware. Amma shi kan Yallaɓai ya kasa gane kaina da ya matsamin sai na ce masa ban ji daɗi ne. "To ko mu je asibiti ne? Me ke damun ki? Kai tsaye na ce" Ba sai mun je ba. Ciwon kai ne kaɗan zai bari zuwa anjuma." Kasa fita ya yi saboda yadda ya ga ina basar dashi ya san halina dole akwai wani abu da ya yi mini ne. "Sadiya don Allah ki faɗa min me ya faru? Na ce masa bakomai ba sau adadi amma bai yarda ba. Ganin ya damu sai na ɗan saki raina saboda na ga ya na damuna da tambaya tun da ba gaya masa abin da ke danuna zan yi ba gwara na saki raina ko zai kyaleni da tambayoyin sa. Na ɗan sakin masa har muka zauna muna ta hira sai muka ganganro kan mganar kayan salla ya ce yana jiran cikon payment na aikin da suka yi a Rano ne a wannan sati sai a yi mganar kayan salla da ɗinki da sauran su ya so ba zai fita ba ne sai kuma Musbahu ya kira shi ya ce wasu mutane sun zo suna jiran shi. Da zai fita sai na ce bari na shirya ya sauke ni Gwammaja na duba Nene, da gayya na faɗi haka saboda na ji me zai ce sai kuma bai ba ni kunya ba. "Nene ta samu sauƙi fa. Ke da ba ki da lafiya, ki bari ko zuwa jibi tunda ba ki ji daɗin kema." Kai tsaye na ce" Na ji sauƙi mu je ka sauke ni zan iya zuwa." Na ɗauka zai ƙara mgana sai kuma ya yi shuru sai da muka jira Saude ta zo na bar mata gidan daman mun yi wanka mun shirya ni shadda na saka da farim mayafi shi kuma sai ya saka kananun kaya. Da ya kai ni Gwammaja bai shiga ba saukeni kawai ya yi ya wuce office ni kuma na shiga ciki sai da na lelleƙa daƙunan su Hajiya iya muka gaisa sannan na ƙarisa ɗakin Nene na ganta garas da ita ita kaɗai ce a shashen ita ta ke faɗa mini Gimbiya ta leƙa wajen aiki. Da na yi mata ya jiki ta na mirmishi ta ce" Tafida sai da ya ta so ki? Ɗan zazzabi ne Gimbiya ta ɗaga masa hankali tun jiya ina shan mganguna na warware." Sai na yi mata fatan samun sauƙi bayan tambayan yara na ce suna makaranta mun ɗan taba hira da ita anan na yi azahar ina shirin tafiya sai ga Gimbiya ta dawo mun gaisa sama sama kamar yadda muka saba. Ta dai tambayi su jidda na ce suna makaranta.   Ƙarfe biyu na koma gida na.  Daga kuma ranar ko a fuska ban ƙara nuna ma Yallaɓai wani abu ba. Ban damu da ma ƙara saka masa ido ba saboda mu zauna lafiya amma ni na san ba ta fasa kiran shi da tura masa saƙo ba, amma dai bai ƙara buɗe baki a waje ba sai a gida mun shiga goman karshe an fara ibadar na tahujjud Yallaɓai masallaci ya ke zuwa ni kuma in ta da yara mu yi namu a gidaa.   Ranar da za mu ɗau azumi na ashirin da 24 Yallaɓai ya dawo daga masallaci ya ɗan kwanta huɗu da rabi na tashe shi sai ya shiga tiolet yana wanke baki a lokacin na ga Gimbiya ta na kiran shi bayan ta katse sai ta tura mssa saƙo zuciya ta rinjaye ne na ɗau wayar na duba saƙon na ta. "Daddy jiya ba ka zo ba? Kuma fa na yi maka kunin tsamiya mai daɗi" Motsin fitowarsa na ji da na so na yi saurn ijiye masa wayar ne sai kuma na fasa sai da ya fito. Ya yi mamakin ganina tsaye da wayarsa sai da ya matso gabana sannan na miƙa masa wayarsa ya karɓa kafin ya samu sararin mgana na ce. "An tura maka saƙo."   Ina gama faɗin haka na fice na san kuma bayan ya duba saƙon ya ji nauyi domin ba na ce kunya ba tunda maza ba su san kunya ba. Har ya fito muka yi sahur jikinsa a sanyaye ni kuma sai na yi masa bariki ban nuna masa ko a fuska na ji haushi ba sai ya ɗan saki jikinshi amma a raina na kudiri niyyar koya masa hankali daga shi har Gimbiyar ta shi. Washegari ya tura mini kuɗin kayan salla nawa da na yara sai na su Nene da na Gwaggo. Daman yana yi musu kaya duk shekara. Dija collaction na tura ma kuɗin daman mun yi mgana na zaɓi komai har Marwa na yi ma kaya da Saude saboda mun yi waya a gida za ta yi salla in ta dawo sai kuma ta gama pratical ɗin ta za ta koma makaranta. Kuma daman ta turo mini kayan na zaɓa tuni suna wajen ɗinki kuɗin ne sai da ya tura mini bayan mun gama lissafi na tura mata.   Ni da yara kala huɗu ya yi mana. Leshi biyu atamfa biyu. Nene Atamfofi biyu su Hajiya Iya kowacce ɗaya sai Jawahir kala biyu Adanan kuɗi ya tura masa sai Gwaggo guda ɗaya Alhajinmu kuma shadda mai kyau. Sai ni mayafai guda biyu da Hijabi ni da yara sai takalman mu har Nene an siya mata takalmi da Hijabi gabaɗaya tun lokacin da a ka kawo kayan na nuna masa ya ce komai ya yi. Telanmu kuma daman na yi masa mgana kuma ga kuɗi har da na Nene na kai mana ɗinki tare da na Jawahir da Marwa Saude kuma na ta na bata mamanta na ɗinki ita za ta ɗinka mata. Gwaggo kuma da Alhajinmu na kai musu na su suna ta godiya duk da suma su Yaya Hamza duk sun yi musu. Nene ma na kai mata takalmi da hijabinta na ce kaya na wajen ɗinki ta na ta saka albarka. Ranar da muka ɗau azumi na ashirin da shidda Mimisco ta aiko da kaya yan kanti kala biyu biyu na jidda da baby. Anty Bahijja ma ta aiko musu da material a ɗinke sai Anty Maimuna itama kala biyu amma Bby uku ta yi mata har da wani riga da wando masu kyau da takalma. Gimbiya kuma Yallaɓai ta ba ma kayan ya kawo ma su, kayan kwalliya ne sai hijabai da mayafai sai takalma masu igiya sai abun hannu da ɗan kunne sai kwalban da ake kitso da shi kayan kuma ta ce suna wajen ɗinki duk Yallaɓai ne ya ke koramin jawabi nan yaran suna ta murna shima bakin shi ya ƙi rufuwa. Daga gani ya ji daɗi kuma har hakan ya nuna a saman  fuskar shi.   Ni dai ban nuna masa komai ba na yi godiya har ya na saka min kati a waya ta ni kuma na san na kiran da na ce zan yi ma Gimbiya na yi mata godiya ne. Kai namiji munafuki ne wallahi.   Ranar da muka ɗau azumin ashirin da bakwai ɗaure Yallaɓai ya yi saboda na zo tashin shi na ga Gimbiya na kiran shi sai kawai raina ya ɓaci ban tashe shi ba. Ni kaɗai na yi sahur saboda Jidda na ce ta huta jiya ta sha wahala. Yallaɓai bai tashi ba sai da aka fara kiran salla lokacin ina zaune na idar da raka'atul fajir, ya tashi ya na kalle kalle kiran sallar da ya jiyo ne ya sa ya kalleni cikin muryan barci ya na faɗin "Sadiya mun makara ne? Na ji kamar ana kiran salla? Sai da na kalle shi kafin na ce" Kai dai ka makara. Ni na yi sahur ɗina." Cikin mamaki da tuni barcin ya sake shi ya ce" Ban ga ne ba? Ni fa? Kai tsaye na amsa masa da cewa" Ba ka yi ba." "Me ya sa ba ki tashe ni ba? Sai da na yi shuru kafin na ce" Ban tashe ka ba. Saboda na ga wacce ka rabama girki da ita na kiranki sai na koma a tunanina ta tashe ka yau ɗin" Galala ya yi ya na kallona sunana ya kira na yi masa banza sai kawai na miƙe na kabbarta salla ganin haka yasa shima ya mike amma sai ya ya ɗau wayarsa ya duba sannan ya mike ya fita zuwa tiolet ya ɗauro alwala ya fita zuwa masallaci sanda ya dawo ina ji da na yi baricn ƙarya weekend ne yara ba makaranta sun ma yi hutu jiya jumma'a.   Na san mganar da na faɗa masa na cin ransa bai iya hakuri ba ina barci ya tashe ni da mganar wai bai gane me na ke nufi da ya raba mana girki ba? Da wa ya raba mana girki? Kai tsaye na ce" Da wacce ta ke yi maka girki kana zuwa ka ci ka biya tuƙwaici mana."   Wani kallo ya yi mini ni kuma ina shirin na juya na koma barci ya riƙo ni ya na kiran sunana. "Sadiya." Ido na sakar masa kafin na ce" Na'am Yusuf." Kawai sai ya girgiza kai bayan ya saki hannuna kafin ya ce" Sadiya karki fara abin da ba halin ki ba ne. Bincike mini waya kike yi yanzu saboda ba ki yarda da ni ba? Kai tsaye na ce" Allah shi kyauta. Kawai dai akasi aka samu na gani." Komawa na yi na kwanta ina faɗin" Karka damu ba wani abu fa." Miƙewa ya yi ya na kallona ni kuma sai na ja bargo har saman kaina. Hannu ya saka ya janye bargo ya na faɗin" Ki tashi mu yi mgana" Sai na ƙi tashi na riƙe bargon ina faɗin" Wata mgana? Ai mun gama mganar nan ko? Zura min ido ya yi kafin ya ce" E duk da haka na ce ki tashi mu yi mgana." Na ko ƙi tashi na juya zan gyara kwanciya a saman kaina Yallaɓai ya yi min tsawa. "Sadiya na ce ki tashi mu yi mgana ko? Kar ki bari raina ya ɓaci wallahi." Yadda ya yi mganar ne ya sa na gane ranshi ya ɓaci sai na miƙe na zauna a saman gado shima sai ya zauna ya na mai sauke ajiyar zuciya. "Sadiya wallahi ba komai tsakanina da Daughter fa. Kawai dai kin san am her favorite ne tun a baya. Kuma ni tana kira ne ba domin ta san ba ni da mata ko wani abu ba just normal na yan'uwan juna kin gane? Sai kawai na gyaɗa masa kai, domin ni na san kawai yana faɗa ne. "Kar ki ɗauke shi a wani abu don Allah. Ni ina mijinki haƙƙi ne a kanki ki tashe ni kamar yadda kika saba." "To ba za a ƙara ba." Na faɗa saboda na gaji da jin mgananunsa. "Kuma game da abinci in na je duba Nene sai ta yi mini ta yi in na ce ba zan ci ba sai Nene ta ce ko kaɗan ne na taɓa. Kin san dai ba zan yi ma Nene gaddama ba. Mganar tuƙwaici kuma wannan kyautatawa ce kema kuma ai ina yi miki ko? Ina ta kallon shi dai amman na kasa mgana. "Ba ki son kiran ne? Sai na ce mata ta daina Sadiya ta ba ta so." Wani kallo na yi masa kamar in yi dariya saboda na ga zai raina min wayau amma ban yi ba. "Zan faɗa mata ta daina kirana da asuba gashi yau ta ja mini yin ɗaure." Ya faɗa ya na yar dariya har yana shafa min kumatu. Yaƙe kawai na yi masa ban yi mgana ba. Hamma ƙarya na fara yi masa sai ya ce na koma na kwanta shi zai fita can falo akwai aikin da zai yi har ya ɗau laptop ɗin sa ya fice ina bin shi da kallon mamaki. Ajiyar zuciya na sauke ko ba komai a zuciyar Yallaɓai game da Gimbiya ita har gobe shi ne zaɓin ta tsoro  na ɗaya wannan karon mafarkinta zai iya zama gaskiya in dai ba wani ikon Allah ba tunda ba ta da shamaƙi da hakan ta kowanni fanni. Tun kuma daga mganar da muka yi ba mu ƙara tada mganar ba. Ita ma ta daina kiran asuba ina tunanin da gasken ya yi mata mgana sai na ji daɗi ko ba komai  ya nuna mata ni matarsa ina da daraja. daga nan nima sai na watsar da abin da ke cikin zuciyata na kishi na rumgumi mijina. Sai cefanen salla tare muka je kasuwan muka siyo komai sauran kayan miya kuma Musbahu ya ce ya ba ma kuɗi zai kawo minibana gobe salla nama kuma daman a can gida sa suke yankawa a raba gabaɗaya amma dai ya siya mana na kasuwa kilo huɗu sai kaji muka haɗa da shi ni kuma a gida na siya fulawa zan yi cincin da cake da donut ga masu tayani Saude da Marwa da ta zo mini salla duk tare muke ayyukan gefe ɗaya kuma ina ta mana shirin Annirvesary ko Yallaɓai bai san shirina ba da ya tambayeni nace masa kawai ya tura mini kuɗi suprise ne shima ya ce a ranar akwai suprise ɗin da zai ba ni ina ta murna har ina zolayanshi na ce Yallaɓai ko ka biya mini Umra ne? Yana mirmishi ya ce in sha Allahu za mu je Umra Sadiya ta. Da ni da yara duk mun yi ƙunshi salla wata Hajjaju ce maƙoyar su Rahila na kira har gida ta yi mana kunshi na biya ta. kitso kuma mai yi mana kitso ta zo gida ta yi ma su Jidda har da Marwa da Saude bayan ni na wanke musu kan na su a gida.    Ni dai ana gobe sallah na je shagon Amesty ta yi mini Saloon. Ban cika son yin kitso ba saboda Yallaɓai ya fi son in bar gashina a haka ta bakin shi ya ce ya fi mai daɗin taɓawa. *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU #1k NE KACAL, AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY)* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Kz6koexT4Yj4o2zO4xVzrU INA MATAN DA SUKA DADE SUNA NEMAN MAGANIN SANYI WATO INFECTION MAI KYU BASU SAMUBA, ANYI MAGANI ANYI MAGANI HAR ANGAJI, TOH KICE ALHAMDULILLAH, SABODA ALLAH YA HADAKI DA MAGANIN DA ZAI MAGANCE MIKI KO WANE IRIN CUTTAN SANYI WATO INFECTION DA YA KAMAKI CIKIN SATI GUDA DA YARDAN ALLAH. SHIGO GIDAN BUZAYE WAHALANKI TA YANKE HAJIYA💃💃 INA MAI NEMAN KAYAN GHARA ZAFAFA, MASU INGANCI, MASU KARFI, WANDA ZAI KANKARO MIKI MUTUNCINCI DA KIMARKI, WANDA ZASU DAWO DA HANKALIN ME GIDA GAREKI, SU SA YA MAKALE MIKI DA ZAZZAFAN SOYAYYANSHI, YA DINGA SAKE MIKI KI WARWASA YANDA KIKE SO💃💃 TO ER UWA SHIGO GIDAN BUZAYE KIGA IKON ALLAH DON KUWA ALLAH YA KAWO MIKI KARKEN MATSALANKI NA RASHIN DACEWA DABAKYAYI NA KAYAN GHARA😁💃💃 KUSHIGO GIDAN BUZAYE KU GYARA KUGA IKON ALLAH *🅿️19* Mun yi azumi ashirin da tara 29 ɗaya ga watan shawwal ya kama ranar asabar ne a ranar muka sallaci salla ƙaramar salla. Mun je idi mun sallaci salla tare da al'ummar Musulman duniya gabaɗaya ni da Yallaɓai da yara sai Marwa da ta yi salla tare da mu. Bayan mun dawo idi na saka Marwa ta dafa jallop ɗin shinkafa mai nama. Tun a daran jiya muka gama duka soye soyen mu Saude da Marwa sun taimaka mini ƙwarai shi ya sa jiya da Saude za ta tafi da daddare Musabahu ya zo gidan da shi na haɗa su na ce ya kai ta gida tunda akwai motar Ya Usman a hannun shi tun lokacin biki bai koma da ita ba. Na dibar mata naman salla da kayan fulawan da muka yi sannen na ba ta ɗan kunne da takalmin sallar da na siya mata sai pant da bara da na siya musu tare da Marwa sannan na diɓa mata shinkafa kayan miya kuma na ba ta kuɗi na ce ta kai ma Mamansu ta siya kayan miya su yi abincin salla tunda na wajen nawa an niƙa gabaɗaya na tafasa.   Yallaɓai na gida bayan ya ci abinci da nama yana falo yana amsa wayar ƴan'uwa nima 5k ya saka min kati ya ce na kira barka da sallah. Na samu kiran wasu yan gidanmu waɗanda ba su kira ba ni na kira su Alhajinmu dai da Gwaggo su na fara kira Nene itama na kira ta yi musu barka da salla sannan na kira Inna Mariya da su Kawu Nafi'u na yi musu barka da sallah. Har Yaya Murja ni na kirata Ma'u ce dai ita ta kirani kafin ni na kirata. Amma na kira Baaba ban ji mamakin da ta ce ba ta gane ni ba. Domin ba ta da lambata sai da na faɗa mata sunana bayan ma na faɗan sai da ta ce. "Wata Sadiyar? Kai tsaye na ce" Ta Yaya Sulen." Sannan ta ce au muka gaisa sama sama su Jidda ta tambaya na ce suna lafiya daga nan muka yi sallama. Da ga ita na kira Baba Aminu da Baba Sani suma na yi musu fatan an yi salla lafiya. Da ga su sai Rahila sannan na kira Yaya Muntari shima na yi masa barka da sallah. Bayan dangina sai na kira dangin Yallaɓai daman bayan su Alhajinmu na kira Nene na yi mata barka da sallah. Sai Mimisco Anty Maimuna na sameta mun gaisa amma Anty Bahijja ba ta ɗauka ba sai daga baya ta kirani. Na kira Faridan Tariq sai su Hauwa dukkansu na yi musu barka da salla Anty Zabba mutanen fatakol ita ta kirani muka gaisa har ta ke gaya min yara na nan gwammaja sun zo sallah. Da ya ke lokacin ya yi kusa an haɗu da biki ba lalle wannan sallan yan nesa su samu zuwa ba. A ranar Yallaɓai sai yamma ya fita zuwa Gwammaja kuma bai daɗe ba ya dawo washegari lahadi ban je ko'ina ba saboda ƴan yawon sallah. An kawo min su Sahla sai yaran Munnira sannan Jawaheer ta zo tare da ya'yan Anty Zabba da suka zo daga fatakol. Daga ɓarayina ƙannen Marwa ne kaɗai su ka zo min yawon salla daman su sun saba zuwa ban saka rai da su Antin  Yaya Murja ba domin na san in da suke zuwa. Na ba su nama da kayan fulawa sannan na yi shinkafa da miya da salat suka ci da za su tafi da yamma na ba su kuɗin adaidaita sannan da kuɗin barka da sallah. Sun tafi kenan sai ga su Firdausin Anty Balki su biyu ita da ɗiyar ƙanwar babanta suka ce mini daga gidan Yaya Abubakar suke har ina yi musu tsiyan sai da yamma ne za su zo mini? Su bari sai gobe mana.   Suna dai sunne kai ba su ce komai ba, Allah ya taimaka bayan mangariba sai ga Musabahu da Adnan daman ina ta tunanin wanda zai kai min su gida tare da Yallaɓai suka shigo gidan. Ganin su ya sa na ce su jira su in za su tafi su a jiye min su a anguwansu ko daga bakin titi ne. Sai wajen tara na dare suka tafi tunda bayan sun ci abinci suna falo suna hiran su na ƴan'uwa acan falon shi. Amma sai da na kira Yaya Balkin na faɗa mata su Firdausi na gidana zan saka a dawo da su. Jidda da Baby daman a gidan Mimisco suka yi ni ta kira ni ta ce Direba zai dawo da su. Gwammaja kuma sai zuwa gobe za mu je can mu yini. Su Musbahu sun tafi da Firdausi ba daɗewa sai ga Direba ya dawo da su Jidda gida da Nama da yawa a leda da cake har da su lemuka da kuɗi da yawa sabbin yan ɗari ɗari suka ce Daada ne ya ba su wato mijin Mimisco daman sunan da ƴaƴan shi da ita kanta Mimiscon suke kiran shi kenan. Ranar litini ya kama ukun salla tun asuba na tashi ni da Marwa waina za mu yi saboda zan kai Gwammaja zan kuma aika da shi Ɗorayi da Gandun albasa. Saude na kira waya na ce ta zo da safe ta taya mu aiki. Saboda ina da mataya ko kafin sha biyu na rana mun gama toya waina duka miya daman tun safe na haɗa ta. Yallaɓai ya siyo mana manshanu daman na zuba a cikin miyan ga kayan ciki ga naman rago sannan ga ƙashi. Miya sai tashin kamshi ta ke yi Yallaɓai na sauri zai fita Rano zai je za su haɗu da Uncle Abba da Tariq da suka zo sallah sai na zuba masa ya ci ya na santi sannan ya tafi amma sai da ya ba ni goron salla ta na 10k sabbin yan 200 goron salla da kuɗin kwalliya domin na yi masa ado kuma ya burgeshi.      Muna gamawa su Marwa suka gyara gidan saboda rage kaya Yallaɓai na ce ya yi mini gaba da su Jidda zuwa Gwammaja da wainar su ni daga baya sai mu taho da Marwa. Saboda daman ranar a can muke yini sai washegari yinin salla na huɗu kowacce sai ta je gidan su. Saude ma kuɗin a daidaita na bata bayan na diɓar mata na su wainar sai kuma na bata na gidanmu a babban kula na waina sai ledan da na saka Nama da kayan fulawa na ce ta kai ma Gwaggo in ji ni. Ni kuma sai da na sake wanka na sauya kaya na saka leshin da Yallaɓai ya yi mini na yi amfani da mayafi da jaka da takalmi kalan adon leshin jikina na saka ɗan kunnayena masu kyau da yarari na fito na yi ras da ni na san duk in da na shiga ba wanda zai raina ni. Da muka fito daga gida ba Gwammaja muka fara zuwa kai tsaye ba sai da na biya Gandun Albasa gidan su Mama na kai musu abincin salla da Naman salla sai kayan fulawan da na yi ban jima sosai a can ba duk na ga su Inna Mariya da sauran yaran su muka gaisa na yi musu rabon barka da sallah daman duk sallah ina kai musu abinci kuma ina zuwa tunda ni kaɗai ce mace a kano Amina ta yi nisa sai in wani abu ya faru ta zo. Ni ɗin ce na ke ƙoƙarin sada zumunci suma kuma suna da kirki duk abin da zai faru damu suna zuwa sannan Ya Auwal ma in ya zo garin ya kan je ya gaishe su kuma taimako dai dai gwargwardo ya na yi musu abin da bai gagara ba.   A can Gandun albasa muka yi azahar sannan muka wuce Gwammaja. A can na iske su Hauwa da Munnira gida cike da ƴa'ƴa da jikoki. Domin kaf ɗin su yaran gidan sun zo sai dai waɗanda ke nesa irin su Jafar da Muhammad sani Yaya Usman daman sai yaran shi kawai ne suka zo. Su Anty Bahijja gabaɗaya suna nan da gayyarsu ban ga Gimbiya ba sai na ji Anty Maimuna na faɗin ta tafi Rano ɗazu da safe. Naja'atu ta zo amma ina gidan ta yi shirin tafiya gidan iyayen mijinta can za ta ƙarishe yininta Halima ma ta zo da yaranta ta yi kiɓa ita da jajariyarta mai kyau da ita har na ɗauke ta. Lokacin da na zo Nene ta kwanta sai da ta tashi muka shiga muka gaisa na kai mata Nama da kayan fulawan da na zo da shi ta yi ta saka mini albarka. "Sadiya Tafida ya kawo mana waina. Sannu da aiki Allah ya saka da alheri." Na amsa da Amin haka Nene ta ke komai sai ta yi maka godiya. Daman su Hajiya iya duk na shiga mun gaisa na kai musu na su Naman salla, tunda haka na ke yi duk shekara sai dai Yallaɓai in ya je ya ji suna masa godiya nima haka suka yi ta min godiyar waina, Suwaiba har tana min tsiyan shi ya sa Yaya Tafida ya fara ijiye tumbi ashe daɗin girki na ne ina ta mata dariya. Maman farko ta ce ai ta diɓa ta boye za ta ɗumama ta ci da daddare wainar ta yi mata daɗi. Da ya ke shekara biyu kenan ban yi waina ba wancan shekaran tuwo na yi musu da miyar agushi wannan ne na ce bari na yi waina saboda a sauya baki. Kowa ya ganni tare da Marwa sai ya ce Sadiya ina kika samo yar budurwa mai hankali da kunya haka? Saboda da yara sun ɓata ɗakin Nene za ta ɗauko abun shara ta share. Ga shi ta na son yara goye take ma da ɗiyar wajen Halima har Nene sai da ta yi mgana na ce ɗiyar Yayata ce Marwa na tuna ma Nene ai ta na zuwa gidana hutu kuma na sha zuwa da ita gidan nan.   Nene cikin mamaki ta ce" Allah Sarki girman ɗan mutu ba wuya. Ita ce ta girma haka? Ina dariya na ce ma Nene wallahi ita ce. Nene ta yi ta saka albarka Anty Bahijja ta saka mana baki da tambayan a ina take karatu na ce a tsafe makarantar koyin aikin jinya sai ta taɓe baki ba ta yi mgana ba ni kuma ban damu ba sanin halinta akwai son ta ji ƙwaf kuma in an faɗa mata ta nuna kamar ba ta so ta ji ba. Ganin ɗakunan su Nene cike da ƴayansu zuwa jikokinsu sai mu surukan gidan muka tsame kan mu zuwa ƙasa shashen su Jawahir ba ta nan ma tun safe an ce ta tafi can gidan kakaninta na bangaren uwa ita da Adnan. Da ni da Hauwa da Muniira muka zauna acan muna ta hira muna shewa. Muna ƙara ma junan mu sani kan abin da bamu sani ba. Muna mgana kan kayan gyara ne Munnira ke faɗin rabon ta da wani gyara tun haihuwan Mufeedan ta. Cikin mamaki na kalleta kafin na ce" Ke kam Munnira me ya sa me ki? Mufeeda yanzu ai ta shekara uku ko Hauwa? Na faɗa ina kallon Hauwa wacce kafin ma ta bani amsa Muniiran ta karɓe da faɗin" Shekaranta uku da wata biyu." Jinjuna kai na yi kafin na ce" Ki ce waje duk ya yi tsatsa. Gaskiya ba ki kyauta ma Nasir ba." Na faɗa ina hararanta ita kuma tana dariya kafin ta ce" Ke ni fa gani na ke yi duk ba sa wani yi asara ne. Kuma ni in dai ba shi zai ba da kuɗin a siya ba sai na ke ƙyashin fidda kuɗina na siya wallahi."   Mamakin Munnira ya kamani daman har yanzu akwai mata masu tunani irin na Munnira? Ko dai ta yi ma kalmar gyaran mummunan fahimta kamar yadda wasu matan suka yi ma kalmar. Ban samu zarafin mgana ba Hauwa ta karɓe mganar da cewa" Haba Munnira ke da kan ki ma? Mata ai yanzu sun waye kowa ta san abin da za ta sha ya gyara ta ba wai kuma wanda zai zama cuta gare ta ba. Kuma kin manta hausawa na cewa in kana da kyau sai ka ƙara da wanka? Kina da yaƙinin tun gyaran da kika yi da haihuwan Mufeeda ya na nan a jikin ki? Haba ai yakamata dai ko yaya ne ki ɗan ƙara gyarawa ko dai baki sha komai ba yan kayan marmarin nan da za su ƙara miki cika da Ni'ima."   Daga ni har Munnira baki muka saki muna kallon Hauwa. Sai da ta gama bayaninta ta ga irin kallon da muke yi mata sai ta ji kunya ta kauda kai tana faɗin" Me ya faru kuke kallona? Ko ba gaskiya na faɗa ba." Ina ɓoye mirmishina na ce" Kin faɗi gaskiya Hauwa uwargida a gidan Mutaƙƙa shi ya sa har gobe bai kallon kowa sai ke ashe sirrin da kika riƙe kenan? To mu ma a ɗan gaya mana sirrin mana ko Muni? Na faɗa ina kallon Munnira da ta kwashe da dariya har ta na bani hannu muna tafawa cikin dariya ta ce" Shegiya Hauwa ta zama yar gari. Maza gaya mana sirrin." Hauwa na dariya ta ce" Shawarwarin ku ne fa, sannan daga Rano akan ɗan aiko mini da gumba da sauran abin da ba za a rasa ba. Sai wacce Sadiya ta haɗa ni da ita na kan ɗan siya mganin infection sai kaza in na samu kuɗi kuma Alhamdulillah ina ta ganin canji."   "Allah Hauwan Mutaƙƙa ? Na faɗa ina kallonta sai kawai ta ɗaga mini kai. Tare muka saka dariya Munnira har ta na ɗaga kafa saboda dariya kafin ta ce" Ke Sadiya yaushe Hauwa ta yi baki haka? Kuma abin ɗanwaken zagaye ne? Hauwa kaɗai kike so ta gyara ban da ni ko? Ina ɗaga hannuna sama na ce" A'ah ita ta min mgana ta ce tana so saboda ranar tana gidana aka aiko min da saƙon. Sai ta ce min tana so sai na haɗa su kema in kina so ai ta kwana gidan sauƙi waya kawai za a yi mata." Munnira sai ta gyara zama kafin ta ce" To wai kuma yana yi sosai? Na kalleta ban yi mgana ba Hauwa ce ta ba ta amsa da cewa" To ai ke tunda kin riga kin saka wasi wasi ko kin siya ba zai yi miki aiki ba." "Ko? Haka ta ce tana kallon mu ni ko sai na gyara zama ina faɗin" Gaskiyan Hauwa. Kuma son kuɗi ne ba zai barki ki yi gyaran ba karki kashe kuɗi ko? Zauna Nasir ya samu wasu ƴan kudaɗe ya nemi chanji lokacin za ki yi bayani ne." Tana dariya ta ce" Haba. Ai ya yi ƙanƙanta da Mata biyu. Yallaɓai dai ke kan hanya daman ana ta cewa tunda Yaya Usman ya buɗe hanya Yallaɓan ki ne zai biyo baya."   Wani kallo na yi mata sai ta kama dariya Hauwa na taya ta. Nuna ni take yi tana faɗin" Ta firgita ta. Kin gan fa Hauwa." Ta faɗa tana nuna ni ture hannunta na yi ina faɗin" Firgitan me? A kaina za ta zauna? Allah ya kawo ta lafiya." Hauwa da Munnira na ta danne dariya haushi ya kamani na ce" Wai dariyan na menene kuma? Ko kin ji labarin auren ne ni ban sani ba? Da sauri Hauwa ta ce" A ina? Wallahi wasa ne kawai ba abin da muka ji." Hararan su na yi domin na ga sun maida ni abin zolaya. Munnira ce ganin na haɗe rai ina faɗin" Ko za a mini kishiya sai an yi miki Munnira in sha Allahu." Da karfi ta amsa da cewa" Wallahi ba Amin ba. Cab" Ina mirmishi na ce" Au ashe ba daɗi? Sai ta marairai ce tana faɗin" Daga Wasa? To a bar mganar kawai."   Ni kuma na ce sai an yi ta. Munnira uwar kishi ta ce ita fa ta tsani labarin kishiya. Ganin na na ce ina cewa Nasir sai ya yi aure nan kusa in sha Allahu Hauwa na taya ni sai kawai ta sauya mganar da cewa" Na ce ba ya mganar kayan gyaran can ɗin? Ina ga zan siya nawa nawa ne? Ni da Hauwa har muna tafawa saboda dariya sai da na gama ja mata aji sannan na yi mata bayanim ingancin kayan gyara na Hajiya Surayya Halin yau. Cikin mamaki Munnira ta ce" Da gaske suna da kyau? Ba su dai cutarwa ko? Kai tsaye na ce" In da suna cutarwa da tuni sun cutar da ni. Ke Munnira ki cire wannan tunanin a ranki na matan da ba su san kansu ba. Yanzu mata sun fahimci muhimmamci gyara a jikinsu wanda ba zai zama cuta a gare su ba. Kin ga mganin infection ɗin nan yana da kyau duk bayan wattani uki mace ta riƙa shan shi. Saboda shi infection 90% na mata muna dashi sannan mu ke zuwa gidajen biki da suna muna mu'alama da banɗakuna mabambamta. Kin ga kowani lokaci za mu iya ɗauka sai mun dage da mgani sannan maganar gyara Munnira ba wanda zai cutar dake ba yar gumbar nan ta mata ɗan kazan nan na haɗin uwargida ba komai a cikinta sai itatuwan maganin da zai ƙara miki Ni'ima. Bayan nan za ki riƙa gyaran ki a cikin gida kayan marmarin nan ki riƙa shan su madara su rage kayan ganye da sauran su duk suma suna taimakama wajen dawo da ruwan jikin mu kin gani nan duk bayan wata uku sai na siya mganin infection na sha sannan na bi da kayan gyara bayan kuma ina yin nawa dubarun a cikin gida hatta fatata ban  zauna ba bayan wani lokaci ina siyan mayukan gyaran jiki domin kaina da kuma Mijina. Ba kuma domin shi ɗin ba sai domin ka riƙe wannan martaban da Allah ya ba ka na ƴ'a mace. Sannan yana da kyau ka yi gyara domin ka farantama mijinka Munnira ba sai an kawo maka wata ka haukace ba. Wanda ko da watan ta zo sai dai ita ta yi gasa da ke ba dai ki yi da ita ba tunda komai ta zo ta iske ki kin san shi kuma kina yi saboda haka ki yi ma kanki faɗa ki gyara jikin ki da kanki saboda martaban ki Munnira" "Gaskiya ne Sadiya mganar ki Haƙƙun."   Hauwa ta faɗa tana mai jinjina kai.  Munnira da ta yi tagumi ta na saurerena sai ta sauke ajiyar zuciya kafin ta ce" Kuma gaskiyan ku ne. To zan dage in sha Allahu. Kuma kamar na fara ganin wani alamu a wajen Nasir duk da bai yi mini mgana ba." "Alamun me? Na tambaya ina kallonta. Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce" Yanzu ba ya daɗewa da mun fara mintina goma sai ya sauka kuma da ba haka ya ke yi ba" Ni da Hauwa muka kalli juna kafin na maida kallona kan Munnira ina faɗin" You see. Akwai sanyi ajikinki kuma a yadda na fahimta ba ya wani jin daɗin ki yana dai yi ne saboda fita haƙƙi ki sai kin dage Munnira" Tuni ta natsu tana faɗin" To zan dage gaya mini mafita. Allah Sadiya ba na ƙaunar kishiya" Yadda ta yi mganar ne cikin tausayi ya sa muka tsintsire da dariya ni da Hauwa kamar za ta yi kuka ta ce" Don Allah ba dariya ba. Ku taimaka mini." Sai na gyara zama ina faɗin" Za mu taimake ki amman ke ma sai kin miƙe kin taimaki kanki." Sai ta ce ta ji duk za ta yi nan take na ɗauko wayata na kira Hajiya Surayya Halin yau. Bayan mun gaisa sai na ce zan haɗa ta da Munnira domin ta yi mata bayani ina ba ta wayar sai na ce ta shiga ciki yadda za ta samu damar yi mata bayani sosai. Sun ko jima suna waya sannan Munnira ta kawo min wayar nan Surayya ke faɗa min za ta fara shan na infection kafin haɗin kayan gyaran ya biyo.   Mun rabu akan Munniran za ta karɓi lambar wayarta su ƙarishe mgana. Washegari ma ta ce za ta aiko ma da Munnira saƙon ko ba ta saka kuɗin ba tunda ta hannuna ne. Duk mai bukatar mganin infection sadidan, ko mganin gyaran uwargida da amarya contact Surayya Halin yau. +234 803 277 3332. Kano Nigeria.   Nuna Gwammaja har wajen ƙarfe goman dare. Domin da mazajen namu suka shigo gidan can bayan sallar isha'i gabaɗyansu suna falon Nene da ƴan'uwansu suna ta hira a tsakaninsu. Mu kuma muna ƙasa mun yi sallah mun koma muna ta zaman hira. A lokacin mganar haihuwa muke yi sun sin ina son na ƙara haihuwa ko daga yadda na ke kan hanyar yawon asibiti. Hauwa ce ke tambayata ya ake ciki ne yanzu? Kai na rausayar kafin na ce" To ana dai kan gwaje gwaje duk da kamar guda biyu suka rage amma Likitan tana ta ba ni tabbacin ba matsala ko ma akwai ba wacce za ta gagare su ba ne."   Tare da Munniran suka haɗa bakin faɗin" In sha Allahu ma ba wata matsala." Sai na amsa da Allah ya sa cikin wani yanayi na ce" Yallaɓai na son yara sosai. Biyu sun yi masa kaɗan ni na sani." Hauwa ta ce" Amma ai ba ya nuna damuwa ko? Sai na gyaɗa mata kai Munnira ce ta karɓe da cewa" Yallaɓai fa bai da damuwa. Damuwar su ne su Anty Bahijja. Ni da na ji ma wani batu amma dai ba ri na yi shuru."   Sai na kalleta gabana ya faɗi saboda na san tabbas abin da ta ji ya shafe ni. Da sauri Hauwa ta ce"Gwara ki yi shurun Munnira. Ni ma da na je Rano cikin azumi na ji batun a gida." Sai kawai na kallesu kafin na yi mgana Munnira ta ce" Au kema? To me za a ɓoye mata ai mgana ce ba cewa muka yi ya tabbata ba. Kuma zaman tare kenan gwara mu faɗa mata ta san halin da ake ciki ko da ta faru ma  ta san in da za ta bullo ma lamarin." Cikin ɗauriya na ce" Wai menene? Ku faɗa min ai ban isa na hana Allah ya yi ikon shi ba." Hauwa ce ta kalleni kafin ta ce" A bakin  Autar gidanmu na ji wai ƙannen Gimbiya ke faɗin Tafida za ta aura. Da na ce ban san da wannan mganar ba Innamu ta ce itama ta ji kuma a bakin makusantan ita Hajiyar Tafidan an ce daman tun farko Hajiya Nene da Hajiya tafidan sun so su haɗa zumunci na auran Gimbiya da Tafida Allah bai yi a wancan lokacin ba. Mutuwar mijinta ya nuna cewa rabon Tafida ce." Ina kallon Hauwa amman na kasa mgana Munnira ta karɓe da cewa" Nima haka na ji wallahi. Kun san wacece ta min mganar? Hauwa ce ta girgiza mata kai ni dai ko motsi ban yi ba "Suwaiba ce fa kwanaki da ta zo gidana ta ke min zencen. Wai Anty Bahijja ta ce wannan karon Gimbiya Rabon Tafida ne. Shi ya sa ma wai ƙila aka dawo da ita wajen Nene." Hauwa ta ce" Ni kaina na yi mamakin dawowarta. In aiki ne ai ba kullum ta ke zuwa ba kuma tunda tana da mota za ta iya zuwa a ranar kuma ta koma gida." Munnira ta ce" Har Nasir na yi ma mgana ya ce mini shi bai sani ba gulma ce ta mu ta mata. Amma wallahi Sadiya na hango gaskiya ba rami me zai kawo mganar rami? Da man ta yi ta shige masa ni fa wallahi haushi ta ke ba ni." Hauwa ta yi tagumi kafin ta ce" Ni kaina na fara hango hakan. Mganar fa daga bakin ƙannen Gimbiyar ta fito. Kin ga ko sun ji ana mganar ne."   Ganin yadda na yi shuru kawai ina sauraran su ya sa Hauwa ta dafa kafaɗata tana faɗin" Kar ki damu Sadiya. Ni na san ko auranta Yallaɓai ya yi ba za ta sha gaban ki ba." Munnira ta taɓe baki kafin ta ce" Ni wallahi da wata ta waje ne wacce ba a sani ba. Amma wannan Gimbiyar fa ban so. Sai Sadiya ta zama mujiya Allah su Anty Bahijja ware ta za su yi daman ya ya a ka cika? Hauwa ta yi ajiyar zuciya kafin ta ce" Da wannan kuma da wanman." Munnira cikin jin haushi ta ce" Har fa wani suna take kiran shi Daddy shi kuma ya ce mata me ne ma? "Daughter" Na faɗa ina kallon Munnira da ta yi tsaki kafin ta ce" Ke kuma wai duk kika ƙyale? Suna waya to? Sai na gyaɗa kaina kafin na ce " Suna yi mana." Gabaɗayansu suka kalleni cikin mamaki sai na yi mirnishi kafin na ce" To ai ban isa na hana shi yin waya da ita ba tunda yar uwanshi ne ko da na aure shi suna tare. Hauwa Munnira daman tun da na ji Mijin Gimbiya ya rasu da irin hidiman da ta ke yi ma yarana na san gwara na shirya domin watan wata rana ko Yallaɓai bai yi tunanin auranta ba za a tusa masa tunanin. Bakomai in ma ya auro ta fatana Allah ya zaunar damu lafiya abu ɗaya na sani ba zan yi ma Yallaɓai baƙin ciki domin ya ƙara aure ba. Sannan ba zan yi faɗa da dangin shi ba amma na kudiri niyar in sun yi mini hallaci na yi musu in ba su yi mini ba wallahi ba zan yi musu ba sai dai gayyar ta watse." Munnira ta ce Hmm! Ta ma kasa mgana Hauwa ce ta ƙara ba ni hakuri da cewa kar na damu tana da tabbacin Yallaɓai ba zai taɓa juyamin baya ba. Kallonta kawai na ke yi amman ban yi magana sai dai kuma a cikin raina sai da na ce Namiji ne fa mai chanza launi daga baƙi zuwa fari lokaci bayan lokaci. Muna cikin yin mganar ne Yallaɓai ya kira ni a waya ya ce na fito za mu tafi ya na faɗa min yara har sun yi barci. Jin haka yasa gabaɗayanmu muka fito zuwa ɗaƙin Nene muka yi musu sallama su Suwaiba nan duk anan gida za su kwana. Mu muka fara tafiya Hauwa Musbahu ne zai kai su gida ko a fuska ban nuna ma Yallaɓai wani abu ba har muka koma gida. Marwa na bari da Baby na ce ta yi mata shirin barci. Ni da Yallaɓai muka wuce bedroom ɗim mu kafin mu kwanta sai da muka yi soyyyarmu sannan muka yi wanka muka kwanta duk da yadda na ke jin wani abu ya tsaya min a ƙasan zuciya amman ban nuna masa ina ƙoƙarin gaya ma kaina gaskiya. Ban isa na hana shi abinda Allah ya ce ya yi ba. Sannan ba zan yi masa baƙin ciki domin ya ƙara aure domin samin wasu zuru'an ba. Amman a ƙasan raina ina tunanin saboda akwai ta in da na gaza ne. Na gaza ta bangaren ba shi zuru'a masu yawan da ya ke fata. Washegari tun safe muka shirya. Na yi abinci shinkafa da miya da nama sai salat ɗin da na saka shi a wani filet Babba muka rufe da leda Karfe goma a Ɗorayi ta yi mana Yallaɓai ya kai mu,  ranar kaya iri ɗaya muka saka da ni da yara har Marwa Atamfar da Yallaɓai ya yi mana mai adon ja a jikin ta. Na yi kyau sosai gashi daman na ɗan rame kaɗan sai kayan ya zauna a jikina riga da sikat na yi.   Duk sammakona sai da na tarar da Yaya Balki a gidan mun je ba daɗewa sai ga Ma'u itama da na ta gayyar yaran sai ƙanwarta Zainab sai Anti ƙila can ta yi mata salla Itama da abinci niki niki. Wannan sallar daman su Yaya Hamza ba su zuwa salla gida sun fi zuwa a sallar layya. Can ba jimawa sai ga Zaitunan Yaya Abubakar sai ga Yaya Murja ta ƙarshen ita ce Yaya Aina da ƙannen Marwa gifa fa ya cika ya yi albarka tun da kaf ɗin mun mun zo da yaran mu sannan har Datti a gida ya yi salla Alhajinmu ya ji daɗi bakin shi har kunnen gashi ga jikokinshi suna ta fira Gwaggo ma ta kasa zama sai ina za ta saka damu take yi. *Janafty* *TURKEN GIDA.* *Wattpad:Jamilaumar315* *Arewabooks:Jamilaumarjanafty* *SADAUKARWA GA BARRISTER SALAMATU DOMA(MOMMY* Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Kz6koexT4Yj4o2zO4xVzrU INA MATAN DA SUKA DADE SUNA NEMAN MAGANIN SANYI WATO INFECTION MAI KYU BASU SAMUBA, ANYI MAGANI ANYI MAGANI HAR ANGAJI, TOH KICE ALHAMDULILLAH, SABODA ALLAH YA HADAKI DA MAGANIN DA ZAI MAGANCE MIKI KO WANE IRIN CUTTAN SANYI WATO INFECTION DA YA KAMAKI CIKIN SATI GUDA DA YARDAN ALLAH. SHIGO GIDAN BUZAYE WAHALANKI TA YANKE HAJIYA💃💃 INA MAI NEMAN KAYAN GHARA ZAFAFA, MASU INGANCI, MASU KARFI, WANDA ZAI KANKARO MIKI MUTUNCINCI DA KIMARKI, WANDA ZASU DAWO DA HANKALIN ME GIDA GAREKI, SU SA YA MAKALE MIKI DA ZAZZAFAN SOYAYYANSHI, YA DINGA SAKE MIKI KI WARWASA YANDA KIKE SO💃💃 TO ER UWA SHIGO GIDAN BUZAYE KIGA IKON ALLAH DON KUWA ALLAH YA KAWO MIKI KARKEN MATSALANKI NA RASHIN DACEWA DABAKYAYI NA KAYAN GHARA😁💃💃 KUSHIGO GIDAN BUZAYE KU GYARA KUGA IKON ALLAH *🅿️20* Rahila ce jirgin danƙaro ita ce karshen zuwa har sai da na yi mata tsiyan tana kusa amma itace ƙarshen zuwa. Tana dariya ta ce " Ni fa na ɗauka ni ce ma farkon zuwa kawai sai na ga gida ya cika." Muna ta mata dariya ni da Ya Balki. Amina ta kira waya da ta ji gida cike kowa da kowa na nan kamar ta yi kuka ta ce ta yi missing. Ta so zuwa amma ba ta samu dama ba sai dai ta ce sallar layya in sha Allahu da ita za a yi. Ya Auwal kuma ni na kira shi a waya ya ce sun ɗan fita da laila ne da yara gidan shuru sallar duk ba daɗi sai ya ce na kunna data ya kira Video call nan ne fa suka gaisa da kowa har da Gwaggo da Alhajinmu an kai musu sun yi mgana da juna. Ya Hamza kuma na kira wayarsa ba ta shiga ba sai na kira na Khaleesat. Ita ke faɗin ya kwanta ashe bai jin daɗi zazzaɓi kuma ya hana a faɗa ma kowa. Muna cikin wayar ya tashi sai ta bashi wayar dukkanmu muka karɓa muka yi masa sannu da jiki ya ce ya ji sauƙi ya je asibiti maleria ne an yi masa allura kuma an bashi mganguna. Ba mu jima muna mgana da su ba tun da bai jin daɗi daga nan muka yi masa sallama da fatan samun lafiya. Datti dai za su fara jarabawa Jiya da yamma ya koma makaranta.   Dukkan mu muna ɗakin Mama daman yawancin in dai mun zo gida mun fi zama ɗakin Mama. Gwaggo na ɗakin Alhajinmu suna ta fama da yara. Hira muke yi na can garin mu Yashe bayan sallar nan akwai bikin autar su Ya Muntari wato ɗiyar Baba Aminu kenan Yaya Aina ce ke mganar haɗa guddumuwa daman haka muke in sha'ani ya tashi sai mu haɗa kanmu kowa ta kawo abin da ta ke dashi mu haɗa mu ba ma Gwaggo ita kuma sai ta nuna ma Alhajinmu ya yi ta godiya kuma in sha'anin ya tashi ko ba dukkanmu. Yaya Murja da Yaya Balki suna zuwa ni ce ma ban cika zuwa ba sosai Rahila daman can ne tushen Mijinta tana yawan zuwa amma wannan karon tunda na ji bikin na ce sai na je Yashe na yi sati in sha Allahu tun da na daɗe ban je ba tun ina da cikin Baby da babbar ɗiyar Baba Sani ta rasu muka je gaisuwa kuma a ranar muka dawo ba mu kwana ba.   Bikin bayan salla da sati uku ne. Yaya Aina ta ce ana jibi biki za mu tafi saboda Matar Baba Aminu magajiya mai yi ce ba ta wuce duk wani sha'anin mu ko ba ta zo ba ƙannen Yaya Muntari za su zo gaskiya tana da ƙoƙari daga ita har Baba Aminun suna da riƙo kan zumunci. Muna cikin hiran ne Marwa ta shigo sai dai ta ce sannanun ku gabaɗaya a ka amsa mata in da na ke zaune ta nufa tana faɗin" Umma Baby ta jiƙa kayanta da ruwa." (Daman Umma ta ke ce mini kamar yadda su Jidda ke kirana.) Kai na jinjina kafin na ce" To ai sai ta zauna dashi. Domin ban zo mata da wasu kayan ba." Da sauri ta ce" Gwaggo ta ce a cire rigar a shanya kar zazzaɓi ya kamata." Kafin in yi mgana Rahila ta karɓe da cewa" To ba wasu kayan? In sanyi ya kamata fa" Yaya Balki ce ta yi mgana wannan karon da cewa" Sadiya ce fa da tsiyarta. Ba za a rasa wasu kayan su Baby a gidan nan ba." Yaya Murja na gefe ta ce" Ko ba na ta ba. Ba za a rasa kayan da za ta saka kafin na ta ya sha iska ba." Muna cikin mganar Marwa ta fita sai ga Gwaggo ta leƙo ta na faɗin ita ta ce a cire mata rigar a shanya ta samu wata riga ta ba ma Marwa ta saka mata na amsa mata da to Gwaggo. Yaya Balki ce ke mganar ta ga Marwa ta yi mata girma ne a ido ina mirmishi na ce" Ai na kusa yin suruki in sha Allahu." Yaya Balki ta amsa da Allah ya sa. "Aina can Marwa ta yi salla gidan Sadiya ne?   Ya Murja ta faɗa ta na mai kallon Ya Aina wacce ta amsa da mata da cewa" E. Tun kafin ta dawo daga makaranta ta dame ni da ni Mama a gidan Umma Sadiya zan yi salla na ce to. Ta na dawowa ta gaya ma Baban shima yana dariya ya ce to yar gidan Umma Sadiya a dawo lafiya." Ina mirmishin jin daɗi na ce" Ai wallahi na ji daɗin haka. Ni da za ku bar mini ita a wajena Ya Aina." Yaya Balki na dariya ta ce" Topha ƴan mata ba su ishe ki ba ne Sadiya? "Ina fa suka ishe ni. Ban ƙi dozin ba Yaya Balki." Muka saka dariya gabaɗayanmu Rahila ce ta ce" Sai Ya Aina ta baki. Ki haɗa da Jidda ki riƙe gabaɗaya." Ma'u na gefe ba ta ce komai ba ta na latsa wayarta. Ya Murja na sauraran mu amma ba ta yi mgana ba Ya Aina ke faɗin Marwa za ta fara pratical a asibti kuma babanta ba zai bari ba amma don ta riƙa zuwa miki  hutu lokaci bayan lokaci ba zai ce komai ba.   na marairacewa na ce" Haba Ya Aina. In kika saka baki zai bari mana." Dariya kawai ta yi ba tare da ta yi mgana ba Yaya Balki ce ke faɗin" Topha! Lalle lamarin Sadiya azimin ne. "Da gaske take yi." In ji Rahila ni kuma na juya ina rantse musu da gaske nake yi. "To ke in kina son ɗauka shi Yallaɓan na ki na so ne? Ya Murja ta faɗa tana kallona da sauri na ce" Haba Ya Murja na ɗauka ke mai shaidar Yallaɓai na ne. Ba Marwa ba ko wacce bai sani ba ne na kawo na ce ina so zan riƙe wallahi ba zai ce komai ba. Ballatana ma Marwa shi ya fara cewa ko za mu karɓo Marwa ne ta dawo wajen mu da zama Sadiya? Shi ya sa ma kika ji na yi mgana." "Oh." Kawai ta ce ba ta ƙara mgana ba. Yaya Balki ce ta karɓe mganar da cewa" Kuma fa hakane. Yallaɓan na ki ba shi da matsala gaskiya." Rahila ma ta amsa da cewa" Shi da ke son yara. Allah ne dai bai bashi da yawa ba." Ita dai Yaa Aina ba ta ce komai ba sai dai ta na ta mirmishi daga karshe ta kashe mganar da cewa babanta ba zai bari ba ni kuma na ce zan sako Yallaɓai a gaba mu zo tambaya Rahila na dariya ta ce" Shike nan ma an kashe boss ɗin." Muna ta dariyan mu cikin nishaɗi. Daman fa ko haɗuwa aka yi waje ɗaya Ma'u da Ya Murja sun fi tsame kansu gefe ana hira sai jifa jifa suke saka baki tun ballatana ma in ina wajen. Ni kuma ban damu da su ba in suka sako ni na yi da su in ba su sako ni ba na juya na yi da waɗanda ke yi da ni. Zaitunan Yaya Abubakar tana ɗakin Gwaggo tun da ta zo sai barci kamar wata kasa Yaya Balki ta ce Allah ya sa ba ciki ne da ita ba Ma'u ta kwashe da dariya ta na faɗin" Kuma kamar kin san ta yi yaye ba." Ya Aina ta ce" Kai wannan mata ta Abubakar. Allah ya sauwaƙe." Ni kuma sai na kada baki na ce" Ku barta ta haihu. Iya rabon ta a duniya fa za ta haifa. " Sai Rahila ta ce kuma gaskiya ne. Gwaggo ce ta leƙo ta ce an kira salla ga ƴayanmu can har sun yi alwala mu ma sai mu tashi jin haka yasa muka firfito domin yin alwala ni ban samu buta ba sai na zauna ina jira Anti ta gama da na ta butan ta bani sai da ta idar da alwalan sannan ta kawo min na amsa ina faɗin" Su Anti an zama yan mata." Ta na dariya ta rufe fuska kafin ta ce" Anty Sadiya ina goron sallah na." Kai tsaye na ce" Gorom sallah kike so? Sai ta gyaɗa min kai. Ni kuma sai na rausayar da kai kafin na ce" Goron salla ai a gida ake ba da wa Anti. In kina son goron salla sai ki zo gidana ki karɓa. Yanzu ma kin makara salla ta wuce sai dai kuma ta layya in muna raye." Ita Anti ba ta damu da mgana ta ba cikin dariya ta ce" Kai Anty Sadiya." Nima ina mata dariyan na ce" Ƙwarai Anti. Salla layya in kina son goron salla ki zo gidana da wuri ni kuma sai na cika miki jaka da kuɗi." Gwaggo na bakin famfo tana alwala ta na jin mu ta dai yi mirmishi ba ta saka mana baki ba. "To Anty Sadiya in sha Allahu zan zo. Wannan salla a gidan Umma Ma'u na yi shi ya sa." Ina mata mirmishi na ce" To ai shiken nan na ma san Ma'u ta cika miki jaka da goron sallah ba ki buƙatar tawa ko? Har ga Allah ni a wasa na yi mganar kawai sai gani na yi Ya Murja ta bankaɗo labule ta fito da hijabi a jikinta da alamun ta idar da salla ne kallona ta yi daga sama har ƙasa nima ko cikin mamaki na ke kallonta sai kawai ta daka ma Anti tsawa ta na faɗin ta wuce ta je ta yi sallah sai yarinyar ta wuce ɗakin Gwaggo da sauri. Kamar zan yi mgana sai na fasa na fara tafiya wajen famfo Gwaggo ta taso za ta shiga ɗakinta. "Ke Sadiya.." Ya Murja ta yi mini kira cikin gatsali sai na juya ina kallonta cikin mamaki. Ba ma ni kaɗai ba hadda Gwaggo. "Me ya faru Ya Murja? Na faɗa ganin kamar tana sakin huci kawai sai ta nuna ni da yatsa ta na faɗin" Daga yau in kina so ki yi min rashin kunya ki zo gare ni kai tsaye ne ba sai kin rakuɓe a jikin ƴa' ta kina gaya min mgana ba. Ba na son rashin kunya." Galala na yi da baki ina kallonta kafin na samu zarafin mgana Gwaggo ta tsawarta da cewa" Murja me kuma ya kawo wannan mganar? A fusace ta ce" Ba ki ji mganganun da ta ke faɗa ma Anti ba ne? Ta nuna kamar da gayya ne ban tura Anti gidanta ba na tura ta gidan maƙiyarta Ma'u ba. Duk na fahimci mganganunta." Gwaggo ta yi tsaki kafin ta ce" To ni ban ji haka ba. Mganar su kawai suke yi na tsakanin uwa da ƴa." Nan fa Ya Murja ta ce ita fa k a taufau da ita na ke yi. Ƙara nuna ni ta yi da yatsa kafin ta ce" Daman ba tun yau ba kin sha faɗan wai na fi son Ma'u da ke da ita kawai na ke shiri yayana ma gidanta suka sani. To yadda kika faɗan ne domin Ma'u ta fi ki ladabi da biyayya sannan ita ta ja ƴa'ƴana a jiki ke kuma da ba ƙi kaunar su ba ki ja su a jiki ba. Kin ga ko kar ki ga laifin su in ba su je in da kike ba. Gidan kuma Ma'u da ki ke jin haushin suna zuwa yanzu suka fara zuwa. Sai dai baƙin ciki ya kashe ki Sadiya" "Murja me ye haka don Allah.? Ya Aina bayan ta fito daga ɗakin Mama itama sanye da hijabi ita da Ya Balki da Rahila. Ma'u dai ba ta fito ba ni kuma tsabar mamaki ma na kasa magana. "Ya Murja Alhajimmu na ciki fa. Gaskiya wannan ba girman ki ba ne. Sadiya fa ba da ke ta ke mganarta ba." A fusace Ya Murja ta ce" Ba za ku gane ba ne. Ni na san ga in da ta dosa. To me ye na damuwa don ƴaƴana ba su je in da ta ke ba. Marwa da kika zaɓa kina so ita ai kin gayyaceta kuma ta je suma in kika nuna kina so su je ɗin za su je." Sai a lokacin na fahimci haushina ta ke ji saboda Marwa. Kai wannan mata ta ɗoramin karan tsana. Ba na so na yi hayaniya saboda Alhajinmu kawai sai na yi mirmishin takaici kafin na ce" Ki yi hakuri Ya Murja na ga ƙin ɗau zafi har ga Allah ba da wata munafa na faɗi mganar da na faɗa ba. Amma in ta ɓata miki rai Allah ya baki haƙuri. Mganar Anti na zuwa gidan Ma'u ban taɓa sawa a kaina ba domin da ni da Ma'u  duk ɗaya ne. Ke ma kuma ina so ki gane wani abu da Anti da Marwa ɗaya suke a wajena ba Bambamci."   Ina gama faɗin haka na juya na wuce wajen famfo ina taran ruwa a buta. Na san dukkansu sun yi mamakin sanyina har sai da Gwaggo ta ce" Shike nan Sadiya kin gama magana. Ke kuma Babba kwabo kin ji kunya tunda har yau Sadiya ta fi ki hangen nesa." Ganin ban kulata ba ya sa ta koma ɗaki fuu. Kuma kowa ita ya ba ma rashin gaskiya a wajen. Sai bayan da na ɗauro alwala na shigo cikin ɗakin ne Ma'u ta ke ce min" ki yi hakuri Sadiya ki fahimci Ya Murja don Allah itama ba da wata munafa ta yi miki mganar ba.' Kallonta kawai na yi ni kam wani makircin Ma'u ne ban gani ba sai kawai na ce" Bakomai. Ita za ki ƙara ba ma hakuri saboda na ga kamar ta ɗau zafi da ni." Ina gama faɗin haka na saka Hijabi na ta da salla. Bayan na idar sai muka ci abinci na ga dai Ya Aina ta keɓe da Ya Murja na kuma san faɗa ta ke yi mata shi ne na ga ta ɗan saki ranta a raina na ce matar nan me na yi mata wai ta tsane ni ne? Muna cikin cin abinci sai ga Ya Abubakar ya shigo ganin abinci kala kala muna ci ya sa ya ce"Kai. A ina aka samo abinci nau'i nau'i haka kamar an samu sabon restaurant? Rahila ce ta faɗa masa kowaccem mu ta dafo abinci daga gidanta sai shima ya samu waje ya zauna ya na faɗin" To shi ne ana wannan shagali aka manta da ni? Ni ne fa the head of the family" Ya Balki ta ce" Mun ɗauka Zaituna ta yi maka kyakyawan beta kafin ta fito gida"   Ta faɗa ta na kallon Zaitunan da ke ta cin abincinta jin an taɓo bangarenta ya sa ta yi saurin cewa" Laa shi ya ce in taho ba sai na tsaya na yi abinci ba." Rahila ta ce" Ehem daman na san za a rina." Yaya Aina ke faɗin" Ke kam Zaituna ban san yaushe za ki wayau ba. Ko mu kin ga mun taho ba mu yi girki ba? Ga shaida nan tunda gashi nan kina ci in da kin dafa kafin ki fito mijin ki zai zo ya na neman abinci? Kanta na kasa ba ta yi mgana ba Yaya Abubakar ya wani girgiza kai kafin ya ce" Ƙyaleta Aina ta yi lokaci ne." Daga haka kawai ya miƙe ya ce ya na ɗakin Alhaji a kawo masa abinci. Zaitunan Ya Aina ta tasa ta ce ta saka mai ta kai masa ta na fita Ya Murja ta ce" Mata kamar mai almatsutsai" Ya Aina ta ce" Lafiyan ta ƙalau iskanci ne kawai da ta samu shi Abubakar ɗin mai sanyi." Ni dai ina jin su ban tanka ba ina ta cin abincina ni shinkafa da waken da Rahila ta dafa na ke ci su kuma su Ya Aina sun ci nawa sun kuma ci na Ma'u ita waina ce da Sinasir. Mganar gaskiya duk cikin mu Mijin Ma'u ya fi kuɗi kowa kuma ya san haka amma duk da haka dukkanmu ba za a ce muna cikin halin rayuwa ba dai dai gwargwado mazajen mu na da rufin asiri. Mijin Ya Murja ne ma sai a hankali domin ya samu matsala can kwanaki an kore shi daga wajen aiki ya fi shekara uku a gida amma dai an ce ya koma shi ya sa Ma'u ta samu dama tana taimakonta ita kuma kwaɗayi ya sa idanuwanta ya rufe. Ni ba na kyautar ganin ido ko ka gode min in na yi niyyar yi maka alheri na yi, in ban yi ba shike nan ba zan yi domin duniya ko kai da zan mawa ka yabeni ba ita kuma Ma'u daman halinta ne ta yi alherin da duniya za ta sani a yabe ta a kuma san tana yi ɗin da son nuna ita fa mijinta na da kuɗi domin in dai Ma'u ta san za a zo gida a haɗu ƙarshen kayanta a kyau da tsada ta ke sakawa. A fuska ba ta nuna wani abu amma ga ni da na san halinta ni na san ta na da halin son a sani.   Yanzu ma muna cin abincin ta na ba da labarin Alhaji Mustapha ya ce zai ba ta jari na miliyan biyar ta fara kasuwanci shi ne take neman shawarammu wata sana'a za ta fara. kowacce na faɗin albarkacin bakinta nima sai na tofa nawa na ce ta saro dogayen riguna da takalma da mayafai na mata ta fara saidawa mu gani ko za su tafi. Sai Ya Aina ta ce yauwa ta ƙara har da atamfofi da kayan yara ni kuma sai na ce kayan yara ta jinkirta tukunna zuwa gaba ta fara da waɗanan dai ta gani yadda kasuwan za ta kaya. Cikin mirmishi ta ce" Haka ma Shema ta ce. Da ya ke mun yi mganar da ita ta waya. Ya ce dai na tsaida shawara visa na fitowa Egypt za mu je a can zan yo sarin kayan nawa in sha Allahu." Ya Murja ta washe baki tana faɗin" Ma sha Allah. Allah ya sa albarka ƙanwata." Ta amsa mata da Amin Amin. Ita kuma Ya Balki ta ce " Sai ki faɗa ma Gwaggo da Alhaji su suka albarka." Sai ta ce za ta faɗa musu sai mata fatan alheri suke yi nima na yi mata ta re da fatan Allah ya sa a fara a sa'a ta amsa lokaci ɗaya ta na kallona kafin ta ce" Amin Sadiya. Amma fa kema ya kamata ki zo ki fara wata sana'ar zama haka ba daɗi." Wani abu ya tsaya mini a maƙogawaro. Ma'u ta bala'in raina min wayau. Kuma kawai sai su Ya Balki suka amsa da wallahi kuwa Sadiya. Rahila ce ke faɗin" Ita fa Sadiya Shagon saloon da gyaran jiki take son buɗewa" Ya Balki ta ce" To wannan ai lissafi ne me yawa. Ta dai yi tunanin fara wani abun kafin ta yi ƙarfin da za ta buɗe saloon ɗin." Duk yadda na so na yi mgana sai kuma na kasa. Da na so na mayar mata da martanin mganarta ne sai kuma na yi tunanin ina yi magana za a ce ni ce fitinanniya Ma'u ta yi min mganar arziƙi na maida shi ta tsiya   Sai kawai na kalli Ma'u nima sai na mayar mata da martanin mirmishinta kafin na ce" Kar ki damu ki maida hankali kan naki. Nima soon in sha Allahu Suprise zan ba ku." Sai ta ce Allah ya yarda ta na min wannan dariyan na ta na mugunta. Ya Aina ko sai faman mgana take yi ta na cewa sana'a ita ce mace ko da mijinki na maka komai to ka yi dogaro da kan ka ko domin wata rana. Ya Balki ta ce" Har da ma rayuwa Ya Aina." Rahila ma na ji tana fadin itama za ta fara awo a cikin gida Ya Aina ta ce kasuwanci mai kyau. ita Ya Aina tana saida kayan miya da kayan nau'in ɗanɗanon girki ita kuma Ya Balki tana saida gwanjuna. Ni ce daman ban saida komai sai Rahila Ma'u kuma daman tana nuna mijinta na mata komai sai yanzu ne ta zo da labarin za ta fara na ta kasuwamcin.   "Albishirin ku" Na faɗa ina musu mirmishi. Na gama cin abinci tuni har na sha ruwa na yi gatsa. "Goro fari ƙal." In ji Rahila da Ya Balki har suna haɗa baki. "Nan da kwana uku za mu cika shekara sha biyar da aure ni da Yallaɓai na. Haka ma Rahila da Ya Muntari." Na faɗa ina musu mirmishi. Ya Balki ta fara cewa" Ma sha Allah. Allah ya ƙara muku zaman lafiya. Kai ashe kun daɗe kamar jiya ne na ke ganin bikin ku fa ke da Rahila? Rahila na dariya ta ce" Sadiya ta na lissafi ni fa mancewa na ke yi. Ko da muka yi shekara goma sai da na ga sun yi walima ne na ce ma Ya Muktar yau auran mu shekaru goma Cif." Ya Aina ta ce" Shekarun suna gudu ba wuya. Allah ya ƙaro muku zaman lafiya da kwanciyar hankali ya raya muku zuru'a." Muka amsa da Amin Ya Murja ma ta yi addu'a muka amsa mata. Sai Ma'u da ta gyara zama tana fadin" Ma sha Allah. Allah ya ƙara ɗankon kauna Mrs Yallaɓai da Mrs Ya Muktar." Ni ce na amsa mata Rahila ta na jin kunya Zaituna ce ta yi karaf ta na faɗin" Sadiya akwai walima ne? Ina mata dariya na ce" Akwai amma ta iya ni da Yallaɓai ce da yara." Ma'u ta ce" Allah? Ban damu kenan? Ina mata fari na ce" Ai kun gama na ku tunda kun yi addu"a. Ya Aina ta ce" Shi ne ko babban mgana." Zaituna na kallah ina faɗin" Tambayi Rahilan Hubby ƙila za su haɗa mana walima." Duka ta ɗaka min a cinya ta na faɗin" Sadiya ban son wulaƙanci." Kamar zan yi kuka na ce" Wai don na ce Rahilan Hubby shi ne har da duka? Rahila sai kawai ta balla min harara kunya duk ya kamata mu kuma gabaɗayanmu muka fashe mata da dariya. Sai ta ji kunya ta tashi ta fita, ta na fita Ya Balki ta ce" Daga Rahilan har Muntari masu kunya ne." Ya Aina ta ce" Wallahi ba su da hayaniya. Alhajinmu ya sha cewa tabbas an ijiye kwarya a gurɓinta."   Ranar yini muka yi ana ta hira a yi daɗi a yi tsiya bayan mangariba Gwaggo ta ce Alhajinmu ya ce kowacce ta yi shiri ta koma gidanta yinin ya isa haka. Jin haka yasa muka fara shiri saboda tun da Alhaji ya yi mgana to dole fa kowa ta kama hanya. Ni dai Yallaɓai na kira sai ya ce bari a yi sallar isha'i sai ya zo mu tafi gida. Ma'u ta fara tafiya Alhajinta ya zo ɗaukansu ita da yara haka ya yi mana yayyafim kuɗi goron salla damu da ya'yanmu ban sam kuma nawa ya ijiye ma Alhaji da Gwaggo ba. Su suka tafi da Zaituna da ƴaƴanta za su sauke su a gida daga can na ji Ma'u na faɗa ma Gwaggo za ta biya gidan su Shema'u. Kafin ya zo daman Ma'u ta sanar da Alhajimmu da Gwaggo mganar jarin da ya ce zai ba ta su ka yi ta masa godiya da saka albarka. Nima da Yallaɓai ya zo mun je gaban Alhaji na faɗa masa nan da kwana kaɗan auran mu zai cika shekara goma sha biyar da ni da Rahila.   Alhajinmu ya yi mirmishi kafin ya ce" Ma sha Allah. Shekaru goma sha biyar masu albarka da tarin albarka zuru'a. Allah ya ƙara haɗa kawunanku. Haƙiƙa Yusufa da Muntari sun cika ƴaƴa tunda duk tsawon wannan shekarun ba su taɓa kawo min ƙaran ku da sunan kun yi musu wani abu ba hakan ma abin alfaharina ne. Allah ya yi muku albarka ya bar ku tare har jikokin ki." Kan mu na ƙasa ni da Yallaɓai muna ta amsawa da Amin Amin. Gwaggo na gefe ta na ta saka albarka kafin ta ce" Jiya ba yau ba. Allah ya ƙara muku zaman lafiya. Na tuna da Mama itama shekarunta a ƙasa kenan Allah ya jiƙanta ita da Hajiya gabaɗaya." Muka amsa mata da Amin Amin da za mu tafi shima Yallaɓai ya ba ma yaran su Ya Murja goron sallah Marwa dai ta ce za ta bi Ya Aina zuwa gida amma jibi za ta dawo. Yallaɓai ya ba ma Alhajimmu kuɗi da Gwaggo amma ban sam ko nawa ba ne. Daga nan muka yi musu sallama ya ɗauke mu zuwa gida.   Sai da muka koma gida har mun yi shirin kwanciya muna rumgume da juna Yallaɓai na shafa gashin kaina ya ce. "Sadiya ta." "Yallaɓai na" Na amsa masa cikin so da ƙauna. Sai kawai ya ce" Gani na ke yi kamar jiya jiya muka yi aure sai ga shi wai mun kusa cimma shekaru goma sha biyar da aure cikin yan kwanaki ƙalilan masu zuwa." "Nima haka na ke ji a zuciyata." Haka na faɗa masa na ke jin kamar jiya muka yi auran ashe shekarun sun tafi. Ƙara kamkameni ya yi kafin ya ce" Har yanzu ba ki sauya daga Sadiyar da na fara sani yar shekara sha tara ba." Nima ina mirmishi na ce" Kai ma har gobe baka sauya min a wannan gwarzon matashin da na aura a shekaru ashirin da bakwai ba." Sai kuma muka kalli juna ta cikin duhun ɗakin da ɗan hasken da ya kan shigo ta window ɗin cikin bedroom ɗin kafin ya sumbaci goshina ni ma sai na maida masa martani na sumbaci kumatunsa kafin mu koma mu kwanta yama ƙamƙame dani kamar za mu koma abu ɗaya. ****** Wed.13 JULY 2015. Rana ta ƙara zagayowa ranar da a irinta ne aka ɗaura mana aure ni da Yallaɓai a irin kuma ranar ne muka zama miji da mata. Jiya Yallaɓai ya dawo domin tun washegarin ranar da muka dawo daga Ɗorayi ya je kaduna sai jiya da daddare ya dawo. Kuma yau tun safe ya fita saboda Nene ta kira shi a waya tana son ganin shi. Bai ko tsaya a gida ya ƙarya ba ya fita wanka kawai ya yi. Su Jidda sun koma makaranta tun jiya sun tafi gidan ba kowa sai ni kaɗai Marwa ba ta dawo ba amma na kira Saude na ce ta zo ta ta ya ni mu gyara gidan.   Na ba da a yi mana cake babba sannan a gida na ce zan yi mana zoɓo muna da sauran naman sallah na ce kawai sai mu yi amfani dashi bayan haka na yi dambun nama da yawa ya na nan. Kawai dai yar walima ce daga ni sai mijina sai ƴa'yana. Saude ta zo da wuri tare muka gyara gidan ko'ina muka turare shi da turaren kamshi. Saude na saka ta dafa farar shinkafa tunda ina da miya da na yi a frigde sai na koma ɗaki na ɗau wayata na kira telanmu domin na ɗinka wani material mai kyau saboda wannan ranar na tuna masa yau zan yi amfani da shi sai ya ce zai aiko min da shi anjuma kaɗan. Sauran kazar da na siya wajen Surayya Halin yau na ce Saude ta ɗumama ta kai mini falon yara ni kuma sai na kunna data na shiga ina ganin saƙonni. Na ga group ɗin gidanmu ana ta tagging ɗina ina shiga sai na ga  Ma'u ce ta sanar da Anniversery ɗin mu ana ta yi mana fatan alheri ni da Rahila da Ya Muntari. "Mrs Injinya Allah ya ƙara dankon ƙauna." In ji Yaya Auwal shi kuma Ya Hamza tagging ɗina ya yi kafin ya ce" Yallaɓiya an gangara a bautar ubangiji.. Allah ya zaunar da ku lafiya." Haka suka yi ta ma Ya Muntari shaƙiyanci wai ɗankwali ya ja hula. Nima na shiga ina amsawa cikin farimciki. Na je na yi status amma ban saka hoto ba na dai saka Alhamdulillah! Sannan sai na rubuta" "Shekaru goma sha biyar cikin farinciki Alhamdulillah." Duk da ban yi caption ba sai aka fara mini mgana ta private ana mana addu'a yawanci duk yan makarantar mu ne da muka yi BUK tare waɗanda na ke da lambarsu.   Sai Adnan ɗin su Yallaɓai da ya gani ya ce min" Ma sha Allah Happy Wedding Anniversery Mrs Yusuf Muhammad Tafida." Musabahu ma haka ya ce mini" Ma sha Allah Allah ya ƙaro danƙon kauna ta Yallaɓai" Duk na amsa su. Sauran dai su Anty Bahijja ban ga sun gani ba. Zuwa na yi na zaƙulo hoton Rahila a waya na ranar sunan ɗiyarta da aka ɗauka na saka a status ɗina na c " Happy 15 years Wedding Annivesary Mrs Muntari Amini yashe(Hubby)" Sai na ƙara da emojin rawa da murna da dariya. Ina ta dariya saboda na san in ta gani sai ta yi mgana Ya Hamza ya fara gani kawai sai ya yi tagging ɗin status ɗin da cewa. "Ina na ki hoton? Ina dariya na ce ni ban da hoto ya ce ban isa ba. Kowa sai ya ce wai ina hotona da na Yallaɓai tunda na saka na Rahila. Ganin sun dameni ya sa dauko hoton da ranar idi ne ma Marwa ta ɗauke mu da wayata ni da Yallaɓai yana tsaye ni kuma na jinginar da kafaɗata a saman kafaɗarsa. Shi waya ma ya ke yi bai san ana hoton ba ni kuma ina mirmishi. Hoton ya yi kyau sosai yana sanye da farar shadda mai babban riga sai dai ya cire babban rigan. Ni kuma na saka leshi mai ruwan haske akwai zanen marun a jikin leshin sai ya haskani gabaɗaya. Ina mirmishi shi kuma Yallaɓai ya ɗan sunkuya yana kallona aka ɗau hoton shi na saka a kasan hoton sai na saka. "Barka da shekaru goma sha biyar cikin Aminci, soyayya, sadaukarwa a gare ka ya amintattace na. MRS HALIMATUSADIYA YUSUF MUHAMMAD (YALLAƁAI NA)" Na ƙara da gayyar emoji kafin ka ce kwabo duk yan gidanmu sun ce na tura musu  a group ɗin gida na tura hotunan tuni har sun sakamu a status daga ni har Rahila ni a bayan wannan sai na saka hoton Jidda da Baby shima da wannan sallan aka yi musu na yi mgana a ƙasa da cewa. " A shekaru 15 da auren mu ga albarka da Ubangiji ya yi mana nan. Allah ya raya ku HAUWA'U YUSUF MUHAMMAD(Jidda) DA MAIMUNATU YUSUF MUHAMMAD(Baby)." Kowa sai addu'a ya ke yi. Har ta Ma'u sai da ta ce na tura mata itama ta saka ta yi mana addu'a na amsa mata ko da bai kai zucci ba. Na duba Yallaɓai ba ya online na kuma kira layin shi ba ta shiga. Sai kawai na tura masa test massages. "Happy Wedding Anniversy Yallaɓai na" Na jira na jira amman bai turomin amsa ba sai na yi tunanin ƙila Network ya sa bai shiga ba. Da ya tafin na kira shi na ji ko Jikin Nenen ne ya tashi sai ya ce mini yanzu ya iso gidan lafiyanta ƙalau sai hankalina ya kwanta. Na yini cikin farincikina ina ta amsa wayoyin yan' uwa da abokan arzuƙa har mutanen fatakol Anty Zabba ta kirani ta na min fatan alheri Haka Munnira Hauwa dai wayar ta ya lalace ba ta sani ba. Amma har Nafisa Muhammad Sani mun yi mgana da ita, sauran yan gidansu Yallaɓai duk waɗanda suka ga status ɗina mun yi mgana hatta da Halima Autar su Yallaɓai amma ban ga Anty Bahijja ko Anty Maimuna sun gani ba Mimisco dai tana online amma ba ta duba ba. Ban damu ba, na cigaba da harkokina. Saude sai wajen uku ta tafi gida ni kuma salla kawai ke ta da ni a inda na ke Yallaɓai har lokacin bai dawo ba na kuma kira shi ta shiga bai ɗauka ba na ƙara kira shuru sai can ya turamin saƙon zai kirani ya je wani waje ne ni kuma sanin sabgoginshi sai ban damu ba. Na cinye sauran kazar hadin uwargida duka na sha gumba sannan na sha kayan marmari ranar ko abinci ban ci ba har Jidda suka dawo makaranta daman na gaya musu in Yallaɓai ya dawo da daddare za mu yi walima Jidda ta ce" Umma waliman mene? Ina mirmishi na ce" Na cikar mu shekaru sha biyar da aure ni da Abbanku." Da ya ke ta na da wayau sai ta ce" Umma Allah ya bar ku tare." Na amsa da Amin Baby kuma sai tsallen murna ta ke yi, ko kafin mangariba har ɗinkina an kawo min daman kunshin sallar da na yi bai fita kitso kuma daman bai dameni ba ƙara gyara kaina kawai na yi, na saka Jidda ta ƙara gyara gidan ta kunna turaren wuta. Ina da bloons na ma Baby ne jidda ta kama min muka hura su na ɗaura su a falon mu wajen guda ashirin kala kala. Sai falon ya yi kyau sai bayan mun yi sallar mangariba sannan mai cake ta aiko mini dashi da kwatance sai gashi a gidana ta online na siya ƙanwar wata mate ɗina ce da muka yi Buk ce ke  yi. Sannan na siya ma Yallaɓai gift wani agogo mai kyau 25k shima a wajen wacce muka yi BUK na siya daman kayan maza take saidawa na saba siyayya a wajenta in dai zan siyam Yallaɓai wani abu na gift wajenta na ke siya. Bayan mun idar da salla mangariba muka ƙara kawata falon a center table na ijiye cake ɗin sai muka zagaye shi da voul na nama da dambun nama cake, da donut sai lemuka da ruwa. wajen ya yi kyau muna gamawa na ce Jidda ta kashe hasken falon in an ji motar Yallaɓai yana shigowa sai a kunna daga nan na ce su je ta yi wanka ta yi ma Baby na ce su saka dogayen rigunan da na siya musu yan kati ita na Jidda riga da wando ne. Baby kuma doguwar riga ce kala ɗaya na siya musu mai kalan baƙi da fari. Nima na shiga bedroom ɗina na tuɓe na faɗa Tiolet na yi wanka amma a ƙasan raina ina tunanin ina Yallaɓai ya je? Ko kaduna ya je? Ya ce zai kirani amma shuru har na fito wanka ina wasi wasi. Daman na yo alwalata ana kiran isha'i na kabbarta salla bayan na idar ne na zo na zauna gaban madubi na tsantsara kwallya mai ƙayatarwa. Na gyara gashina na sake shi baya na yi ɗauri mai kyau ɗinki riga ds sikat ne sun kamani sun yi mini cif a jikina haka na yi ma kaina barin turaren humra ko'ina na gifta ina tashin kamshi na saka wani takalmina baƙi mai ɗan tsini kaɗan ina tafiya ya na ɗan ba da sauti kaɗan ƙwas! Ƙwas   Falon yara na shiga na gansu sun yi kyau suma. Jidda ma ta ce" Umma kin yi kyau" na ce na gode  sai na ja su muka yi ta ɗaukan hotuna sun ɗan yi ma duhu saboda dare tare muka zauna sun kunna cartoon ni kuma waya ce a hannuna ina ta kiran Yallaɓai wayarsa a kashe tun ina duba agogo ina saran dawowar Yallaɓai har na sare Baby ta gaji har ta fara barci ita kanta Jiddam ma barci ta ke ji. "Umma Abba bai dawo ba? "Yana kan hanya in sha Allahu." Na faɗa mata cikin karfin hali. Tashi na yi na fara zagayen falon ina yi ina duba agogon wayata. Tara da rabi ta yi shuru sai hankalina ya tashi na fara tunanin ba lafiya goma na yi na ce bari na kira Nene na ji ko yana can ai kuma ya san da ina gida ina jiran shi. Na latso lambar Nene kenan zan kira sai kira ya shigo mini na ɗauka Yallaɓai ne jikina na rawa na koma na zauna sai dai kuma sunan wacce ke kira ne ya sa sai da gabana ya faɗi Ras! Haka kurum na ji kamar ba alheri ba ne ya sa ta yi min wannan kiran karfe goma na dare. "Ma'u ce.'   Jikina sai ya kama rawa har ta katse ban ɗauka ba. A ƙoƙarina na kira Nene amma ba ta bari ba kawai sai ga wani kiranta ya ƙara shigowa cikin dauriya da shahada na ɗaga kiran "Ma'u." Na faɗa kafin ma na yi mata sallama. Sai ta amsa mini cikin yanayin muryanta amma cikin farinciki. "Na'am Sadiyar Yallaɓai." Yadda ta faɗi sunan ne sai na ji ban yarda da ita ba. Kafin na samu zarafin mgana ta cigaba da faɗin" Na san za ki ce kira cikin daren nan ko? . Da sauri na ce" E ina fatan lafiya." Sai da ta yi wata irin dariya kafin ta ce" Lafiya sumul. Murna cika shekaru sha biyar da aure na kira na yi miki sannan tare da ba ki wani kyakyawan albishir." Sai kawai na ji zuciyata ta tsinke amma sai na ɗaure cikin karfi hali na ce" Na gode. Ina jin ki wani albishir ne wannan da ba za ki iya jiran safe ba ki ka kira cikin daren nan? Tana dariyan nan na ta na mugunta ta ce" Ba na so wani ya rigani ne. Na fi so ki fara jin wannan albishir ɗin daga bakina." Juyawa na yi sai na ga Jidda har ta fara barci daga kan kujera sai kawai na miƙe na buɗe kofar falon Yallaɓai na shiga na maida ƙofar na rufe a cikin duhun nan na lalubi kujeran dining na ja na zauna ina faɗin" Uhm ina jin ki Ma'u." "Zan kashe wayata yanzu. amma ki kunna data ki hau whatspp na tura miki saƙo." Ko kafin na ce wani abu ta kashe wayarta.  Ni fa na gama sakankancewa daman ba alheri Ma'u za ta nuna min ba. Amman ban taɓa tunanin ganin abin da na gani ba. Jikina na rawa na buɗe data saƙonni na shigowa amma ba ta su na ke ba Ma'u na ke nema ina ko ganin ta tura mini abu kamar hoto na faɗa hannuna na rawa na danna sama yana buɗewa. Wallahi tallahi yana buɗewa ne amma kamar yana buɗewa da gudun numfashina ne. Yana gama buɗewa na ji kirjina ya amsa. Kaina ya sara, hannunawana sun fara  ƙarkawa saboda jikina da zuciyata suna rawa ne a lokaci ɗaya a lokacin idanuwana sun firfito ba domin na ji mamakin abin da na gani ba ne. Sai domin ban taɓa tsammacin shi a lokaci kusa haka ba. Ina wannan rawan jikin da na zuciyan kiran Ma'u ya sake shigowa ban ɗauka zan samu kuzarin ɗaukan wayarta ba amma sai gashi na ja na ɗauka na kuma ƙarata a kunnina duk da yadda zuciyata ke gudu da sauri da sauri.   "Ina fatan kin ga irin kyakyawan albishirin ɗin da na ke so na gaya miki ko Sadiya? Runtse ido na yi zuciya na fat fat! Amma sai wata zuciyar ta ce Sadiya kar ki bari a ga gazawarki daman shi Ma'u take jira kamar an dake ni na dawo hayyacina sai na saki wani mirmishi wanda ya fi yin kuka daɗi na ce" Haba ai kin makaro Ma'u domin Yallaɓai ya riga ki yi mini wannan albishir ɗin' Shuru ta yi domin ni na san ta yi mamakin jin kalamaina. Ban bari ta ƙara mgana ba na ce" kin yi gaggawa Ma'u da kin jira da ni da kaina zan kira ki na faɗa miki Yallaɓai YA ƘARA AURE" Ban ƙara ba ta wata damar mgana ba na cigaba da faɗin" Walimar da na shiryama ma a gida saboda Anniversary ɗin mu ne da kuma taya shi Murnan ƙaruwan da ya samu na aure." Ina gama faɗin haka kit na kashe wayar saboda sai na ji kamar santsi na ja na ina shirin na sumulmiyo daga kan kujeran da na ke zaune. Sai na kama jikin kujeran da hannuna ɗaya na ƙanƙame jikina ba inda ba ya rawa. Zuciya ta da tunanina sun tsaya waje ɗaya cak na kasa yin ma wani tunani. Ji na ke yi kamar ina zaune ne amma jiri na ke gani shi ya sa na ƙamƙame kujeran da na ke zaune amma ban san lokacin da na ji na sulmiyo ƙasa ba.  Sai ga ni zaune a kan mazaunaina a ƙasan tayel ina kokawa da numfashina wayata ta yi zaman dirshan a kan jikina na saka hannunawa da suke rawa na ɗauka na buɗe na koma whatpps na shiga kan sunan Ma'u ina kallon hoton da ta tura mini sai a lokacin na lura da in da Ma'u ta ga hoton.   Sunan Anty Bahijja ne a saman sreenshoot ɗin da ta yi, sannan hoton na GIMBIYA CE(SAUDATU) tsohon hotona kamar ma a gidanta na Abuja ne kafin mijinta ya rasu. Tana tsaye a falon gidanta a lokacin ta na mirmishi ta saka wata doguwar riga ne a hoton. Abin da ya fi ɗaukan hankalina shi ne kalaman da aka yi amfani dashi a ƙasan hoton. "Allahu Akbar alƙawarin Allah ya tabbata. Congratulation Mrs Yusuf Muhammad(Tafida)." An ce wai ka yi ma hawaye rahama ne. Sai yanzu na amince da wannan mganar, na kasa jin kuka ya taho mini ma idanuwana sun ƙeƙashe. Shi kenan ta faru ta ƙare an yi ma mai dami ɗaya sata. Daman shi ne suprise da Yallaɓai ya ke ta faɗin zai ba ni? Lalle ko na karɓi kyakyawan suprise. Ban san lokacin da ya shigo gidan ba domin ban ji ƙaran buɗe get da shigowar motar sa ba ba.  Sai da na ji lokacin da ya ke saka ɗan makulli yana ƙoƙarin buɗe kofar falon kamar an jani an mikar dani tsaye sai ga ni a tsaye a kan kafafuna. Wayata kuma tana jimƙe a hannuna. Ya buɗe kofar kenan ya shigo ni kuma sai na fara takawa ƙwas ƙwas ina ji jikina na rawa amma na daure na isa ga makunnin wuta na kunna dai dai yana ƙoƙarin ciro wayarsa daga aljihu domin haska fitila. Haske ya gauraye falon. Ya bi ko'ina da kallo dai dai lokacin kuma wasu daga cikin bloons ɗin da na saka afalon suka fashe ji ka ke yi tus! Tus! Sai da ya ɗan waiga sannan  ya juyo yana  sauke kallon shi a kaina dai dai ni kuma ina tsaye a gaban shi na harɗe hannayena a bayana. Na ƙasa takawa zuwa gare shi,  saboda sai na ga kamar ba Yallaɓaina bane kamar wani ne wanda ban saba dashi ba, sai na ke jin kamar wannan Yallaɓan yanzu akwai wata tazara da ya shimfiɗa a tsakanimu daga yau. Kafafuna sun yi sanyi kamar gara ya kama su in na ce zan cire ƙafa zan iya zubewa saboda firgici. Shi ma sai na ga ya tsaya yana kallona amma kuma bai tsawaita ba da sauri ya kauda kanshi. Mirmishi ya ke gayyato ma fuskarshi sai dai ban bari ya gayyato ma kanshi ba ni na fara gayyato ma kaina mirmishi lokaci ɗaya ina faɗin. "HAPPY 15 YEARS WEDDING ANNIVERSARY YUSUF MUHAMMAD TAFIDA." Na faɗa ina kallon ƙwayar idanuwanshi. Yadda ban je gare shi domin na rumgume shi ba. Shima bai yi saurin takowa gare ni ba. Ajiyar zuciya ya sauke yana mai ijiye ledojin da ya shigo da su a hannun shi a ƙasa wanda ban san abin da ke ciki ba. Kafin ya ɗago kansa cikin ƙwayar idanuwanshi na ga rauni. Kasala tsoro da wani abu da na kasa ganewa. A kuma yanayin ya  kira sunana cikin wata irin muryan da ban taɓa sanin Yallaɓai  na da ita ba. "HALIMA." Zan iya kirga sau nawa Yallaɓai ya taɓa kirana da sunana Halima, a da in ya kirani ina jin kaina ya yi girma. Amma ban da yau domin sai na ji kamar ya kwarara min ruwan zafin a cikin jikina. Har ina jin tururunshi da hucin shi daga fatar jikina. Sai na ji kamar komai yana sauyawa kamar  duk wata kyakyawan alaqan da muka gina ta tare da Yallaɓai tana zangayewa tana komawa ruwa. Kamar kuma ruwan ya fara zuba a ƙasa ya na kwarara da ƙarfin gaske wanda daga ni har shi ba za mu iya tare shi ba. *Ƙarshen littafi na Ɗaya* _*Nan na kawo ƙarshen littafi na ɗaya na labarin Sadiya da Yusuf, ba zan ce komai ba domin kun gwadani kun gani, yanzu ma muka tsoma hannu a cikin labarin, ba mu fara komai ba gundarin Labarin na cikin littafi na biyu da na uku, kuma na sanar da ku a manhajar Telegram za mu yi 2,3 ɗin shi, in kuma tsarin VIP ne to mu haɗu a AREWABOOKS, zamu tafi hutu kamar yadda muka saba har sai mun samu adadin mutanen da muke so kafin mu fara, ku yi gayya, ku ba da labarin TURKEN GIDA, ku sanar da wanda bai karanta ba da ya fara domin za a iya barin shi a baya. Wallahi tallahi ina da kyakyawan yakini akan abin da na rubuta kuma ina mai ba ku tabbacin za ku samu labarin nan fiye da hasashenku a kaina, In sha Allahu ba zan ba ku kunya ba, ku biya kudin karatun ku, da zaran kun kai adadi za mu fara kuma ba jira har sai mun dire in sha Allahu. NA GODE*_ *TURKEN GIDA LITTAFIN KUƊI NE, BOOK 1 ZAI ZO A MATSAYIN KYAUTA. BOOK 2,3 KUMA ZAI ZO A MATSAYIN NA KUƊI, KU BIYA KUƊIN KARATUNKU  #1k NE KACAL,  AKAN MANHAJAR TELEGRAM TA WANNAN ASUSUN BANKIN 9069067488 JAMILA UMAR OPAY, KO TUNTUƁA TA WAƊANNAN LAMBOBIN.* 09069067488. 08032773332. *MASU ƁUKATAR A TALLATA MUSU HAJOJINSU ZA SU IYA TUNTUƁARMU TA LAMBOBIN DA KE SAMA. MUN GODE* *Janafty* *25 November, 2024* *17/May/2025*