📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI(Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 My Facebook group :Fadila Sani https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ ALHAMDULILAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH, ALLAH INA GODIYA GAREKA DA KABAN IKON GAMA SO NE SILA LAFIYA. OGA HABIB YADDA NA FARA LAFIYA ALLAH KASA IN GAMA LAFIYA. ABINLURA. BANYI OGA HABIB BA DA NIYYAR CIN ZARAFIN KOWA BA. GARGAD'I! BANYADA BA BAN KUMA LAMINTA BA, WANI KO WATA YA CANZA MIN LABARI BA BATA RE DA IZININA BA, KO A JUYAMIN LABARI BA, YIN HAKAN KUSKURE NE BABBA, AKIYAYE!!. SADAUKAR WA. OGA HABIB DAGA FARKON SHI HAR K'ARSHEN SHI SADAUKAR WA CE GAREKI 'YAR'UWTA D'AYA TAR KAM DA DUBU, OGA HABIB KYAUTA CE GAREKI KIYI YADDA KIKE SO DA SHI, HASSANA SANI MPAPE ABUJA BARRISTER. SAK'ON GAISUWA GAREKU ABIN ALFAHARINA. YAYA SAIFULLAHI SANI MPAPE ABUJA. BARRISTER HASSANA SANI MPAPE ABUJA. AUNTY ZEE MPAPE ABUJA. AMARYA MAMAN AMATULLAH MPAPE ABUJA. AUNTY MARIYA FUNTUA. AUNTY ZAINAB YAHAYA BAKORI. SISTER HAFSAT YAHAYA BAKORI. GODIYA. INA GODIYA GA MASOYANA A DUK INDA KUKE, BA KU DA TA HANYAR DA ZA KU NUNA MIN K'AUNA SAI TA HANYAR COMMENT D'IN KU. DUNIYA KAMAR INUWARKA CE;DUK INDA KA TAFI ZA TA BI KA, AMMA IDAN KA TAFI NEMAN TA ZA TA RIK'A GUDU, KUMA BA ZA KA TAB'A CIM MA TA BA. WASU MUTNE KAMAR SUKARI SUKE A CIKIN RAYUWARKA. KO KA DAINA GANIN SU AMMA D'AND'ANONSU YANA NAN. ALLAH YAYI MI KI RAHAMA MAHAIFIYATA. Shafi na 1&5. Bismillahir rahamanir rahim. GARIN ABUJA. Wani tabkeken Company ne, asamansa ansa,: SANAT YOGHURT. Daga k'asan sunan kuma ayi rubutu da k'anan bak'i, kamar haka, :sanat yoghurt company , zone e apo Abuja. tsaye nake ina kallan tsaruwar SANAT YOGHURT company, ina nan tsaye, sai naji wani yana cewa, "Barka da fitowa Oga Habib ". koda na juya dan ganin wannan wanda aka kira da Oga Habib. Na makara sai dai motar da yashiga nabi da kallo, koda na duba motar da kyau sai naga, corolla S ce. Motar nabi da kallo, motar black ce, mai pure white glass. Gudu sosai motar ke yi. Sunyi tafiya mai nisa sosai, dan har sun shiga garin kaduna. Tafiya suke sosai, su biyu ne a motar Oga Habib, sai driver shi. Habib cikin siririyar muryar shi, mai cike da izza, ya ce, "Bilya tsaya!. D'an tsawa ce ya yi maganar, wanannan nature ne na Habib haka yake abisa lurar da nai me. Bilya, cikin girmama Ogan shi, ya ce, "Oga Habib Lafiya zamu tsaya anan? kabari mushiga gari mana, kasan yanzu ba ko'ina ake parking ba". Habib cikin tsawa, ya ce, "Bilya na ce kayi drup d'ina anan kana kawo min wasu Questions". Bilya tsayawa ya yi, Habib ya d'auki faron da yasha ya rage ya fita da shi. Bilya driver da mamaki, ya bi Habib da kallo, ya ce, "Oh wai dama gayannan fitsari zai yi ya ke min wani muzurai. Habib da sauri ad'an tsorace ya dawo ya na haki alamun kamar yaga wani abun tsoro. Bilya driver da sauri ya bud'e ma Habib burfin motar ya shiga. Bilya cikin girmama ya ce, "Oga Habib lafiya kuwa? ". Habib kamar ba zai magana ba, sai kuma ya ce, "Bilya gawar mutum nagani anjefar". Bilya cikin tsoro ya ta da motar zasu ta fi. Habib ya da ka mai tsawa yace, "meye haka?, baka ji abinda na ce bane!? ".Bilya driver cikin bin umarnin Ogan shi Habib, ya tsaya da motar, ya kalli Habib, ya ce, "Oga Habib zamu d'augawa ne a mota?, kasan fa yanzu rayuwa ba kamar daba, gaskiya ricks ne Oga mu d'auki gawar da...... ". Tsawar da Habib ya yi ma Bilya ne, ya sa ya yi shiru. Habib cikin d'aga murya, ya ce, "ka fita ka duba min ka gani". Bilya fita yayi kawai dan bashi da yadda zai yi, amma a ainihin gaskiya a tsorace ya fita. Bilya cikin tsoro ya fita ya dudduba amma bai ga wata gawa ba. Bilya dawo wa ya yi, ya kalli Habib cikin girma, ya ce, "Oga Habib banga gawar kowa ba fa". Habib tsaki ya ja, ya fito daga motar. Habib na ta fiya, Bilya na binsa aba-abaya. Habib kallan Bilya ya yi, yana nuna mai abinda ya gani, ya ce, "Can me ye? ". Da d'an k'arfi ya yi maganar. Yana nuna gawar mutum da yagani kwance agun. Bilya cikin tsoro ya ce, "Oga Habib zamu fa jefa rayuwarmu cikin had'ar...... ". Tsawar da Habib ya yi ma Bilya ce tasa ya yi shiru, ya kama bakinsa bai k'arasa fad'in abinda ya ke fad'aba. Habib cikin b'acin rai dan ya tsani arik'a jayayya da shi, cikin fushi ya ce, "Your very stopped, ina maga kana quarrel da ni, Bilya baka da wani amfani Wallahi". Idan da sabo Bilya yasaba da fad'an Habib. Hakan yasa Bilya cikin bin Umar nin Ogan shi yak'arasa inda gawar ta ke. Bilya cikin al'ajabi ya ke, kallan gawar matashiyar budurwar, Bilya matsawa ya yi kusa da ita sai yaji kamar tana numfashi kad'an-kad'an.Hakan yasa Bilya dawo wa inda Habib ya ke tsaye. Cikin girmamawa Bilya ya ce, "Oga Habib ba gawa bace,dan da alamun tana numfashi". Habib batare da ya kalli Bliya ba, ya ce,"ka d'akkota ka shigo mu tafi". Bilya da mamaki ya kalli Habib, amma gudun kar ya yi laifi yasa baice ko mai ba ya bi Umarnin Ogan nashi, ya je ya d'akko ta. Habib tashi ya yi ya koma site d'in driver ya zauna. Ita kuma Bilya ya shimfid'ar da ita a mazaunin baya. Tafiya kad'an ta idasa da su Oga Habib kano. Suna shiga kano sun yi tafi bawani sosai ba. Habib ya ce, "Bilya samu gu kai parking" Bilya tsayawa ya yi, kamar yadda Ogansa ya Umar ce shi, ya ce, "Oga Habib mun tsaya". Wata private hospital Habib ya nuna ma Bilya ya ce, "Bilya ka shiga hospital d'in nan ka kaita". Bilya kamar zai yi kuka, dan shi a ganinsa idan ma tai mako Habib d'in ya ke son yi tom shi yi yi mana da kanshi ba sai ya bashi wahala ba. Baliya badan ya soba ya d'akko wannan baiwar Allah da ke kwance kamar matatta ya shigar da ita hospital d'in. Bilya na shiga aka amsheta. Bilya kallan likitar ya yi, ya ce, "Likita dan Allah tare da Ogana muke, ki bata duk wata kulawa da ya ka mata zan dawo yanzu". Likitar cikin mamaki ta kalli Bilya ta ce, "Haba bawan Allah ya za ai bamu sanka ba, ka kawo mana yarinyar da bamu san taka mai-man abinda ke damunta ba, kuma ka ce mana wai za kaje ka dawo. Gaskiya ammana irin haka da yawa anan kano kuma basu dawowa. gaskiya haka ba zai yuwuba ". Bilya cikin rok'on likitar ya ce, "Karki damu Insha Allah ni zan dawo nai miki alk'awari". Likitar kallan Bilya ta yi ta ce, "sure". Bilya cikin tabbatar wa ya ce, "Yess am very sure insha Allah ". Bilya number shi ya ba likitar ya ce zai dawo ba da dad'ewa ba. Bilya fitowa ya yi inda ya yi parking d'in motar Oga Habib, ya shiga. Habib bai tambayi Bilya ya sukai ba, shin tana da rai ko bata da rai make damunta, bai tambayi komai ba. Shima kuma Bilya ganin bai tambaye shi ba yasa shima yaja bakinsa ya yi shiru. Direct inda Oga Habib keda Meeting Bilya ya kai shi. bliya na yi parking Habib ya sauka, hotel d'in da za su yi meeting d'in. Lokacin da Habib ya shiga har sun gaggaji da jiran shi, dan harma sun fara fidda ran zai zo, in da shi Ka d'ai su ke jira dama. Habib be fi hour d'aya da shiga taron ba ya fito ranshi a b'ace. Habib cikin jin haushi ya bud'e murfin motar ya shiga ranshi da alamun b'ace ya ke. Habib na shiga ya kalli Bilya cikin jin haushi, ya ce, "Jamu bar gurin nan aikin banza ai kin wofi". Bilya da sauri ya sa ma motar key suka bar gurin. Bilya cikin jin tsoro ya kalli Habib ganin ranshi kamar ab'ace ya ke, ya ce, "Oga Habib ina zamu". Habib shiru ya yi ya yi banza da Bilya. Bilya cigaba da tafiya ya yi batare da yasan ina zasu ba, so yake ya k'ara tambayar Habib amma kuma yana jin tsoro. Wayar Habib ce ta yi ringing, Habib da sauri ya yi picking call d'in, dan ringing tone d'in mommy shi ce. Habib cikin sakin fuska da murmushi, dan indai kaga Habib na waya yana murmushi tom mutum d'aya ce, wato Mahaifiyarshi. Habib cikin sweet voice d'in sa, ya ce, "Mommyna kina lafiya". Banji mai akaje ba daga can b'angaran sai dai naji Habib ya ce, "Mommy ina hanya fa, na kusa dan Allah kijirani mana". Banji mai Mommyn Habib ta kuma cewa ba, sai ji nai ya ce, "Mommy ki barsu kawai, ni dama nasan bawai maganar kirki bace dan dai ma kin matsamin ne shiyasa nazo, Mommy wai fasaha suke so mu saida masu, suma su rik'a irin yoghurt d'in mu ak'asarsu, Wallahi Mommy tsabar haushi ko magana ban musuba nabar gun, dan dana san wannan maganar ce Allah Mommy da banje ba". Can b'angaran bajin me ake cewa nake yi ba, sai dai naji Habib nai mata fatan Allah ya dawo da ita lafiya, kuma dan Allah karta dad'e kamar yadda ta yi wannan karan. Bilya ko jin wayar Oga Habib ce ta sa ya fahimci, Habib yagama abinda ya kawo shi kano, yanzu Abuja zasu nufa. Hakan yasa Bilya ya kama hanyar Abuja. tafiyar 4 hour's ta kai su garin Abuja. Bilya direct gida ya yi da Habib dan ya san ba zai koma Company ba, in dai ya yi tafiya ba ya komawa sai washe gari. Bilya na aje Habib , Ya koma Company, dan Bilya aiki biyu ya ke ma Habib, yana aiki a SANAT YOGHURT. Sanan kuma shike driving d'in Habib duk in da Habib zashi. Albashi mai tsoka Habib ke biyan duk mai aikacin da ke aiki ak'ark'ashin sh. Wannan shine da lilin da yasa kusan duk suka jure cin mutuncin da Habib ke masu. Bilya bayan ya koma SANAT YOGHURT COMPANY har an tashi ya koma gida, da ya ke gidan Oga Habib ya ke zaune. Bilya bayan ya koma gida ne wayar shi tai ringing yad'aga, daga can b'angaran, fad'a sosai ta ke, ta ce, "Haba ya za ai kabarni da yarinya mara lafiya gashi ta farkaba tun d'azu amma kuma baka dawo ba". Bilya zaune ya tashi daga kwancan da ya ke, dan ya manta sham da maganar, wata Yarinya. Bilya cikin damuwa alamun shima bai ji dad'in haka ba, ya ce, "Ayyah dan Allah ki yi hak'uri Wallahi na manta sham. kuma Wallahi yanzu haka ina Abuja, amma ki yi hak'uri da safe zan ma Ogana magana". "Gaskiya ni ba inda zan kaita, sai dai in tasan in da zata. Cewar likitar. Bilya kashe wayar ya yi, ya ce mata dan Allah yana zuwa ta bashi minti d'aya. Bilya cikin fargaba dan yasan Oga Habib ya hana shi kiran shi in dare ya yi. Habib na kwance kan makeken gadonsa na alfarma sai game ya ke awayar shi dan shi Mayan game ne. Habib na cikin game kira ya shigo wayar shi. Habib k'in picking call d'in ya yi, har sai da Bilya ya yi mai kira Uku. Habib d'aga kiran ya yi ya, ya kanga akun nan shi, yana sauraran abinda Bilya zai ce masa. Bilya ko cikin tsoran halin Ogan nashi da ba wuya ka b'ata mai rai, ya ce, "Oga Habib dama Yarinyar da muka tsinta ce d'azu, wadda muka kai hospital , tom shine likitar da naba Yarinyar ta kirani, yanzu , akan in zo ta far.......... ". Habib cikin tsawa ya katse, Bilya ya ce, " Bilya kana ko da full sense, awannan lokacin zaka kirani kana min wannan maganar!?, Yarinya kuma da ka ke magana,duk yadda kaga dama kayi da ita bai shafan ba, karka kuskura ka sake min magana akanta!. ". Wata zufa mai zafi ce ta fara karyoma Bilya. Ko tunanin mafita Bilya bai fara yi ba, kira ya kuma shigowa wayar shi. Bilya koda ya duba yaga Number likitar nan ce, Bilya cikin rashin sanin abinda zai ce mata ya yi picking d'in call d'in. Tun kafin ta yi magana, Bilya ya rigata da cewa, " Ki yi hak'uri kinga yanzu dare ya yi ba damar in zo Kano, amma zuwa gobe zaki ganni". Likitar jin abinda Bilya ce yasa ta kashe wayarta. Bilya sosai abinda Habib ya yi mai ya b'ata mai rai, taya zai ta kuramai ya d'auki ya rinyar, yanzu kuma yazo yana nai man lik'amai bala'i. Bilya shiru ya yi, ya na nazari, ya ce, Tom ni yanzu ko ma kano nace zan je in d'akko ta ina zan kaita. Bilya da sauri ya ba kanshi amsa da cewa, Wallahi sai dai in barma likitar ita, idan ma ta sake kirana bazan d'agaba. Bilya blocking number likitar ta ya yi. Cikin jin dad'in shawarar da yankema kanshi bacci ya kwasheshi. Washe gari misalin k'arfe goma na safe, kamar yadda Habib ya saba sai ya je office sannan ake kai mai abin break fast , haka aka yi. Bilya ko dama so ya ke ya yi magana da Oga Habib , amma bai samu dama ba, dan tunda ya d'akko shi da safe ya ke waya har suka isa company bai dai na ba. Wanan shine ya hana Bilya yi ma Oga Habib maganar Yarinyar. Ga shi kuma tunda safe likitar ta da mai da kira, dan tana ganin ya yi blocking Number ta ta kira shi da wata Number. Hakan yasa Bilya ya ke son ganin Ogan nashi sosai. Gashi in dai Habib ya shiga office d'in shi ganin shi na da wuya sosai, sai dai in Allah yasa ya fito. Bilya na nan tsaye yana nai man hanyar da zai bi yaga Oga Habib , Sai ga masu kawo mai break fast sun iso, tattawan mata ne guda biyu, amma ba wai sun tsufa bane sosai. Bilya na ganinsu cikin da bara, ya yi gurin su, ya ce, "Baba lami sannunku da k'ok'arin kula da Ogan mu ". Tsofaffin cikin girmamawa su ka amsa ma Bilya. Bilya kallan Baba Lami ya yi, ya ce, "Baba abin k'arin Ogan mu ne ko? ". "Eh Bilya shi ne". Suka bashi amsa. "Baba ku kawo dan Allah in kai mai dama ina son magana da Oga Habib Wallahi amma narasa yadda zan yi". Wadda ya kira da Baba lami, wayayyar tsohuwa, murmushi ta yi, ta ce, "Tom Bilya ka dai son ko mai,ka san babu wanda Hajiya turai ta yadda ya ba Oga Habib abinci hannu da hannu sai mu, tom kuma dai kasan Oga Habib yadda ya ke abu kad'an za kai mai babu ruwansa da bashi ya d'auki mu aiki ba, yanzu sai ya da katar da Mutum aiki ba ruwansa, dan haka kayi hak'uri, amma idan nashiga zan gwada mai magana kana son ganinsa k'ila idan akaci sa'a yabari ka shiga". Godiya Bilya ya yi ma Baba lami. Sannan suka shiga. Su Baba lami sun dad'e atsaye suna jiran Comment. Amma shiru. Habib sai da ya gama abinda ya ke sannan ya basu izin shigowa. Bayan sun Baba lami sun kaima Habib abin break fast ne. Har za su fita, Baba lami ta yi k'arfin halin bada sautin Bilya. Baba Lami cikin girmamawa kamar yadda ta saba ba Habib d'in, ta ce, ", Oga Habib, dama yaran nan ne, driver ka, Bilya ya ke Son magana da kai wai". Habib batare da ya kalli Baba Lami ba, ya ce, "Ba yanzu ba". Baba Lami fita ta yi, tana alawadai da dukiyar da zata sa Mutum ya d'auki kan shi haka, kamar yadda Habib ya d'auki kan shi. wata zuciyar ta ce mata tom kodai kyan shine yasa ya ke yin haka ne.Nan dai su Baba Lami suka fito suna mai Allah wa dai da ji da kai da tak'ama irinta Habib. Bayan su Baba Lami sun fito ne. Bilya ya k'arasa in da suke da saurinsa ya ce, "Yauwa Baba ya ce in shiga ko? ". Baba Lami cikin nuna rashin jin dad'in ta, ta ce, "ka yi hak'uri Bilya kasan yaron nan dama ba wai mutunci gare shiba, bai ganin kowa da Mutun ci, Wallahi ya hana. Sai dai ka yi hak'uri idan ya fito, ko in za ka kaishi wani gun". Bilya cikin d'an bacin rai ya ce, "Wallahi Baba Oga Habib na mulkamu yadda ya ke so, amma babu da muwa, ko mai nada lokaci, akwai lokaci". Baba Lami ta fiya su kayi bayan sun ba Bilya Hak'uri. Bilya ko yana nan tsaye yana ganin fitowar Habib amma shiru, har akai Sallar azahar. Bilya na nan tsaye kira yak'a shigowa wayar shi tai ringing, Bilya na dubawa yaga Number likitar ce, sosai gabansa ya fad'i dan k'aryarsa ta k'are. Biya na d'auka ya ce, "Ki yi hak'uri dan Allah nima banso haka ta faruba, ko ba komai na k'arya alk'awarin da nai miki, amma Wallahi duk abinda kika ga ya faru ba laifina ba ne laifin Ogana ne, amma bari yanzu in turomiki Number sa, dan Allah ko kinkira bai d'aga ba karki gaji ki ta kira zai d'aga". Bilya na kashe kiran ya tura mata Number Habib. aiko tana ganin Number ta danna mata kira, dan bata son yau ta sake kwana mata agida. Habib ko na zaune a Office d'in shi yana aiki a laptop, kira ya shigowar shi. Habib ko duba Number bai tsayiba ya ci gaba da aikinsa. Ita ko da yake taji abinda Bilya ya ce mata, hakan yasa taita kira. Habib cikin jan tsaki ya d'aga kiran ya sa akunne, yana sauraran mai magana. Ita ko likitar tana jin and'aga kiran ta ce, "Ranka shi dad'e dan Allah, kuzo ku amshi amanar da kuka ban dan Allah ". Habib cikin rashin fahimtar maganar, ya ce,"Wrong Number ". Yana fad'in haka ya katse kiran. Likitar ko bata gaji ba k'ara kira ta yi, cikin b'acin rai ta ce, "Oh wai kunyi satar Yarinyar ne kuke tsoran asirinku ya tuni, koko ku 'yan kidnappin...... ". Habib cikin daka tsawa ya tsayar da ita, yana kunfar baka. Magana ya ke son yi ya kasa, kawai sai ya kashe wayar shi baki d'aya, dan shi harga Allah ya manta wata yarinya da suka kai hospital. Bilya ko tunanin ko anda ce ne, yasa yakira, likitar dan ya ji yadda su kai da Habib. Likitar cikin b'acin rai ta ce,ma Bilya "Karka rainamin hankali malam, yarinya kuma ku kuka sani, amma daga yau na gama kwana da ita". Bilya hak'uri ya ba likitar sosai sannan ya ce, mata,"Wallahi ba maganar wasa gobe zai yi samma kon zuwa kano d'in ". Ai ko haka akayi Bilya tun da daddare ya nemi permission gurin Ogan shi, akan tafiya kano. Washe gari da wuri Bilya ya tafi kano, hakan yasa 12:00pm a kano tai mai. Bilya bacin ya biya likitar hak'uri Sosai ya ba ta.Sannan ya zauna yana jiran fitowar 'yar tsuntuwar tasu, shiga Ogan shi, wanda shi ya ma manta da batunta. Bilya na nan zaune 'Yar tsuntuwar su ta fito sanye ta ke da wata doguwar riga ta atamfa wadda likitar ce ta bata dan ganin bata da kaya, yasa likitar ta bata a tamfar. Bilya kallanta ya yi, sannan ya ce, " 'Yan mata ke 'Yar wana gari ce, yanzu in kaiki gidan ku, dan mu ahanyar mu ta zuwa kano muka tsince ki". Matashiyar budurwar da bazata haurama shekara goma sha bakwai ba. Cikin siririyar muryarta ta ce, "Ni marainiya ce, bani da kowa, dan Allah ka tai ma ke ni". Bilya da tausayi ya ke kallanta, dan shi aganinshi tabbas marainiyarce. Bilya shiru ya yi, dan yasan bai da in da zai kaita. Ito ko Yarinyar ganin Bilya ya yi shiru alamar ba zai tai maka mata ba, ya sa, ta ce, "Dan Allah katai makan Allah banda kowa". Bilya cikin tausaya mata ya ce, "zan tai make ki ki, amma tai makon ba mai tsawo bane, zan tai make ki ne kafin Hajiya turai ta dawo,kuma ni ba nan nake ba Abuja nake kin yarda zaki bini?, Sannan kuma duk sanda Hajiya turai ta dawo zaki kama gabanki , kin yarda? ". Da sauri ta ce, "Eh na yarda na godee. Bilya tashi ya yi Yarinyar na binshi aba suka je in da ya yi parking d'in motarsa da Ogan sa Habib ya yi masa kyautarta, suka tafi. Suka kama hanyar Abuja . Kasan cewar Bilya yana gudu sosai da mota, hakan ya sa, ana Sallar magriba suka shiga gida. Allah ko ya tai maki Bilya sosai dan lokacinda suka shiga ba kowa, duk 'yan aikin gidan sun shi cikin gida, hakan yasa tana fitowa daga mota Bilya yaja hannunta da sauri ya kaita d'akin shi. Dan yasan gidan cike ya ke da magulmata. Bilya dama tun kafin ya iso ya kira Baba lami ya yi mata bayanin ko mai, hakan yasa Bilya na isowa ya kira Baba Lami ya sanar da ita sun iso. Baba lami na shiga d'akin Bilya. Bilya ya kalleta ya ce, "Tom Baba kin san dai yadda gidan nan ya ke, Baba lami ga Yarinyar nan, dan Allah ta zauna gunki kafin Hajiya turai ta dawo". Baba lami batare da taima Bilya magana ba, gudun matsala dan ba wani lokaci sosai,Baba Lami taja hannun 'Yar tsuntuwar ta yi d'akinta da ita da sauri. Bayan sun shiga d'akine Baba Lami ta kalli Matashiyar budurwar ta ce, " 'Yan mata ya sunan ki? ". Cikin sanyin murya ta ce, "Sunana Hassana". "Yauwa Hassana dan Allah ki yi zamanki nan, karkisake ki fita waje, muta nan gidan nan magulmata ne, dan Allah ki kula, kafin Bilya ya samarmiki gurin zama". Sosai Baba Lami ke k'ok'arin b'oye Hassana. Sai dai kash abinda Baba bata sani ba, aminiyarta wadda su ke aiki tare da ita da kanta ta kira Hajiya turai ta kai gulmar Lami ta kawo wata bak'uwar yarinya agidan, kuma abisa lurar da ta yi, Bilya ne zazo da Yarinyar ya ba Baba Lami ita". Hajiya turai ko, sosai hakan yab'ata mata rai, acewar ta ba laifin Bilya ba ne, lafin Oga Habib ne, saboda shi ya ba Bilya damar shigowa kai tsaye gidan. Hajiya turai ranta ad'an b'ace takira Habib awaya. Habib ko lokacin yana zaune a office d'in shi na SANAT YOGHURT, kiran Mahaifiyar shi abin soyuwa a zuciyar, ya shigo wayar shi Habib cikin kirarin da ya saba yi ma Mommy shi, ya d'aga kiran ya ce, "Sai Mommyna ni kad'ai Allah ya k'arami lafiya, lafiya dai ko wannan kira haka a wannan lokacin? ". Hajiya turai cikin basar da zancen Habib d'in ta ce, "Habib wacece ta ke zaune a gida". Habib cikin rashin fahimtar abinda Mahaifiyarta shi ta ce,ya ce, "Mommyna bangane maganarki ba". "Habib za kai min maganarta ka ko ta banza, tom wacece aka ce min Bilya ya kawo gidan da zama?, Habib ni fa ina tsoran abinda ya faru ne ya sake faruwa". Habib cikin kwantar ma Mahaifiyar shi hankali, dan yaga alamar ta tsorata sosai da abinda ya faru Kwanakin baya. Habib cikin sanyin muryar shi, ya ce, "Mommyna Allah ban san da zaman kowa ba, amma ki bari zan yi bincike yanzu". Hajiya turai kashe wayarta ta yi. Habib ko Mahaifiyar shi na kashe kiran, ya kira Number Bilya. Bilya na d'agawa Habib ya ce, "Bilya da kai da wadda ka kawo da kuma wadda ka ba ajiyarta, kuzo yanzu". Cikin bilya sai da ya yi k'ara jin abinda Habib ya ce, hakan yasa da sauri ya bar SANAT YOGHURT, ya koma can gidan Habib d'in. Bilya tun kafin ya isa yakira Baba Lami awaya ya ce su had'u wajan get harda Yarinyar da yabata ajiya. Bilya na zuwa suka ya iske Baba da Hassana wajan get d'in suna jiranshi. Bilya kallan Baba ya yi, ya ce, "Baba Wallahi ban tab'a ganin muna fukai ba kamar 'yan aikin gidannan ba, yanzu wai har an samu wanda ya kaima Oga Habib gulmar zaman Yarinyar nan agidannan, yanzu haka yana nai manmu mu dukanmu". Baba lami dafe k'irji ta yi, ta ce, "Bilya kasan Allah yaron nan korarmu zai yi". Bilya kallan Baba Lami ya yi, ya ce, "Baba ni ba abinda ke damuna ba yanzu kenan". Bilya a motar shi ya d'auki su Baba, zuwa SANAT YOGHURT. Koda suka shiga wajan Hassana kallan sunan da ke d'auke da tank'ameman Company ta ke, da kuma tsaruwa irin ta gurin, ko ina 'yan akine sanye da Uniform d'in su green and orange . kasan cewar Habib ya san da zuwan su Bilya , hakan yasa kai tsaye suka shiga tank'ameman Office d'in Oga Habib. Habib na zaune yana ta aikinsa a laptop d'in shi, yana jin su Bilya amma yaci gaba da aikinshi. Habib sai da yagama abinda ya ke yi, sannan ya d'ago kai yana kallan su d'aya bayan d'aya. Habib mai da kallan shi ga Bilya ya yi, ya ce....................... Labari ne mai cike da CAKWAKIYA, ku dai ku bini asannu zaku fahimce ni nan gaba kad'an🤝 DUk mai son kasan cewa a group d'in Oga Habib.Tom Comment dole ne 'Yar'uwa. In kinkaranta daure ki Comment. COMMENT PLEASE 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* RUBUTWA DA TSARAWA FADILA SANI BAKORI(Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 My Facebook group:Fadila SANI https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Ba kowane lokaci ne mutane za su fahimce ka ba. K'aramar k'wak'walwa ba ta gane manyan kalamai. Babban kifi sai babbar gora. Allah kasa mu dace. Shafi na 6&7. ..... Bilya wacece wannan?, Habib ya yi maganar ba alamun fara'a a fuskar shi. Bilya cikin girmamawa ya fara magana, kamar haka, "Oga Habib ita ce Yarinyar da muka tsinta, kace in d'akko ta ranar da muka je kano". Habib wani banzan kallo ya yi ma Bilya, sannan ya ce,cikin fad'a-fad'a " da nace ka d'akkota sai kuma nace ka kaita gidana!? ". Bilya cikin alamun ban hak'uri, ya ce, "ka yi hak'uri Oga Habib, na aikata kuskure, insha Allah haka bazai sake faruwa ba". Habib banza ya yi da Bilya yaci gaba da typing d'in sakon da ya ke yi, a laptop d'in da ke gaban shi. Habib sai da yagama abinda yake yi, duk su Bilya na tsaye suna jiran sakamakonsu. Sannan ya d'ago kai ya kalli Bilya ya ce, "Bilya daga nan karku koma min gida ku dukanku". Bilya cikin tsorata da jin kalaman Oga Habib, duk da dai yasan zai iya ai kata hakan,Bilya ya ce, "Oga Habib dan Allah k........ ". Habib hannu ya d'agama Bilya, sannan ya nuna masu k'ofar fita". Baba Lami da sauri ta k'araso in da Habib ya ke, ta ce, "Oga Habib dan Allah ka yi hak'uri munsa.... ". Habib ranshi a d'an b'ace ya nuna ma Baba lami k'ofa ya ce, "Baba dan Allah ku fitarmin Office! ". Baba lami fita tayi tana mai da nasanin amincema Bilya da ta yi ta amshi Hassana, gashi abin ja mata kurarta aiki. Bilya ya je dai-dai k'ofar fita ya tsaya, cikin taushin murya raunanna, ya ce,"Ka yi hak'uri Oga Habib da abinda zan ce maka. Oga Habib amma da kasan bazaka taimaki yarinyar ba, da baka sani na d'akkota ba, Oga Habib sanin kankane bani da gida, ni ba d'an garinnan ba ne, yanzu da kakoreni ina ita zan kaita?, da ace mun barta a'inda muka ganta da Allah zai kawo wanda zai tai maketa, amma mu tai makon da mu kai mata ya zamana bashida amfani. Oga Habib ita fa mace ce,Idan munbarta tatafi ina zata?, Oga Habib dan Allah ina rok'onka dan Allah idan ka koreni tom ita dan Allah ka yi k'ok'ari ka ci ka aikin alkairin da ka yi niyyaryi tun farko akanta. Inda dama kai kayi niyyar taima kon....". Habib katse Bilya ya yi, alamun ranshi ya fara b'aci da magan-ganun Bilya. Ba kamar maganar shi ta k'arshe ba, wai dama shi ya yi niyyar taimakon ta bashi ba. Habib wani banzan kallo ya yi ma Bilya sannan ya ce, d'an zafafe, "Bilya ni na ce maka zan taimaketa?, dama da nace ma ka ka d'auketa sai aka cema hakan na nufin agidana zata zauna kenan!? ". Habib ya tambayi Bilya cikin d'aga murya. Bilya shima da yake sosai Habib ya b'ata mai rai, cikin k'ok'arin danne fushinshi, dan yasan in dai ya ce zai sa fushi tom Habib ba zai ya yi abinda ya ke so ba, gara ya yi hak'uri ya danne fushinshi. Hakan yasa Bilya cikin danne fushinshi ya ce, " Oga Habib hak'uri za kai ka tai maka mata, dan na tambayi yarinyar garinsu in kaita, ta ce min ita marainiya ce, shine ma dalilin da yasa nakaita gidanka". Habib cikin had'e rai ya ce, "Sai aka cema kuma shi maraya bashi da 'yan'uwa, kira min yarinyar". Bilya fita ya yi, ya iske Baba Lami da Hassana tsaye. Baba Lami kallan Bilya ta yi, ta ce, "Bilya ya hak'ura ne? ". "Hmmm Baba wannan ne zai hak'ura da wuri haka bai wahalar da mutane ba. Ni Baba Lami dama abinda ke damuna wannan yarinyar ya nuna Hassana da ke tsaye, kuma shine yasa ni taimakonta, shine na ke son yasan yadda zai yi da ita inda shi ya yi niyyar tai makon dama bani ba, shine yanzu da nai mai complain akanta, shine ya ce in kira mai ita". Baba lami kallan Hassana ta yi, ta ce, "Je ki kinji Allah ya tai make ki, yabarki. Baba lami mai da kallanta ta yi ga Bilya ta ce, " Bilya mufa? ". "Baba Lami ki rabu da shi kinji, ni na san yadda zan mai, Hajiya turai ta yarda da ni sosai, kuma kinga kema ta yarda da ke, shiyasa ta zab'eki da ki rik'a yi ma Oga Habib girki, dan haka ki bari kawai nasan yadda zanyi, Allah dai yasa in nakirata ta d'aga". Ameen Baba Lami ta ce. Bilya kallan Hassana ya yi da har yanzu ta ke tsaye ta k'i tafiya, ya ce, "Je ki Office d'in ce inda muka fito yanzu". Hassana ko da bata fatan k'ara ganin Habib, kallan Bilya ta yi, ta ce, "Dan Allah ni dai kutai dani inda zaku, ni bana son zuwa dan Allah ". Bilya dariya ya yi, dan yaga alamar ta tsorata da Habib sosai. Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce, "kinga ni yanzu haka nasan ni da Baba zai mai da mu, saboda Mahaifiyar shi tana son mu, da ma ke nake ji, inda bazasu yarda ba ki zauna agidansu, dan yanzu suna tsoran bak'o saboda abinda ya faru da su kwanakin baya, ki yi hak'uri ki je, idan Allah ya taimaka, duk da Oga Habib shegen mutum ne, k'ila ya barki". Hassana a tsorace ta tura Office d'in Habib ta shiga, dan ita bata son wulak'anci kuma ta lura OgaHabib irin masu wula k'anta mutanan nan ne, saboda kud'insu. Habib na zaune yana mai cigaba da typing d'in da ya ke a laptop d'in shi, kayan da za'a kawo masu ne ya ke ta aikin lissafawa. Habib na zaune ya ji anturo k'ofa anshigo ba naiman izini ba komai. Habib d'ago kai ya yi yana mata kallan baki da hankali ne, Banza Habib ya yi da ita, ya ci gaba da typing d'in shi ya barta nan tsaye. Hassana ko magana ta ke son yi tana tsoro dan taga Bilya ma yana mai fad'a bare ita. Hassana jin ya yi banza da ita babu alamunma zai gama abinda ya ke yi bare har ya yi mata magana. Hakan yasa ta ce,cikin rawar murya, kamar yadda ta lura kowa na cewa, "Oga Habib dama Oga Bilya ne ya ce min kana kirana". Habib ko cigaba da aikin da ya ke yi ya yi kamar bai jita ba, bamu ma wata ala da ta nuna mata yaji abinda ta ce, hakan yasa ta kuma cewa, "Oga Habib dama Oga bilya ne ya ce min inzo kana son gani n...... ". Tsawar da Habib ya yi mata ce yasa ta yi shiru, cikin d'aga murya Habib ya nuna ta da d'an ya tsa, ya ce, "get out from my Office ". Hassana fita ta yi jikinta na rawa, dan sosai ta tsorata da tsawar da Habib ya yi mata. Hassana inda tabar Baba lami da Bilya ta je, amma bata gansu ba. Hassana guri ta samu ta zauna ta yi shiru kamar za tai kuka, tabbas tun yanzu da ba aje ko ina ba, ta fara da na sanin barin gida. Hassana na nan zaune tana kallan ma'aikan gurin kala-kala sai aikinsu suke, can wani d'aya daga cikin staff d'in gurin wanda tun d'azu ya lura da Lokacinda Hassana ta fito daga Office d'in Oga Habib. Inda Hassana ta ke tsugunne ya zo ya sameta, kallan Hassana ya yi, ya ce, "Bai war Allah lafiya kuwa? Nalura da ke tun d'azu keke gurinnan. Idan aiki kika zo naima aiba Office d'in Oga zaki ba, gurin manager zaki". Hassana d'aga kai ta yi tana kallan shi, sannan ta ce, "Ni ba aiki nazo naima ba, amma inna samu aikinma zan yi". "Ok, amma dan Allah ko zan iya sanin mekika zo naima, in ba aiki ba? ". Hassana kallan shi ta yi, sai taji bata da zab'i kamar ta fad'a mai, inda taimo ta ke naima k'ila ya tai maketa. Hakan yasa Hassana ta kallai, ta ce, "Bansan kowa ba a nan Abuja, su Oganku suka tsinceni ahanyarsu ta tafiya kano,suka kawo ni nan, shine yanzu shi Wanda ake kira da Oga Habib, wai bazan zauna agidan shiba, shine shi Oga Bilya ya ce in je Office d'in shi ya na kirana, tom na je kuma ya Koreni". murmushi ya yi, staff d'in nan, ya ce, "Bilya ai ba wani bane staff ne kamar kowa anan, dan dai shi yana driving d'in Oga Habib ne, kuma in dai Oga Habib ne ya ce yana kiranki a Office d'in shi zai saurareki, sai dai in da kika je ne, kin mai ba dai-dai bane. Kuma maganar gaskiya in ma komawa kikayi ki mai magana kan ya d'aukeki aiki, amma maganar gaskiya Oga Habib ba zai kaiki gidan shiba, dan gidansu akwai tsaro sosai. Idan harshi ya ce kije, ki tashi ki koma ki je zai saurareki, in da yasan da zuwanki". Hassana tashi ta yi ta nufi office d'in Oga Habib, saboda bata da zab'in da ya wuce ta tashi ta je d'in. Staff d'in nan kallan Hassana ya yi da tausayawa, dan mata masu ajima Oga Habib ba saurararsu ya ke ba bare ita. Habib na zaune yana waya da Mommynshi, Hassana ta yi sallama ta shigo. Habib kallo d'aya ya yi mata ya d'auke kanshi ya ci gaba da wayar shi. Jinai Habib na cewa, "Mommyna dan Allah ki barsu kawai, idan mutum na laifi irin haka ya kamata ai funishiment d'insa. Banajin abinda akecewa daga can b'angaran, sai dai naji Habib ya ce, "Ok, Mommy zasu dawo, amma ni idan tanine ma nafi son inyi driving d'in kaina. Abinci kuma ki rabu da Baba Lami inda ga Baba dije nan". Mahaifiyar Habib sosai ta nuna ma Habib in dai bai dawo da su bilya ba ranshi zai b'ace. Tana kaiwa nan ta kashe wayarta. Habib ranshi b'ace ya kira bilya awaya, kira d'aya bilya ya d'aga, yana d'agawa Habib ya ce, "Bilya kazo Office d'ina yanzu". Habib mai da kallan shi ya yi ga, Hassana da ke gefa tsaye arakub'e. Doguwar rigar da Likitarnan ta bata ce har yanzu ajikinta, sai wani haif hijab da tasa. Habib d'auke kai ya yi daga kallanta, sannan bazato ba tsammani Hassana ta ji ya ce, "Ke 'yar wata jaha ce?,kuma me yarabo da ke daga gidan ku? ". Hassana kallan Habib ta yi taga ba'ita ya ke kallo ba hankalinsama akan laptop d'in gabansa ya ke, ba akanta ba. Hassana muryarta na cracking ta ce, "Ni yar kano ce, mamana da babana duk 'yan jahar kano ne, Babana nada mata biyu. matar Babana tana da fad'a sosai, kuma macece mai son kanta da yawa. Babana tunda ya auri mamana Allah bai bata haihuwa ba, hakan yasa kakata wato Mahaifiyar Babana ta matsama Babana ya k'ara aure. Babana ya auri Umma Rabi ba dad'ewa Allah ya bata ciki ta haifi Aunty jamila, sai da Umma Rabi ta haihu uku sannan Allah ya ba Mamana cikina, tom kuma itama Umma Rabi lokacin tana da ciki, kusan tare sukayi rainon ciki ita da Mamana. Mamana ta haihu da kwana biyu Umma Rabi ma ta haifo yarinyarta mace. Hakan yasa Babana ya ce, sai dai ahad'a sunan mu. Tom Mamana dama tunda ta haifeni bata da isassar lafiya, hakan yasa kwanana biyar aduniya Allah ya yi ma Mamana rasuwa. Babana sosai hankalinsa ya tashi da mutuwar Mamana saboda yafi jin dad'in zama da ita fiye da Umma Rabi. Tom mamana da ma ita ma ita kad'aice awajan Iyayanta kuma Allah ya yi masu rasuwa dad'ewa, hakan yasa Babana badan ya soba sai dan bashi da yarda zai yi ya d'auke ni ya ba Umma Rabi ni, ya ce ta had'amu ta shayar damu tare da 'yarta. Da da farko Umma Rabi ta Nuna ma Babana baza amsheni ba, amma sai Babana ya nuna mata dole ta amsheni, in da bai san Wanda zai kai ma niba. Hakan yasa dole Umma Rabi ta amsheni. Ranar suna Babana ya sa mana Hassana da Usaina ni da yarinyar Umma Rabi. Nasha wahala sosai awajan Umma Rabi dan ko kuka nake sai taga dama ta ke ban nono insha. Kuma koda zan riga Usaina tashi in dai Usaina ta tashi tom Umma Rabi sai ta d'auki Usaina ta lallasheta ta yi shuru sannan koda zata kulani. Ahaka har muka girma. Tunda nafara wayau na fahimci Umma Rabi tafi son Usaina akaina. Babana dawuri ya samu Islamiya, ita Usaina bata cika zuwa ba saini, saboda ni kona ce ba zani ba dole za'a turani. Tun ina 'yar k'arama ta na iya duk wani aikin gida, dan hatta wankinmu Nida Usaina ni ke mana, acewar Umma Rabi ni ce babba. Babana duk lokacin da zaizo gida ya iske ina aiki sai yi ta fad'a ya ce Usaina tazo muyi tare. Wannan abinda da Babana ke yi shiya k'ara jawo min tsana sosai gurin Umma Rabi. Ahaka rayuwa taita tafiya har muka girma , muka shiga secondary school. Tom da akwai wani teacher mu, wanda ya ke kula da duk abinda ya shafemu Nida Usaina, sai dai yana yawan yi min complain, akan wai Usaina ta fi ni tsafta, ni dai ban tab'a fad'amai wani abuba game da gidanmu, shine ya tsinto labari acikin gari. Tunda teacher Kabir ya tsinci labarin halinda nake, ya zamana yake yawan yimin kyautar kud'i. Sosai teacher Kabir ke min hidima hakan yasa har Babana ya sanshi. Muna gama j. S. E. Babana ya ce, bazamu cigaba da karatuba aure zai mana. Tom dama ita Usaina akwai wini dake zuwa gunta harma ya yi ma Babana magana, ni kuma dama teacher Kabir shike Sona shima ya naimi izini gurin Mahaifina ya kuma bashi. Lokacin da Babana ya je ma da teacher Kabir maganar ya turo manyasa gidanmu ai maganar aurena da teacher Kabir . Teacher Kabir rok'on Babana ya yi akan dan Allah ya barni in kamma secondary school sannan. Kasan cewar Babana na son tarayyata sosai da teacher Kabir yasa ya yarda da abinda teacher Kabir ya ce. Koda Babana ya kaima Umma Rabi maganar saina kamma secondary school sannan za ai aurena, cewa ta yi itama Usaina abarsa sai ta kammala sai ayi duka tare. Aiko haka akayi. Muna S. S. S 3 first term, Babana ya sa ranar aure na da Teacher Kabir. Ita kuma Usaina da wani Jamilu d'an layinmu. Umma Rabi bata son tarayyar Jamilu da Usaina ko ka d'an bakamarma da taga teacher Kabir na min hidimaba sosai, ita kuma Usaina babu abinda ke shiga tsakaninta da Jamilu na kyauta. Da akwai wata rana teacher Kabir ya kawo min waya. Wannan kyautar da ya yi min tab'ata ma Umma Rabi rai sosai,hakan yasa tace sai dai in maida mai wai in ya auran ya sai min agidansa. Babana koda yazo yaji abinda Umma Rabi ta ce hanawa ya yi in maida ma teacher Kabir wayar shi". Hassana shiru ta yi, tana goge hawayanta saboda wani kuka da ke son k'wace mata, saboda tunowar rabuwarta da teacher Kabir ta k'arshe da ta yi. Hassana cikin murya mai kama da ta kuka taci gaba da magana kamar haka, "Ranar da bazan mantataba arayuwata, ita ce ranar wata laraba, Iyayan teacher Kabir suka zo gidan mu wai d'ansu Kabir ya janye maganar auran shi dani ya mai da ta kan Usaina. Bani ba har Babana ya girgiza da jin haka, mamaki da al'ajabi suka cika shi, saboda shi kanshi asanin kanshi Kabir bama sa wani jutuwa da Usaina, sai yau rana tsaka wai ace Kabir ya janye maganar auran shi da Hassana ya maida kan Usaina. Babana cema Iyayan teacher Kabir ya yi tom su bari zaiji daga bakin Kabir d'in sannan. Aiko haka akayi Babana kiran teacher Kabir ya yi ya tambayai ya akan maganar da Iyayanshi suka zo da ita". Bud'ar bakin teacher Kabir sai cewa ya yi, "Eh hakane shi Usaina ya ke so". Wannan maganar sosai ta d'aga hankalin Babana. Washe gari da safe Babana ranshi b'ace ya je d'akin Umma Rabi. Babana nazuwa ya kalli Umma Rabi, ya ce, "Rabi ina son kisan wani abu duk k'ula-k'ular da kika yi, ki ka maida auran Hassana ya koma kan 'yarki tom tun wurima ki warware shi, dan ni bazan tab'a aura auran Usaina da Kabir ba, garama kisani tun wuri. Haka Babana ya gama fad'anshi Baba Rabi bata tanka mai ba. Abu kamar wasa yazo ya zamana gaske, dan teacher Kabir idan yazo gidanmu sai inga Usaina taje suna hira, ni ko ko gaisuwata baya amsawa. Abin ya daman Sosai, hakan yasa na kaima Babana k'arar teacher Kabir. Babana kallona ya yi cikin alamun tausaya min, dan ya lura ina son teacher Kabir sosai. Hakan yasa Babana cikin lallashi, ya ce, "Hassana kinsan dai wani baya aurar matar wani ko?, haka kuma wata bata auran mijin wani, inji hausawa sunce matar mutum kabarinsa. Tom Hassana dan Allah karki tambayan dalili dan nima ban sani ba, amma ina so ki hak'ura da Kabir ". Wannan magana da Babana ya fad'a ji nai kamar ya lumamin wuk'a azuciya, dan Allah ya sani ina son teacher Kabir sosai, kodan shine saurayina na farko. Kuka na fashema Babana da shi jin abinda ya ce. Babana duk wata magana mai dad'i da zai fad'amin wadda zata sa in yi shiru ya fad'amin, amma ina na kasa. Sosai kukana ya d'agama Babana hankali. Ni ko kafin kace me sai ciwan kai tsabar kukan da nayi haka kaina ya yi ta min ciwo. Aranar dai da ciwan kai na kwana. Iyayan Kabir ko sun yi ake kamar me akan Babana ya maida auran Hassana da Kabir kan Usaina ya k'i. Umma Rabi ko ganin Babana yak'i amsar maganar Usaina da Kabir, yasa taturasu wajan k'aninta. Tom da ya ke shima k'anin nata gashi ga irin shi. Hakan yasa batare da binciken komai ba, ya amshi maganar, nan dai ya yi jagoranci aka tsaida ranar auran Usaina da Kabir, wata biyu masu zuwa. Wannan ranar nayi kuka kamar raina zai fita. Wannan kukan da nayi sosai ya tadama Babana hankali. Kafin kace me hawan jinin Babana ya tashi. Washe gari da safe shiri-shiru Babana be ne meniba. Hakan yasa na lallab'a na tashi dan kaina sosai ya ke min ciwo. Ina tashi d'akin Babana natura nashiga. Ganin Babana kwance kuma harna tura d'akin bai tashi ba, yasa na k'arasa gun shi ad'an tsorace. kiran sunan Babana nayi ina bubbuga k'afarshi amma shiru. Kuka na fasha dan duk da ban san Mutuwa ba jikina ya bani kamar babu rai ajikinsa. Babana ya tafi yabarni yatafi in da bazan sake ganinsa ba. Haka akai zana'izar Babana. Nayi kuka sosai dan Babana shine abokin shawara, shine abokin firata idan yana gida, shine wanda abu in yasaman nake fad'amawa sai ko teacher Kabir, tom shima anrabani da shi. Bayan wata d'aya da rasuwar Babama, abubuwa sun cakud'e min, ga aiki na gidan duk ni ke yi, wanke-wanke, shara, girki, wankin kayan mu. Ana gobe d'aurin auran teacher Kabir da Usaina na gudu saboda zuciyata bazata iya jure ganin auran teacher Kabir da wata ba, ba ni ba............ idan dai kin karanta daure ki yi Comment 'yar'u. More comment more typing 🖊 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Abokai na gaskiya suna da wuyar samu, suna da wuyar bari, suna da wuyar mantawa. Allah ka had'amu da abokai na gaskiya. Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 My Facebook group Fadila Sani. https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Shafi na 8&9. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, Oga Habib, wannan shine dalilin da ya sa, nahad'a kayana dadaddare na gudu, batare da kowa na gidanmu ya sani ba. Koda na fita gida lokacin duhu ya yi sosai. Tafiya nake amma ban san ina zani ba, ga duhun dare ya farayi, gashi tsakaninmu da titi akwai nisa sosai, haka na kama hanya ina tafiya ina sauri ga damuwa da tayi min yawa, ga yunwa rabona da abinci harna manta, sai dai in naji yunwa ta daman in dama kunu insha. Damuwa da yunwa da gajiyar da na yi ce, tasa na yanke jiki na fad'i ban sani ba, shine kuka tsinceni ainda kuka gani". Hassana kallan Habib ta yi, ganin har yanzu bai fasa typing d'in da ya ke yi ba. Ita fa gani ta ke kamarma duk surutannan tana yin shine kawai amma bajinta ya ke ba. Hassana kallan Habib ta kuma yi, cikin fargaba ta ce, "Oga Habib Wannan shine da lilin barina gidanmu". Hassana ta yi maganar da dad'ewa , dan hattacire ran Habib zai bata amsa ma.Sannan zuwa can ya d'ago kai yana kallanta, sai da Habib ya gama yima Hassana kallan cin mutunci sannan ya ce, "ya sunan ki ma kika ce? ". Hassana bakinta harrawa ya ke wajan ba Oga Habib amsa da cewa, "Hassana". Habib Kallanta ya yi, ya ce, "Hassana ke ba abin tausai ba ce, idan ke abin tausai cema tom ni ban tausaya miki ba, kuma ni bazan tai makeki ba. Duk wadda ta gudu daga gidan Iyayanta tom yawan bariki ta fito, dan haka fitar min daga office ". Habib ya fad'i maganar cikin d'aga murya. Jikin Hassana rawa ya farayi dan sosai ta tsorata da Habib. Hassana kuka ta farayi, cikin muryar kuka ta ce, "Oga Habib dan Allah ka yi hak'uri, Wallahi bayawan bariki na fito yi ba, kona zauna gidan b........ ". Tsawar da Habib ya yi ma Hassana ce tasa ta yi shiru. Habib nuna mata hanyar fita ya yi da hannu, ya ce, "fitar min daga Office na ce, stupid kawai! ". Hassana da saurin ta har tana d'an tintib'e ta fita daga office d'in. Saura kad'an Hassana su yi karo da Bilya shi kuma lokacin yazo shigowa. Bilya da d'an damuwa ya bita da kallo dan duk da bai san labarin yarinyar ba, sosai ta ke bashi tausai, acewar shi yarinya k'arama haka ace bata san ina zata ba. Bilya cikin tausan Hassana ya k'arasa office d'in Oga Habib.Bilya cikin girmawa, ya ce, "Barka da hutawa Oga Habib, ka yi hak'uri dan Allah ka kirani banzo da wuri ba, bana kusa ne". Habib kallan Bilya ya yi, sannan ya ce,fuskar shi a d'aure, alamun ranshi ab'ace ya ke. "Bilya me yasa ka kai k'arata wajan Momyna". Habib ya yi maganar cikin d'aga murya, dan shi aganinshi bai kamata ace yaron shiba, wanda ya ke ci ak'ark'ashin shi ya zartar da hukunci akanshi ace ya kai k'ararsa wajan mahaifiyarsa ba. Bilya cikin kame-kame ya ce, "Oga Habib ba...... ". Habib d'agama Bilya hannu ya yi, ya ce, "ka adana kala manka, amma kabar kama k'afa da son da Mahaifita kema, dan kar hakan yasa kaji zaka iya yin koma, wannan shine last worning da zanma, duk sanda ka sake ma hajiya complain akaina, daga ranar Bilya kabar aike a k'ark'ashin Sanat yoghurt". Habib na fad'in haka ya kalli Bilya, ya ce, " Bilya da kai da Baba Lami na baku, suspension na one month". Bilya da alamun tsoro ya d'ago kai yana kallan Habib, jin wai ya da katar da shi har wata d'aya.Bilya magana zai yi Habib ya nuna mai hanyar fita. Fita Bilya ya yi, batare da yace ko mai ba. Bilya na fita ya iske Hassana can bakin get d'in wajan tsaye, ta yi shiru ita kad'ai. Bilya gurinta ya k'arasa, kallanta ya yi sannan ya ce, "korarki ya yi ko? ". Hassana kai ta d'agama Bilya. Bilya shiru ya yi sannan, ya ce, " Ni Wallahi duk namarasa abinda zance miki, ni kaina yanzu haka ya dakatar dani aiki harna tsawan wata d'aya, ga aurena saura wata biyu masu zuwa, ni kaina yanzu kinga in da munyi haka dashi ba damar in kwana gidansu sai dai in koma d'akin abokina da kwana. Tom kuma itama Baba Lami bata san kowa ba a Abuja, kuma kinga ya dakatar da ita aiki itama, yanzu na san sai dai ta koma garinsu. Bilya shiru ya yi, yana tunanin yadda zai yi da Hassana amma bai sani ba,hakan yasa, ya ce, "Hassana ni yanzu ma kaduna zan tafi, ki zauna nan anjima kad'an zaki ga manager ya fito, zaki ganshi da red d'in shirt da black jeans. Ki mai magana, in dai ya amince ya d'auke ki aiki shikenan, Oga Habib babu ruwansa da d'aukar ma aikata". Hassana kallan Bilya ta yi, ta ce, "Tom Oga Bilya, wajan kwana fa?, in ya d'aukeni aikin? ". Shiru Bilya ya yi dan shi yama manta da wajan kwana sai yanzu ya tuna. Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce, "Hassana ki ci gaba da zama nan, idan kika ga Oga Habib ya fito, ki je ki sa ke rok'anshi, k'ila ya amince". Bilya na kaiwa nan, ya yi ma Hassana fatan alkairi ya tafi. Hassana cigaba da zama ta yi kamar yadda Bilya ya ce mata, tana jiran fitowar Oga Habib. Hassana har 8:00pm tana gun zaune, tana jiran taga fitowar Oga Habib amma shiru, Hassana tunini ta rik'ayi k'ilama ya tafi bata sani ba, inda ta je sallah. Wata zuciyar ta ce mata, tom idan ko haka ne ina zata kwana,uhm tom wai in ma naganshi lallene ya taimakan d'in. Hassana na cikin wannan tunanin taga motar Oga Habib ta fito. Hassana da saurinta har tana tuntub'e ta matsa wajan motar Habib d'in, shikuma lokacin ya tsaya yana ma mai gadin gun magana. Hassana ko kafin tak'arasa Habib ya yi ma motar shi key. Hassana tsabar furgici da rashin sanin yadda za tayi, kawai sai ta zauna gun tana kuka. Hassana na nan zaune tana kuka kamar wata ta b'abb'a, manager gun ya fito domin tafiya gida. Tsayawa ya yi ganin mutum a zaune, kuma bisa ga alama kamar kuka ya ke ji. Tsayawa manager ya yi ya fito daga motarshi, inda Hassana ta ke zaune tana kuka ya k'arasa. Tsananin hasken gun yasa tun kafin ya k'arasa ya k'are mata kallo. Kallanta ya yi da kyau sannan cikin siririyar muryar shi ya ce, "ke lafiya?, zaki zo nan ki zauna da daddarannan? ". Hassana da sauri ta d'ago kanta tana kallan manager. Manager ko jin Hassana ta yi shiru tana kallan shi, ya sa ya k'ara cewa, ", ke bakya ji ne! ? ". Ad'an tsawace ya yi maganar. Hassana kallan Manager ta yi, cikin muryar kuka ta ce, "Bansan ina zani ba ne". Manager da mamaki ya kalli Hassana, ya ce, "kamar ya baki san ina zaki ba?, tom waya kawoki nan? ". Hassana kai tsaye batare da tunanin komai ba, ta ce, "Oga Habib ne ya tsinceni shida Oga Bilya, shine ya kawo ni nan, ni kuma bansan kowa ba a Abuja, kuma ya hana in sake zuwa mai gida". Hassana ta idasa maganar cikin kuka. Manager shiru ya yi yana mai ci gaba da kallan Hassana, dan shi gaba d'aya bai gane takan maganarta ba. Manager waya ya ciro ya kira Oga Habib. Kira d'aya Habib ya d'aga yana tambayar manager lafiya, dan manager bai cika kiran shi airin wannan lokacin ba. Manager ko Habib na d'agawa ya ce, "M. D. Dama wata Yarinya ce nan na gani wajan get zaune tana kuka, shine dana tambayeta ta ce min wai kaika kawota, ni dai gata nan bama wai gane kan zancan nata nayi ba". Habib ba tare da tunani wata yarinya ba ce, dan in yaga dama yanada girki. Habib shiru ya yi sannan ya ce, "Manager kawo ta nan gida". Habib na cewa haka ya kashe wayarshi. Manager ko kallan Hassana ya yi, ya ce, "zo mu je". Hassana motar manager ta shiga. Manager gidan Habib ya kai Hassana kamar yadda Habib ya ce mai, ya kawo ta.Daya ke duk masu gadin gidan sun san Manager hakan yasa suna ganin shi suka bud'e mai get d'in ya shiga. Manager direct falon Oga Habib ya nufa, Hassana na biye da shi, sai kalle-kalle ta ke. Hassana azuciyarta ta ce, "Tabbas dole Oga Habib ya yi wulak'anci, ga kyau, ga kud'i, ga ilimi". Manager ko da ya je bakin k'ofar Habib nocking ya yi. Kasan cewar Habib ya san manager ne ya sa, ya ce, "yashigo". Manager shiga ya yi, da Hassana da ke biye da shi. Hassana sosai ta rud'e da had'uwa irin ta falon Oga Habib. Ko mai na falon milk & Orange ne. Habib ko kallo d'aya ya yi ma Hassana ya gane ta. Hakan yasa cikin d'an fad'a ya ce, "Manage dama wannan yarinyar ce? ". Manager cikin girmamawa ya ce, "M. D, ita ce". Habib kallan manager ya yi ya ce, "Manager me za ayi mata? ". "Tom M. D, nima dai ban sani ba, amma idan na fahimce ta kamar bata da wajan zama ne". Manager kallan Hassana ya yi, ya ce, "Dame za a tai maka miki? ". Hassana cikin sanyin muryarta mai cike da rauni ta ce, "Dan Allah aiki nake so kuban, sai kuma gurin da zan rik'a kwana". Manager kallan Oga Habib ya yi, sai yaga Habib ya d'auke idon shi akan shi. Hakan yasa manager ya ce, "Shikenan za ki rik'a mana swapping & mopping, morning &evening , zaki iya?" Manager ya kalli Hassana yana tambayarta. "Eh zan iya ". Cewar Hassana. Manager batare da tambayar Habib ba dan yasan in dai ya ce Habib zai tambaya, tom ba abin cewa zai yi ba, amma in ko ya riga ya yanke hukunci ya san sai dai ya yi mai tsiya daga baya. Hakan yasa manager ya ce, "Shikenan wajan kwana kuma sai ki rik'a kwana site d'in 'yan aikin gidan nan". Hassana cikin jin dad'in abin Manager ya ce, ta ce, "Nagode sosai, Allah ya saka maka da alkairi ". "Ameen". cewar manager. Manager Kallan Habib ya yi jin bai ce komai ba, hakan yasa manager Kallan Hassana ya ce, "Biyo ni in nuna miki site d'in worker's d'in gidan. Shi dai Habib na jin manager bai ce mai ko mai ba. Haka manager da kan shi ya kai Hassana b'angaran masu aikin gidan. Bayan ya kaita ne, ya koma yima Oga Habib sallama. Habib kallan manager ya yi, ya ce, "Manager ya zama First and last, ban hanaka d'aukar staff ba a company, amma ba dai zama nan ba, dan duk wata worker da ka gani agidan nan, Hajiya kawai suke ma aiki, amma ba Company ba". Manager hak'uri ya ba Habib, sannan ya ce, "Insha Allah, M. D, haka ba zai kuma faruwa ba, wannan ma tausai ta ban, ganinta mace bahaushiya da nayi, kuma daga ganinta tana buk'atar tai mako, amma ka yi hak'uri ". Banza Habib ya yi da shi. Manager tafi ya yi, dan ya san fushin kafin gobe ne, Oga Habib akwai saurin fushi, amma kuma baida wuyar sauka. Hassana ko da ta k'arasa b'angaran masu aikin, cikin girmawa ta gaida su, sai dai duk kansu wani irin kallo suke ma Hassana.Hassana cikin tsarguwa da kallan da suke mata ta gaidasu,. D'aya daga cikin su ce, ta ce, ma Hassana, "Baiwar Allah daga ina? ". "Nima ma aika ciyace kamar ku, sai dai ni ba acikin gidan nan zan rik'a aiki ba, a Sanat yoghurt zan rik'a aikina". Da mamaki dukkan su suka kalli Hassana, dan su aiya saninsu 'yan aikin gidannan ne kawai Hajiya turai ta yadda da su zauna anan. Wata wadda ake kira Jimmai daga cikin su, kallan Hassana ta yi, ta ce, "Baiwar Allah waye ya kawo ki gidannan? ". "Oga Habib". Hassana ta basu amsa kai tsaye , dan ta gaji da tambayoyin da su ke mata. Hassana guri ta samu d'an nesa da su ta kwanta, dan ta gaji sosai dan ma Allah ya tai maketa ta yi sallarta. Hassana kallan ma'aikatan gidan ta ke tana mamakin tom aikin me sukeyi haka, suke da yawa. Hassana kwanciya ta yi, tana kwanciya bacci ya d'auketa. Ma'aikatan gidan Hajiya turai sun sabo tun k'arfe shida na safe kowa ke tashi ya yi aikin da ya ke mazaunin nata. Hassana ko saboda gajiya kasa tashi ta yi. Jimmai wadda ta ke kusan sa'a da Hassana zuwa ta yi, ta bubbuga Hasana da ke kwance tana baccin gajiya. Hassana bud'e ido ta yi tana kallan jimmai. Jimmai ma kallan Hassana ta yi, ta ce, Baiwar Allah ki tashi hakanan, ki yi sallah mana. Hassana tashi ta yi tana kallan jimmai, ta ce, "Dan Allah ina make wayinku? ". Jimmai hannun Hassana ta kama ta ce, "muje in kai ki. Jimmai har toilet d'in su na ma'aikatan gidan ta kai Hassana sannan ta juyo ta dawo. Hassana da sauri ta yi sallah sannan ta kalli jimmai ta ce, "Dan Allah idan zani Sanat yoghurt, idan zan hau keke napep ina zan ce? ". Jimmai kallan Hassana ta yi, ta ce, "amma dai ke ba 'yar garinnan ba ce ko? ". "Eh ni ba 'yar nan ba ce ". "Ok, in kin samu keke napep ki ce zone, e nepar Sanat yoghurt duk wanda ya ke garin Abuja ai yasan sanat yughurt, za akaiki, har Sanat yoghurt. Hassana godiya ta yi ma Jimmai sannan ta kalli jimmai ta ce, "Dan Allah ko zaki ranta min kud'in keke napep d'in zan bi yaki, wallahi banda ko sisi". Jimmai kallan Hassana ta yi da tausayawa ta ce, "Nawa zan baki? ". "Nawa su ke kaiwa? ". Hassana ta tambayi jimmai. Jimmai d'ari biyu ta ba Hassana ta ce, "Gashi D'ari biyu ne ai ba nisa". Hassana amsa ta yi taima Jimmai godiya. Hassana har ta juya zata tafi Jimmai ta kirata ta ce, "Ba dai da kayan jikinki zaki tafi ba ko? ". Jimmai ta tambayi Hassana ganin kamar da kayan jikinta zata tafi.Hassana kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Banda kaya haka nazo ni kad'ai ". Jimmai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ya su nan ki ne?, kuma dan Allah ko zan iya sanin labarinki". Hassana ji tai zuciyarta ta aminta da Jimmai hakan yasa ta ce, "Sunana Hassana, kallo d'aya nai miki sai naji zuciyata ta aminta da ke, dan haka zan baki labarina amma ba yanzu ba, yanzu ina sauri zan tafi". Hassana na kaiwa haka ta juya zata tafi. Da sauri Jimmai ta kamo hannun Hassana ta ce, "Duk da baki ne mi sanin Sunana ba, Sunana Jimmai, idan ba zaki damuba kirik'a sa kayana kafin ki samu naki". Hassana sosai ta ji dad'in abinda jimmai tai mata, dama sosai ta ke jin kunyar fita da kayan jikinta dan sunyi datti sosai. Jimmai ko ta kurama Hassana ta yi tai wanka ta yi break fast sannan tata fi. Lokacin da Hassana ta isa sanart yoghurt, lokacin k'arfe goma na safe, ita da aikinta sharane da goge-goge su da ake buk'atar su je da wuri kafin kowa ya je dan su yi aikinsu. Hassana na shiga gurin ta na cin karo da manager. Sosai Manager ya yi ma Hassana fad'a akan zuwanta lale da ta yi, bayan yagama yi mata fad'ane ya mik'ama mata file d'in hannun shi, ya ce, ta kai Office d'in Oga Habib. Hassana tsayawa ta yi, tana kallan file d'in, sannan manager ad'an tsawace ganin bata amsa ba, ya ce, "Ki amsa mana ki kaima Oga Habib, ki ce mai ya yi marking d'in abubun da muke buk'ata ". Hassana amsa ta yi dan bata da yadda zata yi, amma bata so har ta gama aiki agurinba ta kuma shiga office d'in Oga Habib. Hassana cikin sanyinta ta tura k'ofar office d'in Habib ta shiga. Habib ko alokacin ya na kishingid'e kan sit, ya ji anturo k'ofar Office d'in shi an shigo.... ............ PLEASE COMMENT & SHARE. 📚OGA HABIB📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Mak'iyanka mutane uku ne:Mai k'in ka, da mai k'in masoyinka, da mai son mak'iyinka. Mai son uwa dole ne ya so d'anta. Allah ka had'amu da masu son mu fisabilillahi. Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA ZA A FARA POSTING. KI GARZA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 10&11 Habib da kallo ya bi Hassana da shi. Hassana ko cikin da burcewa da kallan da ya ke mata, ya sa ta mik'a mai file d'in hannunta, ta ce, "Oga Habib ga shi inji manager ya ce ka yi marking d'in abubun da ake buk'ata". Hassana ta idasa maganar muryarta na rawa. Habib amsar file d'in ya yi, batare da ya kalli ko inda ta ke. Habib na amsar file d'in Hassana ta juya da saurinta tafita office d'in. Hassana na fita office d'in Habib ta had'u da wata staff itama agun ta ke aiki, amma ita tana cin masu programme d'in sanat yoghurt. Hassana da sauri ta k'arasa gunta ta ce, "Baiwar Allah dan Allah tambaya na ke? ". Wadda Hassana ta kira da ke, juyowa ta yi tana ma Hassana wani kallan lafiya. Hassana itama kallanta ta yi, azuciyarta ta ce, kai gaskiya 'yan aikin gunnan suncika ji da kai, sai kace wasu masu aikin banking. Ita ko staff d'in nan jin Hassana ba ta ce mata ko mai ba, ya sa juya ta cigaba da tafiyarya zuwa inda zata. Hassana ganin ta tafi ta barta gun tsaye da sauri tasha gabanta, ta ce, "Yi hak'uri dan Allah office d'in manager na ke nema? ". Wani irin kallo ta ke ma Hassana dan ita bata tab'a ganin Hassana ba a ma'aikatar nan ba. Hakan yasa ta kalli Hassana ta ce, "Wacece ke? ". Hassana batare da tadamu da irin kallan da ta ke mata ba, ta ce, "Ni new worker ce a factory nan". Da hannu ta nuna mata office d'in manager ta juya tayi tafiyarya. Hassana ko kanta a k'asa ta juya ta nufi office d'in manager. Hassana na zuwa cikin girmamawa ta gaida manager dan tana ganin girmansa sosai, tai makon da ya yi mata. Hassana kallan manager ta yi, ta ce, "Oga Manager dama bansan site d'in da zan rik'a mopping bane". Manager kallan Hassana ya yi, ya ce, " supervisor zaki ma magana. Ki ji Office d'in kusa da nawa ita zata fad'a miki site d'in da zaki rik'a morpping d'in". Hassana fita ta yi daga Office d'in manager ta shiga office d'in ku sa da na shi. KyKkyawar budurwa ce, a ganinda nai mata baza ta wuce twenty five years ba. Zaune ta ke tana ta aikin dan na laptop d'in da ke gabanta. Hassana cikin girmamawa ta ce, "Barka da aiki Aunty". Da sauri Billy ta d'ago tana kallan Hassana jin sunan da ta kirata da shi. Cikin b'acin rai Billy ta ce, dan ita jin kanta ta ke kamar wata 'yar seventeen years. Hakan yasa cikin d'aga murya Billy ta ce, "Uwar ki ce Aunty ".dan ita aganinta Hassana kallan girma tai mata shiyasa ta kirata da Aunty. Ita ko Hassana girmamata ta yi. Hassana cikin girmawa ta ce, "Yi hak'uri dan Allah, ban sanda sunan da zan kiraki da shi bane, shiyasa". Billy kallan Hassana ta yi, ta ce, "me ki ki so? ". "Ni sabuwar ma aikaciyarku ce, Oga manager ne ya d'aukan aiki zan rik'a shara da goge-goge, shine Manager ya ce inzo Office d'in ki, ke ce zaki fad'amin b'angaran da zan rik'a sharewa da gogewa".Billy kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ai muna da 'yan mopping da yawa, amma inda ya riga ya d'auke ki, ki rik'a mopping d'in site d'in da engine su ke, amma fa dole zaki rik'a zuwa da wuri". Hassana kallan ta ta yi, ta ce, "Aunty ai bansan site d'in ba". "Ki samu wata staff d'in ki tambayeta zata nuna miki". Hassana godiya ta yi mata ta juya zata tafi.Hassana ta na fitowa daga Office d'in supervisor ta had'u da wani staff da suka had'u jiya. Cikin zakin fuska da washema Hassana baki, yak'araso inda Hassana ta ke. Kallan Hassana ya yi, ya ce, " 'Yan mata ina fatan dai kin samu aiki". Hassana cikin sakin fuska itama ta bashi amsa, ta ce, "Eh Wallahi na samu". "Kai amma nai miki murna, kina cikin masu programme d'in sanat yoghurt ko? ". Hassana kai ta girgiza mai ta ce, "Ni aikina sharane da goge- goge". "Ok, karki damu wata rana zaki zamama d'aya daga cikinmu, wasinmu duk daga haka suka fara, kin san dai aikin Company sai nada hak'uri, dan haka ki yi hak'uri ba kamar da supervisor d'in mu ba".Hassana kallan shi ta yi, ta ce, "Dan Allah inane site d'in ku d'in can ne b'angaran da ta ban aikin". Staff d'in nan da mamaki ya kalli Hassana, ya ce, "Kai, kin sanfa da yake batada hankali taba masu sharar gun suspension, gaskiya gun ya yi miki yawa ke kad'ai. Amma kinga yanzu ke new worker ce be kamata ki fara kai complain tun yanzu ba, amma daga kin yi one week ina yi bata dawo da wa inda ta ba suspension ba, tom ki kai ma manager complain akan haka". Hassana godiya ta yi, mai sannan suka jera ya je ya nuna mata inda zata rik'a sharewa da gogewa, duk Hassana ta saba aikin wahala agida amma tasan wannan gun yafi k'arfin sharar mutum d'aya. Hakan yasa Hassana ta kalli staff d'in da ya rakora gun ta ce, mai"gaskiya gunnan ya yi min girma, bazan iya shareshi da goge shi ba ni kad'ai ba". Kallan Hassana wannan staff d'in ya yi sannan ya ce, "Gaskiya sai dai ki yi hak'urin kwana ko biyu ne tukun nan, dan kinga wa inda ta dakatarma jiya su biyu daga sun mata magana akan tak'aro masu wasu gun ya yi masu yawa su kad'ai, shikenan wai su je gida su huta na wata biyu sai su dawo, Kin san manager gun nan sonta ya ke shiyasa ta ke abinda taga dama, ita kuma hankalinta nakan Oga Habib". Hassana shiru kawai ta yi, amma tasan zata sha wahala ace aikin da wasu sukeyi su biyu suka kasa abata shi ita kad'ai.staff d'in nan kallan Hassana ya yi, ya ce, "Tom ni dai Sunana kabiru, amma mutane na kidana da barber for ladies,ki fa ya sunan ki? ". murmushi Hassana ta yi mai sannan ta ce, "Sunana Hassana". kabiru kallan Hassana ya yi, ya ce, "kai amma gaskiya kinada suna mai dad'i , bari in je in yi abinda zanyi, sai anjima in munhad'u". Kabiru ta fiya ya yi yabar Hassana gun tsaye tana kallan yadda ma aikatan ke ta aikin d'ura yughurt d'in da akai cikin robobi. Hassana na nan tsaye tana kallan aiki ga wani irin k'amshin swtrovery da ke tashi agun. Hassana na nan tsaye ta ji, andafa ta. Da sauri Hassana ta waigo tana kallan wadda ta da fata.matashiyar budurwar ce, zasu iya zama sa'a da Hassana, kallan Hassana ta yi, ta ce, "Amma dai ke new worker ce anan ko? ". Kai Hassana ta d'aga mata. "Ai dama tunda naga kina sauraran kabiru na san ke sabuwar ma'aikaciya ce nan, abinda zan fad'amiki ki rabu da Kabiru dan daga ganinki kina da mutunci da kamun kai, kabiru ko d'an iskan mai rai ne, biki ji sunan shi ba, barber for ladies,sannan idan supervisor tazo ta ganki tsaye ahaka, zaki samu matsala. B'angaran me ye aka d'auke ki". Hassana kallanta ta yi, ta ce, "shara da goge- goge". "Tom kinga ga rack can d'akko shi zaki yi, duk abinda ya zube kina gogewa, ki tafa bata yadda ta ganka a tsaye ba". Hassana godiya ta yi mata, sannan ta zo gusa da su, da morpper d'inta duk abinda ya zube tana gogewa. Kafin lokacin tashi ya yi Hassana ta share duk inda ya ke ak'ark'ashin ai kinta. K'arfe 8:00pm Hassana ta fito domin ta fiya gida, sai a lokacin Hassana ta tuna bata da ko sisi, gashi tun d'azu taga fitar manager bare ta fad'a mai inda taga alamar yana da kirki sosai. Hassana wajan parking space ta shiga tana zuwa ta motar Oga Habib agun, azuciyar ta tace bai tafiba kenan, Ya Allah banda yadda zan yi kuma bazan gane gidan ba, Allah ka bashi ikon d'aukata. Hassana guri ta samu ta zauna tana tunanin yadda zata iya yima Oga Habib magana ya d'auketa. Wata zuciyar ta ce, kai Wallahi bazan iya ba, dan ko nayi ma ba d'aukata zai yi ba, wata zuciyar ta ce mata, tom idan baki mai magana ba, ai kin kwana a titi. Hassana na zaune tana wannan tunanin ga tunwa duk ta da meta, tun tea d'in da Jimmai ta bata da safe tasha har yanzu shi kad'ai ne a cikinta, d'azu tana gani staff d'in gunna fita cin abinci amma ita bata da kud'i sai dai ta hakura. Hassana na nan zaune, ta ga fitowar Oga Habib, yana zuwa ya fad'a motar shi. Hassana da sauri ta tashi ta nufi gun motar Oga Habib............... TOFA IDAN OGA HABIB BAI D'AUKI HASSANA BA, YA ZATA YI????? 🙆‍♀️🙆‍♀️ ANYA KO KUNA GANIN OGA HABIB ZAI IYA D'AUKAR HASSANA????? COMMENT & SHERE PLEASE 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy Baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 My Facebook group:Fadila Sani. https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ MATSALOLINMU A YAU GUDA BIYU NE:MU YI AIKI KAFIN MU YI NAZARI, KO MU YI TA NAZARI BA AIKI. ALLAH KASA MU RIK'A AMFANI DA LOKUTAN MU. SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA ZA A FARA POSTING. KI GARZA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 12&13. Hassana cikin fargaba ta k'arasa gun motar Oga Habib. Sai dai Hassana na k'arasawa gun shi kuma yana sama motar shi key ya bar gurin. Hassana d'agama Habib hannu ta ke amma Habib na lure da ita, ya yi tafiyar shi, yana maganar zuci, ba dai yarinyar nan tana nufin in d'auketa bane a motata ko. K'wafa Habib ya yi yaja motar shi ya tafi. Hassana ko rasa yadda zata yi ta yi, hanya ta kama takama tafiya a k'asa dan tana ganin zata Kane gidan. Tafiya sosai Hassana ta yi sannan ta isa gidansu Oga Habib. Lokacin 11:30 pm.Hassana na zuwa ta iske anrufe get d'in gidan, tom dama daga Habib ya dawo ake rufe gidan.Hassana cikin fargaba ta fara bubbuga get d'in gidan. Hassana ta dad'e atsaye tana bubbugawa sannan d'aya daga cikin get man's d'in gidan yazo yana tambayar waye. Hassana cikin tsoro da jin yadda ya yi mata magana ta ce, "Hassana ce sabuwar ma aikaciyar da Oga Habib ya d'auka jiya". Tom a k'a'idar gidan su Oga Habib duk 'yar Aikin da aka d'auka sai an nuna ma masu gadin gidan gaba d'aya ita dan su shaida fuskarta. Wannan umarnine daga Hajiya turai. Hakan yasa ya koma ya tambayi sauran masu gadin, akan ko sun san da d'aukar sabuwar mai aiki a gidan. Nan suka ce mai a'a. Jennies dawowa ya yi, ya ce, ma Hassana, su babu wata mai aiki da aka d'auka jiya, dan haka tabar gun kafin ya fito. Hassana cikin kuka da da nasanin barin gidansu da ta yi, ta ce, "Wallahi da gaske na ke, ka tambayi Oga Habib, ni ce wadda Oga Bilya drivern Oga Habib ya kawo, tom jiya suka d'aukan aiki, ko yau ta get d'in nan na wuce". Shiru ya yi dan ya ji maganar ta kamar da k'amshin gaskiya, hakan yasa ya ce, "Ok, bari in kira Oga Habib tukun, idan yace abarki ki shigo tom zan bud'e miki, amma idan yak'i sai dai ki yi hak'uri". Jennies number Habib ya kira. Lokacin Habib ya yi nisa sosai a bacci, ringing d'in wayar shine ya ta da Habib daga bacci. Habib cikin murya bacci ya d'aga wayar batare da ganin Number ko waye ba, ya sa akunne. Jennies naji Habib ya d'aga wayar ya ce, "Oga Habib dama wata Yarinya ce ta zu yanzu tana nocking get wai jiya aka d'auketa aiki a gidannan". Habib najin haka ya yi tunanin yarinyar nan ce, acewar shi. Habib ce mai ya yi karka bud'e mata. Yana cewa haka ya kashewar. Jennies buga get d'in ya yi, ya ce, ma Hassana "knji ko, Oga Habib ya ce bai sanki ba, dan haka ki bar nan yanzun nan! ". Hassana matsawa ta yi daga jikin get d'in. D'annesa da get d'in, Hassana zuk'unna ta yi tana kuka.Habib ko tashi ya yi, ya zira jallabiyar shi ya nufi wajan get yana jan tsaki. Habib na zuwa ya yi ma d'aya daga cikin ma'aikatan magana, ya ce, "kubud'e min get ". Bayan an bud'e ma Habib get d'in fita ya yi, can nesa da gidansu yahangi Hassana zaune ta tura kanta tsakankanin cinyoyinta tana kuka. Habib daga idan ya ke tsaye, ya kira Hassana ya ce, "keee!! ". Hassana cikin tsoro tata shi zata gudu. Sai ji ta yi, Habib ya kuma cewa, "kee bakya jine". Hassana da katawa ta yi daga gudun da za ta yi, ta k'arasa in da Habib ya ke tsaye. Habib kuma yana ganin Hassana ta taho ya shiga cikin gidan. Hassana shiga ta yi ita ma, Hassana nashiga ta iske Habib tsaye kamar ita ya je jira. Hassana k'arasawa in da Habib ya ke ta yi. Habib wani irin kallo ya yi ma Hassana mai cike da ma'anoni da dama, sannan ya ce, "Daga yau in dai kika wuce 7:00pm baki dawo ba, tom karki kuma buga ma mutane get, idan ba haka ba kuma Habib ya nunata da hannu, ya ce, "Sai dai ki nai mi gurin zama, amma ba dai gidannan ba". Habib na fad'in haka ya tafi yabar Hassana nan tsaye k'irjinta na dukan uku-uku.Hassana cikin sauri ta je site d'in su, har sun rufema ta buga masu, suka bud'e mata. Jimmai ce ta tashi ta bud'e ma Hassana k'ofar, dama tun da zu ta ke tunanin lafiya, jin Hassana shirun da ta yi.Jimmai na bud'ewa ta kalli Hassana ta ce, "Hassana lafiya dai ko?, na jiki shiru tun d'azu". "Kud'in napep ne banda shi, a k'asa na dawo shiya sa". Jimmai sosai ta tausayama Hassana sannan ta d'akko ma Hassana abincin da ta d'ibar mata ta bata". Hassana nagama cin abincin ta kwanta ta kama bacci, dan sosai ta gaji. Washe gari da wuri Hassana ta tashi ta yi wanka, ta sa kayan Jimmai kamar yadda jimmai ta ce ta rik'a sawa, Sannan Jimmai ta ranci kud'in napep gurin karima, taba Hassana. Hassana sosai ta yi ma Jimmai godiya sannan ta ta fi. Hassana na isa ta ta cigaba da sharar b'angaran ta. Kafin wani lokacin Hassana ta gama share gurin ta goge". BAYAN SATI D'AYA. Yau sati d'aya kenan da fara aikin Hassana a sanat yoghurt. Kullum Jimmai ke rantar kud'in napep tana ba Hassana, da sunan idan wata ya yi, anyi albashi Hassana ta biya su. Yau ma Hassana da wuri tata shi domin tafiya sanat yoghurt Company. Hassana sai da tama shirinta, ta tambayi Jimmai kud'in napep. Jimmai kallan Hassana ta yi ta ce, "Hassana Wallahi yau sai dai ki yi hak'uri , kin san ni dama daga wata ya yi an bani salary na na ke kaiwa gidanmu, tom wadda na ke rantar mi ki kud'i gurinta kuma, Wallahi ita ma kud'inta sun k'are". Hassana shiru ta yi tana tunanin mafita , dan tasan sai dai ta je ak'asa, kuma idan har ta je a k'asa tom tabbas baza ta iya sharar da ta ke ba, dan yanzu haka ciwan baya ta ke, dan gurin nada girma kuma ita kad'ai ke aikin sharesa da gogesa. Hassana kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Jimmai ya zanyi?, dan Wallahi supervisor d'in mu bata da kirki ko ka d'an,bata karb'ar uzirin mutum in dai bai je aiki ba". Jimmai dafa Hassana ta yi, ta ce, "K'awata ni gani na ke yi ki yi hak'uri da zuwa yau inda ya za ki yi, ba ki da kud'in napep ". Hassana kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Jimmai zata fa iya korata aiki akan haka, nace miki bata da kirki".Shiru Jimmai ta yi, sai zuwa can ta ce, "Yauwa k'awata ko zaki je wajan get ki jira idan Oga Habib zai tafi sai ki fad'a mai baki da kud'in napep yau ba za ki samu zuwa aiki ba"Hassana da fe k'irji ta yi ta kalli Jimmai, ta ce, "Jimmai rufa min asiri, kin san ko waye Oga Habib!?". Dariya Jimmai ta yi, ganin yadda Hassana ta dafe k'irji, ta ce, "Hmm Hassana ke nan, ni ko nasan waye Oga Habib, bashi da d'igon kirki ko kad'an, dama dan naji kin ce shiya d'auke ki aiki ne,shi yasa. kuma tunda har ya barki ki ke zaune anan ai ke da dama-dama, ni da ko hanya bana so ta had'ani da shi, dan ni Wallahi tsoran shima na ke ji". Hassana kallan Jimmai ta yi da mamaki, ta ce, "Ki ce ba ni ka d'ai ke tsoransa ba, amma shine ki ka ce in rok'ai kud'in napep, bacin kin san ba ban zai ba, sai dai ma k'ila ya yi min wulak'anci". "Hakane k'awata ki yi hak'urin zuwa yau, zuwa gobe insha Allah zamu san yadda za ai". Hassan tom kawai ta ce ma Jimmai dan bata da yadda zatai. Amma tana tunanin yadda zasu kaya da supervisor d'in". Can sanat yoghurt ko,haka akai aiki gun batare da anshare ba, ko angoge. Yau kwana uku kenan Hassana na zaune gida bata da kud'in zuwa company. Tom kuma dama Hassana ce kad'ai mai sharar b'angaran, Billy duk ta ba sauran masu sharar suspension. Yaune kuma abokan Habib wa inda su kai karatu tare suka kawo mai ziyarar bazata. Habib na zaune a office d'in shi ba zato ba tsammani, ya ji nocking. Izinin shiga Habib ya basu. Sai dai Habib sumar tsaye ya yi, da mamaki ke kallansu, rungume su su duka biyu Habib ya yi, ya ce, "Faruq, Nasir, zan rama, nima duk sanda zan yi visiting naku, sai dai ku ganni, ba bu Anousing". Habib zama ya yi yana nuna masu gurin zama. Wanda Habib ya kira da faruq, kallan Habib ya yi, ya yi murmushi ya ce, "Habib Allah ba zuwan siri bane mu kai, yanzu dai babu lokaci, mu shiga ciki Nasir yaga factory naka". Habib jagora ya yi masu yana kaisu kona suna gani. Wanda aka kira da Nasir ko sai yaba girman gurin ya ke, da tsaruwa irin ta gurin ya ke. Faruq, kallan Habib ya yi, ya ce, "Habib kasan Allah ina jin dad'in Yoghurt d'in ku sosai,dan gaskiya mutanan Taraba, suna son yughurt d'in ku sosai, dan manyan-manyan restaurant d'in Taraba duk inda kaje zaka samu sanat yoghurt". Murmushi Habib ya yi mai, ya ce, "Kasan ko kwanannan na ke son juwa Taraba dan bud'e sabon Company acan". "kai Habib, wai yanzu state nawa ke da branch a can". "Kano, Kaduna, sai nan Abuja". Habib suna tafiya suna tattauna da abokansa har suka isa, site d'in da ake Yoghurt d'in. Duk company babu inda ya kai gun girma, kuma site d'in ne Hassana ke aikin sharewa da gogewawa. Gashi yau har kwana uku kenan Hassana bata zoba, gun ya yi datti sosai dan har k'udaje ke ke waye gun saboda yadda ya yi. manager ko yau satin shi d'aya kenan da yin tafiya, yabar komai a hannun supervisor. Habib sosai ya ji kunyar yadda friend's d'in sa suka ga gurin. Hakan yasa Habib ya ja su suka koma Office d'in shi. Habib na kai su Office ya dawo gun ranshi ab'ace yana kallan ma'aikatan gun, Habib cikin daka tsawa da b'acin rai, ya kalli ma'aikatan gun ya ce, "Aikin waye wannan!? ". Yafad'i maganar ya na nuna gurin da hannu shi. Dukkan su shiru su kai dan ba sanin sunan Hassana su kai ba. Hakan yasa Habib ya kalli d'aya daga cikin staff d'in ya ce, "ki ramin supervisor ". Wanda Habib ya aika da saurinsa yabar gun ya nufi office d'in, Bill. Billy na zaune da waya rik'e a hannunta tana charting ta ji ana mata nocking. Billy izinin shigowa ta bata. Staff d'in da Habib ya aika, kallan Billy ya yi, ya ce, "Sister Billy Oga Habib na kira". Billy kallan staff d'in ta yi, ta ce, ka ce mai ganinan zuwa, yana office d'in shi ne? ". "A, a yana site d'in mu". Yana fad'in haka ya juya ya tafi. Billy kuwa jin Habib na kiranta powder ta k'ara shafawa da lipstick abakinta, sannan ta fita. Habib na tsaye ranshi ab'ace, ga shi shi a ganinshi Billy ta b'ata mai lokaci. Habib na nan tsaye yana huci Billy ta tahu tana yauk'i ita Allah dole ga wadda Oga Habib ke kira. Billy na zuwa gaban Habib ta tsaya kamar zata shige jikinsa, ta ce, "Oga Habib ga ni". Habib ko, kallan k'askanci ya yi ma Billy sannan, ya ce, "Yama sunan ki? ". Billy cikin mamaki wai ita Habib ke ce ma ya sunanta. Billy kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib yanzu kamant.... ". Habib hannu ya d'agama Billy sannan ya ce,"Daga nan zuwa minti shafiyar idan har ba agyara gurin nan ba, tom ki gama aiki a sanat yoghurt, sannan wannan ya zamana na farko da na k'arshe, aiki kika zo yi ko shirme?, in dai baki gyara ba tom zamu da katar da ke! ". Habib na fad'in haka ya juya ya bar gun ranshi b'ace ya bar gun. Billy kuka ne kawai ba tai ba , dan a cewarta Habib ya tozartata gaban staff. Hakan yasa Billy ranta b'ace ta ce, "Wata idiot d'in ce ke kula da site d'in nan". Wata daga cikin sttaf d'in ce ta ce, "supervisor new worker d'in nan ce, kuma yau kwana uku kenan bata zo ba, ina jin bata da lafiy.... ". Tsawar da Billy tai mata ce yasa tai shiru, ta ce"Allah yasa ubanta ne ya mutu tabar aiki amasana'artannan, kuma sai naci mutuncinta fiye da wanda Oga Habib ya ci min............ COMMENT &, SHERE PLEASE 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Fabby baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 Facebook group :Fadila Sani. https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ IDAN KA MUTU AN RUFE LABARINKA, AMMA ABUBUWA UKU SUNA RAYUWA A BAYANKA: ☝🏻ILIMI DA ✌️HAIHUWA SAI AIKIN ALHERIN DA KA SHUKA. ALLAH KA SA MU DACE👏. SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA ZA A FARA POSTING. KI GARZA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 14&15. B'angaran friend's d'in Habib, Habib na koma wa Office d'in su kai mai sallah su kace tafiya za su yi. Habib godiya ya yi masu sosai, sannan yasa aka cika masu bayan But d'in su da yoghurt. B'angaran Hassana ko, Yau ta tashi da niyyar ko ak'asa ne sai ta je aiki dan zaman ya isheta, ga tsoran supervisor d'in su da ta ke yi, dan ana yawan fad'a mata rashin mutuncinta. Hassana da wuri ta shirya kamar yadda ta saba shiryawa ta kama hanya ak'asa ta tafi. Hassana ba ita ta isa sanat yoghurt ba, sai 9:30Am. Ita da ke zuwa tun seven o'clock. Tom dama Billy ta bada sak'o ta ce idan Hassana tazo aiki ace mata tana nai manta a office d'in ta. Hakan ce ta kasan ce, Hassana na zuwa wata daga cikin staff d'in ta sanar da ita sak'on supervisor d'in. Hassana cikin fargaba ta tura Office d'in supervisor ta shiga. Lokacin Billy na zaune tana aikin danna waya. Hassana cikin girmama ta ce, "Barka da aiki supervisor". Da kai Billy ta amsa ma Hassana. Hassana kuma ci gaba da tsayuwa ta yi, tana jiran hukuncinta. Ita ko Billy tama manta da wata Hassana, hakan yasa ta kalleta ta ce, "Lafiya za ki zo ki tsamin akai? ". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Supervisor dama wata staff ce ta ce kince idan nazo aiki nazo kina kirana". Hassana ta ci gaba da cewa, "Supervisor Wallahi rashin kud'in napep ne ya hanani zuwa aiki, kwana uku da banzo ba, ko yauma ak'asa nazo". Billy bar abinda ta ke yi awaya ta yi, ta d'aga kai tana kallan Hassana, ta ce, "Ki ce mai sharar site d'in da ake yoghurt ko? ". "Eh ni ce". Cewar Hassana. "Billy kallan Hassana ta yi da b'acin rai dan sai abinda Habib ya yi mata yadowo mata farko, hakan yasa cikin d'aga murya ta ce, "Hassana ki ke ko me!?, mun da katar da ke aiki a k'ark'ashin sanat yoghurt Company ". Hassana cikin tsoro da fargaba jin abinda Billy ta ce mata, ta ce, "Supervisor dan Allah ki yi hak'uri insha Allah daga yau haka bazai kuma faruwa ba". Billy ko inda Hassana ta ke bata kalla ba ta ce, "Nariga na gama magana, ki kalli time kigani ko yanzu k'arfe nawa kikazo aiki?, bama aiki da wanda bashi da experience, fitar min daga Office! ". Hassana fita ta yi batare da ta k'ara cewa ko mai ba, Hassana na fita ta nufi Office d'in Manager ".manager na zaune Hassana tai mai nocrking. Izinin shiga manager ya ba Hassana. Hassana shiga ta yi,Hassana cikin girmamawa ta gaida manager. Manager cikin sakin fuska ya amsa ma Hassana, ya ce, "Hassana lafiya dai ko? ". Hassana kamar zata yi kuka ta ce, "Manager supervisor ta dakatar da ni aiki". Manager cikin tsoro ya d'aga kai yana kallan Hassana. Shiru manager ya yi na d'an wani lokaci sannan ya kalli Hassana ya ce, "me kika yi mata? ". Hassana cikin sanyin muryarta, ta ce, "Banzo aiki ba kwana uku, bani da kud'in napep, ko yauwa ak'asa nazo". Shiru manager ya yi, sannan ya ciro kud'i yaba Hassana ya ce, "Hassana amshi kud'innan kinji sai ki amfani da su, ki yi hak'uri kinji naso kiyi aiki anan, tom amma inda haka ya faru sai dai hak'uri ". Hassana amsa ta yi taima manager godiya jin abinda ya ce, ta fita daga Office d'in. Hassana na ta fito daga Office d'in manager ta had'u da staff d'in da ta bata sak'on supervisor na kiranta. Staff d'in cikin tausayama Hassana ta k'araso inda Hassana ta ke, ta ce, ta koreki ko? ". Kai Hassana ta d'aga mata ta ce, " Ta kore ni, na yi ma manager ma magana ma ko zai sa baki, amma ya ce min inyi hak'uri ". staff d'in kallan Hassana ta yi ranta ad'an bace, ta ce, "Ni da nasan zaki gurinsama da na hanaki, ai indai supervisor ta yanke hukunci bai iya yin komai, sai dai ya baka hak'uri bai iya sab'a maganarta". Hassana sallama ta yi ma staff d'in ta tafi dan maganar ma da kyar ta ke yinta. Cikin kud'in da manager ya ba Hassana ta hau napep ta koma gidansu Oga Habib, duk da zuciyarta cike ta je da bargabar komawa gidan, in da yanzu tabar aiki ak'ark'ashin su, haka nan Hassana ta koma inda bata da yadda zata yi.Jimmai cikin mamaki ta ke kallan Hassana ganin Hassana ta dawo gida yanzu.Jimmai k'arasawa inda Hassana ta ke ta yi, ta ce, "Hassana lafiya kuwa naganki kin dawo? ". "Supervisor ta koran aiki". Jimmai ta fe k'irji ta yi tana salati, ta ce, "manager kuma ya sani? ". "Eh ya sani, wai budurwarsa ce ba ya musu da abinda ta ce, inji wata staff". Jimmai shiru ta yi, tana jimamin abinda ya faru. Hassana kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Jimmai tom kina ganin babu damuwa inci gaba da jama gidannan yanzu bana aiki ak'ark'ashin su? ". Jimmai kallan Hassana ta yi ta ce, "Tom nima dai ban sani ba, amma dai yau Hajiya turai zata dawo ai, shiyasama kikaga ko ina gidan aiki ake, tom ki bari ta dawo mugani". WACECE HAJIYA TURAI?. Hajiya turai babbar macece cikakkar 'yar boko. Ita kad'ai ce awajan mijinta wato Alhaji Idris mai kanti. Tun Habib na yaro Mahaifinsa ya rasu, hakan yasa Habib bai san Mahaifinsa ba. Hajiya turai babbar 'yar jarida ce, yanzu haka Hajiya turai a B. B. C, London ta ke aiki, hakan yasa kusan koda yaushe Hajiya turai bata Nigeria.Ji da kai da miskilanci Habib duk a gurin Mahaifiyar shi ya gada. Hajiya turai tun da ta haifi Hassana k'anwar Habib ta tsaida haihuwa, dan ita gani ta ke baza ta iya d'awai niyar yara uku ba. Hassana ta yi girma kusan 18 years sannan Allah ya yi mata rasuwa, sanadiyar wata bak'uwar 'yar aiki da Hajiya turai ta d'auka aiki, ashe had'in kai ne akai da ita aka zuba ma Hassana guba ta ci, wannan ne sanadiyar mutuwar Hassana har lahira. Mutuwar Hassana sosai ta d'agama Habib hankali dan idan ka cire Hajiya turai mahaifiyar Habib, tom babu wanda Habib ya ke zama dashi sunyi hira su ci abinci tare sai Hassana, yana kiranta da sanat, wannan shine dalilin da koda zai bud'e Company yin yoghurt ya sa ma mai suna Sanat yughurt. Tun rasuwar Hassana ya sa Hajiya turai ta bar yadda da kowa yana shigo mata gida barkatai. Wannan shine dalilin da yasa Hajiya turai har 'yan Aiki ta daina d'auka tuma ta ke rik'e wa inda ta ke dasu da mahimmanci bata yadda Habib ya koresu ko sun yi wani abun, duk da ta yi kashedi sosai akan d'aukar wata sabuwar mai aki bata nan, wannan shine dalilin da yasa koda aka kai mata labarin zuwan Hassana taima Habib fad'a. Wannan ke nan". Sosai 'yan aikin gidan Hajiya turai ke shirin tarbar ta. K'arfe hud'u na yamma jirginsu ya sauka, idan Habib da kan shi ya je ya d'akkota. Habib har falon Hajiya turai ya kaita, sanan ya kalleta yana murmushi ya ce, "Mommyna kin gaji ki yi wanka ki kwanta ki huta, sai kici abinci ko? ". Murmushi Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Tom Habib ko na kwanta worker's d'in gidan baza su barni in yi bacci ba, nasan yanzu zasu fara yimin aikin sannu da zuwa". Habib d'an b'ata rai ya yi, sannan ya ce, "Mommyna ki kwanta ni zan yi gadinki babu wadda zata shigo falon ki sai in kin tashi". Habib na fad'in haka ya fita ya ce, yana zuwa. Habib b'angaran 'yan aikin gidan ya je, kafin ya k'arasa ya samu Hassana da Jimmai suna wanki tare. Habib wani kallo ya yi masu wanda ya rikirkitasu du kansu, duk suka daburce. Bakamar Hassana ba da ta ke tsoran ko gurinta yazo yasan ankore aiki yazo ne ya koreta shima, hakan yasa Hassana cikin sark'ewar murya ta ce, "Ina wuni Oga Habib ". Habib banza ya yi da Hassana, sannan ya kellesu dukan su ya ce, "Hajiya ta dawo, kar wadda ta yi kuskuran shiga gurinta yanzu, sai bayan magriba". Habib na fad'in haka ya juya. Hassana ko da Jamila kusan tare suka had'a baki wajan cewa, "tom babu wanda zai shiga zamu fad'a ma sauran". Habib na tafiya, Jimmai ta kalli Hassana ta ce, "Ni dai Hassana duk da halin Oga Habib na wulak'anta mutane Wallahi yana burgeni sosai". Kai Hassana ta jinjina ta ce, " Ni dai abinda nasani kawai, nasan Oga Habib mai kyau ne shi, dan duk inda ake nai man maza masu kyau za asa shi, amma Wallahi bai tab'a burgeniba". kai Jimmai ta jinjina sannan ta ce, "Hassana bari in je in sanar da sak'on Oga Habib, dan yanzu za kiga 'yan iyayi sun fara shiga". Jimmai sak'on Habib ta je ta sanarma duk wata wadda ke aiki agidan. Bayan jimmai ta dawo ne ta kalli Hassana ta ce, "Hassana zaki gaida Hajiya ko?, dan idan ma baki jeba sai magulmata sun kai mata gulma, kuma in dai suka rigaki zuwa gaskiya akwai damuwa". Shiru Hassana ta yi, sannan zuwa can ta ce, "Zan je, kawai dai ina fargaba ne idan tak'i amintar zamana". "A'a insha Allah zata zauna da ke, ai Hajiya bata da wani damuwa sosai". Nan dai Jimmai taita kwantarma Hassana hankali akan zuwa gaida Hajiya Turai da zasu anjima. Aiko kamar yadda Habib ya tsara haka akai, dan babu 'yar aikin da tashiga gaida Hajiya Turai, kamar yadda suka sabayi da. Hajiya Turai bayan tata shine masu kai mata abinci sun kai mata taci, ta gama ci, tana zaune a falon ta, nan fa worker's d'in gidan suka fara zuwa da d'ai-d'ai da d'ai-d'ai suna gaidata, Habib na zaune gefan Hajiyarsa suna fira, dan idan Hajiya Turai ta dawo dama indai yana gida tom yana falonta, babu inda zaka ga Habib sai a falon Hajiya Turai. Jimmai da Hassana sune kusan k'arshen zuwa, Hassana cikin fargaba da fad'uwar gaba ta shigo falon Hajiya Turai, dan sallama ma sai dai Jammai ce ta yi masu. Tun kafin su zauna Hajiya Turai ta nuna Hassana da hannu ta ce, "Jimmai wacece wannan? ". Kafin Jimmai ta yi magana Baba lami wadda ke aiki cikin falon Hajiya Turai, ta ce, "Hajiya ai wannan zata yi sati biyu agidannan, nima dai ina ganinsu da Jimmai, dan rashin wayar da nayi ne ma da na sanar da kai ". Hajiya Turai kallan jimmai ta yi da ta yi shiru tana kallan Baba Lami, tana cewa azuciyarta dama ita ce me kaima Hajiya Turai gulma in bata nan. Hajiya Turai ko cikin alamun son d'aga murya ta ce, "Jimmai bakya ji ne?, na ce wacece wannan? ". Ta fad'i maganar tana nuna Hassana da hannu". Jimmai cikin dabir cewa, ta ce, "Hajiya sabuwar 'yar aiki ce ". Hajiya Turai kallan Hasssana ta yi ta ce, "Waye ya d'auke ki aiki? ". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "manager ne". Hajiya Turai cikin mamaki ta ce, "Manager kuma, wana manager? ". Hassana ada barce taba Hajiya Turai amsa, da cewa, "Manager me aiki Company sanat yoghurt". Hajiya Turai mai da kallanta ta yi ga Habib da ke zaune kamar bai jin abinda ake cewa, ta ce, "Habib wai me yarinyar nan ta ke son ce min ne?, nina cema manager Ina naiman k'arin mai aki da zai d'aukar min 'yar aiki, kiramin manager kabanshi awaya". Habib kallan Hajiya Turai ya yi yadda ta ke fad'a daga cewa an d'auki me aiki. Habib cikin sanyi ya ce, "Mommy ki bari anjima zan kira miki shi please ". Hajiya Turai mai da kallanta ta yi gun Hassana ta ce, "Ki je sai kuzo da manager ". Hassana tsuk'unnawa ta yi, kamar za tai kuka ta ce, "Hajiya dan Allah ki yi hak'uri, bansan gidan manager ba, hasalima ya koran aiki".Hajiya Turai rasa takan zancen Hassana ta yi. Hajiya Turai magana ta za ta yi, sai ji tai Habib ya ce, "Me yasa manager ya koreki aiki? ". Yadda Habib ya yi maganar babu yadda za ai ka ce da Hassana ya ke". Hassana kallan Habib ta yi, sannan ta ce, "Bani da kud'in napep ne, kwana uku banje aiki ba, ranar da aka koranma ak'asa naje, amma ko da naje sai aka ce Supervisor ta ce in je office d'in ta tana kirana, shine da naje ta ke sanar dani ta dakatar dani aiki, da nafad'ama mana yace sai dai in yi hak'uri ". Hassana ta idasa maganar cikin fargaba dan tana tsoran kar Habib ya ce sai dai tabar masu gida. Habib batare da ya kalli Hassana ba ya ce, "Go be ki koma aiki, kuma karki yadda ki wuce magriba baki dawo ba, Hajiya ta dawo dawuri zamu rufe gida, wuce ku tafi". Hassana da Jimmai da sauri suka tashi suka bar falon. Bayan su Hassana sun tafi ne, Hajiya Turai ta ce, "Habib bangane ba, kasan dai bana buk'atar k'arin mai aiki ko? ". Habib kallan Hajiya ya yi, cikin na tsuwa ya bata labarin yadda akai suka tsinci Hassana shida Bilya, da kuma labarin Hassana gaba d'aya haka Habib ya ba Hajiyarsa dan hankalinta ya kwanta, dan ya lura ta tsorata sosai da abinda ya faru shekaru biyu da suka wuce. Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Shikenan ba damuwa ta ci gaba da aikinta ". Nan Habib ya zauna suka cigaba da hira da Monmynsa sai dare sannan ya je ya kwanta. Washe gari Hassana da wuri tata shi ta yi shirin zuwa aikinta da kud'in da manager ya bata da su ta biya kud'in napep. Hassana cikin fargaba da fad'uwar gaba tashiga sanat yoghurt, dan tana tsoran yadda zasu kwashe ita da supervisor................. COMMENT & SHERE PLEASE 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 Facebook group :Fadila Sani. https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ BABBAN MABUD'IN ALHERI SHI NE ISTIGFARI. IDAN KA YAWAITA SHI MATSALOLINKA ZA SU KAUCE, DAMUWARKA ZA TA GUSHE, SAUK'I ZAI ZO MAKA. ALLAH KASA MU DACE👏👏👏. SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA ZA A FARA POSTING. KI GARZA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 16&17. Hassana cikin tsoran Billy ta shiga cikin Sanat yughurt. Hassana direct inda ta ke sharewa ta nufa ta kama aikinta. Duk staff d'in da tazo da mamaki ta ke kallan Hassana, dan su asaninsu duk wadda Billy ta dakatar ta tafi kenan, hakan yasa suke bin Hassana da kallon mamaki. Hassana ta gama share gun tana morpping Billy ta shigo site d'in. Billy tun daga nesa ta ke kallan Hassana, dan tabbas idan idonta ba gizo ya ke mata ba, yarinyar da ta kora aiki jiya ce ta dawo yau. Hakan yasa Billy ta k'arasa inda Hassana ta ke.Billy kallan Hassana ta yi da kyau sannan ta ce, "Ke ba ke bace jiya na dakatar da ke aiki a Company nan? "? Hassana d'agowa ta yi tana kallan Billy sannan ta ce, "Ni ce". Wani kallo Billy taima Hassana sannan ta ce, "Ok, biki ji bane sai na kuma maimai tawa ko me!? ".Hassana kallan Billy ta yi, ta ce, "supervisor Oga Habib ne yace in dawo in cigaba da aiki". Billy kallan mamaki tai ma Hassana, dan tana da tabba cin k'arya tai ma Oga Habib. Hakan yasa Billy kallan Hassana ta ce, "Ke kafin insa ad'aukeke afitar dake daga nan, ki sauri ki bargunnan stupid kawai". Hassana kallan Billy ta yi ta ce, "Supervisor Wallahi Oga Habib ne ya ce in dawo". Shiru Billy ta yi tana tunanin tom ina Hassana zata ga Oga Habib, dan ko ita sai da dalili mai k'arfi ta ke shiga office d'in Oga Habib bare kuma Hassana, cewarta acikin zuciyarta. Hakan yasa Billy kallan Hassana ta ce, ki bar aikin kisaman office d'in manager". Billy na fad'in haka ta juya ta tafi office d'in manager. Hassana bayan Billy ta fi, ta sameta office d'in manager kamar yadda Billy ta buk'ata. Billy ko na shiga office d'in, manager ta kalli Manager tana nuna mai Hassana ta ce, "manager waya dawo da yarinyar nan aiki? ". Manager shima da mamaki ya kalli Hassana, ya ce, "Hassana waya dawo da ke aiki, bacin Supervisor ta dakatar da ke? ". Hassana kallan manager ta yi, ta ce, "Oga Habib ne ya ce indawo in cigaba da aiki". Billy ranta b'ace jin abinda Hassana ta kuma cewa ta ce, dan ita yanzu tafi tunanin manager ne yadawo da Hassana ya ce tace Oga Habib ne yadawo da ita. Inda ita a tunaninta Hassana ina zata ga Oga Habib, in ma taganshi tasan bata isa ba ta kai mai k'arar andakatar da ita aiki. Hakan yasa Billy ranta b'ace ta kalli manager ta ce, "Manager yau d'in nan zan aje aiki, Inda ni ban'isa in yanke hukunciba, in dai yarinyar nan bazatabar aiki anan ba, tom sai dai ni in aje aiki! ". Manager cikin damuwa ya kalli Hassana ya ce, "Hassana taya M, D, ya san ankoreki aiki? ". Hassana kallan manager ta yi ganin yadda ya damu jin Billy ta ce zata bar aiki. Manager dakama Hassana tsawa ya yi ganin Yana tambayarta ita kuma tunanin ta ke, ya ce, "Ke bakya jine?, nace taya M. D, yasan andakatar da ke aiki!? ". Hassana kallan manager ta yi ta ce, "Jiya Hajiyar Oga Habib ta dawo, tom bacin naje gaidata ne, ta ke tambar waya d'aukeni aiki, tom shine bayan nasanar da ita, nake fad'a mata amma andakatar dani aikin, tom da yake Oga Habib na gurin zaune, shine ya ke tambayata waya dakatar dani shine nace mai supervisor ce, shine yace yau in dawo aiki".manager kallan Billy ya yi yace tom kinji yadda akai". Billy itama kallan manager ta yi ta ce, "Wai bangane ba, idan nagane kana nufin yarinyar nan causing d'in Oga Habib ce ko me?, naji tana maganar gidansu ta ke ne kome ?". Manager kallan Hassana ya yi ya ce," je ki cigaba da aikinki". Hassana fita office d'in ta yi tabar manager da Billy". Bayan Hassana ta fita ne, Billy ta kalli manager ta ce, "Manager ni fa gaskiya banyarda da dawowar aikin yarinyar nan ba". Manager cikin taushin murya ya ce, "Tom Billy yanzu ya ki ke so ayi, aidai kinji daga m, d, ne dawowar ta". "Eh naji daga Oga Habib ne, amma ai yanzu idan kaje kasamu Oga Habib ka ce mai kai ka dakatar da ita, nasan zai yarda, idan kuma bahakaba ni zan bar aiki anan, dan sai ta d'auka ita sa'atace, shiyasa ni na koreta aka dawo da ita". Manager kallan Billy ya yi, ya ce, "Billy Yarinyar nan da kike gani m, d, da Bilya driver m, d, ne suka tsinceta, tom bata da Inda zata zauna shine dalilin ma da yasa M, D, barinta gidansu, nina rok'anmata, yanzu idan ya koreta ina zata?, ki yi hak'uri daga yau zata gyara ". "Shikenan badamuwa amma ta kiyaye ta rik'a zuwa aiki da wuri". cewar Billy, sannan ta fita daga Office d'in manager". Hassana ko komawa ta yi taci gaba da aikinta, Hassana na tsaka da aiki ne, wata staff ta kalli Hassana ta ce, "Ke ce Hassana? ". "Eh ni ce". "Tom Supervisor ta ce idan kin gama morpping d'in ki je tana kiranki". Hassana da tom ta amsa. Aiko Hassana na gama wa ta je office d'in supervisor ta ce, "Supervisor ance kina kirana". Billy sai da tagama abinda ta ke yi, sannan ta ba Hassana wani Cup ta ce taje ta wanke mata. Hassana amsa ta yi ta je ta wanke mata ta kawo mata. Bayan Hassana ta dawo ne, Billy ta kalli Hassana ta ce, "Hassana ki ke kome, dama kunne zanja miki, sannan kinsan ya zama dole a hukuntaki abisaga laifin da ki kai, na fashin da ki kai baki zoba, daga yau sai 10 o'clock zaki rik'a close". Hassana kallanta Billy ta yi ta ce, "Supervisor dan Allah ki yi hak'uri,Oga Habib ya ce kar in wuce magriba ban dawo ba".Billy Cikin d'aga murya ta ce, "Oh!, kina nufin duk da laifin da ki kai har wani ragin lokaci kika samu, tom wannan kuma ke ya shafa ni dai kinji abinda na ce miki, idan kuma kink'iji zamu rage a salary d'inki". Shiru Billy ta yi sannan ta nuna ma Hassana hanyar fita, ta ce, "fitar min daga office. Hassana fita ta yi tana mamakin yadda Billy ke nuna mata tsana k'iri-k'iri". Hassana magriba na yi, kamar yadda Habib ya ce mata ta koma gida, magriba na yi Hassana ta shirta ta koma. Tun daga wannan rana ya zamana kullum Hassana ta je aiki Billy ta dinka sata aiki kenan, daga yi min wancan sai yi min wancan, har wankin toilet d'in gun Billy Hassana ta ke sawa, acewarta abakacin tashin da wurin da ta ke yi. Ita kuma Hassana ta yi ma kanta alk'awarin duk abinda Billy ta sata zatayi baza tai mata musuba, hakan ya sa Hassana ta kuma ramewa sosai. BAYAN SATI D'AYA. Hassana sosai ta dage sai goge-goge ta ke yi so ta ke tagama tai ma manager magana ta tafi gida, saboda ciwan da kanta ya ke mata. Hassana na Cikin aiki wata staff ta ce, Hassana kije Office d'in manager ana kiranki". Hassana sauri ta yi tak'arasa abinda ta ke yi, sannan ta je office d'in manager. Hassanan da mamaki ta ke kallan shi ta ce, "Oga Bilya kaine, yau she kadawo? ". Bilya murmushi ya yi ma Hassana sannan ya ce, "Hassana tun jiya na dawo,ya kike ya aiki? ". "Lafiya klau, barka da dawowa Oga Bilya". Bilya kallan Hassana ya yi yace, " Yauwa Hassana, zaki iya ko mawa ki ci gaba da aikinki, dama nakiraki ne mugaisa. Hassana kallan manager ta yi tace, "Manager bani da lafiya, dan Allah ina son zuwa gida yau da wuri in samu magani insha". Manager kallan Hassana ya yi, sannan ya ce, " ki fad'ama supervisor ". Hassana shiru ta yi dan tasan in dai ita ce ma babarinta za tai ba, amma ance mai naima baya fushi, hakan yasa ta fita Office d'in manager ta shiga na supervisor. Hassana na zuwa ta kalli supervisor ta ce, "Supervisor bani da lafiya, ina son zuwa gida dan Allah, zan sha magani". ko inda Hassana ta ke Supervisor bata kallaba, ta ce, " Idan kin je karki dawo". Hassana najin haka tafita office d'in supervisor dama tasan ba barinta za tai ba. Hassana haka ta koma guri d'aya ta zauna dan bata iya komai tsabar ciwan kan da kanta ke mata. Hassana ba ita ta tashi ba sai magriba kamar yadda ta saba tashi. Hassana tafiya ta rik'ayi a k'asa kafin tasamu napep ga wani irin ciwo da kanta ke mata". Bilya ko yadawo bakin aiki, saboda Hajiya Turai na dawowa tasa Habib ya dawo da shi. Habib da sauri ya fito domin tafiya gida baya son magriba ta sa mai anan. Bilya ko dama yana ganin time d'in tafiya gidan Habib ya yi, ya shiga motar yana jiran fitowar Habib. Hakan yasa Habib na shiga Bilya jaya motar suka kama hanya. Bilya tsaye ya hanki Hassana can gefan titi daga gani abin hawa ta ke jira. Bilya Kallan Habib ya yi, ya ce, "Oga Habib dan Allah ga Hassana can ko zamu rage mata hanya? ".Habib banza ya yi da Bilya. Bilya ko jin Habib ya yi banza dashi yi tunanin ko be ji abinda ya ce bane, hakan yasa ya k'ara cewa, "Oga Habib ga Hassana can na ce, dan Allah ko murage mata hanya? ". Habib tsaki ya ja alamun Bilya ya da mai, Bilya ko najin haka ya kama bakinsa yayi shiru. Bilya yana ji yana gani suka wuce Hassana tsaye badan yaso ba, sai dan bashi da yadda zai yi. Habib sai da ya yi Sallar magriba sannan ya shiga site d'in Mommynsa. Habib na shiga ji yayi kamar ya juya ya koma, sai dai bashida yadda zai yi tariga ta ganshi, hakan yasa Habib ya kuma tamke fuska ya shiga falon.Farida da saurinta ta tashi zata yi welcoming d'in Habib. Habib hannu ya d'aga ma Farida. Farida ja tai tatsaya tana Kallan Habib kamar za tai Kuka, ta ce, "Broz Habib kana nufin bakai murnar ganinaba? ". "Yess ". Cewar Habib. "Farida bana murnar ganinki saboda shirman da kike min". Farida Kallan Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Mommy kinji fa abinda Broz Habib ya ce, wai baya murnar ga nina". Farida ta fad'i maganar kamar zata yi kuka. Hajiya Turai hannun Farida ta kamo tana murmushi ta ce, Farida rabu da Habib shi bai san wacece Farida bane"., Habib ko ji yayi ba zai iya jure zama ba afalon Hajiya Turai hakan yasa Habib Kallan Momynsa ya ce, "Mommy zan shiga ciki ki bada tea akawomin". Hajiya Turai Kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib gobe zan wuce, jirgin safe zan hau". Habib Kallan Hajiya Turai ya yi , cikin damuwa ya ce, " Kai Mommy wannan karan kin koma da wuri".murmushi Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Habib kamar kana da damuwa Allah kalli face d'in ka ? ". "Babu abinda ke damuna Mommy". Habib na fad'in haka ya wuce. Habib falon shi ya je yana jin wani iri acikin jikin shi, amma yarasa gane shikan shi me ke damunsa. Habib na nan kwance Farida ta shigo rik'e da tea a glass cup. Habib bai cika cin abinci ba da daddare sai dai yasha tea. Farida har inda Habib ya ke , ta k'araso, tea d'in hannunta ta mik'ama Habib ta ce, "Broz Habib gashi in ji Mommy ta ce kasha dan Allah badan ni ba".Farida ta yi hakane saboda tasan da wuya Habib ya sha tea d'in. Habib amsa ya yi ita kuma Farida ta fita dan bataga fuskar zama ba. Habib haka ya ke jin shi wani iri ahaka ya samu sha tea d'in. Yana gama sha ya tashi ya yi Sallar issha'i sannan ya kwanta, dan sosai ya ke jin jikin shi ba dad'i, bakamar brain d'in shi ba tana mai ciwo sosai, haka dai Habib ya samu wani wahalallan bacci ya kwasheshi. Washe gari tun asuba, Hajiya Turai taima Habib magana, ya shirya dan seven o'clock Am, ta ke son tafiya. Habib tashi ya yi badan wai yaji sauk'in yadda ya ke ji ba, wanka ya yi, ya yi shirinsa Cikin wata dark blue suit. Habib mota ya zauna yana jiran fitowar Hajiyarsa. Hajiya Turai da Farida suka fito Farida na rik'e da jakar Hajiya Turai. Hajiya Turai amsar jakarta ta yi hannun Farida ta ce, Farida ki koma gida. Farida ba Hajiya Turai ta yi saboda bata so tana mata musu. Bayan Hajiya Turai ta shiga motar, kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib ko dai zuwan Farida ne yasa naganka haka so silent". Habib kallan Mahaifiyarsa ya yi, ya ce, "Mommyna bashi bane, nima haka na ke jin jikina duk babu dad'i, ga jiya nayi wani mafarki da yaban tsoro sosai, amma karki damu nayi addu'a, kuma yanzu normal na ke jina". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Shikenan Habib, amma dan Allah kaje Hospital ka yi check up, dan Allah Habib na sanka da shiririta". Habib ganin Hajiya Turai ta damu, yasa ya kalleta yana murmushi, ya ce, "Mommyna normally fa nake jina yanzu, karki damu yanzu daga na kaiki airport zan je ganin likita". Habib action ya rik'ayi kamar mai lafiya, dan yasan in ya nuna ma mommysa ba ya jin dad'in jikinsa tom bazafa tatafi ba. Koda Habib ya kai Hajiya Turai airport. Hajiya Turai rak'on Habib ta yi sosai akan ya je Hospital aduba shi, nan dai Habib ya yi mata sallama ya nufi sanat yoghurt Company". Habib na zuwa Office d'in shi ya shiga, Habib na shiga ya kira Bilya awaya, ya ce, "Hello, Bilya ina sanat yoghurt, ka biya restaurant d'in kusa damu ka tahomin da abin break fast". Habib na fad'in haka ya katse kiran. Bilya ko lokacin da Habib ya kira shi tashinshi a bacci kenan, hakan yasa Cikin sauri Bilya ya shirya yaja motar shi yafita. Da safe da kuma dare Habib tea kawai ya ke iya sha, sai wainar k'wai. Bilya na shiga Sanat yughurt , ana sauke Hassana ita kuma a napep. Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce "Yauwa Hassana dan Allah amshi break fast d'in nan ki kai Office d'in Oga Habib. Hassana tsayawa ta yi tana kallan Bilya ta ce, "Oga Bilya dan Allah ka kaimai da kanka Allah bana son shiga office d'in Oga Habib. Bilya mik'ama Hassana ya yi, ya ce, "Hassana haka nan zakiyi Hak'uri ki amsa, tun d'azu Farida ke kirana in zo in kawota Sanat yughurt, Wallahi na manta sham sai yanzu na tuna, tom shine ke so inje in d'akkota, yanzu idan na shiga office d'in Oga Habib zai iya sani wani abun, ba zai barni in fito yanzu ba, dan Allah ki amsa ki kai mai". Hassana amsa ta yi ta ce, "Haba Oga Bilya, ai Umarni zaka bani na aikata ba sai ka rok'eniba". Dariya Bilya ya yi ya ce, "Bakomai Hassana girmanki ne, bari in je in dawo dama Wallahi ina son wata magana mai mahimmanci da ke". Hassana itama murmushin ta yi tace, "Tom Oga Bilya sai kadawo". Bilya tafiya ya yi Hassana kuma tana rik'e da break fast d'in Habib ta nufi office d'in shi". Hassana nocking ta yi. Tad'an dad'e atsaye tana nocking sannan Habib ya bata izinin shiga. Hassana na zuwa Cikin girmama ta ce, "Barka da safiya Oga Habib ga shi inji Oga Bilya, ya ce yanzu zai dawo". Habib batare da ya amsa gaisuwar Hassana ba, dan zuwa yanzu sosai ya ke jin ciwo acikin jikin shi. Habib kallan Hassana ya yi, sai zuwa can ya tashi kamar zai amshi jug d'in hannun Hassana, sai kuma ya fasa, ya dafe kanshi da hannun shi guda d'aya ya mik'ama Hassana d'ayan hannun nashi, yana rin tse ido, ya ce da k'arfi dan har wanda ke waje sai da yaji. "Ahhhh rik'e min hannunaaaa!!? Habib ya fad'i maganar da k'arfi yana mik'ama Hassana hannun shi. Hassana sosai ta tsorata, Hakan yasa ta saki jug d'in hannunta ta bud'e k'ofar Office d'in zata fita. Sai dai ina ta makara kafin ta bud'e kofar sai dai taji anjawo hannunta da k'arfi..................... A'A, WAI ME KE FARUWA NE?, NI FA BANGANEBA. NASAN WASINKU DA DAMA ZASU CE HAKA. KARKU DAMU ZAKU GANE. LABARIN YANZUN YAFARA💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 BANDA LAFIYA DAN ALLAH INA BUK'ATAR ADDU'ARKU. COMMENT & SHERE PLEASE 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI ( Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 My Facebook group :Fadila Sani. https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ 🍃 Ibnul-Qayyim (Allah Yayi masa Rahama) yana cewa: *"Lalle damuwa, baƙin ciki da qunci suna faruwa ne ta dalilai guda biyu: _Daya daga cikinsu shine son duniya da nemanta (ta kowace hanya), na biyu kuma rashin aikata ayyukan kwarai da (kyautata) ibada"_* 📒 [Iddatus-Saabireen - P. 265]. Allah kasa mu dace. SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA ZA A FARA POSTING. KI GARZA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 18&19. Hassana sosai ta tsorata, hakan yasa ta saki jug d'in hannunta ta bud'e k'ofar Office d'in zata fita, sai dai ina ta makara kafin ta bud'e k'ofar sai dai taji anjawo hannunta da k'arfi, an dawo da ita baya. Hassana cikin tsoro ta d'aga kai tana kallan Habib". Habib ko rik'e hannun Hassana ya yi da k'arfi da d'ayan hannunsa, d'ayan hannun kuma ya dafe kan shi da shi. Hassana da Habib kusan atare suka yi k'ara wadda duk kusan wanda ke cikin Sanat Company babu wanda bai ji k'ararnan ba". Ita Hassana k'arar tsoran yanayin da taga Habib ne ta yi, shi kuma Habib ta sabon yanayin da yatsinci kan shi cike ce. Hassana cikin tsoro ta kalli Habib tana cewa, "Wayyo hannuna Oga Habib dan Allah ka yi hak'uri kasakanmin hannu". Hassana ganin Habib kamar ba cikin hanyyacin shi ya ke ba, kuma ya rik'e hannunta katakam, ga zafin rik'on da ya yi mata take ji. Hakan yasa Hassana ta dage sai ihu ta ke". Dai-dai likacin ne kuma Bilya da Farida suka shigo Sanat company. Bilya da Farida da saurinsa suka k'arasa shiga cikin Sanat company. Inda suke jiyo ihun suka nufa. Dai-dai lokacin shima Manager ya fito daga Office d'in shi da sauri ya nufi na Oga Habib dan anan ya ke jiyo sautin k'arar. Atak'aice dai duk wani ma'aikacin da ke cikin Sanat yughurt, da saurinsa ya ke nufa inda ya ke jin alamun k'arar mutum". Manager da Bilya kusan atare suka turo k'ofar office d'in Oga Habib, inda Farida da Billy suka mara masu baya. Bilya cikin tashin hankali ya nufi inda Habib ya ke, ganin yarik'e hannun Hassana kata kam, yak'i saki, sai wasu magan-ganu da yake yi kad'an-kad'an, bazaka iya jin me yake cewa ba, kodan ihun da Hassana ta ke yine". Bilya cikin girmama da fargabar ganin yanayin da yaga Habib, ya ce, "Oga Habib lafiya karik'e mata hannu?, idan laifi taima dan Allah ka yi hak'uri ". Habib kallan Bilya ya yi yana zazzare ido. Bilya kallan Habib ya kuma yi da kyau, dan sosai abinda Habib ya yi ya ke naiman d'aure mai kai, dan asanin Bilya mata ma masu aji Habib bai kulaba bare kuma Hassana da ke a k'ark'ashinshi. Sannan idan ya lura da kyau kamar Habib bacikin hayyacin shi ya ke ba. Hakan yasa Bilya kama hannun Habib da niyyar fusge hannun Hassana. Wani duka Habib ya ke ma Bilya a wuya, wanda sai da Bilya ya yi k'ara. Bilya da sauri ya matsa yana kallan Habib. Bilya manager ya kalla yana dafe gefan wuyan shi inda Habib ya nusai, yace, "Manager lafiyar Oga Habib k'alau kuwa? ". Manager kallan Bilya ya yi, ya ce, "Nima abinda nake tunani kenan, amma bari mugani". Manager matsawa ya yi kusa da Habib ya ce, "M. D, dan Allah ka yi hak'uri idan laifi taima, kasakar mata hannu yau zamu koreta daga ma'aikatar nan baki d'aya ". manager ganin Habib ya yi banza da shi yana kallan shi, hakan yasa ya kama hannun Habib da niyyar b'amb'are na Hassana". Habib duka ya kawo ma manager. Allah ya tai maki manager ya kauce da sauri. Tun daga nan fa kowa ya fara baya-baya. Hassana ko ganin haka suna nai man fita subarta daga ita sai Habib, ya sa ta fasa kuka tana cewa, "Wayyo Allah Oga Bilya dan Allah karku tafi, manager dan Allah kuzo ku taimaka min". Bilya kallan manager ya yi dadamuwa yace, manager akwai damuwafa, Wallahi Oga Habib baida Lafiya, dan kai kasan wannan abinda da yake yi ba halinsa bane, idan zaka kalli idon shima kamar baya cikin hayyacinsa". Manager numfasawa ya yi sannan ya ce, "Wallahi maganarka hakane, nima abinda nake tunani kenan, yanzu ya kake ganin za ai? ". Shiru Bilya ya yi, Sannan ya ce, "Ni gani nake kawai mu kwaci yarinyar nan daga hannun shi, mu kai shi gida, ala bashi sai a kira likitan k'wak'walwa ya duba shi". "Eh haka za ayi". Cewar manager. Manager wasu k'arfafan samari da ke aiki gurin guda biyu yasa su tai maka masu". Bilya da manager ne suka yi jarimtar rik'e Oga Habib, sannan sauran staff d'in guda biyu suka k'wace hannun Hassana daga hannun Oga Habib da kyar. Sosai su manager suka sha wahala wajan sa Oga Habib a mota. Sannan Bilya ya shiga ya tuk'a motar da manager da Faruq kuma suka rik'e Oga Habib. Ahaka dai suka samu suka k'arasa gidansu Oga Habib". Hassana ko bayan ta samu an kwaceta da kyar daga hannun Oga Habib guri ta zamu tazauna tana sare hawayanta, da kuma al'ajabin abinda yasa mu Habib. Hassana na nan zaune supervisor tazo tana mata wani irin kallo mai ma'anoni da dama. Billy kallan Hassana ta yi tace, "Hassana ki ke ko?, sannu Hassana gaskiya kinyi k'okari, sai dai ina baki shawar duk abinda ki kaima Oga Habib kafin Hajiyarsa ta dawo ki yi gaggawar warware shi". Billy na fad'in haka ta juya ta tafi, tabar Hassana nan tsaye da baki sake tana kallanta". Hassana maganar zuci tafara, "Tom wai me supervisor ta ke nufi da duk abinda ta yi ma Oga Habib, tom ita mai tai me?, me zata yi gaggawar warware wa?". Nan dai Hassana ta gama tunaninta bata gane takan zancan Billy ba ta tashi". Can gidan su Oga Habib ko, da kyar su manager su kama Oga Habib suka shigar dashi d'aki, sai dai suna sashi suka rufe d'akin. Bilya hankalin shi ta she ya ke kallan manager ya ce, "Manager karfa ace Oga Habib hauka ya ke, dan abin ya tadamin hankali, kalli yadda ya ke bige-bige! "."tom Wallahi nima haka ne tunani, dan bisaga alamu wannan abinda ya ke kamar hauka ne, tom yanzu in ma munkira likita taya zai duba shi ayarda ya ke haka d'innan? ". Cewar manager. Shiru Bilya yi yi sannan ya ce, "Gasakiya na fara tunanin kiran Hajiyarsa in fad'i mata halinda Oga Habib ya ke ciki, kasan hausawa sun ce da zafi-zafi ake dukan k'arfe, gara ai gaggawar fad'a mata, in dai Hajiya ce a yauma zaka iya ganinta, ko gobe da wuri". Haka ko akai, Bilya kiran Hajiya Turai ya yi yi, Bayan sun gaisa ne ya ce," Hajiya a kwai damuwa fa, Oga Habib bashi da lafiya, kuma gaskiya yana yin ciwan yana buk'atar ki zo kusa da sauri". Hajiya Turai shiru ta yi , sannan cikin damuwa ta ce, "Bakomai Bilya ganinan zuwa, idan na sauka idan nasamu ticket zan juyo yau". Hajiya kamar yadda ta ce haka akai, tana sauka jirgi ta nemi ticket d'in Nigeria Allah ya te maketa ta kuma samu". K'arfe sha biyu na dare, jirginsu Hajiya Turai ya sauka. Bilya ne ya je d'akko Hajiya Turai. Hajiya Turai na issowa ta kalli Bilya cikin tsantsar damuwa, ta ce, "Bilya kai ni in ganshi". Bilya cikin lallashi ya kalli Hajiya Turai ya ce, "ki yi hak'uri Hajiya yanzu nasan k'ila ya samu bacci zuwa gobe sai ki ganshi". Hajiya Turai cikin d'aga murya ta ce, "Bilya kana nufin in kwanta in yi bacci banga halinda Habib ya ke ba, kai yanzu kana ganin zan iya bacci batare da na duba jikin Habib ba? ". Shiru Billy ya yi, sannan ya ce, "Hajiya ki yi hak'uri, Wallahi bazai yuwuba ne ki ganshi, ki dai bari sai goban"."You are very stupid, Bilya ko kana hauka ne!, ko-ko wani abinne ya sa mai kuke b'oyemin!!? ". Hajiya Turai ta idasa maganar kamar zata yi kuka. Sannan ta ci gaba da cewa, "Bilya wai baku kira Family doctor mu bane ya duba shi? ".Bilya ganin Hajiya Turai tana nai man rud'ewa ya sa, Bilya cikin sanyin murya mai kwantar da hankali, ya ce, "Hajiya ki yi hak'uri, ina mai bak'in cikin sanar da ke halin da Oga Habib ya ke ayanzu haka, Hajiya Wallahi da kyar muka samu daga Sanat Company muka kawo shi gida, ayanzu haka maganar da na ke miki babu mai iya shiga inda Oga Habib ya ke, amma ban sani ba ko inda ke Mahaifiya ce zaki iya ganin shi". Hajiya Turai kuka ta fasa, ta ce, "Innalilahi'wa inna'ilaihirraji'un , Bilya muje inga Halinda ya ke, dan Allah Bilya muje ka kaini". Hajiya Turai hanyar part d'in Habib ta yi cikin tashin hankali ta na goge hawan da ke zubar mata". Bilya tsayawa ya yi yana jiran Hajiya Turai ta shiga. Hajiya Turai ko na zuwa ta bud'e kofar ta afka. Sai dai kwance ta iske Habib yana bacci ya yi kaca-kaca da d'akin. Hajiya Turai zuk'unnawa ta yi tana kuka kad'an-kad'an gudin karta tada Habib daga bacci. Bilya jin Hajiya Turai shiru, ya sa ya shiga d'akin, cikin damuwa Bilya ya kalli Hajiya Turai dan sosai ta bashi tausai, hakan yasa Bilya cikin damuwa ya kamo hannun Hajiya Turai, ya ce, "Ki yi hak'uri Hajiya kizo muje ki kwanta ki huta karki tada shi". Hajiya Turai tashi ta yi tabi bayan Bilya tana goge hawayanta, bayan sun fita ne, Hajiya Turai ta kalli Bilya ta ce, "Bilya dan Allah ko zaka koma ka kwana da shi? ". Shiru Billy ya yi sannan ya kalli Hajiya Turai, cikin taushin murya ya ce, "Hajiya Wallahi ko ke dan Oga Habib na bacci ne kika samu ganinshi, amma Wallahi idan idon shii biyu bazaki tab'a iya shiga inda ya ke ba, kwana wajan shi da akwai had'ari". Hajiya Turai tana kuka ta kalli Bilya ta ce, "Bilya kana nufin Habib duka yake?, idan haka ne kana son cemin Habib hauka ya ke kenan? ". "Tom Hajiya bandai sani ba , amma dai tabbas Oga Habib duka ya ke". Hajiya Turai ta fiya tayi tana Kuka tashiga site d'inta". Hajiya Turai adaran kusan zaune ta kwana, tsabar fargabar abinda ke damun Habib. Bayan Hajiya Turai ta Idar da Sallar asuba ne ta tashi ta shiga room d'in da Farida ta ke kwana, dan taga alamar Farida bata san ta dawo ba. Sai dai maganar da Hajiya Turai ta ji Farida na yi ne yasa ta tsaya. Hajiya Turai tsayawa ta yi cikin furgici da gigin jin abinda Farida ta ke cewa, "Mommy Wallahi na so zuwa Office d'in nashi kafin ciwan ya riskeshi, amma sai drivern gidan ya yi min shiririta, ni yanzu abinda ke damuna shikenan yanzu babu yadda za ai yarinyar da yafarka ya gani shikenan da ita zai rik'a yadda ke nan? ". Daga can b'angaran na ji tace, "Haba Farida me yasa tun da kika tabbata ya sha tea d'in ka yadda kika rik'a nesa da shi?, bacin kinajin abinda malam mai buzu ya ce miki, ko ajiyan Farida sai da nakiraki nace miki karki yadda ki nesa da Habib, tahakanne zamu zasu abinda muke nema cikin sauki". Farida shiru ta yi sannan ta ce, "Mommy ya zanyi dan Allah? ". Daga can b'angaran aka ce, "Farida kina jina ko? "? "Eh Mommy inaji". "Yanzu Hajiya Turai ta dawo gidanne? ". Farida cikin tabbarwa inda batasan da dawowar Hajiya Turai ba, ta ce, "A'a Mommy ina tunanin yau zata dawo". "Ok, yasunan yarinyar da kika ce alokacinda ciwan ya same itace kusa da ita? ". Shiru Farida ta yi dan ita batatab'a ganin Hassana ba ma sai jiya da abin yafaru, hakan yasa, ta ce, "Mommy bansan sunan yarinyar ba, amma ina tunani a Company nin shi yarinyar ta ke aiki". "Shikenan ki yi k'ok'ari ki samomin sunan yarinyar". Nan Farida taima Mahaifiyarta sallama ta kashe kiran". Hajiya Turai ko mutuwar tsaye ta yi, da ta gama jin duk abinda Farida ke cewa ita da Mahaifiyar. Daya ke Farida a Hans free ta sa wayar shi yasa Hajiya Turai taji duk abinda suka ce.......... TOfA WAI meke faruwa ne, nifa har yanzu bangane ba?????. Karki damu ke dai kibini ahankali zaki gane😘😘😘😘😘 Dan Allah ayi hak'urin jina da akayi kwana biyu shiru, ina ba duk wani mai bibiyar littafin Oga Habib hak'uri, na jina shiru da aka yi kwana biyu, Allah Aimin uziri insha Allah haka bazai k'ara faruwa ba. Masoya wa inda suka nuna min kulawa ta hanyar ganin text messsage d'in su nagodee, da masu kiran waya duk ina godiya sosai👍🏻👍🏻👍🏻 COMMENT & SHERE PLEASE 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy babuy). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ *☘️ADDU'A DAGA BAKIN ANNABI S.A.W.☘️* _🩸Ya Allah Ina Neman Tsarinka Daga Sharrin Jina Da Ganina, Da Sharrin Harshe na, Da Sharrin Zucuya ta, Da Kuma Sharrin Sha'awa ta... Yana Nufin Tsiraicinsa.🩸_ Abu Dawud,Tirmizy Da Nasa'i Suka Rawaito Shi. SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA AKE POSTING. KI GARZAYA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 20&21 Hajiya Turai zufa ce ke keto mata ko ta'ina , dan sosai abinda ta ji Farida na fad'a ya tada mata hankali, ya rud'ata, Hajiya Turai maganar zuciya ta fara, tana cewa, "Yanzu abinda kunnena suka jimin hakane kuwa?, Kai ina bazai yuwuba ace Hajiya Murja zata iya had'a baki da 'yarta su juya brain d'in Habib? ". Hajiya Turai zuciyarta ce ta bata amsa, da cewa, "Tom idan kince k'arya ne, abinda da kunnanki su ka jimiki fa? ". Shiru Hajiya Turai ta yi, sai zuwa can ta ce, "Tabbas abinda kunnena suka ji min hakane, tom amma meyasa Hajiya Murja zata juya k'wak'walwar Habib?, me Habib ya yi mata?, Sannan me Farida ta ke nufi da taso ace lokacinda lallurar ta samu Habib tana kusa dashi?, tasan da da'ita zai rik'a yarda?, me suke nufi da haka?, Sannan wata yarinya ce suke maganar lokacinda Habib ya farka da ita yayi tozali ?". Hajiya Turai dafe kanta tayi kamar zata sa kuka tace, "Wayyo Allah wa zai amsa min wa'innan tambayoyin?, Yallah ga Habib nan kai kasan dalilin shigar wannan lallura jikinshi Ya Allah kakawo mai sauk'i". Hajiya Turai fasa shiga d'akin Farida ta yi ta juya tana mai goge hawayan dake ambaliya cikin fuskarta. Hajiya Turai Bilya ta kira awaya, dan duk ma aikatan gidan mutum biyu ne Hajiya Turai ta yadda da su wa inda har ta ke naiman shawara agunsu, wato Bilya da Baba Lami. Bilya na kwance tunanin halinda Habib ya ke Shikanshi kusan ya hana shi sakat. Bilya na awannan halinne kiran Hajiya Turai ya shigo wayar shi. Bilya cikin hanzari ya d'aga wayar, banji mai Hajiya Turai ta ce ba, sai dai naji Bilya ya ce, "Ok, Hajiya ganinan zuwa". Bilya tashi ya yi ya nufi part d'in Hajiya Turai. Bilya zaune ya iske Hajiya Turai tana kuka. Cikin damuwa Bilya ya samu gu ya zauna, sannan cikin sanyi murya mai cike da rauni ya kalli Hajiya Turai ya ce,"Hajiya tabbas na san dole kishiga damuwa, tom amma ita damuwar ce babu maganin abinda zatayi mana, ki yi hak'uri kima Oga Habib addu'a, dan ayanzu addu'arki ya ke buk'ata , nasan zata taimaka mai sosai wajan rage mai halinda ya ke ciki". Hajiya Turai da katawa ta yi daga kukan da ta keyi, ta d'ago tana kallan Bilya, Hajiya Turai cikin raunin murya mai kama da kuka ta ce, "Bilya ayanzu ba halinda Habib ya ke ciki ba nake ma kuka"HajiyaTurai shiru ta yi ta da kata nad'an wani lokaci, sannan ta ce, "Bilya d'akin Farida nayi sammakon shiga da niyyar in sanar da ita dawowata, amma sai kunnuwana suka ji min wasu zantuka da ta ke yi, tabbas Bilya da ace wanine ya fad'a min abinda kunnena yaji min yau Farida na fad'a Wallahi da bazan yarda ba".Hajiya Turai shiru ta yi sannan ta ce, "Bilya alokacinda lallurannan ta samu Habib wata yarinya ce kusa da shi? ". Bilya cikin mamaki ya kalli Hajiya Turai jin abinda ta ce, amma sai ya waske kawai, ya ce, "Hajiya Hassana ce yarinyar da ke aiki Sanat company ta ke kwana gidannan". "Me ya shigar da ita Office d'in Habib?. " " Eh tom gaskiya ban sani ba". Hajiya Turai kallan Bilya ta yi ta ce, "Kaje yanzu ka tahomin da yarinyar ina son ganinta". Bilya kallan Hajiya Turai ya yi zai yi magana ta d'aga mai hannu. Hakan yasa Bilya ya juya ya tafi yana tunanin lafiya Hajiya Turai ke son ganin Hassana, can wata zuciyar ta ce mai, "Tom ko dai maganar da tace taji, cemata akai ana zargin Hassana ne, ita taima Oga Habib wani abun".Haka dai Bilya ya idasa b'angaran masu aikin gidan yana tunani kala-kala, shi dai addu'ar shi d'aya in ma wani sharinne aka k'ullama Hassana Allah ya kub'utar da ita. Bilya Jimmai ya gani tana shara. Kallanta ya yi, ya ce, "Hassana fa? ". "Tana ciki Oga Bilya". "Ki ce mata Hajiyar naiman ta yanzu, tazo yanzu". Bilya na fad'in haka ya juya ya tafi". Jimmai kuma barin sharar ta yi ta shiga ta kira Hassana. Lokacin Hassana na kwance tana bacci, Jimmai ta bubbuga ta ta ce, "Hassana ki tashi Hajiyar Oga Habib na son ganinki yanzu". Hassana tashi ta yi tana kallan Jimmai ta ce, "Jimmai lafiya dai ko? ". "Tom nima dai bansani ba amma ki je kiji". Hassana tashi ta yi ta sa Hijab d'in Jimmai ta tafi kiran da Hajiya ke mata, zuciyarta na cike da fargaban kiran". Hassana sallama ta yi, tana jiran abata izinin shiga. Daga cikin falon Bilya ya ce, "Hassana ki shigo mana". Hassana shiga ta yi, ta zuk'unna can gefa ta gaida Hajiyar Habib. HajiyaTurai ba tare da ta amsa gaisuwar da Hassana tai mata ba, ta kalli Hassana ta ce, "Hassana tambayarki na ke son yi, kuma ina so kifad'amin gaskiya? ". Hassana kallan Hajiya Turai ta yi gabanta na fad'uwa ta ce, "Inaji Hajiya, kuma insha Allah zan fad'amiki gaskiya". Hajiya Turai, kallan Hassana ta yi na second's sanan ta ce, "Watanki nawa da fara aiki a Sanat yughurt? ". "Wata na biyu na ke Hajiya". Cewar Hassanan. "Ok, alokacinda lallurar nan ta samu Habib ance min kina Office d'in shi, hakane? ". Wata irin fad'uwar gabace ta samu Hassana dan sai maganar Billy ta dawo mata farko da ta ce mata, "Hassana ki yi gaggawar warware duk abinda ki kaima Oga Habib tun kafin Hajiyarsa ta dawo". Bilya ne ya kalli Hassana ganin ta fad'a kogon tunani, ya ce, "Hassana ke fa Hajiya ke saurare". Hassana kallan Hajiya Turai ta yi, sannan cikin sanyin murya ta ce, "Eh Hajiya inanan". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Me yashigar da ke Office d'in shi alokacin?". Hassana Bilya ta nuna ma Hajiya Turai ta ce, "Hajiya Oga Bilya ne yaban ruwan tea in kaime". shiru Hajiya Turai ta yi, dan tabbas idan bata mantaba taji Hajiya Murja ta ce ma, Mahaifiyarta, indai Farida ta tabbata ta ba Habib ruwan tea d'in yasha shikenan, Hajiya Turai azuciyarta ta ce, "Tom ko dai had'a kai su kai harda Bilyan ma?, nan dai Hajiya Turai da taga bata da mai amsa mata, maida kallanta ga Bilya ta yi, ta ce, "Bilya waya ce ka kaima Habib ruwan tea bacin kasan daga nan ake kai mai? ".Bilya cikin natsuwa ya ce, "Hajiya shi yace in kaime, nima bansan dalilinshi ba nahakan". Hajiya Turai kallan tuhuwa taima Bilya sannan ta ce, "Tom meyasa baka kaime da kanka ba kaba Hassana? ". Bilya cikin full Confidence, ya ce, dan yaga kamar Hajiya Turai yau zarkin shi ta ke yi, hakan yasa ya ce, "Hajiya tun kafin in Tashi bacci Farida ta matsamin da kira akan sai dai in kaita Sanat yughurt, amma nace mata sai nayi wanka, rok'ona ta yi akan dan Allah in kaita, alabashi idan na dawo sai in yi wankan, tom ni kuma bazan iya musa mata ba, hakan yasa sai nace mata ganinnan zuwa, tom shine fa bayan takatse kiran ni kuma na yi sauri nashiga wanka. Tom ina fitowa daga wanka Oga Habib ya kirani akan in siyo mai tea in kai mai yanzu. Tom nasan idan Oga Habib ya na son Abu yadda yake, hakan yasa ina fitowa na manta da Farida na jirana na tafi, sai da nashiga Sanat company sannan natuna da tun d'azu Farida ke jirana. Tom nasan Oga Habib idan nashiga dakyar idan zai barni in fito yanzu zai iya sani wani abun, hakan yasa da naga Hassana na bata tea d'in nace ta kaime, ni kuma na dawo da niyyar d'aukar Farida, tom ahanyama muka had'u ta gaji da jirana ta taho a napep,na tsaida napep d'in na d'auketa. Shine fa muna shiga cikin Company muka ji wata irin razanannar k'ara Oga Habib ya yi". Bilya kallan Hajiya Turai ya yi ya ce, "wannan shine abinda nasani Hajiya, amma ga Hassana nan sai ta idasa miki bayani". Shiru Hajiya Turai ta yi dan tabbas a kwai alamun gaskiya a magan-ganun Bilya, hakan yasa Hajiya Turai ta kalli Hassana ta ce, "Hassana bayan shigarki Office d'in Habib me yafaru, alokacin? ". Hassana cikin sanyin murya ta ce, " Hajiya Duk da Oga Habib nada idan mutum ya yi nocking ya dad'e bai amsa mai ba, amma gaskiya a Jiya da zan shiga office d'in shi, naji shirun ya yi yawa, dan har saida nafara tunanin ko dai baya office d'in ne, sannan zuwa can yace in shigo, koda nashiga jug d'in hannuna na mik'a mai na ce inji Oga Bilya ya ce zai dawo yanzu". Shiru Hassana ta yi ta d'an numfasa, sannan ta ci gaba da cewa, " gaskiya tunda nashiga Office d'in Oga Habib zan ita cewa babu lafiya atattare da yadda naga yana yin shi, dan koda na bashi sak'on Oga Bilya, bai amsamin ba bai kuma kallan ba, sai dai ya tashi tsaye ayanayin yadda naga jikinshi kamar rawa yake, hakan yasa sai naji tsoro naja baya, sai ji nai ya mik'on hannun shi ya ce, dan Allah in rik'e mai. Tom ni dama gaskiya ko ayanayin yadda naji maganarsa nasan ba lafiyar shi k'alau ba, hakan ya sa naruga zan bud'e k'ofa in fita, amma kafin in fita har yarik'omin hannu, dan su Oga Bilya ne ma suka k'watan daga hannun shi". Shiru Hassana ta yi sannan ta ce, "wannan shine abinda ya faru, Hajiya da nashiga office d'in Oga Habib kai mai tea d'in ". Shiru Hajiya Turai ta yi tana kallan Hassana, dan akwai alamun gaskiya a maganar Hassana d'in, dan yanzu ta san abinda kunnan ta yaji mata hakane, Farida ce ta ba Habib wani tea d'in kenan, wato idan ta fahimta farida taso zuwa office d'in Habib kafin abinda ya sa mai ya sa mai. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana je ki abinki". Bayan Hassana ta tafi ne, Hajiya Turai ta kalli Bilya ta ce, Bilya kaje Zaria yau d'in nan ka tahomin da Baba lami, dan ina buk'atarta sosai, amma dan Allah kafin munje akaima Habib abin break fast, nasan tunjiya baici komai ba, inda bacikin hankalinshi ya ke ba.Bilya tashi ya yi Hajiya Turai, tafi bayansu suka tafi ganin halinda Habib ya kwana, tare da kai mai abin break fast. Bilya tsayawa ya yi daga k'ofar d'akin ya ce, "Hajiya ko za ki yi gaba? ". Hajiya Turai gaba ta yi batare da ta tankama Bilya ba.Hajiya Turai zaune ta iske Habib, sai dai kafin ta k'arasa inda ya ke Habib ya yo kan Hajiya Turai". Wani irin rik'o Habib ya yi ma Hajiya Turai, yana wujijjigata. Hajiya Turai tun tana daurewa tana cewa, "Habib ni ce fa, Habib mahaifiyarka ce fa ni, Habib kamanta ni ne ?, sakanni Habib da zafi! ". Haka Hajiya Turai ta idasa maganar cikin tashin hankali. Daga k'arshe da taga Habib tabbas bacikin hankalinshi ya ke ba, hakan yasa ta fasa k'ara ta ce, "Wayyo Bilya kana ina zo ka tai makamin! ". Bilya da saurinsa ya shiga, kan Habib ya yo, Habib ko na ganin Bilya ya saki Hajiya Turai ya yi kan Bilya, sai dai Bilya na ganin haka ya fita da gudu. Hajiya Turai ko ta k'ofar baya ta fita itama. Hajiya Turai falon bedroom d'in da Habib ya ke ta zauna tana, kuka. Bilya zagayawa ya yi ta baya yashiga falon Habib d'in, zaune Bilya ya iske Hajiya Turai tana kuka ". Bilya k'arasawa inda Hajiya Turai ta ke ya yi. Bilya cikin lallashi ya ce, "ki yi hak'uri Hajiya shi kuka da kika gani babu wani abunda zai miki sai dai ya samiki wani ciwan, yanzu abinda ya kamata muyi musan abinda ke damun Oga Habib". Hajiya Turai d'aga kai tayi tana kallan Bilya ta ce, "Bilya na san meke damun Habib, shi yasa nake son ganin Baba lami da sauri, ka tafi Zaria yanzu dan Allah Bilya ka tahomin da Baba Lami". "Shikenan Hajiya babu damuwa insha Allah yau d'innan zaki ga Baba Lami. Bilya na fad'in haka ya yi ma Hajiya Turai sallama ya kama hanyar Zaria. Hajiya Turai ko na nan zaune tana tunanin, magan-ganun Farida na d'azu, ta ce, "wato idan nagane maganar Farida tana nufin wadda Habib ya tashi ya farka a halinda ya ke yagani, zai iya yadda da ita kenan.kai wai tom meye niyyar Farida ne akan Habib?, ya Allah ka kawo min Baba Lami yau". Hajiya Turai fitowa daga falon Habib ta yi, tana fitowa ta had'u da Farida ita kuma da shirinta na barin gidan". Farida cikin mamaki ta kalli Hajiya Turai ta ce, "Kai Mommy ashe kin dawo?, yaushe kika dawo? ". Hajiya Turai ji tai kamar tai banza da Farida, sai da bata son ta nuna ma Farida komai, akwai lokaci acewarta. Hakan yasa Hajiya Turai ta ce, "Jiya da daddare lokacin kinyi bacci, Ina zaki ne haka? ". Hajiya Turai ta tambayi Farida."Sak'o Mommyna ta aikan in amso mata, yanzu zan dawo". "Ok". Hajiya Turai ta ce mata sannan ta juya ta tafi. Hajiya Turai Bilya ta kira awaya, Bilya na d'agawa tace, "Hello Bilya kana jina ko? ". "Eh Hajiya Ina ji". "Yauwa, Bilya idan baka riga katafi ba, ka je Sanat company yanzu dan Allah, ga Farida nan zata je yanzu, kayi k'okari ina son sanin abinda ya kaita". "Shikenan babu damuwa, bari inje kafin ta isa". Bilya na fad'in haka, ya juya yakama hanyar Sanat company". Hajiya Turai nagama wayar sai ga wata binta da ke mata wanki, Hajiya Turai kiranta ta yi, ta ce, "Binta kiramin yarinyar da ke aiki a Sanat yughurt". Binta da saurinta ta juya ta tafi dan ida sak'on Hajiya Turai". Hassana na zaune ita kad'ai dan soran worker's d'in Kowa ya kama gabanshi dan yin aikin da ya ke amazaunin nashi, binta tazo ta ce, "Ke Hajiya na kiranki, ta ce ki sameta a falonta". Gaban Hassana fad'uwa ya yi jin wai Hajiya na kiranta. Azuciyarta ta ce, "Tom bayanzu ta kirani ba ba dad'ewa, Allah dai kasa lafiya". Hassana tashi ta yi tanufi site d'in Hajiya Turai. Hassana zaune ta iske Hajiya Turai a falonta. Hassana cikin sanyin muryarta ta yi sallama, d'annesa da Hajiya Turai Hassana ta zauna, bayan Hassana ta zauna ne, ta kalli Hajiya Turai ta ce, "Hajiya gani ance kina kirana". Hajiya Turai abin break fast d'in da suka kaima Habib suka dawo dashi ta mik'ama Hassana ta ce, "Kin san site d'in Habib? ". "Eh na sani". "Yauwa, Hassana dan Allah me ba Habib abinci ne baya nan, na aikai Zaria, shine dan Allah nake son ki kai mai". Hassana cikin girmamawa ta ce"Tom". D'aukar abin break fast d'in Hassana tayi ta tafi.Hajiya Turai tashi ta yi ta yi bedroom d'in ta fita tashiga Falon Habib ta na jiran zuwan Hassana taga ikon Allah, ta ga maganar da Farida ta fad'a gaskiya ne kok'aya". Hassana ko, tambayr kanta ita kad'ai ta yi, ta ce, "Tom oga Habib ya warkene? ".Nan dai bata da mai bata amsa, haka Hassana ta nufi site d'in Habib da abincin gabanta na fad'uwa. kasan cewar Hassana ba taji labarin Habib na dukaba, hakan yasa ba wata fargabar hakan, ta bud'e k'ofar ta shiga kai tsaye......... COMMENT & SHERE PLEASE 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA AKE POSTING. KI GARZAYA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 22&23. Habib na kwance ya juya baya, motsin bud'e k'ofar da yaji yasa ya juyo da sauri. Habib batare da yasan ko waye ba ya tashi da sauri ya yo kan Hassana. Hassana ko ganin yadda Habib yayo kanta da sauri sai abin ya bata tsoro, duk da bata san yana duka ba, Hassana gefe d'aya ta takure da break fast d'in dake hannunta. Hajiya Turai da ke lekyan Hassana ta window, dafe kai tayi dan a tunaninta Habib zai rufe Hassana da duka ne, amma sai taga akasin hakan. Habib na zuwa inda Hassana ta ke da sauri ya kamo hannunta yana janta cikin d'akin, Hassana da mamaki tabi Habib da kallo. Habib ko kan lover chair d'in shi ya zaunar da Hassana shima ya zauna kusa da ita, ba baki sai dai kallanta kawai da yake yi. Hassana ko koda ganin yadda Habib yake kallanta da yanayin yadda yake acting ta kuma tabbatar da Habib bacikin hankalinshi ya ke ba. Hassana so ta ke ta kwace hannunta daga na Habib amma ta kasa, gashi duk cikin tsoro ta ke. Cikin jarumta da rawar murya Hassana ta ce, "Oga Habib ga abin break fast d'in ka, Hajiya ta ce in kawo ma". Hassana ta nuna ma Habib abin break fast d'in. ruwan Lipton ne sai gwangwanin madara da na Nescafe da milo, Sai wainar k'wai. Habib kalla kawai ya yi batare da yace ma Hassana ko mai ba. Hassana ko ganin Habib bai ce mata ko mai ba, sai ta kuma cewa, muryarta na rawa, "Oga Habib ka sakanmin hannuna in had'ama tea d'in ". Habib sakin hannun Hassana ya yi. Hassana kuma da sauri tatashi ta had'ama Habib tea d'in, bayan tagama had'a mai, kallan shi ta yi cikin rawar murya ta ce, "Oga Habib ga tea d'in? ". Habib hannu ya mik'ama Hassana ta mik'amai tea d'in. Hassana ko ganin ta yi abinda ya kawota tashi ta yi daniyyarta ta tafi. Habib ya yi saurin rik'o hannunta. Hassana cikin tsoro ta kalli Habib dan ita yanzu tsoro ma ya ke bata, dan daga ganin shi kasan bacikin hankalinshi ya ke ba, Hassana kamar zata yi kuka, ta ce, "Oga Habib Hajiya ke jirana dan Allah ka sakanmin hannu".Habib kafad'a ya mak'alema Hassana alamun nak'i d'in. Babu yadda Hassana batayi ba Habib ya sakar mata hannu amma yak'i, Hassana kamar zata yi kuka ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib dan Allah katai maka kasanmin hannuna dan Allah". Hassana ta fad'i maganar kamar zatayi kuka. Habib sake mak'ema Hassana kafad'a ya yi. Hajiya Turai ko tananan tsaye jikin window tana kallan duk abinda ke faruwa tsakanin Habib da Hassana. Hajiya Turai ganin Hassana ta fara kuka akan Habib ya saketa shi kuma yak'i yasa ta fita da sauri ta zagaya ta shiga bedroom d'in Habib d'in . Habib ko naganin Hajiya Turai ya saki Hassana ya yi kan Hajiya Turai. Habib na isa yarik'e Hajiya Turai yana jijjigata. Hajiya Turai bata san sanda ta fasa kuka ba, bawai jijjigar da Habib ya ke mata bace tasata kuka ba, a'a, bak'in cikin yadda aka rabata da d'anta guda ne yake sata kuka, ace wai ita ce yau Habib bai son gani in har yaganta sai dai yayi ta jijjigata, hakan yasa Hajiya Turai tai ta kuka, Habib kuma na ci gaba da jijjigata". Hassana ko ganin yadda Hajiya Turai ke kuka, yasa cikin tsoro ta nufi gurin da ta ke dan itama tsoro ta ke kar Habib ya yi mata yadda ya ke ma Hajiya Turai. Hassana na zuwa cikin tsoro da fargabar kar Habib itama ya yi mata abinda ya ke ma Mahaifiyar shi. Hassana tana kuka ta rik'e hanun Habib tana cewa,cikin kuka" Oga Habib dan Allah ka saketa, Mahaifiyarka ce fa, ka barta ". Hassana anshe Hajiya Turai ta yi daga hannun Habib. Hassana kama hannun Hajiya Turai ta yi tazaunar ta ita bakin gadon Habib tana cewa, "Hajiya dan Allah kiyi hak'uri kibar kuka, kinsan Oga Habib bazai miki hakaba cikin hankalin shi ba, ki yi hak'uri dan Allah kibar kukan Hajiya ". Hajiya Turai da katawa ta yi da kukan ta d'aga kai tana kallan Hassana, Hajiya Turai batare Da ta ce ma Hassana ko mai ba tashi ta fita daga d'akin". Hassana da kallo tabi Hajiya Turai, sannan itama ta tashi tabi bayan Hajiya Turai, sai dai kafin ta fita Habib ya yi saurin dawo da ita ta hanyar rik'o hannunta. Hassana kamar zata yi kuka ta kalli Habib, ta ce, "Oga Habib kasa kan min hannu dan Allah ina so zan tafi ne". Habib mak'ema Hassana kafad'a ya yi. Duk yadda Hassana taso Habib ya saki hannunta k'i ya yi, k'arshe ta fashe da kuka.Haka Hassana ta yi kukanta ta gaji daga k'arshe ta yi shiru". Shiko Habib koda yaga Hassana na kuka kallanta kawai ya ke, kuma har yanzu yana rik'e da hannunta. Hajiya Turai bayan ta koma falonta kuka ta yi sosai sai da ta gaji dan kanta sannan ta yi shiru. Hajiya Turai tashi ta yi ta koma falon Habib, ta window ta lek'a ta hango Hassana zaune da Habib kusa da ita yana rik'e da hannun Hassana kamar wata wadda tai mai laifi. Hajiya Turai kiran Hassana, ta yi,ta ce, Hassana kizo yanzu". Hassana kallan Hajiya Turai ta yi, dake magana jikin window ta ce, "Hajiya tun d'azu nake son tashi Oga Habib ya hanani". Hassana ta fad'i maganar kamar zata yi kuka. Hajiya Turai cikin sanyin murya mai cike da rauni ta ce, "Hassana ki yi hak'uri kin ji dan Allah nasan yanzu Bilya zai shigo". Hajiya Turai na fad'in haka tabar gun tana share hawayanta, dan sosai halinda Habib ya ke ciki ya ke damunta, uwa-uba kuma ganin yadda ya ke mata in tashiga wajan shi, wannan abin shike k'ara d'agama Hajiya Turai hankali". Bilya bashi ya dawo daga Zaria ba sai 3:13Pm. Haka Bilya da Baba Lami suka jera suka shiga falon Hajiya Turai. Zaune suka isketa kan caution ta yi ta gumi. Bilya cikin tausayama halinda Hajiya Turai ta ke ciki ya yi sallama falon Hajiya Turai. Hajiya Turai d'aga kai ta yi tana kallan Bilya, sannan cikin sanyin murya ta amsa mai sallamar. Bilya da Baba lami shigowa sukai cikin falon suka zauna da nesa tsakaninsu da Hajiya Turai". Bilya Kallan Hajiya Turai ya yi ya ce, "Hajiya ga Baba lamin nan, bari inje inyi sallah ahanya ta saman". Bilya na fad'in haka yatshi zai fita. Hajiya Turai Kallan Bilya ta yi, cikin sanyin murya ta ce, "Bilya tun safe yarinyar nan na gurin Habib ya hanata fitowa, dan Allah ko za kai ma su musa magana ku shiga ku fito da ita? ". Bilya cikin damuwa da fad'uwar gaba ya kalli Hajiya Turai ya ce, "Ok, bar in yi sauri muje". Bilya na fad'in haka ya juya ya fita daga falon. Bilya cikin tashin hankali ya nufi k'ofar da zata sada ka da falon Habib, ta window Bilya ya lek'a, dan a tunanin shima yanzu Habib ya yi ma Hassana illa, dan har yanzu Bai manta wujijjigawar da Habib ya yi ma Hajiya Turai ba, tom ita da ta ke mahaifiyarshima bare Kuma wata Hassana da tun lokacinda abin yasa meta da kyar aka kwaceta awajanshi. Bilya na maganganun zuci ya isa k'ofar, ta window Bilya ya lek'a da yake window abud'e ya ke". Zaune Bilya ya hangi Hassana da Habib da ke rik'e da hanbuta kata kam kamar irin yana tsoran za a kwace ta . Ajiyar zuciya Bilya ya yi ganin Hassana lafiya klau. Hassana ko zaune ta ke sai zazzare ido ta ke kamar wadda tai k'arya asirinta yatonu. Bilya komawa ya yi ya je bakin get yakira Musa. Musa yana d'aya daga cikin masu gadin gidan". Bilya na zuwa kusan mamayar Habib su kayi, amma dakyar suka iya k'wace Hassana daga hannun Habib. Hassana ko naganin Allah ya taimaketa ta kubuta daga hanun Habib da saurinta har tana tuntub'e wajan rugawa site d'in su. Bilya ko suna kwace Hassana suka yi sauri suka rufe k'ofar suka bar Habib shi kad'ai". Hajiya Turai ko bayan fitar Bilya Kallan Baba Lami ta yi, ta ce, "Baba barka da zuwa, ya hanya, ki yi hak'uri Baba zaki ce ban ne mekiba lokacinda Habib ya koreki sai yau da buk'atata ta tashi, Baba dan Allah taimako zaki min kamar yadda ki kaimin kafin mutuwar Mahaifin Habib? ". Baba Lami Kallan Hajiya Turai ta yi, dan duk bata gane takan zancan ba ta ce, "Hajiya ina ji, wana irin tai mako zan baki? ". Shiru Hajiya Turai ta yi, tana tunanin ta inda zata fara yima Baba Lami bayani, sannan zuwa can ta ce, "Baba Habib ne baida lafiya, kuma ciwannashi kamar hauka, dan Baba Lami yanzu ko ni ban isa inje d'akin Habib ba, sai yarinya d'aya agidannan dan yauma ita akaba abin break fast d'in shi ta kai me, amma cikin ikon Allah ita Bai mata komai". Baba Lami Kallan Hajiya Turai ta yi ta ce, "Hajiya to aiko idan haka ne akwai alamar tambaya ajikin yarinyar nan, wata yarinyar ce? ". Hajiya Turai Kallan Baba Lami ta yi ta ce, "Yarinyar da ya koreki keda Bilya akanta". Shiru Baba Lami ta yi, Sannan ta ce, "Hajiya wai meye musabbabin ciwanne?, koko sai dai kuka wayi gari kuka ganshi ahaka?". "Eh Tom Baba Lami, maganar ce nada mamaki da kuma d'aure kai, wato Baba Lami naje d'akin Farida sai naji tana waya da Hajiya Murja tana cewa ita yanzu abinda ke damunta yarinyar da ciwan ya riski Habib da tana wajan yanzu da ita zai rik'a yarda ba ita ba, ita abinda ke damunta kenan, tom da yake a speaker wayar ta ke, sai naji ita Hajiya Murja na cewa, Farida kuma kin tabbata kin bashi tea d'in ya sha, Farida ta bata amsa da Eh, tom shine fa ta ce wai ta binciko mata sunan yarinyar da ciwan yamu Habib agabanta". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ci gaba da cewa, "tom Baba Lami kinjin abinda ke faruwa, dan Allah ki taimakamin kamar yadda ki kaimin lokacinda Mahaifin Habib na da rai! "? "Karki damu Hajiya insha Allah, mu bari sai gobe inda yanzu yamma ta yi". "Tom Allah ya kaimu goban Lafiya". Cewar Hajiya Turai ". B'angaran Hassana ko yanzu haka kwance ta ke tana mamakin da Oga Habib Bai yadda da kowa ya shiga inda ya ke sai ita, abinda ya k'ara d'aurema Hassana kai har Mahaifiyar shi ma taga bata isaba tashiga inda ya ke ba, nan dai Hassana ta na tunane-tunananta ta bacci ya kwasheta inda dama ba sallah zata yi ba". Bilya bashi ya k'ara shiga part d'in Hajiya Turai ba sai da ya yi Sallar magriba sannan. Zaune Bilya ya isketa kan sallaya ta yi ta gumi. Hajiya Turai na ganin Bilya ta ce, yauwa Bilya dama maganarka na keyi azuci yanzu haka,kamar kasan san ganinka nake yi. D'azu da nace ma kabimin bayan Farida, ya akayi? ". "Hajiya kamar yadda ki kayi tunani Sanat yughurt taje, tana zuwa suka had'u da supervisor gun, bayan sun gaisane da yake sunsan juna tom shine Farida ke tambayar supervisor sunan wadda Habib ya rik'ema hannu lokacin da lallurar ta sameta, dan acewarta ga supervisor ke kika aikota wai kina zargin Hassana, tom nan dai ta fad'a mata sunan Hassana". Shiru Hajiya Turai ta yi Sannan ta ce, "Bilya dan Allah ka mik'ama Habib abinci kota window ne, dan ni Wallahi tsabar rud'ewa na manta kona rana ban bashi ba". Bilya amsar abinci ya yi ya je ya jira ma Habib shi ta window kamar yadda Hajiya Turai ta ce. Sai dai abinda basu saniba Habib ko Kallan abinci bai yiba". Washe gari Hajiya Turai da Baba Lami da wuri suka yi sammakon zuwa zaria, inda Bilya ne zai kaisu. Bayan sun fitone Hajiya Turai ta lek'a ta window tana kallan Habib zaune yake inda yasaba zama. Hajiya Turai ganin abinci jiya ta yi yadda aka kaishi yana nan ahaka. Hajiya Turai Bilya ta kira ta nunamawa ta ce, "Bilya kaga abincin jiya ko Habib bai ciba? ". "Eh Wallahi Hajiya nima haka nagani". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta kalli Bilya ta ce, "Bilya ku jirani amota kaida Baba Lami ina zuwa". Hajiya Turai site d'in worker's d'in gidanta ta je, wata daga cikin masu yima Hajiya Turai aiki, Hajiya Turai ta aika takiramata Hassana. Hassana ko lokacin tana kwance tana baccin safe,Binta ta shigo ta tada Hassanan, ta ce, "Hassana ki tashi Hajiyar Oga Habib na waje tana jiranki! ". Binta na fad'in haka ta juya ta tafi badare da ta tsaya taji amsar Hassana ba". Hassana ko tashi ta yi ta tafita tana mai addu'ar Allah yasa Hajiya Turai ba abinci zata kuma cewa ta kaima Habib ba. Hassana na wannan tunanin ta isa inda Hajiya Turai ke tsaye tana jiran fitowar Hassana". Hassana har k'asa ta juk'unna ta gaida Hajiya Turai tare da tambayarta ya mai jiki. Hajiya Turai cikin sanyin murya ta ce, "Lafiya klau, Hassana dan Allah taimako zaki min na k'arshe? ". Hassana cikin girmamawa ta ce, "InajI Hajiya". "Hassana dan Allah abinci zaki taimakamin ki kaima Habib, tun abincin jiya da kika kai mai haryanzu baici komai ba, jiya da nasa aka kaime nadare Yanzu haka abincin nacan baiciba, dan Allah Hassana ga abin break fast d'in shi can, dan Allah kije ki kai mai". Shiru Hassana ta yi, sannan ta ce, "Tom Hajiya". Hassana tashi ta yi tanufi site d'in Hajiya Turai d'akko break fast d'in Habib. Hajiya Turai amota ta samu su Bilya suka kama hanyar zaria". Hassana na tafiya zuwa b'angaran Habib tana tambayar kanta, "Wai meyasa ni Oga Habib baya dukana? , dan ayadda na lura kowama duka ya ke, kuma meye dalilin shina hanani fita da yake yi?". Hassana shiru ta yi dan bata san mai amsa mata tambayoyinta ba. Hassana ta window ta fara lek'a Habib. Kwance ta hango shi kan caution d'in falon, ya yi kwanciyar rubda ciki. Hassana kallan yadda Habib ya ke ta yi sai taga kamar yaji sauki, dan ayarda ta ganshi babu yadda za ai kace wai wani abu nadamun shi. Bud'e k'ofar d'akin Hassana ta yi tashiga". Habib na jin alamun shigowar mutum ya tashi da sauri yayo kan Hassana. Dan sai da Hassana ta ji tsoro ganin yadda ya yo kanta, amma kuma yana zuwa inda ta ke sai ya kamo hannunta ya ida shigoda ita falon". Hassana bayan ta zauna kallan Habib ta yi ta ce, "Oga Habib ga abin break fast d'in ka ". Hassana ta fad'i maganar tana mik'ama Habib kunun gyad'a". Habib amsar kukun ya yi, kafin kace me ya shanye shi tass. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib in k'arama? ". Habib Kallan Hassana kawai ya ke, amma ba bakin magana. Hassana ganin ba magana zai mata ba, yasa ta kuma k'ara mai kunun ta mik'a mai. Habib amsar Cup d'in ya yi ya kuma d'agawa ya shanye tass, ya mik'a mata Hassana cup d'in. Hassana amsa ta yi tana mai tsananin jin tausan Habib. Mutumin da komai nashi anatse ya ke yi wai ace yau shike irin wannan shan kunun. Hassana k'ara ma Habib kunun ta yi, nanma ya d'aga kai ya shanye shi tass lokaci guda ya aje cup d'in. Bayan Habib ya gama shan kunun ne, Hassana ta tashi da niyyarta ta tafi. Amma Habib ya rik'eta ya hanata tafiya kamar jiya. Hassana cikin sanyi murya kamar ance mata Habib d'in jinta ya ke ta ce. "Oga Habib dan Allah kabarni in tafi zanyi wanki ne, innagama zan dawo ". Habib mak'ema Hassana kafad'a ya yi. Bubu irin wayan da dubarar da Hassana batai ma Habib ba dan yabarta ta tafi amma yak'i yana mai irik'e da hannunta. Dole Hassana ta yi hak'uri ta zauna tana mai addu'ar Allah yasa Hajiya Turai ta dawo da wuri". B'angaran su Hajiya Turai ko, sun isa zaria. Hajiya Turai ce ta kalli Baba Lami ta ce, "Baba Lami zadai ki gane gidan ko? ". Murmushi Baba Lami ta yi sannan ta ce, "zan gane mana Hajiya". Haka Baba Lami taita nuna ma Bilya hanya har ya kaisu gidan malam Ishu........... Idan kin karanta ki daure ki yi Comment sister 🤝 SHERE & Comment PLEASE 👏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 Facebook group: https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ 🍁 Ibnul-Jawzī (rahimahulLah) yana cewa: *“Ka kiyayi roqon Allah game da wani lamari ba tare da ka rokeshi alherin dake cikin abin ba. Haƙiƙa, wani abinda zaku roqa game da rayuwar duniya na iya zama sanadin halakarku."* SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA AKE POSTING. KI GARZAYA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 24&25. Haka Baba Lami tai ta nuna ma Bilya hanya har ya kaisu gidan malam Ishu. Bilya na yin parking ya kalli Hajiya Turai ya ce, "Tom Hajiya ina jiranku". Hajiya Turai kallan Baba Lami ta yi, ta ce, "Baba Lami muje". Baba Lami da Hajiya Turai sallama suka yi suka shiga gidan malam Ishu. Lokacinda da suka shiga lokacin malam Ishu baya gida. Malam Ishu fitattan malami ne mai almajirai, duk wata lallura da ke damunka in dai kaje gun shi insha Allah zaka sami sauk'i da yardar Allah. Inda malam Ishu ke sauke bak'in shi aka kai su Hajiya Turai. Su Hajiya Turai na nan zaune Malam Ishu ya dawo". Cikin girmama juna Hajiya Turai suka gaisa da Malam Ishu, bayan sun gama gaisawa ne. Hajiya Turai ta kalli Malam Ishu ta ce, "Malam dan Allah nazo ne katai makamin akan yarona d'aya shikenan min". Malam Ishu kallan Hajiya Turai ya yi ya ce, "Hajiya meke damun shi? ". Hajiya Turai cikin natsuwa ta fara yima malam Ishu bayani". "Malam ciwanne kamar hauka-hauka, inda yanzu haka bacikin hayyacin shi ya ke komai ba". Malam Ishu da katar da Hajiya Turai ya yi tahanyar ce mata, "Hajiya ko ke baya ganewa? ". Hajiya Turai cikin sanyin murya ta ce, "Malam yanzu haka ko shiga d'akin shi nayi sai dai akwaceni hannun shi, bawai duka ya ke ba, amma idan yarik'e mutum yana shan wuya gun shi sosai, dan wujijjiga mutum ya ke, sosai". Shiru Malam Ishu ya yi sannan ya ce, "Babu damuwa insha Allahu zai warke, da akwai rubutun da zamu rik'a mai duk sati insha Allahu kodama iskace ta shafe zata kauce, idan ma sihirine zai karye, ke kodama ace da aljani aka had'ashi ya mai da shi haka insha Allah ayar Allah zata karya duk wani abinda ke jikinshi". Malam Ishu kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Hajiya ina zuwa". Malam Ishu fita yayi daga d'akin, ya kai kamar minti sha biyar da fita sai gashi ya dawo da gallon k'anana guda biyu a hannun shi. Malam Ishu mik'ama Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Hajiya ga wannan arik'a bashi wannan na farar jarkar sha biyun rana d'aya da kuma sha biyun dare, wannan kuma safe , rana, dare, insha Allah kome ke damunsa Allah zai mai maganin shi, duk sati zaku rik'a zuwa kuna amsar mai, yanzu idan ya shanye wannan sai muga yadda jikin nashi zai yi, sannan insha Allah za'ai mai saukar alk'ur'ani mai girma". Godiya sosai Hajiya Turai tai ma Malam Ishu, sannan ta bashi kud'i masu yawa sosai, sannan sukai mai sallama suka tafi". Su Hajiya Turai suna a mota suna tafiya, Hajiya Turai ta kalli Baba Lami, ta ce, "Baba Lami nikam ina tunanin yadda Habib zai sha maganin nan, Kinga dai yadda akeyi da shi, sannan wa zai rik'a tashi yana ba Habib magani sha biyun dare?, ni kuma Baba Lami kinga yadda ya ke min, Wallahi duk hankalinama ya tashi narasa yadda zanyi gaba d'aya ". Hajiya Turai ta idasa maganar tana share hawayan da ke zibo mata". Shiru Baba Lami tayi, dan itama tun d'azu tunanin da take yi kenan. Ahaka dai suka isa gida batare da Baba Lami ta ce komai ba". Bayan Bilya ya yi parking sun fiffita a motar ne, Hajiya Turai ta kalli Bilya ta ce, "Na bani Bilya namanta tun d'azu na tura Hassana kema Habib abin break fast, Wallahi ina zuci-zucin ince ma mubari ya gama ku fitar da Hassana sannan mu tafi, amma Wallahi na manta sham, da nazo na shiga mota kawai muka tafi, dan Allah muje mugani ko yabarta ta fita". Wajan window Habib Hajiya Turai ta tsaya ta lek'a, zaune ta iske Hassana kamar jiya, Habib kuma na rik'e da hannunta. Hajiya Turai cikin damuwa ta kalli Bilya ta ce, "Bilya ka gani ko, ashe har yanzu yarinyar nan na nan yak'i barinta ta fita! ". "Tom Hajiya ni kaina Wallahi abun shiru kawai nake yi, amma ita kanta Hassana yanzu ta fara ban tausai, dan ita ke jinyar Oga Habib kusan". Shiru Hajiya Turai ta yi, Sannan ta ce, "Bilya kira Musa dan Allah ku fito da ita, nasan k'ila ko abinci basu ciba su duka, inda babu wanda zai yi hausar kai musu". Bilya kiran Musa ya yi shuka shiga d'akin Habib don fito da Hassana. Habib ko na ganin su ya tashi da saurinsa ya yo kansu. Bilya da Musa rik'e Habib suke ita kuma Hassana ta tashi ta fita da saurinta, sannan suma suka saki Habib d'in suka gudu". Hassana sauran kad'an tabige Hajiya Turai, dan bata san da ita ba, saboda fitowar da tayi da gudu. Hajiya Turai kamo hannun Hassana ta yi, ta ce, "Sannu ko Hassana Allah ya yi miki albarka". Da Ameen Hassana ta amsa. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Bakici abincin rana ba ko? ". kai Hassana ta d'agama Hajiya Turai. Hajiya Turai kallanta ta yi, ta ce, "Hassana ya sha kunun da kika kaime? ". "Eh Hajiya yasha sosai dan duka ya shanye shima". Hajiya Turai hannun Hassana ta kama tace, "Sannu da k'okari, muje falona kici abinci kema". Hajiya Turai tana rik'e da hannun Hassana har suka isa falon ta. Hajiya Turai d'aya daga cikin masu aikinta ta sa ta had'ama Hassana abinci, sannan tasa suka kai mata kan derning space . Hassana ko daya ke yunwa ta ke ji dan ko karyawa bata yi ba Hajiya Turai tasa ta kaima Habib abin k'arinshi. Sosai Hassana ta ci abincinta". Hajiya Turai ko tunaninta taya zata kuma rok'on Hassana ta kaima Habib shima.Hajiya Turai so take ta rok'i Hassana amma sai ta kasa dan tana tsoran kar Hassana tai mata kallan mai son kanta da yawa. Haka Hassana ta gama cin abincinta ta tashi ta yima Hajiya Turai godiya ta tafi. Hajiya Turai nason yima Hassana magana ta rok'eta ta kaima Habib abinci, amma ta kasa, haka nan ta yi hak'uri badan taso ba tana gani Hassana ta tafi". Hajiya Turai bayan ta yi Sallah ne, ta aika aka kira mata Baba Lami. Bayan Baba Lami ta zo ne, Hajiya Turai kallanta ta yi tace, "Baba Lami nace taya kike gani Habib zai sha maganin nan? ". Shiru Baba Lami ta yi, sannan ta ce, "Hajiya ni gani nake kamar yadda kike sa Bilya da Musa su kwace Hassana daga hannun Oga Habib, haka zaki sasu su d'ura mai maganin nan". "Tom Baba Lami idan hakan ta yuwu na daran fa? ". Shiru Baba Lami ta yi, dan itama shi tafi tunani, sannan zuwa can ta ce, "Hajiya ni gani nake kima Bilya da Musa magana su rik'a tsayawa wajan Habib har lokacin shan maganin, alabashi idan sun bashi magani sai su koma inda suke kwanciya su kwanta, alabashi sai ki biyasu, bare kuma nasan daga Bilya har Musa sunada kirkin yi miki haka". Shiru Hajiya Turai ta yi sannan ta ce, "Baba Lami kina ganin ba damuwa zasu yi ko? ". "Sosai ma kuwa, Hajiya ai Bilya da Musa dukansu 'yan gidan Oga Habib ne, ina da tabbaci zasu yi". Hajiya Turai kallan Baba Lami ta yi, ta ce, "Baba kiramin Bilya sai muyi magana da shi, inji ta bakinshi". Baba Lami fita tayi sai gata da Bilya sun dawa. Baba Lami kallan Hajiya Turai ta yi ta ce, "Hajiya ga Bilyan nan naki rashi"., Hajiya Turai cikin sanyin murya ta ce, "Bilya dan Allah tai mako zakai min?, magani akaba Habib ya rik'asha sha biyun rana da na dare , shine dan Allah nake nai man alfarmarka kai da Musa kurik'a bashi, zan biyaku dan Allah Bilya ku yi min wannan tai makon". Hajiya Turai ta idasa maganar cikin rok'o". Shiru Bilya ya yi sannan ya ce, "Hajiya Oga Habib matsayin shi agunmu ya wuce haka zamu iyamai abinda yafi hakama, amma matsalar guda d'aya ce, na farko dai kinsan baya yarda da kowa yashiga inda yake, na biyu kuma Hajiya kina gani jiya da aka kaima abinci yadda aka kaishi haka aka d'akko shi, amma idan kina da wata shawarar sai mubi". Shiru Hajiya Turai ta yi bata ce komai ba". Baba Lami ce ta ce, "Bilya ni dama shawarata sai inga d'ura mai za kuyi, amma dama indai ta lallimice ai ba zai shaba". Bilya gudin kar Hajiya Turai taga kamar yak'ine yasa ya ce, "Shikenan ,Yaune za'afara bashi magani? ". Baba Lami ce ta amsa mai ta hanyar cewa"Eh". Hajiya Turai rubutun ta d'akko ta mik'ama Bilya ta ce, "Bilya wannan shine zai sha yanzu, wannan kuma shine na sha biyun daran,wannan kuma sai gobe zai fara shashi, dan Allah sai kai ma Musa bayani yanzu sai ku bashi". Bilya amsar rubutun ya yi batare da yace komai ba yafita". Bayan fitar Bilya ne,Hajiya Turai ta kalli Baba Lami ta ce, "Baba ni ko duk yau banga Farida ba? ". "Nima kam yanzu nagama zancan azuciyarta". Cewar Baba Lami". Farida ko tun safe tabar gidan, tana ganin fitar su Hajiya Turai itama ta fita, dama yaune sukai da Mahaifiyarta Hajiya Murja zata je. Bayan Farida ta isa gida ne, Hqjiya Murja kallanta tayi tace, "Farida sanin kankine bamu da wani wada tattan lokaci amma shine kikak'i zuwa da wuri, tun shekaran jiya da naima Malam magana aiki ya lallace ya ce kizo da wuri dan asan ta inda za ab'ulloma lamarin amma kikak'i sai yau! ". Farida cikin shagwab'a kamar zata yi kuka ta ce, "Mommy kefa kika ce min bakya so Hajiyar Oga Habib tasan zanzo, tom yaune suka tai zaria naimanma Oga Habib magani, shine fa suna tafiya nasamu nafito". Shiru Hajiya Murja ta yi, sannan ta ce, "Shikenan tashi muje gidan malam". Farida tashi ta yi suka tafi a motar Hajiya Murja". Farida da Mahaifiyarta zaune agaban Malam mai biyan buk'ata dole. Hajiya Murja kallan shi ta yi, ta ce, "Malam kamar yadda nafad'ama aiki dai kuskure aka samu bai yiba". Bak'in katon da Hajiya Murja ta kira da Malam, cikin fad'a-fad'a ya ce, "Hajiya kunzo nan keda yarinyarki akan in muku aiki asama Yaron nan son yarinyarki nace muku ba zai yuwuba, saboda mu munayin abinda zai yuwune, sannan yaron nada wani murd'add'an hali, aikin zai bamu wahala, Nina baku shawarar juya gwagwalwar yaron nan, sannan asa mai k'inyarda da kowa sai 'yarki kad'ai, sai kuyi amfani da damar yarda da 'yarki da yake yi kuhad'asu aure, bayan aure in warware aikin da nai me, sannan kafin in baku maganinnan wana irin jan kunnene ban muku ba, na dad'e Ina nana ta muku karku sake yarinyarki tayi nesa dashi, amma taya kuka yi sakaci haka ta faru? ". Farida cikin rawar murya ta ce, "Wallahi yaron shine yajamin, yanzu dan Allah asake min wani abun wanda zaiwarware wancan konawane zan bada". "Wata irin dariya ya yi sannan ya ce, "Ya sunan yarinyar da yake yadda da ita? ". Farida da Hajiya Murja had'a baki sukai wajan cewa, "Hassana". Wani 'yan Zane-zane ya yi sannan ya ce, " Abin bawani mai wuya bane, amma dole sai yaron nan ya kusanci yarinyar da yake yarda da ita yanzu haka, sannan koda wannan makarin sai karye, yanzu akwai abinda zan baki ki tabbatar kinba yarinyar taci shima yaron yaci, idan har ya kusanci yarinyar shikenan, zaki zama dake kad'ai yake yarda Mahaifiyarshi da kanta zata had'a auranki da shi". Hajiya Murja kallan bak'in k'aton banza ta yi, ta ce, "Ba komai ka bata abinda zata basu d'in, sannan ita yarinyar in sonsamune gudin matsala muna so arabata da gidan ". Wata mahaukaciyar dariya yayi ya ce, "Shikenan damuwarku da zo k'arshe, sai ni Malm mai biyan buk'ata dole, da kazo gurina buk'atarka bata biyaba, gara in bar aiki". Haka yagama yi ma kanshi kirari sannan ya d'auki wani bak'in abu kamar d'inya ya ce, "Wannan abun da kike gani, daga kin je gida yanzu zaki jik'ashi aruwa ya kwana tom ruwanne zaki ba yarinyar ta sha shima yaron yasha". Wata muguwar dariya ya yi sannan ya ce, "Aikinki yagama ci yarinya". Godiya sosai Hajiya Murja tai mai sannan takama hannun Farida suka bar gun suka je inda su kai parking d'in motarsu suka shiga suka kama hanyar gida. Suna cikin tafiya Farida ta kalli Mahaifiyarta ta ce, "Mommy nifa gaskiya ban yarda da abinda Malamin nan yace ba, gaskiya ni bazan bari ya kusan ci k'azamar yarinyar nan ba, kuma ko ba ma haka ba, ni dai ina kishin haka". Kallan baki da hankali Hajiya Murja tai ma Farida, sannan ta ce, "yanzu ya kike so ayi, kina jidai abinda ya ce hakane kad'ai makarin abin, amma idan kina da wata shawarar tom? ". Eh ina da ita Mommy.......... Idan kin karanta daure kiyi Comment sister 🖊 SHERE & comment please 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 Facebook group : https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ _🍃 Baya halatta likita ya ke6anta da mace mara lafiya (ya zanto daga shi sai ita) don duba lafiyarta, dole ya kamata a samu mijinta a wurin ko wani muharraminta a lokacin da ake dubata._ 📒 فتاوى اللجنة الدائمة 422/24 SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA AKE POSTING. KI GARZAYA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 26&27. Farida cikin shagwab'a ta fara yi ma Mahaifiyarta bayani, "Mommy ni dai gaskiya banyarda da maganar Malam ba, inajin kishin ace Oga Habib ya kusanci yarinyar nan, gaskiy inajin kishin haka sosai Mommy, dan Allah ayi wani abun, basai Oga Habib ya kusanci Hassana ba". Hajiya Murja hannun Farida ta kamo ta ce, "Farida ki yi hak'uri, sadoda Malam mai biyan buk'ata dole abinda zai yuwu ya ke yi, amma inda kink'i yarda,yanzu idan nakira shi me kike son ince mai? ". "Mommy ce mai za ki yi, konawa ne zaki biyashi, duk yadda zai yi yayi ya k'arya abin batare da Oga Habib ya kusanci Hassana ba, zaki bashi konawa ne". Hajiya Murja kiran Malam mai biyan buk'ata dole ta yi, yana d'agawa ta ce, "Hello Malam, dama Farida ce ta ce wai babu yadda za ai dole sai Habib ya kusanci yarinyar?, dan Allah idan akwai yadda za ai Malam dan Allah zan biya konawa ne, dan Allah atai makamin, abiyamana buk'atar nan". Cikin fad'a-fad'a Malam mai biyan buk'ata dole ya ce, "Hajiya tun farko fa sai da nafad'a muku ni abinda zai yuwu nake yi, dan haka hakane kawai makarin abin, dole sai yaron ya kusanceta sannan". Yana fad'in haka ya kashe wayar shi". Dayake wayar a speaker ya ke shiyasa Farida ta ji duk abinda Malam ya ce. Hajiya Murja kallan Farida ta yi ta ce, "Farida kin dai ji abinda Malam ya ce ko?, dan haka ki yi hak'uri, kinga dai ita yarinyar rabata da gidanma za ai". Farida cikin shagwab'a ta ce, "Mommy naji nayrda, amma ni ina gudun matsala ne, idan fa aka samu kuskure". Hajiya Murja cikin kwantarma Farida hankali, takamo hannunta, ta ce, "Farida Wallahi kinji narantse ko zan k'arar da abinda na mallaka ne sai kin auri Habib, dan haka kirkiji komai ni na san Waye Malam mai biyan buk'ata dole, shifa akinma da bazai iya ba baya amsar shi, karfa ki manta ko yanzu daga gurinmu aka samu matsala, ba daga gun Malam ba, tun farko da ace kina gun abin ya riski Habib da yanzu anwuce gun, dan haka ki kwantar da hankalinki, indai Habib ne ki d'auka kin aurai kin gama". Farida cikin jin dad'i ta rungume Mahaifiyarta, ta ce, "Mommy wannan shine burin rayuwata in auri Oga Habib, kai Mommy Allah da nafi kowa sa'a, ga kyau, ga Ilimi Mommy, Uwa-uba ga kud'i ".ita dai Hajiya Murja murmushi kawai ta yi ma Farida bata ce komai ba. Nandai sukai ta firarsu. Dai-dai junction d'in area gidansu Habib Hajiya Murja tai parking, kallan Farida ta yi, ta ce, "Farida ki hau napep ki k'arasa, bana son idasawa ciki, idan Hajiya Turai ta tambayeki ina kika je kice mata guna kikazo, nace gobe zanzo gaida Habib inda rud'ewa tasa ta manta bata fad'amin ba". Farida napep ta samu ta hau tak'arasa da ita gidan su Habib. B'angaran Bilya ko tunda Hajiya Turai ta bashi maganin Habib ya samu Musa suka shiga ba Habib magani. Zaune su iske Habib inda ya ke zama. Habib na ganin shigowarsu Bily yayo kansu kamar yadda ya saba.Nan fa su Bilya suka rik'e Habib. Sai dai ina Habib ya fi k'arfinsu, dan duk yadda suka so su d'ura ma Habib rubutun abin yaci tura, dole suka hak'ura suka rabu da shi, daga k'arshe suka sashi a bedroom shi suka rufe shi, suka suka gudu". Bilya kusan karo suka ci da Farida ita kuma lokacin zata shiga falon Hajiya Turai, shima kuma ya taho da saurinsa yana nishin wujijjigasu d'in da Habib ya yi". Hajiya Turai na zaune Bilya ya k'araso inda take, Bilya cikin alamun damuwa ya ce, "Hajiya Wallahi duk yadda za muyi munyi, amma Oga Habib yak'i shan rubutun nan". Hajiya Turai da ta rasa abinda zata ce kawai sai ta sa, kuka. Bilya cikin damuwa ya ce,"Hajiya dan Allah ki yi hak'uri, shi kukan babu abinda zai miki, insha Allah Oga Habib zai ji sauk'i nan bada dad'ewa b, Hajiya dan Allah indai dan maganar rubutu ne ki yi hak'uri zai sha, gashinan nasa ankiramun Hassanar". Bilya be rufe baki ba sai ga Hassana ta shigo". Hassana cikin girmamawa ta gaida Hajiya Turai, sannan ta ce, "Oga Bilya gani ance kana kirana". Bilya kallan Hassana ya yi yace, "Hassana dan Allah magani zaki ba, Oga Habib da abincin shi? ". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Tom Oga Bilya ". Bilya mik'ama Hassana maganin ya yi.Hajiya Turai kallan Bilya ta yi jin bai cema Hassana da nasha biyun dare ba, ta ce, "Bilya na daranfa, wazai bashi? ". Kafin Bilya ya yi magana Hassana ta yi wuf ta ce, "Ni zan bashi Hajiya". Hajiya Turai cikin jin dad'i ta rik'e hannun Hassana ta ce, "Hassana nagode Allah yasaka miki da mafificin alkairi". Da ameen Hassana ta amsa". Hajiya Turai kallan Bilya ta yi, ta ce, "Bilya dan Allah tai makon da kai kuma zakuyi min kai da Musa, idan Hassana taba Habib maganin sha biyun daran, ku kuma dan Allah sai kuje kufitomin da ita, Allah bashi sai ku kawota wajena ta kwana". Bilya cikin girmamawa ya ce, "Insha Allah Hajiya badamu". Hassana bayan ta amshi rubutun da zata ba Habib, kallan Hajiya ta yi, cikin sanyin muryarta ta ce, "Hajiya duka za abashi yanzu? ". "A'a wannan nafarar gorar shine na sha biyun dare, wannan kuma sai gobe ma za afara amfani da shi". Hassana d'aukar maganin Habib ta yi sai abincin shi ta nufi part d'in Habib d'in. Farida da kallo ta bi Hassana acewarta samun guri, wato yauma anan zata kwana, wani tunanine yazo ma Farida, aiko da saurinta ta tashi ta fita, dan Hajiya Turai na mata maganama sai ce mata tayi zata dawo yanzu". Farida na fita waya ta d'aga ta kira Mahaifiyarta. Hajiya Murja na d'aga kiran, Farida ta ce, "Mommy dama wata dama ce tasamu yanzu, yarinyar nan yanzu zata kaima Oga Habib maganin shi, shine nace me zai hana muyi amfani da damarnan mu basu maganin su sha?, tom kuma sai na tuno Malam yace sai anjik'a shi ya kwana tukun, shine na kiraki kikira Malam ki mai bayani idan zai yuwu tom kawai muyi amfani da damarnan mu basu maganin ". Hajiya Murja cikin gamsuwa da maganar Farida ta ce, "Shikenan Farida bari in kira Malam awaya in fad'i mai". Hajiya Murja Malam mai biyan buk'ata dole ta kira, yana d'agawa ta ce, "Hello Malam dama Farida ce ta kirani yanzu, wai yarinyar da ake so abama maganin da ka bada ita da Habib, tom shine wai yanzu haka yarinyar zata shiga d'akin Habib d'in, shine idan badamuwa muke so muyi amfani da damarnan mu basu maganin su sha, tom amma kuma kace sai anjik'a maganin aruwa ya kwana sannan, shine nace ko za a'iya amfani da shi a yau d'in ? ". Daga can b'angaran Malam mai biyan buk'ata dole ya ce, "A'a ba damuwa ku basu su sha, gobe sai kizo da wuri ki amshi na barin yarinyar gidan". Hajiya Murja godiya ta yi ma Malam mai biyan buk'ata dole, sannan ta kira Farida dan yi mata bayanin abinda ya ce. Farida na d'agawa Hajiya Murja ta ce, "Hello Farida yace zaki iya basu, sannan ya yi mun albishir d'in gobe-gobannan yarinyar zata bar gidanma baki d'aya, gudin matsalama". Farida cikin jin dad'i ta ce, " Shikenan Mommy sai anjima bari in yi sauri in ba yarinyar kafin ta wuce". Farida na fad'in haka ta kashe wayarta, ta nufi Falon Hajiya Turai". Farida na zuwa cikin hikima ta d'akko maganin acikin jakarta sannan ta fita. Part d'in Habib ta nufa. Farida na zuwa ta fara nocking d'in k'ofar". Hassana ta sowa ta yi ta bud'e mata, Farida na shigowa Habib ya yo kanta, da gudun Farida ta fita, Hassana kuma ta yi saurin rufe k'ofar. Farida wajan window ta koma tana kiran Hassana. Habib na rik'e da Hassana ka takam Hassana ta je kiran da Farida ke mata. Hassana kamar yadda ta ji worker's d'in gidan na cema Farida itama haka ta ce, "Aunty Farida gani? ". "Yauwa Hassana dama Mommy ce taban maganin nan ta ce in kawo miki kisha". Hassana cikin mamaki ta ce, "Aunty Farida ko dai in ba Oga Habib ya sha". Farida cikin d'aurewa ta ce, "ke ni banda hankali ne da bazan gane ke aka ceba!, kowa ta bashi yasha nima bansan na meye ba, gana Oga Habib ma, shima ta ce abashi yasha". Hassana ko da yake bata kawo ma ranta komai ba batare da fargabar komai ba, Farida na mik'a mata maganin, Hassana ta d'aga ta shanye maganin". Allah sarki Hassana batare da fargabar komai ba Hassana ta shanye, sannan ta mik'a mata na Habib d'in ta ce shi kuma ki bashi wannan". Farida na fad'in haka ta juya ta tafi da saurinta gudun kar Allah ya kawo Bilya gun". Hassana ko amsar na Habib ta yi, t kamo hannun Habib d'in ta ce, "Oga Habib muje ka gama cin abincinka sai ka sha magun-gunanka". Hassana kafin suka k'arasa kan Caution d'in da suke zaune taji wani irin abu ya tsarka mata tun daga kanta har tafin k'afarta. Hassana cikin wani irin sabon yanayin da ta riski kanta yanzu-yanzu ta tsaya cak ta kasa tafiya tana mamakin abinda ke damunta, dan abun tana jin shi kamar duk seconds k'aruwa ya ke. Hassana cije lips d'in ta ta yi tana mai duk addu'ar da tazo bakinta". Hassana cikin tsoran halinda ta ke jinta ta samu ta lallab'a ta mik'a hannu ta d'akko Maganin Habib d'in batare da tasan ko wanne ba ta d'akko ba ta mik'ama Habib". Habib ko ana bashi magani ya amsa ya shanye duka. Hassana ko da take jin wanirin abu da ta kasa gane ko menene, cikin fitar hayyaci Hassana ta fara tub'e kayan jikinta.Haka Hassana ta ya yi ma kanta tsirara haihuwar uwara. Tana mai dafe da mararta ta fara takowa har izuwa inda Habib ya ke , Hassana na zuwa ta fad'a kan Ha.............. K'ara-k'ara k'ak'a, Hassana ta sha magani Habib ma yasha, kome zai faru........ 🤐🤐🤐 Ayi manage da wannan. Inkin karanta daure ki yi comment sister 🤝 Comment & Share please 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 My Facebook group :https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Abokai na gaskiya suna da wuyar samu, suna wuyar bari, suna da wuyar mantawa. Allah ka had'amu abokai na gaskiya. SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA AKE POSTING. KI GARZAYA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 28&29. Hassana cikin fitar hayyaci ta fad'a kan caution d'in da Habib ya ke. Haka Hassana tai ta juyi akan caution d'in, tana goga jikinta akan Habib. Habib dai kallanta kawai ya ke bamagana. Hassana hannu Habib ta kamo tana shashshafawa ajikinta ko zataji sauk'in yadda take ji. Hassana ta kai wani dogon lokaci bataji wani sauk'i ba daga yadda ta ke ji. Ana ahaka taji nocking d'in k'ofar Bilya.Cikin azaba ta tashi ta shige bedroom d'in Habib, shi kuma Habib dama ya zama bita zai-zai, duk inda Hassana ta yi yana biye da ita, haka ya tashi da sauri ya bita, kusan atare suka fad'a kan bed d'in ". Bilya ko kallan Musa ya yi, ya ce, "Musa kaga sai bubbuga K'ofar nan nake amma shiru, kodai bacci ne ya kwashe yarinyar nan?, tom idan hakane ko kaga ko maganin ma bata bashi ba kenan". Bilya kallan Musa ya yi yace, "Musa bari in lek'a ta window nan in gani". Window Falon Bilya ya lek'a amma daga Hassana har Habib babu kowa a Falon. Musa ne ya kalli Bilya ya ce, "Bilya kamar nishin mutum nake ji? ". "Wallahi Musa nima naji". Bilya cikin alamun tsoro da ya bayyanar mai, ya ce, "Musa Lafiya kuwa?, kodai Hajiya zamuyi ma magana, nifa gaskiya abin yafara ban tsoro, tom nishin waye haka, nifa Musa ina tsoran kar Oga Habib ya yi ma yarinyar mutane wani abun! ". Musa kallan Bilya ya yi, ya ce, "Malam duk kawani tada hankalinka, babu wani abun zai faru, nafi tunanin bacci ne ya kwasheta, kuma kasan wani idan yana bacci zaka rik'a jin yana nishi". Bilya cikin rashin yadda da abinda Musa ya ce, ya ce, "Musa tom me yasa basa Falon?, me yashigar da ita bedroom d'in Oga Habib? ". Ko daga jin yadda Bilya ya ke magana kasan cikin fargaba ya ke, sosai". Musa cikin mamaki ya ke kallan Bilya, sannan ya ce, "Haba Bilya kasan me kake son cewa kuwa?, karfa ka manta Oga Habib fa bacikin hankalinshi ya ke ba, sannan koda ace cikin hankalin shi yake kai sanin kanka ne, Hassana bata isai kallo ba, dan haka ka saisaita kalamanka". Bilya cikin jin haushi maganganun Musa, ya juya ya tafi yabar Musa agun tsaye. Musa ma biyan Bilya ya yi suka tafi". Hassana ko najin maganganunsu Bilya sama-sama amma batajin me suke cewa. Hassana haka taita malelekuwarta a gadon Habib. Habib ko duk inda Hassana ta yi ya na biye da ita, ahaka bacci ya kwashe Habib yana rik'e da hannun Hassana. Hassana ko sai gab da asuba taji sauk'i daga yadda ta ke ji, nan fa bacci ya d'auketa". Habib ko koda ya tashi ya ga Hassana kwance tana bacci, kwanciya ya yi shima gefanta ,ya na rik'e da ita". Hassana sai 7:00am ta farka. Cikin mamaki da tsoro Hassana ta ke kallan kanta, jikinta babu kaya ga ta kwance da Habib a gado d'aya, ya na rik'e da ita. Hassana tsabar tashin hankali da tsoro kawai sai ta sa kuka ta tashi da sauri ta nufi falo dan d'akko kayanta. Habib kuma na ganin Hassana ta sauka kan bed d'in shima ya yi sauri ya sauka ya bi bayanta. Hassana ta d'akko rigarta kenan zata sa sai ga Habib ya fito, tasan gurinta zaizo hakan yasa Hassana cikin kuka ta d'aga ma Habib hannun, alamun da katarwa, ta ce, "Oga Habib karka k'araso inda nake Wallahi! ".Hassana ta fad'i maganar cikin kuka. Habib ko da kallan Hassana kawai ya ke ba gane meta ke cewa ya ke ba, inda ta ke ya zo, yana zuwa ya rik'e hannunta kamar yadda ya saba". Hassana ko naganin Habib ta yi sauri ta jira rigarta,dama doguwar rigace.Sannan ta d'akko Hijab d'in ta ta saka.Ta ci gaba da kukanta. Har yanzu Hassana kuka take, zaune ta ke kan Caution d'in Falon tana kuka Habib kuma na rik'e da hannun yana aiki kalkonta". Hassana tunanin ta farayi ahankali, tana tuno abinda ya faru da ita ya fara dawo mata kad'an-kad'an. Tabbas idan bata mantaba tabbas tunda tasha maganin da Farida ta bata, ta rasa natsuwarta, Hassana kallan wanda ta bata taba Habib ta yi. Alhamdulillah Hassana ta ce, ganin wanda Farida ta bata tace taba Habib bata bashi ba, dan tabbas wanan maganin nada wani sinadari na b'atar da hankali cewar Hassana, amma kuma ai Aunty Farida "yar'uwar su Oga Habib ce, bazata bashi abinda zai cutar da shiba, tom amma ni meyasa maganin ya yi min haka?, haka dai Hassana ta gama tambayar kanta ba amsa, kuma still bata bar kukan da take ba. Hassana nan zaune tana kuka, ta ji nocking. Share hawayanta ta yi, sannan ta je ta lek'a ta window ". Hassana Bilya ta gani tsaye ya yi crossing d'in hannun shi yana mata wani irin kallo da yasa ta sha jinin jinin jikinta. Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, tana didduk'ar da kai kamar muna fuka, ta ce, "Oga Bilya ina kwana". Me makon Bilya ya amsa ma Hassana gaisuwarta sai cewa ya yi, "Hassana jiya me yasa da muka buga k'ofa biki bud'e mana ba? ". Hassana cikin rawar murya ta ce, "Oga Bilya bacci ne ya kwasheni". "Amma meyasa baki kwanta falo ba! , kika shiga bedroom d'in Oga Habib? ". Hassana sosai ta tsora da kalaman Bilya da yana yin yadda ya ke mata magana, hakan yasata, cikin rawar murya ta ce, "Oga Habib ne ya kaini". Bilya kallan Hassana ya yi, ya dad'e yana kallanta sannan ya ce, "Hassana me yasaki kuka? ". Shiru Hassana ta yi tana wasa da fingers d'inta. Bilya k'ara mai-mai ta ma Hassana tambayar shi ya yi, ya ce, "Hassana nace me yasa ki kuka? ". Hassana kuka ta sa, still ta kasa yin magana". Farida ko da zuwanta kenan tazo ganin k'wak'waf, da sauri ta lab'e tana mai jin dad'in ganin Hassana da ta yi tana kuka, dan ko ba afad'a mata ba, tasan mai faruwa ta faru, tsakanin Hassana da Habib. Farida cikin jin dad'i ta koma d'akinta, tana zuwa ta fad'a kan bed d'inta tana jin dad'in abinda ta gani, dan tabbas Hassana kukan da ta ke yi na kusantarta ne da Habib ya yi, acewar Farida.waya Farida ta d'akko ta kira Mahaifiyarta, Hajiya Murja dan yi mata albishir. Hajiya Murja na d'auka Farida ta ce, cikin jin dad'i, "Mommyna albishirinki? ". Daga can b'angaran, Hajiya Murja ta ce, "Goro fari k'ar kato". Farida cikin murna da d'oki ta ce, "Mommyna Wallahi na yarda da aikin Malam mai biyan buk'ata dole, Mommyna aiki ya k'arye dan Oga Habib ya kusanci Hassana, yanzu haka maganar da nake miki kuka ta ke, yanzu Mommy ki je gun Malam ya baki na barinta gidan sai kizo da shi, dan ni Wallahi bana son ta k'ara kwana a gidannan". Hajiya Murja itama cikin jin dad'in nasarar aikin da su kayi ta ce, "Tom Farida yanzu sai hankalinki ya kwanta ko, kinga dai alamun nasara, yanzu bari inyi breakfast , idan nagama inyi wanka sai in je gun Malam d'in, daga can zo nan"."Tom Mommy sai kin zo". Farida na fad'in haka ta kashe wayar, tana mai jin farinci aranta". Can b'angaran su Hassana ko, Bilya cikin damuwa ya ce, "Hassana please mana, dan Allah karki sani confused mana, me yasa kike kuka? ". Hassana cikin shasshek'ar kuka ta ce, "Oga Bilya bana son k'ara zuwa gurin Oga Habib dan Allah ". Shiru Bilya ya yi yana mai kallan ganin yadda ta ke kuka. Sannan ya ce, "Shikenan Hassana ki shiru haka nan kar kanki ya yi ciwo,in dai gurin Oga Habib ne ki yi hak'uri, insha Allah daga yau bazaki k'ara zuwa ba, nina san mai zan cema Hajiya ". Duk maganar nan da Hassana da Bilya su ke yi, ta Window su ke yinta. Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce, "Bari in kira Musa muzo mu fidda ki". Kai Hassana ta d'aga ma Bilya, ya juya kai ya tafi". Bilya ya tafi ba dad'ewa sai ga shi ya dawo da Musa. Musa kallan Bilya ya yi ya ce, "Bilya abata abin breakfast ta bashi mana, inda naji kana cewa daga yau ba zata k'ara zuwa bashi abinci ba". Shiru Bilya ya yi sannan ya ce, "Musa Wallahi anfara shiga hakin yarinyar nan, yanzu haka maganar da nakema kuka nazo na sameta ta nayi, amma bari in amso abin breakfast din in kai mata ta bashi". Bilya wajan Baba Lami ya je, ta had'o mai abin breakfast d'in Habib". Bilya amsa ya yi, yana zuwa ya yi nocking d'in k'ofar. Hassana ta sowa ta yi. Bilya kallan Hassana ya yi ya ce, "Hassana ga breakfast d'in Oga Habib nan dan Allah ki bashi, ni nai miki alk'awari daga yau ba mai kuma k'arasaki kawo ma Oga Habib abinci ko magani". Hassana amsa ta yi tashiga da shi, kunun gyad'a abinda Habib ya fi so. Hassana zuba ma Habib ta yi ta mik'a mai ya amsa ya shanye. Doya da kwan ta bashi ita kuma ya k'i ci. Habib na gama shanye kunun Hassana tai ma Bilya magana da ya ke, Bilya na bakin k'ofar suna jiran Hassana ta gama ba Habib abin breakfast d'in . Hassana juyowa ta yi tana kallan Habib da ke rik'e da hannunta, sannan ta kai wasu mintoci tana kallan Habib sannan ta ce, "Oga Habib sakan min hannu zan tafi, sai watarana bazan k'ara shigowa inda kake ba, jiya nariski kaina awani kallan yanayi mai wuyar fassarawa, bana fata haka ya k'ara faruwa dani, bansan nan gaba mai zai faruba, idan haka ya kuma faruwa". Hassana rik'e hannun Habib ta yi, ta ce,"Oga Habib ina maka fatan alkairi, Allah ya baka lafiya". Hassana na fad'in haka ta juya zata fita, Habib ya rik'e hanunta. Hassana cikin sanyin muryarta ta kira Bilya, ta ce, "Oga Bilya nagama ku shigo". Bilya ko da Musa suna tsaye bakin k'ofar, dama Hassana suke jira suzo su fitar da ita". Da k'arfi su Bilya suka b'amb'are Hassana daga hannun Habib kamar yadda suka saba. Hassana ko mai-makon ta je Falon Hajiya Turai, b'angaran su na "yan aiki ta wuce". Farida ko da taji shiru, Hassana bata shigo Falon Hajiya Turai ba, tashi ta yi ta nufi part d'in worker's d'in gidan. Farida nesa da b'angaran su Hassana ta tsaya yadda babu wanda zai ji abinda zata cema Hassana. Farida na nan tsaye d'aya daga cikin worker's d'in ta zo wucewa, Farida kiran ta ta yi, ta ce ta kiramata Hassama". Hassana ko na kwance tana jinta duk ba dad'i, ga halinda ta tashi taga kanta duk ya da meta, dan har yanzu ko mai batasa abakinta ba. Binta kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana Aunty Farida na kiranki". Hassana batare da tace mata komai ba ta tashi ta fita, dan amsa kiran Faridar". Tsaye Hassana ta iske Farida tana jiranta. Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ke kukan me d'azu naganki kinayi? ". Hassana da mamaki ta kalli Farida dan tambayar tazo mata abazata.Farida ko jin Hassana ta yi shiru tana kallanta ya sa cikin k'osawa ta ce, "Nace me yasa ki kuka d'azu?, da naganki tsaye da Bilya a wajan window Falon Oga Habib ". Hassana rasa abinda zata ce ma Farida ta yi, ka wai sai ce mata tayi. "Aunty Farida banda lafiya ne". Farida cikin d'aga murya ta ce, dan tana tunanin Hassana so take ta b'oyemata Habib ya yi mata Fyad'e, hakan yasa cikin d'aga Murya , Farida ta ce, "K'arya kike Wallahi, me kika ce ma Bilya Oga Habib ya yi miki?, ko kina tunanin banji bane? ". Hassana da mamaki ta ke kallan Farida, sannan cikin sanyin murya ta ce, "Wallahi Aunty Farida bance ma Oga Bilya Oga Habib ya yi min ko mai ba, kawai dai ina kuka ne shine ya ke tambayata abinda ya sani kuka". Farida da saurinta kamar wani zai rigata ta ce, "Tom meye yasaki kukan? ". Hassana kallan Farida ta yi kamar za tai kuka ta ce, "Nagaji da kaima Oga Habib abinci ne, shine yasani kuka". Wani murmushi Farida ta yi ma Hassana , dan ita a d'aukarta Hassana tana karewa ne, bata son taji Habib ta yi mata Fyad'e ne. Hakan yasa Farida ta d'aurai fuska, ta kalli Hassana ta ce, "Hassana ni zaki yi ma k'arya, saboda kina tunanin bansan abinda ya faruba". Hassana ko rud'ewa ta yi jin abinda Farida ta ce, sai ta ke ganin kamar ko taganta ne lokacinda jiya ta cire kayanta , bayan shan maganin da ta kawo mata. Hakan yasa Hassana cikin zubba kwallah ta ce, "Aunty Farida Wallahi babu komai, amma idan baki yadda ba ki kira Oga Bilya ki tambaye shi". Wani tunanine yazoma Farida, kallan Hassana ta yi, ta ce, " nasan dai kinsha maganin da na baki ko? ". Kai Hassana ta d'aga ma Farida. "Ok, tom na Oga Habib fa da nace ki bashi, kin bashi? ". "Aunty Farida ki yi hak'uri banba shiba, wani na bashi wanda Hajiya taban in bashi, nama zaci wanda kika banne, sai yau da natshi nagan shi, amma yanzu zanje in bash.......... ". Marin da Farida taima Hassana ne, yasa Hassana tai shiru. Farida nuna Hassana da d'an yatsa ta yi, ta ce, "Dan uwarki ni zaki sa in yi asara, tom Wallahi baki isaba kin yi kad'an..... ". Ringing tone d'in wayar Farida ne yasa ta yi shiru ta maida kanta da kallan wayar. Farida na dubawa taga Mahaifiyarta ce, hakan yasa Farida ta yi saurin barin gurin, sannan ta d'aga kiran. Hajiya Turai sanar da Farida ta yi gata nan zuwa. Farida cikin tashin hankali ta ce, "Mommy dan Allah ki yi sauri ki zo , Wallahi akwai damuwa sosai". Farida ko cikin damuwa ta koma falon Hajiya Turai dan sanar da ita zuwan Mahaifiyarta". Farida zaune ta iske Bilya da Baba Lami da Hajiya Turai a falon, Farida gu ta nema ta zauna, dan tana son jin tattaunawar da suke. Hajiya Turai kallan Bilya ta yi, ta ce, "Bilya kai fa muke sauraro baka ce mana ko mai ba, kace kuma kana son magana dani". Hajiya Turai ta idasa maganar cikin damuwa". Bilya sosai ya ji yana jin tausan Hajiya Turai saboda abinda zai ce, amma ganin ta matsu da ta ji, yasa, cikin sanyin murya ya ce, "Hajiya dama akan Oga Habib ne, jiya kince muje mu fito da Hassana bayan ta ba Oga Habib magani, amma Hajiya Oga Habib kinsan bai barin yarinyar nan fita, dan yanzu abin yafara cin tura ma, dan ko yau da safe dakyar nida Musa muka kwaceta daga hanun Oga Habib, Wallahi Hajiya biki ga yadda yarinyar ke kuka ba, tana rok'ona dan Allah ita dai bazata k'ara zuwa kai ma Oga Habib ko mai ba". Shiru Bilya ya yi sannan ya ci gaba da cewa, "Tom Hajiya shine nake son dama musan yadda zamu b'ulloma lamarin, inda ita yarinyar ta nuna gajiyawarta, duk da zuciyata na zargin kamar wani abun ya yi mata". Hajiya Turai cikin tsantsar damuwar da ta kasa b'oyewa ta ce, "Bilya ya zanyi da Habib, dan Allah kakiramin ita ta rik'a ba Habib magani ni Wallahi konawa ne zan biyata, dan Allah Bilya, ku tai makeni, Habib shikenan min, shi kad'ai ne wanda yarage min nake kallo inji dad'i, dan Allah Baba Lami kisa baki, wa zai ba Habib magani idan yarinyar nan tak'i? ". Hajiya Turai ta idasa maganar cikin rud'ewa". Shiru Bilya ya yi, dan gaba d'aya tausan Hajiya Turai ya cika zuciyar shi. Baba Lami kallan Hajiya Turai ta yi ta ce, "Hajiya ni inada wata shawara duk da dai kamar ba mai yuwuwa bace, amma idan aka so zata yuwu? ". Hajiya Turai kamar zata sa ihu ta ce, ", Baba Lami wata shawara ce, ina jinki? ". Shiru Baba Lami ta yi tana tunanin ta inda zata fara ba yani, dan ita kanta tasan lamarin babba ne, sai da Baba Lami, ta d'auki dogon lokaci sannan ta ce, "Hajiya ni gani nake, inda Oga Habib bai yarda da kowa sai yarinyar nan, ko abinci in bata gu bazai ciba, bare magani, rok'onta zamu taru muyi,ta auri Oga Habib kafin nan da yaji sauk'i, Allah bashi sai ayi auran asirri babu wanda zaima sani, Allah bashi duk radda Oga Habib ya warke shikenan, ki naimi zaki bata konawa ne, amma ya kika gani Hajiya? ". Hajiya Turai cikin sanyin ta ke cewa, "Dan Allah Baba Lami ku taimaka ku rok'anmin ita, Wallahi nima tunanina kenan, amma inajin shakkar furtawa dan kar aimin kallon mai son kanta da yawa". Baba Lami kallan Bilya ta yi tace, "Bilya baka ce komai ba, ya kagani? ". "Eh gaskiya Baba Lami wannan kam shine abunda zai fi, amma kuma shi Oga Habib d'inne, baku tsoran ranar da zai farka ya riski wannan labarin? ". Shiru Baba Lami ta yi, Sannan ta ce, "Bilya ni kaina nasan Oga Habib ba zai zauna da Yarinyar nan ba, dama dai auran kafin yaji sauk'i ne". Sosai Bilya ya amsu da shawarar dan yafi kowa sanin waye Oga Habib. Hajiya Turai kallan Bilya ta yi, ta ce, "Bilya kiramin Hassana yanzu ". Bilya tashi ya yi zai fita dai-dai kuma Hajiya Murja ta shigo , shigo warta kenan". Dakyar Hajiya Turai ta daure wajan sakin fuskarta ta yi ma Hajiya Murja sannu da zuwa. Nan dai suka gaggaisa da kyau kamar kusan yadda suka saba gaisawa. Hajiya Murja kallan Baba Lami ta yi, ta ce, "Baba Lami wannan meeting d'in fa ,na meye? ". Baba Lami ko da yake tasan abinda ke faruwa, da gayya ta ce, "Na auran d'anki ne, Habib". "Haba-haba aure kuma shidawa? ". Nan Baba Lami ta labarta mata komai game da yadda suka tsara na had'a Hassana aure da Habib kafin ya samu lafiya". Da kyar Hajiya Murja ta iya b'oye damuwata tana washe baki ta ce, "Hakan ko ya yi ya yi kyau sosai" Shigowar Hassana da Bilya ce, tasa Hajiya Murja ta yi shiru ta maida kallanta ga Hassana. Hajiya Turai ko hannun Hassana ta Kama, ta ce, "Hassana zaki ji". Hajiya Turai shigar da Hassana bedroom d'in ta ta yi". Bilya ko na kawo Hassana ya Kama gaban shi, Baba Lami ma hakan ta ke. Falon ya rage daga Farida sai Hajiya Murja". Farida ko tunda ta ji maganar had'a Hassana da Habib aure, ta tusa kanta tsakankanin cinyoyinta tana kuka, mai had'e da tashin hankali". Hajiya Murja ganin Falon ba kowa sai su kad'ai tashi ta yi, ta je inda Farida ta ke tana kuka. Hajiya Murja hannun Farida ta kamo ta ce, "Kishiru Farida dan Allah, karki d'orama kanki wani ciwan". Farida kai ta d'ago tana kallan Mahaifiyarta ta ce, "Mommy ko mai bai yi ba, dan yarinyar nan bata ba Oga Habib maganin nan ba, kuma yanzu kinji maganar da suke yi, Wallahi Mommy idan har haka ta tabbata tom baki sake ganina, Mommy zan tafi wani gu wanda nima bansan inane ba, bazaki k'ara ganinba". Farida ta idasa maganar cikin matsanancin kuka". Hajiya Murja cikin tashin hankali da jin abinda Farida ta ce dan tasan zata yi fiye da abinda ta ce, Hajiya Murja kallan Farida ta yi, ta ce, "Farida Wallahi! Wallahi!! Wallahi!!!, kinji narantse, Wallahi auran nan ba zai yuwu ba, dan haka kima kwantar da hankalinki, ko yanzu bada ga gurin Malam me biyan buk'ata dole bane matsala ta samu, daga gurin mune, dan haka karma ki d'aga hankalinki, da ke za a d'aura auran nan, karma ki sama kanki damuwa ko d'aya". Farida kallan Hajiya Murja ta yi, dan sao taji hankalinta ya d'an fara kwanciya jin abinda Mahaifiyarta ta ce, dan tasan akanta babu abinda Hajiya Murja ba za tai ba, bakamar ce mata d'in da tayi bazata k'ara ganin ta ba". Farida rik'e hannun Mahaifiyarta ta yi, ta ce, "Mommy ina tsoran asamu kuskure irin wannan karan? ". Murmushi Hajiya Murja ta yi ta ce, "Farida Wallahi Habib bashi da mata sai ke, tashi muje wajan Malam mai biyan buk'ata dole ayita ta k'are, ". Farida tashi ta yi, suka tafi da Hajiya Murja.............. Idan kin karanta daure ki yi comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 My Facebook group :https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Mak'iyanka Mutane uku ne:Mai k'in ka, da mai k'in masoyinka, da mai son mak'iyinka. Mai son Uwa dole ne ya so d'anta. Ya Allah ka had'amu da masu son mu a duk inda suke👏. Ina gaisuwa, sister Hassana barrister, Allah ya tai makeki aduk inda kike, miji nagari nai miki fata🤝 SANARWA! SANARWA!! SANARWA!! YAUNE NAKE FARIN CIKIN SANAR DA KU, MASHIYAR HAZIK'R MARUBUCIYAR NAN TAKU, WADDA TA SABA NISHA D'AN TARKU DA HAZIK'AN LITATTAFAN, IRINSU, :RAYUWAR GIDAN MU,JALILAH , SHAIRIN SO.TOM YAU GATA TAFE DA WANI SABON LABARI WANDA YASHA BAMMA DA SAURAN, NASAN WASUN KU ZASU CE MIN HARDA SU JALILAH, DA SHAIRIN SO, TOM HADDA SU.TOM KUDUBI HAD'UWA DA TSARAWA NA LITTAFINTA MAI SUNA K'AWAYE, AMMA ARADU WANNAN LITTAFIN YA DOK'E SHI. NA SAN MASOYAN LITTAFIN AUTAR MAMA, DAMA WA IN DA SUKE JIN LABARIN LITTAFANTA SUN K'OSA SUN MATSU DAN JIN SUNAN LITTAFIN.TOM GA SU NAN NAN 👇🏻 K'ABILA CE! K'ABILA CE!! K'ABILA CE!!! KU DAGA JIN SUNAN KUN SAN YAZO DA SABON SALO MAITAFIYA DA ZAMANI. K'ABILA CE! :SABON LITTAFINE DA AKE POSTING. KI GARZAYA KI RUGA DA GUDU DAN KI ZAMA D'AYA DAGA CIKIN MASU KARANTA K'ABILA CE! WHATSAPP CONTACT 👇🏻 08142904255. Shafi na 30&31. Hajiya Murja da Farida zaune gaban Malam mai biyan buk'ata dole. Hajiya Murja cikin damuwa ta ce, "Malam Wallahi ko mai fa ya lallace! ". Bakin k'aton da aka kira da Malam, kallan Hajiya Murja ya yi da jajayan idon shi, cikin fad'a-fad'a ya ce, "Hajiya kamar ya, bangane aiki ya lallace? ".Hajiya Murja cikin damuwa ta ce, "Malam abubuwa fa sun b'ace, wato maganin da kaba Farida kace taba yarinyar ta sha ta ba Oga Habib shima ya sha, tom Wallahi Malam kuskure aka samu, yarinyar ita kad'ai tasha bata ba Oga Habib ya shaba, tom yanzu dai Malam duk ba ma wannan ba, yanzu babban abin tashin hankalin, had'a auran yarinyar da Oga Habib zu ke so suyi". Hajiya Murja ta idasa maganar cikin yanayin damuwa". Wani 'yan zane-zane ya yi ak'asa sannan ya ce, "Yanzu me kuke so ayi, dakatar da auran za ai?, koko amintar yarinyar da shi kuke so araba?, koko gidan za a koreta gaba d'aya?". Hajiya Murja kallan Farida ta yi, ta ce, "Farida mi ke so ayi, a cikin abinda Malam ya lissafo? ". Shiru Farida ta yi tana tunani, sannan zuwa can ta ce, "Malam ni yanzu auran nan da suke maganar had'awa nake so afasa, maganar ta yi shiru kamar ba ayi ba, sannan a raba yarinyar da gidan gaba d'aya". Yadad'e yana zane-zane ak'asa sannan ya ce,"aikinki mai sauk'i ne, amma fa dole sai anraba amintar yaron da yarinyar, maganar aure kuma inda akayi ta anan za'abarta baza su k'ara tada maganar ba". Wani magani yad'akko ya mik'ama Farida, ya ce, "Wannan maganin zaki zuba shine a abinci ko abinsha, duk wanda ya ke da hannu da tsaki amaganar azuba maganin nan abinci ko abin sha aba shi yaci, magana ta k'arae, babu wanda zai kuma tadata". Wani maganin ya kuma d'akkowa ya ba Farida, ya ce, "Wannan kuma irin wanda na baki ne, zaki ba yarinyar da yaron su ci a abinci ko abin sha". Farida amsar maganin ta yi, ta ce, "Malam kenan dole ne ya kusanci yarinyar? "."Eh dole ne, ta hakane za'araba amintar shi da yarinyar".shiru Farida ta yi, sannan ta ce, "Malam ba a iya raba yarinyar da gidan, inda idan akai hakanma kamar anraba shi da yarinyar ne". "Idan haka kike so za ai miki, amma fa zai ci gana da k'in aminta da kowa, kamar yadda ya ke yi ayanzu, idan har kina son komai ya tafi dai-dai tom dole sai anraba amintar yaron da yarinyar sannan". Shiru Farida ta yi sannan ta ce, "Shikenan Malam, ayi hakan". Malam mai biyan buk'ata dole, mik'ama Farida maganin ya y, ya ce, "ki daure ki yi maganin nan yadda ya akace, buk'atarki zata biya 'yan mata". Cikin jin dad'i Farida ta ce, "Allah yasa Malam". Dariya bak'in k'aton wanda aka kira da Malam ya yi, ya ce, "Karki damu buk'atarki zata biya, aikin da mukaga baza mu iyaba bama karb'arsa, ke ko mun hango nasara a tattare da aikinki, nine Malam mai biyan buk'ata dole, buk'atarki zata biya yarinya". Kud'i masu yawa sosai Hajiya Murja taba shi, sannan su kai mai sallama suka tafi". Hassana da Hajiya Turai zaune bakin bed d'in Hajiya Turai. Hajiya Turai hannun Hassana ta kamo, ta ce,"Hassana nasan zaki yi mamakin shigo da ke bedroom d'ina da nayi".Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ci gaba da cewa, "Hassana Allah ya jarabceni, ya d'orama Habib lallurar da baya son kasan cewa da ni, Hassana zuciyata na ciwo sosai a duk sanda na kalli Habib naga halinda ya ke". Shiru Hajiya Turai ta yi sannan ta ci gaba da cewa, "Hassana anban magani in ba Habib, amma babu dama, taya zan ba Habib magani baya yarda in je inda yake... ". Kuka ne ya kwace ma Hajiya Turai ". Hassana cikin damuwa da tashin hankali ganin Hajiya Turai na kuka, ta ce, "Hajiya dan Allah ki yi hak'uri, kibar kukan, insha Allah Allah zai ba Oga Habib lafiya". Hajiya Turai saukowa ta yi daga bakin bed d'in, ta zuk'unnama Hassana ta koma hannun Hassana, ta ce, "Hassana dan Allah ki tai makeni ki auri Habib". Hassana da ke zaune bata san-sanda ta mik'e tsayeba tana kallan Hajiya Turai, cikin yana yin furgita da jin abinda Hajiya Turai ta ce". Hajiya Turai ma ta shi tayi tsayan tana kallan Hassana ganin yadda furgici da tsoro ya bayyana a idon Hassana. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana dan Allah ki tai makeni ki auri Habib, banda mai ba Habib magani, Hassana ke kad'ai ce Habib ke yarda da ke, in ba ke kika bashi maganin nan ba, bazai shaba, kina ganin ko abinci indai bake ba baya ci". Shiru Hajiya Turai ta yi sannan ta ce, "Hassana dan Allah zaki yardar ki auri Habib? ". Hassana kai ta rik'a girgizama Hajiya Turai , tana zazzare ido kamar wadda tai k'arya asirinta yatonu". Hajiya Turai itama cikin sanyin murya mai cike da fargaba ta ce, "Hassana dan Allah ki auri Habib, duk abinda kike tunani bahaka bane, idan yau Habib ya ji sauk'i shikenan". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana zaki aurai? ". Still Hassana kai ta girgizama Hajiya Turai ".. Shiru Hajiya Turai ta yi, Sannan ta ce, "Hassana nasan k'ila kina tsoran halin Habib ne shiyasa kika k'i yarda da Auran shi, ni nai miki alk'awari Hassana insha Allah babu abinda zai faru, kamar yadda nace miki daga yaji sauk'i shikenan". Shiru Hajiya Turai ta yi sannan ta kamo hanun Hassana ta ce, "Hassana kin yarda dan Allah? ". Hassana kai ta girgizama Hajiya Turai tana zubda hawaye". Hajiya Turai hannu tasa tana gogema Hassana hawayanda ke zuba aidonta, ta ce, "Kishiru kinji my daughter, nasan dama maganar zata zo miki wani iri, amma na baki nan da gobe ki yi tunani dan Allah, kinji?, idan har kika yarda da buk'ata ta auran Habib, nai miki alk'awarin baki duk abinda kike so, ki je kiyi tunani kinji My daughter, idan Allah yasa kin yarda da buk'ata ta gobe nake son ayi komai, saboda shan maganin Habib". Hajiya Turai na sakin hannun Hassana, Hassana ta fita da saurinta". B'angaran su Farida kuwa tare da Hajiya Murja suka dawo gidan Hajiya Turai. Bayan Hajiya Murja ta yi parking a parking space agidan Hajiya Turai. Hajiya Murja kallan Farida ta yi, ta ce, "Farida yanzu taya kike ganin zaki basu wannan maganin na rufe bakinsu da maganar auran nan? ".Farida kamar jira take ta ce, "Wallahi Mommy nima abinda nake tunani kenan, dan bana son asamu kuskure koka d'an". Shiru Hajiya Murja ta yi sannan ta kalli Farida ta ce, "Har yanzu Balaraba kema Hajiya Turai girki? ". "Eh Ita ke yi". Murmushi Hajiya Murja ta yi, ta ce, "Yauwa komai yazo da sauk'i, dan Balaraba nada son kud'i sosai, nasan zata ita yin komai dan kud'i, dan haka da ita za a had'a kai ayi aikin nan". Farida cikin gamsuwa da maganar Mahaifiyarta ta ce, "Wow Mommyna kuma Wallahi haka ne, Balaraba zata iya, amma na Oga Habib d'in fa, dan yanzu yarinyar ta ce bata k'ara shiga kaima Oga Habib abinci ko magani, shinema da lilin da Hajiya ta naimi had'asu aure, shigiya k'ilama tasan Hajiya za tai hakane yasa ta ce haka, tom aiko bata isaba dan ita ba ajin Oga Habib ba ce Wallahi! ". Hajiya Murja kallan Farida ta yi, ta ce, "Yanzu ke babu yadda zaki ma yarinyar ta kaima Habib maganin?, ai wayo zaki mata ta kai mai maganin idan ta kai mai, irin minti biyu haka, sai ita kuma kisan yadda zaki bata tasha, idan tasha sai ki tura ta d'akin da niyyar d'akko miki wani abun, ke koma ita bata shaba indai taba Habib d'in yasha shikenan, inda Malam ya ce indai shi yasa ba dole bane ita sai ta sha". Farida cikin jin dad'i ta rungume Hajiya Murja, ta ce, "Sai Mommyna, aikin ki na kyau". Dariya Hajiya Murja ta yi tace, "Tom ba dole in dage ba, daughter zata gudu tabarni ni kad'ai". Hajiya Murja kallan Farida ta yi ta ce, "Muje Farida mugaisa da Hajiya Turai in tafi gida". Hajiya Turai na zaune a falonta ta yi nisa acikin tunani su Hajiya Murja suka shigo ita da Farida. Hajiya Turai cikin sanyin murya ta amsa sallamar da sukai. Hajiya Murja cikin nuna damuwa ta ce, "Hajiya ai ni fushima nake dake, dan bacin hankalina yak'i kwanciya Allah da bazan zo ba, wai yanzu ace lallura ta samu Habib amma bazaki fad'amin ba, sai jiya da Farida ta je nake ji". Hajiya Turai cikin al'ajabi da mamakin furicin Hajiya Murja, ta ce"Ki yi hak'uri rud'ewa nayi, dan abin ya taba k'wak'walwata sosai"."Wallahi nima bikiji yadda naji ba, da Farida ta kaimin labari jiya, dan bacci gagarata ya yi, tom yaza mu yi sai dai fatan Allah ya bashi lafiya". Da ameen Hajiya Turai ta amsa'". Nan dai Hajiya Murja taita ba Hajiya Turai baki akan kar ta d'ora ma kanta damuwa insha Allah Habib zai ji sauk'i. Ita dai Hajiya Turai da uhmmm kawai ta ke binta". Hajiya Murja ganin Hajiya Turai wani iri ba tai tunanin komai ba, dan aganinta ciwan Habib d'in ne yasa ta ke ma ta haka. Hakan yasa ta tashi taima Hajiya Turai sallama tare da addu'a Allah yaba Habib lafiya. Ita dai Hajiya Turai da ameen ta ke amsa mata". Farida tashi ta yi zata raka mahaifiyarta. Bayan sun fita daga part d'in Hajiya Turai ne. Hajiya Murja ta kalli Farida ta ce, "Yanzu Farida ina zanga Balaraba? ". "Tana site d'in worker's d'in gidan, bari in kirata". Farida zuwa kiran Balaraba ta yi, babu dad'ewa sai gata da Balaraban sun dawo tare". Balaraba cikin girmamawa ta gaida Hajiya Murja. Hajiya Murja kallan Balaraba ta yi, ta ce, "Balaraba wani aiki nake son ki min, zan biyaki kud'i masu yawa, kuma bana son asamu kuskure, zaki iya? ". Balaraba cikin girmamawa ta ce, "Hajiya ai babu abinda zaki sani wanda bazan iyaba, umarninki kawai nake jira". Hajiya Murja muskilin murmushi ta yi, sannan ta ciro kud'i masu yawa taba Balaraba, ta ce, "Gashi wa innan somin tab'ine". Maganin da bokan Hajiya Murja ya basu taba Balaraba, ta ce, "Balaraba a abincin zaki dafa yanzu nake son kisa maganin nan, zaki iya? ". Shiru Balaraba ta yi, sannan ta ce, "Hajiya zan iya, amma tsorona d'aya idan ya kasan ce nakisa ne, saboda bincike zai iya fad'owa kaina". Hajiya Murja cikin b'acin rai ta kalli Balaraba ta ce, "Balaraba kinada hankali kuwa! ,tom bana kisa bane,wani abu na ke nema gun Hajiya Turai". Balaraba cikin yanayin fargaba ta ce, "Hajiya indai bana kisa bane zanyi, amma indai shine bazan iya ba, dan gaskiya ina tsoran tonuwar asiri". Hajiya Murja kallan Balaraba ta yi ta ce, "Balaraba bashi bane, idan kinsan bazaki iyaba kiban abuna, dan Wallahi dan kika b'ata min aiki bazan barki ba". Balaraba jin Hajiya Murja ta kuma jaddada mata bana kisa bane ta ce, "Shikenan Hajiya zan iya wallahi, ya za ai da maganin? ". "A abinci zaki zuba shi". Hajiya Murja sai da tajama Balaraba kunne sosai akan yin wani kuskure, sannan ta tafi". B'angaran Hassana ko tun bayan fitowarta daga part d'in Hajiya Turai, ta ke zaune inda ta ke, ta yi ta gumi damuwa duk ta isheta, dan ita gaskiya baza ta iya auran Habib ba, dan shid'in tasan ba ajin auranta bane, Habib mijin first class girl's ne ba itaba, wadda ya kema kallan k'ask'antarta,dan haka cema Hajiya Turai za tai baza ta iya ba, amma ta yadda zata rik'a bashi abincin da maganin harya warke". Hassana na nan zaune Jummai tazo kusa da ita ta zauna amma Hassana bata jiba. Jimmai hannun Hassana da tai ta gumi ta kamo ta ce, "Hassana tun d'azu da kika dawo kiran Hajiya nalura kike cikin damuwa, haba Hassana meye amfanin amintata da ke, idan har bazaki iya fad'amin damuwarki ba, koda banda abinda zan miki ai na taya ki da addu'a". Hassana d'ago kai ta yi tana kallan Jimmai sannan, ta ce, "Jimmai narasa yadda zanyi, amma ni bazan iya abinda suke so in yiba". Jimmai kallan Hassana ta yi dan bata gane takan zancan ta ba, ta ce, "Meye suke so ki yi? ". Shiru Hassana ta yi, sai zuwa can ta kalli Jimmai ta ce, "Jimmai kinsan Oga Habib tunda ya fara wannan ciwan baya yarda koda Hajiya tashiga gunshi sai dai ni, idan har bani na bashi abinci ba, ko magani tom ba zai shafa, hasalima da kyar ake fiddani duk lokacinda nashiga gurinsa, tom shine fa wai yanzu Hajiya take rok'ona akan in auri Oga Habib kafin yaji sauk'i in zauna dashi in yi jinyar shi".Jimmai cikin mamaki ta ke cewa, "Hassana dan Allah da gaske kike, Hajiya ta yi miki tayin auran Oga Habib? ". Kai Hassna ta d'agama Jimmai. Jimmai cikin rud'ewa da jin maganar ta ke cewa, "Amma dai Hassana kinzo gidan nan asa'a, dama ni, tom Wallahi ina baki shawara karki sake ki yi gangancin cema Hajiya baki yarda ba, haba Hassana wai meke damunki ne, wannan babban arzik'in nakiranki tsiyana na hure miki kunne". Hassana kallan Jimmai ta yi ta ce, "Jimmai baki tunanin ranar da Oga Habib zai bud'e ido yaga ni yake aura, arzik'in kawai kike hanga? ". Shiru Jimmai ta yi, sannan ta ce, "Hassana bafa ke kika naimi haka ba, su suka rok'eki, sannan lakacinda zai warke kamar yadda kike cewa, kingama arzik'i, kinga koma auran yak'are daga nan kingama zama Hajiya. Sanna ko ba haka ba da kunya ki koma ki cema Hajiya baki yarda ba, amma idan zaki iya tom , haba Hassana ke baki da burin komai ne arayuwarki?, wannan fa dama ce Allah ya baki, karki bari wannan damar ta wuce ki". Shiru Hassana ta yi tana tunanin maganganun Jimmai sannan ta kalli Jimmai ta ce, "Jimmai kina ganin ba matsala, bazan sa kaina a damuwa da tashin hankali ba, auran Oga Habib? ". "Hassana babu matsala ki yarda dani". "Shikenan Jimmai na yarda, amma daga Oga Habib yaji sauk'i nagama zama agidan nan baki d'aya ". Jimmai cikin kwantarma Hassana hankali ta ce, "ke dai ki yi addu'a Malam, amaryar Oga Habib". Hassana duka ta kaima Jimmai a baki ta ce, "Allah zaki sa in fasa". Nan dai Jimmai tai ta ba Hassana shawarwari masu kyau ". B'angaran Balaraba maganin da Hajiya Murja ta bata a bakin zaninta ta nannad'e shi, tana d'ora girkin ta d'akko shi ta juye tass kamar yadda su Hajiya Murja suka ce tayi.Tana gama girkin ta sanar da Hajiya ta gama, nan ta kaima Hajiya nata, da duk wani wanda ki ci ana su Hajiya irin su Bilya da Baba Lami". Farida ko tana ganin angama girkin ta tashi da kanta ta je ta samu Hassana, Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana dan Allah abinci Oga Habib zaki kai mai? ".Hassana tom kawai ta ce ma Farida". Farida da kanta ta kai Hassana Falon Hajiya Turai ta d'auki abinci Oga Habib ta nufi part d'in shi". Hassana ta yi nisa sannan Farida ta bi bayanta ta ce, "Hassana ga maganin Oga Habib ki bashi inji haji". Hassana amsa ta yi ta tafi, tana zuwa kai tsaye tashiga. Habib kamar yadda yasaba da saurinsa ya yo kan Hassana yana zuwa yarik'o mata hannu" Hassana sai da tagama ba Habib abincin sannan ta bashi maganin da Farida ta bata ta bashi. Farida da ke lab'e ta window tana ganin Hassana taba Habib maganin wani ihun dad'i ta yi, sannan ta je, ta kuma rufe k'ofar Falon ta baya, yadda koda Hassana ta ce zata gudu ba zata iya ba................... Tofaaaa🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️🙆‍♀️ Idan kin karanta daure ki yi comment sister 🤝 Share &, Comment please 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI(Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 Facebook group : https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Allah ka zaunar da k'asarmu lafiya, Allah kabamu kwanciyar hankali ak'asarmu, Allah ka tsare musulminka aduk inda yake, dan Allah jama mu daure murik'a karanta HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKIL 11 duk sanda muka idar da sallar asuba. A bisaga Allah ya bamu zaman lafiya ak'asarmu. Shafi na 32&33. Farida na rufe k'ofar ta gudu ta bar gurin cikin jin dad'i. Habib ko nashan maganin da Hassana ta bashi baifi da minti goma ba, ya fara jin wani irin yar ajikin shi. Mik'a Habib ya farayi yana kuma damtse hannun Hassana da yake rik'e da shi, yana kuma jawo ta kusa da shi. Ita dai Hassana kallan mamaki tabi Habib da shi dan, idan ya rik'e hannunta shikenan daga haka, bai jajjawota jikinshi kamar yadda ya ke yi yanzu. Hassana kallan Habib ta yi ganin yadda ya ke rintse ido yana kuma damk'e hannunta yana ja wota jikin shi, kamar zai sata kan cinyar shi. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce cikin sanyin muryarta, "Oga Habib baka da Lafiya ne? ". Habib shi dai kallan Hassana kawai ya yi, ita kuma Hassana Sannu tai mai ganin yadda ya ke makyarkyatar sanyi, yana kuma damk'e hannunta. Can Hassana sai dai taji Habib ya fisgota da k'arfi ta fad'a kan shi, dan sai da sukai karo yana yin yadda ya fusgota d'in. Kafin Hassana ta yi yin k'urin yunk'urawa ta tashi daga jikin Habib sai ta ji, ya finciko hijab d'in jikinta yana k'ok'arin cirewa". Hassana rik'e hijab d'in ta tayi sosai tana kallan Habib dake ciku-cikun cire mata hijab. Hassana ganin yau Habib d'in, wani iri bakamar yadda ta saba ganin shiba, ga shi wai har yana ciku-cikun cire hijab d'in jikinta. Hassana dak'arfi ta fusge hannunta a hannun Habib, sannan ta juya da saurinta da niyyar fita. Sai dai ina kafin ta kai bakin k'ofar Habib har ya risketa, yana juwa ya rik'ota ta baya, yana rik'eta kuma Allah ya bashi sa'a ya fisge hijab d'inta" Kafin Hassana ta gama tunanin lafiya sai dai taji Habib na k'okarin yaga rigar da ke jikinta. Nan fa kusan damme ya b'arke tsakanin su. Habib k'okarin cire rigar dake jikin Hassana ya ke, Hassana kuma tak'i bashi damar haka. Da yake zani ne single ajikinta, hakan yasa Habib yana jan shi ya kwance. Hassana k'ara ta saki ganin Habib ya kwance zanin jikinta. Hassana mak'alk'ale Habib ta yi sosai tak'i bashi dama. Habib ko da dama bacikin hankalinshi ya ke ba, kuma ank'ara birgera k'wak'walwar, hakan yasa ya zamarma Hassana mahaukacin asali. Habib da k'afin tsiya ya yi wurgi da Hassana kan caution, sannan ya yi saurin binta, kan caution d'in. Hassana ko kafin Habib ya zo tayi sauri ta tashi zata gudu. Habib garin ya jawo Hassana yana jawota ya jawo rigar jikinta ta yage . yarage daga Hassana sai brazier da pant. Habib cikin fitar hayyaci ya cire komai da ke jikin shi ya tsaya haihuwar uwarci". Hassana cikin rud'ewa ta fara ihu tana kiran Hajiya Turai , da Oga Bilya. Duk yadda Habib zai yi ya kwantar da Hassana ya kasa, dan firgitar da Hassana ta yi sai hakan yasa mata k'arfi. Habib ko cikin rashin sanin meye ya zai aikata, meye ya ke yi bai sani ba. Ya damk'i breast d'in Hassana. K'ara Hassana ta yi jin azabar yadda ya damk'i breast d'in ta. Cup d'in da ke kusa da Hassana na maganin da Farida ta bata ta ba Habib, ta d'akko ta buga ma Habib shi tun k'arfinta akai". Habib jin azaba ya sakin Hassana yana tab'a gurin da Hassana ta buga mai cup d'in". Hassana ko Habib na sakinta ta tashi ta ruga da gudu. Tana rugawa Habib ya bita. Kafin ya kamata Allah ya bata sa'a tab'ud'e toilet d'in bedroom d'in Habib ta shige ta rufe tana nishin wahala". Habib ko bakin k'ofar ya tsaya yana jijjiya k'ofar kamar zai b'alleta". Hassana sosai ta rud'e dan yadda ta ji Habib na jijjigar k'ofar gani ta ke zai b'alleta. Habib ko gajiya ya yi da jijjiga k'ofar ya zauna jikin k'ofar ya jingina da ita". Hassana tana jiyo nishin Habib daga toilet d'in. Hassana shiru ta yi da kukan da take yi tanaaa sauraron nishin Habib tare da tunanin me ya sa mai haka. Wani tunani yazoma Hassana, dan tabbas idan bazata manta ba, itama kusan shigan haka ta yi lokacinda Farida ta bata magani ta sha ta ce mata inji Hajiya Turai. Tom wannan wana irin magani ne haka?, kuma meyasa nima da nasha naji haka?, sannan meyasa Hajiya bata tab'a ban da hannunta ba sai dai ta aiko Aunty Farida ta kawo min?, shiru Hassana ta yi, tana nazarin tambayoyin da tai ma kanta, tana naiman amsarsu. "Kai gaskiya wannan maganin akwai alamar tambaya atare da shi,tom amma kuma Aunty Farida ai bazata aikata abinda zai cutar da Oga Habib ba, ko da yake ai bashi zai cutar ba ni zai cutar, dan idan har tunanina haka ne da ace Allah yaba Oga Habib sa'a akaina tom da Fyad'e ya ke k'ok'arin yi min, kai gaskiya ban yarda da Aunty Farida ba, tom wai meyasa ma rannan ta maran dan nace mata banba Oga Habib maganin da taban in bashi ba?, tom kuma nima ai aranarne nashiga irin kusan halinda Oga Habib yashiga yau, dan idan bazan mantaba nima ranar haka naima kaina tsirara, kai gaskiya ban yarda da Aunty Farida ba, tom ni yanzu wazan fad'amawa abinda ke faruwa ya taimakan da amsar tambayoyina?. Gaskiya bazan iya fad'ama Hajiya ba, kuma bazan iya fad'ama Oga Bilya ba,inajin Jimmai zan fad'amawa dan nayarda da Jimmai tana ban shawarwari masu kyau, amma gaskiya ban yarda da maganin nan da Aunty Farida ta banba". Hassana ta dad'e a toilet d'in Habib tana tunane-tunananta. Tun tana jiyo nishin Habib har taji shiru bajin nishin shi. Hassana ta dad'e sosai a toilet d'in, dan har sai taji kiran sallar azahar sannan ta lallab'a ta bud'e k'ofar a hankali ta lek'o kanta. Kwance Hassana taga Habib akasa kusa da toilet d'in yana bacci.Hassana sosai hankalinta ya tashi ganin yadda taga Habib, dan ita sai yanzu ta kallai, sauri ta yi ta kauda kanta tana jinta duk wani iri bad'i. Hassana fita zata yi daga bedroom d'in Habib sai kuma taji tsoran Bilya yazo yaga Habib a haka, gudin zargi Hassana badan ta so ba, ta je falon ta yi sauri ta jira hijab d'inta ta d'aura zaninta, rigar kuma ta riga ta yage sosai bazata sawuba, hakan yasa ta k'udin-dine rigar ta tusata a kayan Habib, sannan ta d'akko kayan Habib tana rinrintse ido ta samai, tana samai tana duk addu'ar da tazo bakinta dan tana tsoran karya tashi. Hassana nagama sama Habib kayan shi ta yi sauri ta fita daga d'akin Habib d'in". Hassana da sauri-sauri kamar munafuka ta koma site d'in su na 'yan aiki. Hassana na zuwa taga Jimmai sai aikin bama flower's d'in site d'in su ruwa ta ke, Hassana inda Jimmai ta ke ta k'arasa ta ce, "Sannu da aiki". Murmushi Jimmai ta yi ta ce, "Yauwa Hassana aike ke aiki, ke da ke kula da Ogan mu". Hassana hannun Jimmai ta kamo ta ce, "Jimmai dan Allah zoki ci wata magana, Wallahi abinda ya daman, narasa wanda zan gayamawa". Jimmai jan hannun Hassana ta yi suka samu guri suka zauna, Jimmai kallan Hassana ta yi da damuwa dan ita har ga Allah bata son damuwar Hassana, Jimmai cikin sanyin murya ta ce, "Hassana karkiji komai kinji kifad'amin duk da muwarki, ni kuma zan baki shawara irin wanda zan ba k'anwata, ko kuma kaina". Hassana kallan Jimmai ta yi ta ce, "Jimmai ya Aunty Farida su ke da Oga Habib ne? ". Shiru Jimmai ta yi jin tambayar da Hassana tai mata, sannan ta ce, "Kin san Hajiya Murja ai ko?, friend d'in Hajiyar Oga Habib, tom ita ce ta haifi Aunty Farida, Farida 'yar k'awar Hajiya Turai ce". Jimmai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana meyasa ki kai min wannan tambayar? ". Shiru Hassana ta yi, sannan zuwa can ta ce, " Sister Jimmai Shekaran jiya Aunty Farida ta kawomin wani magani ta ce, wai inji Hajiyar Oga Habib, ta ce insha in ba Oga Habib shima yasa, nayi mamaki sosai jin wai insha, tom amma da naima Aunty Farida magana sai ta balbaleni da fad'a wai ita bata da hankaline da bani aka ce taba ba zata ban, wai suma duk sun sha dan haka nima insha. Haka na d'auki maganin nasha". Shiru Hassana ta yi sannan ta ci gaba da cewa, "Sister Jimmai aranar d'akin Oga Habib na kwana, dan ina shan maganin nafita daga hayyacina, wani irin abu narik'a ji ajikina, haka na tashi naganni tsirara haihuwar uwata, muna kwance tare da Oga Habib guri d'aya . Wannan shine dalilinma da yasa kikaji nace bazan kuma kaima Oga Habib abinci ba, ko magani. Tom bayan nabar part d'in Oga Habib na dawo nan sai ga Aunty Farida tazo tana tambayata wai me Oga Habib ya yi min, na bata amsa da bai min komai ba, wai k'arya nake in fad'a mata dan tasan komai wai ai ta ganni ina kuka Ina fad'ama Oga Bilya, nan dai nace mata ta tambayi Oga Bilya ni bance mai ko mai ba, na dai ce mai bazan k'ara ba Oga Habib abinci ba, ko magani. Shine ta ke tambayata wai na ba Oga Habib maganin da taban in bashi. Wallahi sister Jimmai bikiji ba marinda tai min da nace mata ban bashi ba na manta. Tom jiya ba tazo kirana ba? ". Kai Jimmai ta d'agama Hassana. Hassana ko ta ci gaba da cewa, "Tom abinci ta rok'an in kaima Oga Habib, bayan na kaimai abincine ta biyoni da wani magani wai in ba Oga Habib inji Hajiya, ni kuma na amsa bayan Oga Habib ya gama jin abinci na bashi. Wallahi sister Jimmai tunda naba Oga Habib maganin ya fita daga hayyacinsa, ya kamani ya rik'e". Hassana d'agama Jimmai hijab d'inta ta yi, ta ce, "kin gani sister Jimmai harta rigata sai da ya yagata". Jimmai cikin tashin hankali ta ke, tambayar Hassana, ta ce, "Hassana baidai miki komai ba ko? ". "Eh sister Jimmai bai min komai ba, amma Allah ne kawai ya k'watan ahannun shi, amma niya yayi ya yi min Fyad'e Allah ya amsheni daga wajan shi". "Tom Alhamdulillah". Cewar Jimmai, sannan ta yi shiru tana tunanin me yasa Farida ta aikata haka. Jimmai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana ke a tunaninki me yasa Farida ta ai kata haka? ". "Tom nima bansani ba, nayi nazari sosai na kasa ganowa". Shiru Jimmai ta yi sannan ta ce, "Tom ni dai nasan Aunty Farida na son Oga Habib sosai, dan ance saboda shinema ta ke zuwa gidannan. Tom amma kuma ai ba zata so wani abu ya faru irin haka ba, tsakaninki da Oga Habib ba, dan Aunty Farida na son Oga Habib sosai, saboda sun tab'a fad'a da wata itama yarinyar friend d'in Hajiyar Oga Habib ce, akan Oga Habib". Shiru Jimmai ta yi, Sannan ta ce, "Tom koda gaske ta ke Hajiyar ce ta aikota ta kawo maganin, dan gaskiya Aunty Farida ba za tai abinda zai sa Oga Habib ya kusance kiba, dan tana kishi akan shi sosai gaskiya". "Tom nima haka dai nake gani". Cewar Hassana". Jimmai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana kin san me? ". Kai Hassana ta girgizama Jimmai. Jimmai ta ci gaba da cewa, " Idan har Aunty Farida ta zo ta tambayeki kin ba Oga Habib maganin, ki ce mata Eh, tom daga nan duk tambayar da tai miki, shikenan magana ta k'are zargi ya hau kanta". "Tom shikenan, Sister Jimmai sai in tazo d'in". Jimmai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana yaune fa zaki fad'ama Hajiyar Oga Habib sak'onta na amintarki, dan haka ki tashi yanzu kije ki sanar da ita kin abince,Allah bashi kamar yadda ta ce duk abinda kike so za tai mik, ki ce mata kina son jali ke".Shiru Hassana ta yi, sannan ta ce, "Sister Jimmai Allah zan amsa ma Hajiya ne kawai, amma zuciyata ta k'i aminta da maganar har yanzu". "Karkiji komai Hassana dan k'ilama har ayi auran agama Oga Habib ba zai sani ba, inma shikike tsoro, dan itama Hajiya ta san halinshi sosai bazata bari ya sanda maganar ba, dan haka kije ki fad'ama Hajiya kin amince, dan kar taga kamar kina jamata raine". Hassana ta shi ta yi tanufi part d'in Hajiyar Oga Habib, da tarin fargaba aranta, danma hankalinta nad'an kwanciya inda ance Oga Habib ba zai san damagar auran ba, daga ya warke shikenan. Hassana cikin sanyin muryarta ta yi sallama ta shiga falon Hajiyar Oga Habib ". Hajiya Turai na zaune ta ji sallamar Hassana, d'agowa tai tana kallan Hassana. Hassana cikin girmamawa ta gaida Hajiya Turai, sannan ta ce, "Hajiya maganar da mu kai jiya, na amince........... Tofa ko Hajiyar Oga Habib zata amince???,🤐🤐🤐 Koya Farida zata yi, idan ta gano gaskiyar Habib bai kusanci Hassana ba??? 🤐🤐🤐🤐 Idan kin karanta daure ki yi comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI(Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 Facebook group : https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Ina mai farin cikin taya k'asata Nigeria murnar cika shekara 61.Allah ka k'aro mana zaman lafiya, da kwanciyar hankali mai d'aurewa ak'asarmu👏👏👏. *MUTUWA ZATA IYA RISKARMU DAGA YANZU ZUWA KOWANNE LOKACI KO A KUSA KO A NESA ALLAH SHINE MAI YANZU YANZU, ALLAH KASA MU CIKA DA IMANI. Shafi na 34&35. Hassana cikin girmamawa ta gaida Hajiya Turai, sannan ta ce, "Hajiya maganar da mu ka yi jiya na amince". Hajiya Turai cikin jin dad'i ta rungume Hassana, ta ce, "Nagode sosai my daughter, Allah ya yi miki albarka, me kika so in biyaki da shi". Shiru Hassana ta yi, dan ita harga Allah dan Allah ta yi, badan Hajiya Turai ta biyata ba". Hajiya Turai jin Hassana ta yi shiru, kan Hassana ta d'ago dake duk'e ak'asa ta ce, "My daughter karkiji komai kinji, fad'amin da me kike so in biyaki da shi". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "A'a Hajiya, ba komai dan Allah nayi miki". Hajiya Turai k'ara rungume Hassana ta yi tana mata duk addu'ar da tazo bakinta, ta ce, "Nagode miki my daughter Allah ya saka miki da mafificin alkairi, yanzu zan kira Bilya in mai magana idan anshiga sallar azahar sai a d'aura auran lokacin". Hassana d'agowa ta yi tana kallan Hajiya Turai gabanta na fad'uwa ta ce, "Uhm Hajiya ba kince auran sirri za aiba?". "Eh My daughter, ko yanzuma ai auran sirrine, inda kinga ba friend's d'in Habib da zai san da maganar auran kod'aya, sannan nima babu 'yan'uwana da suka san maganar,dan haka karkiji komai, indai Habib ne ma bazai san da maganar auran ba, inda nalura tsoran shi kike ji". Hajiya Turai ta idasa maganar tana murmushi,dan sosai ta ji tana farinciki da amincewar da Hassana da ta yi". HajiyaTurai kallan Hassana, ta yi, ta ce, "Shikenan my daughter nagode, kije anjima zan ne me ki". Hassana tashi ta yi ta tafi". Hassana na fita daga falon Hajiya Turai suka ci karo da Farida. Farida da sauri ta kamo hannun Hassana ta ce, "Yauwa dama ke nake naima , naje nai manki site d'in ku banganki ba". Farida jan hannun Hassana ta yi suka matsa can gefe, sannan ta kalli Hassana ta ce, "Lafiya jiya bayan na baki maganin da Mommy ta ban tace kiba Oga Habib naji k'ararki? ". Hassana shiru ta yi tana kallan Farida, tabbas zarginsu ya tabbata". Farida ko cikin k'osawa da Hassana ta bata amsa, ta bugama Hassana tsawa ta ce,"Ke bada ke nake ba!, zaki tsaya kallona, nace lafiya naji kinyi k'ara ? ". Sana cikin son taka ma Farida ta ce, "Auntu Farida k'ara kuma?, anya kuwa ni ce". Gaban Farida ne ya fad'i, amma sai ta daure ta ce, "Ke bansan shirme,angaya miki banji bane, me yasa me ki kikai k'ara alokacin?, ko Oga Habib ne ya yi miki wani abun? ". Hassana kallan Farida ta yi, sannan ta ce, "Eh Aunty Farida na tuna, Oga Habib ya yi min wani abu". Farida cikin sauri da k'osawa, ta ce, "Me ya yi miki? ". "Aunty Farida glass Cup ya bugamin a kai". Farida cikin jin haushin abinda Hassana ta ce, ta ce, "Sannu, bayan nan fa be miki komai ba, danni naji k'ararki sosai, kina kiran Mommy da Bilya, dan haka fad'amin gaskiya ". Hassana cikin danne mamakin Farida da ta ke yi, ta ce, "Aunty Farida Allah bai min komai ba, k'arar da kikaji nayi zafin Cup d'in ne yasani k'ara, amma babu wani abu". Shiru Farida ta yi tana nazarin maganganun Hassana azuciyarta, sannan ta ce, "Na bani kaddai ace Oga Habib bai kusanci yarinyar nan ba! ". Farida cikin rud'ewa ta kalli Hassana ta ce, "Ke kinko ba Oga Habib maganin da nace miki Mommy ta ce abashi? ". "Eh Aunty Farida na bashi". "Kinfa bashi kika ce? ". Farida ta tambayi Hassana. "Eh Wallahi Aunty Farida na bashi".Farida cikin rashinsanin me ta ce, ta ce, "Amma kuma kika ce Oga Habib me biki komai ba". Hassana cikin mamakin Farida, da al'ajabin dama da akwai abinda ta k'ula kenan, ta ce, "Aunty Farida na ce miki ya buga min Cup mana". Wata irin tsawa Farida ta bugama Hassana, ta ce, "Dan Uwarki abinda na tambayeki kenan!, tom nufina Oga Habib bai kusanceki ba? ". Hassana cikin tashin hankali da al'ajabi ta ke kallan Farida, sannan ta ce, "Subhalallah Aunty Farida wannan kuma wata irin magana ce? ". Shiru Farida ta yi dan sai alokacin ta dawo hayyacinta ta tuna da irin tab'argazar maganar da tayi. Hakan yasa Farida cikin kame-kame, ta ce, "Eh dama da naji kinyi k'arane nayi tunanin haka, amma dai ai ba haka bane, bai kusance kiba ko? ". Hassana kamar zata yi kuka ta kalli Farida ta ce, "Eh hakane". Hassana na bata amsa ta juya zata tafi, dan sosai Farida ta b'ata mata rai, wato dama burinta kenan Oga Habib ya lallatamin tarbiya". Farida ko cikin zafi ta jawo Hassana ta ce, "K'arya kike munafuka bakiba shi maganin ba, kuma Wallahi bazaki barnan ba sai naji dalilin da yasa baki bashi maganin ba yasha! ". Hassana da mamaki ta ke kallam Farida, sannan cikin sanyin muryarta, ta ce, "Aunty Farida ta ya kika san ban shi maganin ba, bacin na tabbatar miki da naba shi? ". Farida shiru ta yi sannan ta saki Hassana, gudin kar Hassana ta zargi wani abu". Hassana harta tafi Farida ta kuma kiranta,ta ce, "Me kikaje yi part d'in Mommy ". "Maganin Oga Habib ta tambayan yasha". Hassana ta fad'ama Farida hakane, dan ita bata son Farida ta ji auranta da Oga Habib inda ance mata Farida na son shi". Hassana tana tafiya tana mamakin dalilin Farida na ba Habib magani ya kusanceta, tom meyasa za tai haka?, inda dai ita son shi take, ai yakamata ace tana kishinshi, kai gaskiya k'ila dai tana da mugunnufi ne akaina, tom amma kuma shi Oga Habib d'in fa?, kuma ni mai nai mata?". Nan dai Hassana ta yi shiru dan babu mai amsa mata tambayoyinta". B'angaran Hajiya Turai ko, Hassana na fita ta kira Bilya awaya. Bilya cikin mintina kad'an yazo". Hajiya Turai kallan Bilya ta yi da murnarta ta ce, "Bilya dama yarinyar nan ce da kanta tazo ta ce min ta amince da maganar had'ata aure da Habib da Mukayi, tun shine dama nakiraka dan yau nake son d'aura auran idan kunfito sallar azahar ". Bilya kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Hajiya aure kuma, Yaushe akai maganar, ni dai gaskiya bansan da wata magana ba". Hajiya Turai da mamaki ta kalli Bilya ta ce, "Bilya maganar da mukayi jiya-jiyan nan amma kace min baka san da magana ba, bari in kira Baba Lami ta tunama". Hajiya Turai Baba Lami ta kira". Bayan Baba Lami ta zo ne, Hajiya Turai ta kalli Baba Lami ta ce, "Baba dama maganar da muka yi da ku jiya na had'a Hassana da Habib aure, tom shine yanzu nakira Bilya Ina mai maganar dan yau nake son ad'aura auran shine ya ke cemin wai shi bai sanda maganar ba, shine nakiraki ki tunamai". Baba Lami ma kallan Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Hajiya ban fahimci maganarki ba, aure kuma,bangane ba, kimin bayani dama zaki had'a Oga Habib aure ne da.. .". Hajiya Turai cikin b'acin rai ta ce, "Baba Lami bana son shirme, taya munyi magana daku yanzu kozo ku nuna min basu san magana ba, bacin ke cema kika kawo shawarar amma yau zaki nuna min baki sanda maganar ba, idan kuna ganin kamar cutar yarinyar mutane zanyi ai gara kufad'amin bawai ku nunamin baku san da magana ba". Baba Lami kallan Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Wallahi Hajiya da gaske nake bansan da maganar nan ba, sai dai ko Bilya k'ila da shi kuka yi". Bilya bud'e baki ya yi zai magana Hajiya Turai ta d'aga mai hannu ta ce, "Naji ya isa, ku tashi kufita kuban guri! ". Hajiya Turai ta idasa maganar cikin fad'a, dan ita aganinta wannan raini ne, taya zasu yi magana, yanzu sununa mata basu san anyiba". Bayan su Bilya sun fita Hajiya Turai tunani ta fara, "Tom ko dai su Bilya basa san aurane yasa suka had'a kai da Baba Lami su kai min haka, tom ni dai Allah kasani, banda yadda zanyi, banda wanda zai kulamin da Habib, inda baya yarda da kowa, dan haka Wallahi in da har yarinyar nan ta furta da bakinta ta amince, Manager zan kira in mai magana yashigarmin gaba ad'aura auran, yau-yau d'innan. Hajiya Turai kiran manager ta yi awaya ta ce tana nai manshi dan Allah yazo yanzu". To abinda ya faru, tunda Habib ya fara ciwo tashin hankali yasa Hajiya Turai bata iya cin abinci, sai dai abu mai ruwa-ruwa, shiyasa ko abincin da Balaraba ta girka mai magani Hajiya Turai bata ciba, tea ta sha,shiyasa abin ita bai yi aiki akanta ba. Wannan kenan ". B'angaran Farida kuwa, Hassana na tafiya,waya ta d'akko ta kira Mahaifiyarta. Hajiya Murja na d'auka,Farida ta fasa kuka, ta ce, "Mommy nashiga uku, yarinyar nan bata bashi maganin ba, dan Wallahi Mommy be kusanceta ba". Daga b'angaran Hajiya Murja, shiru ta yi sannan ta ce, "Tom maganar auran fa, kinji sun k'ara magana". "A'a banji ba". "Tom shikenan ki zo yanzu sai mu koma gurin Malam, muji ya Akai haka ta faru, amma dan Allah Farida kibar kuka, wai bani nai miki alk'awarin auran nan baza ayi shiba, kumama kince baki ji sunsake tada maganar ba, tom duk da hakama babarin maganar zamuyiba, kizo yanzu ki saman mu tafi gurin Malam". Farida mayafinta kawai ta d'akkko takama hanyar tafiya wajan Mahaifiyarta. Kasan cewar banisa tsakaninsu sosai, hakan yasa cikin lokaci Farida ta isa.Dama Hajiya Murja ta shirya Farida kawai ta ke jira, hakan yasa Farida nazuwa, suka tafi". Hajiya Murja da Farida zaune a gaban Malam mai biyan buk'ata dole. Hajiya Murja bayan ta gaida Malam boka, cikin girmamawa ta ce, "Tom Malam mai biyan buk'ata dole, yarinyar nan fa, munajin haryanzu tak'i ba yaron maganin, ga guri sai k'ara k'urewa ya ke, dan Allah nidai atai makan, ayi wani abu malam". Hajiya Murja ta idasa maganar cikin rok'o". Malam mai biyan buk'ata dole, wani k'ok'o ya d'akko, sannan ya kalli Hajiya Murja ya ce, "zoki gani da idonki Hajiya". Hajiya Murja da Farida da sauri suka kango kansu dan ganin abinda ya ke nuna masu". Cikin al'ajabi Farida da Hajiya Murja suke kallan k'ok'an. Hassana ce rik'e da maganin da ta ba Habib. Ata kaice dai haka su Farida sukaga abinda ya faru tsakanin Hassana da Habib bayan ta bashi maganin, haka suka kallah kamar, T, V, ". Farida cikin takaici, ta ce, "Shegiya wato toilet dama ta shiga ta b'oye, amma yanzu malam ya za ai, kuma ya maganar auran da suke so su had'a?, dan munriga mun basu maganin sunci, dan wanda mukaba maganin ta zuba ta tabbatarmin ta zuba". K'ok'an da ya nuna masu abinda ya faru tsakanin Hassana da Habib, shi ya k'ara d'akkowa, ya ce, "Zuku gani da idonku abinda ya faru". Farida da Hajiya Murja lek'a k'ok'annan suka k'arayi, sai ga foton Balaraba ya bayyana lokacinda ta ke zuba maganin a abincin. Daga nan kuma sai lokacinda ta rarraba abincin ta kaima Baba Lami da Bilya, sai kuma ga wani ta d'akko ta nufi site d'in Hajiya Turai. Balaraba na zuwa cikin girmamawa ta ajema Hajiya Turai abincinta. Balaraba har ta juya zata tafi Hajiya Turai ta kirata ta ce, "Balaraba zoki d'auki abincin nan bana iya cin komai yanzu, garama abu mai ruwa, nakan iya daurewa insha".sai ga Balaraba annuno ta d'auki abincin ta fita da shi. Daga nan Malam mai biyan buk'ata dole ya kauda k'ok'an. Kallan Farida ya yi, ya ce, "Tom kinji abinda ya faru, ita Wanda ke da ruwa da tsaki a maganar bataci maganin ba. Yanzu su wa'inda sukaci maganin kuzo ku gani". K'ok'an ya k'ara kanga musu. Sai ga Hajiya Turai da Bilya lokacinda ta ke mai maganar auran Hassana da Habib , ya nuna shi kwata-kwata bai sanda maganar ba, suna ganin lokacinda Hajiya Turai ta tashi ranta b'ace ta kira Baba Lami, tana mai-mai ta mata maganar auran, nan itama ta nuna ma ta bata san da maganar ba. Daga nan Malam mai biyan buk'ata dole, ya kauda k'ok'an, ya ce, "Tom Hajiya kunga abinda ya faru, wato ita Uwar yaron da kusan dan ita akai, bataci abincin ba, kuma yanzu haka ta kira wanda zai shigar mata gaba ad'aura auran". Farida cikin tashin hankali ta kalli Malam mai biyan buk'ata dole ta ce, ", Malam dan Allah ko me kake so zanma Wallahi, dan Allah kada katar da auran nan, kada ya yuwu, ka dawo da shi kaina, dan Allah ". "Karki damu yarinya koda ma ace auran ya yi wu, tom nai miki alk'awari babu inda auran zai je, yanzu ga wannan, ki yi k'ok'ari ki zuba shi ainda Mahaifiyar yaron zata tsallaka, Indai hakan ta faru, shikenan kar kuji komai, amma fa sai kunyi sauri, dan ana son azuba abunne kafin ta yi magana da wanda ta yi magana da shi awaya". Farida kallan Malam mai biyan buk'ata dole ta yi, cikin damuwa ta ce, "Malam idan ta riga ta yi magana da shi shikenan ko mun zuba mata ta k'etara ba zai yiba? ". "Eh hakane, ba zai yiba". Shiru Farida ta yi, sannan ta ce, "Tom gaskiya indai hakane Malam ba zanyi amfani da maganinnan ba, dan Allah Malam kai min wanda daga anyine kawai magana ta k'are". Yadad'e yana zane-zane ak'asa, sannan ya ce, "kina son aiki d'aya daga shi shikenan? ". Kai Farida ta d'agamai. Ya ce, "Hakan zai yuwu amma fa sai kinyi hak'uri anyi auran yarinyar da Yaron, dan ta hakane kad'ai zamu samu biyan buk'ata, dole sai yaron ya kusanci yarinyar, tom kinga idan akai auran ai zasu kasance tare, tom alokacinne ke kuma zaki basu maganin". Ya mik'ama Farida maganin, ya ce, "Ki yi hak'uri za ayi aure amma auran ko sati ba zai yi ba, dan dama maganin zaifi tasiri idan yarinyar tana kusanci da shi sosai. Yanzu ki yi k'ok'ari ki basu maganin abinci ko abinsha, ki kwantar da hankalinki ni Malma mai biyan buk'ata dole nai miki alk'awari sai naraba tsakanin Yarinyar nan da yaron, ke kuma aure da shi babu fashi". Farida godiya taima Malam mai biyan buk'ata dole , sannan suka tashi suka tafi jikin Farida ba wani k'wari dan bata so haka ba, taso ace kar a d'aura auran nan kwata-kwata amma yaza ta yi inda Malam ya ce ta yi hak'uri ta bari ayi, aikinsu zaifi ci tahaka". Haka su Farida suka tafi bama mai kowa magana tsakaninta da Hajiya Murja, kowa da tunanin da ya ke yi". Can ko b'angaran Hajiya Turai, tana zaune ta ji sallamar manager. Bayan sun gaisane, Hajiya Turai ta kalli manager ta ce, "Manager kasan Habib tunda ya fara rashin lafiyar nan, baya yadda da kowa sai Hassana da ke aiki wajanku, tom shine na yanke shawarar had'asu aure, tana bashi magani da kula dashi kafin yaji sauk'i, shine nakiraka dan Allah ka zamarma Hassana waliyi zanma musa magana shi kuma sai ya zama waliyin Habib". Manager kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Kai Hajiya amma hakan ya yi sosai, amma bakya tsoran ranar da M, d, sai ji sauk'i yaga Hassana a matsayin matar shi? ". "Eh nasan wannan, dama daga yaji sauk'i shikenan zan warware abun cikin sauk'i, insha Allah badamuwa shiyasama nake son auran yazamana nasirri". Hajiya Turai Baba Lami tasa ta kira mata Hassana. Bayan Hassana tazo ne, Hajiya Turai ta d'akko kud'i kimanin dubu d'ari, ta mik'ama Hassana , ta ce, "My daughter amsa". Hassana amsa ta yi, bayan Hassana ta amsa ne, Hajiya Turai ta kalli Hassana ta ce, "My daughter wannan sadakinki ne, kiba Manager su, shi ne waliyinki". Hassana gabanta ne yafara fad'uwa, cikin rawar hannu ta mik'ama manager sadakin. Hajiya Turai kallan manager ta yi, ta ce, "shikenan maganar zaka iya tafiya, dan Allah daga kunshiga sallah nake son ad'aura auran, kaga yanzu 12:39pm, yanzu za a kira Sallah, dan Allah ka hanzarta ".. Manager tashi ya yi ya tafi yana mamakin had'in nan da Hajiya zata yi". Hajiya ko kallan Hassana ta yi, ta ce, "My daughter kije kiyi duk wani shiri da zaki yi, anjima zan ne me ki". Hassana tashi ta yi ta tafi tana mai jinta wata iri kamar mara lafiya". B'angaran manager ko ana idar da Sallar azahar dama ya yi ma Liman bayani. Ana idarwa aka d'aura auran Hassana da Habib, abisa saki dubu d'ari. Inda manager ya zamana waliyin Hassana , Liman d'in masallacin kuma ya zama waliyin Habib, dan sun jira musa baizo ba". Bayan and'aura auran ne manager ya taho tan sanar da Hajiya Turai an d'aura aure........... Idan kin karanta daure ki yi Comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Gaisuwar ban girma gareki sister Hafsat Yahaya Bakori, Alkairin Allah ya isarmiki aduk inda kike, rashin network ya hanani jin muryarki, nayi missing d'inki da kyau Wallahi 😭😭😭😭. *ISTIGHFARI TANA SANYA NUTSUWA A ZUCIYA TANA KAWO BIYAN BUKATU WAJEN UBANGIJI UWA UBA KUMA ISTIGHFARI TANA BADA TICKET NA ALJANNA DIRECT😭* Shafi na 36&37. Hajiya Turai na zaune a falo, Manager ya yi sallama ya shigo.Hajiya Turai amsa Sallamar manager ta yi, sannan ta ce, "Bismillah manager ka zauna mana! ". Bayan manager ya zauna ne, ya kallai Hajiya Turai cikin nuna jin dad'insa ya ce, "Hajiya an d'aura auran". Hajiya Turai hawaye cike da idonta ta kalli manager ta ce, "Nagode manager". Can kuma sai kuka, manager cikin damuwa da ganin Hajiya Turai na kuka, cikin sanyin murya ya ce, "Hajiya dan Allah ki yi hak'uri, nasan maganar auran nan ce tasaki kuka, tom ya za'ayi haka Allah ya hukunta, addu'ar zakima m, d, Allah ya bashi lafiya". Hajiya Turai cikin muryar kuka ta ce, " Manager Wallahi ayanzu ba ciwan Habib nakema kuka ba, yanayin rayuwa nakema kuka, nagode maka manager Allah ya sakamama da alkairi nagode ". Manager sai da ya kwantarma Hajiya Turai da hankali sosai sannan ya tafi". Hajiya Turai na zaune har kusan magriba amma shiru Hassana bata shigoba. Hajiya Turai jin shirun ya yi yawa aikawata yi aka kira mata Hassana". Hassana ko wunin yau haka take yinshi duk bata jin dad'in jikinta, daga ta tuno wai za'a d'aura mata aure yau, gabanta sosai yake fad'uwa bakamar in ta tuno wanda za'a had'ata auran dashi ba, har wani d'an zazzab'i ke jin ya rufe ta. Hassana na zaune ita kad'ai ta yi ta gumi, d'aya daga cikin worker's d'in gidan ta zo kiranta. Hassana sai da gabanta ya fad'i jin Hajiya Turai nakiranta. Tashi ta yi kamar mara lafiya tabi bayan mai kirannata". Hajiya Turai na zaune,Hassana ta yi sallama cikin sanyin muryarta mai tattare da rauni. Hassana guri ta samu d'annesa da Hajiya Turai ta zauna, sannan cikin girmama ta gaida Hajiya Turai, ta ce, "Hajiya gani". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi da kyau, sannan ta ce, "Zoki zauna kusa dani, kinji my daughter". Hassana tashi ta yi ta zauna inda Hajiya Turai ta nuna mata". Hajiya Turai kud'in dake hannunta ta sama Hassana su a hannu, ta ce, "My daughter kirik'e da kyau, kud'in sadakinki ne ki yi wani abun da su". Gaban Hassana har wani fat-fat, ya ke saboda fad'uwa. Ita kuma Hajiya Turai ta ci gaba da cewa"My daughter d'azu da Sallar azahar aka d'aura auranki da Habib". Shiru Hajiya Turai ta yi nad'an wani lakaci, sannan ta ci gaba da cewa, "My daughter dan Allah karki sama kanki damuwa kod'aya akan auran nan, Kamar yadda na fad'amiki indai Habib kikeji tom ki saki ranki, dan bazaima sanda maganar auran ba, kamar yadda na yi shi bai saniba, haka zan warware shi bai sani ba, dan Allah daughter ki saki ranki, babu abinda zai faru insha Allah ". Hassana goge hawanda ke zubar mata ta yi, sannan ta kalli Hajiya Turai ta ce, "Babu komai Hajiya, insha Allah babu damuwar da zansa maraina". "Yauwa daughterna, amma daga yau karki kuma cemin Hajiya, kirik'a cemin Mommy kinji?".kai Hassana ta d'agama Hajiya Turai ". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "daughter daga yau zaki koma site d'in Habib da kwana, saboda rubutunda aka bashi, kinga ya kamata afara bashi rubutun, yanzu kije ki d'akko komai naki dake site d'in ku ki kai sie d'in Habib ki aje". Hassana da tom ta amsa ma Hajiya Turai, sannan ta tashi ta fita zuwa b'angaran su". Hassana na zuwa ta iske Jimmai tana alwallar magriba, Hassana kud'in hannunta ta mik'ama Jimmai". Jimmai kallan Hassana ta yi ta ce, "Hassana wa innan kud'infa?, ina kika samosu? ". Hassana bud'e baki ta yi za tai ma Jimmai magana kuka ya kub'uce mata". Jimmai cikin tashin hankali ta ke tambayar Hassana ta ce, "Dan Allah Hassana kimin bayani mana, kin kawomin kud'i dayawa haka kin tasani kina kuka, kud'in waye? ". Hassana sai da tagama kukanta sannan ta kalli Jimmai ta ce, "Kud'in sadakina ke". "Kud'in sadakinki kuma!? ". "Eh, yanzu haka maganar da nake miki Hajiya ta sanar dani and'aura aur... ". Kukwane ya hana Hassana k'arasa abinda ta ke fad'i". Jimmai ko cikin jin dad'i, ta ce, "Dan Allah and'aura auran? ". Hassana da kai ta ba Jimmai amsa". Jimmai kallan Hassana ta yi gala-la, ta ce, "Haba Hassana yanzu wannan shine abin kuka, dan Allah meye abin kuka aciki ?, nidai indai zakiji nasihata tom kibar kukannan, ni Wallahi dani nasamu damar nan taki Hassana inajin saina yi party, dan Allah ni dai in dai kina son tarayyata da ke ta d'ore tom kibar kukan nan muyi magana! ". Hassana share hawayanta ta yi, tana kallan Jimmai. Jimmai ma kallan Hassana ta yi, ta ce, "Yanzu ke me ki kaga zakiyi da kud'in nan? ". Shiru Hassana ta yi, sannan ta ce, "Zan barsu agunki ki ajemin". "A'a, ba haka za ai ba, nishawar da zan baki kisai kayan sawa, kinga dai baki da wasu kaya, kinaji Hausawa nacewa sutura itace mutum, dan haka ki samu dogayan riguna guda Shida (6) ki saya". Hassana kallanta ta yi, sannan ta ce, "Tom taya zan siya, nida bansan ko inaba? ". "Nizan siyo maki gobe a wuse market ". Shiru Hassana ta yi, Sannan ta ce, "Shikenan ki rik'e kud'in awajanki goban sai ki yi amfani da su". Hassana kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Sister Jimmai zan tafi, Hajiya na jirana". Hassana kayanta ta d'akko sannan ta tafi". Jimmai ko har kusan part d'in Hajiya Turai ta raka Hassana tana k'ara kwantar mata da hankali, tana cewa"Wallahi Hassana ki saki ranki kici arzik'i kibar arzik'i". Nan dai Jimmai ta tafi tabar Hassana". Hassana kan abin Sallah ta iske Hajiya Turai. Hassana zama ta yi tana jiran Hajiya Turai ta idar. Hajiya Turai ko na idarwa ta kalli Hassana ta ce, "kin yi Sallah? ". "A'a, banyi ba". Hassana taba Hajiya Turai amsa". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Shiga bedroom d'ina ki yi alwallah kizo ki yi". Hassana tashi ta yi tashiga bedroom d'in Hajiya Turai tashiga toilet d'in ta. Hassana ta dad'e tsaye tana yaba tsaruwa da had'uwa na toilet d'in Hajiya Turai, dan sai yafi burgeta fiye da na Habib. Hassana alwallah ta yi tazo bayan HajiyaTurai ta tada sallarta". Bayan Hassana ta idar da sallar ne tana nan zaune har ake sallar isha'i ta tashi ta yi. Bayan duk sunyi sallah ne, Hajiya Turai ta kalli Hassana, ta ce, "Hassana ki d'auki kayanki sai ki kai site d'in Habib d'in, zan aiko miki da abinci da maganin shi. Rubutun farar roba shine nadare d'ayan kuma na safe da rana sai dare". Hassana tom ta ce ta tashi ta tafi tana jinta duk ba dad'i". B'angaran Farida ko cema Mahaifiyarta ta yi, bazata dawo gidansu Habib ba sai zuciyarta ta lafa, dan hankalinta atashe ya ke game da maganar auran Habib da Hassana. Duk da mahaifiyarta tana ta yi mata kalamai masu sanyin akan auran, acewarta bazai je ko ina ba, dashi da babu duk d'aya ne, dan hakakama karma ta d'aura makanta damuwa". B'angaran Hassana cikin sanyi ta bud'e k'ofar Falon Habib tashiga. Allah sarki Habib zaune yake yana jin alamun shigowar mutum ya tashi da sauri, dan wannan ita ce d'abi arshi. Shiyasa kusan duk lokacinda Hassana zata shiga sai gabanta ya fad'i, dan in yayo kanta sai ta ga kamar itama wujijjigata Zai yi irin yadda ya ke ma mutane. Hakan yasa indai ya taho jikin k'ofar ta ke jingina da d'an alamar tsoro. Habib na k'arasowa inda Hassana ta ke, Kamar yadda ya saba ya rik'o hannunta ya k'arasa da ita cikin Falon. Habib kan caution ya zauna ya zaunar da Hassana kusa da shi kamar yadda ya saba". Hassana ko kanta ak'asa ta kasa kallan Habib, dan gaba d'aya yau ta kasa sakewa da Habib kamar yadda ta ke yi kullum. Hassana na nan zaune Baba Lami tai mata nocking , tana kiranta.Hassan da saurinta ta tashi ta nufi wajan k'ofar. Nan fa shima gogannata ya tashi da sauri ya bita. Hassana bud'e k'ofar ta yi da niyyar amsar abincin. Habib ya yi kan Baba Lami. Hassana da sauri ta irik'e Habib, Baba Lami kuma ta yi saurin aje abincin da rubutun hannunta ta ce, "Kai Hassana Sannu da k'ok'ari dama haka yakema mutane aini bansani ba". Hassana cikin sanyi ta ce ma Baba Lami "Eh Baba haka yake yi". Hassana rufe k'ofar ta yi sannan ta kalli Habib da ke rik'e da hannunta ta ce, kamar za tai kuka"Oga Habib kasa kar min hannu dan Allah in d'auki abincin in shigar da shi ciki". Habib kafad'a ya mak'ema Hassan. Alamun bazai saki ba. Hassana bakin k'ofar Falon ta zauna ta ce, "Tom sai kaci abincin anan inda kak'i sakina in shigar da shi ciki". Habib na ganin Hassana ta zauna shima ya zauna. A gurin Hassana ta zubama Habib tuwan shinkafa da miyar a gushi. Habib sosai Ya ci abincin, sannan sauran da yarage Hassana ta d'auka itama taci dan tun kusan safe bataci komai ba". Bayan Hassana ta gama cin abincin ne ta ta ta shi takoma kan caution d'in Falon ta zauna, Habib ma zama ya yi kusa da ita yana mai rik'e da hannunta. Nan dai Hassana ta fara gyan-gyad'i , dan jiya kusan bata yi bacci ba. Hassana ganin zata fad'i yasa ta kwanta kan caution d'in da yake 3 seater ce". Habib ma ganin Hassana ta kwanta, shima bin bayan Hassana ya yi ya kwanta, akan caution d'in kusan kan Hassana, inda gurin ya yi masu kad'an. Hassana da sauri ta ta shi tana kallan Habib, ta ce, "Oga Habib ka tafi bedroom d'in ka ka kwanta". Habib mak'ema Hassana kafad'a ya yi, irin nak'i d'in. Hassana tashi ta yi ta kai Habib bedroom d'in shi, ta zauna bakin bed d'in ta ce, "Tom kakwanta". Habib kallan Hassana ya yi, yana zaune kusa da ita dan shima zama ya yi kamar yadda yaga ta zauna". Hassana hawa ta yi kad'an kan gadon ta kwanta, inda taga sai abinda ta yi ya ke yi. Aiko take shima ya kwanta bayanta. Hassana tashi ta yi da sauri ta ce, " tom ka kwanta ka yi bacci ". Tanu falon. Tana tashi Habib ma ya tashi yabi bayanta". Hassana na zuwa ta kwanta kan caution d'in duk ta tattare yadda babu yadda Habib zai yi ya kwanta, dan bata bar guba, duk ta babbake caution d'in. Habib ko nazuwa yabi kan Hassana ya kwanta". Hassana cikin tsabar nauyin shi da taji ta ture shi ta milmilo k'asa da sauri tana nishi ta kwanta. Habib d'in ma k'asan ya biyota ya kwanta shima. Hassana juyowa ta yi tana kallan Habib, dariya ma ya bata, aiko ta haudariyarta. Damamaki sai taga Habib d'in shima yana murmushi. Hassana kallan shi ta yi ta girgiza kai. Dan baccinma sai taji ya wuce. Hassana cigaba da kwanciyarta a k'asa ta yi, ahankaki-ahankali ta ji bacci na son d'auketa. Tashi ta yi ta zauna dan tasan indai ta yi bacci tom bazata iya tashi ba taba Habib maganin shi, hakan yasa tana tashi ta d'akko wayar Habib da ta ke gani a Falon ta duba taga. 11:57Am. Hassana maganin Habib ta tashi zata d'akko da mamaki tabi Habib da kallo ganin ya tashi ya biyota dan duk atunaninta bacci ya ke. Hassana rubutun ta d'akko ta tsiyaya a cup. 12:00Am nacika ta mik'ama Habib maganin. Habib k'in amsa ya yi. Hassana ta san dalili dan ya k'oshine, dan ta lura indai ya k'oshi kome zata bashi baya amsa. Hakan yasa Hassana ta kai Cup d'in bakinshi ta ce, "Tom sha". Habib bud'e baki ya yi yana sha. Nan ya shanye wanda ta zuba mai". Hassana nagama ba Habib maganin ta ci gaba da kwanciyarta ak'asa Habib ma k'asan ya bita ya kwanta. Hassana duk yadda zatai ma Habib ya tafi bedroom d'in shi ya kwanta ta yi mai amma yak'i. Hassana kwanciyarta ta yi tana jan tsaki, dan duk sai taji badad'i yadda Habib duk ya kanannad'eta, gashi yasa hannu d'aya ya rik'o k'ugunta, hakan yasa ta kuma jinta wani iri ba dad'i. Hassana hannu Habib ta kama ta rik'e dan ba tajin dad'in yadda ya rungumota ta baya. Shiko Habib hannun shima da ta rik'e ya isai, dan dama gani ya ke kamar zata gudu ne, yana ko jin ta kama mai hannu shikenan". Hassana cikin dare ta tashi domin yin fitsari dan ita tana da tashin fitsarin dare. Abin mamaki tana tashi Habib ma ya tashi". Hassana da kallo tabi Habib, sannan tanufi bedroom d'in shi dan acan ne toilet d'in shi ya ke. Hassana na tafiya Habib ya bi bayanta. Hassana ta bud'e k'ofar toilet d'in ta shiga, kusan tare da Habib suka shiga. Hassana kallan Habib kawai ta ke, sannan ta ce, "Oga Habib kafita mana, baka ganin nan toilet ne". Shidai Habib da ido ya bi Hassana da kallo. Hassana ganin Habib ba fita zai yi ba, kuma fitsari ya matseta ya sa ta zuk'unna ta yi fitsarinta". Hassana na zuk'unnawa Habib ma ya zuk'unna bayanta shima yana fitsarin. Hassana na gamawa ta fito shima Habib ya tashi ya fito. Wato so dadama idan Habib ya yi wani abun, Hassana sai taga kamar mai hankali, sai dai in yayi wani abunne zaka tabbatar da k'wak'walwar ta tab'u". Hassana komawa kan bed d'in Habib ta yi ta kwanta, d'an ak'asan sanyi gashi ana sanyi-sanyi". Habib bayan Hassana yabi ya kwanta, Hassana ko kojuyowa bata yi ba, jin ankwanta bayanta dan tasan kowaye". Kiran sallar asuba, Hassana ta farka ta ga Habib kamar wanda ke shirin shigewa cikinta, yadda ya kanannad'eta ga hannu d'aya yasa ya rik'e k'ugunta da shi. Hassana cire habnun Habib ta yi daga jikinta, sannan ta d'an ture shi daga jikinta ta tashi. Tana tashi yana tashi yabi bayanta. Atare kusan sukai alwallar dan duk abinda ta yi sai ya yi. Sallarma tana ta dawa shima yazo kusa da ita ya tsaya yana yin duk yadda ta yi, ahaka dai suka idar da sallar. Sai da ka gari ya yi haske sannan Hassana ta tashi. Ta koma kan caution zata kwanta sai ta tuno daga ta kwanta mutuninta shima zai ce zai kwanta kuma gurin ba isarsu zai ba, hakan yasa ta fasa ta koma kan sallayar ta kwanta. Aiko shima kusa da ita ya kwanta". Bacci mai nauyi ya d'auke Hassana, dan bugun da akema k'ofar ne ya sa ta tashi a furgice ............... Idan kin karanta d'aure ki yi Comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ *YAN UWA KULLUM KARA KUSANTAR KABARI MUKE KWANAKINMU SUNA KAREWA AJALINMU YANA KUSANTOMU AMMA BAMA FARGA DA HAKA😭😭!*ALLAH KASA MU CIKA DA IMANI👏👏👏👏👏👏👏. Shafi na 38&39. Hassana cikin furgici ta tashi tsabar yadda ake buga k'ofar. Hassana tashi ta yi da saurinta dan zuwa ganin mai bugun k'ofar. Baba Lami ta gani tsaye da abin breakfast d'in su a hannunta. Hassana kallan Baba Lami ta yi tana murza ido ta ce, "Baba dama ke ce, Wallahi har naji tsoro! ". Dariya Baba Lami ta yi, ta ce, "Haba wannan wana irin bacci ne, tun d'azu fa nake tsaye nake buga k'ofar nan, amma shiru". Hassana mutsitsika ido ta k'arayi ta ce, "Ina kwana Baba ". "Lafiya k'alau Hassanan, ya mai jikin? ". Hassana cikin alamun kunya tace ma Baba Lami, "Da sauk'i ". Baba Lami kallan Habib ta yi dake tsaye kusa da Hassana ta ce, "Hassana ki matsar da mutumin naki sai in shigo in kawo muku abin k'arin,". Hassana bud'e ma Baba Lami k'ofar ta yi ta matsa da Habib daga jikin k'ofar. Amma duk da haka bai hana Habib yunk'urowa ba ya ce zai kamo Baba Lami. Baba Lami ko da saurinta ta aje abin breakfast d'in ta gudu". Hassana zuwa tai ta rufe k'ofar, sannan ta je cikin kayanta da tazo da su, ta d'akko brush d'inta tashiga toilet d'in Habib ta yi brush. Habib ko tsaye ya ke cikin toilet d'in shima yana kallan Hassana, Hassana kallan Habib ta yi bayan ta gama brush d'in, ta ce, "Oga Habib kaima za kai? ". Habib dai da ido yabi Hassana da kallo. Hassana d'aya daga cikin tooth brush d'in da ta gani a toilet d'in ne ta matsama Habib toothpaste ta mik'amai. Habib amsa ya yi yana kallan Hassana. Hassana hannu Habib ta gama ta kai brush d'in bakin shi ta ce, "Yauwa tom wanke bakinka ko? ". Habib kafad'a ya mak'ema Hassana alamun bazai wanke ba. Hassana amsar brushi d'in ta yi daga hannun shi ta ce, "Tom bani ni in wankema". Habib sakarma Hassana brush d'in ya yi. Hassana ta ce, "Yauwa tom bud'e bakin". Habib bud'e bakin ya yi. Hassana ta tura brush d'in cikin bakinshi tana wankema. Sai dai fa mai makon ya zubar shanyewa ya ke. Hassana kallan shi ta yi, ta ce, "Kai Oga Habib ba fa shanyewa ake ba, karik'a zubarwa kaji?, yauwa tom zubar haka". Hassana ta tofar da miyau abakinta, tana gwadama Habib shima yadda zaiyi ". Nan dai ashiririce aka dama wanke bakin. Hassana break fast d'in da Baba Lami ta kawo masu ta d'akko tana bud'ewa, kunun gyad'a ne ya yi haske sosai sai k'amshin kunun ya bid'e falon. Sai soyayyar doya da akai ma miyar k'wai. Hassana tsiyayama Habib kunun ta yi, tana bashi ko ya amsa ya fara sha. Hassana soyayyar doyar taba Habib amma ya k'i ci. Rubutunshi ta d'akko ta bashi, sannan itama ta zubama kanta kunun tasha, bayan ta gama shanyewa ne ta ci doyar. Habib shima ganin Hassana na cin doyar d'auka ya yi yana ci. Hassama sosai ta ci doyar. Bayan Hassana sun gama break fast d'in ne, taji tana son yin kwanka inda dama ta saba wankan safe ta ke, amma kuma bata san yadda zatai da Habib ba. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib ka zauna nan zanyi wanka, indai kuma ka biyoni tom zan b'ata da kai zan tafi in barka, kaji? ". Habib shi dai kallan Hassana ya yi da ido". Hassana ko, tashi ta yi ta nufi bedroom d'in Habib.abin dariya kusan tare suka shiga bedroom d'in. Hassana tsayawa ta yi tana kallan Habib ta ce, "Oga Habib Allah yau zan b'ata da kai indai baka zauna ba kajirani nayi wanka, ka zauna nan kaji rani". Habib mak'ema Hassana kafad'a ya yi alamun yak'i d'in". "Hassana ta ce, "Na shiga uku, tom wai kai komai zanyi sai ka bini". Hassana hannun Habib ta kama ta zaunar da shi bakin gado, ta ce, "Yauwa, tom zauna anan in yi wanka ". Habib kallan Hassana ya yi. Hassana ko ganin Habib bai mak'e mata kafad'a ba, sai ta yi tunanin bazai bita ba, ya hak'ura zai zauna, hakan ya sa,Hassana tashi ta nufi toilet d'in. Aiko tana shiga kusan atare suka shiga". Hassana cikin jin haushin Habib d'in ta d'aure fuska ta ce, " Oga Habib fita".Hassana ta fad'i maganar tana nunama Habib hanyar fita. Habib ko da ido ya bi Hassana da kallo. Hassana ko ganin haka sai tafara tura Habib. Sai dai ko motsi Habib bai ba. Hassana duk yadda za tai da Habib ya fita yak'i dole ta rabu da shi ta fasa yin wankan ta fito, ta zauna bakin bed d'in Habib cikin jin haushin Habib ya k'ifita yabarta ta yi wanka". Habib ko zama ya yi kusa da Hassana zai kama hannunta. Hassana cikin jin haushi ta fusge hannunta ta ce, "Da Allah ni sakarmin hannu, aina b'ata da kai tunda kak'i barina inyi wanka. Habib ko kallan Hassana kawai ya yi. Hassana na nan zaune taji yo nocking d'in k'ofa. Tashi ta yi da sauri, mutumin tama ya mara mata baya". Hassana tana zuwa abin mamaki Hajiya Turai ta gani tsaye jikin k'ofar. Hassana cikin sanyin murya ta ce, "laa Mommy ki ce, bari in bud'e miki". Hajiya Turai da katar da Hassana ta yi ta ce, "A'a my daughter bari basai na shigoba, nazo ne in ganku, inji ya kuka tashi". Hassana cikin girmama Hajiya Turai ta ce, "A'a Mommy dan Allah ki shigo". Hajiya Turai murmushi ta yi tace, "My daughter so kike yau in kasa bacci, dan wujijjigawar da yayi min rannan har yanzu ina jinta ajikina, dan haka barni kawai ba saina shigoba". "Mommy Allah naga kamar ya rage, dan ko yau da Baba Lami ta shigo kawo abin breakfast naga bai ce zai bita ba, ki shigo ai ina nan". Hajiya Turai shahada ta yi ta ce ma Hassana tom bud'emin". Hassana bud'ema Hajiya Turai ta yi". Habib ko da yake tsaye kusa da Hassana yana rik'e da hannunta yana ganin Hajiya Turai ta shigo ya yi kanta. Hassana da sauri ta jawo Habib ta ce, "Oga Habib Mommy ce fa?, kamanta ta ne, kabarta kaji? ". Habib mak'e kafad'a ya yi". Hajiya Turai ko naganin haka ta ce, "My daughter rabu da shi bari in fita ". Hajiya Turai ta yi maganar kamar za tai kuka". Hassana kai ta girgizama Hajiya Turai ta ce, "A'a Mommy dan Allah ki zauna babu abinda zai miki insha Allah ". Hajiya Turai d'annesa da su Hassana ta zauna kan 1 seater. Hassana ma zama ta yi, kan 3 seater, Habib ma ya zauna kusa da Hassana". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Daughter ya jikin nashi kike gani tsakanin jiya da yau? ". "Tom da sauk'i inda naga kamar yanzu yarage cewa zai bugu duk wanda ya shigo sai dai hargagin zai bugun, inda kinga ko d'azu da Baba Lami ta shigo sai dai har gagin ya yi". Hajiya Turai cikin jin dad'i ta ce, "Alhamdulillah Allah ya kawo sauk'i gaba d'aya ". "Ameen ya Allah ". Cewar Hassana. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "My daughter inda naga alamun sauk'i yafara zuwa, inda gani har kusa da Habib bai min komai ba, abinda da bahaka ba, yanzu insha Allah nan da sati idan naga yanayin jikin zan je London, wajan aiki sun daman da kira, zan je ko sati d'aya inyi in dawo, yanzu baki da wata matsala ko? ". "Eh Mommy babu"."Ok, yau zanba Bilya kud'i ya sayo miii waya idanma kina buk'atar wani abun sai kikirani awaya, inda naga mutumin naki babarinki fita zai yi ba". Murmushi Hassana ta yi ta ce, "Tom Mommy nagode". Hajiya Turai fita tayi tabar Hassana da Habib.Hassana na nan zaune tana tunanin yadda za tai tai wanka sai ta ji nocking d'in k'ofa, da yake tunda Hajiya Turai ta fita Hassana bata tashi ta rufe ba, yasa ta ce, "Shigo". Duk da bata san kowaye ba". Jimmai ko da mamaki jin ance ta shigo ta shiga, tana mamakin wai yau ita ce zata shiga falon Oga Habib, Lallai wani abu sai ciwo, ammma in bahakaba waneni acewar Jimmai". Jimmai ko ko da ta shiga d'annesa da Hassana ta tsaya tana k'arema falon kalo da jinjina had'uwa irin ta falon Habib". Hassana ganin hankalin Jimmai gaba d'aya ya tafi a kallon falon ya sa, ta ce, "Barka da safiya sister Jimmai". Jimmai cikin jin kunya ta ce, "Hassana kingani kamar wata sakarya ko?, ina nan ina kallan tsaruwa ta falon Oga Habib, dama kayan da mukai da ke jiya zan siyo miki ne, na kawo miki". Hassana cikin mamaki ta kalli Jimmai ta ce, "Kai dan Allah har kin sayo, amma gaskiya kinyi sauri". Jimmai mik'ama Hassana ledar kayan ta yi". Hassana amsa ta yi ta bud'e tana gani, dogayan rigunane kala masu kyau, kala shida, sai riga da siket kala uku, sai da wando suma kala uku. Hassana kallan Jimmai ta yi tana jin dad'in kayan dan sosai su kai mata kyau, ta ce"Kai sister Jimmai amma gaskiya kayan sunyi min kyau sosai, nagode Allah ya saka da alkairi". Ameen Jimmai ta ce, sannan ta mik'ama Hassana sauran kud'in ta ce, "Ga sauran kud'in kirik'e a hannun ki". "A'a, ki bari kirik'e a hannunki". Jimmai tafiya ta yi da kud'in kamar yadda Hassana ta buk'ata". Hassana ko har yamma tana nan zaune bata yi wanka ba,abin har ya fara damunta. Dan bawai a gidan ba, tun kan Hassana ta zo gidan su Oga Habib ta saba wankan safe, hakan ne yasa yau take jinta duk ba dad'i. Hassana kallan Habib ta yi da ya ke kusa da ita rik'e da hannunta yana wasa da shi ta ce, "Ayyah Oga Habib kaga ban iya daurewa in banyi wanka ba, dan Allah zaka zauna nan kajirani inyi wanka da sauri in dawo? ".Habib mak'ema Hassana kafad'a ya yi.Hassana kamar za tai kuka ta kuma cewa, "Dan Allah Oga Habib, inje zaka jirani? ". Yanzu Habib banza ya yi da Hassana ya kalleta kawai". Hassana kuma ganin bai kuma d'aga mata kafad'a ba tashi ta yi, ta nufi toilet. Kusan tare da Habib suka isa toilet d'in. Hassana cikin jin haushin Habib d'in ta ke kallan shi, sannan ta ce, "Tom yi haka". Hassana ta rufe idonta tana numa Habib shima ya rufe". Habib rufe idon shi ya yi kamar yadda yaga Hassana ta rufe". Hassana ko naganin Habib ya rufe idon shi ta yi saurin cire doguwar rigar da je jikinta da bra da pant d'inta. Tana yi tana kallan Habib gudun karya bud'e idon shi. Hassama matsawa ta yi inda Shower ta ke ta kuna". Habib ko najin sud'in fitar ruwa ya yi saurin bud'e idon shi". Hassana ko ta juyama Habib baya, tana wanke jikinta da sauri da soso gudun kar Habib ya bud'e ido. Sai jin mutum ta yi bayanta yana k'ok'arin fusge sosan da take hannunta". Hassana cikin rud'ewa ta juyo tana kallan Habib. Kafin ta yi wani abuma ya fusge sosan dake hannunta yana wanke jikinshi shima kamar yadda yaga tana yi". Hassana lokaci d'aya dariya ta kamata ga b'akincin bud'e idon shi da ya yi ga kuma dariyar yadda ya ke wanke kayan jikinshi da soso shi ala dole wanka ya ke yi. Hassana baya ta kuma juyama Habib ta ci gaba da wankanta da soap ka d'ai ba soso". Habib ma aje sosan ya yi , ya dawo d'aukar soap d'in yana gogawa a kayan shi kamar yadda yaga Hassana na gogawa ajikinta". Hassana ko ganin Habib ya aje sosan d'auka ta yi ta ci gaba da wanke jikinta da shi" Habib ganin ta d'auki sosan, shima aje soap d'in ya yi ya fusge sosan daga hannunta". Hassana wanke jikinta ta yi da ruwa ta d'aura towel d'in da ta gani agun an rataye". Habib ma towel d'in ya d'akko shima ya d'aura akan kayan shi kamar yadda yaga Hassana ta yi". Hassana ko kallan Habib ka wai ta yi tai murmushi ta barshi ta fita daga toilet d'in. Habib ma bayan Hassana ya bi shima". Hassana dressing mirror d'in Habib ta je ta d'auki lotion d'in shi tana shafawa, Hassana jin k'amshin man ya yi yawa yasa ta kuma dubawa dan ta gani kodai turare ne bata sani ba. Dubawa ta yi taga mai ne". Habib shima tatsa ya rik'ayi yana shafawa, kamar yadda yaga Hassana na yi". Hassana d'aya daga cikin doguwar rigar da Jimmai ta siyo mata sata. Bayan Hassana ta gama shiryawa Habib ta kalla da ya ke tsaye yana kallanta kayan shi duk sun jik'e har d'iga suke. Hassana wajan kayan Habib ta je ta d'akko mai k'ana marasa nauyi ta kawo mai ta ce, "Oga Habib ga kayanka ka sa". Habib kallan Hassana ya yi. Hassana tunanin Habib ba amsa zai yi ba da ta yi, yasa ta kama hannun Habib d'in ta zaunar da shi kan lover chair d'in bedroom d'in. Hassana rigar Habib da ke jik'e ta cire mai ta sa mai wata, sannan ta rufe idonta ta kama wandonma ta zare mai, ahaka dai da rintse ido Hassana ta sa ma Habib kaya ". Hassana nagama shirya Habib aka kira sallar magriba. Toilet d'in ta koma ita da mak'ake mata d'inta suka yi alwallah, tazo ta shimfid'a sallahya ta tada sallah. Nan dai duk yadda tai Habib ya yi ahaka tai sallar. Tana idarwa Baba Lami ta kawo masu abincin dare. Hassana sai da tayi sallar Ishsha'i sannan ta tashi daga kan abin sallar". Tuwan semo miyar kuka ta ji naman rago. Hassana hannu tasa tasa ma Habib ma nashi suka ci tare. Suna gamawa ta wankema Habib hannu itama ta wanke nata". Dama Hassana ta sa da baccin wuri, suna gama cin abinci ba dad'ewa ta tashi ta nufi bedroom d'in Habib ta kwanta. Inda shima oganta ya mara mata baya, ya kwanta kusa da ita, 12:59Am Allah ya tai maki Hassana ta tashi ta ba Habib rubutun shi". Washe gari Hassana bayan ankawo masu abin kari sun karya. Tashi ta yi takama rigar jikinta ta cire ta d'ora towel. Habib ma naganin haka shima ya kama tashi ya cire kamar yadda yaga Hassana ta yi. Tom da yake ita Hassana ba dogon wando gareta ba bare Habib yaga ta cire shima ya cire. Hassana toilet ta shiga Habib ya fita". Wanka Hassana ta yi duk yadda ta yi Habib na yi kamar jiya ahaka dai suka gama wankan". Wajan shama haka sukai duk yadda Hassana ta yi Habib na yi ahaka ya shafa mai, Hassana ta ciroma Habib kayan shi ta samai kamar jiya, itama ta sa cikin wa inda Jimmai ta siyo mata". Hassana bayan ta shirya ta shirya Habib. Kallan Habib ta yi ta ce, "Tom Oga Habib yau Mommy za mu je mu gaida ". Hassana fita ta yi ta ja k'ofar ta rufe. Habib kuma kama hannun Hassana ya yi katam ya rik'e". Ahaka Habib da Hassana suka jera suka nufi part d'in Hajiya Turai. Duk 'yan aikin gida da mamaki suke kallan Hassana, dan duk cikinsu ba kowa bane yasan Hassana na kula da Habib, bare kuma magar auran su banda Jimmai babu wanda yasan da maganar auran Hassana da Habib ba". Hassana dai-dai zasu shiga site d'in Hajiya Turai sai ga Farida da zuwanta kenan gidan". Farida cikin tashin hankali da damuwa ta ke kallan Hassana da hannunta ke cikin na Habib...... Idan kin karanta d'aure ki yi Comment Sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA NA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Ayi hak'uri da wrong typing ina ciwan ido ne👁️👁️. Shafi na 40 & 41. Farida cikin tashin hankali da damuwa ta ke kallan Hassana da hannun ke cikin na Habib amak'ale. Hassana ko da bata lura da Farida ba ta gaban Farida ta wuce, batare da ta lura da ita ba. Farida ko cikin jin zafi da haushi ta da kama Hassana tsawa, ta ce, "Ke wata irin sakarya ce!, kuma ubanwa yasa ki ki fito da Oga Habib!? ". Hassana da kwatakwata bata lura da Farida ba, sai tsawarata ta ji, cikin tsoro ta juyo tana kallan Faridar, ta ce, "Ayyah Aunty Farida dan Allah ki yi hak'uri, Wallahi ban lura da ke bane". "Dama taya zaki lura dani, kanki narawa ke ga Amaryar Oga Habib ko?, Tom bari kiji Wallahi daga yau har uzuwa ranar da auran nan zai zo k'arshe karki yadda karki kuskura kik'ara fitowa da Oga Habib, idan kuma ba haka ba zan nuna miki ainihin kalata, dan haka ki mai dashi inda kika fito da shi sakarya kawai! ". Hassana harga garanta bataji dad'in yadda Farida ke zaginta ba. Hassana kama hannun Habib ta yi suka juya". Hajiya Turai ko da hayaniyar Farida ta sa ta fito, kallan Farida ta yi, tana kuma kallan bayan Hassana ta ke tafiya, ganin kamar gunta suka zo kuma ta ga sun juya, tabbas ko ba a fad'a mata ba tasan Farida ce ta koreta, inda taji yo hayaniyar fad'an Farida. Hajiya Turai kallan Farida ta yi, ta ce, "Farida ke da wa kike hayaniya haka? ". Farida cikin alamun ta ji haushin abinda Hassana tai ta ce, "Mommy wannan 'yar iyayin yarinyar ce mana, ta wani kama ta fito da Oga Habib ,kowa wama yasata". "Ok kiramin ita ". Cewar Hajiya Turai ". Farida ko cikin b'acin ciki dajin haushi ta je kiran Hassana, dan ita a ganinta rainine kamarta ta je kiran Hassana. Farida tun kan tak'arasa inda Hassana ta ke ta ce, "Ke! ". Hassana tsayawa ta yi amma bata waigoba". Farida k'arasowa inda Hassana ta ke ta yi, ta ce, "Lallai, kin isa, tom Mommy na kiranki, kuma Wallahi Kin dai ji kashai din da nai miki, kar in kuma ganin kin fito da Oga Habib , idan kuma ba haka ba, zaki gani! ". Ita dai Hassana bata ce ma Farida ko mai ba, kama hannun Habib ta yi suka k'arasa inda Hajiya Turai ke tsaye". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter lafiya kika fito ke da Habib? ". Hassana cikin sanyin muryata ta ce, "Mommy munzo gaida ke ne? ". Hajiya Turai cikin nuna jin dad'in ta ta ce, "Kai, ka ce yau inada manyan bak'i tom ku shigo ciki". Hassama ta na rike da hannun Habib suka Shiga tan k'ameman Falon Hajiya Turai. Bayan Hassana ta zauna ne, ta gaida Hajiya Turai cikin grimamawa kamar yadda ta saba". Hajiya Turai da sakin fuska ta amsa ma Hassana ta ce, "Lafiya lau daughter ya kike?, ya Habib da jikin da fatan ana ganin sauk'i ? ". "Eh Mommy da sauk'i, inda kinga yafara sakewa da mutane bakamar da ba". Hajiya Turai cikin jin dad'i ta ce, "Alhamdulillah Allah yak'aro sauk'i". "Ameen ya Allah ". Cewar Hassana". Hajiya Turai shuru ta yi na 'yan second's, sannan ta kalli Hassana ta ce, "Daughter mai ya had'aki da Farida? ". Hassana cikin sanyin muryarta ta fara ba Hajiya Turai amsa kamar haka"fad'ata tai min wai kar in sake fitowa da Oga Habib ". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ita ta sa kika koma da shi ko? ". "Eh Mommy ita ce". K'wafa Hajiya Turai ta yi, ta ce, "zata sani dan taga ina barinta ne". Hajiya Turai kiran Maimuna ta yi ta ce ad'ora girgi yanzu, kuma tana buk'atar abinci mai dad'i dan acewarta tana da manyan bak'i ". Hassana dai murmushi ta yi, jin Hajiya Turai na kiransu da manyan bak'i ". B'angan Farida ko, cikin damuwa ta shiga d'akinta. Waya ta ciro ta kira Mahaifiyarta. Hajiya Murja na d'agawa Farida ta sa mata kuka. Hajiya Murja cikin damuwa ta ke tambayar Farida abinda ke damunta. Farida ko cikin kuka ta ce, "Haba Mommy taya zaki tambayan meke damuna bayan kinsan damuwata, yanzun haka fa, yarinyar nan na Falon Mommy ita da Oga Habib, bikiga yadda Mommy ke nan-nan da ita ba, har da sawa wai ai mata girki mai dad'i wai tana da manyan bak'i ". Daga can b'angaran Hajiya Murja ta ce, "Yauwa Farida kina jina ko?, ai abun yazo da sauk'i yanzu ki je kiba Balaraba maganin da Malam ya baki, ki ce nace ta zuba shi a girgin da za tai ma su". "Mommy ba fa Balaraba ta sa girkinba, Maimuna ta sa, amma ki bari duk yadda zanyi yanzi, yau d'in nan na bazasu k'etarema maganin nan ba, ke dai Mommy ki taya ni addu'a, Allah yaban nasara akansu". Daga can b'angaran Hajiya Murja ta ce, "Farida ai ke ke da nasara akansu, ke dai kamar yadda kika ce duk yadda zaki yi ki yi ki zuba masu maganin komai yazo k'arshe in samu hankalinkina ya kwanta". Nan dai su kai Sallama Farida tana mai k'ara tabbatarma Mahaifiyarta yau sai sunci maganin". B'angaran su Hajiya Turai ko, Hajiya Turai sai jan Hassana da fira ta ke, cikin wayo kuma tana jin shirrin Hassana da wacece ita. Suna ahaka ne aka kira Sallar azahar ". Hajiya Turai tashi ta yi taje tai alwallah, bayan ta yi alwallah ne ta kalli Hassana ta ce, "Daughter ki je kiyi alwallah ki zo ki yi sallah". Hassana tashi ta yi Habib ya tashi shima zai fita". Hassana koma ta yi ta zauna ta kalli Habib ta ce, kamar mai yima k'aramin yaro wayau ta ce, "Oga Habib ka zauna nan kaji rani, in yi alwallah yanzu zan fito kaji? ". Habib mak'ema Hassana kafad'a ya yi". Hajiya Turai ko abin dariya ma ya bata ganin Hassana wai ita wayo zata tai ma Habib. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ku je tare, danni tsoro nake ma kibarni daga ni sai shi, ya wijijjigani". Hassana kama hannun Habib ta yi suka nufi bedroom d'in Hajiya Turai, inda acan toilet d'in ya ke". Hassana duk yadda ta yi haka Habib ke yi, ahaka dai asiririta suka gama alwallar. Hassana kwata-kwata bata luraba sai da suka gama alwallar taga yadda hannun rigar Habib ya jik'e sosai. Hassana kallan shi ta yi ta ce, "Oga Habib haka ka jik'e rigarka gashi ba yanzu zamu tafi ba". Hassana jan hannun shi ta yi suka fito". Hajiya Turai ko da tun d'azu ta idarar da sallar ta, kallan Hassana ta yi tana murmushi ta ce, "Daughter hala Habib wasa ya yi da ruwa? ". Hassana sosa k'eya ta yi, ta ce, "Mommy Allah ban lura ba, kuma shi sai yace duk yadda nayi sai ya yi". Murmushi Hajiya Turai ta yi, ta ba Hassana gu ta ce, "Tom zoki tada sallar ". Hassana tada sallah ta yi, Habib ma yazo ya tsaya kusa da ita duk yadda ta yi ya yi, ahaka aka idar da salar". Hassana na idarwa ya yi dai-dai da zuwan Maimuna ta sanar da Hajiya Turai ta gama girkin ta jera koma a darnin space". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana kin zoma Habib da maganin shi? ". "Mommy da yake banyi tunanin zamu dad'e ba, shiyasa amma bari in d'akko mai yanzu in dawo". Hassana tashi ta yi zata tafi Habib ma ya tashi ya bi bayanta. Hassana kallan shi ta yi ta juya zata tafi, ya rik'o hannunta shima ya bita". Farida ko da ke alab'e tana son samun damar zuba maganin, tana ganin Hassana ta je site d'in Habib ta yi saurin nufar derning space d'in". Farida cikin kwanciyar hankali ta san har ta gama Hassana baza dawo ba. Farida maganin ta d'akko da ke d'aure a zaninta ta zuba a abincin sosai,Sannan ta goge gurin yadda babu wata alama da zata nuna alamun barbad'an wani abu. Farida na gamawa ta yi sauri ta bargun, tana mai jin dad'in yau target d'in ta zai kama su Hassana". Hassana maganin Habib ta d'akko ta canja mai riga inda tashi ta jik'e. Sanna ta kamo hannun Habib suka dawo Falon Hajiya Turai ". Suna dawowa Hajiya Turai ta kalli Hassana ta ce, "Daughter mu je kuci abinci". Hasssana kama hannun Habib ta yi, suka tafi site d'in derning space. Sosai Hassana ta rud'e da tsaruwa irin ta gurin cin abinci. Zama ta yi , mutu minta ya zauna kusa da ta, dan sai da Hassana ta matso da chair d'in kusa da ita, dan tasan in ba haka ba zai iya cewa zai zona kanta". Hajiya Turai wani abin ya bata mamaki wani ya bata dariya. Dan ko wajan cin abincin Hajiya Turai da ta zuba ma Habib nashi a plate ta mik'a mai, ko kallan shi bai yi ba , na Hassana da yaga tana ci yasa hannu shima ya kama ci". Allah sarki haka su Hassana suka ci abincin da Farida ta zuba magani sosai batare da sanin su ba". Farida da ke lab'e tana ganin sun fara cin abincin, ta fita tana rawa tana jin dad'in burinta ya gama cika gobe iwar haka.......... ✍️ Wayyo Hassana ta ci magani a abinci, Habib ma ya ci😭😭😭😭. Idan kin karanta d'aure ki yi Comment sister 🤝 Idan Allah yaban lafiya zaku ga posting gobe insha Allah, ayi managa da wannan. Kwana biyu anji ni shiru, a yi haku ri banda lafiya ne. Ina barar addu'a dan Allah idona ciwo ya ke😭😭😭. Comment & Share please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Ina ba duk wani mai bibiyar littafin Oga Habib hak'uri, naji na shiru da akayi kwana biyu, haka ya faru ne saka makon ciwan ido da nayi. Masu text massage da masu kiran waya nagode da nuna kulawarku gareni, nagode da kulawa sosai👍🏻, Allah yabar zuminci🤝. Masu comment na last page na gani kuma nagode sosai, a yi hak'urin rashin replying da ban samu yi ba👏. Shafi na 42&43. Farida da ke lab'e tana ganin sun fara cin abincin ta fita, tana rawa tana jin dad'in burinta ya gama cika gobe iwar haka". Hassana ko na aje spoon d'inta Habib ma ya cire hannunshi. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ba dai kin k'oshi ba? ". Hassana kanta k'asa tana wasa da finger's d'in ta, ta ce, "Eh Mommy na k'oshi". Girgiza kai Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Garama Habib naga yaci sosai, amma ke cinnaki shiririta ne, dan haka yau kina nan har dare, yanzu dai nabarki k'ila wannan bai miki dad'i bane, daddare zan ga d'an abinda zaki kuma ci". Ita dai Hassana bata ce komai ba, murmushi tai ma Hajiya Turai ". Hajiya Turai tashi ta yi, ta ce, "Tom ku tashi mu koma Falo". Hassana tashi ta yi, Habib na rik'e da hannunta suka koma falon Hajiya Turai. Bayan sun zauna ne, Hajiya Turai ta kalli Hassana ta ce, "Daughter bari inyi baccin 30 min's in fito ko? ". "Tom Mommy, afito lafiya ". Bayan shigar Hajiya Turai bedroom d'in ta bai fi da 20 min's ba, Hassana da hankakinta duk kusan ya tafi a american film d'in da ta ke kallo, duk da tun d'azu tana jin jikinta wani iri, tana shashsharewa ne kawai, da kuma film d'in ya kuma tai ma ka mata wajan kaudar da hankakinta a abinda ta ke ji. Hassana babu zato sai ji tai Habib ya jawota ta fad'o kan shi. Da sauri ta yunku'ura jata tashi daga kan shi, ya rik'e ta kata kam ya kwantar da kanshi cima kanta yana wani irin nishi kad'an-kad'an alamun magani ya fara aiki". Hassana fara kokwawar k'wacewa daga ruk'un da Habib ya yi mata ta yi, amma ta kasa". Habib ko da maganin boka keta k'ara ta siri ajikinsa, rigar jikinsa, ya cire ya wurgar gefe yana k'ok'arin yage taji kin Hassana". Hassana ganin ciwan Habib d'in kamar irin na rannan, kuma a d'akin Hajiya Turai da rana, Hassana cikin ammafani da k'arfin da Allah ya bata ta yunk'ura ta tashi zata gudu, cikin rashin sa'a ta fad'i agurin. Tana ta fud'uwa Habib ya bita k'asan, ya jawo rigarta da k'arfi ya yaga wanda sai da rigar ta dire har k'asa". Hassana cikin tashin hankali ta yi k'arar da bata san ta yi taba, tana kiran sunan Hajiya Turai, tana cewa, "Wayyo Mommy ki fito dan Allahhhhh!!! ". Hajiya Turai cikin daddad'an baccin da ya kwasheta, ta jiyo ihun Hassana tana kiran ta. Hajiya Turai da sauri cikin tashin hankali yadda ta ji Hassana na ihu tana kiran ta ta nufo falon". Hajiya Turai da bata san meke faruwa, ita dai atunaninta dukan mutane da Habib ke yi ne, yau kuma abin ya fad'o kan Hassana. Hakan yasa Hajiya Turai cikin jarumta, ta afkama Habib da ta gani kwance kan Hassana, Hassana kuma tana ta kwala ihu tana bige-bige tak'i ba Habib wata damar zai aikata wani abu kanta". Hajiya Turai na , zuwa da k'arfin da bata san tana da shiba ta ture Habib daga jikin Hassana. Hassana kuma ta yi saurin yunk'urawa ta tashi. Nan fa aka fara guje kuje a Falon Hajiya Turai, duk inda Hassana ta ruga Habib ya fita da gudu,ita kuma tana ihu tana kiran Hajiya turai ta tai maka mata, dan Hassana gaba d'aya ta gama tsorata da Habib. Duk inda Hassana tai Habib ya fita, kuma Allah yasa har yanzu ya kasa kamata, da yake abin bacikin hankalinshi bane, babu dabara". Hajiya Turai ko ganin haka jug d'in da ke gurin ta d'akko ta wurgama Habib. Aiki cikin sa'a tana wurga mai Allah ya taimaka ya sa Habib d'in ya yi wata muguwar fad'uwar da sai da ya ba Hajiya Turai tsoro". Hassana ko naganin Habib ya fad'i ta afka bedroom d'in Hajiya Turai ta rufe tana nishin wahala". Habib ko ya d'an dad'e a kwance gun yana nishin wahala dan sosai ya fad'i dan gefan bakin shi sai da ya fashe". Hajiya Turai ko ganin Habib bai tashi da wuri ba, da sauri cikin damuwa ta k'asaro inda ya ke kwance. Hajiya Turai na juwa ta kamo hannun Habib da niyyarta ta ta da shi. Habib naji ana tab'a shi ya tashi da sauri, ya nufi bedroom d'in Hajiya Turai inda yaga Hassana ta shiga, sai dai kashh, yana tura k'ofar ya ji ta kam-kam. Haka Habib ya tsaya sai bugun k'ofar ya ke kamar zai karyata". Hajiya Turai gudin kar Habib ya jima kan shi ciwo ganin yadda ya ke bugun k'ofar ya sa ta tashi ta zo zata kama hannun Habib d'in, ya kai mata duka, da sauri ta kauce bai sa metaba, ta zauna tana mai tausayama d'an nata guda, tare da mai addu'ar Allah ya bashi lafiya, ya dawo mai da hankalin shi". Habib ya dad'e gun yana wujijjiga k'ofar kamar zai karya ta, yana wani irin nishi. Sannan zuwa can ya kwanta bakin k'ofar , ya dad'e yana malele kuwa agun, sannan wani wahalallan bacci ya yi awan gaba da shi". Hajiya Turai cikin tausayama Habib ta zo gaban shi ta zuk'unna tana kallan k'asan leb'anshi inda ya fashe fad'uwar da ya yi. Hajiya Turai tanan zuk'unne hawaye na zuba mata kad'an-kad'an na tausayin d'an nata. Hajiya Turai ta dad'e gun zuk'unne kusa da Habib sannan ta tashi, ta lek'a ta window ta hango Hassana kwance akan love chair d'in bedroom d'in, sai malele kuwa ta ke. Hajiya Turai magana ta yi a hankali gudin kar Habib ya ji, ta ce, "Daughter zo ki bud'e min". Hassana tashi ta yi ta bud'ema Hajiya Turai k'ofar. Hajiya Turai ko bayan tashiga kallan Hassana ta yi da ke ta juye-juye tana cije baki ta ce, "Daughter yaji miki ciwo ko? ". Hajiya Turai ta fad'i maganar da alamun damuwa". Hassana cikin cije baki ta ce, "A'a Mommy ". "Haba daughter me yasa zaki b'oyemin bacin gashiinan sai cije-cije kiki, bari in kira doctor ya duba minke". Hassana rik'e wayar Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Mommy karki kira doctor dan Allah, nina san maganin nan ne irin narannan akasa a abincin nan, dan iri d'aya da yadda nake ji ayanzu haka". Hajiya Turai cikin mamaki ta kalli Hassana ta ce, "Daughter magani kuma?, wani maganinin?, waya zuba muku maganin?". Hassana da sai yanzu ta ankara da barin zancan da ta yi, shiru ta yi. Hajiya Turai ko kuma maimaitama Hassana tambayarta ta yi, ta ce, "Daughter kimin bayani mana kinyi shiru?, bangane ta kan maganganunki ba, waya zuba muku magani?, kuma maganin me akazuba muku?, karki damu kinji daughter yi min bayani nima nasan wasu abubun da ke faruwa, amma ba duka ba, fad'amin waya zuba muku maganin?". Hassana cikin sanyin muryarta, ta ce, "A'a Mommy ba wai ina nufin anzubamana magani bane, amma dai irin yanayin da Oga Habib ya ke a yau, da irin wanda ya shiga kwanaki iri d'aya, kuma nima iri d'aya da wanda na tab'a shiga". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Shi maganin da ke magana wana irine? , kuma waya baki maganin?,". Hassana cikin na tsuwarta ta cigaba da zuboma Hajiya Turai bayani kamar haka, "Mommy ranar da nafara ba Oga Habib maganin sha biyun dare, tom aranar Aunty Farida har na tafi sai ta biyoni da magani wai kince in sha in ba Oga Habib ya sha, sai na yi mamakin abinda Aunty Farida ta ce, jin harda ni, amma koda na tambayeta na ce, Aunty Farida ni kuma, sai ta ce min wai itama ta sha, kuma anba kowa yasha, wai ni na wane wannan zan sha, ta tsareni nasha agabanta, ta ban na Oga Habib in bashi, kafin in ba Oga Habib nashi maganin sai nake jina wani iri duk ba dad'i, kafin wani lokacin nakasa ba wanda taban inba Oga Habib. Washe gari ta ke tambayata wai me Oga Habib ya yi min nace mata ba komai ta ce min wai k'arya ne, nan dai da na rantse mata sai ta yarda, shine ta ce amma ban bashi maganin da taban ba in bashi, na ce mata Eh, amma yau zan bashi, nan tai ta min fad'a harda mari". Shiru Hassana ta yi, sannan ta ci gaba da cewa, " kuma Mommy ranar da aka d'aura auran nan ma haka abin ya faru,ranar ma ta kawo min magani wai injiki in ba Oga Habib, tom Wallahi Mommy da nabashi maganin ranar ma baki gani ba, Allah ne yakwaceni daga hannun shi. Washe gari shima tazo tana tambayata wai Oga Habib ya kusan... ". Shiru Hassana ta yi dan sai taji maganar tayi nauyi, bazata'iya maimai kalar tambayar da Farida tai mata ba". Hajiya Turai ko tun kusan farkon maganar Hassana ta fahimci maganin da Farida ke ba Hassana ta ba Habib , sai dai abin sosai ya d'aure mata kai, da mamakin dalilin Farida nayin hakan. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce,".Daughter daga yau kikina jina ko, kar wanda ya k'ara baki abu ya ce injini kiba Habib ki amsa ki ka yi amfani da shi". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "kin iya girki? ". "Eh Mommy na iya". "Tom daga yau gudin samun matsala ki rik'a muku girkinku acan, kar wani ko wata ya kuma baki abu ya ce injini, ki amsa ki yi amfani da shi batare da sanina ba, yanzu jeki watsa ruwa ajikinki, sai in kira doctor ya dubaki ". Hajiya Turai Family doctor su ta kira ya duba Hassana. Magunguna kawai na kuzarin jiki ya bata, dan kafin yazo abinda ta ke ji ta ji sauk'in shi sakamakon ruwan da ta watsa. Hassana na fitowa Hajiya Turai ta bata wata abayarya ta saka, duk da ta yi ma Hassana yawa. Hassana na gama shiryawa ta tada sallar la'asar, tana idarwa a kan sallayar bacci ya kwasheta. Hassana ba ita ta farkaba sai gab da magriba ta tashi, tana tashi ta shiga toilet tai alwallar magriba. Hassana ta idar da sallar tana nan zaune kan sallayar Hajiya Turai ta shigo". Hajiya Turai cikin damuwa ta kalli Hassana ta ce, "Daughter anya ko lafiyar Habib k'alau kuwa? , saboda tun d'azu fa bai tashi daga inda ya ke kwance ba". Hajiya Turai ta idasa maganar cikin damuwa". Hassana ma cikin sauri ta tashi daga kan sallayare tana mai nufar hanyar falon ta ce, "Mommy muje in gani?". Hajiya Turai bayan Hassana ta bi". Hassana na zuwa ta durk'usa inda Habib d'in ya ke kwance, Hassana a hankali ta rik'a kiran sunan shi, tana cewa, "Oga Habib! Oga Habib!! Oga Habib!!! ". amma shiru.Hajiya Turai da tafa rasa na tsuwarta kuka ta fara yi". Hassana ganin Habib ko motsi bai yiba, ya sa itama hankalinta ya fara tashi, hakan yasa ta sa hannu tana bugun bayan Habib d'in da d'an k'arfi, tana cewa, "Oga Habib dan Allah katashi mana". Hassana d'ago kan Habib d'in ta yi da ya ke ak'asa ta d'ora a kan cinyarta, tana mai cigaba da girgiza shi hankalinta a tashe". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter kawo min ruwa cikin fresh". Hassana tashi zata yi da niyyar d'akko ma Hajiya Turai ruwan, Habib ya rik'e Hassana ". Daga Hassana har Hajiya Turai mamaki su kai . Hassana kallan Habib ta yi ta ga idonshi rufe ya ke, hakan yasa ta kira sunan shi, ta ce, "Oga Habib! ". Still idon Habib a rufe idan ka saurara zaka ji yana nishi kad'an-kad'an". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ko dai maganin nan ya yi mai 'illa ne? ". Shiru Hassana ta yi tana kallan Habib d'in da ke juya kan shi akan cinyarta da takwantar da kanshi. Hannu Hassana ta kai da niyyar ta garama Habib d'in kwanciya ajikinta, amma sai ta ji kanshi zafi rau. Hassana kallan Hajiya Turai ta yi da alamun damuwa ta ce, "Mommy Oga Habib baida Lafiya , ki tab'a jikinshi kiji zafi". Hajiya Turai tab'a jikin Habib ta yi taji zafi sosai, dan ko tab'a Habib d'in da ta yi kawai ya barta ta san ba lafiya, dan inda da da lafiyar shi ba kamar yau ba, ba ta isaba ta tab'a shi". Hajiya Turai likitan da takira ya duba Hassana shi ta kira ya duba Habib. Yana zuwa ya yi ma Habib duk aune-aunan da suka kamata, amma shiru Habib bai hana ba, dai dai ya kallesu da ido sai ya koma ya kwanta. Likitan ko Magunguna ya je ya kawoma Habib d'in na zazzab'i da na ciwan kai. Babu yadda likitan bai yiba dan su d'auki Habib su mai dashi ciki amma yak'i, dan acewar likitan sanyin k'asan zai kara mai zazzab'in". Bayan likitan yaba da Magungunan da za a ba Habib d'in ya tafi. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Daughter tom ya zamuyi mai da kwanciyar k'asan nan? ". Hassana cirema Habib kan shi ta yi da ke kan jikinta. Tom dama da yake jikin k'ofar bedroom d'in Hajiya Turai suke ta yi sauri ta shige bedroom d'in Hajiya Turai". Habib haka ya tashi yana layi kamar d'an k'waya ya bi Hassana. Hassana gudin kar Habib ya fad'o mata ta yi sauri ta kwanta kan gadon Hajiya Turai, dan tasan in ba haka ba, zai iya cewa zai kwanta kanta". Allah sarki Habib bayan Hassana yabi ya kwanta, yana mai rik'e ta da d'ayan hannun shi. Hajiya Turai bayan su tabiyo". Hassana ko naganin Hajiya Turai ta yi sauri ta yunk'ura ta tashi zaune, dan sai taji kunya sosai yadda Hajiya Turai ta ganta kwance kusa Habib ga shi duk ya wani kananna d'eta. Hajiya Turai maganin ta mik'ama Hassana ta ce, "Daughter ga maganin shi ki bashi, bari inje site d'in shi in d'akko mai rubutunshi ki bashi, yau dai banda na safe duk bai ma shaba". Hajiya Turai fita ta yi ta nufi site d'in Habib ta d'akko mai rubutun shi". Hassana kallan Habib ta yi, tana tunanin yadda zata yi taba shi magungunan, dan babu yadda zatai mai ya tashi. Hassana maganin ta d'akko ta ce, "Oga Habib bud'e bakinka ka sha magani". Hassana ta fad'i maganar tana nufar bakin Habib. Hassana tusama Habib maganin ta yi, ta tada kan shi ta zuba mai ruwan faron da Hajiya Turai ta had'a mata dashi, da kyar Hassana ta samu da dabara ta rik'a sakama Habib maganin tana zuba mai ruwa ahaka-ahaka ya shanye magungunan". Hassana na gama ba Habib maganin Hajiya Turai ta shigo da rubun Habib d'in. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi da ke gefan Habib zaune Habib kuma na kwance ya yi matashi da cinyarta. Hajiya Turai rubutun ta mik'ama Hassana ta ce, "Daughter ga rubutun ki bashi". Hassana cikin taushin murya ta ce, "Mommy Wallahi magungunan ma da kyar ya sha kibar rubutun sai gobe". Hajiya Turai da tom da amsa ma Hassana badan ta saba, sai dan kawai ta lura da Habib d'in basha zai ba, dan ma Hassanar nada k'ok'ari. Hajiya Turai kallan Hassana ta ya, ta ce, "daughter karki bacci bari in kawo miki tea ki sha". Hajiya Turai da kanta ta had'ama Hassana tea ta kawo mata. Sannan jamasu k'ofar ta baya tai masu good night". Hassana sosai ta ji dad'in tea d'in da Hajiya Turai ta kawo mata. Bayan Hassana ta gama shan tea d'in ne ta cire kan Habib da ke kan cinyarta ta kwanta gefan shi". Cikin dare zazzab'i sosai ya rufe Habib sai makyarkyatar sanyi ya ke, irin ta masu zazzab'i. Hassana cikin bacci ta ke jin yadda Habib ke kyarma yana k'ara shishige mata. Hassana farkawa ta yi, tana mai kai hannu kan jikin Habib d'in ganin yadda ya ke rawar sanyi, zafi sosai Hassana ta ji jikin Habib d'in, Hassana cikin tausayin Habib ta kuma rungume Habib ajikinta sosai, tana mai jan bargo ta rufe su, tana cewa, "Sannu Oga Habib Allah ya baka lafiya, nasan duk wannan maganin ne da kasha ya yajazama wannan zazzab'in , Allah yasakama, Sannu kaji. ". Habib da ke kwance kusan rabin jikinsa ana Hassana amai ya ke sosai kusan ajikin Hassana. Hassana cikin rud'ewa da ganin halinda Habib ya ke ciki ta tashi zaune tana mai rik'e shi, tana aikin mai Sannu". Hajiya Turai ko cikin bacci ta ji yo k'arar aman Habib. Cikin tashin hankali Hajiya Turai ta shigo d'akin. Hajiya Turai kan gadon ta hau, tana mai rik'e Habib d'in itama ". Hajiya Turai da Hassana suna rik'e da Habib sai da ya amaye duk abinda ke cikin shi sannan ya koma ya kwanta yana nufarfashi". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi cikin damuwa, ta ce, "daughter meke damun shi ne? ". "Mommy daga zazzab'innan dai shine fa ya kuma kama amai". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "ki shiga toilet ki wanke jikinki bari in ciro miki wata rigar saiki sa, inda ya amaye maki taki, kamarke kikai amman, shi babu komai ajikinsu, Sannu kinji daughter Allah ya biyaki da mafificin alkairinsa". Da ameen Hassana ta amsa, sannan ta tashi da niyyar shiga toilet ta wanke jikinta Habib ya rik'e hannunta". Hassana kallan Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Mommy ban rigar in sa hakanan Oga Habib bazai barni in tashi ba". Hajiya Turai abayar irin ta maka single d'in nan taba Hassana, sannan ta yaye abuwan gadon da Habib ya b'ata ta fita da su, sannan ta d'akko wani bargon ta mik'ama Hassana, tai mata good night ta wuce". Hassana koda ta sake tab'a jikin Habib sanyi ta ji sosai, alamun zazzab'in ya sauka, Alhamdulillah ta ce sannan ta ja masu bargon ta rufe su". Washe gari Hassana sai 6:50Am ta farka, da sauri ta sako gado ganin gari ya yi haske, Hassana na sakkowa mutuminta ya biyota. Alhamdulillah dan yauma tare sukai alwallah duk yadda ta yi ya yi, Hassana ko ga yadda taga Habib na kazar-kazar d'in shi tasan sauk'i ya samu". B'angan Farida ko tunda taji ihun Hassana tana nai man agaji, ta shirya ta bar gidan, dan cewar ta zatafi farin ciki tazo ta iske Habib ya yi ma Hassana irin wujijjigar da yake ma mutane, ala bashi sai ta taho maganin da malam ya ce zata bar gidan da kanta ba sai an koreta ba, indai aka zuba shi ta taka ko ta k'etare". Washe gari Farida da wuri ta yi sammakon dawowa, sai dai abinda idonta ya gane matane ya tada hankalinta, Hassana da Habib zaune a derning space, suna break fast, hannu Habib rik'e da na Hassana, ga Hajiya Turai gefe guda. Farida cikin rud'u ta juya zata fita, Hajiya Turai kallanta ta yi, ta ce, "Farida zonan!! ........... .. ✍️ Idan kin karanta d'aure ki yi Comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Shafi na 44&45. Farida gefan Hajiya Turai ta je, ta tsaya ta ce, "Mommy gani? ". Hajiya Turai ta dad'e tana kallan Farida sannan ta ce, "Farida daga ina kike? ". "Daga gidan Mommyna". Shiru Hajiya Turai ta yi, tana kallan Farida sannan ta ce, "Farida kina so ki canza hali,saboda da duk inda zaki kina sanar min, amma yanzu sai dai ki fita kai tsaye, tom kar hakan ya kuma faruwa kar ki sake fita kibar gidannan bada sanina ba,ke koda ban gari karki kuma". Hajiya Turai na kai haka ta ce, "zaki iya tafiya". Farida fita ta yi tana mai jin zafin Hajiya Turai ta na tuhumarta inda ta je gaban Hassana". Hassana ko bayan sun gama break fast, kallan Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Mommy bari in d'akko kayan da zan sa ina son zanyi wanka". "A'a ki kama Habib ku tafi tare, abu daga zuwa gaisuwa ai anyimin k'ok'ari nagode". Hassana ta d'an jima zaune, sannan ta tashi ta kalli Hajiya Turai ta ce, "Mommy zan tafi, ina so zanyi wanka ne? ". "Tom daughter nagode sosai,dan Allah arik'a kulawa da rubutun Habib inda muna ta k'ara ganin sauk'i ". Cewar Hajiya Turai. "Insha Allah Mommy ". Hannun Hassana cikin na Habib a haka suka jera suka koma part d'in Habib. Hassana na zuwa ta shiga wanka ita da mutu minta, inda ta cire mai shirt d'in jikin shi da dogon wandon jeans d'in shi, ta bar shi daga shi sai d'an garami na ciki. Suka shiga tare kamar yadda suka sabo, Hassana sai da ta gama wankanta sannan ta kalli Habib da ke ta famar jagwalgwalan wankan shi. Hassana amsar sosan ta yi daga hannun Habib ta wanke mai jikin shi tass, sannan suka fita". Hassana lotion ta d'akko zata shafa, Habib ya mik'o hannu zai ta tsa kamar yadda yaga tana yi. Hassana d'akko ke man tayi tab'oye tana ta tsa kad'an-kad'an tana shafama jikinta, saboda Habib ko ta bar mai ba shafawa ya ke ba, wasa kawai ya ke yi da shi. Hassana sai da ta gama shafa man, sanna ta shafama Habib shima, tana gama shafa mai ta ciro mai wasu kayan ta sa mai kamar yadda ta saba sa mai tanayi tana rintse ido gudin kar tai mugun gani, tana gama sa mai kayan shi ta bashi rubutun shi yasha". BAYAN SATI D'AYA. Yau sati d'aya kenan da zuwan Hassana part d'in Hajiya Turai ita da Habib, kuma tun daga ranar bata k'ara zuwa ba, sai dai Hajiya Turai kullum zata shigo ta ga jikin Habib. Maganar abinci ko Hajiya sosai ta jama Maimaina kunne akan karta kuskura ta ka mata da aikata mata rashin gaskiya, Hajiya Turai duk da kunnan da ta jama Maimuna hakan bai mata ba, duk lokacin Maimuna zata yi girki takan je gun ta zauna. Farida ko Hajiya Turai ta hana ta fita gaba d'aya, dan tana jin tsoran fitarta gani ta ke kamar wani abun zata iya zuwa ta yima Habib". B'angaran Farida ko, sosai ta shiga damuwa da fitar da Hajiya Turai ta hanata yi yanzu,Hassana sosai ta dage wajan kula da Habib, dan yanzu ta gama sabawa da mak'ale mata d'in da Habib ya ke yi, na duk inda zata ya ke binta, toilet ko ta gama sabawama da binta d'in da ya ke yi. Sosai Hassana ta ke kula da ba Habib maganin shi, duk da dai har yanzu babu wani cigaba da suka k'ara gani game da Habib d'in, sai dai yanzu babu ruwan shi da kowa. Yanzu haka Hassana zaune ta ke tana ba Habib magungunan shi, Hajiya Turai ta shigo, Hassana cikin jin dad'in ganin Hajiya Turai dan ta fara sakin jikinta ta ita, ta ce, "Oyoyo ga Mommy ". Murmushi Hajiya Turai ta yi, sannan ta zauna kusa da Hassana, Hajiya Turai waya ta mik'ama Hassana ta ce, "Daughter ga wayar nan kirik'eta a hannunki zan rik'a kiranki akoda yaushe inajin jikin Habib, gurin aiki sun matsamin da kira, yau zan tafi jirgin 6:00 pm zan hau" .Numfasawa Hajiya Turai ta yi, sannan ta ci gaba da cewa, "Daughter zan sama muku kayan abinci a kitchen ki rik'a girka muku, kinga yanzu bananan, duk da dai na hana Farida fita ko ina, daughter ki kula sosai dan Allah,Farida kuma duk lokacin da ta kuma zuwa ta sa meki tai miki magana ki fad'amin, kuma karki yadda ta kuma baki wani abun ta ce injini kiba Habib ki amsa". Sosai Hajiya Turai taita ankarar da Hassana wasu abubun, duk da bata fito fili ba ta fad'a mata dalilin ciwan Habib d'in ba". Hajiya Turai fita ta yi tasa aka shigomasu Hassana da duk wani abinda zasu buk'ata na girki, aka samu su a kitchen d'in Habib, sannan Hajiya Turai ta kalli Hassana ta ce, "daughter bari zan shirya nan da minti 30 zan tafi". Hajiya Turai cikin k'ank'anin lokaci tagama shirinta ta, sannan ta shiga part d'in Habib, Hajiya Turai cikin sanyin muryar ta ce, "Daughter na tafi kirik'a aje wayarki kusa da ke ". Hassana cikin sanyin murya mai cike da rauni ta ce, "Tom Mommy Allah ya kiyaye hanya ya kaiki lafiya". Haka Hajiya Turai ta tafi tana mai jinta duk ba dad'i, tana mai tunanin aje aikin kawai zatai ta zo ta zauna da d'anta". Haka Hajiya Turai wannan karan ta yi tafiyar duk bata jin dad'in tafiyar, ko da Bilya ya kaita airport Hajiya Turai kallan Bilya ta yi, ta ce, Bilya dan Allah karka manta da amso rubutun Habib duk k'arshe sati". "Insha Hajiya bazan manta ba". Hajiya Turai kud'i ta ba Bilya sannan ta tafi". Hassana ko jin abinda Hajiya Turai ta ce mata baza a kawo masu abincin dare ba yau, , ya sa Hassana na idar da sallar magriba ta shiga kitchen tai masu jolop d'in indomie". B'angaran Farida ko tana ganin Hajiya Turai ta tafi, ta kira Mahaifiyarta awaya, dama kuma Hajiya Murja ce ta ce ma Farida ta yi hak'uri da fita kamar yadda Hajiya Turai ta hanata, sai ta tafi inda ta kusa ta fiya. Hakan yasa Farida yin hak'urin dole ba dan ta soba. Hakan yasa Hajiya Turai na tafiya Farida tashirya ta nufi gidan Mahaifiyarta". Bayan Farida ta isa gidansu ne, Hajiya Murja kallan Farida ta yi, ta ce, "Farida ki ka ce min Yaron nan har yanzu bai kusanci yarinyar nan ba? ". Shiru Farida ta yi kamar ba za tai magana ba, sannan ta ce, "Mommy nifa banyi niyyar kuma mai mata maganarnan bama, na ce miki babu abinda ya shiga tsakanin su, kuma Mommy ni daga yau bazan k'ara zuwa gurin Malamin nan ba, wai shi mai biyan buk'ata dol..... ". Hajiya Murja saurin rufe ma Farida baki ta yi, ta ce, "Farida ki yi shiru mana, kibar fad'in haka, amma ni nasan Malam Mai biyan buk'ata dole ya iya aiki, kawai dai akwai kuskuran da aka samu, ki yi hak'uri ki tashi muje". "Kin san Allah Mommy bazan tafi ba na gama zuwa gun mak'ary.... ". Nan ma Hajiya Murja saurin k'ara rufe ma Farida baki ta yi, ta ce, "Farida kiban dama ta k'arshe daga wannan karan in dai mukaje gurin Malam buk'atarmu bata kuma biyaba, tom Nijar zamu tafi". Farida kallan Hajiya Murja ta yi, ta ce, "Kin d'auki alk'awari?". "Wallahi Farida dagaske nake miki, ni kaina nagaji da sab'anin nan da ake samu, yanzu tashi mu tafi, indai wannan karanma bai yi ba, sati mai zuwa Wallahi Nijar zamu tafi, kima kwantar da hankalinki, sai kin auri Habib koda ko abinda na mallaka zai k'are Wallahi sai kin aurai". Farida kwanciya ta yi jikin Mahaifiyarta cikin raunin murya ta ce, "Mommy kina ganin Hajiyar Oga Habib zata bari kuwa in auri Oga Habib? , ni fa 'yan kwanakin nan naga d'auke min kai ta ke, tabar zama dani ta yi fira kamar da, Wallahi mommy yanzu Hajiyar Oga Habib tafi ji da 'yar iskar yarinyar nan akaina". Farida ta idasa maganar tana kuka". Hajiya Murja cikin damuwa ta kama Farida ta ce, "Yi hak'uri My sweet daughter kibar zubar da hawayanki kinji, Hajiya Turai kuma nina san tana sonki, kawai dai tashin hankalin ciwan Habib ne yasa kike ganin kamar tana shashshareki, ita kuma Hassana sunan ta kome?, tana janta ajikine ganin yadda ta ke kula mata da Habib, amma karki damu, auran ki da Habib babu bashi Wallahi, tashi mu tafi gun Malam kinga dare nak'arayi, danma babu wani nisa". Hajiya Murja da Farida zaune agaban Malam mai biyan buk'ata dole. Bayan su Hajiya Murja sun gaida shine, Hajiya Murja ta ce, "Tom Malam ni dai ina d'aya daga cikin wa inda zasu yaba k'warewarka a aiki, dan kai min aiki ba d'aya ba, ba biyu ba, kuma duk naga biyan buk'ata, amma Malam wannan karan aikin yazu da matsala, dan har yanzu Yaron nan bai kusanci yarinyar nan ba, kuma gashi kace dole sai ya kusanceta shine makarin amintarshi da ita, tom amma Malam kaga yadda abin ya ke ta faruwa". Tun da Hajiya Murja ta fara bayani Malam mai biyan buk'ata dole ya ke ta zane-zane a kaskon da ke gaban shi, har ta kai bayanin ta, sannan shima ya tsaya daga zane-zanan da ya ke yi, sannan zuwa can cikin kausassar murya ya ce, "Wannan karan bada gunkuba aka samu matsala, daga Mahaifiyar yaron ce, ita ta taimakama yarinyar , ta tai maketa, ta kub'utar da ita daga hannun shi, amma bacin haka babu abinda zai hana bai kusan ceta ba". Hajiya Murja cikin sanyayyar murya irin ta masu rok'o ta ce, "Malam dan Allah atai maka aimana wani abun dan Allah ". Wani farin abu mai laushi ya mik'ama Hajiya Murja ya ce, "Ki barb'ata masu wannan a hanyar da zasu bi, ana so ne suk'etarashi, ke da kanki zaki ban labarin abinda ya faru". Hajiya Murja amsar maganin ta yi, tai ma malam godiya sosai sannan suka tafi". Bayan sun isa gida ne, Farida ta kalli Mahaifiyarta ta ce, "Mommy kin matsamin mun sake komawa gurin Malam mai biyan buk'ata dole na je, tom amma fa ki sani daga wannan Wallahi idan har Oga Habib bai kusanci yarinyar nan ba cikin wannan ritsin, tom tafiya Nigar fa ta kamamu, dan gobe zan yi abinda Malam ya ce, idan bai ba, jibi zamu tafi nijar dan haka kima fara shiri". "Karki damu Farida ai bana son Hajiya Turai ta zo ta iske yarinyar , kodan haka nima na dage, dan haka ba fata muke ba, idan har wannan karan ko ba ayi as'a ba shima, tom ashirye nake ki zo mu tafi Nijar d'in ". Washe gari Farida da wuri ta yi sammakon komawa gidan Hajiya Turai dan zuwa ta ida aikinta, tana zuwa direct ta nufi part d'in Habib, dan acewarta gudin kar Hassana ta ki fitowa har falon zata shiga ta barbad'a masu, inda taga yanzu Habib ya bar duka". Lokacinda Farida ta isa bakin k'ofar falon, dai-dai lokacin Hassana suka fito wanka ita da Habib, daga ita sai d'an k'aramin towel iya cinya, tana cikin tsane jikinta ta ji nocking, Hassana tunani ta fara tom waye, dan jiya Bilya ya tafi zaria, Hassana ta fiya ta yi ta ji waye dan tana tunanin ko Jimmmai ce. Hassana na zuwa bakin k'ofar ta tsaya ta ce, "Wacece..............✍️. Idan kin karanta d'aure ki yi Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ *ISTIGHFARI TANA SANYA NUTSUWA A ZUCIYA TANA KAWO BIYAN BUKATU WAJEN UBANGIJI UWA UBA KUMA ISTIGHFARI TANA BADA TICKET NA ALJANNA DIRECT. ALLAH KASA MU DACE* Shafi na 46&47. Farida da ke tsaye bakin k'ofa sosai ta ji zafin maganar Hassana, wai ita ta ke cema wacece. Farida danne zuciyarta ta yi, dan cikar burinta ta ce, "Hassana bud'e nice". Hassana ta gane muryar Farida sarai, amma sai ta nuna ma Farida bata gane ba, ta ce, "Bangane kice ba?, kece wa? ". Farida da ranta yagama b'aci cikin zafin rai ta ce, "Farida ce ki bud'emin zaki wani tsaya kina min shirman tambayoyi Saboda kina ganin kamar kin isa! ". Hassana daga can ciki, ta ce, "Ayyah Aunty Farida wai ke ce?". Farida cikin jin haushi ta ce, "Ke ki bud'emin mana, ko bikiji abinda nace ba ne?". Shiru Hassana ta yi, tana tunanin ma fita, sannan ta ce, "Ayyah dan Allah ki yi hak'uri duk da bangane mai magana ba, amma Hajiya kafin ta tafi ta hana komawaye yashigo inda Oga Habib ya ke, amma idan kanji haushi ki yi hak'uri dan Allah, ba laifina bane". Farida da ke tsaye tana sauraran Hassana tsabar al'ajabi ne yahana ta magana, zuciyarta ce ta bata amsa da cewa, "ki yi hak'uri ki fad'a mata kece mana, wata k'ila bata gane ki bane". Farida maganar zuciyarta ta bi, ta za wani uban tsaki sannan ta ce, "Ke da Allah can sakarya kawai 'yar k'auye wadda bata gane mutane, tom Farida ce ta gidannan". Hassana sosai ta ji zafin zaginta da Farida ta yi, amma sai ta shareta ta juya takoma ciki ta barta agun tsaye, dan tasan ba alkairi bane zai kawo ta, dama kuma Hajiya Turai kafin ta tafi ta jama Hassana kunne koda wasa karta ce zata bud'ema Farida ta shiga part d'in Habib, idanma tai magana ta ji ita ce, karta amsa mata. Dama kuma itama Hassana ko da taji Farida ce ba niyyar bud'ewa tai ba, kuma sai Faridar ma ta b'ata mata rai". Farida ko da ke tsaye tana jiran Hassana ta bud'e mata k'ofa ta ji shiru, Farida cikin d'aga murya ta bugi k'ofar ta ce"Ke wai bakya jine!? ". Nanma Farida shiru ta ji, hakan ya tabbatar mata da Hassana tama dad'e da tafiya ta barta tsaye tuntuni. Shiru Farida ta yi tana tunanin yadda zata shiga part d'in Habib ta barbad'a maganin. Farida matsawa ta yi daga jikin k'ofar kad'an ta kira Mahaifiyarta, Hajiya Murja a waya". Farida cikin k'asa da Murya gudin kar wani ya ji, ta ce, "Hello Mommy kina jina? ". Daga can b'angaran, Hajiya Murja ta ce, "Eh Farida inajinki, ya akai kin barbad'a musu maganin ne? ". Daga b'angaran Farida ta ce, "A'a Mommy Yarinyar nan ta fara rainani wai na yi nocking d'in door d'in part d'in Oga Habib yanzu, shine da tazo take ce min wai Hajiya ta ce karta bud'ema koma waye, shine yanzu nake tunanin yadda zan yi in shiga , dan bisa ga alamuma yarinyar kamar bata fitowa yanzu tunda Hajiya ta tafi, bale in zuba mata maganin ak'ofar d'aki, shine Mommy naki raki ki fad'a min yadda zanyi". Shiru Hajiya Murya ta yi, sannan ta ce, "ki kira Hajiya turan sai ki ce mata kin zone kina son gaida Habib, amma kinkira Hassana ta ke kome?, ta ce wai kin hana, ke kuma kina son ganin Habib kiga ya jikinshi ". Farida cikin jin dad'in shawarar da Mahaifiyarta ta bata, ta ce, "Yauwa Mommy bari in kashe in kira". Farida katse kiran Mahaifiyarta ta yi, ta kira Hajiya Turai, amma bata d'aga ba. Farida sai da taima Hajiya Turai kira goma amma ko d'aya ba tai picking ba". Hajiya Turai ko tana ganin kiran Farida da gangan tak'i d'agawa, dan ta tsani Farida Sosai, kawai dai ita Allah ya yo ta mai kawai cice sai kai ta cutarta ta. Hajiya Turai ganin Farida tak'i daina kiranta, kashe wayar ta yi gaba d'aya ". Farida ko koda ta k'ara kiran Hajiya Turai ta ji wayar kashe ba tai tunanin komai ba, dan atunaninta suna wani programs d'in ne, kamar yadda ta tab'a fad'a mata, in dai kakira kaga bata d'aga ba tom suna bakin aiki ne. Hakan yasa Farida ba tai tunanin komai ba, tunaninta ya bata kawai Hajiya Turai na bakin aiki ne". Farida Mahaifiyarta ta sake kira ta shaida mata ta kira Hajiya Turai bata d'aga ba, dan haka ta bata wata shawar". Hajiya Murya cema Farida ta yi,"Farida ki yi hak'uri zuwa anjima sai ki kuma kiran Hajiya Turai awaya, kin san in tana kan aiki bata amsa kira". Farida tom kawai ta ce ma Mahaifiyarya ta kashe kiran, Farida d'akinta ta shiga ta kwanta tana ta malele kuwa , dan jinta ta ke indai ba Hassana ta bar gidan ba, tom bata da sauran na tsuwa, bakamar yau ba da Hassana ta kuma in gizata, dan ta yi ran tsuwar sai ta nuna ma Hassana ruwa ba tsaran kwando bane. Farida da ke kwance da sauri ta ta shi Saboda wani tunanin da yazo mata, hakan yasa ta tashi da sauri ta nufi site d'in worker's d'in gidan".. Farida tsaye ta yi tana Waige-waige, tana nai man wadda tazo gani, cikin sa'a Farida ta hangota tana shanya. Farida da sauri ta k'arasa inda ta ke, cikin sakin fuska, Farida ta kalleta ta ce, Sannu ko? ". "Yauwa Aunty Farida Sannu". Farida cikin sakin fuska ba irin yadda ta saba yima worker's d'in magana ba, ta ce, "Yauwa dan Allah ya sunan ki". Jimmai da mamaki ya cika ta, tun zuwan Farida gurinta, ta ce, "Sunana Jummai". Farida cikin yaudara irin na wayayyun mata ta ce, "Wow nice name, tom dan Allah Jimmai wani tai mako zaki min, zan biyaki konawa ne, na zab'eki kimin wannan aikin ne, Saboda na lura duk gidan nan babu wadda ta fi kusanci da Hassana kamar ke, tom dan Allah Jimmai zaki min wani taimako ne, ba mai wani wuya ba ne".Farida maganin da ke jikin zaninta ta ciro ta mik'ama Jimmai ta ce, "Jimmai dan Allah zaki barbad'amin maganin nan ne, a part d'in Oga Habib". Jimmai ta ke tsoro ya kamata ta ja da baya tana mai mak'e hannunta ta k'i amsar maganin, dan sosai ta tsorata da jin abinda Farida ta ce". Farida ko ganin Jimmai ta tsorata da maganin da ta ke mik'o mata, murmushi ta yi, ta ce, "Malama Jimmai karkiji komai ba maganin cutarwa bane, na san dai kin san ina son Oga Habib, dan nasan duk wanda yake agidan nan yasani, tom maganin nan da kike gani Jimmai bana cutarwa bane, idan ma k'awarki kike ji, itama ba cutar da ita maganin zai yi ba, ni nai miki alk'awari babu abinda zai samu k'awarki, na naimi kimin hakane dan nasan ke kad'ai ce agidan nan ayanzu zaki iya shiga part d'in Oga Habib kai tsaye, dan Allah ki tai makamin ki amsa". Jimmai da ke tsaye al'ajabi ya isheta, amsar maganin ta yi tana ma jin tsoran karna cutarwa ne ya fara aiki akanta". Dubu goma Farida taba Jimmai , ta ce, "Wannan ba biyanki nai ba, sai kin cika aiki sannan nima zan cika ki da abin arzik'i kala-kala". Jimmai godiya taima Farida, ta amshi kud'in , Farida kuma ta wuce tana mai jin dad'in burinta ya kusa cika". Jimmai ko tana ganin Farida ta wuce ta yi sauri ta shiga toilet ta jefa maganin, dan acewarta idan na zutarwa ne k'ilama ita zai fara cutarwa ita da take rik'e da shi. Jimmai sai da ta jefar da maganin sannan ta ji hankalinta ya kwanta. Murmushi ta yi, ta ce, "Aunty Farida baki da arzik'in da zaki ban kisa in zutar da Oga Habib bare kuma Hassana, ya Allah na godema da ka ba ma wannan baiwar taka zuwa guna, bata je inda zata bata ba burinta ya cika, Allah kaika san mai take nema da yarinyar nan, Allah kakareta daga shairinta, duk abinda zata mata Allah ka mai da mata aniyarta". Jimmai zama ta yi gun tana sake yima Hassana addu'a, akan Allah ya kareta daga shairin Farida." WASHE GARI: Farida da wuri ta yi sammakon zuwa gun Jimmai jin shiru bata ga Hassana ba, dan acewar in dai magani ya yi Habib ya kusanci Hassana ai ya isa ace ta ji alamun motsin Hassana. In da in dai akan yadda Malam mai biyan buk'ata dole ya ce musu ne, Hassana da kanta zata bar gidan, wata zuciyar kuma sai ta ce mata" tom koma Hassana ta bar gidan baki sani ba ne bama". Hakan yasa Farida zuwa ta tambayi Jimmai. Farida har cikin d'akin su Jimmai ta shiga ta kira Jimmai". Farida kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Jimmai na ce kin ko zubamusu maganin? ". "Eh Aunty Farida na zuba". Farida cikin jin dad'i ta juya ta nufi part d'in Habib, Farida na zuwa ta yi nocking d'in k'ofar, ta ji shiru ta kuma yi nan ma shiru". Hassana ko lokacin ko tashi basu yi ba, dan takan dad'e tana addu'ar in ta idar da sallar asuba, hakan yasa idan ta koma baccin safe ta ke jimawa. Hassana cikin bacci ta ji bugun k'ofa, da saurinta ta tazo dan jin waye. Hassana na zuwa cikin murya mai kama da ta bacci ta ce, "Waye? ". Farida sumar tsaye ta yi, tana tunanin tom idan rannan ance Mommy ta ce ci Hassana yau kuma fa, yau dai daga ita sai Oga Habib, "anya ko maganin mutumin nan nayi?".Farida ta tambayi kanta, dan acewarta ba zai yuwu ba, ace haka na faruwa, sai dai in ko Malamin k'arya ne". Farida shiru ta yi bata amsa ma Hassana ba tabar gurin, tana zuwa ta kira Mahaifiyarta awaya ta ce, ta shirya gata nan zuwa kuma Wallahi yau babu abinda zai hanata zuwa Nijar, dama tun farko Mommy na ce miki bana son aiki irin wannan k'ila wa k'ala, tom gashi nan dai Oga Habib bai kusanci 'yar iskar yarinyar nan ba, dan haka gani nan yanzu ki shirya Wallahi bazan bari Hajiya ta dawo ta isketa a gidan nan ba". Hajiya Murja ko da bata da abin cewa wanda ya wuce ta yi biyayya da abinda Farida ta ce , ta ce, "Shikenan Farida ki zo tom dan nasan kona ce miki ki bari sai gobe ba bari zaki ba". Farida na zuwa ta iske Hajiya Murja ta shirya ita taje jira, direct suka nufi airport sai dai inda suka je sai dai jirgin da zai kai su Katsina suka samu. Cikin isshan lokaci suka isa katsina, tun a airport d'in Katsina suka samu maimotar da zata kai su Nijar ". Kasan cewar ba cancikin Nijar za su shiga ba , farko-farko ne yasa k'arfe hud'u na yamma suka isa gidan friend d'in Hajiya Murja wanda zata tai masu jagora zuwa gun bokan da zasu, in da dama ita ce ta tab'a yima Hajiya Murja hanyar shi". Kasan cewar friend d'in Hajiya Murja ta sanda zuwan su Hajiya Murja yasa a ready ta ke, suna isa babu hutawa babu komai, danma sunci abinci akan hanya".. Hajiya Bilki k'awar Hajiya Murja a motarta ta d'auki su Hajiya Murja ta kaisu har k'auyan da bokan ya ke". Koda suka isa sun iske layi dan har sai da suka jira, sannan suka shiga. suna zuwa ya dakatar dasu ya ce, cikin muryar shi mara dad'in sauraro, "mai buk'ata kad'ai muke son gani, bama son 'yan rakiya, ku jirata a waje". Hajiya Murja da Hajiya Bilki komawa sukai suka bar Farida kad'ai.".. K'urama Farida ido ya yi yana kallanta, dan har sai da Farida ta fara tsorata da kallan da bokan ya ke mata, sai zuwa wani d'an lokaci, ya ce, " me kike so ai miki, auran za'araba?, koko yarinyar ce kike so a kora daga gidan baki d'aya? ". Farida cikin zuciyarta ta ce, "Alhamdulillah kaji aiki". Sannan ta yi sauri cikin jin dad'i ta ce, "So nake araba auran kuma a kori yarinyar daga gidan baki d'aya, sannan ina son a dawo mai da hankalin shi ad'ora mai sona mu yi aure yana cikin hankalin shi ". Batare da bokan ya kuma cewa komai ba, wani magani ya d'akko yaba Farida, ya ce, "wannan zaki tauna shine ahaka zaki cinye shi, wannan kuma zaki wanke fuskarki da shi, wannan kuma zaki yarfa mai ajikine , ai dama ke ce kika haukata shi". Shiru bokan ya yi sannan ya ci gaba da cewa, "Magani na farko da nace miki zaki tauna, duk abinda kika ce, kina so agurinsa zai yi, zai ji maganarki fiye da ta Uwar da ta haifaima, a haka ne zaki bashi umarnin ya kuri ita yarinyar kuma ya saketa, magani na biyu da nace zaki wanke fuska da shi, shi kuma duk wani abun k'i da yake gani wanda ya hana shi sonki tom kamar shine kika wanke, magani na uku kuma wanda nace ki yayyafame, shine wanda zai dawo da shi hayyacinsa". Yana kaiwa nan ya ce, "mungama miki aiki, saura kud'in aiki zaki biya". Farida kud'i ta ciro masuyawa ta ajema bokan, sannan ta ce, "Amma abinda yake ban tsoro ta yadda zanga Oga Habib d'in, dan yarinyar bata barina shiga wajan shi? ". Wani magani ya d'akko ya ce, kikira sunanta sau uku, sannan ki sha wannan, harta bar gidan sai abinda kika ce zata rik'a yi, dan haka daga kince ta ta bud'e miki da sauri zata bud'e". Farida da d'i ya ishsheta , kud'i ta kuma d'ebowa ta ba bokan, sannan ta tafi tana mai farincin nasara".. Farida a cikin mota ta samu su Hajiya Murja suka tafi, gidan Hajiya Bilki. Inda suna tafiya Farida na basu labarin yadda su kai da bokan. Hajiya Bilki ce ta ce, "Ai Farida karki damu tunda kikazo gun kafin gobe..., ai aikinki yagama biya, tun-tuni da muntab'a wannan hirar da Hajiya Murja ai da tuni kin auri Habib angama, nan dai suka ta hirarsu har suka isa gidan Hajiya Bilki inda a nan za su kwana sai gobe zasu wuce". Haka ko akai, washe gari da wuri su Farida suka kama hanyar Katsina, dan daga inda suka je zuwa airport akwai nisa". Su Hajiya Murja sai dare suka shigo Abuja, Hajiya Murja ganin dare ya yi , ta tsare Farida ta kwana awajanta". Washer gari da sassafe Farida ta yi sammakon zuwa gidansu Habib. B'angaran Hassana ko, tun jiya ta kasa gane kan mutuminta, sai wani irin bacci ya ke, duk yau kuma tun safe yak'i cin komai, tayi- tayi yak'i ci, yana cikin baccin ita kuma lokacin tana kitchen tana k'ok'arin had'a musu dinner ta ji wani irin k'ara wadda sai da k'arra ta firgitata, hakan yasa ta rigo da gudu daga kitchen d'in, ta nufi bedroom d'in Habib, tana zuwa zaune ta iske Habib tsayiyar gado yana dafe da kanshi da hannun wanshi guda biyu, yana jijjuya kan yana rirrintse ido. Hassana na zuwa ta hau kan gadon cikin rud'u da yanayin da taga Habib d'in, Hassana na zuwa ta rik'o Habib d'in tana tofa mai duk addu'ar da tazo bakinta. Can Hassana ta ji Habib ya yi wata uwar gyatsa da k'arfi. Can kuma sai taga ya saki kanshi da hannu wanshi da yasa ya daddafe kai d'in ". Habib d'ago da kanshi ya yi yana kallan Hassana. Hassana kuma cikin jin dad'in ganin Habib ya bar abinda ya ke, da alamu ya ji sauk'i, ta rungumo shi, ta ce, "Ayyah Oga Habib Sannu ko, tsakanin jiya da yau kana shan wahal...... ". Hassana tsawar da ta ji ce tare ta turota k'asan da Habib ya yi yasa bata k'arasa abinda ta ke fad'aba". Allah sarki Hassana bata damu da abinda Habib ya yi mata ba, ta shi ta kuma yi zata hau gadon, Habib ya kuma daka mata tsawa , wadda tafi waccan, ya ce, "Ke ! , wacece ke!?, kuma me kike yi anan? ". Hassana cikin tsoro da al'ajabi ta ke kallan Habib, dan idan taji da kyau sai taji kamar Habib ne yake magana, kuma kamar yadawo hankalinshi abisa ga yadda ya ke maganar............ ✍️ Tofa wai meke faruwa ne, Habib kamar yadawo hankalin shi nake gani🤐🤐🤐🤐. Ga kuma su Hajiya Farida da tarin Magunguna ko ya abin zai kaya???. Idan kin karanta daure ki yi Comment sister, Comment ke k'aramin kwarin gwiwar update da wuri. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI. https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Lale watan alkairi, watan da ummulkairi, Amina zatil fatahi ta haifi d'a al sugaba, lale watan da duka aljanu suke ta ce wa sun bani dan basu k'ara ci gaba. Yau ne sha biyu ga watan rabu Auwal, wata mai girma mai daraja, watan da fitayyan halitta yazo duniya, Allah kak'ara mana k'aunar annabi Muhammadu (S, A, W). Happy maulud. Shafi na 48&49. Hassana cikin murna da manta waye Habib, ta kalli Habib, tana mai k'okarin k'ara hawa gadon, ta ce, "Wayyo Oga Habib ka warkene ko ko magana ce ta samu? ". Hassana ta fad'i maganar tana mai saurin rik'o hannun Habib d'in. Habib ko da al'ajabi ya bi Hassana da kallo". Hassana ganin haka, yasa ta d'an girgiga Habib ta ce, "Wayyo Oga Habib kafara magana ko? , dan Allah ka ce wani abu, ko zanji dad'i". Habib da ke zaune yana jin maganganun Hassana mamaki ne sosai ya cika shi, wanda yasa ya kasa cewa komai, hakan yasa yafara tunanin wai lafiya ko dai mafarki ya ke, idan kuma mafarki ne tom wacece haka tazo mai da siffar da bai sani ba". Hassana ko ganin Habib ya yi mata shiru yana kallanta, yasa ta kuma kai hannu da niyyar ta girgiza shi. Wani ma haukacin mari Habib ya wanke Hassana dashi yana mai sake turota k'asa, ya ce, "Wacece ke?, kuma me ya shigo da ke nan? ". A hankali sosai Habib ya ke maganar. Hassana da marin Habib ya farkar da ita ta dawo hayyacinta, da fe inda Habib ya fareta ta yi, tana kallan shi da idonta da ya kad'a ya yi ja". Habib ko cikin d'an d'aga murya ya kuma cewa, "Fita ki bar nan kafin inyi k'asa-k'asa da ke! ". Still Hassana na tsaye dan ko motsawa bata yi ba, daga inda ta ke. Take Hassana ta shiga wani hali mai wuyar fita, dan indai dai-dai ta ke gani, kuma jinta ma dai-dai ya ke, tom tabbas Habib ya samu lafiya, dan ko daga kalar kallan da yake mata, hakan ya tabbatar mata Habib ya dawo hayyacinsa". Habib ko ganin Hassana kamar bajin abinda ya ke cewa ta ke ba, sakkowa ya yi daga kan gadon, ya na kallan Hassana cikin ido, ya ce, "Wacece ke?, kuma me yakawo ki nan?, nace ki fita ko! ". Hassana cikin rawar murya ta fara magana, da cewa, "uhm ba komai". "Ba komai ".Habib ya mai-mai ta. Hassana d'aga ma Habib kai ta yi, ta ce, "Eh". Kasan cewar rashin k'arfin da Habib ba ya ji ajikin shi koka d'an, dan ji yake kamar zai fad'i, dan ko maganar da yake ma Hassana da kyar yake mata ita, hakan yasa batare da Habib ya kuma cewa komai ba, ya nuna ma Hassana k'ofar fita da hannu, shi kuma ya koma bakin gadon ya zauna yana mai dafe kan shi". Hassana juyawa ta yi ta kama hanyar fita bedroom d'in Habib, har ta kai bakin k'ofa ta juyo ta kalli Habib d'in da yake dafe da kanshi yana rirrin tse ido. Hassana da sauri ta dawo cikin bedroom d'in, dan ita har yanzu bata gama yadda Habib ya warke gaba d'aya ba. Hassana cikin damuwa da yanayin da taga Habib d'in ta kamo hannun Habib d'in ta ce, "Ayyyah Oga Habib Sannu, nasan yunwa kake ji, inda yau kak'i cin komai, in kawo ma abinci kaci? ". Habib da mamaki ya d'ago kai yana kallan Hassana, gashi abin haushi yana jin kamar baya iya magana, tsananin ciwan da kanshi ya ke. D'agowar kan da Habib ya yi Hassana ta kalli k'wayar idon shi ta ga ta yi jawur. Hassana cikin tausan Habib d'in kamar zatai kuka, dan ita harga Allah bata mai kallan wanda ya warke gaba d'aya, kawai dai tana mai kallan ciwan nashi ya canza sifiri ne. Hakan yasa Hassana ta kuma cewa, "Oga Habib in kawo ma abinci ko? ". Hassana ganin Habib ba amsa mata zai yi ba, yasa ta rabu tashi ta je kitchen ta zibo mai jolop rice d'in da ta yi, ta kawo mai, dan dan tun jiya take fama da Habib akan cin abinci yak'i". Hassana kusa da Habib ta zauna ta d'ibo abincin a spoon, kamar yadda ta saba yi ma Habib d'in wani lotun, ta ce, "Oga Habib bud'e bakinka please kaci ko kad'an, kaga tun jiya baka ci abinci ba". Habib ko da ciwan kai ya dama, da mamaki ya ke kallan Hassana ga magana ma wuyar yi ta ke mai. Haka nan Habib cikin k'arfin hali ya ce ahankali canciki, "Kin san Allah idan har biki bar d'akin nan ba, na tashi,,,,, ". Habib ya k'arasa maganar da girgiza kai". Hassana aje abincin ta yi, tana mai k'ara gasgata maganarta ta Habib ya warke. Hakan yasa Hassana aje mai abincin ta juya ta fita. Hassana wayar da Hajiya Turai ta bata ta d'auka, ta kira Hajiya Turai, Allah ko ya tai maka, kira d'aya Hajiya Turai ta d'aga". Hasssana cikin murna, ta gaida Hajiya Turai, bayan sun gama gaisawa ne, Hassana ta ce, "Mommy Wallahi Oga Habib ya warke,yanzu haka maganar da nake yi dake Oga Habib na magana". Hajiya Turai cikin tsantsar farinciki ta ce, "Daughter nasan ba kimin wasa, dan Allah da gaske Habib d'ina ya warke?, kuma har kinji maganar shi? ". "Mommy Oga Habib ya warke tabbas, kuma naji maganar shi". Cewar Hassana. "Tom me yace miki, daughter? ". Hassana shiru ta yi, dan sai yanzu ne ma taji zafin abinda Habib ya ce mata". Hajiya Turai ko jin Hassana ta yi shiru ya sa, ta ce, "Hello daughter kina jina, kuwa, ba Habib d'in wayar". Hassana koma wa bedroom d'in Habib ta yi, har yanzu Habib na zaune kamar yadda ta bashshi. Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Oga Habib Mommy na magana a waya? ". Habib d'ago kai ya yi yana kallan Hassana, sannan jin ta ce, Mommy ya amshi wayar ya kanga a kunne, duk da yana jin kamar ba zai iya magana ba". Hajiya Turai ko, cikin k'osawa ta ce, "Hello Habib kana jina? ". Habib cikin dauriya da jarumta da yadda ya ke ji, ya ce, "Eh Mommy inaji". Hajiya Turai cikin murya mai kama da ta kuka ta ce, "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! alhamdullah!!!, Allah nagode maka da kanuna min wannan rana, Habib kana jina? ". "Eh Mommy inaji". Habib magana ya ke so yima mahaifiyar tashi doguwa, amma ya kasa, tsabar ciwan kai". Hajiya Turai cikin Sanyi ta ce, "Sannu Habib Allah ya baka lafiya baki d'aya, ina nan da wowa gobe insha Allah, yanzu ba daughter wayar". Habib daughter ya mai-mai ta azuciyar shi, yana mamakin ita d'in wacece.Habib mik'ama Hassana wayar ya yi, yana mai nuna mata hanyar fita, alamun ta amshi wayar ta fita. Hassana amsar wayar ta yi ta fita, tana mai sauraran Hajiya Turai. Hajiya Turai ko ta ci gaba da cewa, "Daughter naji har yanzu bashi da lafiya, tom nasan Habib da gaddama mare in kira Family doctor mu ya duba shi, amma insha Allah gobe da wuri zan shigo". "Tom mommy Allah ya kawoki lafiya, mommy ki kira idan da akwai Wanda Oga Habib zai yarda ya kwana da shi". Cewar Hassana. Hajiya Turai cikin sauri ta ce, "Daughter ke fa? ". "Mommy wallahi ya ce in dai ya tashi ya ganni a d'akin zan sani, ni dai Mommy dan Allah part d'in ki zani in kwana". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Tom shikenan daughter amma dan Allah da safe ki yi k'ok'ari kizo da wuri ki duba shii, dama Bilya na nan ne, tom kinga Bilya na zaria, amma zan kira shi yanzu in ce mai yadawo gobe". Hajiya Turai kashe wayar ta yi". Hassana ko juyawa ta yi ta fita , ta nufi part d'in Hajiya Turai". B'angaran Habib ko da kyar ya iya tashi ya d'auki abincin da Hassana ta kawo mai ya ci. Habib na gama cin abincin wani wahalallan bacci ya d'auke shi. Shine fa Habib bashi ya farka ba, sai washe gari, dalilin Farida". Farida na shiga gidansu Oga Habib, tsayawa ta yi dai-dai k'ofar Falon Habib d'in, ta ciro maganin da boka ya bata ya ce, ta tauna duk abinda ta ce ma Habib zai yi. Aiko haka Farida ta ciro maganin ta tauna, sannan ta ciro wanda ya bata ya ce duk abinda tasa Hassana ba za ta yi mata gadda ma ba, shima ta tauna, sannan ta d'akko na wanke fuskar ta wanke fuskarta, shi kuma wanda ya ce, duk wani aibunta da ya hana Habib d'in ya so ta, tom kamar shine ta wanke. Farida nagama magungunan ta, ta fara nocking d'in k'ofar falon Habib da k'arfi". Habib da tun baccin jiya da ya kwanta bai tashi ba, bayan ya gama cin abincin da Hassana ta kawo mai. Habib cikin bacci ya jiyo yadda ake bun k'ofar, cikin mamaki da al'ajabi Habib ya tashi, Alhamdulillah yau sosai yaji k'arfin jikin shi, sai abinda ba'arasa ba, Habib cikin sauri yanu fa k'ofar dan ganin mara hankalin da yake mai nocking haka. Habib na zuwa cikin fad'a-fad'a ya ce, "Wa ye? ". Farida da k'osawa ta sa ta kasa fahimtar muryar waye, ta ce, cikin k'osawa, kuma ita ma cikin fad'a-fad'an dan ta zaci Hassana ce, ta ce, "Bud'e ki gani mana, 'yar rainin hankali, daga yau ne dai". Habib cikin b'acin rai ya bud'e k'ofar, yana kallan Farida fuska d'aure babu alamun fara'a ya ce, "Farida dama nafara wasa da ke? ". Farida cikin al'abi da mamaki ta ke kallan Habib, kai ko dai maganin da boka ya bani ne ya warkar da shi, tun kafin in sa mai, Farida kallan Habib ta yi tana sosa k'eya ta ce, "Oga Habib dama wata magana ce nake so muyi dan Allah ". Habib ko da mamaki ya kalli Farida, amma ganin sammakon da tayi, da kuma yana son tambayarta dan yana buk'atar amsar tambayar shi kafin Hajiya Turai ta dawo. Habib cema Farida ya yi, "Ok, inajinki? ". Farida ko najin haka ta kuma tabbatar da maganinta ya yi wato yana jinta, Lallai wata sabon gani, hakan yasa Farida dan k'ara tabbatarwa ta ce, "Uhm Oga Habib dan Allah mu shiga daga ciki mana? ". Habib batare da yayi ma Farida musu ba, yashiga, Farida kuma tabi bayan Habib tana mai tabbatar da aiki yagama yi". Habib kallan Farida ya yi, alamun inajinki. Farida cikin bada umarni, ta ce, "Oga Habib so nake ka saki Hassana yau-yau d'innan ". Habib da mamaki ya ke kallan Farida. Farida kuma ganin Habib na kallata ta ce, "Ko ba zaka iya bane? ". Habib shiru ya yi, na farko abinda ya bashi mamaki ganin yadda Farida ke mai magana cikin bada Umarni, na biyu kuma, tabbas yarinyar da yagani jiya ita ce Hassanar, idan ita ce, tom meye dangan takar shi da ita? ". Farida ko ganin Habib ya shiga kogon tunanin, ya sa ta kuma cewa, "Oga Habib dan Allah kai nake jira, kace ka saki Hassana saki Uku, idan Mommy ta tambaye ka kace mata kai bazaka iya zaman aure da ita ba, kai ni kake so". Habib dafe ganshi ya yi, dan tabbas ko a yadda ya ke jin jikin shi ya tabbatar mai akwai abinda ke faruwa dashi, jiya ya farka yaga wata atare dashi ad'akin shi, yau kuma wannan ma haukaciyar tazo tana mai wasu maganganu marasa ma'ana, Habib kallan Farida ta yi, ya ce, " Tom jeki zanyi". Habib ya ce ma Farida haka ne kawai dan baya son ya kuma jin wata maganar da zata k'ara mai wani tunanin, hakan yasa ya ce ma Farida, tom ta je zai yi".Farida fita tayi tana mai jin dad'in furicin Habib, dan tabbas aiki ya yi, dan idan ba haka ba, tasan Habib sare da yazun ya yi maganin ta". Habib ko zama ya yi shi kad'ai yama rasa kalar tunanin da zai yi, wai meke faruwa da shine?, me Farida ke nufi ne?". Habib wayar shi ya fara naima ya kira Bilya dan samun amsoshin tambayoyin shi. Babu inda Habib be duba ba, amma ba wayar shi. Toilet ya shiga ya yi wanka, bayan ya fito ne ya shafa lotion ajikin shi, sannan ya bud'e sip d'in kayan shi, amma abinda ya bashi mamaki kayan mace agefan kayan shi, Habib cikin al'ajabi da mamaki ya ke bin kayan Hassana da kallo. Habib daurewa ya yi ya kauda komai, ya ciro kayan shi ya sa, ya adana tambayoyin shi sai Hajiya Turai ta dawo, amma tabbas ya san akwai babban al'amari da ke faruwa da shi, ko kuma ya faru da shi, dan ko yana yin yadda yake jin jikin shi yana kuma tabbatar mai da hakan. Bayan Habib ya gama shiryawa, kitchen ya shiga, nanma yasha mamaki, nan ma dai haka ya kauda mamakin shi gefe ya had'a ma kanshi tea ya fito". K'arfe goma sha d'aya na safiya jirgin su Hajiya Turai ya sauka. Kasan cewar Hajiya Turai ta san Bilya baya nan, yasa ta d'au drop d'in mota ta kawota gida". Hajiya Turai direct part d'in Habib ta nufa. Habib na kwance ya ji nocking , ya zo sai dai sosai abin yazo mai a ba zata, dan bai yi tunanin dadowar Hajiya Turai yau ba , dan bata cewa gata nan tazo sai tai sati tana sa rana". Hajiya Turai cikin tsantsar farincin da ta kasa b'oyewa ta rungume Habib tana mai cewa, "Alhamdulillah, tabbas duk abinda ya yi farko zai yi k'arshe, kuma babu abinda ya gagari Allah, Sannu Habib Allah yasa wannan ce k'arshen wahalarka a duniya da lahira"."Ameen Mommyna, mu shiga ciki ki futa". Hajiya Turai tana rik'e da hannun Habib suka shiga ciki, Hajiya Turai zata zauna kenan, Habib ya ce, "Mommy karki zauna zoki ga wani abu". Hajiya Turai tashi ta yi ta bi Habib". Habib ko wajan sip d'in kayan shi ya kai Hajiya Turai, bud'e sip d'in ya yi, sannan ya ce, yana mai nuna kayan Hassana ya ce, "Mommy kayan Waye nan?". Hajiya Turai kallan Kayan Hassana ta yi, dake jere kusa da na Habib. Hajiya Turai kama hannun Habib ta yi, ta ce,............ ✍️. In kin karanta daure ki yi Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Shafi na 50&51. Hajiya Turai kama hannun Habib ta yi, ta ce" Habib ka yi hak'uri in nasamu natsuwa zuwa anjima sai mu yi magana". Habib da tom ya amsa ma ma haifiyar shi ba dan ya so ba, so ya yi ta bashi amsa yanzu. Hajiya Turai kallan Habib ta yi ta ce, "Bari in shiga ciki, zuwa anjima sai kazo muyi maganar inda naga ka matsu". "A'a Mommy ba wai na matsu bane, kawai dai ina mamakin yadda kayan mace ya had'u da kayana ne waje d'aya, kuma na farka naganta anan, tom shine abin ke ban mamaki, kuma duk bansan ta yadda hakan ta faruba, sannan yau Farida ta zo mun da wata magana wadda ta kuma tabbatar min da akwai wani b'oyayye al'amari da ke faruwa". Habib ya idasa maganar cikin damuwa. Hajiya Turai kallan Habib ta yi, sannan ta ce, "Shikenan ni zan shiga ciki, kasaman anjima kamar yadda na ce ma, sai muyi maganar". Hajiya Turai fita ta yi daga side d'in Habib ta nufi nata part d'in. Hassana na kwance tun da ta tashi da safe ta ke kwance kan caution, haka nan Hassana ke jinta wani iri duk ba dad'i, kamar a mafarki Hassana ta ji sallamar Hajiya Turai. Hassana cikin nuna murnarta naganin Hajiya Turai ta tashi ta zauna tana, "Oyoyo Mommy". Hajiya Turai murmushi ta yi tace, "Oyoyo daughter". Hassana cikin fad'ad'a fara'ar fuskarta suka gaisa da Hajiya Turai. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ya k'ok'ari na tafi na barki da mara lafiya, ikon Allah yau satina biyu kenan da tafiya". "Kai Mommy har kin yi sati biyu? ". Cewar Hassana. "Eh daughter, bari in shiga ciki in watsa ruwa in kwanta ". Hajiya Turai bedroom d'in ta ta shiga ta watsa ruwa sannan ta kwanta". Hassana ko haka taita juyinta kan caution, ita kanta bacin kayanta na side d'in Habib da wanka ta yi, amma tasan ko karan hauka ya cijeta ba zata iya zuwa ba ta d'akko ba. Hassana na nan kwance har aka kira sallar azahar, tashi ta yi tai alwallah ta tada sallah, Hassana na zaman tahiyar k'arshe Habib ya yi sallama ya shigo falon. Kan 2 seater Habib ya zauna yana jiran fitowar Hajiyarsa, dan a tunanin shi tana ciki tana sallah. Shiru-shiru Habib ya ji har yanzu Hajiya Turai bata fito ba, dan in sallah ta ke, yaci ace ta idar. Habib jin shirun ya yi yawa, yasa ya nufi bedroom d'in Hajiya Turai, kwance Habib ya isketa tana bacci Sosai, kamar karya ta data, amma ganin lokacin sallah ya yi yasa ya tada ta. Hajiya Turai kallan Habib ta yi ta tashi zaune tana mai ma mamakin ganin lokacin da ta d'auka tana bacci. Habib ma kallan Mahaifiyarsa ya yi, ya ce, "Mommy anyi sallah fa". "Subhallah!, wannan wana irin bacci nayi haka, da har akai sallah ban ji ba ". Hajiya Turai ta shi ta yi ta nufi toilet, saida ta kuma sama jikinta ruwa sannan ta yi alwallah ta fito, lokacinda ta fito Habib ya fita ya koma falo. Hajiya Turai sai da ta shirya ta yi sallah, sannan ta je falon, inda ta iske Hassana zaune kan sallaya, Habib kuma kwance kan 3 seater kan shi sama. Hassana da ke zaune tana jinta duk a takure ganin Habib a falon, cikin na tsuwa Hassana ta kalli Hajiya Turai ta ce, "Barka da fitowa Mommy ". "Yauwa daughter, Maimuna ta ko san da dawowa ta?, ko ta shigo da abinci ne?". "A'a Mommy bata shigo da abinci ba, ina jin bata san kin dawo ba". Cewar Hassana. Hajiya Turai waya ta ciro ta kira Maimuna, maimuna nad'agawa, Hajiya Turai ta ce, "Hello Maimuna ya naga har yanzu ba'a shigo da abinci ba". daga can b'angaran Maimuna tace, "Hajiya Wallahi ban san kin dawo ba, kuma yanzu ba girki akema Oga Habib ba, amma yanzu bari ayi da sauri, me za ayi Hajiya? ". " ki yi Simple food kawai". Cewar Hajiya Turai, sannan ta datse kiran". Hajiya Turai zama ta yi, sannan ta kalli Hassana ta ce, "Daughter zo ki zauna nan mana". Hajiya Turai ta nuna ma Hassana kusa da ita". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Mommy ina son zan yi wanka ne". "Tom ki je ki yi mana daughter, ki shiga toilet d'ina ki yi". Hassana tom ta ce, sannan ta ce, "Mommy kayana na can". Habib sai yanzu ya waigo ya kalli Hassana jin ta ce kayanta na can, wato ita ce ta sa kayanta cikin nashi". Hajiya Turai sanyi ta yi itama , ganin yadda Hassana ta yi sanyi kamar a takure ta ke, dan ko yana yinda ta ke magana kasan takure ta ke. Hajiya Turai tashi ta yi tazo har inda Hassana ta ke tamo hannunta ta ce, "zo ki je ki yi wankan ki, kinada kayan sawa nazo muki da kaya bari in aika a d'akko miki, nabar jakar kayan wajan mai gadi, lokacinda na iso mai gadi d'aya ne awajan get d'in". Hajiya Turai na rik'e da hannun Hassan suka shiga bedroom d'in Hajiya Turai. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Daughter ki saki jikinki mana, kinga ko yadda kike yi?, ko kina so Habib ya rainaki ne?, kina nufin Saboda Habib kike d'ari-d'arin nan?, tom banji dad'in ganinki haka ba, ina son in rik'a ganinki kamarda, in ma d'aurewrar Habib ce tom karki yi tunanin ko mai, nature na shi ne, haka Habib ya ke tun yana yaro, idan ba ni ba ko friend's d'in shi, tom zan iya ce miki babu wanda zakiga Habib ya zauna da shi suna fira, tun abin na damuna har ya ma daida damuna, kuma ak'idarsa ce ko nima bai cika min yawan magana ba idan yana ganin wani kusa, dan Allah daughter ki saki ranki ki dawo kamar da ". Bud'e baki Hassana ta yi za tai magana, Hajiya Turai ta rufe mata baki, ta sa mata d'an ya tsa abaki, ta ce, "ki shiga ki wanka daughter idan kin shirya sai muyi maganar da kike son yi". Hassana juyawa ta yi ta shiga toilet d'in, kamar yadda Hajiya Turai ta buk'ata. Ita kuma Hajiya Turai fita ta yi, ta sa aka d'akko mata jakar kayan da ta siyoma Hassana, ta kai ta bedroom d'in ta, ta ce, "Daughter ga kayan nan, naki ne duka kisa wanda kike so". Sanan Hajiya Turai ta fita ta koma falon. Hajiya Turai na zama Maimuna na shigowa ta ce, "Hajiya ko mai na dernin". "Ok, me kika dafa ne? ". Cewar Hajiya Turai. "Cous-cous". Maimuna taba Hajiya Turai amsa".. B'angaran Hassana ko tana fitowa ta shafa lotion d'in da taga Hajiya Turai ta aje mata, sannan ta bud'e jakar kayan da Hajiya Turai ta ce tata ce duka, Sosai Hassana ta ya ba da kyan kayan, dogayan riguna ne kala-kala da riga da siket na kanti, da gyalilluwa da ta kallama na sawa masu kyan gaske, Hassana ganin kayan da yawa wata doguwar riga red color da ta ji adon stone ta d'akko ta sa, sannan ta d'akko d'an kwakin rigar da yake babba ne ta yafa ta samu gu ta zauna, dan tafi son lokacinda zata fita ace Habib baya nan ya tafi". Can b'angaran Hajiya Turai ko jin Hassana shiru, tashi ta yi ta nufi bedroom d'in ta, zaune ta iske Hassana. Hajiya Turai girgiza kai kawai ta yi, sannan ta ce, "Daughter muje mu ci abinci, ke muke jira". Hassana bayan Hajiya Turai ta bi suka fita. Sai dai Hassana bata ji dad'i ba ganin Habib har yanzu yana falon. Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib muje ga abinci can". Habib b'ata fuska ya yi ganin Hassana kusa da Hajiya kenan harda ita zasu ci, Habib sharewa kawai ya yi badan ya soba ya tashi ya nufi derning space d'in". Hajiya Turai da kanta ta yi seven's d'in Hassana da Habib. Ba laifi Habib ya ci dadama amma Hassana tsakura kawai ta yi, Hajiya Turai dai na kule da Hassana, amma sai bata tanka mata ba. Bayan Habib ya gama cin abincin, kallan Hassana ya yi, ya ce, "Bamu gu zamu yi magana". Dama Hassana tun-tuni ta aje spoon d'in ta alamun ta k'oshi. Habib ko na cewa bamu gu, kamar jira ta ke ta tashi zata tafi. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce ,"daughter koma ki zauna". Hassana komawa ta yi ta zauna. Habib haka d'in da Hajiyarsa ta yi, shi kuma sai ya b'ata mai rai, acewar shi bazai magana gabanta ba, hakan yasa ya tashi ya ce, "Mommy please ina wayata zan yi amfani da ita ne? ". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ina wayar shi? ". Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Mommy tana sip d'in k'ayan shi". "Ok jeki d'akko mai". Cewar Hajiya Turai. Hassana tashi ta yi ta fita". Habib kuma ganin haka komawa ya yi ya zauna, ya kalli Mahaifiyarsa ya ce, "Mommy wai ita d'in Wacece?, kuma me ya kaita side d'ina da har zata aje kayanta anan?, wai Mommy taya haka ma ta faru bansani ba!? ". Habib ya fad'i maganar cikin damuwa. Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Habib wato abu mai girma ya faru da kai, idan zaka iya tunawa lokacinda zan tafi London ka ce min kana fama da wani irin ciwan kai, ahaka dai na tafi nabarka, mu kai da kai zaka je hospital adubaka, tom Habib bayan tafiya ta akakirani ake sanar dani wai baka da lafiya yanzu haka baka san inda kanka ya ke ba, kuma abinda ya tada masu Bilya hankali da sauran ma'aikatan wajanku sai ciwan yazo maka da duka, dan duk wanda ka rik'e sai an kwace shi , Hassana ka d'ai ya rinyarda ke aiki a Sanad yoghurt, yarinyar da ke zaune gidan nan, da ita ka d'ai kake yarda da ita,dan Habib ko ni da na dawo ban isa in shiga inda kake ba. Hassana kad'ai ke baka abinci ka ci, ita kad'ai ke baka magani kasha, ita kad'ai ke shiga inda kake ta zauna, amma in ba itaba duk wanda ya shiga sai an k'wace shi a hannunka, wannan da lilinne yasa na had'a ka aure da Hassana, dan ba zai yuwuba tana shiga inda kake har ta kwana a matsayinta na mace wadda ba muharramarka ba". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Tom kaji abinda ya faru Habib, amma abinda baka gane ba zaka iya min tambaya". Shiru Habib ya yi kamar ba zai yi magana ba, sai zuwa can ya ce, "Mommy ciwan hauka na yi kenan". Habib ya fad'i maganar cikin damuwa. "Eh Habib kusan haka za'ace, amma ai yanzu komai ya wuce sai dai kuma ka gode ma Allah da ya baka lafiya, da kuma Hassana , dan ita taima komai". Habib kallan Mahaifiyarsa ya yi ya ce, "Ko mai kamar me da me mommy? ". "Habib komai da kasani Hassana kema shi, danma wani abun da ka fara kwaikwayanta ne, aka samu sauk'i, kake ma kanka". Habib cikin damuwa da tashin hankali ya ce, "Wanka fa , wake min? "., ya yi maganar kamar zai yi kuka. Ita Hajiya Turai dariya ma yaso ya bata, sannan ta ce, "Habib yarinyar nan fa ba kad'an ta yi aiki da kai ba, ko mai da kasani ita kema". "Wayyo Mommy kin kasheni, taya ma za'arasa wadda zata kula da ni sai wannan yarinyar, haba Mommy wanan ma ai Islamicaly babu kyau! ". "A'a nikam banga rashin kyu ba, dan haka nema gudin sab'ama mahaliccin mu aka had'a ku aure". Cewar Hajiya Turai. Habib kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Mommy ina fatan babu wanda ya san da maganar auran nan a cikin friend's d'ina? ". "Eh babu". Cewar Hajiya Turai. "Yauwa naji dad'i, amma Mommy ai shikenan ko kin warware auran ko? ". Shiru Hajiya Turai tai ma Habib. Habib ko jin Hajita Turai bata bashi amsa ba, sai ya ce, "Shikenan Mommy nawa kika ga ya kamata a biya yarinyar?,, dan zuwa yanzu ma ya kamata ace ta koma gidansu". Nan ma dai Hajiya Turai shiru tai ma Habib bata tanka mai ba". Habib ko bai gaji ba, ya ci gaba da cewa, "Mommy banga Bilya ba, dan zuwa gobe nake son ya kaita gidansu, dan ya kamata ace ta koma gidandu haka nan". Sai yanzu Hajiya Turai ta d'ago kai tana kallan Habib, sannan ta ce, "Babu inda zata Habib ta na nan, nan zata ci gaba da zama, maganar kud'i kuma da kake cewa zaka biya Hassana abinda tai ma, Habib baka da abinda zaka biyata, amma kash kai baka sani... ". Sallamar Hassana yasa Hajiya Turai tai shiru". Hassana cikin girmamawa ta mik'ama Hajiya Turai wayar Habib. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Daughter bashi". Hassana mik'ama Habib wayar ta yi cikin girmawa. Habib ko ko kallan Hassana bai yi ba, ya amshi wayar shi, sanan ya tashi ya fita". Habib part d'in shi ya koma yana tunanin yadda zai yi ya rabu da yarinyar nan, dan babban abin kunya ne kamar shi abokan shi su ji labarin yana auran staff d'in shi, ina ba zai yuwu ba, sttaf d'in ma mai mopping, nan dai Habib ya gama zan can zucinsa bai samo mafita ba". Ana sallar magriba Bilya ya shigo gidan, da wowar shi kenan daga zaria. Bilya sai da ya yi sallar issha'i sannan ya shiga side d'in Habib. Bilya da murnar shi cikin girmamawa ya gaida Habib da jin dad'in ganin Habib d'in ya warware. Bayan sun gama gaisawa ne Habib ya ba Bilya kud'i ya siyo mai tea da wai nar kwai dan ba zai shiga side d'in Hajiya Turai ba, dan baya san ganin Hassana acewar shi". Bilya cikin k'ank'anin lokaci ya yo ma Habib had'in tea d'in da ya saba siyo mai ya kawo mai. Habib zama ya yi sha tea d'in sanna ya kwanta dan da wuri ya ke son zuwa Sanad yoghurt". Washe gari da wuri Habib ya tashi ya yi duk abinda zai yi, sanan ya yi shirinsa na alfarma kamar yadda ya saba yi, sannan ya kira Hajiya Turai a waya, bayan ya gaidata ne, ya ce, "Mommy dama karki ga ban shigo bane, ina sauri ne zani wajan aiki". Hajiya Turai cikin nunama Habib ba komai ta ce, "Bako mai sai ka dawo". Habib ka she kiran ya yi, sannan ya nufi wajan mota inda Bilya ke jiran shi". Bilya cikin girmamawa kamar yadda ya saba, ya gaida Habib. Habib amsawa ya yi, sannan ya ce, "Bilya ka je ka ce ma yarinyar nan ta zo aiki". Bilya da mamaki ya kalli Habib ya ce, "Oga Habib wata ya rinyar? ". "Yarinyar da ke aiki a sanad ". Shiru Bilya ya yi sannan ya ce, "Oga Habib Hajiya ta warware auran ne? ". Cikin tsawa da hargagi Habib ya ce, "Bansani ba! , ka je ka yi abinda nace ma! ". Bilya fita ya yi ya nufi side d'in Hajiya Turai, shi dai aganin shi yana ganin rashin da cewar hakan. Bilya sallama ya yi ya shiga falon, Hajiya Turai, in da ya iske Hassana kad'ai a falon zaune............ ✍️ Labarin yanzu aka fara dear😍😍. Idan kin karanta daure ki yi Comment sister 🤝 Comment & Share please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ IDAN KA MUTU AN RUFE LABARIKA, AMMA ABUBUWA UKU SUNA RAYUWA A BAYANKA: ILIMI DA HAIHUWA SAI AIKIN ALHERIN DA KA SHUKA. ALLAH KA SA BAMU IKON BARIN AIKIN ALKAIRI,BAYAN RANMU🤲🤲🤲. Shafi na 52&53. Bilya cikin fa'ara suka gaisa da Hassana kamar yadda suka saba gaisawa, sannan bilya ya kalli Hassana ya ce, yana mai kame-kame dan sosai ya ke ganin rashin da cewar hakan, ya ce, "Uhm dama Oga Habib ne ya aikoni ya ce wai kije aiki yau". Hassana cikin rashin damuwa da abinda Bilya ya ce mata, ta ce, "Tom Oga Bilya ganinan zuwa, bari in tashi in shirya". Hassana tashi ta yi, dama ta yi wanka gyalan doguwar rigar da ta sane ta d'akko, sosai Hassana tai kyau, kwalliyar ta sake fito da haskenta, kasan cewar abayar lemon green ce ta ji adon tsones". Hassana har bedroom d'in Hajiya Turai ta je , bayan ta gaida ta ne, ta ce, "Mommy sai na dawo ". Hajiya Turai da mamaki ta kalli Hassana ta ce, "Daughter sai kin dawo kuma?, ina zaki? ". "Mommy yau zan koma aiki". Cewar Hassana. Shiru Hajiya Turai ta yi dan bata yarda Hassana niyyar kanta bace zata je aiki, tafi tunanin daga Habib ne, hakan yasa Hajiya Turai kallan Hassana ta ce, "Daughter nasan Habib ne ya ce kije aiki ko?". "Eh Mommy, kuma nima ina son inje". Cewar Hassana". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter babu wani aikin da zaki". Hassana badan taso ba ta hak'ura, saboda bata son jayayya da Hajiya Turai, amma tana tsoran rashin mutincin Habib narashin zuwanta " . B'angaran Habib ko, sosai ma'aikatan Sanat yughurt ke murna da ganin Ogan nasu yaji sauk'i. D'aya bayan d'aya staff d'in ke shiga suna gaida Habib. Hakan yasa Habib bai wani aiki ba". 6:00PM Bilya ya zo yi ma Habib magana jin ya ji shi shiru har yanzu bai fito ba, saboda Habib ya saba inda Hajiyar Oga Habib na gida, tom a gida Habib ke sallar magriba.Habib kallan Bilya ya yi, ya ce"Bilya sai 9 o'clock yau zan je gida". Bilya fita ya yi yana mamaki dan yasan indai Hajiya Turai na nan Habib da wuri ya ke komawa gida". Habib sai 9 o'clock sanna ya koma gida kamar yadda ya ce, Habib kiran Hajiya Turai ya yi awaya, bayan sun gaisane, ya ce, "Mommy naso in shigo amma kuma ban dawo da wuri ba, sai gobe zan shigo"."Tom Allah shi kaimu". Cewar Hajiya Turai. Dan ta san abinda Habib kema kema guje-gujan". Washe gari Habib da wuri ya yi shirinsa na tafiya Sanat yughurt, cikin blue d'in suit. Bayan Habib ya gama shirinsa ga ba d'aya ne, ya shiga part d'in Hajiya Turai". Habib har bedroom d'in Hajiya Turai ya shiga, dan yawanci irin wannan lokacin yasan bata fitowa falo . Habib cikin girmamawa ya gaida Hajiya Turai, sannan ya tashi ya ce, "Mommy zan tafi, ina sauri ne sai in na dawo zan shigo". Habib tashi ya yi zai fita, Hajiya Turai ta kallai ta ce, "Habib koma ka zauna". Habib komawa ya yi ya zauna kamar yadda mahaifiyar shi ta umarce shi". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, sannan ta ce, "Habib ya maganar auranka da Hassana da nai ma?, ko akwai abinda baka gane bane abayanin nau? , in sake mai-mai ta ma? ". Habib zuk'unnar da kai ya yi, ya yi shiru. Hajita Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib kai fa nake sauraro?". "Mommy naji kin min maganar aure da ki kai, amma Mommy ai kinsan wannan auran ba mai yuwuwa bane, na farko dai ni gaskiya babu aure a tsarina yanzu, na biyu kuma gaskiya abun kunya ne friend's d'ina suga ina auran staff d'ina, staff d'in ma cleaner , sannan yarinyar nan ma fa Mommy bamu san asalinta ba, ni Mommy ko bama komai kwata-kwata bana son yarinyar nan gaskiya!, sannan inajin nau yin aganta ace ita ce wadda nake aure, gaskiya Mommy kema ki duba ki gani, wannan ba abu bane mai yuwuwa..! ". Hassana da shigowarta kenan dan gaida Hajiya Turai, taji maganar Habib ta k'arshe, Hassana na shigowa ta gaida Hajiya Turai cikin girmamawa kamar yadda ta saba,sai dai muryara na rawa sosai, Hassana kallan Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Mommy ke ki kai min alk'awari Oga Habib ba zai tab'a sanin da auran nan ba, amma Allah bai nufaba sai da ya sani". Shiru Hassana ta yi, sannan ta ci gaba da cewa, "Mommy dan Allah ina son yau ki cika min alk'awarin da kika d'aukar min yau, dan Allah ki warware auran nan yau ".Hassana ta idasa maganar kamar za tai kuka dan sosai ta ji zafin maganganun Habib, wai yana jin kunyar aganta ace ita yake aure". Hajiya Turai shiru ta yi, dan tasan Hassana taji abinda Habib ya ce. Habib ko tashi ya yi, ya ce, "Mommy ni zan tafi, dama ba da yarda ta akai ba".Habib na fad'in haka ya juya ya tafi ". Hajiya Turai ko shiru ta yi tarasa abinda ke mata dad'i, dan itama sosai maganganun Habib su kai mata zafi, sannan ya kuma daf kawa, wai shi zai tafi dama bada yardar shi akai ba". Hajiya Turai kallan Hassama ta yi da ke zuk'unne kanta ak'asa. Hajiya Turai kamo hannun Hassana ta yi, sannan ta ce, "Daughter ki yi hak'uri, nasan kinji duk abinda Habib ya ce". "Babu ko mai Mommy, ai abinda ya fad'a haka ne ba asan asalina ba, ni yanzu Mommy abu d'aya zaki min dan Allah ki datse auran nan, insha Allah gobe zan tafi garinmu". cewar Hassana. Hajiya Turai cikin damuwa ta ke kallan Hassana jin abinda Hassanar ta ce. Sannan Hajiya Turai ta ce, "Daughter tafiya kuma? ". "Eh Mommy tafiya nake son yi dan Allah karki hanani". "Shikenan daughter share hawayanki, yau she kike son ki tafi? ". Cewar Hajiya Turai"."gobe". Hassana ta ba Hajiya Turai amsa a dak'ile". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta kalli Hassana ta ce, "daughter kije ki yi break fast, Allah ya kaimu goban ". Hassana cikin sanyi ta tashi ta ta fita". B'angaran Farida ko, yau ta shirya dan zuwa gidansu Hajiya Turai dan ganin lafiya, dan a yadda tai ma Habib magana akan sakin Hassana ya nuna ya amshi maganar, tom tunjiya taso zuwa, amma Hajiya Murja ta hanata ta ce, ta bari sai nan da kwana biyu tuk'un ta san kafin lokacin Habib ya rabu da Hassanar, Allah bashi sai su san ta yadda zasu b'ullo mai ya auri Farida, hakan yasa Farida yau ta yi shirinta ta na tafita gidandu Habib, in da yau ne Mahaifiyarta ta ce mata ya kamata ta je". Farida k'arfe sha biyu na rana tazo gidansu Habib. Direct Farida part d'in Hajiya Turai ta nufa". Hajiya Turai Farida ta iske zaune a falon ita kad'ai, Farida kamar yadda ta saba, haka ta je ta gaida Hajiya Turai. Hajiya Turai ko ta amsama Farida a dak'ile, babu yabo babu fallasa. Farida d'an nesa da Hajiya Turai ta zauna, tana Waige-waige ko zata hango Hassana, dan ta k'osa ta ji har yanzu Hassana na gidan. Farida kallan Hajiya Turai ta yi, cikin sanyi ta ce, "Mommy Hassana fa?, banganta ba". "Tana ciki". Hajiya Turai ta kuma ba Farida amsa a da k'ile". Farida shiru ta yi tana tunanin tom Habib ya saki Hassana ne ko ko?". Farida zama ta yi tana jiran Habib ya dawo ta kuma zuwa ta tunkarai da maganar ta ji abinda zai ce". B'angaran Habib ko, dan karma ya dawo da wuri ya had'u da Hajita Turai, yauma k'in dawowa ya yi, sai 9:50Pm, kamar jiya. Yana dawowa ya kira Hajiya Turai a waya, bayan sun gaisane ya ke sanadar da ita, ya ce, "Mommy yauma bandawu da wuri ba, shigowata kenan yanzu, sai dafe na shigo". "Allah ya kaimu Hajiya Turai ta ce, ta yi rejecting call d'in ". Farida ko ganin Habib bai dawo da wuri ba, yasa ta adana kala manta sai washe gari ta yi ma Habib ". B'angaran Hassana ko yau haka ta wuni duk ba fara'a, dan ko abinci tsakura kawai ta ke. Ko da yaushe ko saurare ta ke, ta ji Hajiya Turai ta ce mata ta warware auranta da Habib, dan sosai ta ji hankalinta ya koma gida, mahaifarta kawai ta ke son tafiya, inda ga abin da barin gida ya jawo mata, har ana ik'irarin ba asan asalinta ba, tabbas bata tab'a, kawo ma ranta wata rana wani zai mata gori da hakan ba, hakan ne ya sa da akai mata ya tada mata hankali , taji gaba d'aya hankalinta ya koma ga mahaifarta. Adaran dai haka Hassana ta yi bacci duk ba dad'i". Washe gari. :washe gari bayan Hassana ta idar da sallar asuba gari ya fara aske, kamar yadda ta saba haka ta je gaida Hajiya Turai, sai dai Hassana koda ta tura bedroom d'in Hajiya Turai sai taji kamar ansa key, Hassana cikin mamaki ta juyo, ta koma d'akin ta. Hassana ta zauna babu dad'ewa Maimuna ta yi sallama ". Hassana amsawa ta yi, sannan ta fito tana tambayr Maiamuna lafiya. Takardar da ke hannun maimuna ta mik'ama Hassana, ta ce, "Dama Hajiya ce ta ban ta ce in baki". Hassana amsa ta yi tana bin letter da Maimuna ta bata da kallo, sannan ta mai da kallanta gun Maimuna ta ce, "Ina Mommy fa?". "Hajiya ta yi sammakon tafiya". cewar Maimuna. Hasssana ba ta k'ara bin takan zancan Maimuna ba, ta bud'e letter tana karantawa kamar haka. :Assalamu akaikum. Da farko dai ina baki hak'uri daughter na sab'a alk'awarin da nai miki, hak'ik'a naso in raba auranki da Habib kamar yadda nai miki alk'awari, sai dai kash !, na kasa hakan. Daughter ba zan b'oye miki ba bazan iya raba auranki da Habib ba, sai dai idan Allah ya yi babu rabon zaman aure a tsakanin ku. ki yi hak'uri da rashin sallamr da ban miki ba. Daughter bana iya had'a ido da ke ne, dan ina jin kunyar abinda Habib ya yi miki. Dan Allah daughter ki lura yanzu akwai aure kanki, dan Allah ina rok'onki karki ce zaki tafi da aure kanki. Ki yi hak'uri insha Allah komai zai dai-dai ta tsakaninki da Habib.,ki yafemin daughter, bissalam ". Hassana ko da ta kama karanta letter da Hajiya Turai ta bada a ba ta, gun ta zauna tana kuka. Cikin kukan tana cewa, "Haba Mommy biki ji abinda Oga Habib ya ce bane, koda ace ni 'yar asali ce, tom baya sona kwata-kwata azuciyar shi. me yasa zaki min haka!! ". Haka Hassana tasha kukanta ta gaji ta lallashi kanta ta yi shiru". Farida ko da kukan Hassana ya ta data, ta window ta lek'o tana kallan Hassana. Hassana ko nan ta tashi ta bar letter da Hajiya Turai ta bata agun". Farida ko na ganin Hassana ta tashi ta zo da saurinta ta d'au letter tana karantawa ". Farida ko da ta kagama karanta letter, kuka itama tasa, dan ta yi tunanin Hassana nakukan Habib ya saketa ne. Farida share hawanta ta yi sannan ta d'akko tan figigin mayafinta ta yafa, ta nufi gidan Mahaifiyarta, da letter a hannunta". B'angaran Habib ko bayan ya gama shirinsa ya fito, ya nufi part d'in Hajiya Turai. Bilya ne ya yi saurin da katar da shi ta hanyar cewa, "Barka da safiya Oga Habib, ga shi inji Hajiya ta ce in baka". Habib amsar letter da Bilya ya mik'a mai ya yi yana mamakin ta me ye. Habib bud'e letter ya yi ya fara karantawa kamar haka. :Habib raina b'ace na kema magana, hak'ika na ji zafin maganganunka na jiya akan Hassana, kuma ina son ya zama farko da k'arshe da zaka k'ara furta mata wata kallama mai muni irin haka. Habib na koma wajan aiki, hak'ika idan na kalli fuskarka ayanzu tana tuna min ne da kalmomin da ka fad'ama Hassana marasa dad'in ji. Daga k'arshe idan har ka saki Hassana koda ko ita ce ta naimi hakan Allah ya isa ban yafema ba Habib!!! ". Wata irin zufa ce ke keto ma Habib lokacin da yagama karanta letter. Sosai ranshi ya b'ace da furicin Mahaifiyarshi akan shi, akan me za tai mai haka, koko ana zaman aure ba so ne, tom idan ma anayi gaskiya shi ba zai iya haka ba. Habib wayar shi ya ciro ya kira Hajita Turai, amma har ta gama ringing bata d'aga ba". Habib ranshi b'ace ya kalli Bilya ya ce, "Bilya kiramin waccan yarinyar ". Bilya ko tunda yaga haka ya yi tunanin babu lafiya, dan lokaci guda idon Habib ya kad'a ya yi ja sosai". Bilya kallan Habib ya yi, ya ce, "Oga Habib wata yarinyar? ". "Bansani ba Bilya!, ai kasan yarinyar da nake nufi". Bilya ta fiya ya yi yana mai tunanin anya ko ba k'arya zai koma ya yi ma Habib ba, anya idan yaga Hassana ahalinda ya ke yanzu , ba zata ji da kyau ba, tom amma kuma nasan halinshi sare zai iya zuwa da kanshi kiranta. Bilya na wannan tunanin ya isa falon Hajiya Turai............ ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Idan naga Comment da yawa gobe insha Allah zaku ga Update da wuri Allah. Idan na raina comment tom zafa kuji shiru🤐🤐🤐. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Shafi na 54&55. Bilya ta fiya ya yi yana mai tunanin anya ko ba k'arya zai koma ya yi ma Habib ba, anya idan Habib yaga Hassana a halinda ya ke yanzu ba zata ji da kyau ba, tom amma kuma nasan halinshi sare zai iya zuwa da kanshi kiranta. Bilya na wannan tunanin ya isa falon Hajiya Turai. Sai dai ko da ya shiga ba kowa Falon, sallama Bilya ya yi da k'arfi, amma shiru. Bilya fita ya yi yana mai jin dad'in rashin ganin Hassana da bai ba , dan shi dama ba son isar da sak'on ya ke ba, aganin shi hakan bai kamata ba ". Habib na tsaye inda Bilya ya barshi, Bilya ya dawo. Bilya kallan Habib ya yi ya ce, "Oga Habib inajin bata side d'in Hajiya, dan na yi magana naji shiru, babu alamun mutum". Habib batare da ya tankama Bilya ba ya shiga mota. Bilya ma ya shigaya yaja motar suka tafi". B'angaran Farida ko tana isa gidan Hajiya Murja, ta wurga ma Hajiya Murja letter da Hajiya Turai ta ba Hassana, ta ce, "Mommy nikam nagaji!, sai yaushe zan zama mai sa'ane, kince muje wajan wancan wai shi mai biyan buk'ata dole, ya ce sai Oga Habib ya yi hauka zan samu in aure hankali kwance, ya yi haukarshi ya gama k'arshe mai-mai kon a had'a auran da ni da wata aka had'a, yanzu munyi takakkiya munje gun wannan shima kinga shirman da yabamu, nifa nagaji zan yanke hukuncin da zai min dai-dai in huta da rayuwar bak'incikin nan da nake, Mommy koda yaushe ina fad'a miki Oga Habib shine cikar farincikina, duk wani farinciki indai ba ina tare da shiba tom jabu ne, dan haka ni yau d'in nan zan yanke hukuncina na k'arshe! ". Hajiya Murja sosai hankalinta ya tashi da furincin Farida dan ta san Farida babu wani hukuncin da zata yanke wanda ya wuce ta ce zata tafi ta barta". Hajiya Murja hannun Farida ta kama ta ce, "Farida ki yi hak'uri kinji, bari in kira Hajiya Zaliha in mata bayanin halinda nake ciki nasan zata tai maka min da wani abun". Hajiya Murja wayrta ta d'auka ta kira Hajiya Zaliha kamar yadda ta ce. Hajiya Zaliha na d'aga Kiran Hajiya Murja tai mata bayanin halinda ta ke ciki. Hajiya Zaliha cewa ta yi ta bari anjima zata shigo unguwar zata biyo". Hajiya Murja kallan Farida ta yi ta ce, "Farida ki yi hak'uri kamar yadda kika ji nace miki, indai kika sa hak'uri aure zakaninki da Habib babu fashi, kinga ma dai shi Habib ba son yarinyar ya ke ba, son Hajiya Turai ko ai na banza ne inda ba ita zata zauna mai da ita ba, dan haka ke dai ki yi hak'uri ki ban nan da isowar Hajiya Zaliha". Hajiya Murja na nan sai aikin ba Farida baki take, sunanan zaune Hajiya Zaliha ta iso. Bayan sun gaggaisa ne Hajiya Zaliha ta kalli Hajiya Murja ta ce, "Hajiya naji duk ba yaninki, amma yanzu zamu gwada da basirar da Allah ya bamu ne, dama ai k'issar baka tafi ta malam, dan haka inda Malaman sun kasa sai mu yi da k'isssar mu ta mata". Hajiya Zaliha kallan Farida ta yi, ta ce, " Haba Daughter kina so kiban kunya sai kace wata 'yar kyauye, yanzu ke baza ki iya yaudarar namiji da kalaman bakinki ba ya soki, sai kin had'ashi da Malam, Tom ni Wallahi a zamanina da kallo nake yaudarar d'a namiji, bare ke da kike da dama kina zaune gidansu. Yanzu dai ki bud'e kunnanki da kyau ji ji abinda zan fad'amiki, amma fa sai kin jure, dan shi dama mai nema sai ya jure indai kika sa juriya tom zakiga ribar abin. Yanzu dai da farko zakina yawan tusa kanki aduk abinda ya shafi Habib agidan, amma zaki yi abin a Sannu, dan karki kuskura kina nuna zak'ewa wajan tusa kanki,duk wani abu da ya dan ganci Habib ki yi k'ok'ari ya kasance ke zaki mai, ke idan zai yuwuma duk wani abu nashi ya dawo hannunki, ita kuma yarinyar dama kunce ba sonta ya ke ba, zakina nuna rashin iyawarta duk abinda tai a gabanshi, ko da ya yi kinuna mata ba haka ake ba. Shi kuma Habib d'in kina nuna mai kina jin tausan shi na had'a shi da yarinyar da akai , dan kwata-kwata ba ajinshi ba ce". Hajiya Zaliha kallan Farida ta yi ta ce, "Daughter ina fatan kina fahim tata?, yawan kwalliya ko ki dage da saka kayan da zaija hankalinshi, ita ko yarinyar in ma mai son kwalliya ce ki sanyadda zaki kina hanata". Farida cikin jin dad'i ta rungume Hajiya Zaliha, ta ce, "Wayyo Mommy, dama nasan hakane ai da tuntuni gunki nazo da yanzu na auri Oga Habib anwuce gun".Dariya Hajiya Zaliha ta yi, ta ce, "Banni da shi daughter, k'aryar muskilanci yake. Sannan kina yawan kirana awaya ina k'ara miki wasu darisan". Hajiya Zaliha ta dad'e tana kuma koyama Hassana dabarun da zata ja hankalin Habib, batare da ta had'a shi da boka ba ko malam". Farida ko nagama jin k'issoshin da Hajiya Zaliha ta koya mata, ta tashi ta ce, "Ai tafiyama za tai". B'angaran Habib ko bayan sun isa Sanat yughurt, kallan Bilya ya yi, ya ce, "Bilya ka tabbatar da yarinyar nan gobe tazo aiki! ". Magana Bilya ya ke son yima Habib amma baiga fuska ba, sai dai cewa ya yi, "Tom insha Allah Oga Habib". B'angaran Hassana ko tsabar kukan da ta yi ne ya saukar mata da ciwan kai, hakan yasa ta kwanta, ba ita ta farka ba sai azahar, bayan ta yi sallah ne ta je derning space ta ci abinci, duk da bawani na kirki ta ci ba, danma yunwa ta ke ji inda tun jiya rabon ta da abinci". Gaf da magriba Farida ta shigo gidan. Sai dai ko da tazo Falon bataga Hassana ba, hakan yasa ta zarce room d'in ta, wanka Farida ta yi sannan ta zauna ta rangad'a kwalliya kamar mai shirin zuwa gasar kyau. Falo Farida ta dawo ta zauna, duk da tana mai fargabar kar Habib yak'i ganin wannan wankan, inda in Hajiya Turai bata nan Habib ba ya dawowa da wuri. Farida na nan zaune Hassana ta fi to ta nufi kitchen tana son had'a tea dan shi kawai ta ke jin zata iya sha". Hassana wucewa ta zo yi zata shiga kitchen, Farida ta ce, "Ke! ". Hassana juyowa ta yi tana kallan Farida, amma harga zuciyarta bata jin dad'in ke d'in da Farida ke ce mata ba". Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ki taho min da abinda zanci". "Tom". Hassana ta ce, ta juya ta shiga kitchen ta had'a tea d'in ta, sanann ta d'iboma Farida abincin ta kai mata . Hassana mik'ama Farida abincin ta yi ta tafi, Farida kallan Hassana ta yi, ta ce, "Da hannunki zan ci? ". Hassana batare da ta tanta mata ba, ta koma kitchen ta d'akko mata spoon ta kawo mata". Washe gari da wuri Bilya ya shigo falon Hajiya Turai yana sallama. Hassana da taji yo sallamar Bilya , fitowa ta yi, bayan sun gaisa ne Bilya ya kalli Hassana ya ce, "Dama Oga Habib ne ya aikoni ya ce, "Yau ki je aiki". Bilya na fad'ima Hassana haka ya juya ya fita". Hassana dama ta yi wankanta, cikin kayan da Hajiya Turai ta sai mata, ta d'akko wata abaya da yake duk kusan dogayan riguma ne, tasa. Sannan ta d'auki ma yafin rigar da yake yana da girma ta yafa, takama hanya zata tafi. Farida da fitowarta kenan, kallan Hassana ta yi damamaki ta ce, " Ke ina zaki? ". Hassana batare da ta kalli Farida ba ta ce, "Aiki". Hassana na fad'in haka ta juya ta tafi abinta. Tabar Farida gun tsaye, ko ba komai taji dad'in hakan dan hakan ya tabbatar mata Habib bai damu da Hassana ba". Hassana ko kasan cewar babu kud'i a hannunta wajan Jimmai ta je. Jimmai da murnarta ta rungume Hassana ta ce, "Dama talaka irin mu na ganinki!, Wallahi bacin sanin da naimi ba d'an ka d'an bane da babu yadda za ai in gane ki. Hassana kinganki ko yadda kika dawo, kinyi fari kinyi k'iba.. ". Hassana murmushi ta yi, ta ce, "Uhm Sister Jimmai kenan, ni wata k'iba zan wani yi, ni dai yanzu sauri nake ban 1k a kud'innan,". Shiru Jimmai ta yi tana kallan Hassana, sannan ta kauda tunanin da ta ke yi, ta ce, "Wai Hassana ina zaki ne haka? ". "Aiki zani". Cewar Hassana ". Jimmai kallan Hassana ta yi da alamun mamaki a tattare da ita, ta ce, "Aiki kuma?". "Sister Jimmai ban dan Allah, Allah akwai damuwa idan na je late". Cewar Hassana ". Jimmai kallan Hassana ta yi da alamun tuhuma, ta ce, "Hassana ni na san jin sauk'in Oga Habib zaki fuskanci abubuwa da yawa agun Oga Habib, sannan zaki fuskanta agun Aunty Farida ma. Hassana ya auranki da Oga Habib yana nan ko ba ya nan?". "Bayanan". Hassana ta ba jimmai amsa. Jimmai kallan Hassana ta yi ta ce, "Bana son maganar wasa dan Allah, Hajiya ta raba auran ne koko? ". Hassana shiru ta yi sannan ta kalli Jimmai ta ce, "Sister Jmmai dan Allah kiban in tafi, idan nadawo zanzo muyi magana". Jimmai shiga ta yi ta d'akkoma Hassana 1k kamar yadda ta ce, ta ba ta. Sannan Hassana ta tafi". Hassana ba ita ta je Sanat yughurt ba sai 11:15PM. Abinda Hassana ko bata sani ba tuni Billy ta canza wata madadin Hassana. Hassana ko da ta je Sanat yughurt stuff's d'in gurin wa inda suka saba da da ita, da murnarsu suka tarbi Hassana suna tambayarta lafiya tabar zuwa shiru haka? ". Duk wanda ya tambayi Hassana sai ta ce mai batada lafiya ne. Dariya sosai sukayi sannan Amina wadda tasu tafi zuwa d'aya da Hassana, ta kalli Hassana ta ce, "Sister ki canza wata k'aryar, amma wannan bata amsu ba, kallakki fa, yadda ki kai kyau, kika wani canza kamanni, da kyar muka iya gane ki, bacin ma wannan voice d'in taki da bazamu shaidaki ba, amma shine zaki wani ce mana kinyi ciwo ne ".ita dai Hassana murmushi kawai tai masu, sannan ta ce, "Ni yanzu tunanina d'aya yadda zamu k'arke da supervisor". Amina dariya ta yi, ta ce, "kuma kinsan rashin mutuncinta sai abinda ya yi gaba, dan Wallahi muna ganin mulkin mallaka". Hassana kallan Amina ta yi, ta ce, "Sister Amina yanzu ya zanyi?, in da kince ta maida wata a mazaunina? ". "Zuwa zakiyi ki sa me ta sai ki mata bayanin rashin zuwaniki, amma fa karki ce mata ciwo kikai kamar yadda kika ce mana, dan Wallahi ba zata yarda ba, garama kice mata tafiya ce ta kamaki lokaci guda, k'ila idan kikaci sa'a ta yadda ki ci gaba da aiki". Hassana da addu'a ta shiga office d'in supervisor. Hassana cikin girmamawa ta gaidata. Ita ko Billy bata gane Hassana ba, hakan yasa ta ce mata, "Lafiya?, kina son meye? ".dan ta zaci Hassana surpleaar ce. Hassana cikin sanyin muryarta ta ce, "Supervisor Hassana ce, wadda ta yi aiki wata Uku da suka wuce, ina b'angaran mopppiny, tom dama tafiya ce ta kamani lokaci guda shiyasa ban samu damar zuwa na sanar ba". Kallan baki da hankali Billy tai ma Hassana, sannan ta ce, "Tom yanzu me kike so? ". "Na dawo aikina". Cewar Hassana. Kallan rainin hankali Billy taima Hassana, sannan ta ce, "Hassana ko da ace kin d'auki permission, tom mungama aiki da ke, bare kuma baki sanar ba, tuntuni mun maida wata ma zauninki, zaki iya tafiya". Hassana a zaman da tai da Billy ta san halinta, hakan yasa bata kuma cewa ko mai ba, ta fita daga Office d'in. Hassana shiru ta yi tana tunanin komawa gida, tana kuma tsoran Habib, ga shi in tace zata gudu, bata son tafiya da aure kanta. Bilya ne ya fad'oma Hassana a rai, hakan yasa ta fita ta je side d'in da Bilya ya ke aiki ta sa mai". Bilya cikin fara'a yace da girman kujerarki, amarya agidan Ogan mu, mai makon ki aiko akirani, sai kizo da kanki". Hassana b'ata fuska ta yi, ta ce, "Oga Bilya dan Allah bana son sunannan, dan Allah ". "Yauwa tom nima ki bar cemin Oga Bilya ". Cewar Bilya, dan shi yana ma Hassana yanzu kallan girma ne, dan ko ba komai, acewar shi akwai auran Ogan su akanta". Hassana kalla Bilya ta yi kamar za tai kuka ta ce, "Oga Bilya Allah ba zan iya fad'in sunan ka kai tsaye ba, kaine wanda ya taimaka min alokacinda banda yadda zanyi, kaine ka had'ani da manager, amma kuma in rik'a Kiran sunan ka kai tsaye, gaskiya bazan iya ba". "Shikenan nima zanci gaba da kiranki da amaryar Ogan mu". Hassana kauda maganar ta yi, dan tasan indai Bilya ne sai dai suyi ta ta yin ta , hakan yasa Hassana ta kauda maganar baki d'aya". Hassana kallan Bilya ta yi, ta ce, "Oga Bilya Supervisor ta dakatar dani daga aiki, kasan ban sanar da itaba na daina zuwana". Shiru Bilya ya yi, dan ko ba adad'eba sai da Habib ya tambaye shi wai yarinyar nan tazo dai aiki ko.Dan haka yasan aikin Hassana dole ne, hakan yasa Bilya kallan Hassana ya ce, "Karki damu, bari in ma manager magana". Bilya Office d'in manager ya shiga, bayan sun gaisane, Bilya ya kalli manager ya ce, "Manager dama Oga Habib ne ya ce Hassana ta dawo bakin aiki, tom ta dawo kuma supervisor wai ta kureta, shine nazo in ma magana kai mata magana". Manager Kallan Bilya ya yi, ya ce, "Wai kana nufin yarinyar da Hajiyar M,D, ta had'a aure da shi, alokacin da yana ciwonnan? ". "Eh ita". Cewar Bilya. "A'a tom auran fa, ko kana nufin M. D, har ya warga tsa shi, dan nasan zaiyi wahala dama ya zauna da ita, dan gaskiya M. D, yana da damuwa, amma in ba hakaba ai yarinyar tana da kyau". Cewar manager yana kallan Bilya. "Tom abin na Oga Habib sai dai shiru". Cewar Bilya ". Manager kallan Bilya ya yi, ya ce, "Babu damuwa bari in ma Billy magana ". Manager tashi ya yi ya shiga office d'in Billy . Zama ya yi sannan ya kalli Billy, ya ce, "Sweetheart ki yi hak'uri dan Allah ki bar yarinyar nan ta dawo bakin aikinta". Billy kallan manager ta yi, sannan cikin fad'a-fad'a ta ce, "Na dai gama kula da son yarinyar nan kake, haka wancan karan da nakoreta akai ma kai min!, kuma banda ita babu wanda nake kora aiki kazo kai min magana sai akanta, dan haka Wallahi bazanyi magana biyu ba, sai dai ni in bar aikin! ". Manager kama hanun Billy ya yi ya zaunar da ita, sannan ya ce, "Sweetheart ki gane yarinyar nan bazata koru ba.. ". Billy saurin amshe zan can ta yi, da cewa, "Saboda me ba zata koru ba ?". "Saboda Oga Habib ke son ta yi aiki anan gun, kuma yanzu haka matar shi ce". Billy cikin firgita ta ce, "Matar Wa wai? ". Manager cikin natsuwa ya ba Farida labarin yadda akai auran Hassana da Habib, daga k'arshe ya d'ora mata da cewa, " Habib yana son Hassana tai aiki anan ne dan kawai ya nuna mata shi ba sa'anta bane, nina san haka, dan nasan Oga Habib sosai". Farida cikin zuciyarta ta ce, "Aiko zan taya shi nuna mata shi d'in ba sa'anta bane". Wani murmushi Farida ta yi, sannan ta kalli Manager ta ce, "Ok, badamuwa zata iya ci gaba da aiki....... ✍️ Idan kin karanta, d'aure ki Comment dear🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). MASU COMMENT NA LAST PAGE NAGANI NAGODE SOSAI👍🏻👍🏻👍🏻👍🏻 A YI HAK'URI DA REPLY DA BAN SAMU YI BA🙏. MARASA COMMENT 🤐🤐🤐🤐. https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://m.facebook.com/groups/565235401564189/ Shafi na 56 & 57. Wani murmushi Farida ta yi, sannan ta kalli manager ta ce, "Ok, badamuwa zata iya ci gaba da aiki, idan ka fita ka turomin ita". Manager cikin jin dad'in amincewer Farida ya tashi ya fita daga Office d'in ta". Tsaye manager ya iske Hassana da bilya. Manager kallan Hassana ya yi, ya ce, " Ki je Supervisor na kiranki". Hassana office d'in supervisor ta Shiga". Hassana ta dad'e tsaye, kafin Billy ta d'ago tana kallanta, sannan ta ce, "tom kamar yadda nace miki mun dakatar da ke aiki, hakane, saboda mun maida wata a madadin ki , amma yanzu za kina wanke toilet d'in gunnan, safe da kuma dare, sannan sai 10:00PM zaki rik'a close". Manager kallan Hassana ta yi, da ta kai baya nan ta, ta ce, "Za ki iya tafiya". Shiru Hassana ta yi, dan gaskiya ita bazata iya wankin toilet ba, saboda tana da kyankyami sosai. Batare da Hassana ta ce ma Billy ko mai ba ta fita daga office d'in, direct Hassana gun Bilya ta koma. Hassana kallan Bilya ta yi, cikin damuwa ta ce, "Oga Bilya gaskiya bazan iya aikin da ta banba, badan komai ba, inada kyankyami sosai". "Wana side ta mai da ke? ". Cewar Bilya ". "Wankin toilet, na wajan nan". "Wankin toilet kuma!?". Bilya ya fad'i maganar dak'arfi". "Eh Oga Bilya ".cewer Hassana ". Shiru Bilya ya yi sannan ya ce, "kin gane ko, ki ci gaba da aikin da kike yi da, ki rabu da ita, amma Wallahi karki sake ki wankin toilet". Sosai Hassana ta gamsu da maganar Bilya, hakan yasa tai mai godiya ta tafi". Kasan cewar Hassana bata je da wuri ba, hakan ya sa duk kusan aikin da ta ke yi, anyi. Ya zamana Hassana sai zamanta ta yi, kusa da Amina tana taya su nasu aikin, su suna side d'in da ake yoghurt ne". Hassana na Sanat yughurt har yanzu 9:15PM, abu d'aya ke da munta yadda zata koma gida dan idan dare ya yi gun akwai wahalar samun abun hawa, Hassana na nan zaune ita kad'ai dan Amina tun 8:00PM tai close. Kuma dama kusan da ita ne su ka saba. Hassana na nan zaune sai ga Bilya". Bilya kallan Hassana ya yi da murmushin shi, ya ce, "Idan kin gama abinda ki ke yi ke na dawo d'auka". Hassana da mamaki ta ke kallan Bilya, ta ce, "Oga Bilya ni kuma". "Eh mana, yanzu nake Oga Habib, shi yasa na dawo kai amaryar shi itama ". Cewar Bilya yana dariya, dan ya lura Hasssana bata son yana had'a ta da Habib ". Aiko d'aurewa ta yi, ta ce, "kai! Oga Bilya, dan Allah na cema bana son wannan sunan". Dariya Bilya ya yi, ya ce, "Tom in dai bakya son sunan, nima daga yau ki bar cemin Oga, mijinki shine ya can-canta da sunan". Hassana tafiya ta yi tabar Bilya gun tsaye, dan ya gama b'ata mata rai ". Bilya da dariya ya bi bayan Hassana. Motar da Bilya ke d'aukar Habib da ita yazo ya d'au Hassana". Can gida ko, Habib ji ya yi yau babu abinda zai iyaci da daddare in ba kunun gyad'a ba, hakan yasa Bilya na aje shi ya Shiga part d'in Hajiya Turai da niyyarshi ko zaiga Baba Lami ya sata tai mai kunun". Sai dai Habib na Shiga da Farida ya ci karo, tana kwance kan 3 seater tana charting. Farida na ganin Habib amma sai ta yi kamar bata gan shi ba, hakan duk yana cin darisoshin Hajiya Zaliha". Habib kallan Farida ya yi, yai tsaki, ganin bata ma wai ganshi ba, hakan yasa cikin d'an d'aga murya ya ce, "Ke ina Baba lami". Farida tashi ta yi, zaune, cikin sanyayyar murya irin ta masu son yaudara, ta ce, "Oga Habib ka manta?, ai Baba Lami bata cika zama ba, in Mommy bata nan, kana son wani abune? ". Habib shiru ya yi, yana danna wayar hannun shi, sannan ya ce, batare da ya kalli ko kusa da inda Farida ta ke ba,ya ce, " Kin iya kunun gyad'a? ". Farida kamar tace a'a, inda ba iyawa tai ba, sai kuma ta yi tunanin ai hakama da mace, gara ta kira Mommy'n ta awaya ta fad'a mata yadda akeyi. Hakan yasa Farida ta ce, "Eh na iya, Oga Habib kana so inma? ". Dai-dai lokacin Hassana ta yi sallam cikin cool Voice d'in ta". Hassana ja tai ta tsaya, dan tana rasa na tsuwarta sosai, aduk lokacinda zata ga Habib, tarasa me haka d'in ke nufi, dan da ba haka ta ke ji ba. Hassana jarumta ta yi ta k'arasa shigowa falon, sannan ta ce, "Ina wani Oga Habib". Habib banza ya yi da Hassana yana mai ci gaba da danna wayar shi, sannan ya kalli Farida ya ce, "Ki damanin yanzu sai ki kawomin". Farida ko cikin jin dad'in abinda Habib ya yi ma Hassana, ta ce, "Tom Oga Habib ". Habib kuma juyawa ya yi ya fita, ya bar Hassana da zan can zuci, ta ce, "Haka ma fa d'azu da na gaida shi bai amsa min ba, aiko daga yau insha Allah bazan k'ara gaida shiba". Hassana juyawa ta yi zata Shiga ciki. Farida ta kirata da cewa". "Ke". Hassana tsayawa ta yi, tana mai sauraran abinda Farida zata ce mata". Farida kuma ganin Hassana bata juyowa, cikin fad'a-fad'a ta ce, "Ke da allacan bada ke nake magana ba!? ". Hassana juyowa ta yi tana kallan Farida alamun ina jinki? ". "Kin Iya kunun gyad'a? ". Farida ta tambayi Hassana. Shiru Hassana ta yi, dan tasan Habib ne yasa Farida shine ita kuma zata sata. "Eh". Hassana ta ce ma Farida". "Yauwa tom zaki min yanzu nan, ina zuwa". Farida fita ta yi ma Maimuna magana, ta na son ta bata kamu zanyi kunun gyad'a yanzu. Farida kitchen ta shiga ta d'iboma Farida , da yake yana cikin freazier ta kawo mata". Farida kuma Hassana ta kaimawa. Hassana amsa ta yi, ta shiga kitchen d'in falon Hajiya Tura". Cikin minti 10 Hassana ta dama Kunun gyad'ar ta kaima Farida". Farida ko sai da ta kuma shafa powder a fuskarta sannan ta d'auki kunun gyad'an ta yi side d'in Habib da shi". Habib na kwance kan caution, dan yunwa ya ke ji sosai. Farida ta yi nocking. Habib izinin shiga ya bata". Farida cikin yauk'i da kisisina ta isa inda Habib ya ke kwance, ta aje cup d'in kunun, ta ce, "Oga Habib ga kunun nan nagama". Habib kallanta ya yi, kamar Wanda baya son magana, ya ce, "Thanks". Farida har ta juya zata tafi ta dawo tana kallan Habib, ta ce, "Oga Habib idan kana buk'ata zan rik'ama kullum".aiko Habib sosai yaji dad'in hakan, dan babu abinda yake so yasha da daddare in son samu ne kamar kunu. Batare da Habib ya nuna ma Farida jin dad'in shi ba, ya ce, "Eh zaki iyayimin". Tom kawuta lafiya, sai da safe". Farida na kaiwa haka ta fita, tana mai murmushin ganin nasara kusa". Hassana ko na nan zaune tana kallan Farida ta d'auki kunun gyad'an ta fita da shi, ko ba afad'a mata ba tasan side d'in Habib Farida ta nufa. Hakanan Hassana ta riski kanta cikin wani irin bak'in ciki da b'acin rai, haka dai Hassana ta kwanta cikin damuwar da ita kanta a yanzu bata san ta mecece ba, ahaka bacci b'arawo ya yi awan gaba da ita". Washe gari Hassana da wuri ta shirta ta tafi aiki. Sai dai Billy na zuwa ta hana Hassana zama, daga tasata abu tagama sai ta bata wani. Haka dai tai ta kalato aiki tana sa Hassana. Aranar dai Hassana da gajiya sosai ta koma gida". Yauma Bilya ne yazo ya d'auketa bayan ya kai Habib". Hassana na isa gida kuma, ta iske Farida tana jiran ta dawo tai mata kunun ta kaima Habib". Aiko haka akayi, Hassana ko zama bata yi ba, Farida ta ce mata tana son tai mata irin kunun jiya. Hassana haka ta daure ta shiga kitchen ta damoma Farida ta ka wo mata. Farida kuma ta ta d'auka kamar jiya ta nufi side d'in Habib da kunun". Farida tana zuwa taima Habib nocking. Ya bata izinin shiga ta shiga ta kaima Habib kunun". Yauma kamar jiya ba yan ta aje kunun ta kalli Habib ta ce, "Tom Oga Habib na barka lafiya sai da safe". "Yauwa Farida nagode ". Cewar Habib. Dan sosai yaji dad'in kunun, Allah yasa irin na jiya ne yace azuciyar shi". Farida kuma har zata wuce ta fasa, ta ce, "Oga Habib ai kafi k'arfin haka awajena, abin harda godiya dan naima kunu, abinda zan iyama fiye da goma arana idan kana so, ni dai addu'a ta d'aya gareka, Allah ya baka mata ta nunama abokai, irin wadda ta iya f.... ". Tsawar da Habib ya yi ma Farida ce tasa tai shiru, ta fita da sauri". Habib kuma ji yayi ranshi ya b'ace, dan yama manta da wata Hassana, amma wannan mahaukaciyar tana son tuna mai da abinda ya manta da shi". BAYAN SATI D'AYA. Hassana kullum ta je aiki da abinda Billy ke sata, in dai ta samu hutu tom Billy ta yi close ne , sannan Hassana ke samun hutu. Kuma har yau Billy bata san Hassana bata wankin toilet ba". Kuma har yanzu kullum Bilya ke Kai Hassana gida. Daga taje kuma zata iske dama kunun Habib, wanda yake a matsayin Farida ta dama. Hassana har ta saba da dama kunun Habib". Farida ko tun ranarda taima Habib ta tabar gazar zance, ya bar sakar mata fuska in ta kaimai kunun. Kuma kullum in Farida ta kaima Habib kunu ta fita, mai makon ta koma part d'in Hajiya Turai, sai ta zauna awaje ta gama danne-dannan wayarta sannan zata shiga ciki, duk dan Hassana ta d'auka awajan Habib d'in ta dad'e haka". Hassana yauma ta yi kwalliyar ta cikin gayan da Hajiya Turai ta sai mata, ta yi kyau sosai, sai d'an fad'a wa da ta yi kad'an a fuska. Hassana na zuwa Billy ta sata aikin da tasaba sata, da ta gama kuma ta ce ta yi wancan. Bayan Hassana ta gama Mopping d'in Office d'in Billy, ta fi to zata fita Billy kuma zata shigo, suka ci karo da Billy, aiko Billy ta d'aga hannu ta wankama Hassana mari mai gigita k'wak'walwa". Hassana dafe gurin ta yi ta d'ago tana kallan Billy da idonta da ya kad'a ya yi jajir lokaci d'aya ta ce, "Supervisor mari kuma!? ".Billy cikin gadara da ji da masifa ta kuma d'aga hannu ta wanke Hassana da mari, ta ce, "Na mareki!, ki yi abinda zaki y... ". Billy bata rufe baki ba Hassana ma ta wanka mata mari, ji kake fassss, ta kuma sake wanka mata wani ta d'a yan gefan". Ai take danbe ya kaure tsakanin Hassana da Billy. Manager da ke Office da sauri ya fito Office d'in shi ya zo gun fad'an, ammma babu yadda manager bai yi ba ya kasa raba fad'an,Billy wata stick da ke kusa da ita ta d'akko zata bugama Hassana aka samu kuskure ta bugama Manager, kafin kace me duk staff's din suka taru gurin, sannan manager ya rik'e Billy Bilya kuma ya rik'e Hassana". Amma duk da haka Billy fusgewa ta ke ita sai ta koma ta bigi Hassana, manager kuma na k'ara rik'e ta". Habib kuma jin hayaniya ta yi yawa, da sauri ya fito daga office d'in shi. Cikin sauri yak'araso gurin da yaga taron staff's d'in shi agun. Habib yana k'arasowa ya fahimci abinda ke faruwa dan yaga manager na rik'e Billy tana fusgewa tana arabu da ita sai ta yima yarinyar nan hankali. Habib kallan manager ya yi ranshi b'ace ya ce, "Manager karabu da ita mana ta je ta bugeta d'in!, dawa suke fad'an? ". Habib ya tambaya cikin fad'a". Manager nuna ma Habib Hassana ya yi da ke gefe ra kub'e, Habib juyawa ya yi, ya bar gun, ya ce, "Manager su saman a Office ". Manager kallan Billy ya yi, ya ce, "Billy M. D, ya ce kusa mai a Office ". Billy office d'in Habib ta nufa, Hassana kuma ta mara mata baya". Habib na zaune, yaji nocking. Izinin shiya ya bada , Billya ta shiga, Billya na shiga ba dad'ewa Hassana ma ta shiga". Habib ya dad'e yana aikin gaban shi , sannan ya aje pen d'in hannun shi, ya kalli Billy ya ce, "Kafin mu d'aukeki aiki sai da akace miki babu fad'a, me yasa haka ta faru? ". Habib ya tambayi Billy yana kallan ta ". Billy ma Kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib ba laifina bane, kowa yana bin doka a factory nan, amma banda Yarinyar nan". Billy ta nuna Hassana. Ta ci gaba da cewa. "Oga Habib, kullum sai tazo late kuma tana close lokacinda taga dama, shine yau nai mata magana akan late d'in da ta ke zuwa, shine fa nake mata fad'a ina nuna mata ba haka aike aiki ba. Shine fa daga haka sai mari wai ni ban isa in tsaya ina fad'a mata haka ba, wai duk factory nan babu wanda ya isa yasata abinda ba ta yi niyya ba, marinda tai min ne yasa na rama , Oga Habib, dan Allah ka yi hak'uri ". Habib mai da kallan shi ya yi ga Hassana, ya ce, "Ke ma haukaciya ko?, baki da hankali ko?". Habib mai da kallan shi ya yi ga Billy ya ce, "zaki iya yanke mata hukuncin da ya yi dai-dai da abinda ta aikata".Billy cikin salon munafinci ta ce, "Babu komai na yafe mata Oga Habib ". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Rok'arta ta ya fe miki". Hassana shiru ta yi kamar bata za tai magana ba, ta ce, "Oga Habib ni ban mata komai ba, hasalima ita tai min". Billy kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib baka santa bane, ni ce zata rok'a yafiya, dan Allah ka barta kawai, ni ba sai ta rok'an ba ma, na barta da halinta zata had'u da dai-dai da ita". Habib kallan Hassana ya yi alamun ba wasa, ya ce, "Ke rok'arta ta yafe miki? ". Hassana abinda ta mai-mai ta ma Habib ta kuma mai-mai mata mai. "Oga Habib ni ban mata komai ba, hasalima ita ce tai min". Habib sosai ranshi ya b'ace wato maganar Billy gaskiya ce, tom wacece ita, hakan yasa Habib cikin b'acin rai ya tashi daga inda yake ya k'araso inda Hassana ta ke tsaye, ya ce, "Ke rok'eta ta yafe miki nace! ". Ya fad'i maganar cikin fad'a, yana kallan Hassana". Hassana ko tsabar ta kaici cikin kuka ta fara magana kamar haka.........✍️ Idan kin karan ta, karki wuce, daure ki Comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Shafi na 58&59. Hassana ko tsabar ta kai ci, cikin kuka ta fara magana kamar haka, "Oga Habib kamar yadda nace ma ni ban mata komai ba haka ne , hasalima ita ce tai min, dan haka ni bazan iya bata hak'uri ba". Habib da mamaki ya tsaya yana kallan Hassana. Sannan ya ce, "Ok, ke baza ki iya bata hak'uri ba!, ko?". Hassana banza tai da Habib ta ci gaba da kukanta, sai dai ta yi alk'awarin duk abinda Habib zai mata sai dai ya yi mata, amma baza ta tab'a ba Billy hak'uri ba, inda ba tai mata komai ba". Billy ko cikin jin dad'in ganin Hassana na kuka, da kuma yadda Habib ya kafe mata sai ta bata hak'uri, cikin yaudararrar murya, ta ce, " Oga Habib dan Allah ka rabu da ita, ai dama ta ce, duk factory nan babu wanda ya isa yasata abinda ba tai niyya ba, ni na yafe mata". Habib ko da zigar Billy ta shige, bai san sanda ya jawo Hassana da hannu d'aya ba, ya wurgarda ita kefe guda yana huci, ya ce, " Zaki bata hak'uri ko bazaki bata ba, saina yagalgalaki anan gurin!? ". Hassana ko da taji zafin wurgin da ya yi da ita, dan sosai kanta ya bugu, kwanciya tai ak'asan malemale tana kuka iya k'arfinta, tana cewa, "Wayyo Allah Mommy kaina, Wayyo Mommy dan Allah ki dawo na gaji, Wayyo Mommy zasu taru su kasheni". Daga Habib har Billy kallan Hassana kawai suke, Habib kallan Billy ya yi ranshi a d'an b'ace ya ce, "zaki iya tafiya ". Billy kamar karta futa taji, dan bata ji dad'in fita ita kad'ai ba ba Hassana, amma ko ba ko mai taji dad'in yadda Habib ya yi ma Hassana, dan ko a haka ai ya fifitata akan Hassana". Bayan Billy ta fita Habib zama ya yi yaci gaba da abinda ya ke yi, Hassana ta yi k'asa sosai da kukan sai shashshek'a da ta ke yi". Bilya ne yashiga Office d'in Habib kawo mai lunch. Bilya da mamaki ya bi Hassana da kallo da ke kwance ak'asa . Sai dai yanzu tabar kukan sai shashshek'ar kuka , itama kad'an-kad'an ta ke yi. Bilya kallan Habib ya yi, ya ce, "Oga Habib wannan fa lafiya? ". Bilya ya fad'i maganar ad'an rud'e. Habib ko kallan Bilya bai yi ba, balle Bilya ya sa ran zai bashi amsa". Bilya ganin haka, Kiran sunan Hassana ya yi ahankali, ya ce, "Amaryar Ogan m.... ". Da sauri Bilya ya ja bakin shi ya rufe, saka makon kallan da Habib ya yi mai, dama kuma sub'utar baki da yaso ya yi. Bilya cikin sosa kai, ya ce, "Madam". Dan ba zai iya Kiran sunan Hassana kai tsaye ba". Hasssana kuma da wani sanyayyan bacci ya fara d'aukarta, d'ago kai ta yi tana kallan Bilya, Bilya ya ce, "Ki tashi mana akwai sanyi ak'asa kar ya yi miki illah". Hassana cikin k'asa da murya sosai kamar za tai kuka, ta ce, " Oga Bilya bazan iya tashi ba, kaina". Bilya shiru ya yi in da ba damar ya rik'e ta ta tashi , Bilya ganin haka maida kallan shiga Habib ya yi, ya ce". "Oga Habib ga abincinka nan ". Habib sosai yaji haushin Bilya, wato sai da ya gama abinda ya yi niyya sannan zai bashi abincin, hakan yasa Habib ya yi banza da Bilya. Bilya ya ya gaji da tsayuwa k'arshe ya aje abincin ya fita , dan ya lura ya b'atama Oganna shi rai". Habib lokacin da sallar azahar ya yi, ya tashi zai ta fi sallah, kwata-kwata ya manta da Hassana da ke kwance a k'asa, ya tashi da sauri dan ya makara, ya take ta da takalmin shi". Wata uwar k'ara Hassana ta yi, wadda sai da taba Habib tsoro, dan sosai ya ta ke ta. Habib juyowa ya yi da sauri yana kallan Hassana, dan ya manta da ita agun. Habib tsaki ya yi zaja k'ofar ya fita". kasan cewar Hassana ba sallah za tai ba, cikaba da kwanciyarta ta yi tana yarfe hannun dan yadda ta ke ji ta yi tarkad'e a hannun. Haka Hassana dai ta ci gaba da kwanciya tana jinyar hannunta, zuwa yanzu kan ya d'an lafa mata, amma hannunfa sosai ya ke mata zugi". Habib sosai ya yi mamaki da ya dawo ya iske Hassana kwance gun, dan ya yi tunanin zata tashi kafin ya dawo. Tsallaketa Habib ya yi, ya je ya zauna". Abin mamaki Hassana har dare tana kwance a Office d'in Habib. Bilya ko da ya zo dan ganin Habib ko ya shirya su tafi, cikin mamaki ya ke kallan Hassana, Bilya kamar ya juya ya tafi, ganin Habib d'in ya shirya, tsayawa ya yi, ya kira sunan Hassana ya ce, "Madam lokaci fa ya yi, ki tashi". Hassana tashi ta yi ta ta fita daga office d'in, daga Bilya har Habib da kallo suka bita". Bayan Bilya ya kai Habib gida kamar yadda ya saba ya dawo ya d'auki Hassana ma". Amota ne Bilya ke tambayar Hassana me ya had'ata da Oga Habib. Hassana cikin jin zafin abinda Habib ya yi mata, ta ce, "Oga Bilya, da muka Shiga Office d'in Oga Habib, nida Supervisor, kamata ya yi ya tambayi kowannan mu abinda ya faru, amma sai ita kad'ai ya tambaya, ta fad'i mai kaf abinda ba ai ba, shi kuma ya hau ya zauna, wai sai na bata hak'uri, ni kuma nak'i bata, shine ya wurgar da ni a inda ka ganni, da zai tai sallah kuma ya take min hannu, kaga hannun". Hassana ta nuna ma Bilya hannunta da ya kunbura". Bilya kallan Hassana ya yi, ya ce, "Wai ni ko meye had'inki da Supervisor ne? ". "Wallahi Oga Bilya haka nan ta tsanan ban mata komai ba". Cewar Hassana". Dariya Bilya ya yi ya ce, 'aiko kin mata komai, ba ke bace kika aurar mata miji, kin san ita a haukarta so take Oga Habib ya aureta ". Hassana da mamaki ta kalli Bilya ta ce, "Tom amma taya ta san hakan? ". "Wai auranki da Habib?, tom ai Manager shi Hajiya ta sa akan komai a d'aurin Auran, inajin shi zai fad'a mata". Haka dai su Hassana suka isa suna fira da Bilya". Hassana zaune ta iske Farida a falo kamar yadda ta saba, ta ci kwalliya tana jiran dawowar Hassana tai ma Habib kunu, ita kuma ta kai mai, dan yau Habib na da wowa ya shiga falon ya ce ma Farida ta yi mai kunun yanzu. Hakan yasa Farida ta k'osa sosai Hassana ta shigo". Hassanan kuma na shigowa ta nufi bedroom d'in ta. Farida kallanta ta yi, ta ce, "Ke kin manta da kunun Oga Habib ne? ". "Yau bazan samu yi ba, banda lafiya". Cewar Hassana na nai man shigewa ciki". Farida saurin rik'o hannun Hassana ta yi, ta ce, "Aiko biki isa ba, ubanki zai ci idan baki da mamai kunun ba! ". Hassana ranta ad'an b'ace ta ce, "Aunty Farida dan Allah idan muna abu dake kibar zagin ubana, saboda ya mutu baya raye, bana jin dad'in zagin Ubana d'in da kike yi". Farida kallan Hassana ta yi ta ce, "Tom k'arya na yi?, Idan baki dama mai ba Ubanki zai sha? ". Hassana cikin jin haushin zagin ubanta d'in da Farida ta kuma yi, ta ce, "Shikenan Aunty Farida, ni kuma bazan dama kunun ba, sai ya sha abinda zai sha". Hassana ta juya zata shiga ciki. Farida ta fincikota ta ce, "Wallahi sai kin dama shi, biki isa ba dan Uwarki! ". Hassana ko fincikewa ta yi daga rik'on da Farida ta yi mata, ta ce, "Aunty Farida dan Allah ki sakan, inajin kunyarki". Hassana ta fad'i maganar cikin sanyin murya". Farida wujijjiga Hassana ta yi, ta ce, "Wuce muje kitchen ki damame kunun, dan Ubanki so kike ki tona min asiri yasan bani ke dama kunun ba, tom Wallahi biki isa ba! ". Hassana tun k'arfinta ta kwace daga rik'on da Farida tai mata, sannan ta ce, "Haba Aunty Farida tunda nace miki bazan iya ba ai ya kamata ki yi hak'uri, inda kullum ni ke damame, tom yau banda lafiya bazan iya ba". "K'arya kike munafuka, kina jin haushin baya kula kine, ni yake kulawa shiyasa, kunu kuma Wallahi sai kin dama shi". Cewar Farida". Wani k'ayataccan murmushi ne ya sub'ukucema Hassana, ta ce, "Haba Aunty Farida dan me zanji haushi dan Oga Habib ya sakin mai kunu, abinda kowa da matsa yinsa a gunsa". Farida d'aure fuska ta yi, ta ce, "ke muje ki dama kunu". "Wallahi bazan dama ba". Cewar Hassana". Farida ko jawo Hassana ta yi. Hassana ta turota da k'arfinta, Farida ta bige da caution. Aiko tana tashi ta kama Hassana da bugu". Farida na bugun Hassana, Hassana na ramawa, nan fa dambe sosai ya b'arke tsakanin Hassana da Farida". B'angaran Habib ko, jin Farida shiru, tashi ya yi ya zo ya amsa da kanshi, dan yunwa yake ji sosai, inda raban shi da abinci tun break fast d'in da ya yi, Bilya ya b'ata mai rai d'azu , bai ci abincin da ya kawo mai ba". Habib tun kan ya shigo falon ya ke jin hayaniya sosai. Hassana ko Allah ne ya bata sa'a ta samu ta had'a kan Farida da bango, Farida sosai taji azaba haka yasa ta shiga kitchen ta d'akko wuk'a ta bi Hassana da ita. Hassana sosai ta rud'e tana za gaye falon tana ihun nai man d'auki, dan tabbas a yadda taga Farida babu abinda zai hana ta kasheta". Hassana na cikin za gayan nai man d'auki, taji shigowar mutum, da gudu ta ruga ta cimimiye Habib tana "Wayyo Allah Oga Habib tai makanni zata kasheni". Farida ko duk da Hassana ta rik'e Habib bata fasa abinda tai niyya ba, dan ita gani take wannan ma ai dama ce Allah ya bata, dan tasan kota kashe Hassana ta kashe banza, wama yasan Iyayanta, idan ansansu ma basu da abinda zasu yi k'ararsu". Hassana ganin Farida ta kuma yo kanta, bayan Habib ta b'oye, tana ihu. Habib shi kanshi ganin Farida da gaske ta ke, tsawa ya da kamata, cewa, "Ke baki da hankaline, kasheta zaki yi! ". Farida ko ai ko saurarar Habib ba ta yi ba, ita dai so take kawai ta caka ma Hassana wuk'ar. Habib k'ok'arin kwace wuk'ar ya yi amma ya kasa, aiko cikin haka Allah yaba Farida sa'a ta yanki Hassana a hannu". Wata uwar k'ara Hassana ta yi, tana cewa, "Wayyo Oga Habib ka rik'eta, zata kasheni Wallahi". Farida ko yankar da taima Hassana ba tai mata ba so take ta caka mata wuk'ar. Habib ingije Farida ya yi, sannan ya bita ya cigaba da kwad'a mata mari kota ina, yana cewa, "Baki da hankaline, yankar da kikai mata bai miki ba, kasheta kike so ki yi, tom idan kika kasheta kina ganin za a kyaleki ne?, iyye! ". Habib yin kanshi ya bar marin da ya ke ta aikama Farida shi, sannan ya samu gu zauna, mai da kallan shi ga Hassana ya ji, jin tsantsar ihunda da take tana yarfe hannu, ga jini sai zuba ya ke sosai, dan sosai Farida ta yanki Hassana ". Habib tashi ya yi ya nufi inda Hassana ta ke tana yarfe hannu tana kuka. Habib na zuwa hannun Hassana ya kamo yana dubawa ganin yadda jini ke zuba". Habib tsawa ya yi ma Hassana ya ce, "Da Allah can kima mutane shiru, sakarya kawai, mara hankaki". Hassana k'asa tai da kukanta tana mai ci gaba da yarfe hannunta. Habib waya ya yi da Family doctor su ya ce yazo yanzu da first aid box, an yaki wata yarinya a hannu ". Aiko cikin minti goma likitan ya iso, wankema Hassana hannun ya yi, ya nad'e inda aka yanka da bandage". Habib ranshi b'ace ga yunwa da yaje ji, bayan likitan ya tafi ya kalli Hassana, ya ce, "ke wata irin fitinanniya ce, yau da mutum biyu kenan ki kai fad'a, na gaji da ganinki, fitinanniyar yarinya kawai". Hassana da sosai ta ji zafin kalaman Habib, hakan yasa ta ce, "Nima dalili d'aya yasa nake zaune nan, kuma shima naci gaba da zama ne dan rok'on da Mommy tai min kar in tafi da aure kaina, amma Wallahi badan shiba nima nagaji! Nagaji!! Nagaj... ". Tsawar da Habib ya yi ma Hassana ce yasa ta yi shiru". Habib tashi ya yi yana nuna Hassana ya ce, "Wallahi! Wallahi!! Wallahi idan har kina hauka tom ki ki yaye, ki rik'a lura da wanda kike magama , naga kina tak'ama da rashin hankali, amma zanyi maganinki!. ".Habib na kaiwa haka ya juya zai fita. Hassana ko shiru ta yi, dan ta tsorata da gargad'in Habib". Farida ko da k'arfinta ta ce, "Oga Habib baka jiba?". Habib da wowa ya yi yana kallan Farida alamun Ina jinki, ta ce, "cewa ta yi wai ita bata tab'a hauka ba, da zaka kiramata rashin hankali". Habib wai gowa ya yi yana kallan Hassana. Hassana ko naganin haka, ta juya da gudu ta shige bedroom d'in ta, taja zata rufe Habib ya tura da k'arfi". Habib na shiga Hassana ta ce, "Oga Habib tsaya kaji dan Allah, Wallahi Allah k'arya take min Wallahi ni bance haka ba, tana jin haushine dan ta sani in dama mata kunu, nace mata yau banda lafiya ta bari sai gobe, Allah ni bance abinda ta ce ba, tana jin haushina ne tai min shairi". Habib shiru ya yi yana kallan Hassana, yana tunanin dama ba Farida ke dama mai kunu ba. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "k'arya kike Ina kika iya dama kunu". "Allah na iya, koma lakacinda Ina zaune part d'inka aini ke damamana". cewar Hassana". Habib shiru ya yi dan baya son abinda za a tuno mai maganar haukar da aka ce ya yi, abin yana tab'a zuciyar shi sosai". Habib fita ya yi yabar Hassana, Habib na shiga part d'in shi ya kira Hajiya Turai a waya amma bata d'aga ba, hakan yasa ya tura mata text kamar haka.". "Mommy ki yi hak'uri ba zan iya zama da yarinyar nan ba, dan haka gobe insha Allah zan sallame ta, kullum cikin fad'a da muta ne ta ke. Nagaji da rabo Mommy ". Hajiya Turai da ta duba text d'in Habib, tana gani ta kira Habib d'in, aiko kira d'aya ya d'aya Hajiya Turai ta ce, "Habib nima dama nagama duk wani shirina da nake yi, dan haka ka sauraran gobe zan dawo". Habib cikin jin dad'in albishir d'in Hajiya Turai, ya tashi ya shiga kitchen ya had'a makan shi tea, yasha". Washe gari Hajiya Turai, jirgin faro ta biyo, dan taji duk abinda ya faru tsakanin Hassana da Farida". K'arfe sha biyu na rana Hajiya Turai ta iso, Bilya ne ya je ya d'akko ta. Habib ko dama yau bai fita aiki ba". Bayan Hajiya Turai ta huta ta , ta kira Habib, da Hassana da Farida, a Falonta, dan acewarta ta gaji yau zata yi ta ta k'are". Hajiya Turai , shiru ta yi, tana nazarin maganar da ta ke son fad'a, sannan zuwa can, ta ce......... ✍️ Nifa bangane ba?, wai me hajiya Turai ki shirin cewa ne? 🥺🥺🥺. Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Shafi na 60&61. Hajiya Turai shiru ta yi, tana nazarin maganar da ta ke son fad'a, sannan zuwa can, Hajiya Turai ta kalli Farida ta ce, "Farida me ya had'aku keda Daughter wanda zai sa ai fad'a harda wuk'a? ". Farida kamar wadda ke jira Hajiya Turai ta tambayeta ta fara zubo zance kamar haka, "Mommy tunda kika tafi nike damama Oga Habib kunu, tom jiya banda lafiya, gashi kuma Oga Habib har yazo da kanshi ya yi min maganar dama kunun, tom shinefa sai nai ma wannan yarinyar magana". Farida ta nuna Hassana da hannu. "Na ce mata dan Allah zan nuna mata yadda akeyi ta damama Oga Habib kunun, shikenan fa Mommy daga magana wai ai ita ba baiwarshi bace, ta yi bauta da shi alokacin da ya ke hauka , yanzu koma ba zata iya yi ba , kuma duk abinda tai abanza wai keda Oga Habib baku gani". D'an numfasawa Farida ta yi sannan ta ci gaba da cewa, "Mommy wannan maganar da ta fad'a akan Oga Habib ita ce ta tafasamin zuciya ,nai mata magana, karta kuma kirama Oga Habib hauk.... ". Tsawar da Habib ya yi ma Farida ce tasa ta yi shiru, zuciyarshi har wani zul-zul ta ke idan ana maganar ya yi hauka. Hajiyar Turai sosai ranta ya b'ace da kalaman Farida, bakamar da ta juya ta kalli Habib ba, taga yadda idonshi ya kad'a ya yi jawur, kuma tasan ya yadda da kalaman Farida". Hajiya Turai mai da kallanta ga Hassana ta yi, yadda ta yi tsuru, daga gani dai itama cikin tashin hankalin k'aryar da Farida tai mata take". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter me ya had'aki da Farida? ". Hassana cikin natsuwa da sanyin muryarta, ta fara ma Hajiya Turai bayani kamar haka, "Mommy kullum idan Oga Habib yasa Aunty Farida ta dama mai kunu, ni Aunty Farida ke sawa in dama, ban tab'a yima Aunty Farida musu ba sai jiya, shima saboda banda lafiya ne, nace mata bazan iya damawa ba, Aunty Farida tai ta zagina ta uwa ta uba, wai dole sai na dama shi, sai banji dad'in zagin da ta ke ma Babana ba kodan ya mutu, sai nai mata magana, ta kuma zagin shi, ni kuma nace inda haka ne bazan dama kunun ba, shine fa ta kama jana wai sai na dama shi, tana kuma zagina, ni kuma na tureta, daga nan muka kama fad'a ta d'akko wuk'a wai sai ta kasheni, Allah bai bata sa'a ba shine ta yankan, wannan yankar da kika gani Mommy ". Hassana ta fad'i maganar tana nuna ma Hajiya Turai yankar hannunta". Hajiya Turai shiru ta yi, dan dama ita ko bata ji ta bakin Hassana ba, tasan Farida ce bata da gaskiya". Hajiya Turai kallan Farida ta yi, ta ce, "Shikenan Farida ta shi ki shiga ciki, Hassana kuma insha Allahu daga yau zamanta yak'are a cikin gidan nan". Farida cikin farincikin da ta kasa b'oyewa ta d'ago kai tana kallan Hajiya Turai ta ce, "Nagode Mommy ". Sannan Farida ta tashi ta yi kamar ta shiga side d'in ta, ta lab'e dan jin abinda Hajiya Turai za taima Hassana ". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ki yi hak'uri kinji, nasan ban kyauta miki ba, na yi miki alk'awari ban cika miki ba, na tafi, tom a gaskiya na tafi ne alokacin saboda bazan iya raba auranki da Habib ba, kuma banyi niyyar dawowa yanzu ba, amma jin labarin fad'an da kukai da Farida jiya yasa nadawo, saboda nasan hakan na iya k'aramiki tsanar zaman gidan. Wato jiya da nadawo na dawo ne dan in cika miki alk'awarin da nai miki daughter, amma da na zauna nayi tunani sai naga shi kanshi auranki da Habib Allah ne ya k'ulla shi bani ba, me yasa Habib da yafara ciwo bai yadda da kowa ba sai ke, wato kenan Allah ya tsara aure a tsakaninku ne shi yasa k'addarar ta fad'a kanki". Shiru Hajiya Turai ta yi, na d'an wani lokaci, sannan ta kalli Habib, da yake zaune babu alamun fara'a a fuskar shi, kai daga kaganshi kasan bayajin dad'in yanayin". Hajiya Turai sunan Habib ta kira, ta ce, "Habib! ". Habib kallan Hajiya Turai ya yi gaban shi na fad'uwa, dan shi abinda ya k'osa ya ji, ya ji Hajiya Turai ta ce ta da tse auran shi da Hassana". Hajiya Turai, ta kuma cewa, "Habib, ada nayi niyyar raba auranka da daughter, amma ayanzu na fasa saboda wasu da lilaina, sannan auranka da ita wani rubutancan al'amarine, dan haka na soke maganar raba auranku, Ina fatan da ga kai har Hassana zaku min biyyya akan k'udirina? ". Habib shiru ya yi bai tan kama Hajiya Turai ba, sai zuwa can, ya fara magana cikin wata irin murya ". Habib ya ce, "please Mommy idan maganar aure ce da kike min zanyi yanzu, kiban duk lokacinda ya yi miki, amma ki fahimci abinda nake nufi Mommy, da farko ni ban tab'a sha'awar rayuwa da mai aiki a k'ark'ashina ba, sannan Mommy Friend's d'ina zasu yi min dariya suji Ina auran staff d'ina, kuma cleaner, dan Allah Mommy ki fahimtan, ni zanma yarinyar duk abinda kike so, amma banda wannan Mommy ". Habib ya idasa maganar cikin damuwa ". "Habib ba wai kai ba, Hassana ma ayanzu inajin na isa da ita akan maganar nan, nariga na gama magana, yau-yau d'innan zaku tare a gidanka! ". Habib tashi tsaye ya yi daga zau nan da ya ke, yana kallan Hajiya Turai, dan sosai maganarta ta k'arshe ta furgitashi". Habib kusa da Hajiya Turai ya dawo ya zauna, ya ce, "Mommy naji na yarda zan zauna da ita, amma Mommy a gidannan dan Allah ". Hajiya Turai kallan Habib ta yi yadda ya wani rud'e ta ce, "Habib na yanke wannan shawaran ne saboda Hassana idan taci gaba da zama a nan Fad'a zasu yi ta yi da Farida, ni kuma inada kawaici bana iya korarta, shi yasa kawai na yanke shawarar ta koma gidanka da zama". Habib cikin sauri ya ce, "Mommy ni zan kori Farida yau-yau d'innan idan ke baza ki iya ba". "Habib nagama magana dan tun jiya kafin in dawo na sa anke komai agidan, dan haka bana son wata doguwar magana nariga nagama magana, dan haka zaka iya tafiya". Cewar Hajiya Turai ". Habib bai k'ara magana ba ya tashi ya fita. Hajiya Turai saurin juyawa ta yi tana kallan Hassana jin shashshek'ar kuka. Hajiya Turai, hannun Hassana ta kamo, ta ce, "Daughter ki yi hak'uri idan na b'ata miki, amma nasan insha Allah watarana daga ke har Habib zaku fahimce ni, dan Allah daughter ki yi hak'uri na rok'eki, idan ma zaman kad'aici kike tunani zan baki Maimuna ta rik'a d'ebe miki kewa, ke dai abinda nake so da ke karki biyema miskilanci Habib dan Allah , ki gaida shi ko ba zai amsa miki ba, mahakurci mawada ci ne, yanzu kije ki yi wanka ki kwanta ki huta". Hassana kamar jira ta ke, da sauri ta tashi ta shiga bedroom d'in ta. Hajiya Turai da kallo tafi Hassana". Farida ko cikin tashin hankali ta fita ta kitchen ta nufi gidan Hajiya Zaliha friend d'in Mahaifiyarta". Farida nazuwa, ta sama Hajiya Zaliha kuka. Da kyar Hajiya Zaliha ta samu ta lallashi Farida, sannan ta ce, "Yanzu daughter fad'amin me Habib d'in ya kuma yi miki? ". Farida cikin kuka ta ba Hajiya Zaliha labarin duk abinda ya faru, ta had'a mata da tarewar da Hassana za ta yi yau, kamar yadda taji Hajiya Turai ta ce". Hajiya Zaliha lallashin Farida ta yi, sannan ta ce, "barni da su daughter in sun san wata ai basu san wata ba, yanzu bu d'aya ya rage mana inda tabar gidan da zama, ganin Habib da ita zai miki wuya, dan haka abinda zaki yi yanzu aiki zaki naima a Sanat yughurt". "Aiki kuma Mommy? ". Cewar Farida". "Eh aiki zaki naima Farida acan, dan dole sai kina tare da Habib burunmu zai cika idan ki kai nisa da shi abin ba zai yuwu ba, dan haka gobe ki shirya kije neman aiki gun"Wani murmushi Farida ta yi, ta ce, "Tabbas wannan dama ce babba Mommy, ni kuma zanyi amfani da dabarunki in had'a da nawa". Dariya Hajiya Zaliha ta yi, ta ce, "Yauwa daughter kin fara ganewa, yanzu sai goban in kin samu aikin sai mu tsara yadda abin zai kasance". Haka Hajiya Zaliha tafa tsarama Farida yadda zata kasan ce idan ta samu aikin". B'angaran Hassana ko, ko da ta kwanta kasa bacci ta yi, juyi kawai ta ke, dan sosai ta ki jin furgici idan ta tuno wai yau zata tare a gidan Habib. Hassana ganin kwanciyar bayi mata za tai ba, tashi ta yi ta nufi part d'in worker's d'in gidan, ta je wajan Jimmai ko zata ji sauk'in yadda ta ke ji, dan Jimmai ta bata shawarwari masu kyau na kwantar da hankali". Hassana inda ta saba ganin Jimmai ta sameta , Jimmai da fara'arta ta tari Hassana, tana cewa, "Tom yau kuma me yafaru, dan ni dai tunda kika bar nan na bar ganinki sai taki ta kawo ki". "Aunty Jimmai ki yi hak'uri, Ina cikin damuwa Nazo ne ki fad'amin magana mai dad'i ko zanji dad'i". Cewar Hassana ". Jimmai hannun Hassana ta kama suka zauna, sannan ta kalli Hassana ta ce, "Fad'amin damuwaki kinji Hassan? ". Hassana cikin damuwa ta ce, "Sister Jimmai yau zan tare a gidan Oga Habib, Hajiya ta nuna min fin k'arfi ta ce bazata raba auran ba, Wallahi Sister Jimmai idan kikaga yadda Oga Habib ya rud'e tsabar bai son zama dani abin zai ta damiki hankali, ni kaina nasan Hajiya ba taima Oga Habib adalci ba, saboda Oga Habib ya taka mata kai ma su girma da kwari arayuwarshi, ya kamata Hajiya ta had'ashi da dai-dai dashi amma bani ba". Hassana ta idasa maganar tana share hawayanta". Jimmai hannun Hassana ta kamo ta ce, "Hassana ki kwantar da hankalinki Oga Habib bai isa ya raina miki ba, dan haka karma kiwani k'ara tunanin wai ya wuce da ajinki. Yanzu Hassana idan kin ce ma Habib ya sakeki, kin san kin b'atama Hajiya, kuma kina tunanin zata ci gaba da zama da ke, idan kuna kince ki koma garinku, ko kin san zaki fuskanci wata irin rayuwa fiye da wadda kika baro,dan haka ni Ina baki shawarar ki yi hak'uri ki zauna da Oga Habib lafiya, duk abinda zai miki ki yi hak'uri, watarana sai labari. Yanzu me ye kika san Oga Habib naso? ". "Ni ban san abinda ya ke so ba". Cewar Hassana ". Jimmai kallan Hassana ta yi, ta ce," tom ni zan fad'amiki abinda Oga Habib ke so ai farkon zuwana gidan nan, b'angaran Hajiya na fara aiki, Oga Habib na son kunu sosai, dan haka ya kamata ki koyi kunu kala-kala". Hassana Kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Tom ta ya zan koya, idan ma na koya kina tunanin zai sha idan nayi? ". "Tsab ma kuwa zai sha, ai ke zaki sashi ya sha, akwai wata makaranta ta koyan girkegirke idan kin wuce national assembly na nan apo School d'in take, tom amma gaskiya da tsada fa, amma zaki iya girgi kala-kala, yanzu babu yadda za ai ki samu kud'i gurin Hajiya Turai? ". Hassana kallan Jimmai ta yi, ta ce, "Babu, amma tunda na fara aiki a Sanat yughurt basu tab'a biyana ba, dan haka zanma Oga Bilya magana idan suka ban sai in yi amfani dasu". "Yauwa ki mai cikin satin nan ki fara zuwa". Hassana godiya taima Jimmai sannan tai mata Sallama ta tafi". Da daddare bayan Sallar Issha'i, Hajiya Turai jin Habib shiru har yanzu , kiran shi awaya tai, ta ce, "Hello Habib kazo yanzu Ina son ganinka". Hajiya Turai na fad'in haka ta kashe wayarta, sannan ta tashi ta shiga ciki , tana kallan Hassana da ke zaune. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Wai daughter har yanzu biki shiga wankan ba ga Habib nan zuwa, shikenan in bazaki wankan ba in kinje can kinyi ai". Hassana batare da tace komai ba, ta tashi ta shiga wankan. Kafin Hassana ta fito Hajiya Turai ta d'akkoma Hassana wata doguwar riga fara mai ratsin pink da tazo mata da ita, rigar ta yi kyau sosai". Hassana na fitowa Hajiya Turai ta bata rigar, sannan ta fita ta bata gu ta shirya". Hassana sama-sama ta shafa mai ta sa rigar. Masha Allah sosai rigar ta amshi Hassana ta fito mata sosai da sharp d'in ta. Hassana bayan ta shirya ci gaba da zamanta ta yi". Can Falo kuma, Habib zaune gaban Hajiya Turai, Hajiya Turai kallan Habib ta ti, ta ce, "Habib ga Hassana nan amana na baka ita, idan ka cutar da ita ba baki naima ba, amma Allah ba zai barka ba , Habib ko dan halaccin da taima dan Allah karik'eta amana, idan kuma ba kai mata dan haka ba, ka yi dan maraicinta, kasan dai hukuncin wanda ya zalinci maraya, bari in kirata ku tafi, ka sa Bilya ya kaima kayanka ko? ". Habib ciki-ciki ya amsa ma Hajiya Turai da cewa, "Eh ya kai". Hajiya Turai ta shi ta yi, ta je bedroom d'in ta, zaune ta iske Hassana ta yi ta gumi. Hajiya Turai hannun Hassana da tai ta gumi ta koma, sannan ta d'akko oud aribian perfume masu k'amshi ta shafama Hassana, ta ce, "A akayanki da nasa miki, kirik'a shafawa kinji daughter, nasan kuma ke dama mai son tsabta ce, na ba tailor na d'in kayanki, ya d'inka miki, Bilya zai amso miki, dan Allah daughter karki biyema Habib kinji, ko ba komai kinga yanzu yana matsayin miji gareki ki ne, ki kyautata mai kodan kwad'ayin lada agurin Allah, ki rik'a girki da shi kullum koda ba zai ciba karki ki hanashi kinji, daughter, Allah ya yi miki Albarka Allah ya albarkaci auranku, Allah ya kauda fitina a tsakaninku". Hassana kuka take sosai, a haka dai Hajiya Turai ta kawota Falon. Habib na zaune da wayar shi yana danne-danne. Hajiya Turai zama ta yi, ta kalli Habib ta ce, "Habib ga daughter nan nabaka amana, kaji min da ita sosai, karka sake kabar hawayanta su zuba k'asa". Habib tab'e baki ya yi". Hajiya Turai kamo hannun Hassana ta yi, ta ce, Muje in rakaku". Hajiya Turai har Mota ta kai Hassana wadda har yanzu ta ke kuka. Bayan Hajiya Turai ta sa Hassana mota ne Habib ma ya shiga". Hajiya Turai tana nan, tsaye Habib ya tada motar yaja suka tafi. Sannan Hajiya Turai ta koma cikin gida tana hawayan farinci......... ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment Sister 🤝. Idan naga Comment da yawa, Gobe zaku ya Update idan naga kad'an tom zafa kuji🤐🤐🤐. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Shafi na 62&63. Hajiya Turai tana nan tsaye Habib ya tada motar yaja suka tafi. Sannan Hajiya Turai ta koma cikin gida tana hawayan farinciki. Kasan cewar bawani shahararran nisa bane tsakanin gidan Hajiya Turai da gidan Habib, hakan yasa cikin mintina kad'an suka isa. Gida ne babba masha Allah, kallo d'aya za kaima gidan kasan ankashe kud'i sosai wajan yinsa. Habib na yin parking bai bi takan Hassana ba ya fita daga motar ya barta nan, tana aikin kuka. Hassana ko jin Habib ya fita, itama fita ta yi tabi bayan shi". Falon mai ma dai-dai cin girma, wanda ya k'oshi da kayan more rayuwa. Inda akaima falon adon Orange & White, color d'in sai ta kuma fito da madarar kyau na Falon". Habib na shiga falon ya yi side d'in shi, inda ita kuma Hassana ta baje ko linta a falon, ta zauna kan two seater". Haka Hassana ta gama kukanta daga k'arshe ta lallashi kanta ta yi hak'uri ta yi shiru. Hassana na nan zaune ta na tunane-tunane a haka bacci ya kwasheta, batare da ta cire kayan jikinta ba, ko ta naimi inda bedroom d'in ta take ba". Habib ko da ya shiga bedroom d'in shi, toilet ya shiga ya watsa ruwa ko zai ji sanyi a zuciyar shi, shima dai kusan haka ta faru da shi yana fitowa ko mai bai shafaba ya zauna kan lover chair yana tunanin yadda zai yi ma Hajiyarsa idan ta huce Hassana ta koma can da zama ala bashi shi sai ya barmata gidan Hajiyar shi yadawo nan ya ci gaba da zaman shi, Habib na wannan tunanin bacci ya kwasheshi shima anan". Cikin dare yunwa ta tada Habib, dan tun break fast d'in safe raban shi da yasama cikinshi wani abu,dan tunda Hajiya Turai tai ma Habib maganar ta rewar Hassana ya hana kanshi sukuni. Habib tashi ya yi ya je kitchen ko ruwan zafi ya samu yasa tea, dan sosai ya ke jin yunwa". Habib mamaki ya yi da yazo yaga Hassana kwance sai baccinta ta ke. Tsaki ya yi ya tab'e baki ya ce, "Wannan yarinyar bata da hankali kwata-kwata. Habib kitchen d'in yaje, ya samu ya dafa ruwan zafi yazo yasha tea". Hassana tunda ta kwanta ba ita ta farka ba sai 6:00AM, tana tashi, side d'in da ta ke da tabba cin nata ne ta shiga, anan taga kayanta na sawa, Hassana sallah ta farayi, sannan ta cire doguwar rigar jikinta ta samu wata wadda bata kai waccan nauyi ba tasa, ta shiga kitchen ta d'ora ruwan tea, sannan ta soya wainar kwai. Hassana na gamawa ta d'auki na Habib ta kai mai kan derning, ita kuma nata ta shiga bedroom d'in ta dashi. Hassana sai da ta yi wanka ta shirya cikin wata doguwar rigar, inda kayan duk sune, sannan ta zauna ta fara break fast ". Habib ko bayan ya tashi ya yi sallar asuba, komawa ya yi ya kwanta. Sai 7:52AM, Ya farka da sauri ya shiga wanka, yana fitowa ya yi shirinsa na fita. Habib da bai san Hassana ta yi wani abun break fast da shiba, yana gama shirinsa ya fita abinsa". Zaune Habib ya iske Bilya acikin mota yana jiran shi, hakan yasa Habib na zuwa, Bilya yaja motar zasu tafi". Bilya har ya tada Motar Habib ya tsayar da shi ya ce, "tsaya ina zuwa". Bilya da katawa ya yi , Habib ya shiga ciki. Dai-dai nan ma Hassana ta fito itama tana sauri zata tafi dan tasan ta makara sosai". Hassana tsayawa ta yi ganin Habib, kuma kamar gunta yazo, Hasssana baki ta bud'e ta gaida Habib, Habib ya katseta da cewa, "Karki sake kizo aiki yau, sai Hajiya ta koma". Habib na fad'in haka ya juya ya tafi, dan yasan indai Hajiya Turai tasan Hassana na zuwa Sanat yughurt aiki, yasan zata hana, shi kuma baya son hakan ". Hassana ko cikin jin dad'i ta koma ciki, dama ba son zuwan take ba, dan tun abinda Billy tai mata taji ta tsani Sanat Company gaba d'aya. Hassana komawa ta yi tana mai jin dad'in hakan". Wajan misalin 12:15PM, Hajiya Turai da Hajiya Murja mahaifiyar Farida suka zo gidan, lokacin Hassana na zaune a falon tana game awayarta da Hajiya Turai ta bata". Hassana cikin nuna jin dad'in ganin Hajiya Turai ta tarbe su, inda Hajiya Murja sai tab'a baki take, dan acewarta gidan da Farida ya dace ba da Hassana ba". Hassana ruwa ta kawoma su Hajiya cikin fresh, sannan ta gaida su cikin girmamawa, sun d'an jima da zuwa Kafin suka tafi. Dan ita Hajiya Turai bata so zuwan ba ma, Hajiya Murja ce ta matsa mata, ita kuma gulma ta kawota, dan ganin yadda gidan yake". B'angaran Farida ko kamar yadda su kai da Hajiya Zaliha haka akayi, da wuri ta shirya, ta nufi Sanat yughurt nai man aikin". Koda Farida ta isa direct Office d'in Habib ta naimi izinin shiga. Lokacin Habib nata aiki a laptop, Bilya ya shiga Office d'in, ya ce, "Oga Habib Farida ce ke son ganinka, zata iya shigowa? ". Habib shiru ya yi yana tunanin lafiya Farida ke son ganin shi,kai ya d'aga ma Bilya, alamun zata iya shigowa ". Farida shiga ta yi. Bayan ta zauna ne, ta gaida Habib kamar yadda ta saba, sai kuma taja bakinta ta yi shiru. Habib da katawa ya yi da abinda ya ke yi ya yi, ya kalli Farida ya ce, "Lafiya dai ko? ". Farida sosa kai ta yi, sannan ta ce, "Uhm, Oga Habib dama nagaji da zamane haka nan, shine na yanke shawarar inzo nan ko zan samu aiki". Habib kallan Farida ya yi, ya ce, "Gurin manager zaki, bani ke d'aukar aiki ba". Shiru Farida ta yi, sannan ta ce, "Oga Habib ba lallene manager ya d'aukan ba, saboda wata friend d'ina ta tab'a zuwa nai man aiki anan manager yace mata sun b'ar d'aukar aiki suna da wadatattun ma'aikata". "Kije ki ce mai nina turoki, zai d'aukeki". Cewar Habib yana mai ci gaba da abinda ya ke yi". Farida badan ta soba ta tashi ta fita daga office d'in Habib. Office d'in manager Farida ta shiga. Cikin girmamawa da mutunta juna Farida suka gaisa da manager, inda manager yasan Farida sosai a gidansu Habib. Bayan sun gama gaisawa ne, manager ya tambayi Farida lafiya". Farida cikin hikima ta fara magana kamar haka, "Wallahi manager nagaji da zaman gida ne, shine nace bari inzo nan in rik'a ta ya ku aiki".Dariya manager ya yi, ya ce, "Tom ai shikenan, wani b'angare kike so? ". Farida shiru ta yi dan in son samu ne, b'angaran da Hassana ta ke ta ke so, tom amma kuma bata san b'angaran da Hassana ta ke ba, hakan yasa Farida ta ce, "Manager ni ko ina da ruwana". "Ok, tom shikenan, hakanma ya yi ai". Cewar Manager. Hassana kallan manager ta yi, ta ce, "Manager zan iya fara aiki yau? ". "Sosai ma kuwa, zaki iya farawa". Farida cikin jin dad'i ta fita Office d'in manager, haka Farida tai ta aikin duba ko ina ko zata ga Hassana amma bata ganta ba, ahaka dai har lokacin tashi ya yi, Farida bata ga Hassana ba, hakan ya tabbatar mata da Hassana bata zo Aiki yau ba". Washe gari ma haka Farida tazo aiki ,Haka Farida ta wuni bata ga Hassana ba, gaban Farida fad'uwa ya farayi, tana jin tsoran ko dai Hassana ta bar aikine. Yauma dai haka Farida ta tashi batare da taga Hassana ba, gashi bataga wata hanyar da zata samu shiga Office d'in Habib ba, dan sai ya san da zuwanka kake shiga". Hassana ko jita ke kamar kar Hajiya Turai ta tafi dan bata son k'ara zuwa Sanat yughurt, gashi bata iya kai k'arar Habib wajan Hajiya Turai, akan zuwanta aikin". Yau kwanan Hassana shida kenan agidan Habib, kuma har yanzu babu wata magana da tak'ara shiga tsakanin Habib da Hassana, Hassana ganin Habib ko tayi abin breakfast da shi ba sha yake ba, yasa ta daina yin komai da shi, iya cikinta ta ke yin komai. Kafin ta fito da safe Habib ya tafi, da daddare kuma Kafin ya dawo ta koma bedroom d'inta, Habib ko ganin batare da Mahaifiyarsa ya ke ba, yanzu sai kusan 10:00PM ya ke dawowa gida, hakan yasa basa had'uwa da Hassana ". Farida ko yau kwananta biyar kenan da fara zuwa aiki, amma har yanzu bata ga Hassana ba, hakan ya tabbatar mata Hassana ta bar aiki. Hakan yasa Farida yau da kuka ta isa gidan Mahaifiyarta. Bayadda Hajiya Murja ba ta yi da Farid ba ta yi shiru, amma Farida tak'i. Daga k'arshe ma tashi ta yi, ta had'o kayanta ta ce, ita tafiya za tai ta gaji, Hassanar ma tak'i zuwa Sanat yughurt d'in, wama yasani ko Oga Habib ya hak'ura yana sonta yanzu, in da mai yasa tabar zuwa aiki". Hajiya Murja waya ta d'akko tai waya, ita dai Farida duk tana kallanta, Hajiya Murja ta ce, "Hello Habu dan Allah kuzo yanzu aiki za ku yi min adaran yau d'in nan". Farida kallan mahaifiyarta ta yi, ta ce, "Aikin me za su yi miki?, nifa bana son kina tarayya da su habu". Murmushi Hajiya Murja ta yi, ta ce, "karki damu Farida wannan shine aikin k'arshe da zanyi da su". Hajiya Murja na nan zaune ita da Farida su Habu suka shigo gidan su Uku. Babban cikinsu d'in kallan Hajiya Murja ya yi, ya ce, "Hajiya wana aiki za muyi miki? ". "Wata yarinya nake son ku d'auke ku yi nisa da ita sosai sannan ku yi mata gargad'i in ta koma tom kasheta za kuyi". Cewar Hajiya Murja ". Dariya Habu ya yi, sannan ya ce, "Bamu address d'in gidan". Hajiya Murja wata takarda ta mik'ama Habu, mai d'auke da address d'in gidan da kuma photon Hassana". Hajiya Murja kallan Habu ta yi, ta ce, "Na san kun iya aiki, bana son kuskure zan baku dubu d'ari biyu, ya yi muku? ". "Ba komai Hajiya ai ana tare". Cewar habu". Bayan su Habu sun tafi, Farida ta kalli Mahaifiyarta ta ce, "Mommy kin kawo shawara mai kyau, dama tuntuni haka mukai da yanzu mun huta". Dariya Hajiya Murja ta yi, ta ce, "ai shiyasa na zab'i su Habu, nasan sun iya aiki babu kuskure, kuma suna da asiri basa kamuwa". Yau Habib da wuri ya dawo aiki, saboda yana son zuwa gaida Maifiyar shi. Hassana na falo zaune ita kad'ai, sai T,V, da keta aiki , Hasssana najin dawowar Habib, ta ji kamar ta tashi ta shige bedroom d'in ta , sai kuma ta hak'ura ta tsaya, saboda sun rabu da gaisawa, tasan yanzu k'ila yama manta da ita". Hassana na wannan tunanin Habib ya shigo. Hassana cikin sanyin murya ta ce, "Barka da dawowa Oga Habib ". Habib kallan Hassana ya yi ya wuce ci ki, dan ko motsinta baya ji, hakan yasa yama manta su biyu suke rayuwa agidan". Habib cikin sauri ya shirya ya nufi gidan Hajiya Turai. Habib a bedroom ya iske Hajiya Turai zaune kan abin Sallah ta Idar da sallar issha'i. Habib koda ya gaida Hajiya Turai hararar shi ta yi, ta ce, "Ina daughter fa? , bayan nace ma kazo da ita muyi sallama gobe zan wuce da safe" "Ba daga gida nake ba". Cewar Habib". Hajiya Turai, wata leda ta mik'ama Habib ta ce, "Gashi dama ita bake son gani, yanzu ai sai ka kai mata, Habib dan Allah ka yi hak'uri ku zauna lafiya da daughter,Ni dai nasan daughter bata da damuwa, amma kai ka d'auki girman kai ka d'ora ma kanka". Haka Hajiya Turai ta dad'e tana ma Habib nasiha, daga k'arshe ya d'auki ledar da taba shi ta ce ya kaima Hassana , Habib ta fiya ya yi tare da yima Mahaifiyar shi fatan sauka lafiya, inda tace gobe da wuri zata wuce". Habib bashi ya dawo ba, sai 9:15PM lokacin Hassana ta yi nisa a bacci. Habib aje ledar da Hajiya Turai ta bashi ya yi a falon ya shiga bedroom d'in shi, ya kwanta dan yajiya sosai ya ke ji". Hassana ko ta dad'e ba tai bacci ba, dan haka nan yau sai Allah ya jarabceta da tsoro, hakan yasa har sai da taji alamun dawowar Habib bacci ya kwasheta". 1:00AM, k'arar Harbin bindiga ya tada Hassana daga bacci. Su Habib sai da su kai harbi Uku sannan suka fara buga k'ofar falon Habib ". Habib cikin tsoro ya farka ya fito. Hassana ko jikinta na rawa ta fito itama daga bedroom d'in ta. Habib ta gani tsaye yana lek'awa ta wata 'yar hududa". Su Habu wata bingidar su ka kuma k'ara harbawa. Hassana ta fasa k'ara da k'arfi jikinta na rawa, tazo ta rik'e Habib.". Habib ko hannu yasa ya rufe ma Hassana baki, a kunnanta ya yi mata magana, ya ce, "Ke da Allah can ki yi shiru, in ba haka ba zan bud'e k'ofar in wurgaki". Hassana najin haka ta yi, shiru tana mai k'ara rik'e Habib". Habib kuma so yake ya d'akko wayarshi da yabari a bedroom d'in shi, ya kira akawo masu d'auki amma Hassana ta cikwikwiye shi, ta hanashi ta fiya. Hakan yasa Habib cikin fad'a-fad'a ya ce, " Ke mahaukaciyar wana gari ce, bazaki sake ni ba in d'akko waya ta? ". "Wayyo Oga Habib muje kad'akko dan Allah, Wayyo Allah zasu shigo". Su Habu ko wani k'arfe su kasa ji kake k'ofar ta ce, k'asssss. Hassana jin k'ofar ta b'alle wani ihu ta fasa, sannan ta .................. ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝 Comment & Please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Shafi na 64&65. Su Habu ko wani k'arfe su ka sa, ji kake k'ofar ta ce, k'asssss.. Hassana jin k'ofar ta b'alle wani ihu ta fasa, sannan ta bi Habib da gudu bedroom d'in shi, tana cewa, "Wayyo Oga Habib gasu nan, sun shigo sun b'alla k'ofar". Habib ko da ke tsaye yana kiran commissioner 'yan sanda akawo masu d'auki. Hassana jin Habib ya yi banza da ita, yana tsaye ya gama wayar da tsabar rud'ewa bata ji me yake cewa ba". Wani bugu su Habu suka kuma yima k'ofar". Hassana sosai ta rirrik'e Habib tana cewa, "Wallahi sun shigo dan Allah ka b'oye ni! ". Habib tsawa ya yi ma Hassana, dan shima kusan arud'e ya ke gashi har yanzu baiga wani alamun za'a kawo masu d'auki ba. Turai Hassana ya yi daga jikin shi, ya ce, "Idan kika sake rik'eni zakiga abinda zan miki, inda ance miki zasu iya b'alla k'ofar nan ne". Su Habu ko kamar sunji abinda Habib ya ce, suka ce, "Wallahi idan har baku bud'e k'ofar nan ba, muka b'alleta muka shigo duk sai mun kasheku, amma yanzu idan kuka b'ode abu kawai zamu amsa mu wuce salin'-alin". Hassana kuka ta fasa tana kamo hannun Habib ta ce, "Dan Allah Oga Habib muje ka bud'e musu,kaji abinda suka ce ko?, Ni dai ka bud'e musu ". Habib ganin tabbas zasu iya b'alla k'ofar yadda suke bugunta, dan ga k'ofar nan sai wani k'ara take, na alamun ankusa cinnasara da k'ok'arin bud'eta d'in da ake. Hakan yasa Habib ya je ya bud'e k'ofar, Hassana kuma na bedroom d'in shi duk ta rud'e ". Habib na bud'e k'ofar d'aya daga cikinsu ya d'orama Habib bindiga akai, yana nuna mai photo'n Hassana, ya ce, "Ina wannan yarinyar ta ke? ". Habib shiru ya yi bai yi magana ba. Wanda ya d'ora bindiga kan Habib ya ce, "Kai zaka yi magana koko saina bugama bindigar nan". Habib cikin jarumta ya ce, "Abu kuka ce zaku amsa ku wuce,dan haka ku fad'a min me kuke so? , ko meye zan baku".kusan atare suka tun tsire da dariya, sannan wanda ya d'ora mai bindigar ya ce, "kai allaji baka ganewa, ai ita ce abun da muke nufi, amma kaci sa'a bacin ance karmu tab'aka da yanzu kaji jiki". Babban cikin nasu, wanda ya ke kamar shine ogansu, kallan su ya yi, ya ce, "ku bincukota duk inda ta ke, nasan tana cikin gidan nan ". Tashin farko bedroom d'in Habib suka Shiga. Allah sarki tsaye suka iske Hassana ko ina najikinta rawa yake, aiko suna zuwa suka tasa k'eyarta suka ce"Muje ". Hassana ihu ta kama tana rok'ansu tana cewa, "Dan Allah ku yi hak'uri, dan Allah ina rok'anku..... ". Haka Hassana tai ta kuka tana rok'insu su rabu da ita, amma ko sauraranta basu yiba". Suna zuwa dai-dai saitin Habib Hassana ta rik'o hannun Habib tana kuka, tana cewa, "Wayyo Allah Oga Habib dan Allah karka bari su tafi dani... ". Habib kallan Hassana kawai ya yi, yarasa bakin magana, idan ma zai yi maganar bai san me zai ce ba". D'aya daga cikinsu ko tun kud'a Hassana ya yi da k'arfi wanda yasa ta saki hannun Habib bata shirya ba. Habib na tsaye yana kallan su haka suka fita da Hassana tana ihu tana kiran sunan shi". Habib cikin tashin hankali ya ciro waya ya kuma kiran commissioner of police, amma bai d'aga ba, haka Habib ya yi ta kiran shi shi kuma yak'i d'agawa. Can Habib ya ji tashin bindiga kota ina. Habib bud'e k'ofar ya yi ya fito, ji ya yi an fisgo hannun shi. Cikin tsoro Habib ya ke kallan wanda ke rik'e da hannun shi. K'asa-k'asa wanda ya rik'e hannun Habib d'in ya ce, "Ranka shidad'e karka damu, ma'aikatanmu duk suna nan, tun da kakira ai muka zo, yanzu haka anbisu,ka yi hak'uri ka koma ciki insha Allah babu abinda zasu yi mata". D'an sanda kama hannun Habib ya yi ya maida shi har falon shi, sannan yaja mai k'ofar, ya fita". Haka Habib ya zauna yana mai jiran tsammanin ganin andawo da Hassana amma shiru. Wayar shi ya d'auka ya kuma kiran commissioner amma bai d'auka ba. Habib ya'aje wayar kamar da minti biyar kira ya shigo wayar shi, d'agawa ya yi, yana d'auka akace ranka shidad'e Allah ya bamu sa'ar amsar yarinyar, amma bamu kama ko d'aya daga cikinsu ba". "Ok, ina yarinyar... ". Bai idasa fad'in abinda ya ke son fad'a ba, Hassana ta fad'o falon a rikice tana kuka. Tana zuwa ta fad'a kan Habib jikinta ko ina rawa ya ke, dan har yanzu ba wai ta dawo natsuwarta bane". Daga can b'angaran D'an sanda ya ce, "Yauwa kamar ita ce ta shigo ko? ". Jin kukan Hassana da ya yi". Habib da "Eh ". ya amsa mai, sannan ya ce, "Zamuyi magana gobe, saboda baya jin shi sosai saboda kukan Hassana". Habib kallan Hassana ya yi dake rik'e da shi ga jikinta ko ina har yanzu rawa ya ke, Habib d'ago Hassana ya yi, yana kallanta, karo na farko kenan da Habib ya tab'a kallan Hassana haka. Girgizata ya yi sannan ya ce, "Ke kinatsu mana, sun wuce, ki tashi ki je ki watsa ruwa zaki ji sanyi". Habib ya fad'i maganar yana mai tashi da Hassana". Habib daga ya saki Hassana sai ta tafi zata fad'i, Habib cikin fad'a-fad'a ya ce, "Wallahi ki mik'e ko in sake ki ki fad'i". Hassana cikin narkarkar murya ta ce, "Wayyo tom ni ka kaini bedroom d'ina". Habib tsaki ya yi sannan ya rik'e Hassana ya kaita bedroom d'in ta. Habib juyawa ya yi zai fita, Hassana ta yi saurin kamo hannun shi, kamar za tai kuka, ta ce, "Ayyah nifa tsoro nake ji". Habib tsawa ta yi ma Hassana,ya ce, "Tsoran ya kashe ki, dama nasani bari nayi suka tafi da ke kowama ya huta". Habib na fad'in haka yaja k'ofar Hassana ya fita". Hassana guri d'aya ta dun k'ule tana kuka dan tsoro ta ke ji sosai, gani take kamar zasu dawo, ahaka dai wani wahalallan bacci ya d'auke ta". B'angaran Habib ko koda ya kwanta tunane-tunane ya hana shi bacci, dan sosai abin da ya faru ya d'aurai mai kai, yana mamakin wanda ya aiko atafi da Hassana, dan daga ganin abin sasu akayi, ahaka dai bacci ya kwashe Habib ". Washe gari daga Habib har Hassana makara su kai, Habib bayan ya gama shirinsa har zai tafi aiki, sai kuma ya yi wani tunani, fasa tafita ya yi, ya yi nocking d'in k'ofar Hassana". Hassana ko tunda ta samu ta yi sallah ta koma ta kwanta, dan kanta ciwo ya ke mata sosai, bugun da akema k'ofar ta ne ya tadata, tana mai dafe da kai ta zo ta bud'e k'ofar. Hassana cikin sanyin ta gaida Habib ganin shi tsaye". Habib bai amsa gaisuwar Hassana ba, sai cewa ya yi, "Karki sake kice zaki kira Hajiya ki fad'a mata abinda ya faru, sannan kuma dama dan Hajiya na nan ne na dakatar da ke zuwa aiki, dan haka ki koma aiki yau". Hassana da sauri ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib banda lafiya, dan Allah sai gobe". Habib tafiyar shi ya yi yabar Hassana nan tsaye ya ce, "kin dai ji abinda nace miki, ki zo aiki yau". Habib na fad'in haka ya bar Hassana nan tsaye shi kuma ya yi tafiyar shi". Hassana ko tsayawa ta yi tana tunanin ta inda zata fara shiri dan ko a yanzu ta makara. Wanka Hassana ta shiga, tana fitowa ta shiga kitchen da sauri dan samarma kanta abinda zata ci. A falo Hassana ta ci karo da ledar kaya, tsayawa ta yi tana dubawa, atamfofi ne masu kyau sosai sun samu style masu kyau, sai dogayan ri guna na shadda guda hud'u dukan su duk gizina ne sai shampoo ,ka yan sosai suka burge Hassana, ko wanne da gyalan shi ahaka ta ka wo mata su. Hassana sosai ta ji dad'in ganin kayan. Cikin sauri Hassana ta had'a tea ta sha, sannan ta shiga wanka. Wata atamfa blue and brown color tasa, sai ta ya fa gyalan atamfar. Masha Allah sosai Hassana tai kyau. Tana fitowa ta samu Napep ta kaita har sanat yoghurt, lokacin 9:50Am. Ita da lokacin zuwanta ya ke 7:00Am". Hassana koda ta je bata iske wani aiki ba, dan duk wani gu da take sweeping and mopping ta je ta iske duk anyi, hakan yasa ta je wajan su Amina tana taya su nasu aikin". Amina kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana kina jin dad'in ki kinganki kuwa yadda ki kai kyau, sannan sai kinga dama kike zuwa aiki". Hassana Kallan Amina ta yi, ta ce, "Amina Wallahi ba laifina bane". "Tom kaifin waye? ". Cewar Amina". Hassana kallan Amina ta yi, ta ce, "Ke dai kawai awuce maganar". Dariya Amina ta yi, ta ce, "Anwuce".shiru Amina ta yi, sannan ta ce, "An d'auki wata aiki anan, ita ma dai daga ganinta irin supervisor ce, amma abinda ke ban mamaki tun ranar da ta fara zuwa aiki ta ke tambayarki, wai kinzo, kullum tazo sai ta tambaye ki". Hassana shiru ta yi, tana tunanin tom ita wayasanta, can dai tace, "Kila bani ta ke nufi ba". Zuwan Supervisor ne yasa Amina ta yi shiru ta ci gaba da aikinta. Supervisor ko tsaye ta yi tana kallan Hassana sannan ta ce, "Ke !, wannan dama shine aikinki? ". Hassana kallan Supervisor ta yi, ta ce, "A'a da yake banzo da wuri bane, lokacinda nazo kuma angama duk aikinda yake amazaunin nau". Billy sosai ranta ya b'ace da maganar Hassana, wato ita sai ta ga dama take zuwa aiki, sannan idan tazo sai aikin da taga gama ta ke yi". Billy kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ok, ki wanke duk wani toilet da ke wajannan". Hassana kallan Supervisor ta yi, ta ce, "kiban wani abun, amma bazan iya wankin toilet ba, saboda inada kyankyami ". Wani uban ashara Billy ta yi, sannan ta bar gun, direct Office d'in Maganar Billy ta je, tana zuwa ta kalli manager ta ce, "Manager ba fa zai yuwu ba, yarinyar nan sai ta ga dama take zuwa aiki, sannan idan tazo sai taga dama take aiki, aikinma in za tai sai ta zab'a, dan haka Wallahi yau dole ta yi abinda nasa ta". Manager kallan Billy ya yi, ya ce, "Karki damu bari in mata magana da kaina zata yi". Manager da kanshi yasa mu Hassana ya yi mata magana akan ta wanke toilet d'in da Billy ta sata. Hassana, "tom"tace ma manager saboda bata iya yi mai musu, haka Hassana ta wanke duka toilet d'in gun. Sosai ta gaji ga kanta da ke mata ciwo". Yau Farida bata zo Sanat yughurt ba, koda su Habu suka jema Farida da labarin masu samu d'akko Hassana ba saboda harin da aka kawo musu, dan haka sai dai ta yi hak'uri, idan su kai aiki basu yi nasara ba basa kuma k'ara jarabawa, saboda gudin matsala". Habib ko bayan ya tashi aiki police station ya biya akan maganar b'arin da suka shigar mai jiya, tare da amsar police biyu ya kai su gidan shi dan gadi, gudun matsala". Bilya ne yaje ya d'akko Hassana bayan ya kai Habib. Hassana zaune ta iske Habib a falon yana cin abinci, azuciyarta ta ce daga gani dai nasiye ne". Hassana tsayawa ta yi kamar ta wuce, sai kuma ta ga kamar hakan bai da ce ba, ta ce, "Barka da dawowa Oga Habib ". Habib d'ago kai ya yi kawai ya kalli Hassana ya koma yaci gaba da cin abincin shi". Hassana kuma aje gyalanta ta yi ta shiga kitchen ta dafa indomie ta fito, har yanzu Habib na nan zaune, ya dai gama cin abincin. Hassana nesa sosai da Habib ta zauna. Tana cin indomie ta, tana satar kallan Habib da hankalinshi gaba d'aya ya ke akan waya. Can dai Habib ya tashi ya nufi side d'in shi. Hassana shiru ta yi tana tunanin yadda za ta iya kwana ita kad'ai, dan gani take daga ta kwanta b'arayin zasu k'ara zuwa. Sai da bacci ya fara kama Hassana , sannan ta daure ta nufi bedroom d'in ta ta kwanta. Haka Hassana ta samu bacci ya d'auketa tana cikin masifar tsoro. Can cikin dare Hassana taji k'arar bindiga cikin tashin hankali ta diru daga gadon ta fita d'akin da gudu, tana zuwa Allah ya bata sa'a k'ofar Habib a bud'e ta ke bai kulle ba. Hassana cikin tsoro ta haukan gadon Habib ta kwanta bayan shi". Habib sai baccin shi ya ke kwata-kwata baiji shigowar Hassana ba". Hassana ko ta dad'e cikin tsoro sai ta kai hannu zata tada Habib ta ce mai b'arayi sun dawo, sai ta tuna daga ta tada shi zai koreta d'akinta, hakan yasa Hassana ta bar Habib bata tada shi ba". Habib ko bashi ya farka ba, sai asuba. Jin d'imin mutum bayanshi yasa ya juya. Habib da mamaki ya ke kallan Hassana dake baccinta abinta abayan shi, tunani ya farayi tom yaushema ta shigo d'akin, ya akai tazo bai ji zuwanta ba. Habib sauka ya yi daga gadon ya nufi toilet ya yi alwallah yazo ya tada sallah. Habib har ya idar da Sallah yana zaune kan dadduma Hassana bata tashi ba. Habib ta tashi ya yi cikin fad'a-fad'a ya ce, "Ke ". Hassana da sauri ta tashi zaune tana sosa kai tana kallan Habib, ta ce, "Uhm Wallahi Oga Habib b'arayi ne suka k'ara dawowa". Habib kallan Hassana ya yi, ya girgiza kai kawai , sannan ya nuna ma Hassana hanyar fita da hannun shi". Hassana sakowa ta yi tafita. Habib kuma wanka ya shiga ya yi shirin aiki". Hassana ma b'angaran ta ta gama shirinta tsab, Compound d'in gidan taje, dan tana son ganin Bilya. Aiko zaune Hassana ta iske shi cikin mota, yana jiran Habib". Hassana lek'awa ta yi da kai ta ce, "Oga Bilya dan Allah ina son magana da kai". Bilya fitowa ya yi daga motar, ya ce, "Inajinki". "Oga Bilya dan Allah so nake kaima manager magana aban kud'in aikina, tunda na fara zuwa ba'a tab'a biyana ba, kuma yanzu amfani nake so inyi da kud'in ". Cewar Hassana ". "Shikenan badamuwa zanma manager magana, zan amsa in baki". Habib tun daga nesa ya ke kallan Hassana da Bilya". Bilya kuma yana ganin Habib ya ce ma Hassana, "shikenan sai kin zo ga Oga Habib nan ya fito zamu wuce". Bilya bayan ya kai Habib Office d'in manager ya shiga, ya yi mai maganar kud'in Hassana. Manager batare da gaddama ba ya d'akko kud'in wata hud'u yaba Bilya ya ce, gashi ka bata". Hassana yau da wuri tai k'okarin zuwa aiki, tana sauka Napep Farida ma na sauka. Farida cikin jin dad'i tace shegiya ashe kin fara zuwa, ta yi maganar a zuciyarta". Hassana da mamaki ta kalli Farida,sai ta d'auke kanta tashi ge ciki abinta.Farida ko da mamaki ta bi Hassana da kallo wata bazata gaida ni ba, zaki ci ubanki a gunnan yau". Hassana na zuwa ta sweeping and mopping na gun baki d'aya kamar yadda ta saba. Tana gamawa ta samu gu tana hutawa, niyyarta inta gama hutawa ta je ta amshi kud'in da Bilya ya ce mata manager ya bata, ta yi amfanin da take son yi dasu". Hassana na zaune tana hutawa sai ga Bilya da Farida sun nufo inda ta ke, suna nufota suna tattaunawa". Billy kallan Hassana ta yi, ta ce, "me yasa nashiga toilet na gansu da datti baki wanke ba? ". Hassana batare da ta kalli Billy ba, ta ce, "Nayi aikin da yake ma zaunin nau, amma wankin toilet bashi cikin aikina". Farida ce ta amshe zancan da cewa, "Ke 'yar matsiyata zaki je ki wanke ne koko sai jikinki ya gaya miki? ". Hassana da mamaki ta furta, "duka kuma". "Eh ko bazaki bugu bane? ". Cewar Farida". Dariya Hassana ta yi, sannan ta ce, "ko shi mai Sanat yughurt, wanda kuke aiki ak'ark'ashin nafi k'arfin duka agunsa, bare ku da kuke a k'ark'ashin shi... ". Marinda Farida tai ma Hassana ne yasa tai shiru". Hannu Hassana ta d'aga da niyyar ramawa Billy ta rik'e hannun. Haka Farida da Billy suka taru sai bugun Hassana suke. Har hankalin staff ya kai kansu, ga manager baya nan. Da gudu d'aya daga cikin ma'aikatan ya ruga Office d'in Habib ya sanar da shi, ana fad'a". Habib da dama tun d'azu yake jin hayaniya, tashi ya yi dan yasan manager baya nan, ya nufi inda ake fad'an". Hassana kwance ak'asa da Billy da Farida sun taru sai bugun ta soke". Habib da bai san wama ake bugu ba,tsawa ya yi ma su Farida yana cewa, "Baku da hankali ne". Da sauri dukansu suka dawo hayyacinsu". Hassana ko da ta bugu sosai, tana jin muryar Habib da sauri ta tashi tana layi ta rik'e Habib tana kuka". Habib ko da mamaki ya ke kallan Billy da Farida,Habib ya dad'e tsaye yana masu wani irin kallo sannan ya ja hannun Hassana ya nu fi Office d'in shi da ita". Duka ma aikan gun hankalinsu ya koma kan Habib, dan banda Farida da Billy babu wanda yasan akwai aure atsakanin Hassana da Habib ". Habib ko yana rik'e da hanun Hassana suka shiga Office d'in shi..... ✍️ Idan kintaranta daure ki Comment sister 🤝 Share Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Shafi na 66&67. https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ HABIB ko yana rik'e da hanun Hassana suka shiga Office d'in shi. Suna zuwa bazato ma tsammani Habib ya wanke Hassana da mari. Ji kake "Tassss!. Hassana k'ara ta fasa ta dafe gurin ta d'ago tana kallan Habib. Habib ko nuna Hassana ya yi da hannu ya ce, "Ke wace irin fitinayyiyar yarinya ce?, me ye had'inki da su?,tom Wallahi daga nan har kibar aiki anan idan har aka k'ara fad'a dake agunnan zakiga abinda zan miki! ". Hassana zaman 'yan bori ta yi agun tana, bubbuga k'afa tana kuka, mai had'e da magana, "Wayyo kunnena ka fasa min kunne, Wayyo kaina, wayyo ko ina ajikina, Mommy dan Allah ki dawo zasu kashe ni..... ". Wata razanannar tsawa Habib ya yi ma Hassana, ya tsaya yana kallanta da mamaki, yama rasa me zai ce mata". Hassana ko d'an rage sautin kukanta ta yi, sannan ta ce, "Ai baka san me sukai min ba, kuma ni ai ban musu ko mai ba, su suka fara tsokanata". Hassana cusa kanta ta yi tsakankanin cinyoyinta sai kuka ta ke". Habib manager ya kira awaya. Manager na d'auka ya ce, "Hello manager ka ki ramin Farida da Billy ". Habib na fad'in haka ya kashe wayar". Hassana ko k'ara rage sautin kukanta ta yi. Billy da Farida tare suka shigo Office d'in, bayan sun gama tsara yadda su mak'alama Hassana laifin". Habib ya dad'e yana kallansu, sannan cikin kausassar murya ya ce, "me ya had'aku da ita? ". Billy ce tai wuf ta ce, "Oga Habib sanin kanka ne, Hassana bata zuwa aiki sai taga dama, Yanzu haka satin da ya wuce gaba d'aya batazo aiki ba.... ". Hassana wuf tai ta ce, "Eh d'in ai da yake ba shi bane ya hanani zuwa". Wani mugun kallo Habib ya yi ma Hassana, amma bata yi shiru ba sai da ta idasa fad'in abinda ta ke fad'a". Billy kuma shiru ta yi, dan gabanta ya fad'i da jin abinda Hassana ta ce. Sannan dai ta ci gaba da cewa, "Oga Habib sannan bata zuwa aiki sai lokacin taga dama, haka ma close lokacinda ta ga dama take tashi, kuma idan tazo bata aiki, idan ma zata yi sai aikin da taga dama take yi, sannan tai ta tara staff's su yi ta fira, kuma wannan dokar Company ce, banda tara ma'aikata gu d'aya ana labarin duniya, duk wani Company yana yak'i da haka. Tom ni yau badani ake fad'an ba ma, da Farida su ke yi, shine nazo ina mata magana akan abinda ta ke bata kyautawa, saboda naga fad'an nasu tun daga farko, ita ce bata da gaskiya, amma daga magana ta dawo kaina tana zagina.. ". Hassana ita dai da mamaki ta ke kallan su. Habib kallan Farida ya yi, ya ce, "Farida me ya had'aki da ita? ". Farida cikin salon makirci itama, ta fara magana kamar haka, "Oga Habib tun lokacin da mu kai fad'an nan da Hassana , Hassana ke gaba dani, duk inda muka had'u sai harara tsakanina da ita,da maganganu marasa dad'i, tom hakan bai min dad'i, shine yau da nazo naji ta fara maganganun nata, nasa meta nace mata, Hassana ni dai bana jin dad'in wannan gabar ta mu dan Allah ki d'auka komai ya wuce mu dawo mu ci gaba da gaisawa kamar da, shi kenan fa daga wannan maganar , wai ko uwata bata isa ta yi fad'a da ita ba ta kuma shirya da ita bareni , wannan shine abinda ya zafafani na tanka mata Oga Habib.. ". Ai Farida bata gama aje zancan ta ba, Hassana ta amshe da cewa, "Oga Habib duk abinda suka fad'a Wallahi k'arya suke muna fu.... ". Habib tsawa ya yi ma Hassana akan tai shiru, amma tak'i taci gaba da maganar da take". Jawo ta Habib ya yi ta dawo gaban shi, ya ce, "Ci gaba da magana! ". Hassana shiru ta yi ta turo baki tana harararar su Farida". Habib ko babu alamun wasa ya kalli Billy ya ce, "Daga yau babu ruwanku da ita, aiki ne batazo ba, ko kuma k'in yi tayi, ke kome ma ta yi babu ruwanku da ita, ki zo ki fad'amin , ni zanyi maganinta". Habib mai da kallan shiga Hassana ya yi, ya ce, "Ke kuma aci gaba da saki abu kina k'inyi, Idan har kika sake aka kawo min k'ararki, zakiga abinda zan miki". Hassana turo baki ta yi, ta ce, "Tom ai dai ni shairi su kai min, Kuma Wallahi ni bazan wanke toilet ba". Habib ko takan Hassana bai biba, ya ce, "Duk abinda aka sata bata yiba azo a fad'a min, zaku iya tafiya". Farida da Billy fita sukai, ko wannan su da maganar da ya ke yi a azuciyar shi.Hassana ko ta dad'e a Office d'in, sannan ta d'auki maya finta ta fita. Habib ya bita da kallo dan shi yana jinjina rashin hankalinta, bai d'auketa mai hankali ba, shi yasa baya mai da kai a abubu nata da dama ". Farida ko tun zuwanta Sanat yughurt aiki, ta samu Billy ta ce, mata ita tazo nai man aikine dan ta ci Uban Hassana, nan dai ta fad'a mata k'arya da gaskiya akan abinda ya had'asu da Hassana, amma ta b'oye mata tana son Habib". Itama Billy b'angaranta k'arya da gaskiya ta fad'a ma Farida, akan Hassana ta rainata tana mata duk abinda ta ga dama, ita ma bata nuna ma Farida tana son Habib ba. Shine fa suka had'a hannu wajan yadda zasu yak'i Hassana, kuma duk abinda su kai mata Oga Habib yaga Laifin Hassana ne, wannan kenan". Bayan su Billy sun fito Office d'in Habib, Farida kallan Billy ta yi da damuwa, ta ce, "Supervisor ina fa ganin kamar Oga Habib ya fara son yarinyar nan, kalli yadda ta ke mai hauka, amma duk ya d'auka,kuma dubu kashaidin da ya yi mana wai babu ruwanmu da ita duk abinda za tai, ni fa hankalina ya fara tashi". "Bana tunanin yafara sonta, saboda da yafara sonta da ba zai yadda da aikin da ta ke yi ba, ai shima yasan mafi k'ask'ancin aiki ta ke yi, kawai dai shi baya son ana fad'a a nan ne". Cewar Billy". Hassana ko tana fita Office d'in Habib, ta nufi wajan Bilya, bayan sun gaisa ne, Hassana ta ce, "Oga Bilya kaban kud'in". Bilya kud'in da Manager ya bashi ya ba Hassana". Hassana direct gidan su Habib ta wuce. Tana zuwa side d'in worker's d'in ta nufa. Aiko tana zuwa ta iske Jimmai zaune ta gama aikinta". Jimmai da fara'arta ta tari Hassana ta ce, "Oyayyo amarya a gidan Oga Habib, kai amma amarcin ya amsheki, kinga ki yadda ki kai kyau". Hassana ta b'e baki ta yi, sannan ta ce, "Sister Jimmai nazo da kud'in muje inyi register, ga kud'in". Jimmai maya finta ta d'akko suka fita da Hassana". Suna tafiya suna hira, ananne Hassana taba Jimmai labarin yadda su Farida ke ta kura mata, da bugun da su kai mata. Jimmai shiru ta yi, sannan ta kalli Hassana ta ce, "Hassana kina da laifi sosai, duk abinda Farida da Billy ke miki, akan fa Oga Habib ne, tom ke me zai hana kena kiyi fiye da abinda su ke yi ganin kin samu guri azuciyar Oga Habib. sufa nan yak'in nai man soyayyarshi suke, tom sai ke kice bazaki iya ba, ke da komai zaki zaizo miki a sauk'i, tom bari kiji bawai tanadin makaman yak'i zaki ba da su Farida, ta nadin yak'in nai man soyayyar mijinki zakiyi, ki futa daga harkarsu, Idan zaki iya Idan sun miki ki banza da su. Wallahi Hassana ki farka kisan abinda kike, ki tattali mijinki, dan ba wai su Farida ka d'ai bane ke yak'in nai man soyayyar Oga Habib, kawai dai sune kika sani, dan haka tun kan guri ya k'ure miki ya hango wata, ki zamar mai baiwa, ki yi turi da duk wani muskilancin shi, ba wai ki kin mai magana ba ya yi banza da ke dan haka ke bazaki k'ara yi ba, Ina karma ki kuskura ki haka, shi dama mai naima ai hak'uri dole ne ya yi shi, Idan kika sa hak'uri da jura sai kiga tun baya tanka miki watarana ya tanka miki, sannan kina had'awa da addu'a saboda ita ce takofin mumini, kirik'a karanta mai izazaza k'afa d'ari tana ta siri sosai wajan jawo hankalin mutum akanka". Hassana kallan jimmai ta yi, ta ce, "Sister Jimmai na yarda da duk abinda kika ce, amma Oga Habib ya wuce tunaninki, amma zan jaraba duk abinda kika ce, nagode ". "Yauwa k'anwata". Cewar jimmai". Haka Jimmai ta raka Hassana tai register, inda su kai zata fara zuwa gobe ". Hassana daga nan bata koma Sanat yughurt ba, gida ta koma. Bayan ta huta, ta shi ta yi tashiga bedroom d'in Habib ta gyara mai komai, sannan ta shiga toilet d'in ta wanke mai". Bayan Hassana ta gama aikin komai ne, dama ta samo gyad'arta da shinkafar tuwo. Dan yau kunun gyad'a ta ke son yi ma Habib. Hassana sai da ta had'a koma na kunun, sannan ta bari, dan tafi son ta dama shi gaf da Habib d'in zai dawo. Kiran Sallar magriba da akayi Hassana ta je tai sallah, bayan ta idar ne tashiga wanka. Sosai Hassana ta shafe jikinta da oil oud aribian perfume. Sannan ta sa wasu riga da siket cikin wa inda Jimmai ta sai mata da bata saba. Sosai kayan suka amshi Hassana tai kyau na bugawa ajarida sister. Hassana sai da ta yi sallar issha'i sannan ta je ta had'a kunun tasa a flasks. Hassana kan caution d'in Falon ta kwanta tana jiran shigowar Habib amma shiru". Abu kamar wasa Habib har 10:00 Pm Habib bai dawo ba. Wani tunani ne yazo ma Hassana, ta ce, "ko dai tun d'azu ya dawo ina bedroom d'ina ko kuma ina kitchen". Wannan tunanin da Hassana ta yi yasa ta nufi bedroom d'in Habib". Habib na zaune bakin gado da laptop akan cinyar shi, Hassana ta turo k'ofar ta shigo ". Duk lokacinda Hassana zata keb'e da Habib ta kan manta shak'uwar da su kai ada baya cikin hayyacinsa, sai ta rik'a ganin kamar da. Hakan yasa Hassana take abubuwan ta kai tsaye gaban Habib". Hassana d'an d'aure fuska ta yi, ta ce, "Oga Habib dama kadawo?, amma tun d'azu ina falo ina jiran dawowarka, ashema kadawo". Habib d'ago kai kawai ya yi ya kalli Hassana. Hassana kuma zuwa ta yi ta zauna gefan Habib tana lek'a laptop d'in da ke kan cinyar shi, ta ce, "Oga Habib yau ko naima wani abu, kuma nasan zaima dad'i, dan ko Mommy ta ce in nayi yana mata dad'i ". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "In kawo ma kagani? ". Habib a halinda ya ke ciki yanzu Idan son samu ne baya son hayaniya, saboda lissafi yake, hakan yasa ya kalli Hassana ya ce, "Je ki ina abune". Hassana kamar za tai kuka ta ce, "Oga Habib kunu fa nada ma ma baka sone, kuma fa ni dan kai nadama, amma da bazan yi ba, dama lokacin da muna gida ne da nake damama nima na koyi sha, amma shine zanyi wahala indama kace sai anjima kana lissafi ne". Habib kamar yace wayyo da magan-ganun Hassana dan ko yanzu dauriya kawai ya ke yi, amma surutunta yafara b'atar da shi. Habib aje laptop d'in ya yi ya tashi, ya kamo hannun Hassana, ya ce, "wai ke baki da hankali ne bikiji ba nace miki, Ina lissafi ne". Habib tura Hassana ya yi waje, ya ce, "innagama kin kawo min". Hassana fita ta yi kamar za tai ihu, ta ce, "Ni Wallahi ba zan iya ba Sister Jimmai ni bazan iya ba, kina gani ma yanzu turoni waje ya yi wai na Isheshi". Hassana koma wa ta yi kan caution d'in ta kwanta". Hassana bacci ne ya kwasheta, ba ita ta farka ba, sai 11:30 Pm. Tana tashi kamar wata zautata ta d'auki flasks d'in kunun ta nufi bedroom d'in Habib da shi". Habib ko har ya gama abinda ya ke yi ya kwanta, dan bacci ma har ya kwashe shi. Hassana ta turo k'ofar ta shigo, da d'an haskan da ke d'akin Hassana ke kallan Habib. Hassana aje cup d'in kunun ta yi taje ta hau kan gadon, tana bubbuga Habib ta ce, "Oga Habib kai fa kace in kawoma in nagama, amma shine kai bacci". Habib ko da yake yanada nau yin bacci in ya kwanta, kodan baya samun yin narana ne. Hakan yasa bai ji bugun da Hassana ta ke mai ba, duk da kad'an-kad'an ta ke bugun shi". Hassana ko dagewa ta yi, tana bubbuga Habib tana jan abun rufar shi. Can bak'in cikin hawalar dama kunun da tayi, gashi yanzu sai dai tai asara hakan yasa ta fara kuka, tana mai kuma bubbuga Habib". Habib da cikin bacci yaji kukan Mutum, kuma ana bubbuganshi. Tashi ya yi zaune, Habib da mamaki yake kallan Hassana, sannan ya ce, cikin irin muryar wanda ya farka daga bacci. "Lafiya, me yasa me ki? "."kunun da nace ma na damama na kawo ma". Cewar Hassana ". Habib ranshi ne ya b'ace, akan me zata tada shi yana bacci wai ta kawo mai kunu, gashi shi indai ya yi bacci aka tada shi da kyar yake samu wani baccin ya d'aukai. Hakan yasa Habib ya daka ma Hassana tsawa yana masifa, ya ce, "Wallahi ki gaggawar bari nan, dama akan kunu ne zaki tasheni, gashi nan har kin samin ciwan kai, bazan sa kunun ba, tashi kiban guri Kafin in daddakaki a nan gun!". Hassana da sauri hajjikanta na rawa ta tashi ta fita". Washe gari Hassana da wuri ta tashi taima kan ta kad'ai abin breakfast, sannan ta shiga wanka, dan 8:00Am ne time d'in zuwanta, su tashi 2:00 pm. Hakan yasa Hassana nagama shiryawa cikin doguwar rigar shaddar da Hajiya Turai ta kawo mata, ta d'auki jakarta ta tafi". Can Sanat yughurt ko su Billy na ta zuba idon ganin Hassana, amma shiru. Hassana ba ita taje sanat ba sai da ta tashi daga caktrea school, sannan". Su Billy tsab sun lura da lokacinda Hassana tazo Sanat. Hassana na zuwa side d'in su Amina taje tana taya su aikinsu, a haka aka tashi Billy bata tankama Hassana ba, dan acewarta barta sai ta aikata sau uku saboda k'ar Habib ya yi masu kallan masu yawan kan k'ara". K'arfe biyar nayi Hassana ta fito ta tafi gida, dan so take ta je tai aiki, dan ba tai akin komai ba ta fito, kuma tana son ta damama Habib kunu, inda Jimmai ta ce ta yi hak'uri katta gaji". Billy da Farida na lure da Hassana lokacinda ta tafi. Hassana ko na zuwa gida ta shiga bedroom d'in Habib ta gyara ta wanke mai toilet, sanna ta gyara falon ma, ta d'ora mai kunun gyad'an. Hassana na gamawa ta shiga wanka, tai adonta mai kyau. Tana nan zaune a falo Habib ya shigo yau da wuri ya dawo. Hassana cikin nuna kula ta ce, "Barka da dawowa Oga Habib ". "Yauwa". Habib ya ce, ya shige ciki". Hassana sai da ta bari Habib ya isa ace Habib ya gama duk abinda ya ke sannan ta d'auki flasks d'in kunun ta shiga da shi bedroom d'in shi. Lokacin Habib ya gama shiryawa ya na zone yana tunanin kiran Bilya ya kawo mai wani abun dan yunwa yaje ji. Hassana da sallama tashi ga bedroom d'in, zaunawa ta yi kan lover chair d'in bedroom d'in, sannan ta bud'e flasks d'in ta zuba kunun ta mik'ama Habib, ta ce, "Oga Habib dan Allah gashi kasha kaga jiyama sai dai nai wahala baka shaba, kuma yafi wanda Farida ke kawo ma dad'i duk da shima nike yi". Habib amsar kunun ya yi daga hannun Hassana. Ya rik'e yana kallan Hassana. Hassana ma kallan shi ta yi, ta ce, "Tom Oga Habib kasha". "Infa nasha naji badad'i?". Cewar Habib". "Uhm ai Wallahi nasan ma zai ma dad'i, dan ko Mommy da ta tab'a zuwa lokacin nayi mana tasha, tace nafi su Maimuna iyawa". Cewar Hassana". Habib kad'an ya kurb'i kunun, dan jin tasting d'in shi ". Hassana ko ganin Habib ya d'and'ana kunun, kallan shi ta yi, ta ce, "Tom ya, ya kaji kunun, baka tab'a shan irin shi ba ko? ". Habib tab'e baki ya yi, ya ce, "Bai min dad'i ba, kawai dai zan shane saboda kar azubar ayi almubazzaranci". Hassana shiru ta yi, dan tana tunanin Habib da gaske ya ke , yadda yi Maganar, hakan yasa ta kallai ta ce, "Dan Allah dagaske nai bai ma dad'i ba". Habib kai ya d'aga ma Hassana".Hassana hunnu ta mik'ama Habib ta ce, "Ban kunu na inda bai ma dad'i ba". "Yess ba tasting kunun, kawai dai inasha ne sabo da kar ai albazaranci". Hassana mamar Habib ta yi dai-dai zai kai cup d'in kunun bakin shi ta yi, wuf zata amshe, by mistake kunun ya b'arema Habib ajiki". Hassana cikin damuwa da rud'ewa ganin yadda tai ma Habib wanka da kunun". Hassana b'alema Habib mab'alin rigar ta fara, tana cewa, "Ayyah yi hak'uri Oga Habib Allah bada sanina bane". Habib bige Hanun Hassana ya yi, ya ce, "Da Allah ni rabu dani, inda kin zubar da kunun ki tashi ki tafi". "Akwai fa saura, Allah bada sanina bane,". Habib hannun Hassana ya kama ya fitar da ita daga bedroom d'in, sannan ya rufe k'ofar shi.Cire kayan da Hassana ta b'ata mai ya yi, sannan ya shiga ya kuma wani wankan, ya dawo ya zuba kunun yasha. Sosai kunun ya yi ma Habib dad'i, dan ya yadda da Maganar Hassana da tace yafi wanda Farida ta ke sata tai mai dad'i. Sosai Habib yasha kunun Hassana ya kwanta, yana jinjina rawar kai irin na Hassana". Washe gari da wuri Hassana ta tashi tai abin breakfast da Habib, tana gama wa ta shiga wanka, tana cikin shiryawa taji alamun fitar Habib. Hassana da sauri taya fa mayafinta ta fita, dan Habib har ya fita daga falon. Hassana da d'an k'arfi ta kira Habib ta ce, "Oga Habib! ". Habib juyowa ya yi yana kallan Hassana. Hassana kuma da d'an gudu ta k'arasa inda Habib ya ke. Cikin nishin gudun da tayi, ta ce, "Oga Habib ga fa abin breakfast nayi da kai, kuma naga zaka tafi". Habib juyawa ya yi yaci gaba da tafiyar Shi, ya ce, "ni bana break fast da wuri". Hassana da sauri ta sha gaban Habib ta ce, "Uhm amma ai lokacin da na zauna part d'in ka dawuri nake mana, kuma kana sha, kuma kamanta jiya kace zaka shane saboda baka son albazaranci, tom Idan baka shafa sai dai in zubar, kuma kaga anyi albazzaranci inda ni bazan iya shanyewa ba". " ki aje anjima kisha , idan kika yadda kika zibar zaki ga abinda zan miki , waya ce ki yi dani bak'i tambayan ba? ". Habib yana tafiya yana fad'in haka". Bilya yana cikin mota cikin mamaki ya ke kallan Hassana da Ogan nashi," dama sun fara magana haka? ". Bilya ya tambayi kanshi". Hassana ko tana mai bin Habib ta ce, "Wallahi Oga Habib ni bana iya shanye shi ni kad'ai". Habib banza ya yi da Hassana ya shiga cikin motar. Hassana kallan Bilya ta yi, ta ce, "Oga Bilya ga kunu, in kawo ma". Aiko Bilya cikin jin dad'i dan yana son kunun ya ce, "Eh zan sha". Hassana da sauri ta shiga ta kawo ma Bilya kunun, sannan ya ja motar su ka tafi". Yau kwanan Hassana Uku kenan da fara zuwa koyan girki da take yi. Yau Hassana ta riga Habib fita dan yana Falo tazo ta gaida shi ta wuce da sauri". Yaune kuma Billy ta yi shirin kai k'arar Hassana gurin Habib na rashin aikin da bata zuwa sai 2:00pm, wata rana ma har 3 tana kaiwa sannan tazo". Habib na zaune a Office d'in shi. Billy ta yi mai nocking. Habib izinin shiga ya bata, ta shiga. Billy cikin salon muna firci ta gaida Habib, sannan ta ci gaba da cewa, "Oga Habib dama kan Hassana ne, tun rannan da kaimana shara'a da Hassana, tom tun ranar Hassana bata zuwa aiki sai k'arfe uku ko hud'u, sannan Idan tazo bata aikin komai, Idan tazoma bai fi tai awa d'aya ba ta tafi, yanzu haka maganar da nake ma bata zo aiki ba yau". Habib da mamaki ya kalli Billy dan yau ai Hassana ma ta riga shi fita, hakan yasa ya ce, "Ki duba tana nan tazo". Billy cikin tabbatar ma Habib ta ce, "Wallahi Oga Habib bata zo ba, kullum haka ta ke yi". Habib kallan Billy ya yi, ya ce, "Ok, zaki iya tafiya". Habib Bilya ya kira awaya ya ce, "Hello Bilya kaje gida ka duba min wannan yarinyar nan". Bilya zuwa ya yi ya duba ba Hassana gidan yaga Hassana bata nan. Kiran Habib ya yi ya sanar da shi bata nan". Habib kiran Billy ya yi yace, "dan tazo kikiramin ita". Hassana ko yau basu suka tashi ba, sai 4:15pm haka yasa tana tashi ta nufi gida bata biyo Company ba". Habib anayin Ishsha'i ya koma gida, zaune ya iske Hassana a falo. Habib tsaye ya yi yana kallan Hassana sannan ya ce, "Me yasa yau biki je aiki ba? ".kaina ke ciwo". Hassana taba Habib amsa saboda bata yi tunanin ya aiko gidan an duba bata nan ba". Habib sake mai-mai ta ma Hassana tamyar ya yi, me yasa yau biki je aiki ba.......... ✍️ Idan kin karanta daure ki comment sister 🤝. Comment & Share Please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/postsBah/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Ina ma dukkan d'aukakin musulmi barka da juma'@t mubarak, Allah ka had'amu da alkairin da ke cikin wannan rana mai albarka. Ina godiya da addu'a inku gareni, Alhamdulillah Allah yaban lafiya. Nagode 🤝. Shafi na 68&69. Habib sake mai-mai ta ma Hassana tambayar ya yi, "me yasa yau biki je aiki ba? ". "Oga Habib kaina ke ciwo shiyasa banje ba". Cewar Hassana. Habib shiru ya yi yana kallan Hassana, sannan ya ce, "Daga yau Idan kinje aiki kira shiga Office d'ina ina ganin zuwanki, sannan Idan zaki close shima ina son sani". Habib na fad'in haka ya bar Hassana gurin tsaye, ya shige side d'in shi". Hassana Shiru ta yi, tana tunanin wannan duk yana cikin shairin su Billy.Hassana kunin da ta dama ma Habib ta d'auka ta shiga side d'in shi da kunun. Hassana gefan Habib ta zauna, ganin bai d'ago kai ya kalleta ba, ta ce, "Oga Habib ga kunun ka? ". Habib ba tare da ya kalli Hassana ba, ya ce, "Ok, aje anan". Hassana ganin yau Habib ya koma asalin Habib d'in da da ta sani, yasa ta aje inda ya nuna mata, ta tashi ta fita". Washe gari Hassana da wuri ta tashi tai abinda za tai tai shirin ta fiya Sanat yughurt. Bayan ta gama shirinta na tafiya zama ta yi, tana jiran Habib ya rigata ta fiya sannan ta tafi daga baya. Hassana na nan zaune Habib ya fito cikin shirinsa. Hassana ta shi ta yi tana gaida Habib. Babu yabo ba fallasa haka Habib ya amsa ma Hassana ". Habib na tafiya, bai fi da minti goma ba Hassana ma ta tashi ta tafi". Hassana na zuwa Sanat yughurt, Office d'in Habib ta shiga kamar yadda ya umarce ta akan in tazo ta fara shiga Office d'in shi sannan". Habib na zaune da laptop agaban shi, Hassana ta yi nocking. Izinin shiga Habib ya bata. Hassana shiga ta yi, sannan ta kuma gaida Habib ta ce, "Oga Habib gani nazo". "Ok, in zaki close ma ki shigo".Habib ya ce ma Hassana.Hassana kum fita ta yi, dan yau taji haushin rashin zuwa caktrea school d'in ta da ba tai ba. Hakan yasa ta ce kuma aikin bata yi". Hassana side d'in su Amina ta shiga, tana taya su hira, dan aikin ma da da take kamamusu yau ta yi alk'awarin ba za tai ba". Billy koda tazo gun ta iske Hassana, kallanta ta yi, ta ce, "Ke nan ne gurin aikinki?, ki tashi kije ki wanke toilet d'in gunnan, dan an sanar da ni yau babu inda kika share ko kika goge, ki tashi ki yi ba zai yuwu ba, ana aiki kizo ki hanasu aiki da surutu kuma ke biki naki aikin ba". Hassana kamar karta tankama Hassana, sannan ta ce mata, "Supervisor banda lafiya ne, yau bazan iya aiki ba". "Wallahi ko mutuwa zaki yau sai kin yi aiki". Billy na fad'in haka, ta nufi Office d'in Habib". Habib kallan Billy ya yi, yana mai tambayarta "lafiya?". "Ogq Habib dama akan dai Hassana ne, Wallahi har na gaji da kawo report akanta, ni yanzu rashin aikinta ma baya damuna, amma yanzu tana can ta had'a staffs' sai surutu su ke, nai mata magana. Amma ko kallo na ba tai ba, shine nazo na fad'ama ko kai zata ji taka". Habib kallan Billy ya yi, ya ce"kije zanzo in sa meta". Billy fita ta yi tana mai jin dad'i Habib zai tozarta Hassana yau agaban kowa, dan yanzu abubuwan da ta ke yasa wasu sun fara zargin ita wata ce agun , tunanin Billy kenan". Habib ya tashi kenan don zuwa gun Hassana ya ci mutuncinta kamar yadda Billy ta ke tunanin, ringing d'in wayar shi, yasa ya zauna. Habib da fara'arshi ya yi pic d'in call d'in, saboda sunan Faruq da ya gani". Daga can b'angaran mai kiran, ya ce, "Hello Habib, gumu nan yanzu haka muna daf da shigowa Abuja, nida Usman, da Jameel". Daga b'angaran Habib ya ce, "Wannan tafiyar lafiya kuwa? ". Wata uwar dariya Faruq ya yi, sannan ya ce, "Habib zumud'i yasa dole in fad'ima, da dai naso mu mamaye ka ne, Munzo ganin amarya ne, Mommy ta fad'a min ka yi aure, Wallahi Habib na k'osa inzo inga Amarya". Faruq ya fad'i maganar yana tun tsirewa da dariya". Habib cikin d'aurewa da fad'uwar gaba, ya ce, "Eh ina fatan ai Mommy'n ta fad'a muku yadda abin ya faru, kai ka sani nafi k'arfin auran yarinyar da ta had'a ni da ita, dan haka bana fargabar komai, kun dad'e bikuzo kun ganta d'in ba, baza b'ina bace bare ku kushe zab'ina, ammma Faruq Wallahi duk lokacin da nai aure bana shayin kaga zab'ina, kai dai kasan ni kasan waye ni, k'ananun Baby's din da kuke kulawa, kai kasan basu isan kallo ba, wallahi, dan haka baka da bakin magana akai na, sai ka bari sai na yi zab'ina ba wai zab'in Mommy ba, auran da bansan anyi shi ba". Faruq dariya sosai ya k'ara yi, sannan ya ce, "Kai guy baka da bakin magana, kai dai gamu nan zuwa muga amarya, kuma yunwa muke ji, ai mana girki, bama son na siye na amarya muke so". Faruq na fad'in haka ya kashe wayar shi". Habib ko zufa keto mai ta farayi, duk sanyin Office d'in, saboda idan ba zai manta ba, Su Faruq du kansu babu wanda bai kawo mai budurwa ba kyawawan gaske 'yan boko, 'ya'yan manya, amma yana kushesu, yana ce masu duk basu yi ba, shi first class baby zai aura. Habib zama ya yi, sai ya tuno sun ce mai sun kusa shigowa Abuja, Habib tashi ya yi yafita, inda Billy ta ce mai Hassana na nan ya nufa". Habib daga nesa ya tsaya yana k'arema Hassana kallo, azuciyar shi, ya ce, "Wallahi nasan dole ma su rai nani, dan wannan tafi kwarewa a surutu da rashin kunya, kai ya Allah ka fidda ni kunya. Habib k'arasawa inda Hassana ta ke ya yi". Billy kuma sai dad'i ta ke ji, ganin Habib da ta yi ya nufi wajan Hassana, dan dama tafi so ya tozarta gaban worker's d'in". Habib kuma na zuwa, ya kamo hannun Hassana, ya ce, "zo". Habib matsawa ya yi d'an nesa da Staff's d'in.inda hankalin kowa, uwa uba su Billy ya koma kansu". Habib ATM card d'in shi ya ciro ya mik'a ma Hassana, ya ce, "ki koma gida yanzu, friend's d'ina ne zasu zo, ki biya gidanmu ki taho da maimuna ta kamamiki, da akwai wani shago da ake makeup, ki je ai miki, ki yi komai da sauri". Hassana tsayawa ta yi tana kallan Habib, sannan ta ce, "Oga Habib ni ba saina kira Maimuna ba, nima zan iya, sannan kuma ni zan ma kaina kwalliya bazani ko ina ba". Habib nuna Hassana da hannu ya yi, cikin fad'a-fad'a ya ce, " ki yi duk abinda nace, idan kika bari naji kunya..... ". Kad'a kai ka wai Habib ya yi, sannan ya ce, "bari in kira Bilya ya kai ki, idan kina buk'atar wani abun kuma ya siyo miki ". Hassana amsar ATM card d'in ta yi tana turo baki, dan ita bata son irin kalliyar nan". Habib kuma Bilya ya kira awaya ya ce, "Bilya kazo yanzu". Habib na nan tsaye da Hassana Bilya yazo. Habib kallan Bilya ya yi, ya ce, "Ka kaita gida, idan ta gama abinda ta ke ka kaita nan kusa da mu d'innan inda ake makeup ai mata". Bilya cikin girmamawa ya ce, "Tom Insha Allah Oga Habib ". Sannan Bilya ya tafi Hassana ta bi bayan shi. Billy ko da mamaki ta bi su da kallo, baka mar abinya yafi d'aure mata kai ba, ganin Habib ya ba Hassana ATM card d'in shi". Hassana ko a hanya ta sa Bilya ya tsaya ya cirar masu kud'i, sannan suka biya suka sai duk wani abu da suke buk'ata. Hassana na zuwa ta shiga kitchen ta fara girki, ta ce," coconut rice zan yi irin wadda mu kai practice jiya. Cikin k'ank'anin lokaci Hassana ta gama duk abinda ta ke yi, sannan ta had'a masu lemun kwakwa, masha Allah. Ta jera komai a derning space. Bayan Hassana ta gama ko mai ne, ta shiga wanka, ta sa doguwar rigar da Hajiya Turai tai mata ta shadda, sanna ta samu Bilya a waje, suka tafi wajan makeup d'in ". Bilya da kanshi ya ya yi magana da su akan ai mata mai kyau. Wayyo sister haka suka zauna suka cancara ma Hassana kwalliya. Wajan sa eyelashes ne aka samu matsala, dan Hassana cewa tai bata so, da kyar dai ta bari aka sa mata.sannan zuka amshi d'an kwalin suka d'aura mata". Wato had'uwa iya had'uwa Hassana ta had'u, dan shi kanshi Bilya da Hassana ta fito da kyar, ya samu ya kauda idon shi akanta, azuciyar shi kuma yana ganin sakarcin Habib, ya ce, "wai kawai kasa matarka tai ma abokanka kwalliya kawai dan kar a raina ka,Allah ya kyauta ".kiran Habib ne ya katsema Bilya zan can zucinsa". Bayan Bilya ya d'aga, Habib ya ce, "Bilya sun fa iso kun koma gida ne". "Eh gamu a mota zamu koma". Habib datse kiran ya yi, dai-dai nan kuma su Faruq suka shigo Sanat yughurt ". Habib da fara'a ya rirrin gume su, zai yi Office d'in shi da su, Faruq ya ce, "Kai Malam gidanka za ka kai mu". Habib murmushi ya yi, sannan yaja Office d'in ya rufe, dama tun Kafin su iso Habib yasa an kawo mai mota agida. Habib da kanshi ya tuk'a motar zuwa gidan shi". B'angaran Hassana ma kusan zuwan su kenan taji alamun hayanir zuwan abokan Habib d'in. Hassana bedroom d'in ta ta ruga. Su Faruq ko da fara'arsu suka shigo falon". Bayan sun zauna , Faruq ya kalli Habib ya ce, "Kasan nifa banda dauriya, ina amarya?, na zaci ita zata tarbemu, ko dai kasa ta gudune". Faruq ya fad'i maganar yana dariya. Dan yau ya shirya rama duk abinda Habib ke musu akan duk budurwar da suka kawo mai, yadda ya ke kyarar su, daga ya ce bata da kaza sai ya ce, bata iya kwalliya ba, abubuwa dai Kala-kala ". Habib tsaki ya yi, ya ce ma, "Faruq, tom bari kaji ko kad'an bana fargabar ku ganta, saboda ita d'in ba zab'ina bace kamar yadda na cema, zab'in Mommy ce, dan haka sai ku taya ni fad'ima Mommy ba ta yi ba, dan na riga ku fad'a, ya idasa maganar yana yin hanyar bedroom d'in Hassana". Hassana zaune kusa da mirro sai kallan kanta ta ke, dan in dai mudubin nan ba k'arya ya yi mata ba, ta yi ma kanta kyau sosai ". Ta mirro Hassana ta hango Habib, aiko da sauri ta sa hannu ta rufe fuskar. Habib ma da sauri ya idasa gunta ya sa hannu ya janye hannunta, ya ce, "Da Allah can zaki b'ata kwalliyar, ni cire hannun ki in gani ta yi kyau". Hassana cire hannunta ta yi ". Habib ya kai minti biyar yana kallan Hassana. Dan shi dai in dai ya lura da kyau, sai ya ga kamar kwalliyar ta yi. Hassana bud'e idon ta ta yi da ke arufe, bud'ewa ta yi tana kallan Habib ta ce, "Kwalliyar ta yi kyau? ". "Friend's d'ina zasu tantance hakan, bani ba".Habib ya ba Hassana amsa. Sannan ya kamo hannun Hassana ya ce, "Meje su ganki suna falo". Haka Hassana suka jera da Habib hannunsu cikin na juna, suka nufi falon. Faruq da sauran abokan tafiyar nasu, fira suke, amma suna ganin Hassana dukkansu bakinsu ya mutu, dan sosai kyanta ya tafi da imanin su. Jameel ne ya yi k'ok'arin sai ta nazuwar shi, ya ce, "Barka da fitowa Amrya". Sannan su Faruq ma suka dawo na tsuwar su". Faruq yana d'an soka kai ya ce, "Barka da fitowa amarya agi dan Habib, gaskiya kin ciri tuta, ace duk gudun shi sai da kika cin mai, jinjina Amarya". Hassana da ke zaune kusa da Habib murmushi ta yi, ta ce, "Barkanku da zuwa, da fatan kunzo lafiya? ". "Lafiya kalau amarya". Cewar Usman Kenan". Bayan sun gaggaisa ne, Hassana ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib ga abincin su a darnin area, ko akawo nan". "To fa Oga Habib, kunji wani love name". Cewar Faruq yana dariya". Habib ne ya amshe zan can Kafin su Jameel su tanka, ya ce, "Da Allah can kuzo muje kuci abinci, kun tsaya kuna gulma". Habib tasa su Faruq ya yi har derning space d'in, Hassana zuwa tai ta zizziba abincin a plate hud'u ta aje ma kowa a gaban shi, sannan ta aje jug d'in lemun kwakwa da tai masu, sannan tabar gun tana mai cewa, "aci lafiya". Tun kan su Faruq suci abincin k'amshin da ya ke yi kad'ai ya tabbatar masu abincin ya yi. Wayyo dad'i haka suka ci gaba da ci ba ma mai kowa magana. Faruq bayan ya gama cinye wanda Hassana ta sa mai, mik'ama Habib plate d'in shi ya yi, ya ce, "Ni dai idan akwai Habib k'aramin, Wallahi ka yi da ce, yarinyar ta yi ga shi ta iya girki, wato Habib naso ace yau in huce fushina akan abubun da kai mana da, amma matarka bata da abinda zan rama abinda kai min, tabbas Hajiya ta cikama burinka da kace sai First class baby zaka aura, wannan yarinyar ta kai, wai ya sunan ta ne? ". Habib yana mai jin dad'in kunyar da Hassana ta fidda shi, ya kalli Faruq ya ce, "Sunan budurwarka da ta rasu". "Kana nufin sunanta Hassana? ". Kai Habib ya jinjina ma Faruq". Tabbas ba a Hassanar banza, gaskiya ne dole ta zama kyakkyawa, dan kasan Allah ban tab'a ganin Hassana munmuna ba, duk inda zaka gansu zaka ga suna da diri, Allah sarki Allah ya gafarta ma Hassana". Cewar Faruq cikin damuwa. "Ameen ". Habib ya ce". Nan dai suka kama cin abincin su suna santi. Bayan sun gama cin abincin ne, Faruq ya kalli Habib ya ce, "Habib end of this month ne fa bikin Jameel, yanzu haka yana daga cikin abinda ya kawo mu, dan haka sai ka shirya muje gidansu Yarinyar tare, dan yau d'in nan zamu juya". Habib tashi ya yi, ya ce, "Tom ku tashi muje ". "Ok, kira Hassana sai muyi sallama". Cewar Faruq ". Habib bedroom d'in Hassana ya shiga ya kirata. Hassana zuwa tai ta ce, "Ba dai har zai ku wuce ba? ". "Wallahi amarya tafiya za muyi, zamu dawo babu dad'ewa auran Jameel". Kud'i masu yawa suka ajema Hassana a darning d'in, sannan suka tafi". Bayan sun tafi Hassana tazo ta gyara gurin. Habib ko bashi ya dawo ba sai gaf da magriba. Lokacin Hassana na kitchen tana ma Habib kunu. Habib na zuwa side d'in shi ya shige, yana zuwa ya yi wanka, ya tada sallar magariba. Habib sai da ya yi sallar issha'i sannan ya fito falon. Lokacin Hassana bata falon. Habib guri ya samu ya zauna, yana nan zaune Hassana ta fito zata nufi kitchen d'akkoma Habib kunun shi dama wajan shi zata". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Zo". Hassana ci gaba da tafiyarta ta yi tai kamar bata ji ba. Habib da d'an k'arfi ya ce, "Ke bada ke nake ba". Hassana zuyowa ta yi, ta ce, "Oga Habib nifa ba Sunana ke nan ba". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Zo ki zauna nan? ". Ya nuna ma Hassana kusa da shi". Hassana dawowa ta yi ta zauna inda Habib ya nuna mata, ta ce, "Oga Habib gani". Habib kallan Hassana ya yi ya koma hannun ta ya ce, " HaK'ik'a Kin fiddani kunyar Friend's d'ina naji dad'i sosai, dan haka ki zab'i duk abinda kike so, zan miki? ". Hassana bata san sanda ta tashi tsaye ba, ta ce, "Oga Habib kace duk abinda nake so? ". Kai Habib ya d'aga ma Hassana. Hassana zama ta yi tana kallan Habib, ta ce, Oga Habib so nake ka ban matsayin Supervisor..... .. ✍️ Idan kin karanta daure ki comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Shafi na 70&71. Kai Habib ya d'aga ma Hassana. Hasssana zama ta yi tana kallan Habib ta ce, Oga Habib so nake ka ban matsayin Supervisor ". Hassana ta fad'i maganar cikin k'osawa. Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "kamarya in baki matsayin Supervisor,bangane ba, yi min bayani? ". Hassana k'ara gyara zama ta yi, sannan ta ce, "Oga Habib nufina ka sauke Billy a matsayinta kaban". Kai Habib ya girgizama Hassana ya ce, "Haka ba zai yuwu ba, ki canza wani abun". "Tom kaban manager ". Cewar Hassana ". Habib dariya ya yi, jin abinda Hassana ta ce, wai ya bata manager. Hassana tsayawa ta yi, tana kallan Habib, dan bata tab'a ganin shi yana dariya ba. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib dama kana dariya? ". Hassana ta fad'i maganar tana turo baki dan ta san ita yake ma dariya dan ta ce, ya bata manager". Habib bayan yadan dara, kallan Hassana ya yi, ya ce, "kin ban dariya, me zaki da matsayin manager?". "Tom ai ni matsayin nake so, kuma ai kai kai min alk'awari kace duk abinda nake so, dan haka ni babu abinda nakeso wanda ya wuce, haka". Cewar Hassana tana turo d'an mitsitsin bakinta". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Kizab'i wani abun zan miki, amma banda wani abu a Sanat yughurt". "Ni dai acan nake so". Hassana ta fad'i maganar cikin shagwab'a". Habib tashi ya yi, ya ce, "Shikenan kin rasa, ni kam bazan miki wannan ba". Habib na fad'in haka ya tashi ya nufi bedroom d'in shi". Hassana da sauri ta tashi itama, tabi Habib tana rik'o hannun shi, ta ce, "Dan Allah Oga Habib kai fa kai min alk'awari!,". Hassana tana rik'e da hanun Habib tana mai magiya har suka shiga bedroom d'in shi. Habib zama ya yi, bakin gadon Shi, Hassana ma ta zauna tana mai k'ara cewa, "Oga Habib dan Allah kaban". Habib gaba d'aya baya jin dad'in yadda Hassana ke mai, shiya ya koma bedroom d'in shi, ya zaci bazata bishi ba. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Ki je ki kwanta, gobe sai muyi magana". "Wayyo Allah na Oga Habib, Allah ni bazan iya bacci ba, dan Allah kafad'amin yanzu". Habib kwanciya ya yi, ya rufe ido kamar mai bacci, dan bai san me kuma zai kuma cema Hassana ba". Hassana ma kwanciya ta yi, gefan Habib tana kallan shi, ta ce, "Oga Habib bacci kake? ". Habib juyawa ya yi batare da ya tankama Hassana ba, ya juya mata baya". Hassana ma juyawa ta yi side d'in da Habib ya juya, ta ce, "Oga Habib dan Allah". Hassana ta fad'i maganar tana mai kara shigema Habib". Habib bud'e ido ya yi yana kallan Hassana, ya ce, "Banda lafiya ki je ki kwanta gobe zamu yi magana". Habib ya fad'i maganar da sanyi sosai". "Ayyah sannu Oga Habib, Allah yabaka lafiya, tom kace Eh kawai dan Allah sai in tafi". Habib tashi zaune ya yi, ya na kallan Hassana , sannan ya ce, "Shikenan ki zama ma taimakiyar manager". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "da shida Supervisor wane ya fi? ". "Naki yafi". Habib ya ba Hassana amsa". Wayyo Hassana dad'i kasheta. Rungume Habib ta yi tana mai jin dad'in matsayin da Habib ya bata. Ta ce, "Wayyo Oga Habib Nagodeee". Hassana sakin Habib ta yi, ta tashi ta fita daga d'akin". Habib ko runtse ido ya yi, jin shi cikin wani bak'on yana yi. Yana mai jin sanyi cikin k'ofofin ji kinshi. Habib na nan yadda Hassana ta bar shi, Hassana ta shiga rik'e da jug d'in kunun Habib. Hassana cikin sanyi ganin Habib d'in kamar bai da lafiya da gaske kamar yadda ya ce, dan taga kamar yana ciccije baki, ta ce, "Oga Habib ga kunun ka, ka tashi kasha". Habib banza ya yi da Hassana sai da ta sake maimai tawa, sannan ya ce, "ki aje, kije ki kwanta idan na tashi zan sha". Hassana aje cup d'in kunin ta yi, sannan ta hau gadon, ta ce, "Oga Habib baka da lafiya ne? ". Habib cikin fad'a ya ce, "Ban sani ba, tun d'azu bikiji abinda nace bane, ki tashi kije ki kwanta! ". Hassana da sauri ta tashi tun Kafin ta idasa k'ure shi, dan tunnuni ma ta zaci zai mata haka". Habib ko bayan fitar Hassana tashi ya yi ya je ya watsa ruwa, ko zai ji shi ya dawo yadda ya ke da. Bayan ya fito kunun da Hassana ta kawo mai ya samu yasha sannan ya kwanta yana ta juyi shi ka d'ai, ahaka dai Allah ya tai ma kai bacci ya kwashe shi". Washe gari Hassana duk yadda taso ta tashi da wuri sai da ta makara, hakan yasa ta hak'ura da yin abin break fast, ta yi wankanta kawai tashirya. Hassana ta fito zata tafi Habib ma ya fito, Hassana cikin jin dad'in ganin Habib d'in ya ji sauk'i, ta gaida shi, tare da cewa, "Oga Habib kaji sauk'i kenan? ". Habib banza ya yi da Hassana, Hassana kuma kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib kura gemin hanya mana dan Allah ". "Akan me?, kije ki hau abinda kike hawa ya kai ki". "Ayyah Oga Habib kaga fa gidanmu d'aya dan Allah ". Habib banza ya yi da Hassana dama sunzo dai-dai motar shi, ya shige, Bilya ya ja zasu tafi, Habib ya ce yana zuwa ya yi mantuwa. Habib gida ya koma ya d'ako abinda ya manta. Sannan ya dawo suka tafi, tsaye suka iske Hassana tana jiran Napep. "Tsaya" Habib ya ce ma Bilya, bilya tsayawa ya yi,Habib kallan Bilya ya yi, ya ce, "Yi mata magana, tazo mu tafi". Bilya sauka ya yi ya nufi inda Hassana ta ke tsaye. Ita kuma Hassana dama koda tai ma Habib magana akan yarage mata hanya ta yi mai ne, saboda idan shine tasan za tafi zuwa da wuri, kuma yau tana son taje da wurine dan ta fara cika aikinta yau, tana kuma addu'ar Allah yasa ta riga Farida zuwa, wannan ne da lilin da yasa Hassana ta rok'i Habib ya rage mata hanya". Hassana na tsaye tana jan tsakin burinta ba zai cikaba, taji maganar Bilya, yana cewa, "Amaryar Ogan mu, ya ce, aimiki magana kizo mu tafi". Hassana hararar Bilya tafi sannan ta bishi suka tafi". Hassana kusa da Habib ta zauna, tana kallan shi, ganin ya d'auke idon shi ya yi kamar bai san da ita ba, yasa itama ta yi banza da shi. Ahaka suka isa babu wanda ya yi ma kowa magana. Hassana na sauka da sauri ta yi ciki dan tana so taje ta gani Ko su Billy sun rigata zuwa". Habib da mamaki ya bi Hassana da kallo yana mamakin saurin da take yi. Hassana ko na zuwa ta iske Billy ta zo, a wayance Hassana ta duba, ta ga Farida bata zo ba". Hassana tafi hours biyu da zuwa sannan Farida ta zo. Hassana da ke zaune tana jiran zuwan Farida, Farida na zuwa Hassana ta tashi ta isa gunta, wani kallo Hassana tai mata, sannan ta ce, "dama wannan lokacinne ake zuwa Aiki? , tom ko mai Sanat yughurt tun d'azu yazo Aiki, dan haka bazamu laminci haka ba, mun baki suspection na One week, dan haka zaki iya komawa gida, nan gaba idan kika k'ara aikata haka, korarki za muyi". Farida tsabar al'ajabi ne ya hanata magana, kallan Hassana kawai ta ke, tunani Farida ta fara, tom ko anba Hassana wani matsayine, wata zuciyar ta ce mata, tsabar rainaki ne da tayi, ta yi ma Supervisor mana. Farida a zuciyarta ta ce, "Tabbas yau zakici ubanki, yau zaki tabbatar ni ba sa'arki bace"., Farida juyawa ta yi zata shiga ciki, "Hassana ta ce, "Zaki iya jama wadda kika shiga gurinta itama". Farida bangaje Hassana ta yi tashige ciki". Farida Office d'in Supervisor ta shiga,Farida cikin damuwa ta ce, "Supervisor anba yarinyar nan wani matsayi ne? ".Supervisor kallan Farida ta yi, ta ce, "Wata yarinyar kuma? ". "Wata yarinya fa in ba Hassana ba! ". Cewar Farida ". "Ai idan za aba wani matsayi a Company nan sai anyi meeting, da an bata da ke ma kin sani ai, ". Cewar Billy. Shiru Farida ta yi, sannan ta ce, " ke dai kikira manager muji, dan baki ga yadda tai min magana ba, wai ta dakatar dani na sati d'aya, kuma idan na k'ara ai kata haka korata za tai". Billy cikin masifa, kamar ita Hassana ta ce ma haka, ta ce, "Bari mu kira Manager awaya, yau dama ya ce min ba zaizo da wuri ba, amma inda ko karya take Wallahi yau sai ta san ita k'aramar mara kunya ce". Billy kiran manager awaya ta yi, manager na d'agawa, bayan Billy ta gaida shi, ta ce, "Dama dearie naki raka ne in tambayeka, na ce anba Hassana matsayine agunnan, naga sai zuba iskancinta ta ke son rai". Manager ko tsabar dad'in dearie din da Billy ta kira shi da shi, ya sa ya ce, "Ki bar wannan yarinyar kawai zanyi maganinta, duk dan akwai auran M. D, kanta ne ta ke wannan iskancin, kuma shi bai d'auketa komai ba, danma shi mai biyayya ne ga Mahaifiyar shi, ki barni da ita zanyi maganinta". Billy cikin jin dad'i ta kashe kiran, dama a speaker ta sa wayar Farida ta ji duk abinda manager ya ce. Billy kallan Farida ta yi, ta ce, "Muje mu sami shegiyar, Kafin manager yazo muci uban 'yar iska, haba ni dama nasan jin kan Oga Habib ne zai kula wannan, sai dai biyayyar kamar yadda Manager ya ce". Hassana na zaune kan wata rubber chair, Farida da Billy suka zo suka sa meta, Farida kallan Hassana ta yi,ta nuna ta da hannu, ta ce, "Ke kikiyayi kanki dani, nifi k'arfinki nafi k'arfin iskan cinki, dan na girmi shekarunki, ni sa'arkice da zaki fad'amin abinda kika ce min d'azu? ". Hassana murmushi ta yi, ta ce, "Tom da ke da wadda ta rakoki duk na dakatar da ku sai nan da sati d'aya, dan itama ba Aiki ta ke ba, akwai wasa a aikin nata, sannan kuma dama na fad'a miki". Billy wani gigitattan mari ta wanka ma Hassana sannan, ta ce, "Shi wanda kike ta k'ama da auran shi, shi yaban matsayin da nake kai, shakarya mai tak'ama da abinda bata ita yake ba. Hassana tashi ta yi daga zau nan da take tana dafe da kuncinta, ta ce, "Masha Allah garani ko bata ni yake ba, da akwai abinda zanyi ta k'ama da shi, dan nasan hakan ma girma ne, akirani da matar Oga Habib, Allah sarki ku kuma dukkanku da kuke hauka akan shi, ko 'yan matan shi baza akiraku ba". Hassana na fad'in haka ta sa hannu ta wanke Billy da mari, ta rama marinda tai mata, sannan ta ce, "Ki ki ya yi kanki da harshanki Wallahi! ".Hassana bata rufe baki ba, Billy da Farida suka rufe ta da kuka kota ina, suna bugunta tana ramawa , amma ina hauswa sun ce sarkin yawa yafi sarkin k'arfi, hakan yasa su Billy suka ci nasarar Hassana". Kafin kace me staff's d'in gun an taru ana rabo, amma ina fad'a yak'i rabuwa, dan su Billy so suke su yi ma Hassana dukan da zata kiyaye su, ita ko Hassana duk irin buguwar da take gurin su Billy be sa ta hak'ura ta barsu ba, suna bugunta tana ramawa,daga k'arshe suka danneta yadda bata iya ramawa , suka ci gaba da bugunta kota ina. Bilya babu yadda bai yi ba ya raba fad'an amma ya kasa. Hakan yasa Bilya shiga Office d'in Habib ya sanar da shi abinda ke faruwa. Habib tare da Bilya suka zo gurin, Habib tsayawa ya yi bai cema ma su Billy komai ba, yana kallan su. Bilya ganin basu lura da Habib da ke tsaye ba, ya daka masu tsayawa ya ce, "Baku da hankali ne, Oga Habib ke muku magana! ". Farida da ke zaune kan Hassana tashi ta yi tana nishi, inda ita kuma Billy ta tashi ta zauna, ita ma tana nishi. Hassana da suba bari kwance tana nishin wahala ko kanta kasa d'agowa ta yi. Habib gurin Hassana ya je da ke kwance, tana nishin wahala, yana zuwa ya sa hannu ya juyo da i ta, jini sosai ke ziba abakin Hassana, dan bakinta su kaita bugu wai bakin rashin kunya". Habib d'aukar Hassana ya yi ya yi Office d'in shi da ita. Hassana ko na jin Habib ta sake langwab'ewa tai kamar irin wadde ke asume din nan. Habib kwantar da Hassana ya yi kan Table d'in Office d'in shi. Habib Faro ya d'ago yana tsiyayawa a hannun shi yana shafa ma Hassana a fuska. Habib girgiza Hassana ya fara, yana cewa, "Ke bud'e idonki mana". Habib yana yi yana d'an bubbuga fuskar Hassana, yana girgizata kamar d'an rud'e-rud'e ya ke girgizata". Hassana ko najin Habib tai banza da shi, Habib waya ya ciro ya yi kira. "Hello doctor kazo ka saman ina Company na, dan Allah kazo yanzu zaka duba wata yarinya ne". Hassana ko najin maganar likita, ta yi mik'a mai tattare da sakin kuka. Habib da sauri ya matsa kusa da Hassana yana mai d'ago ta". Hassana ko kukan gaske ta ke tana mai cewa, "Wayyo cikina, Wayyo kaina Oga Habib ". Habib shafa fuskar Hassana ya ke yi, ya na cewa, " yi hak'uri ga doctor nan zai zo ya duba ki, yanzu". "Ni bana son doctor ya zo, kace mishi karya zo". Cewar Hassana. Habib na nan tare da Hassana a wannan halin doctor ya zo,nan dai Habib ya labarta ma doctor abinda ke faruwa, magunguna ya rubata ma Hassana, sai allura guda d'aya". Hassana sosai ta ji dadi ganin likitan bai zo da magani ba. Bayan likitan ya tafi ne, Habib ya ce ma Hassana ta tashi ta je toilet ta wanke bakinta inda ke jini, Hassana cema Habib ta yi tana magana da kyar-dakyar, ita bazata iya zuwa ba. Habib hannu ya mik'a ma Hassana ya ce, "Zo in kaiki". Hassana k'iyawa ta yi tana mai ci gaba da kukanta, dan tana jin zafin bugun da su Billy su kai mata. Habib Bilya ya kira ya ba ya siyoma Hassana magungunan da aka rubuta mata". Hassana baccin wahala ne ya d'auke ta. Habib waya ya ciro ya kira manager, manager na d'agawa ya ce, "Hello manager duk inda kake kazo yanzu". Habib na fad'in haka ya kashe wayar". Bilya na kawo ma Hassana magungunan, Habib ya amsa ya ta data ya bata. Hassana nacikin shan maganinne Manager ya yi nocking. Kasan cewar Habib yasan manager ne yasa ya ce, "shigo". Manager cikin girmamawa ya gaida Habib. Habib amsawa ya yi sannan ya ce, "Manager dubu abinda Su supervisor Su kai ma yarinyar nan! ". Habib ya yi managar yana nuna ma manager Hassana". Manager cikin nuna damuwar shi, ya ce, "Wallahi M. D, ban sani ba, kasan yau dama bana zuwa da wuri, bari in kira Su ". Manager na fad'in haka ya fita Office d'in. Manager da Billy da Farida suka dawo Office d'in Oga Habib ". Manager kallan Billy ya yi, ya ce, "Me ya had'aku da ita? ". Farida ce, ta amshe zan can da cewa, "Manager muna kan aikin mu tazo ta saman wai ta bamu suspection na one-one week,saboda bama Aiki, wai da nace mata ta bari sai Munji gurin manager sannan shikenan sai mari". Hassana da ke zaune saurin amshe zan can ta yi da cewa, "Duk abinda kuka ga dama ku fad'a , kuma Wallahi kunji na rantse sai kunyi hutun sati d'aya a gida, kamar yadda nace muku". Hassana ta fad'i maganar tana murguda baki, ba su Billy kad'ai ba har manager kallan mamaki ya ke ma Hassana". Billy ce ta yi, k'arfin halin cewa, "Tom mu dai munsan aikinki a gunnan, shara ne da goge-goge, kuma duk wanda za aba matsayi a gunnan meeting ake yi abashi gaban kowa.. ". Ai Billy bata aje zan can ta ba, Hassana tai wuf ta ce, "Ai da yake ga Oga Habib d'in nan agaban shi nake magana, kuma shi yaban matsayin idan akwai wanda ya isa sai ya cire ni in gani, ni ce ma tai makiyar manager dan haka Billy ke da Farida abisa ga matsayina da mijina kuma shugabana a masana antar nan ya ban, na dakatar da ku Aiki na sati d'aya, kamar yadda nace miki Farida idan kika kuma zuwa irin yadda kika zo yau zamu koreki baki d'aya, ke kuma Billy bisa ga biyema Farida da kike yi, kema mun da katar da ke na sati d'aya, idan kuma kuka sake mai-maita irin haka korar ku zamuyi baki d'aya, zaku iya tafiya.............✍️ Ko ya hukuncin da Hassana ta yanke ya ke????? 🤭🤭🤭 Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Dan Allah ina barar addu'ar ku Mahaifina baida Lafiya 🙏. Shafi na 72&73. Hassana tai wuf ta ce, "Ai da yake ga Oga Habib d'in nan agaban shi nake managa, kuma shi ya ban matsayin, idan akwai wanda ya isa sai ya cire ni in gani, ni ce mataimakiyar manager , dan haka Billy da ke da Farida abisa ga matsayin da mijina kuma Shugabana a masana'antar nan ya ban, na dakatar da ku Aiki na sati d'aya. Kamar yadda nace miki Farida idan kika kuma zuwa irin yadda kika zo yau, zamu koreki baki d'aya. Ke kuma Billy bisa ga biyema Farida da kika yi, kema mun da katar da ke na sati d'aya, idan kuma kuka sake maimai ta irin haka korar ku za muyi baki d'aya, zaku iya tafiya! ". Duka gurin Shiru kowa ya yi da abinda ko ke fad'a azuciyar shi. Manager ne ya yi jarumtar kallan Habib ya ce, "M, D, dokar Company nan kowa ya san ba'a bada matsayi sai anyi meeting, sannan aba mutum gaban staff's dan su shaida, tom amma yanzu kaji abinda ita tace, tom ya maganar ta ke, Shin ka bata matsayin ne ko-ko ? ". Ai Kafin Habib ya yi magana, Hassana ti yi wuf ta ce, "Manager ina tunanin koda ace k'arya nake bazan yi ba agaban Oga Habib, dan haka ina mai tabbatar maka shi yaban matsayin nan jiya, dan haka ina ganin zasu iya tafiya". Manager da sosai ranshi ya b'ace ganin Habib ya yi mai Shiru, wannan k'aramar yarinyar na nai man rugaza soyayyar shi. Manager kallan Billy ya yi ya ce, "Supervisor ku saman a Office d'ina". Manager ya yi maganar daga gani kasan ranshi ya b'ace ya ke, da shirun da Habib ya yi mai" Manager na fita su Billy ma suka bi bayan shi suka nufi Office d'in shi kamar yadda ya ce. Bayan duk sun gama fita ne Habib ya kalli Hassana ranshi b'ace, ya ce, "Dama kin rok'an in baki matsayine dan ki kore su?". Hassana Shiru ta yi tana mai wasa da hannunta, dan yadda ta ga Habib ya d'aure tasan ba wasa. Habib ko cikin daka ma Hassana tsawa ya ce, "Nace dama kin rok'an in baki matsayi ne dan ki kore su!? ". Hassana girgiza kai ta yi, ta ce, "A'a Oga Habib, amma kamar yadda kaji na fad'a Allah haka ne, Supervisor bata aiki, ita kuma Farida..... ". Tsawar da Habib ya yi ma Hassana ce yasa ta yi shiru. Habib hanyar fiya ya nuna ma Hassana da hannun shi, ya ce, "Barnan! ". Hassana fita ta yi, tana fita ta ta yi tafiyar ta caktrea school d'in ta, tana mai addu'ar Allah yasa Habib k'arya da wo da su Farida, idan ma zai dawo dasu, tom Banda Farida, dan tafi jin zafin Farida". Manager ko a office d'in shi kallan su Billy ya yi, ya ce, "Supervisor ku yi hak'uri kuje gida koda na yau ne kad'ai, zan samu M, d, muyi magana zuwa anjima". Billy kallan manager ta yi, ta ce, "Idan har na bar gurinnan da sunan wai waccan bagidajiyar ce ta koran, tom kasani ba zan dawo ba". Manager cikin rashin sanin yadda zai yi ya ce, "Ki yi hak'uri Billy idan har kika tafi ni kuma nayi miki alk'awari zaji dawo da matsayinda take ta k'ama M, d ya bata, ki ce zaki koma kan matsayin". Billy cikin jin dad'i ta d'ago tana kallan manager, ta ce, "Manager ka tabbata? ". "Billy ba wai tabbata wa ba, alk'awari nayi miki, ke dai kin san yadda nake da M,D, ni ke tsara komai na gurin nan, dan haka nasan yadda zan mai , in ma ya bata mataimakiyar tawa da gaske , nasan yadda zanyi na dawo da shi kanki, amma yanzu ina so ki yi hak'uri ki je gida na yau kad'ai, zuwa gobe zaki dawo da matsayinta". Billy cikin jin dad'in kalaman manager, ta ce, "Godiya nake dearie". Sunan da ke kashe manager kenan, dan har Billy ta gano shi. Billy kallan Farida ta yi, ta ce, "Ya kika ji tsarin? ". Dariya Farida ta yi, ta ce, "reshe ya juye da mujiya". Dariya sosai sukai, sannan su kai ma manager sallama suka tafi ". Hassana k'arfe 3 na rana bayan sun tashi ta biya ta Sanat dan ganin, su Billy suna nan ko sun tafi. Hassana babu inda bata duba ba, amma bata gansu ba, hakan yasa ta samu k'awarta Amina, ta tambayeta ko supervisor na nan". Amina kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana Amma dai akwai releshanship tsakanin ki da Oga Habib ko? ". Hassana kai ta girgiza ta ce, "Babu komai tsakanin mu, malam ki ban amsa ta supervisor na nan ko ta tafi?, ita da Farida? ". "Eh naga tafiyar su, ita da Aunty Farida". Cewar Amina, tana kallan Hassana, dan bata yadda da cewar da Hassana ta yi ba babu dan gantakar komai tsakaninta da Habib". Hassana kallan Amina ta yi, ta ce, "Nina wuce, sai gobe insha Allah ". Habib yau da wuri ya koma gida. Hassana ko tana dawowa gida taima Habib kunun shi d'an kullun. Hassana ba ita ta shiga side d'in Habib ba sai da ta tabbatar ya gama komai sannan ta shiga, da kununta a hannu. Lokacin Habib yana waya da Hajiya Turai tana sanar dashi da wowarta gobe. Hassana guri ta samu ta zauna ta zauna tana jiran Habib ya gama wayar. Hajiya Turai ko, fad'a tai kema Habib ta ce yaba Hassana waya ya k'i tun da tazo basu yi waya ba, kuma tana kiran wayarta a kashe, dan haka yanzu ya bata. Habib mik'ama Hassana wayar ya yi. Hassana ko kallan Habib ta yi, tana tambayar shi waye Oga Habib? ". "Kisa a kunnanki kiji". Habib ya ba Hassana amsa". Hassana sosai tayi murna jin Muryar Hajiya Turai da ta yi. Bayan sun gaisa ne, Hajiya Turai ke tambayar Hassana lafiya tana kiran wayarta bata zuwa? ". "Mommy ruwa ta fad'a nayi-nayi tak'i kawowa". Hassana taba Hajiya Turai amsa ". "Zan kawo miki wata kinji daughter ". Hassana godiya ta yi ma Hajiya Turai dan tana son waya sosai. Bayan Hajiya Turai ta kashe ne, Hassana ta kalli Habib ta ce, "Ina wuni Oga Habib ". Habib banza ya yi da Hassana ya ci gaba da danna wayar shi. Hassana kuma cikin sanyin murya ganin Habib ya juya mata baya sosai, dan ko inda take yak'i kallo, kuma kwana biyu ba haka yake mata ba, hakan yasa Hassana cikin sanyin murya ta ce, "Oga Habib? ". Habib banza ya yi da Hassana. Hassana kuma bata gaji ba, ta kuma cewa, "Oga Habib! ". Nan ma Shiru ba amsa. Hassana kamar za tai kuka ta ce, "Oga Habib kaga ko hannuna inajin ya yi tsagewar k'ashi, bana iya d'aukar abu mai nauyi da shi, kuma bakaji ba yadda ya ke min zafi". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Muga hannun? ".Hassana da gaske hannun yana mata zafi amma ba sosai ba, mik'ama Habib hannun ta yi". Habib ko na amsar hannun ya rik'e ya na ja mata shi da k'arfi sosai, yana d'an bubbuga hannu". Hassana da k'arya take hanun ba wani ciwan kuzo kugani hannunke mata ba, ai take ta fara kuka, tana cewa, "Wayyo Oga Habib basshi haka dan Allah ". Habib ko be bari ba cigaba da latsama Hassana hannun ya yi, ita kuma tana ihu, tana rirrik'e hannun Habib. Habib da katawa ya yi yana kallan Hassana, ya ce, "Kin sha maganinki? ". Kai Hassana ta d'agama Habib."banyar da ba, je ki d'akko in gani? ". Cewar Habib". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Nafa manta shi a Office d'inka". Habib shiru ya yi ya ci gaba da danna wayar shi. Hassana kuma so take taima Habib maganar su Billy ta rasa yadda za tai, sai zuwa can ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib dan Allah karka dawo da su Billy sai nan da sati, kaga nima ai kaji dad'i kace na fidda kai kunya ko?, dan Allah Oga Habib kabar su sai sun yi sati, dan Allah, kaji Oga Habib ". Habib ko kamar jiran Hassana ya ke, ya aje wayar hannun shi, ya kalli Hassana ya ce, "Wallahi! Wallahi!! Ida har aka kuma fad'a dake a Sanat... ". Habib kai ya girgiza. "Tom aini bani ke to nan su ba, suke to nona. Hassana kunun da ta damama Habib ta mik'ama mai ta ce, "Oga Habib ga kunun ka karya huce". "Bazan shafa".Habib yaba Hassana amsa". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib me yasa?". Kin b'ata min rai yau". Hassana dama tun a sanat da ta kori su Billy taga irin kallan da Habib yake mata, ita yanzu tashin hankalinta d'aya kar ya ce zai cireta a matsayinta". Hassana kallan Habib ta yi, cikin sanyin murya, ta ce, "Oga Habib dan Allah ka yafe min, Allah bazan kuma ba, koma sun min zan rik'a banza da su, kuma dan Allah karka cireni a matsayina". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "da ga yau karki kuma fad'a da kowa!? ". Ya fad'i maganar cikin gargad'i ". "Allah bazan kuma ba". Cewar Hassana, sanna ta d'akko kunun ta ce, tom gashi kashi". Habib amsa ya yi, yana sha. da yake Habib kan 3 seater ya ke zaune,kafin Habib ya gama shan kunun Hassana da ke kusa da shi zaune, gafen kujerar ta kwanta, tana jiran Habib ya shanye kunun ta fita da Cup d'in. Sai dai Kafin Habib ya shanye kunun bacci ya kwashe Hassana. Habib ko yana gamawa ya ce, "Nagama tashi karki bacci, ki je ki kwanta". Abinda Habib ko bai sani ba, Hassana har ta yi baccinta". Habib jin Hassana ta yi mai shiru, kallanta ya yi, abin mamaki sai yaga ashema baccin ta ke. Habib bubbuga Hassana ya yi, ya ce, "Ke tashi kije ki kwanta zan rufe k'ofana". "Hmmmm". Hassana da ke jin Habib sama-sama ta amsa mai". Habib kuma buga k'afar Hassana ya yi. Hassana da bacci sosai ya kwasheta, ta ce, "Wayyo Allah na, tom ina zuwa". Habib tsaki ya yi ya tashi ya kashe wutar falon, ya nufi bedroom d'in shi, inda dama Hassana a falon shi ta sa mai". Cikin dare Hassana ta farka fitsari, ta ganta cikin duhu, ai take ta fara ihu, dan ta mamanta kwata -kwata ba a bedroom d'in ta ta ke ba. Hakan yasa Hassana ta fara ihu tana laliban makunni amma bata gani ba, ita atunaninta wani ne ya shiga ya kashe mata wuta in da dai ita bata kashe wuta a haske ta ke kwana. Ai Hassana dagewa tai tana ihu ". Habib ko da ya yi nisa sosai a bacci, cikin bacci ya ji yo ihun Hassana a falon shi, da sauri Habib ya tashi ya nufi falon, yana zuwa ya kunna wutar falon. Ko da ya kalli Hassana a furgice ya ga take. Tsaki Habib ya yi, ya ce, "Shikenan ke ako mai baki da hankali". Hassana baki ta turo tana cewa, "Oga Habib nifa na manta ba a bedroom d'ina nake ba, kuma ni bana kwana a duhu. Hassana da fitsari ya matseta, kallan Habib ta yi ta ce, "Oga Habib dan Allah inajin fitsari". "Kije naki toilet d'in ki yi mana". Cewar Habib". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib dan Allah fa, Wallahi ya matsan". Habib yana jan tsaki ya nuna ma Hassana bedroom d'in shi. Hassana da saurinta tashi ga. tana fitowa Ta nufi falon Habib. Habib koma ya koma bedroom d'in shi ya kwanta, Hassana zaune ta yi, a falon Habib, dan ita matsorarciya ce sosai. Sai da Hassana ta tabbatar ya isa ace Habib ya yi bacci sannan ta lallab'a ta shiga bedroom d'in shi ta kwanta can bayan shi, tana addu'ar karya tashi". Habib ko bashi ya farka ba, sai asuba, ananne yaga Hassana kwance a bayanshi sai baccinta ta ke abinta. Habib da mamaki ya ke kallanta tom yaushe ma ta shigo ta kwanta bai ji ba. toilet d'in shi ya shiga ya yi alwallah ya zo ya tada sallah. Habib har ya idar da Sallah Hassana bata tashi ba, hakan yasa Habib ya ja bargon da ta rufe da shi da k'arfi. Hassana da sauri ta tashi tana sosa kai, ta ce, "Oga Habib... ". Habib hannu ya d'ora lips d'in shi alamun Hassana ta yi shiru. Hassana shiru ta yi ta tashi ta fita". Habib wanka ya yi, ya yi shirinsa na tafiya aiki, ya tafi. Habib yana zuwa Office d'in shi babu dad'ewa, manager ya shigo. Bayan manager ya gaida Habib ne, manager ya ce, "M, d, dama game da tafiyar Supervisor gida ne, gaskiya m, d, gurin nan ace babu supervisor akwai fa damuwa, dan sanin kankane yarinyar na k'ok'ari sosai, tana kula da 'yan aiki sosai, ita Hassana ta dakatar da ita ne saboda bata yadda da rashin aikinta , ita sai take gani kamar ta tsaneta ne M, d, Supervisor tasan marketing sosai yarinyar, kuma tana da Experience sosai, Hassana ko bata san marketing ba, idan ake za'a d'auki matsayi irin wannan abata akwai matsala M, d, Dan haka ni idan har ka yarda inda na lura Hassana na son matsayi, tom sai a bata supervisor, ita kuma supervisor inda tafi ta Experience sai abata mataimakiyata. Yanzu idan har ka yarda anjima sai a had'a meeting aba kowa matsayinsa". Habib na yarda da duk wani tsarin da manager ya ke kawo, ba tun yau ba, hakan yasa ya ce, " Shikenan manager babu da damuwa, a had'a meeting d'in ". Hassana da Billy kusan tare suka isa Sanat, inda Hassana ke mamakin ya akai Billy ta dawo aiki. Farida kuma daga baya ta zo". Manager da kanshi ya bi kowana staff ya sanar da shi da akwai meeting k'arfe goma". K'arfe goma nayi aka had'u a a inda aka tana da dan meeting. Kowa yana gurin hadda Habib. Manager ne ya tashi ya fara bayani kamar haka. "Tom kamar dai yadda muka saba yi a masana antar nan, duk wanda za'aba wani matsayi sai anyi meeting yau ma haka za muyi. A bisaga jajircewar Supervisor kamar yadda koma wa sani, mun k'ara mata matsayi abisaga jajircewarta na aiki, an k'ara mata matsayi izuwa ga mataimakiyata, inda ita ma Hassana zamu bata matsayin da Supervisor ta bari. ko akwai Wanda ke da magana? ". Duka gurin suka amsa da babu, Hassana tashi ta yi, ta d'aga hannu , alamun tana da magana". Manager kallanta ya yi, ya ce, " muna sauraranki. Hassana cikin hikima ta fara magana kamar haka...... ........ ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Shafi na 74&74. Hassana cikin hikima ta fara magana kamar haka, " Idan har a atsarin masana'antar nan mutum biyu zasu iya hawa matsayi d'aya, tom matsayin da manager ya ba Supervisor ya yi, amma idan har a tsarin masana'antar nan ba zai yuwu Mutum biyu su hau matsayi d'aya ba, tom ka barta a matsayin ta na supervisor, dan wannan matsayin da ka bata matsayina ne da Oga Habib ya ban, kuma ina nan akan matsayina, amma idan har naji daga bakin Oga Habib cewar ya saukeni matsayin ya ba Supervisor, tom nabar ma ta, amma ina nan a matsina da Oga Habib ya ban, na mataimakiyar manager ". Hassana na gama fad'in haka ta zauna. Duka gurin kowa shiru ya yi, idan wasu suka fara zargin kodai akwai releshanship ne tsakanin Hassana da Habib. Nan dai kowa da tunanin da yake. Inda shi kuma manager jira yake yaji abinda Habib zai ce, amma Habib shiru bai tanka ba, daga k'arshe ma tashi ya yi ya fita gurin, nan dai d'aya bayan d'aya aka fara fita gunan, inda manager shima yana ganin Habib ya tashi, shima ya bar gun. Nan dai a haka aka gama fita. Hassana tashi ta yi zata fita, su Billy suka yi saurin shan gabanta, Billy sai da ta gama yi ma Hassana kallan sama da k'asa, sanna ta yi dariya ta ce, "Hassana kike kome?, ina mai miki albishir gobe zan fara aiki a matsayina na mataimakiyar manager, dan Allah idan kin isa ke mai matsayi ce a gurin Oga Habib kisa ya dakatar da ni. Duk wanda ke Company a yau ya saida ni Billy an k'ara min matsayi daga Supervisor izuwa ga taimakiyar manager, inda ke kuma aka baki nau matsayin, kina b'ab'atun Oga Habib ya baki matsayi, amma kuma ko manager bai shaida hakan ba, kinga mu bamu san da maganar ba. Daga k'arshe ina mai jan kunnanki karki sake shiga gurimina idan ba haka ba, zanyi amfani da matsayina in wahalar da ke a Company'nan! ". Billy na kaiwa nan taja hannun Farida suka tafi suka bar Hassana nan tsaye". Hassana taji zafin magan-ganun da Billy ta fad'a mata sosai, sai dai haka ne, ko manager bai shaida matsayin da Habib ya bata ba kamar yadda Billy ta ce, ita ko kowa ya shaida matsayinta. Hassana Office d'in Habib ta je, babu nai man izini ba komai, Hassana ta tura ta shiga . Dan Habib da ke zaune sai da ya d'ago kai yana kallanta". Hassana nesa da Habib ta zauna ta tura kanta tsakanin cinyoyinta, tana kuka, dan sosai taji zafin maganganun da Billy ta fad'a mata". Habib da mamaki ya ke kallan Hassana, banza ya yi da ita yaci gaba da abinda ya ke yi. Habib har ya gama abinda ya ke yi Hassana bata bar kukan da take ba, kuma ba wai ahankali ta ke kukan ba, ba kuma da k'arfi cancan ba. Habib da katawa ya yi da abinda ya ke yi, yana kallan Hassana, sannan ya ce, "Ke". Hassana ko dama ta tsani ke d'in da Habib ya ke ce mata, ci gaba da kukan ta ta yi, bata d'ago ba". Habib da d'an k'arfi ya kuma cewa, "Ke!, bakya jine ina kiranki". Still Hassana banza ta yi da Habib, kuma bata da kata daga kukan da take ba". Habib kallan Hassana ya yi, ganin yadda take kuka,amma sai magana ya ke mata ta yi mai shiru, ran shi ad'an b'ace ya ce, "Wai lafiya zaki shigo Office d'ina ki ta sani kina kuka, kuma ina miki magana kinyi banza dani, so kike kanki ya yi ciwo wannan kukan da kike yi". Hassana ko bata da kata da kukan da take ba, bare Habib yasa ran ta na ma sauraran shi, ci gaba da kukanta ta yi". Habib tashi ya yi, ya je ya samu Hassana inda ta ke. Habib zama ya yi kusa da Hassana sannan ya d'ago kanta da ta tusa tsakankanin cinyoyinta, ya ce, "Shikenan ya isa haka, ki yi shiru kanki kar ya yi ciwo, yanzu fad'a min me ya faru? ". Habib ya fad'i maganar yana bubbuga bayan Hassana". Hassana rage sautin kukanta ta yi, amma bawai ta yi shiru bane. Habib kallanta ya yi, ya ce, "Oh!, ki yi shiru ki fad'a min mana, kukan ya isa haka". Habib ya fad'i maganar yana jawo Hassana ajikin shi, alamun lallashi". Hassana share hawanta ta yi, ta d'ago kai tana kallan Habib, Habib ma ita yake, kallo, ya ce, "Tom ina jinki? ". Hassana cikin murya irin ta wanda ya yi kuka, ta ce, "Oga Habib ba kai bane kaban matsayi, kuma yanzu manager ya maida matsayin kan Supervisor, bacin tun farko abinda na naimi kaban ke nan, abinda tun farko sai da nace ma kaban matsayin Supervisor kak'i, kace sai dai kaban mataimakiyar manager, shine kuma yanzu manager zai ba Billy, kuma ai kai ne kai min alk'awari kuma kasa min rai". Hassana ta idasa maganar hawaye na zubo mata". Habib handkerchief d'in shi yasa ya goge ma Hassana hawayanta, sannan ya ce, "Tom shi Supervisor d'in da aka baki meye abun shi?, dama tun farko ai abinda kike so kenan, ki yi hak'uri kima wata rana zaki zo duk matsayin da kike so". Hassana mai da kanta ta yi tsakankanin cinyoyinta ta ci gaba da kukanta. Ana ahaka ne kiran Hajiya Turai ya shigo wayar Habib". Habib na d'agawa Hajiya Turai ta ce, "Hello Habib nan da minti goma jirginmu zai sauka, kaje ka d'akko daughter kuzo ku tar ban tare". "Tom Mommy, gani nan". Cewar Habib, sanna ya kashe wayar. Habib kama hannun Hassana ya yi, ya ce, "Zomu je mu d'akko Mommy yanzu zata sauka". Habib handkerchief d'in shi yasa ya goge ma Hassana fuskarta, saboda ta nuna alamun kuka". Hassana bayan Habib tabi suka shiga motarshi yaja suka nufi airport d'in. Hassana ko suna tafiya tana mai ci gaba da kukanta ka d'an ka d'an. Habib na lure Hassana har suka shiga airport d'in. Bayan ya yi parking ne ya kalli Hassana ya ce, "Ya Allah, wai har yanzu kukan nan kike yi, ki yi shiru kinga yanzu babu lokacin da za muyi magana, idan na kai Mommy sai muyi magana, yanzu goge hawayanki". Habib handkerchief d'in shi ya kuma mik'ama Hassana ta goge fuskanta. Ahana ahaka ne jirginsu Hajiya Turai ya sauka". Habib fita ya yi, ya bud'e Hassana, ya kamo hannun ta, suka tsaya dai-dai saitin da zasu ga Hajiya Turai. Habib na hango ta ya za hannun Hassana suka k'arasa gun ta". Hajiya Turai da fara'arta ta rungume Hassana tana Oyoyo daughter. Hajiya Turai na rik'e da hannun Hassana suka k'arasa inda Habib ya yi parking, suka shiga". Bayan sun isa gidan Hajiya Turai ne, Hajiya Turai ta kalli Habib ta ce, "Habib me yasa mu daughter?, daga ganin idonta ta yi kuka ". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Me yasa me ki, ki kai kuka? ". Hassana turo ma Habib baki tayi. Hajiya Turai ta ce, "Zo nan daughter ki zauna, ki fad'a min abinda ya yi miki". Hassana tashi ta yi ta zauna kusa Hajiya Turai kamar yadda ta umar ce ta. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "daughter fad'amin me yasa ki kuka, dan da ga ganin idonki ya nuna kinyi kuka? ". "Mommy ba fa ko mai abu ne ya fad'a min a ido". Cewar Hassana. Hajiya Turai bar maganar kawai ta yi, badan ta yarda da abinda Hassana ta ce ba". Hassana da Habib haddare suna gidan Hajiya Turai. Hassana ko tun d'azu da tai sallar magriba ta kwanta kan abin sallar saboda ciwan da kanta ya ke mata, dama in dai tai kuka sai tai ciwan kai. Habib zuwa ya yi ya yi ma Hajiya Turai sallama ya ce, "Mommy zan tafi sai gobe". "Tom daughter fa?, tun da tai sallar magriba bata fito ba, duba ta kagani ". Habib bedroom d'in Hajiya Turai ya shiga, Habib k'arasawa inda Hassana ta ke kwance ya yi, saboda jiyo sautin kukanta kad'an-kad'an da ya ji. Habib tado Hassana ya yi daga kwan can da ta ke, ya jingina ta da jikin shi, yana cewa, "yanzu dan Allah duk akan magana nan ce, ki ke kuka haka, ga kanki nan har ya d'au zafi, shikenan indai mataimakiyar manager ce na baki, shikenan kukan ya isa haka ". Hassana ko ita tama manta da wata mataimakiyar manager da ta ke so, kanta ke mata ciwo shi take ma kuka, ai ko tana jin abinda Habib ya ce, "d'ago kanta ta yi da yake mata ciwo sosai ta ce, "Oga Habib dan Allah da gaske? ". "Kai Habib ya d'agama Hassana, ya ce, "gobe zansa manager ya tabbatar da matsayin kowa ya sa ni". Hassana da ke zaune gefan Habib bata san sanda ta rungume Habib ba, tana cewa, "Dan Allah Oga Habib karka kuma can zawa, kuma kaima manager magana". "Tashi muje phamarcy d'in kusa da mu abaki magani sai mu wuce gida daga can". Cewar Habib". Hassana tashi ta yi, suka fita da Habib. Zaune suka iske Hajiya Turai a falo. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi ta ce, "Daughter lafiya ko? ". "Mommy kaina ke ciwo". Hassana taba Hajiya Turai amsa". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib ka biya da ita phamarcy ka amsar mata magani ". "Tom". Habib ya amsa ma hajiya Turai ". Hajiya Turai waya ta mik'ama Hassana, ta ce, "daughter ka tsarabar ki ". Hassana da murnarta ta amsa tana ma Hajiya Turai godiya. Sanna suka tafi". Habib sai da ya biya ta pharmacy ya saima Hassana magungunan ciwan kai sanna suka tafi. Kasan cewar sun ci abincin su gidan Hajiya Turai hakan yasa suna zuwa Habib ya zauna a falo, ya d'akko faro ya ba Hassana maganin ciwan kan. Hassana na gama shan maganin, ta kwanta. Habib kallanta ya yi ya ce, "ki tashi ki je bedroom d'inki ki kwanta kakki bacci anan". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib yau ba zan yi bacci ba, kaina kamar zai cire". "Tom ba ke bace kika kama kuka akan abinda bai kai ya kawo ba". Cewar Habib ". "Tom ai kaine kai min alk'awari ka fasa, Wallahi na tsani manager nan, shi dan yaga Billy budurwar shi ce shine zai wani anshe matsayina ya bata, ita kuma sai wani jin dad'i take hadda min gwalo, ni Wallahi na tsaneta ma, naga yadda za tai gobe idan taji an ban min matsayina". "Nifa wasa nake miki, ki tsaya a supervisor d'in da manager ya baki.... ". Ai Habib bai rufe baki ba, Hassana ta fad'o daga kan caution d'in, tana bubbuga k'afarta kamar sabuwar 'yar bori, tana bubbuga k'afarta tana kuka". Habib da sauri ya d'ago Hassana da ga k'asan ya maida ta kan caution d'in ya ce, " Wasa fa nake miki". "Wallahi babu wani wasa nasan daga manager yazo zaka ce mai abar ma Supervisor , ai gashi nan kama fad'a ". Hassana haka ta dage sai kuka take, dan ita fa gani take tabbas Habib da gaske ya ke wasa yake mata, ai rannan ma haka ya yi mata, ya ce ya bata matsayi ashe bai ba ta ba, inda bai bi tsarin da aka ba Supervisor ba". Babu yadda Habib bai yi da Hassana ta yi shiru ba wasa ya ke mata amma tak'i, daga k'arshe d'au karta ya yi ya nufi bedroom d'in shi da ita, Habib aje Hassana ya yi gefan ga don shi shima ya zauna, ya ce, "Kin ga kan ki ciwo yake ki yi shiru, ni wasa nake miki, na baki mataimakiyar manager, kamar yadda nace miki gobe zan sanarda manager, yanzu ki kwanta ki yi bacci ko zaki samu sau k'in kan". "Hassana shiru ta yi, ta kwanta kamar yadda Habib ya umar ceta, dan kukan nan da ta sake yi yasa kan ya sake mata wani sabon ciwan. Ahaka dai bacci ya kwashe Hassana, inda Habib shi kuma ya tashi ganin Hassana tai bacci ya watsa ruwa, sanan ya kwanta shima d'an nesa da Hassana". Washe gari Habib sai da ya yi sallah sannan ya tada Hassana, tana tashi side d'in ta ta nufa. Hassana da wuri ta yi abinda za tai ta yi shirin ta na fiya aiki. Hassana na fitowa taci karo da Habib shima zai tafi. Hassana da sauri ta k'arasa gurin Habib ta ce, "Ina kwana Oga Habib ". 'Lafiya".Habib ya amsa ma Hassana. Hassana da sauri ta k'arasa gurin Habib, ta ce, "Oga Habib in zo mu tafi tare? ". "Kai Habib ya d'aga ma Hassana". A mota Hassana tai ta rok'on Habib, akan dan Allah karya amshe matsayinta, ahaka dai suka isa Habib bai amsa ma Hassana ba". Can b'angaran Billy ma ita ma yau da wuri ta je Sanat, tana zuwa ta shiga Office d'in manager. Bayan sun gaisa ne, Billy ta kalli manager ta ce, "manager wai baka ce komai ba, game da maganar da yarinyar nan ta yi jiya ba? ". "Eh ina so yau zan ma M, d magana , idan yazo, karki ji komai matsayinki na nan". Billy cikin jin dad'in abinda manager ya ce, ta ce, "Manager idan har kai min haka ni kuma nai maka albishir d'in tsaida auran mu cikin watan nan ". "Aiko ki shirya zama amarya , dan ina mai tabbatar miki M, d, zai amshi maganata, nina san ta yadda zan b'llloma mai". Habib na zuwa babu dad'e wa manager ya Shigo Office d'in shi. Bayan sun gaisa ne, manager ya ce, "M, d dama akan maganar da Hassana ta yi jiya, kan matsayin Supervisor da ta ce bata yarda ba. Tom M, d idan zaka duba Hassana bata da Experience d'in da za abata matsayin mataimakiyata, Aganina matsayin Supervisor zai fi da cewa da ita,shine nake so ka ban dama a sake had'a wani meeting d'in, ka sanar da Hassana da kanka za tafi yarda ta yi hak'uri". Habib kallan manager ya yi yace, "Babu damawa". Yauma kamar jiya manager da kanshi ya sanar da kowa ne staff's a kwai meeting yanzu. Cikin k'ank'anin lokaci kowa ya hallata meeting d'in". Manager ne ya tashi ya ce, "Jiya munyi meeting inda muka tabbatar da matsayin Supervisor a mataimakiyata, tom amma kuma sai aka d'an samu matsala, inda Hassana ta tashi ta ce, bata yarda ba, ita M, d, ya ba matsayin. dan haka yau M, d zai tabbatar da matsayin kowa da kanshi, M, d, mismilah". Habib yana a zau ne ya fara magana kamar haka" Nina ba Hassana matsayi kamar yadda ta ce jiya, dan haka matsayinta na nan na mataimakiyar manager, ita kuma Supervisor zata zauna a matsayin..............✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Update d'in d'iya nayi mistake, zan sa shafi na 74&75.Sai nasa 74&74. Dan haka yau zamu tashi a Shafi na 76&78. Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kamma Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i.Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. RAYUWAR HAIDAR Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌 Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828 Shafi na 76&78. Habib Yana a zau ne ya fara magana Kamar haka"Nina ba Hassana matsayi Kamar yadda ta ce jiya, dan haka matsayin ta na Nan na mataimakiyar manager. Ita Kuma supervisor zata zauna a matsayinta na Supervisor".Habib na kai wa nan ya yi shiru. Manager sosai hankalin shi da ranshi ya b'ace Jin abinda M. D , ya ce. Manager da kyar cikin b'oye yanayin b'acin ran da ya ke ciki, ya tashi ya ce, "Tom Masha Allah da fatan ko wa yaji matsayinta, dan haka kowa ya tsaya ya yi aiki sosai, dan zamu rik'a bincika aikin kowa, idan Muna samun mutum da rashin kula da aiki tom zamu d'au ma taki akan shi". Nan taran ya tashi, inda aka bar daga Farida Sai Billy, Billy kallan Farida ta yi, ta CE,"Yau zan aje aiki, dan ba zan yarda ba, inyi aiki a k'ark'ashin yarunyar Nan, danni gaskiya Sai dai mu yi ta fad'a da ita, Kuma ina ga ya tabbata Oga Habib ya fara son yarinyar Nan,tunda ake meeting kin tab'a ganin ya tashi ya yi magana,Amma Yau da kanshi ya tashi Yana tsara yadda za'ai, gaskiya ni Yau zan bar aikin nan! ".Farida kallan Supervisor ta yi, cikin damuwa ta ce," Supervisor idan Kika bar aiki dan yarinyar nan ai wallahi kin fad'o , zama zaki yi mu had'e mata Kai, kinga ke manager ma na jin maganarki, ai idan ki ka ce yanzu kin aje aiki Wallahi ta San dan ita kika aje, ta san tsoro Kika ji, ke dai ka wai ki yi hak'uri aiki ma ai yanzu aka fara , ai Sai mun ga bayan yarinyar nan agurin nan, kina nu fin duk abinda tai Mana zata ci banza ne?, Yanzu abinda nake so da ke, ki aje maganar barin aiki mu fuskanci ta ina zamu fara, Kuma kin ga abin zai zo mana da sauk'i, inda in tana ta k'amar saman ki ta ke, tom ita ma manager ai samanta ya ke, kuma kin ga manager yana jin maganarki, yanzu ki je ki samu manager ki sanar da shi Zaki bar aiki, muji me zai ce". Billy shawarar Farida ta bi, Manager na zaune a Office d'in shi yana tunanin yadda zai b'ulloma Billy , Sai ga Billy ta shigo , Billy kallan Manager ta yi, daga ganin kwayar idon Billy ka san tana cikin damuwa. Manager kallan Billy ya yi, ya fara magana Kamar haka, "Tabbas na San ranki zai b'ace da abinda ya faru, ki yi hakuri.... ". Billy da da katar da manager ta yi ta ce," Manager maganar hak'uri ta k'are dan ni Yau zan bar aiki a Company'nan dan ba zan iya aiki ak'ark'ashin yarinyar nan ba". Manager cikin damuwa da barin aikin da Billy ta ce zata yi,ya ce,"Billy na san zaki bar aiki ne saboda matsinki da M.D yaba yarinyar'nan ,ki yi hak'uri nai miki alk'awarin zan dawo miki da matsayin ki ka fin nan da k'ar shen watan nan ". Billy kallan manager ta yi, ta ce, "ka tabbata dearie? ".murmushin magana ya yi, sannan ya d'aga ma Billy kai, Billy cikin jin dad'i ta tashi ta fita". B'angaran Habib ko yana zaune a Office d'in shi Hassana ta shigo da fara'arta tana zuwa ta idasa inda Habib ya ke zau ne. Babu zato babu tsammani sai dai Habib ya ji Hassana ta rungume shi, ta ce, "Oga Habib nagode, naji dad'in matsayina da ka bayyana agaban staff's, nagode dear.. ". Hassana saurin rufe bakinta ta yi, ta saki Habib zata gudu, dan sukubutar bakin da ta yi". Habib jawo Hassana ya yi, ta dawo ya rik'e ta ya ce, "Mai-mai ta abinda kika ce". Habib ya fad'i maganar yana kallan Hassana. Hassana hannu tasa ta rufe idanta, ta ce, "Nifa babu abinda nace".Habib hannu Hassana ya rik'e yana burzawa. Hassana ihu ta fara, tana cewa , "Wayyo Oga Habib da zafi Allah! ". "Tom mai-mai ta abinda kika ce". Cewar Habib ". "Tom naji sakar ni in mai-mai ta". Habib sakin Hassana ya yi, aiko yana sakin ta ta ta gudu". Habib jin kina ya yi da chair d'in da ya ke zaune kanta, idon shi rufe, ya na mai-mata abinda Hassana ta ce,ya yi murmushi, sannan ya ci gaba da abinda ya ke". Hassana tana fita Office d'in Habib ta wuce wajan koyan girkinta, ba ita ta dawo ba sai la'asar, tana dawowa ta je kan rubber chair ta sauna tana kallan staff's d'in sai aikin su suke, Hassana na nan zaune taga fitowar Farida daga Office d'in Billy. Farida ta zo dai-dai inda Hassana ta ke zata wuce, Hassana ta ce, "Farida me ya shigar da ke Office d'in ca muna tsakiyar aiki? ". Farida da mamaki ta kalli Hassana, sai tai murmushi ta ce, "Zan shiga duk inda nake so a Company nan a duk lokacin da naso, gargad'i na k'arshe kar ki kuma shiga safgata, idan ba haka ba, zan b'atar da ke da ta rihinki, acikin Company'nan". Hassana ta shi tai tsaye, tana kallan Farida dan ta bar shakkarta, ta ce, "Ni kuma ina miki albishirin zanyi amfani da da mata na koreki a Sanat company, ko kin san dan ke na amshi matsayin nan, ba zan tab'a barin Sanat ba sai naga bayanki, mu zuba ni da ke! ".Farida dariya ta yi, jin abinda Hassana ta ce, ta ce, "Aiko in dai danni kika amshi matsayin nan, ina mai tabbatar miki kinyi aikin banza, dama kin tsaya a share-sharanki da wankin toilet da yafi miki, dan ni Farida nafi k'arfin ko ruwa a gurin mutum k'askantaciya irinki, wadda bata da asali!, ni ba Sanat kad'ai zan kore ki ba, har gidan Oga Habib sai nayi amfani da basira na koreki". Sakarya mai aiki a titi babu Office! ". Farida na fad'in haka, ta bar gun kafin taji abinda Hassana zata kuma cewa". Hassana ko zama tai agun tana mai-mai ta maganganun Farida azuciyarta, tabbas sai nayi amfani da matsayina agun nan na mataimakiyar manager Farida na koreki gurin nan. Hassana ta dad'e zaune agun, sannan ta ta shi ta shiga office d'in manager ". Magan-ganun da Hassana ta ji anayi ne a Office d'in manager ya hana ta shiga, manager ne taji yana cewa, "Farida naji duk abinda kika ce, wato ta amshi matsayi ne dan ta kore ki aiki a Company, kar ku damu ku dai ku ban nan da lokaci kad'an, sai tabar Sanat yughurt da k'afafunta, na san yadda zan mata.... ". Hassana ji tai baza ta iya jure sauraro ba kawai ta banka Office d'in ta shiga. Hassana tsayawa ta yi tana kallan su d'aya bayan d'aya, sannan ta kalli manager ta ce, "Manager ada ina maka kallan adali, amma kuma a yau ina maka wani rin kkallo wanda ban san ya zan kira shi ba, sai dai ina mai mu ku albishir daga kai har su buku isa kusa in bar Sanat ba, sai dai ni in barta alokacin da naso". Hassana shiru ta yi, sannan ta ce, "Manager nazo ne ka ban Office ". "M, d bai fad'i a baki Office ba alokacin da ya baki matsayi". Cewar manager ". Hassana juya wa tai zata tafi, Farida ta rik'o hannun ta ta ce, "Ji mana, kina tunanin zaki iya karawa da mutum uku ko?, Yaro man kaza bai san wuta ba sai ya taka tabbas haka abin yake, zaki iya tafiya". Farida ta idasa maganar tana sakin hannu Hassana da k'arfi, Hassana kallan manager ta yi, ta ce, "Manager idan har haka zaka ci gaba da tafiyar da aikin ka, tom ba wai su ba, hatta kai zaka iya barin Sanat cikin k'ank'anin lokaci, kabar ta k'amar kana da power agun Oga Habib, ni zan rugaza power taka". Hassana na fad'in haka taja Office d'in da k'arfi ta fita". Manager da su Billy kallan juna sukai, manager ya ce, "kar ku ji komai zuwa gobe aikin zai fara, ai yarinyar nan sai ta bar gurin nan cikin satin nan, zan yi amfani da barinta gurinnan da ta ke yi, kullum ai ko yau sai da taje inda zata ta dawo taci gaba da aiki, dan haka karku ji komai, cikin satin nan nan komai zai zo k'arshe". Su Farida cikin jin dad'i suka kashe da juna ita da Billy ". Hassana ko gu d'aya ta samu ita ma ta zauna tana tunanin ta ina zata fara b'illo musu, wani tunani yazo ma Hassana ya sa ta tashi ta nufi Office d'in Habib". Hassana zama ta yi tana kallan Habib, sannan ta ce, "Oga Habib ina da tambaya? ". Habib d'agowa ya yi yana kallan Hassana, sanna ya ce ina ji? ". "Oga Habib atsa rin masana'antar nan manager zai iya hakana wasu aiki kawai su keb'e suna hira? ".Habib kai ya girgiza ma Hassana. Hassana kuma ta ci gaba da cewa, " Ni zan iya tsawatarwa akan abinda naga anayi ba dai-dai ba? ". Kai Habib ya kuma d'aga ma Hassana". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "shikenan Oga Habib ni zan wuce gida, akwai abinda zanyi". "Ki bari mu wuce tare". Cewar Habib ". Hassana hak'ura ta yi har lokacin da Habib ya tashi suka wuce tare". Washe gari Hassana ta gama shirinta na fiya aiki Habib ya ce mata yau ba zata ba, Hajiya na kiranta. Habib da kan shi ya d'au ki Hassana ya kai ta gidansu". Yau sati d'aya kenan raban Hassana da zuwa Sanat saboda kullum gidan Hajiya Turai ta ke wuni. Can b'angaran su Manager ko acewar shi sun samu damar dakatar da Hassana aiki, in da bata sanar ba. Aiko haka akayi yau Hassana tazo aiki saboda Hajiya Turai yau taje unguwa bata gida. Hassana na zuwa ta samu gu ta zauna inda ta ke zama, Hassana na nan zaune manager yazo da ta wata takarda ya mik'a ma Hassana ya ce, " mun baki suspection na sati d'aya, saka ma kon rashin zuwa ki na sati d'aya da biki ba, kuma ba bu wata sanarwa ko dalilin hakan". Hassana amsar ta kardar ta yi, ta kalli manager ta ce, "Zan tafi ne kawai dan uzirin kaina, Hassana na kaiwa nan ta tashi ta tafi. kamar yadda manager ya ce mata". Tun daga wannan rana Hassana ta fara zuwa koyan girkinta kullum har na tsawan sati d'aya kamar yadda manager ya bata. Habib ko koda ya tambayi Hassana lafiya ta bar zuwa aiki , fad'a mai ta yi manager ne ya bata suspection, Habib bai cema Hassana ko mai ba. Ahaka dai har Hassana ta yi sati d'aya". Zaman Hassana da Habib ko masha Allah, dan ahanki ahankali shak'uwa keta k'ara shiga tsakanin Hassana da Habib sosai". Yau Hassana da wuri ta tashi tai shirin zuwa aiki, tana zuwa ta samugu inda ta saba zama ta zauna". Billy ko da ke cikin karanta ba babbaka k'arfe biyu tazo aiki. Abin sosai ya yi ma Hassana da d'i, ganin Billy yanzu tazo aiki. Hassana tashi ta yi tana kallan Billy ta ce, " 'Yan matan manager ki ce yadda kika ga dama kike zuwa aiki, tom ki koma gida sai nan da sati biyu ki dawo! ". Billy dariya ta yi, ta ce, "Banda lokacin ki amma ga manager nan bari yazo ya baki amsa. Manager k'arasowa gun ya yi yana kallan Billy irin lafiya? ". Murmushi Billy ta yi, sannan ta ce, " dearie wai ta ban Suspection na two week's ". "Muje ". Manager ya cema Farida". Hassana kuma kallan manager ta yi, ta ce, "Ai wallahi sai ta yi zaman gida na sati biyun da na anbata". Billy kallan manager ta yi, ta ce, " dearie muje ka rabu da karyar". Hassana ranta b'ace ta ce, "Shine kare, shida ke binki kamar. ..... ". Marinda manager ya yi ma Hassana ne yasa bata k'arasa fad'in abinda tai niyya ba, manager hannu yasa zai kuma wanka ma Hassana mari... ". Yaji an ce, "Managereeeeeeeee..... ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kammala Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i. Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌👌 Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828. Shafi na 79&80. Managerrrrrrrrrrrrr.... ". Habib da fitowar shi ke nan daga Office d'in shi, ya ci karo da marin da Manager ya yi ma Hassana, manager ya kuma d'aga hannu zai k'ara mata ne Habib ya yi mai wannan kiran. Habib ranshi b'ace ya k'ara so gun, yana zuwa ya d'aga hannu sai da ya yi ma manager mari kwarara guda uku, sannan Habib ya nuna shi da hannu ya ce, "Manager ashe baka da tunani ban sani ba, yau fa ta dawo aiki daga Suspection d'in da ka bata, haka bai yi ma ba yanzu ta dawo zaka d'aga hannu ka mareta a company'na kuma!, ba komai ba laifinka ba... ". Maganar Hajiya Turai da Habib ya ji ce, ya yi saurin juyowa. Hajiya Turai zuwan ta kenan, ta hango Hassana zuk'un ne agun tana kuka, Hajiya Turai ita duk tunaninta ma Habib ne ya mari Hassana, hakan yasa, tana zuwa ta kamo hanun Hassana da ke zuk'unne agun ta ce, "Yi hak'uri daughter tashi muje gida". Daga ganin yadda Hajiya Turai ke magana kasan ranta a matuk'ar b'ace ya ke". Habib ko da kallo ya bi Hajiya Turai, dan yama rasa ya zai ce mata, Habib bin Hajiya Turai ya yi, dai-dai zasu shiga mota, ya ce, "Mommy ki.... ". "Bana son magana a condition d'in da nake! ". Habib jin abinda Mahaifiyarsa ta ce ne yasa ya ja bakinsa ya yi shiru". Habib Office d'in shi ya koma, ga ba d'aya ya rasa abinda ya ke mai dad'i, ana cikin haka ne, manager ya shigo, manager cikin hikima ya fara magana kamar haka"M'd ka yi hak'uri na kasa control d'in fushina, dan Allah ka yi hak'uri, ta kira ni da sunan da nakasa control d'in kaina ne... ". Tsawar da Habib ya yi ma manager ce tasa ya yi shiru. Habib kallan manager ya yi, ya ce, "Manager wai hak'uri zaka ban!?, kasan abinda ka aikata kuwa? , mari fa!?, tom bari kaji naji haushin korarta aiki da kayi, amma ban nuna ma ba, amma haka bai ma ba..., manager bana son yawan magana dan Allah ka fita kawai! ". Manager kallan Habib ya yi, ya ce, "M. D, dan Allah ka saurare n.. ". "Kafita nace ko!? ". Habib ya fad'i maganar da k'arfi". Manage fita ya yi. B'anga ran Hajiya Turai ko, bayan sunje gida kallan Hassana ta yi ga sawun marin da manager ya yi mata nan kwance a fuskarta, Hajiya Turai kallanta ta yi, ta ce, "Habib d'in ne ya mareki haka daughter? ". Kai Hassana ta girgiza ma Hajiya Turai ta ce, "A, a Mommy ba shi bane manager ne". Hajiya Turai da mamaki ta ce, "Manager kuma?, yanzu har Habib ya ba su manager damar da zai d'aga hannu ya mareki!?, dama da nace ma Habib kar ya sake kije Sanat aiki, da ya ke yaga na tafi shine sai da ya tura ki , ba damuwa ". Ita dai Hassana bata ce ma Hajiya Turai komai ba, dan ta ga tsan tsar b'acin ran Hajiya Turai a fili, na Marin da akai mata". Habib sai bayan magriba ya je gidan Hajiya Turai. Lokacin Hajiya Turai na falo, Habib ya shigo, tun daga yadda Hajiya Turai ta amsa ma Habib sallamar shi yasan akwai matsala. Habib d'an nesa da Hajiya Turai ya zau na, sanna ya gaida ta, Hajiya Turai da lafiya ta amsa ma Habib. Sannan Hajiya Turai ta kalli Habib ta ce, "Habib dama da nace ma kar Hassana ta je Company'ka tai aiki, shi bayan tafiya ta ka tura ta ko!?, shi ne ka wulak'anta ta gaban worker's d'in ka, har kaba wasu damar marina, babu komai bani ka wulak'an ta ba, kuma ita ma ba'ita ka wula k'anta ba, auranka ka wulak'anta". Habib kai ya d'ago ya kalli Hajiya Turai ya ce, "Mommy ki yi hak'uri, insha Allah haka ba zai k'ara faruwa ba". "Tom Habib ai hak'uri ya zama dole, idan ban yi hak'uri ba, zan sa a kama manager ne?, na yi hak'uri saboda wasu 'yan da lilai". Habib jan bakin shi ya yi ya yi shiru, dan bai san mai zai kuma cema Hajiya Turai ba kuma" Hajiya Turai ko tashi tai ta bar Habib shi ka d'ai agun". Habib ya dad'e zaune, sannan ya tashi ya shiga bedroom d'in Hajiya Turai ya yi mata sallama zai wuce. Hajiya Turai ba tare da ta kalli Habib ba, ta ce, "Sai da safe". Habib ganin Hajiya Turai ba tai mai maganar Hassana ba, kuma bai ga Hassanar ba, yasa ya yi tunanin tana gidan shi". Habib yana zuwa ya shige bedroom d'in shi, ya yi duk abinda zai yi har ya kwanta shiru bai ga Hassana ba, dan kullum Hassana ta saba sai ta damama Habib kunun shi ta kawo mai, a haka zasu yi ta fira da Habib, idan zata tafi ta kwanta Habib ya raka ta". Habib jin shirun ya yi yawa, yasa ya tashi ya nufi side d'in Hassana. Habib ko da ya shiga bai ga Hassana ba, hakan ya tabbatar mai da tana gida kenan. Habib ko mawa ya yi bedroom d'in shi ya kwanta". Washe gari Habib bayan ya gama shirinsa na tafiya aiki, sai da ya biya ta gidan Hajiya Turai. Habib zau ne ya iske Hajiya Turai da Hassana a derning space suna break fast. Habib zama ya yi, sannan ya gaida Hajiya Turai. Hajiya Turai sama-sama ta amsa ma Habib, sannan ta tura mai flaks d'in tea, Habib tsiyaya wa ya yi. Sai dai abinda ya d'aure ma Habib kai ganin Hassana ko kallan inda ya ke bata yi ba, bare ya sa ran zata gaida shi. abinda Habib ko bai sani ba, Hajiya Turai ce tasa Hassana karta sake ta gaida Habib ko da yazo. Ita kuma Hassana ta yi hakane kawai dan bin umar'nin Hajiya Turai, amma ita bata ga abinda Habib ya yi mata ba, acewarta, Manager ne ya mareta ba Habib ba, ko a yan zu Hassama ji tai ba dad'i gaida Habib d'in da ba tai ba, hakan yasa Hassana na gama shan tea d'in ta ta shi ta bar gun,Habib da kallo ya bi Hassana. Habib ka d'an yasha tea d'in ya yi ma Hajiya Turai sallama ya tafi". Habib na zuwa babu da d'ewa manager ya shigo Office d'in, manager kallan Habib ya yi, ya ce, "M. D dan Allah... ".Habib hannu ya d'a gama manager ya ce, "Manager dan Allah kaje kawai sai na ne me ka!". Manager fita ya yi". Billy da Farida ne suka tare manager, Billy kallan manager ta yi, ta ce, " Manager ya ku kai da Oga Habib d'in ? ". "Wai inje sai ya nai man". Manager ya basu amsa". Farida kallan manager ta yi, ta ce, "Wai dan ka mari yarinyar nan ne ya ke ma kora da hali haka? ". "Eh haka ne". Cewar manager. Farida ranta b'ace ta bar gurin bata sake iya yin managa ba. Manager kuma fita ya yi daga Company baki d'aya . Inda ita kuma Billy ta koma ta ci gaba da aikinta". Habib yau ma kamar jiya yana tashi aiki ya yo gidan Hajiya Turai. Babu kowa a falon, Habin zama ya yi yana jiran fitowar Hajiya Turai, yana nan zaune ko Hajiya Turai ta fito. Habib koda ya gaida Hajiya Turai da sakin fuska ta amsa mai ba kamar jiya ba, Habib ganin haka, ya sa ya ce, "Mommy kunu na ke so please ". Hajiya Turai da kanta ta shiga kitchen ta dama ma Habib kunu ta kawo mai.Hajiya Turai na ba Habib kunu ta nufi bedroom d'in ta inda ta bar Hassana, Hajiya Turai kwance ta iske Hassana, Hajiya Turai gefan Hassana ta zauna, ta ce, "daughter tashi mu yi magana". Hassana tashi ta yi ta zau na". Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter dama ina tsoran Allah ya kamani da shiga hak'inki da nayi a matsaynki na marainiya, ina tsoran kar Allah ya ka mani da laifi. A kwanakin baya kin nai mi zaki tafi gida na hanaki, saboda ina ganin kamar zaku dai-dai ta tsakaninki da Habib, ashe tunanina ba haka bane, tabbas na yi kuskure saboda aure ya na tafiya yadda ake so ne idan akace akwai Soyayya tsakanin ma'auraratan, amma idan ya kasan ce babu Soyayya tom zaman auran zai ka sance wani iri ne, ko wa ba zai iya jure abinda abokin zaman shi ya yi masa ba, ko ya ya ya ke, tabbas na yi kuskure, amma dan Allah ki yafe min, yanzu haka maganar da nake miki na gama shirya komai na tafiyarki garin ku, yan zu haka idan kin shirya gobe ma za ki iya tafiya, ni zan rakaki, amma sai nayi wani tunani naga bai kamata ba ki tafi da auran Habib akanki ba, dan haka yan zu haka yana Falo ki je ki sa mai ya baki ta kardarki, karki tafi da aure kan ki". Hassana cikin wani kallar ya nayi wanda ita kanta ta kasa gane kallar halin da take ci ki, ta d'ago tana Kallan Hajiya Turai, tama rasa abinda zata ce mata". Hajiya Turai ko hannu Hassana ta kama ta tadar da ita tsaye, ta ce, "Daughter je ki ki amsa kinji karya wuce, gobe nake son mu tafi". Hassana ta na fiya zufa na keto mata kota ina, Hassana tsayawa ta yi ta d'an jin gina da k'ofar bedroom d'in Hajiya Turai, dan jinta ta ke kamar zata fad'i, Hassana tsayawa ta yi tana maida numfashi kamar wadda ta yi wani aiki,Hassana ko so take ta dawo natsuwarta sannan ta tafi, dan sosai ta ke jinta duk a rikice. Hassana ta dad'e sosai gun a tsaye sannan ta samu ta daurar da zuciyarta ta shiga Falon". Habib tun daga nesa ya ke Kallan Hassana , da mamaki ya kuma kallanta ganin ta da ya yi tsaye, kuma, daga gani kamar tana cikin damuwa. Habib ganin Hassana bata da niyyar k'ara sowa inda ya ke, kuma yana yinta ya nuna kamar tana cikin damuwa, Habib tashi ya yi yak'a ra sa inda Hassana take, Habib Kallan Hassana ya yi ya ce, "Sanat lafiya? ". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib gobe zan koma mahaifata, tom bana son in tafi da aure kaina, ina son ka datse igiyar da ke tsakanin mu.......... ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ ALLAH karaya mu dan manzon Allah, ina ma duk kan d'aukakin musulmi barka da juma'@t mubarak, Allah ya had'amu da albarkar da ke cikin wannan rana👏👏👏. Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kammala Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i. Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌👌 Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828 Shafi na 81&82. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib gobe zan koma Mahaifata, tom bana son in tafi da aure kaina, ina so ka datse igiyar da ke tsakanin mu". Habib da ke rik'e da hannun Hassana, sakin hannunta ya yi, ya koma kan caution ya zauna, ya yi shiru yana kallan Hassana, dan yama rasa abinda zai ce mata. Hassana ko ganin Habib ya yi mata shiru ya sa ta matsa in da ya ke, cikin sanyin muryarta , ta ce, "Oga Habib ka yi shiru? ". Habib kallan Hassana ka wai ya yi ya rasa abinda zai ce mata, daga k'arshe ma tashi ya yi zai tafi, Hassana ta yi saurin bin shi ta rik'o hannun shi, ta ce, "Oga Habib gobe da wuri zamu wuce, babu lokaci". Habib cikin masifa ya fusge hannun shi daga na Hassana, ya ce, "Ko yan zu ma ku wuce ma na, sai me!, ita kuma Mommy da ta aiko ki ai bani na had'a abin ba , tun farko, ita da ta had'a, zata iya datsewa ba tare da sani na ba, inda dama bada sani na ta had'a ba! ". Habib na kaiwa nan yaja k'ofar falon da k'arfi ya bud'e ya fita, ya bar Hassana nan tsaye". Hassana komawa ta yi ta zauna kan caution tana mai da numfarfashi kamar wadda ta yi gudu. Hassana kwanciya ta yi kan Three seater, tana magana da zuciyarta ita kad'ai, Wata zuciyar ta ce, "Mommy me yasa kiki so ki ma rayuwata illa?, haba mommy tun-tuni me yasa biki raba ni da Oga Habib ba sai yan zu da zuciyata ta saba da shi... ". Haka Hassana ta kwanta a falon sai zan can zuci ta ke, gaba d'aya ta rasa abinda ke mata dad'i". Hajiya Turai ko jin Hassana shiru ya sa ta biyo Hassanar, kwance ta iske ta a falo, daga gani ta yi ni san kiwo a duniyar tunani. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter ya ba ki ko? ". Hassana tashi ta yi ta zau na, ta kalli Hajiya Turai ta ce, "Mommy cewa ya yi, wai lokacin da akai bai sani ba ai, wai yan zu ma za a iya warware wa bai sani ba". "Ok, haka ya ce ko?, bari in kira shi a waya ". Cewar Hajiya Turai ". Hajiya Turai kiran Habib ta yi, awaya, Habib lokacin yana kwance ko mawar shi kenan gida, yana zuwa ya fad'a kan bed d'in shi ya kwanta sai juyi ya ke shi kad'ai. Yana a wannan halin ne kiran Hajiya Turai ya shigo wayar shi. Habib kamar kar ya d'aga amma kuma sai ya ga garama ya d'aga ya ji abinda zata ce, hakan yasa Habib ya d'aga ya kanga wayar a kunnan shi". Daga can b'angaran kuma Hajiya Turai ta ce, "Hello Habib, naji sak'on ka, tom bari kaji da ina da mar datse igiyar da ke tsakaninka da Hassana da na datse ta tun jiya, tom amma a musulinci ban da huru min hakan, zan iya had'a wa amma raba wa kuma dole sai kai ne zaka yi ta, dan haka gobe kazo da wuri ina sauraranka , ka kawo min takardar ta, idan kuma ba haka ba, ranka zai b'ace sosai! ". Hajiya Turai na kaiwa nan ta kashe wayarta, bata saurari abinda Habib zai ce ba". Hassana ko da ke sauraran magan-ganun Hajiya Turai, ji tai kamar ta fasa ihu, ko Hajiya Turai zata fahimci halinda ta ke ciki. Hajiya Turai kuma kiran Hassana ta yi, ta ce, "Daughter tashi ki je ki kwanta kab bacci ya kwashe ki anan". "Mommy anan zan kwana ". Cewar Hassana ". Hajiya Turai hannu Hassana ta kama ta ce, "Tashi mu je ba za ki kwana a falo ba". Hassana tashi ta yi, ta bi Hajiya Turai ". Washe gari Habib bayan ya yi shirin ta fiya aiki, gidan Hajiya Turai ya biya, Yana zuwa ya iske falon ba kowa, ya da d'e zau ne Hajiya Turai bata zo ba, Habib da ya gaji da zama tashi ya yi ya tafi". Hajiya Turai ko da bata san Habib ya zo ba tada d'e tana sauraran zuwan shi amma taji shiru, hakan yasa ta kira shi awaya, yana d'aga wa, Hajiya Turai cikin masifa ta fara fad'a kamar haka"Habib ni zaka raina ma hankali ko?, nace kazo yau ina jiranka, shine kai min banza kai wucewar ka aiki ko? ". "Mommy nazo banga kowa ba, na dad'e zau ne a falon". Cewar Habib. "Ok kazo yan zu ina jiran ka! ". Hajiya Turai na fad'in haka ta kashe wayar ta ". Hajiya Turai na nan zau ne Habib ya shigo, Habib zama ya yi, Hajiya Turai ta kallai ta ce, "Yau na cema zan raka Hassana mahaifarta, kuma yarinyar nan ta saman ta ce min bata son tafiya da aure kanta saboda idan ta tafi bazata dawo ba, dan haka yan zu nan ina son ka datse igiyar da ke tsakaninka da ita, dama zata dawo ne da ban tsaya jiranka ba, da yan zu mun wace, tom amma ta ce min baza ta dawo ba". Habib da zufa ke keto mai kota ina, bama duka yake gane abinda Hajiya Turai ke ce wa ba". Hajiya Turai da ke jiran Habib ya ce wani abu, ta ji shiru babu alamun ma Habib zai tanka ma ta, hakan yasa Hajiya Turai ta ce, "Habib kai fa nake sauraro amma ka yi min shiru". "Na'am Mommy me kika ce? ". Habib ya tambayi Hajiya Turai, dan har ga Allah Habib ba duka abinda Hajiya Turai ta ce ya ke fahimta ba, shi dai kamar yaji tana cewa tana jiran shi yanzu". Hajiya Turai cikin mafisa ta ce, "Habib ka ban takardar Hassana nace yan zu , saboda gobe zata wuce da wuri!" Habib da bai son hayaniya mai k'arfi irin wadda Hajiya Turai ke mai, dafe kan shi ya yi, ya ce, "Mommy please ki yi a hankali, kaina ciwo ya ke"., Habib ya idasa maganar cikin damuwa ". Hajiya Turai cikin k'ara d'aga murya ta ce, "Idan kana so in yi managa a hankali tom yi abinda na saka ". Habib kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Mommy amma fa karki manta tun farko ta kurawar can ce ta sa ta ta gudu, tom yan zu idan ta koma bamu san irin wadda zata fad'a ba, ni a ganina kawai taci gaba da zaman ta nan Please Mommy'na ". Habib ka ga nifa bani nace mata ta tafi ba, ita taji zata tafi, dan haka ina gani kawai mu rabu da ita ta tafi, bana son wata doguwar mana, kawai ka aikata abinda nace ma, babu ruwanka da rayuwar da zata fuskanta, bama gara zamanta cikin dan ginta ba, akan zamanta nan kana sata aiki a Company'nka , hakan ma bai ma ba, har damar mari kaba wasu a gareta, wai matarka Habib zaka sa tana share-share da goge-! ". Habib shiru ya yi, sannan ya kalli Hajiya Turai ya ce, "Mommy ki yi hak'uri haka ba zai k'ara faruwa ba, Sanat kuma tun-tuni naso in hanata zuwa amma sai naga ita alokacin tana son aikin, shi yasa na barta, Mommy dan Allah ki fahimta ". "Habib.. ". Hajiya Turai ta kira sunan shi". Habib d'agowa ya yi yana kallan Hajiya Turai, da yau ta koma mai wata iri kamar ba Mommy shi ba mai tausan shi. Hajita Turai kallan Habib ta yi, shima ita yake kallo, ta ce, "Habib yau ba zaka bar gidan nan ba, sai ka ban ta kardar Hassan... ".kiran wayar da akai ne ya hana Hajiya Turai idasa abinda ta ke fad'a". Hajiya Turai na duba wa taga Hajiya Murja, wato Mahaifiyar Farida". Hajiya Turai, d'aga wa ta yi, tana sauraran abinda zata ce. Sai dai kukan da taji Hajiya Murja na yi ne ya ta da ma Hajiya Turai hankali. Hajiya Turai cikin rud'ewa ta ke tambayar Hajiya Murja, ta ce, "Hajiya dan Allah ki min baya ni mana, me ya faru ne? ". Hajiya Murja cikin kuka ta ce, "Hajiya dan girman Allah kuzo yan zu ke da Habib dan Allah Hajiya ". "Ki min ba yani lafiya dai ko? ". Cewar Hajiya Turai ". Mahaifiyar Farida cikin kuka ta ce, "Hajiya Farida ce ba lafiya, yau kwana biyu kenan tana aman jini, ance ciwan zuciya ne, dan Allah kuzo Hajiya, muna National Hospital ". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Tashi muje". Habib da ya ke ya ji wayar Hajiya Turai da Mahaifiyar Farida ya ji duk abin aka ce, hakan yasa ya tashi. Hajiya Turai ko Hassana ta kira tace tazo su je tare. Hassana da bata san zuwan Habib ba sai da ta fito falon suka had'u, Hassana kau da kanta ta yi gefe". Habib ne yaja su a motar shi ya kaisu har National Hospital. Suna zuwa suka kira Hajiya Murja awaya, ta fad'a masu number room da suke". Ba wai Hajiya Turai ka d'ai ba, har Habib da Hassana sai da suka tausaya ma Farida ganin halinda ta ke ciki. Hajiya Murja ko Mahaifiyar Farida, kusa da Farida ta matsa ta ce, "Farida bud'e idonki ga Habib d'in yazo". Farida mik'a hannuta ta yi, cikin murya irin ta masu ciwo ta ce, "Oga Habib kana ina?, dan Allah Oga Habib ka kama hannuna". Habib matsowa ya yi kusa da Farida yana kama d'ayan hannuta da ta ke mik'o mai ya ce, "sannu ko Farida Allah ya baki lafiya ". Farida tashi ta yi ta jingina, ta bud'e idonta da ke zubar da hawaye tana kallan Habib, ta ce, "Oga Habib sonka zai zama ajalina, ban tab'a son kowa ba, kuma ba zan tab'a ba koda rayuwata za tai tsawo. Oga Habib kai ne mutum na farko da naso, kuma kai ne mutum na k'arshe, Oga Habib duk zaman da nayi gidanku nayi shine dan kai, ko zan samu Soyayyarka, kuma dan kai naje SANAT nai aki, duk wani abu da ka gani na sa dan ya yi min kyau dan kai nake sashi, inda kai kuma ko kallo ban isheka ba, hak'ik'a Oga Habib sonka shine ajalina, ina nai man alfarma d'aya a gunka dan Allah, kace kana sona, duk da na san nina rok'eka, amma haka zai min dad'i, zan so kafin in mutu ka furta min kalmar so dan Allahhhhh ". Farida ta idasa maganar tana kuka". Tabbas Habib yasan Farida na son shi ba tun yau ba, amma bai zaci son ya kai haka ba. Habib kallan Farida ya yi cikin tausaya mata, Saboda tabbas ya san yadda ta ke ji, wani irin zafi ne mai fita da rad'ad'in zuciya, mai karyar da duk wata gaba dake jikin mutum. Habib cikin muryarsa mai d'auke hankalin 'yan mata masu karyaryar zuciya irin su Amina😜😜. Yace, "Farida ki yi shiru kinji, kin ga likita ya ce kina fama da ciwan zuciya, ki share hawayanki zan aureki. Ba wai Farida kad'ai ta rud'e ba da jin abinda Habib ya ce, duk wanda ke d'akin ne, dan dai suna da ban-ban cin rud'ewa. Hajiya Murja cikin farin ciki ta kamo hannun Habib ta ce, "Allah ya yi maka albarka Habib, Allah ya faranta maka fiye da yadda ka faranta mana". Habib dai bai ce komai ba, Hajiya Turai ga banta dukan uku-uku kawai ya ke yi, inda a zuciyarta ta ke cewa, Wallahi ba zai yuwu ba. Hassana ko ai fad'in halin da ta shiga ma jabu ne". Zuwan likitan da ke duba Farida ne yasa duk suka fiffita. Inda Hajiya Turai tai ma Hajiya Murja sallama tare da fatan Allah ya ba Farida lafiya". Farida ko tun ranar da suka rabu da manager ta koma gida ranta b'ace, ganin abinda Habib ya ke ma manager dan ya mari Hassana. Cikin dare Farida ta farka da aman jini, ko da zuka je a sibiti aka ce masu ciwan zuciya ne". Hajiya Turai ko suna cikin mota suna tafiya komawa gida, ta ce, "Habib abinda ka ce ma Farida da gaske ka ke , ko-ko? ". Habib shiru ya yi sai zuwa can ya ce, "Mommy da gaske nake". "Habib idan har ni na haifeka Wallahi ba zaka auri Farida ". Cewar Hajiya Turai. "Mommy nim ba wai ina son ta bane, kawai dai na tau saya ma halinda ta ke ciki ne, kuma kin ga na riga na furta". Habib na yin parking, fita ya yi, ya yi hanyar side d'in shi, inda Hassana ma tabi bayan shi, Hajiya Turai kuma tana ganin Hassana tai shiru ta rabu da ita,ko zata samu sassauci dan ta lura da irin furgicin da Hassana ta shiga jin wai Habib zai auri Farida". Habib na shiga side d'in shi Hassana ma tashi ga. Hassana sai da ta d'an numfasa sannan ta samu ta iya managa, duk da maganar a rice ta ke yinta. Hassana ba tare da ta kalli Habib ba ta ce, "Na san Mommy ta sake ma magana , amma naji shiru,na bi yoka ne in fad'ama idan Mommy ka ke ma kara ka ki sakina, tom tafi kowa burin rabuwar mu yan zu, dan haka ko ka ban takarda, ko baka ban ba, insha Allah daga gobe ba zan sake kwana a gidan ku ba". Habib in da Hassana ta ke tsaye ya k'arasa, dan d'an nesa dashi ta ke, Habib kallan Hassana ya yi ido cikin ido, ya ce, "Na san bake kika yanke wannan hukuncin ba Mommy ce, tom amma kema yan zu me yasa kike son biye mata? ". Hassana da idonta ya rufe bata san me ta ke cewa ba, ta ce, "Ni na yan ke bani na yanke ba, Oga Habib ba bu ruwanka, ni dai kawai ka ban takarda ta, kuma baka k'ara ganina har'aban-abada". Habib jawo Hassana ya yi, ya ce, "SANAT zo ki ji muyi managa". Hassana fun cike hannunta ta yi ta ce," Oga Habib ni ba wata maganar da za muyi". Habib ya dad'e tsaye yana kallan Hassana sannan ya ce, "Idan na baki ta kardar kina ganin haka ya fi mi ki? ". Hassana tana kuka ta d'aga ma Habib kai. Habib cikin bedroom d'in shi ya shiga, ya dad'e sannan ya fito da wata farar takarda a hannun shi, Habib na zuwa Hassana ta zuk'unna ta ci gaba da kukanta, ganin takardar sakinta a hannun Habib, dan a yadda Habib ya ke nuna mata, duk da bai ta b'a furta mata kalmar so ba, ta sha ba zai iya rabuwa da ita ba". Hassana zuk'unnawa ta yi, tana kuka. Habib ta da Hassana ya yi, ya ce, "Sorry Sanat kukan ki ya na torching heart d'ina, dan Allah ki yi shiru, Habib shiru ya yi, sannan ya ci gaba da cewa, "Sanat ke ce ta farko, ke ce ta k'arshe da na so, na kuma so ace na rayu da ke, zuciyata ta sa ba da ke, gangar jikina zata wahala sosai da rashin zaman ta da ke, amma ke da Mommy kin matsa sai mun rabu,shikenan gashi, Habib ya saka ma Hassana ta kardar cikin hannunta....... ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 Oga Habib 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Ina ba duk wani mai bibiyar Oga Habib hak'uri na jina shiru da akayi kwana biyu, dan Allah ku yi hak'uri, haka ya faru ne saka makon wani uziri da ya rik'eni. Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kammala Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i. Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌👌 Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828 Shafi na 83&84. Habib shiru ya yi, sannan ya ci gaba da cewa, "Sanat ke ce ta farko, ke ce ta k'arshe da na so ace na rayu da ke, zuciyata ta sa ba da ke, gangar jikina zata Wahala sosai da rashin zaman ta da ke, amma ke da Mommy kin matsa sai mun rabu, shikenan gashi ". Habib ya saka ma Hassana takardar acikin hannunta". Hassana najin ta kardar da Habib ya sa mata a hannu kukanta ya k'ara tsananta.Habib cikin damuwa ya kalli Hassana, ya ce, "Sanat dan Allah ki yi shiru mana kada kanki ya yi ciwo".Hassana cikin Muryar kuka ta ce, "Oga Habib sakanni zan wuce". Sabo da Habib na rik'e da Hassana". Habib cikin kunnan Hassana ya yi mata magana a hankali, ya ce, "zan sake ki amma sai kin dai na kukan, tukun". Hassana cikin alamun k'osawa ta ce, "Oga Habib dan Allah kasa kan! ". "Tom bar kukan sai in sake ki". Cewar Habib ". Hassana share hawayanta, ta yi, ta ce, "Oga Habib dan Allah ka sakan, zan wuce ne". Habib sakin Hassana ya yi ganin ta damu. Hassana kuma Habib na sakinta ta ruga da gudu zuwa Side d'in Hajiya Turai. Hajiya Turai na zau ne Hassana ta zo ta wuce ta tana kuka, dan Hassana ko kula ma da Hajiya Turai ba tai ba". Hajiya Turai kuma cikin sauri ta tashi ta bi bayan Hassana, ganin yadda Hassana ta shigo tana kuka, dan bisa ga alama ma ko kula da ita ba tai ba. Lokacin da Hajiya Turai ta shiga bedroom d'in Hassana , lokacin Hassana har ta kwanta tana mai ci gaba da kukan ta. Hajiya Turai cikin tashin hankali ta k'arasa gurin Hassana, Hajiya Turai na zuwa ta ya ye bargon da Hassana ta shiga, Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter lafiya?, mai Habib d'in ya yi miki?". Hajiya Turai duk cikin damuwa ta ke tambayar Hassana ". Hassana tsagaita wa ta yi da kukan, ya share hawayanta ta d'ago tana kallan Hajiya Turai. Hajiya Turai kuma cikin k'osawa ta kuma cewa, "Daughter fad'a min mai Habib d'in ya yi miki? ". Hassana share hawayanta ta yi, ta ce, "Mommy ba komai". "Tom me ya sa ki kuka? ". Hajiya Turai ta tambayi Hassana". "Mommy ba ko mai". Hajiya Turai da mamaki ta kalli Hassana, sannan ta ce, "Tom inda ba za ki fad'a min ba, bari in kira Habib ya fad'a min". Hajiya Turai waya ta ciro zata kira Habib.Hassana ta kalli Hajiya Turai, ta ce, " Mommy dan Allah karki kira shi".Hajiya Turai ta shi ta yi, ta fita. Dan tabbas ko mai Habib ya yi ma Hassana babba ne. Hajiya Turai side d'in Habib ta nufa ranta b'ace, tana zuwa zaune ta iske Habib kan caution kan shi yana kallan sama. Sallamar Hajiya Turai ce ta tada Habib ya d'ago yana kallanta. Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib me kai ma Hassana?". Habib d'ago kai ya yi yana kallan Hajiya Turai ya ce, "Mommy ban mata komai ba". "Ba kai mata komai ba zata fita tana kuka! ". Cewar Hajiya Turai ". "Mommy Allah ni ban mata ko mai ba, nima nan haka ta shigo min tana kuka,amma ni ban mata ko mai ba". Hajiya Turai tunanin auran Farida da Habib ya fad'a zai yi ne yasa Hassana kuka, wannan tunanin ne yasa Hajiya Turai ta fita ta koma side d'in ta". Lokacin da Hajiya Turai ta koma bedroom d'in Hassana har zazzab'i ya rufe Hassana, dan abu biyu suka taru su kai ma Hassana yawa, maganar auran Farida da Habib ya furta, sosai maganar ta firgita ta, sai kuma ga maganar sakin da Habib ya yi mata, dan sosai Hassana ta rud'e da takardar da Habib ya bata, wannan shine abinda ya hargitsa Hassana gaba d'aya". Hajiya Turai cikin sauri ta k'araso wajan Hassana tana tambayarta lafiya, ganin rawar sanyin da ta ke yi". Hajiya Turai cikin damuwa ta k'arasa wajan Hassana tana tambayarta Lafiya ". Hassana ko tsabar rawar sanyin da ta ke ko magama gagararta ta yi. Hajiya Turai cikin damuwa ta kira Habib, Habib na d'aga wa ta ce, " kazo bedroom d'ina yan zu". Hajiya Turai zama ta yi kusa da Hassana tana mata sannu, Hajiya Turai na nan zau ne Habib ya shigo, yana shigowa da sauri ya k'arasa gurin Hajiya Turai yana kallan Hajiya Turai ya ce, "Mommy lafiya me ke da munta? ". "Kira doctor ya duba ta zazzab'i ne". Habib Family doctor su ya kira awaya" Yana zuwa ya duba Hassana, sannan ya bata magunguna. Hajiya Turai ce ta ba Hassana maganin,Hassana amsa ta yi, sannan ta kalli Hajiya Turai, ta ce, "Mommy dan Allah zan je gida, ina son ganin 'yan'uwana"., Hassana tai maganar cikin rauni". "Ki yi hak'uri daughter zuwa gobe sai ki tafi".Hajiya Turai na fad'in haka ta fita, ta ce, "Daughter bari in kawo miki abinci ki ci". Bayan Hajiya Turai ta fita ne, Habib ya zauna gefan Hassana yana kallanta, sannan zuwa can ya ce, "Sanat! ". Hassana ban za da Habib ta yi. Habib ya kuma ce wa, "Sanat ki bar tafiyar ni zan kai ki ". Hassana da gaba d'aya haushin Habib ta ke ji, na sakinta da ya yi, banza ta yi da Habib, Habib kuma bai gaji ba ya kuma cewa, "Sanat please ko da Mommy tai miki maganar tafiya gobe ki ce mata ni zan kai ki ". Habib zai sake magana kenan Hajiya Turai ta shigo. Hakan yasa Habib yin shiru". Hassana tashi ta yi ta amshi abincin da Hajiya Turai ta kawo mata tana ci kad'an-kad'an dan tasan ko ta cema Hajiya Turai ta k'oshi Hajiya Turai ta kura ta zata tai sai taci, shi ya sa ma ta daure tana ci. Wayar Hajiya Turai ce ta yi ringing Hajiya Turai na dubawa ta ga Hajiya Murja mahaifiyar Farida ce. D'aga wa Hajiya Turai ta yi tasa a kunne". Bayan Hajiya Murja ta gaida Hajiya Turai ne, Hajiya Turai ta tambayi jikin Farida, Hajiya Murja ta ce, "Yauwa dan Allah Hajiya idan Habib yana kusa bashi wayar". Hajiya Turai mik'a ma Habib wayar ta yi, Habib amsa ya yi. Bayan ya gaida Hajiya Murja ne ya tambaye ta mai jiki. Hajiya Murja ta ce, "Habib jiki sai dai ace da sauk'i. Habib da ma naki raka ne, game da maganar auran Farida da kace za kai, shine nace ka turo namiji muyi magana inda kaga abu ne da za ai da wuri dan ceto rayuwar Farida, Wallahi yan zu haka baka ji ba, yadda ta ke kiran sunan ka, dan Allah Habib idan zai yuwu kazo yan zu". Kasan cewar wayar a speaker ta ke hakan yasa Hassana da Hajiya Turai sun ji duk abinda Hajiya Murja ta ce". Habib ko bayan Hajiya Murja ta kashe kiran, kallan Hajita Turai ya yi, ya ce, "Mommy bari inje in duba jikin nata". Hajiya Turai, tsabar ta kai ci, "Tom".ta ce ma Habib". Habib kuma tashi ya yi ya fita. Bayan Habib ya fita ne wani kuka ya kwacema Hassana wanda bata shirya yi ba, cikin kukan ne Hassana ta ce, "Mommy dan Allah ina son zuwa garin mu gobe dan Allah karki ce a'a". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Shikenan, daughter ki share hawayan ki gobe insha Allah zan kai ki". Hajiya Turai ta san kukan Hassana gaba d'aya duka ta gane manufar kukan, ita dai tunaninta yana bata akan kishi ne, in da Hajiya Turai bata san Habib ya saki Hassana ba, ita kuma Hassana tana son fad'a ma Hajiya Turai ta kasa". Hajiya Turai hannun Hassana ta kama ta ce, "Daughter dan Allah ki yi hak'uri Ki bar yawan kukan nan ni bana son Habib yaga kina damuwa haka akan shi, Maganar saki kuma ba bu na janye , ni dama wasa nake, ina so ne in gwada son da Habib ya ke miki, tom na gwada kuma nagani, ki bar yawan kukan, aure kuma ki barni da shi bai isa ba ya auri Farida ". Hajiya Turai tana fad'i ma Hassana haka ne ko hankalin Hassana zai kwanta, dan ta lura Hassana ta tada hankalinta sosai, shi yasa ta fad'a mata haka ko zata kwantar da hankalinta, idan ma Maganar Habib ya sake ta ne da ta yi". Hassana ko azuciyarta cewa ta ke, "Mommy kin makaro Oga Habib ai har ya sake ni ma ya gama". Hajiya Turai ko ta dad'e tana lallashin Hassana sannan taba Hassana gu". B'angaran Habib ko ya na zuwa Farida ta ke jin jiki ta tashi ta zauna. Farida cikin murya irin ta mara lafiya ta ce, "Oga Habib dan Allah ka aure ni, auran ka ka d'ai ne zai iya zaman towa sauk'i gareni, idan baka auran ba mutuwa zan yi... ". Habib rufe ma Farida baki ya yi, dan sosai ya tausayama halin da ta ke ciki, Habib cikin miskilancin shi ya fara magana kamar haka" ki bar yawan magana kin ga baki da lafiya, kuma nina ce zan aure ki, ba sai kin sake min Maganar ba, ina sa ne". Habib ya d'an jima sannan ya yima Mahaifiyar Farida sallama tare da ce mata zai samu Mommy shi su yi magana". Habib ta gidan shi ya biya ya d'ebo wasu daga cikin kayan sawar shi, sannan ya wuce gidan Hajiya Turai, dan can zai koma baya jin dad'in zaman shi nan shi ka d'ai" Habib a falo ya samu Hajiya Turai. Zama ya yi sannan zuwa can ya kalli Hajiya Turai ya ce, "Mommy dama Maganar yarinyar nan da nace zan aura, shine mahaifiyarta tai min magana yan zu". Hajiya Turai wani ban zan kallo tai ma Habib sannan ta ce, "Zan yi abu ne yan zu, zuwa gobe kazo sai mu yi magana". Ita ko Hajiya Turai ta yi haka ne, dan tafi son ta ce ma Habib tom ya yi auran karta nuna mai ko mai, tasan idan ya farga yaga ba Hassana, tana da tabba cin ba zai samu na tsuwar auran ba, inda tafi kowa sanin Habib auran tausai zai ma Farida ba wai so ba". Habib ko jin abinda Hajiya Turai ta ce ne yasa ya tashi ya nufi bedroom d'in Hassana da niyyar duba ta. Hajiya Turai dakatar da Habib ta yi, ta hanyar cewa, "yan zu bacci ya kwace ta karka shiga ka tada ta". Habib ba dan ya soba ya juya ya koma side d'in shi". Bayan Habib ya yi sallar issha'i ne ya nufi side d'in Hajiya Turai, amma abin mamaki a rufe Habib ya iske k'ofar falon, waya ya ciro ya kira Hajiya Turai, amma bata d'aga ba. Habib sai da ya yi ma Hajiya Turai kira kusan biyar sannan ta d'aga, ta ce mai ta yi bacci sai gobe kanta ne ke mata ciwo wai ta riga ta kwanta". Habib cikin sanyi ya ce, "Mommy dan Allah ki turo min number Yarinyar nan dan Allah in ji ya jikinta". Hajiya Turai kashe wayar ta yi, ta tura ma Habib number Hassana, tana tura mai ta nufi bedroom Hassana, Hajiya Turai kallanta ta yi, ta ce, "Daughter za'akiraki yan zu kar ki picking Habib ne". "Tom". Cewar Hassana ". Habib ko ta ke Hajiya Turai na turo mai number ya kira Hassana, amma bata d'aga ba. Habib sai da ya yi ma Hassana kira Uku sannan ya hak'ura ya tura mata Text kamar haka.:Sanat Please na san biki bacci ba, ki zo ki bud'e min k'ofar falo ina son ganin jikinki kafin in kwanta". Hassana share hawayanta ta yi da ta gama karanta text d'in , Sannan ta gyara kwanciyarta". Habib ko haka ya gaji da tsayuwa ya tafi. Sosai ya ji haushin shasshare shi d'in da Hassana ke yi, gashi yana son ya rabu da ita amma ya kasa. Habib yana tsaki ya koma side d'in shi". Hajiya Turai ko cikin dare ta shirya ma Hassana kayanta na tafiya,dan tafiyar wuri ta ke so suyi, dan yau zata dawo, Sannan bata son Habib yaga tafiyarsu, tasan zai fi jin zafi idan yazo yaga ba Hassana ". Asubar Fari Hajiya Turai ta tada Hassana ta yi wanka ta shirya cikin wani brown less, masha Allah Hassana ta yi kyau sosai. 7:00Am Hajiya Turai ta fito da babar jakar kayan Hassana taba Bilya ya sa a but. Habib ko da fitowar shi kenan da niyyar zuwa gaida Hassana.Habib tun daga nesa kafin ya k'ara so ya ke mamakin Kayan da yaga Bilya na sawa abut, ga Hajiya Turai da shirin tafiya a tsaye, Habib cikin zuciyar shi ya ke cewa dama yau Mommy zata tafi bata fad'a min ba..... Tunanin Habib cak ya tsaya ganin Hassana ta fito daga side d'in Hajiya Turai da alamun har da ita za ai tafiyar, ta ke tafiyar Hassana danginta ta fad'o ma Habib". Habib kusan atare da Hassana suka isa wajan motar, Hassana ko naganin Habib ta yi saurin d'auke kanta, inda shi kuma Habib ya kema Hassana kallan mamaki". Habib cikin sanyi ya gaida Hajiya Turai. Hajiya Turai ko da taji haushin ganin tafiyar su da Habib ya yi, dan taso ace sai bayan tafiyarsu ya sani tasan haka sai yafi bashi haushi, hakan yasa Hajiya Turai ta k'ara shan mur, Habib kuma cikin alamun damuwa ya ce, "Mommy yau zaki koma ne? ". "Eh". Hajiya Turai ta ba Habib amsa". Habib kallan Hassana ya yi da ke shirin shiga mota ya ce, "Ke fa, rako zaki yi? ". Kai Hassana ta d'aga ma Habib, Habib ganin haka, ya kalli Bilya ya ce, "Billya bari in kai Mommy ". Hajiya Turai cikin alamun ba wasa, ta ce, "Sauka Bilya zai kai mu dan tafiyar mu da nisa, yau Hassana zata koma dan ginta, ban dai so ta tafi da auran ka ba, amma inda kak'i sak'i sau wa k'e mata babu komai, ahaka zata tafi! ". Habib da Maganar Hajiya Turai ta soki zuciyar shi kamar an buga mai mashi haka ya ji, ta ke zufa mai d'imi ta fara keto mai.Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, 'Daughter shigo mu wuce". Habib hannun Hassana ya kamo da sauri ya ce, "Mommy ki yi hak'uri ba bu inda Hassana zata". Habib ya fad'i maganar cikin d'aurewa ". Hajiya Turai wani banzan kallo tai ma Habib ta ce, "Idan ka isa ba sai ka hana in gani ! ". Hassana ko so take ta shiga cikin motar, amma Habib ya rik'e hannunta sosai, Hajiya Turai fitowa ta yi daga motar tazo taja hannun Hassana, amma Habib ya rik'e hannun Hassana da kyau, Hajiya Turai kallan Habib ta yi, babu alamun wasa ta ce, "Habib sakar ta ". "mommy ki yi hak'uri Hassana babu inda zata"., Hassana ko cikin murya irin ta mai son yin kuka ta fara magama kamar haka, "Mommy ki ce mai ya sakan, dan duk Maganar da yake bashi da wani iko akaina, a halin yan zu, dan ya ban takarda ta tun jiya, yan zu haka tana hannuna". Habib da mamaki ya kalli Hassana ya ma kasa magana. B'angaran Hajiya Turai ma da mamaki ta ke kallan Habib. Hajiya Turai Cikin b'oye fushin ta ta kalli Habib ta ce, "Habib da gaske ne ka saki Hassana? ". "Mommy ki tambayeta, amma ni ban sake ta ba". Hajiya Turai mai da kallanta ga Hassana ta yi, ta ce, "Daughter fad'a min gaskiya, yau she Habib ya sake ki!? ". Hajiya Turai cikin fad'uwar gaba ta idasa Maganar, dan tana tunanin tabbas kukan da Hassana ta yi jiya, na sakin da Habib ya yi mata ne" Hassana Cikin tabbatar wa ta ce, "Mommy Wallahi da gaske nake". "kawo min takardar na gani". Cewar Hajiya Turai ". Habib sakin hannun Hassana ya yi, Hassana kuma ta nufi bedroom d'in Hajiya Turai d'akko ta kardar". Hassana babu inda bata duba ba amma bata ga takardar ba, haka ta dawo. Hassana kallan Hajiya Turai ta yi ta ce, "Mommy na duba banga takardar ba, amma abinda na fad'a miki haka n... ". Tsawar da Habin ya yi ma Hassana ce ta sa ta yi shiru, Habib cikin b'acin randa Hassana bata tab'a ganin shi da shi ba ya ce, "Idan kina son tafiya ki tafi mana, sai me, amma akan me agabana zaki min k'arya! ". Hajiya Turai sosai kanta ya d'aure da abinda Hassana ta ce, kuma tabbas ta yadda da Maganar Hassana, dan ta lura da halin da Hassana ta shiga jiya bayan fitowarta side d'in Habib.tom kuma a yananin Maganar Habib kamar bai saki Hassana ba. A zaman da Hajiya Turai tai da Hassana ta lura da yarinyar bata da k'arya, kuma ta lura Hassana na son Habib, ba za tai mai k'arya ba. Hakan yasa Hajiya Turai tai tunanin k'ila Habib d'in ne ya koma daga baya ya d'auke ta kardar, inda ta san shi da fushi, tom k'ila ya yi fushine ya saketa daga baya kuma ya koma ya d'auke ta kardar". Hajiya Turai ranta b'ace sosai ta ce, "Daughter shiga mu tafi! ". Habib saurin rik'e Hassana ya yi, ya ce, "Mommy na yarda ta tafi, amma sai in ta fad'i gaskiya, dan ni k'arya ta ke min ban saketa ba". Habib ya fad'i maganar ran shi b'ace". Hajiya Turai da ranta ke ab'ace, kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib ni zaka raina ma hankali ko, ka saketa na ce!". "Mommy ki saurare ni Please, Wallahi ban aikata abinda ta ce ba". Hajiya Turai d'aga hannu ta yi ta wanka ma Habib mari ta ce, "Sakar mata hannu na ce!". Habib wujijjiga Hassana ya yi, ya ce, " Fad'i ma Mommy gaskiya mai na rubuta miki jikin takardar da na baki........ ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy Baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kammala Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i. Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌👌 VIP group 300 Only👌 , normal kuma 200 ne, zaki yi transfer ta account d'in nan 2111619333. Account name Fadila Sani. Bank Name Zenith bank. Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828 Shafi na 85&86. Hajiya Turai da ranta ke ab'ace kallan Habib ta yi ta ce, "Habib ni zaka raina ma hankali ko?, ka saketa na ce! ". "Mommy ki saurare ni Please, Wallahi ban aikata abin da ta ce ba". Hajiya Turai d'aga hannu ta yi ta wanka ma Habib mari, ta ce, " Sakar mata hanni na ce!. ". Habib wujijjiga Hassana ya yi, ya ce, "Fad'i ma Mommy gaskiya, mai na rubuta miki jikin takardar da na baki? ". Habib ya idasa maganar yana kuma wujijjiga Hassana da k'arfi. Hassana ko da ta tsorata da yadda taga Habib, cikin siririyar murya ta ce, "Ni ban karanta abin da ka rubuta ba, amma na san saki n... ". Tsawar da Habib ya yi ma Hassana ce tasa ta yi shiru bata k'arasa fad'in abin da ta ke fad'a ba. Cikin tsawa Habib ya ce, ", Wallahi zan fasa bakin ki kika idasa! ". Hassana shiru ta yi tana kallan Hajiya Turai jin Hajiya Turai bata sake magana ba. Hajiya Turai ko tama rasa abin da zata cema Habib ya saki Hassana, hakan yasa ta tsaya tana kallan shi". Habib kuma tura Hassana ya yi, Hajiya Turai na mai magama amma bai saurareta ba, ya ce, "Muje ki nuna min inda kika aje letter". Hajiya Turai na ma Habib magana amma bai saurareta ba, haka ya ya tasa k'eyar Hassana har bedroom d'in Hassana". Habib kallan Hassana ya yi babu alamun wasa ko fara'a afuskar shi, ya ce, "Nemo ta kardar ki ban". Hassana tsayawa ta yi, tana kallan Habib ganin yadda ya wani sha mur, Hassana ita kanta cikin ta kai cin hanata ta fiya da Habib ya yi ta ke, kallan Habib d'in ta yi, ta ce, "Oga Habib ni ina ganin babu wani amfanin sai na nemo takardar, saki ne ka rubuta min, tom yan zu kai zaka fad'i saki nawa ka rubut... ". Habib d'aga hannun da ya yi zai mari Hassana ne ya sa tai shiru, ta yi sauri ta b'oye fuskarta k'irgin Habib, tana wani irin kuka. Cikin kukan ne Hassana ta ke magana kamar haka, "Oga Habib me naima da zaka rik'a marina haka?, kasan me ke damuna?, kasan yadda nake ji azuciyata?, na had'a kayana zan tai mahaifata ka hanani, kuma bacin haka ka bini da mari, da me kake son inji? ". Hassana ta idasa maganar cikin matsanancin kuka. Habib d'ago kan Hassana ya yi da ta tusa a k'irjin shi tana kuka, sannan ya jata suka zauna bakin gadon. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Sanat da gaske kike na rubuta miki takardar saki? ". Hassana kai ta d'aga ma Habib.Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "kin karanta takardar ne? ". Kai Hassana ta girgizama Habib. Shiru Habib ya yi, sannan ya ce, " Tom me yasa zaki yan ke hukunci akan abin da bi ki sa ni ba?, Shikenan, zaki iya tashi ki bi Mommy ku tafi, ko ba komai kad'ai ci zai kare min, gobe za'a d'aura aurena da Farida". Habib na fad'i ma Hassana haka ya ja k'ofar bedroom d'in da k'arfi ya fita". Hassana zubewa tai a gadon tana kuka. Hassana ta dad'e tana kukanta sannan ta gaji ta lallashi kan ta tai shiru. Habib ko barin gidan ya yi baki d'aya". Hassana had dare tana nan kwance Sallah ka wai ke ta data sai abinci da d'azu Hajiya Turai ta matsa mata sai ta ci, ta tashi ta ci. Hassana na nan kwance Hajiya Turai ta shigo d'akin, Hajiya Turai zama ta yi tana nazarin Hassana. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter dan Allah ki fad'a min gaskiya Habib ya sake ki? ". Hassana k'asa tai da kan ta, sannan ta ce, "Mommy ban bud'e takardar ba, amma lokacin da zai ban takardar ya fad'i wasu kalmomi ne masu kama da saki".Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "kalmomi kamar wasu iri? ". Shiru Hassana ta yi, sannan ta ce, "Mommy lokacin da naje mai da Maganar ya sakan, ya ban baki nak'i, shine sai ya shiga bedroom d'in shi, ya fito da takardar da ya ban, ya ce wai yaso ace ya rayu da ni, tom amma ni da ke mun k'i yarda, shine ya ban takardar". Shiru Hajiya Turai ta yi, sannan ta ce, "Tom me yasa ke biki duba ta kardar ba? ". "Mommy haka nan ni ban duba ba". Cewar Hassana ". Murmushi Hajiya Turai ta yi, dan tasan fargaba ce ta hana Hassana du ba takardar. Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ina kika aje letter da kika shigo? ". Hassana gadon ta ta nuna ma Hajiya Turai. Hajiya Turai kuma kallan Hassana ta yi, ta ce, "Tashi mu duba mugani". Hassana tashi ta yi suna duba ko'ina a bedroom d'in , amma ba suga letter ba. Hajiya Turai ce ta yi dabarar ya ye bedsheet d'in sai ga ko takardar. Hajiya Turai d'auka ta yi ta mik'ama Hassana sannan ta fita ta barta ita ka d'ai ". Hassana ko zama ta yi, jin yadda zufa keketo mata, dan hannu da ta rik'e takardar ma kanshi rawa yake, dan gani take daga ta bud'e zata ga saki uku. Hassana cikin ja rumta ta bud'e letter ta fara karantawa kamar haka. "SANAT tabbas ban san zuciyata ta shak'u da ke ba shak'uwa mai nisan gaske sai da kika bijiromin da maganar saki. SANAT hannuna ba zai iya rubuta abin da ki ke so ba, na rok'eki ki yi hak'uri, bana son kina furta min lamar da tai shigyan haka". Daga k'arshen rubutun Habib ya sa da manyan bak'i. 'ZUCIYATA TA SHAK'U DA KE SANAT". Hassana koda ta gama karanta letter wani sanyi taji aranta, Alhamdulillah ta ke furtawa, ta ce, "Oga Habib kai zuciyarka shak'uwa ta yi da tawa, inda ni kuma tawa zuciyar ta fad'a tsantsar soyayyarka. Oga Habib ka so ni dan Allah ko rabin yadda na ke son ka ne, Wallahi zuciyata ba zata iya rayuwa ba da kai ba". Haka Hassana tai ta surutanta ita kad'ai. Ringing tone d'in wayar ta ne yasa ta dawo tunaninta. Hassana koda ta duba screen d'in wayar Number da aka kirata ce jiya Hajiya Turai ta ce karta d'aga Habib ne, Hassana tana cikin nazarin Number ne wayar ta tsinke, Wani kiran ne yak'ara shigowa.Hassana d'agawa ta yi ta kanga wayar a kunnan ta". B'angaran Habib ko yana jin Hassana ta d'aga, ya ce, "Helloo SANAT ". Hassana da taji kiran har cikin ranta, rintse ido ta yi". Habib kuma jin Hassana ta yi shiru, ya ce, "SANAT kin yi bacci ne, in kashe wayana? ". Hassana cikin kasalallar murya irin mai kashe jikin masoyi, ta ce, "Ogaa Habibbh ina ji". Habib da ke shingid'e sai da ya tashi ya zauna, jin yadda Hassana ta kira sunan shi, Ogaa Habibbh". Habib numfasawa ya yi, sannan ya ce, "Kina ina yan zu ? ". "Ina bedroom d'ina". Hassana taba Habib amsa. "Ok, ina part d'ina kizo yan zu ki saman". Hassana shiru ta yi, dan bata san ta yadda zata fita ba, tana tsoran Hajiya Turai tazo bata nan. Hakan yasa Hassana ta ce, "Oga Habib kai kazo mana ". "Ok, ke baza ki zo ba? ". Habib ya tambayi Hassana. Shiru Hassana ta ta yi, dan ba zata iya cema Habib, Eh ba". Habib kuma jin Hassana ba ta ce komai ba, ta yi shiru ba amsa, ya ce, "SANAT ki zo yan zu, za muyi magana ne". Habib na fad'in haka ya kashe wayar shi". Hassana ko tashi ta yi, ta lek'a falo taga Hajiya Turai bata nan, da sauri Hassana ta fito kamar muna fuka, ta fita daga Falon Hajiya Turai, ta nufi side d'in Habib". Habib na nan kishingid'e kan caution ya ji nocking d'in Hassana, ta shi ya yi ya bud'e mata". Hassana k'arasowa ta yi ta zauna gefan Habib, tana wasa da 'yan yatsun ta ta, Hassana gaida Habib cikin sanyi, sannan ta ce, "Oga Habib gani". Habib d'ago kai ya yi yana kallan Hassana ganin yadda yan zu-yan zu, ta canza ba kamar d'azu ba ta suka so su fasa mai kai ita da Hajiyarsa. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Ina letter da nace ki ne mo? ". Hassana rufe idonta ta yi da hannu, ta ce, "Na ganta". "Ok, saki nawa akasa aciki? ". Habib ya tambayi Hassana. Hassana sai yan zu abubuwan da tai suke fad'o mata, kallan Habib ta yi, ta ce, "Tom nikam na zaci haka kasa, shi yasa". "Uhm, sabo da shine aranki ba". Cewar Habib ". Habib shiru ya yi sannan ya kalli Hassana ya ce, "SANAT zan auri Farida gobe, kina son zaki zauna nan ne tare da Mommy ko ko, zaki koma can ne da zama? ". Hassana da taji maganar Habib kamar ya buga mata mashi a k'ahon zuciya, shiru ta yi, dan bata ma san mai zata cema Habib ". Habib ko jin Hassana ta yi shiru kai ya d'aga yana kallan ta, abin mamaki hawaye Habib yaga yana zuba a fuskar Hassana. Habib da bai san mai ya yi ma Hassana ba, cikin damuwa ya rik'ota, ya ce, "SANAT me yasa kike da saurin kuka haka ne?, ki yi hak'uri in dai tafiya ce ni zan kaiki, ko kuma in sa Bilya ya kai ki". Hassana tashi tai tsaye ta juyama Habib ba ya, sannan ta ce, "Oga Habib wai me yasa baza ka sake ni bane!? ". Hassana ta idasa maganar da kuka". Habib da mamaki ya kalli Hassana, sannan ya tashi ya ce, "SANAT Kin ce kinga letter da na baki bikiga abin da nasa bane ajiki?, ". Habib ya fad'i maganar a raunane". Hassana juyowa ta yi suna fuskantar juna da Habib sannan ta ce, "Oga Habib ka aje Farida duk in da ya yi maka nan ko can, amma ni garinmu nake son tafiya ka ban takardar ta ! ". Hassana ta k'arashe maganar da tsawa". Habib da mamaki ya ke kallan Hassana, jin yadda ta ke mai magana da ihu, wai shi yau mace ke mai magana da ihu, Habib ma cikin zafin rai ya ce, "Bazan bayar ba, idan kinga dama ko yan zu ki tafi mana". Hassana cikin kuka ta ce, "Wallahi Oga Habib sai ka ban takardata Ba zan tab'a zama da kai da Farida ba, na tsaneta bana son ta, bana son ta!!! ". Hassana duk cikin kuka ta ke maganganun nan. Habib ko zama ya yi yana kallan ta, sannan ya tashi ya jawo Hassana ya zaunar da ita gefan shi, ya na kallanta, ganin yadda ta ke kuka. Habib kallan Hassana ya yi cikin damuwa, ya ce, "Tom naji ki yi shiru please, yan zu mai kike so? ". "Aini ba ce ma ka nayi ina son wani abu ba, amma dai nace in dai ka auri Farida sai dai ka saka..". Habib saurin rufe ma Hassana baki ya yi, da hannu ya ce, " Tom ki yi shiru na fasa auran ta d'in, ya yi? ". Habib ya fad'i maganar yana kallan Hassana, ba wai ya fad'i haka da gaske bane ya fad'a ne kawai dan Hassana ta yi shiru. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Sanat me yasa baka son in auri Farida, ba kya tausaya ma halinda ta ke ciki ne? ". Hassana da ta tsagaita da kukan da ta ke turo baki ta yi, ta ce, "Oga Habib ni dai Allah in dai ka ce zaka auri Farida sai dai ka sake ni". Habib tsayawa ya yi yana kallan Hassana, sannan ya ce, "Biki ji ba ne, na ce miki zuciyata ta saba da ke , hannuna ba zai iya rubuta miki saki ba. ". "Tom yan zu zaka auri Farida ke nan!? ". Habib tsoran cema Hassana Eh ya yi, gudun rigimarta, hakan yasa ya girgiza mata kai, alamun a'a. Hassana kwantar da kanta ta yi jikin kafad'ar Habib ta ce, "Oga Habib dan Allah karka aure ta". Habib kan Hassana ya shafa ya ce," tom naji". Hassana ko tsabar dad'in abin da Habib ya ce, rungume Habib ta yi, ta ce, "Yauwa Oga Habib, nagode ". Habib dai shiru ya yi, dan bai san yadda zai yi ba ya kau ce ma auran Farida inda ya riga ya furta Maganar". Hassana ko tashi ta yi, ta ce, "Oga Habib zan tafi, tashi ka rakani". "Inna rakaki ni wa zai rakoni? ". Cewar Habib. Hassana ko kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib ai kai baka jin tsoro". "Uhm sabo da ni ba mutum ba ne". Habib ya ce ma Hassana ". Hassana ko ganin Habib ba rakata zai yi ba, ta shi ta yi tai ma Habib sallama zata tafi, Habib ya san Hassana na da tsoro hakan yasa ya ce, "Duk abin da kika gamu dashi babu ruwana". Ai Hassana kamarma taga abun, da sauri ta fad'a jikin Habib, tana cewa, "Dan Allah Oga Habib ka raka ni ". Habib kallan Hassana ya yi ce, "Nikam tashi kije, biki san kin yi k'iba ba zaki fad'o min haka salan kikaryani". Hassana turo baki ta yi, ta ce, "Oga Habib ni yau she ma nayi k'ibar da zan karya ka". Habib tashi ya yi, ya ce, "Tom sarkin surutu ni na tafi sai da safe". Hassana tashi ta yi, ta rik'o hannun Habib ta bi shi. Hassana na zuwa ta kwanta gefan gadon Habib ta ce, "Oga Habib tun baka da lafiya ra bona da kwana gadon nan". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Dama gadon kike kwana?, tom waya ce ki kwana min gado". "Kai kasa". Hassana taba Habib amsa". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Da nai me ne nasa? ". Hassana tuna ranar da Farida ta bata maganin da ya hirgitsa rayuwarta ta yi, ranar da ta fara kwana kan gadon Habib. Hassana tuna haka ne, yasa tai sauri ta juya ma Habib baya, ta ce, "Da Kai ko mai ma, tom kai Oga Habib me ye ma ba kai ba". Habib zaro ido ya yi waje , ya ce, "kamar me da me? ". Hassana kwanciya ta yi, taja bargon Habib ta rufe kanta duka, ta ce, "Oga Habib sai da safe, bacci nake ji". Habib rabuwa ya yi da ita dan maganarta ta k'arshe ta sashi tunani, da ya yi komai ma, tom kai Oga Habib me ye ma ba kai ba. Ya mai-maita maganar Hassana, kai k'arya ta ke Habib ya fad'a azuciyar shi". Habib wanka ya shiga yana ta repeating d'in maganar Hassana, wata zuciyar ta ce mai tom ko shiyasa Mommy ta had'a aure na da ita. Habib wannan tunanin da ya yi yasa ya yi sauri ya gama wankan shi, ya fito,doguwar rigarshi ka wai yasa, ya hau gadon , Habib shiga bargon Hassana ya yi, Hassana da ba tai bacci ba tana jin duk wani motsin Habib, Habib rungumo Hassana ya yi, ya ce, "Sanat zan tambayeki ki fad'a min gaskiya please ". Hassana rintse ido ta yi, jin yadda Habib ya rik'e ta, Habib kuma ya ci gaba da cewa, "Me yasa Mommy ta had'a aure na da ke? ". Hassana shiru ta yi, sannan ta ce, "Sabo da idan nazo kawo ma abinci baka barina in tafi, sai dai in kwana nan". "Shine da lili Habib ya tambayi Hassana". "Eh shine dalili". Hassana taba Habib amsa ". Habib kallan Hassana ya yi da idonta ke a rufe, ya ce, "Ya kika ji lokacin da Mommy tai miki ta yi aurena? ". Hassana bud'e idonta ta yi tana kallan Habib ta ce, "Na shiga tashin hankali sosai". "Me yasa kika shiga tashin hankali? ". Habib ya tambayi Hassana. "Sabo da ina tsoran ranar da zaka farga kaga ni ce Mommy ta had'a ka da ita". Cewar Hassana ". Shiru Habib ya yi, sannan ya ce, "Tom ya kika ji lokacin da na samu lafiya? ". "tom da farko dai naji dad'i sosai lokacin da na tabbatar kaji sauk'i, danni lokacin na saba da kai, sai dai ina cikin mugun tsoran kasan Mommy ta had'a ni aure da kai". Habib shafa kan Hassana ya yi, ya ce, "Mai tsoro ka wai. "Tom Oga Habib ba dole mutum yaji tsoranka ba, kai fa ko dariya baka yi". Murmushi Habib ya yi. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib kai ya kaji da kasan Mommy ta had'a mu aure? ". "Banji komai ba". Habib ya ba Hassana amsa". Turo baki Hassana ta yi, ta ce, "Allah ba wani nan, abin da ina ganin ka kana hararata idan kashigo". Murmushi Habib ya sake yi, sannan ya ce, "Serious lokacin da nasan Mommy ta had'a ni aure da ke banji ko mai ba, kawai dai ina kunyar friend's d'ina suji ina auran staff d'ita". Uhm, Hassana ta ce, Sannan ta ce, "Tom yan zu fa ya ka ke ji ". "D'aya da yadda nake ji da, kawai dai na yi hak'uri ne ganin Mommy na son ki". Hassana ta shi ta yi da sauri zata sakko kan gadon, Habib ya rik'e ta sosai yadda ko motsi bata iya yi. Hassana kamar za tai kuka ta ce, "Allah Oga Habib ka sakan ni tafiya zan yi, ba zan kwana nan ba". Haka Hassana tai ta cucu-cuku ita ala dole bazata kwana nan ba. Habib ganin da gaske ta ke, dan Hassana ta iya birkicewa. Habib cikin kunann Hassana ya fara magana kamar haka, "SANATT Allah wasa nake, yan zu Ina jinji cancikin tsakiyar lugun k'arshen zuciyata, Sanat ke d'aya ce ina soooon ki". Wayyo dad'i wato kalmar soyayya tafi komai dad'i idan ta fito daga bakin wanda kake so". Hassana wani rin sanyin dad'i taji yana shiga cikin k'ofofin jikin ta. Hassana hannu tasa ita ma ta rungume Habib ta kasa furta komai a bakin ta. Habib ko jin Hassana ta yi shiru bata ce komai ba, sai dai shige mai da ta ke kuma yi, hakan kad'ai ya tabbatar mai ta yi appreciate d'in maganar. Habib cikin kunnan Hassana ya rad'a mata ya ce, "SANAT kin yarda mu zama d'aya ni da ke a yau....... ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝. Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). https://chaveryt.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7 https://www.facebook.com/groups/301023561618950/ Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kammala Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i. Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌👌 VIP group 300 Only👌 , normal kuma 200 ne, zaki yi transfer ta account d'in nan 2111619333. Account name Fadila Sani. Bank Name Zenith bank. Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828 Shafi na 87&89. Habib cikin kunnan Hassana ya rad'a mata ya ce, "SANAT kin yarda mu zama d'aya ni da ke a yau? ". Hassana shiru ta yi kamar bata ji abin da Habib ya ce ba. Habib ko jin Hasssana ta yi mai shiru kuma kiran sunan ta ya yi ya ce, "Sanat kin yi shiru? ". Hassana cikin sayi can k'asa-k'asa ta ce, "Sai da safe bacci zan yi". "Tom biki ban amsa ta ba? ". Habib ya tambayi Hassana". Hassana ko da bata san amsar da zata ba Habib ba shiru tai mai, Habib ya gaji da magana shima yaja bakin shi ya yi shiru. Ahaka dai har bacci ya kwashe Habib. Washe gari Habib bayan ya tashi ya yi sallah ya tada Hassana ta tashi ta yi, Hassana na yi sallah ta kalli Habib ta ce, "Ina kwana Oga Habib ". "Lafiya". Habib ya amsa ma Hassana. Hassana tashi ta yi zata tafi, Habib ya kalleta ya ce, "Ina zaki? ". "Zan tafi bana son Mommy ta tashi bata ganni ba". Hassana ta ba Habib amsa". Habib tashi ya yi ya ce, "Muje in rakaki". Hassana tashi ta yi, Habib na rik'e da hannun ta suka nufi side d'in Hajiya Turai. Hassana na shiga side d'in Hajiya Turai dai-dai locin ita kuma ta fito, kallan-kallo aka tsaya yi. Habib ko da yaji dad'in ganin su da Hajiya Turai ta yi, cikin jin d'in hakan Habib ya gaida Hajiya Turai. Hajiya Turai amsawa ta yi babu yabo ba fallasa. Hassana ko ba tare da ta yadda ba sun had'a ido da Hajiya Turai ba ta ce, "Ina kwana Mommy ". "Lafiya ". Hajiya Turai ta amsa ma Hassana exactly yadda ta amsa ma Habib". Habib juyawa ya yi ya tafi yabar Hajiya Turai da Hassana nan tsaye. Hajiya Turai kallan Hassana ta ti, ta ce, "Daughter na shiga bedroom d'in ki ban ganki ba, ina kika je? ". Hassana cikin rashin sanin amsar da zata ba Hajiya Turai ta ce, " Mommy Oga Habib ne ya ki rani in kai mai letter da nagani,shine bacci ya kwashe ni acan". Hajiya Turai kama hannun Hassana ta yi suka zauna, Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter Shi na miji ba ka fitowa tun da farko kana rawar kai akan shi, Habib fa har yan zu babu wani kwakkwaran horo da ki kai mai, ba wai na ce dole sai kin hora shi bane, amma dai ki yi abin da zai san ke d'in mai aji ce, ba wai nace Kibar mai magana ba, a'a ki rik'a mai magana kamar yadda kukeyi, amma daga yau karya k'ara kiranki side d'in shi kije". Hassana dai kai kawai ta d'aga ma Hajiya Turai". Hajiya Turai tashi tai ta bar Hassana a falon zau ne, dan ita da Hassana ta biye mata sai ta wana Habib sosai sannan ko za ta rik'a kula shi". Hassana tashi tai cikin sanyi ta shiga bedroom d'in ta tana zuwa toilet d'in ta ta nufa tai wanka, Hasssana na fitowa kiran Habib na shigowa wayarta, Hassana na d'agawa Habib ya ce, "kina ina? ". "Ina bedroom d'ina". Hassana ta ba Habib amsa. "Tom ki fito falo yan zu zan shigo ". Habib na fad'in haka ya kashe wayar shi.Hassana ko da sauri-sauri ta shirya ta nifo falon. Zau ne Hassana ta iske Habib da Hajiya Turai suna fira. Hassana can gefan Hajiya Turai ta zau na, Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Ki je ki yi break fast ". Hasssana tashi ta yi ta nufi side d'in derning. Habib kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Mommy nima ban yi break fast ba, bari in sha ko tea ne ". Habib bai saurari abin da Hajiya Turai zata ce ba ya tashi ya tafi". Zau ne Habib ya iske Hassana na had'a tea. Habib zama ya yi, bai cema Hassana ko mai ba, itama bata ce mai ba, Hassana tana gama had'a tea d'in ta fara sha, ta d'aga Cup d'in zata sake kai wa bakinta Habib ya rik'e hannun Hassana ya kai tea d'in ba kin shi, ya ce, "inda biki had'a min ba sai musha naki tare". Hassana barma Habib ta yi, da ya mik'o mata tak'i amsa, ta ce, "kasha zan had'a wani". "Ni naki nake son sha ai". Habib kai tea d'in ya yi bakin Hassana, ya ce, "bud'e bakin". Hassana bud'e bakin ta ta yi Habib ya tsiyaya mata tea d'in, haka dai suka gama shan tea d'in Habib na sha yana ba Hassana ". Bayan sun gama shan tea d'in ne Habib ya tashi dan yau yana son yaje Company ya gani, Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Sanat zan je aiki yau". "Tom sai ka dawo". Hasssana na fad'in haka ta juya zata tafi, Habib jawo hannun ta ya yi ya ce, " Ban wani abu mana, da zan tuna da ke in naje". Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Wani abu kamar me? ". Hannun Hassana Habib ya ja wo ya yi mata Uhhmm muahh lips d'in ta. Hassana da babu zato babu tsammani ta ji sauk'ar kiss aleb'anta. Habib ya ce, "Kamar irin haka nake nufi". Hassana fusge hannun ta ta yi ta gudu tabar Habib tsaye agun, Hassana kusa da Hajiya Turai ta Fad'a ta zau na, tana sauke ajiyar zuciya, Hajiya Turai wai gowa kawai ta yi ta kalli Hassana ta girgiza kai. Hassana ko sai yan zu ta lura da Hajiya Turai". Habib sallama Ya yi ma Hajiya Turai ya tafi. Habib ko da ya je Company, Alhamdulillah ya iske kumai na tafiya yadda ya kamata, dan yan zu Bilya da Billy suke jan ragamar komai. manager ko dama ya ce ma Billy daga ta ga M. D, ya zo ta kira shi ta fad'i mai. Aiko Billy tana ganim Habib ya zo ta kira manager a waya ta sanar da shi". Habib na zau ne a Office d'in shi Manager ya yi nocking, Habib izinin shiga ya ba shi, manager cikin sanyi ya gaida Habib sannan ya ce, "M. D, hak'ik'a na san nayi kuskure kuma tabbas nayi nadamar abin da ya faru, dan Allah ka yi hak'uri". Shiru Habib ya yi yana kallan manager , sai zuwa can ya d'aga kai yana kallan manager ya ce, "Manager abu d'aya zai sa in yafe ma kuma abun d'aya ya hana ban d'au ma taki akan ka ba, saboda ayan zu kai kamar sirikina ne, zan ma hak'uri ne sabo da haka, Sannan kai ka shige gaba wajan aure na da Sanat, zan ya fema dan haka,amma duk da haka sai da yaddar Sanat, dan haka ka saurare ni zuwa gobe". Manager godiya ya yi ma Habib ya tafi, dan yadda ya ke samun kud'i a Sanat ba zai yarda ba aikin ya sukub'uce mai ba". Habib gaf da magriba ya tashi aiki ya koma gida. Side d'in shi ya shiga sai da ya watsa ruwa ya yi sallah sannan ya nufi b'angaran Hajiya Turai. Habib Hajiya Turai kad'ai ya iske a Falon, zama Habib ya yi gefan Hajiyarsa ya gaida ta. Shiru-shiru Habib bai ga Hassana ba, Habib Hajiya Turai ya kallah ya ce, "Mommy ina yarinyar nan? ". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Wata yarinyar? ". Kai Habib ya sosa ya ce, "Mommy Sanat fa nake nufi". "Ok, tana ciki... ". Hajiya Turai bata rufe baki ba Hassana ta fito, Hassana gefan Hajiya Turai ta zau na. Hassana na zama Hajiya Murja na yin sallah ma ta shigo, Hajiya Murja na zuwa ta je ta rik'e k'afafun Hajiya Turai tana kuka, ta ce, "Hajiya dan Allah ki bar Habib ya rufa min asiri ya ceto rayuwar yarinyar nan ya aure ta, Wallahi yan zu haka Hajiya Turai na barota sai aman jini take,Habib dan Allah ku tai maka". Habib da tausan Hajiya Murja ya kama shi, gyaran murya ya yi, ya ce, "Mommy ki yi hak'uri ni nai miki alk'awari kuma zan cika miki insha Allah". Habib mai da kallan shi ga Hajiya Turai ya yi ya ce, "Mommy ku yi hak'uri dan Allah ke da Sanat zan auri Farida ne ba dan soyayya ba, zan aure ta ne dan ceto rayuwarta, dan Allah Mommy ku yi hak'uri ". Hajiya Murja kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib in dai ka yarda zaka ceto rayuwar Farida tom kazo mu je yan zu ga waliyin Farida nan cikin mota, kai kuma sai ka samu naka, yan zu ad'aura auran idan an idar da Sallar issha'i ". Habib kallan Hajiyarsa ya yi da fata furta koma ba, ya mai da kallan shi ga Hassana da ita ma shi ta ke kallo, Habib jin du kan su babu wanda ya yi magana, kallan Hajiya Murja ya yi, ya ce, "ki je gida kawai zan nai mi wanda kika ce kuna tare yan zu mu yi magana". Hajiya Murja godiya ta yi ma Habib sannan ta tashi ta tafi, Hajiya Murja ta tafi bai fi da minti goma ba Habib ma ya tashi jin kiran Sallah zai tafi. Hassana ko da ta san Habib daga wajan Sallar za'a d'aura auran shi da Farida, Hassana ta shi ta yi da sauri ta rik'o hannun Habib, Hassana cikin kuka ta ce, "Wallahi Oga Habib Allah baza ka fita ba sai ka sakan ai tun jiya haka mu kai da kai, ka sakan sai kaje ka aure ta in da tausan ta ka ke ji! "Habib tsayawa ka wai ya yi yana kallan Hassana yama rasa me zai ce mata, Hassana kuma ta kama Habib kata kam ta rik'e ta k'i saki. Hajiya Turai ko da ita kanta bata san mai zata cema ba,tashi tai ta ba su gu". Habib kallan Hassana ya yi cikin sanyin murya ya ce, "Haba Sanat wai ke biki san abin da kike fad'a babu kyau ba, dan Allah me yasa kike yin haka ne, ki zauna in je Sallah in dawo sai mu yi magana". "Ai ina ji kace idan kaje sallah za'a d'aura auran acan, ni dai kawai ka ban sannan ka tafi, amma ni bazan tab'a zama da Farida ba!". Duk maganar da Hassana ta ke yi cikin kuka ta ke yin ta". Habib hannun Hassana ya kama suka zauna, hannu Habib ya sa ya goge ma Hassana hawayan ta, ya ce, "Sanat ki yi shiru tom muyi magana". Hassana shiru ta yi tana kallan Habib alamun ina jinka. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Yan zu me ye damuwar ki da auran Faridar? ". "Ni ban iya zama da ita ba ne". Hassana ta ba Habib amsa. Magana Habib zai k'ara yi ringing d'in wayar shi ya hana. Habib d'aga wa ya yi, daga can b'angaran Hajiya Murja ta ce, "Habib dan Allah naji shiru ga waliyin Farida ya kirani wai yaji ka shiru"."Ok, gani nan zuwa". Habib ya ba Hajiya Murja amsa". Habib tashi ya yi zai tafi, Hassana ta rik'e Habib tai tana kuka, tana cewa, "Dan Allah Oga Habib karka je, dan Allah, Allah in ka aure ta ba zan ji dad'i ba, dan Allah ". Haka Hassana ta rik'e Habib tana kuka tana rok'an shi. Dan tai mai ma kurarin sakin amma bai ji ba". Habib jikin shi sosai ya yi sanyi da yadda yaga Hassana tana kuka, ga Hajiya Murja na jiran shi. Habib rasa yadda zai yi ya yi, komawa ya yi ya zauna dan Hassana ta k'udin-dine shi ta hana shi fita, ga kukanta na da mun shi sosai, dan ya lura in dai tai kuka bata da wuyar ciwan kai". Habib rungume Hassana ya yi yana lallashin ta, ya ce, "Shikenan na fasa, tom ki share hawayan ki". "Ai jiya ma haka kace min" Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Kina son in fasa auran Farida? ". Kai Hassana ta d'aga ma Habib". Habib kallan Hassana ya yi, yana na zari, dama yana son Hassana ta koma gidan shi da zama tom yasan Mommy ba zata bari ba, ba kamar yan zu ba da yasan ya k'ara b'ata ma ta rai ba, hakan yasa Habib cema Hassana, "Sanat na fasa auran Farida, amma in dai kin yarda sai dai yau ki koma gidanki ki bar gidan Mommy, kuma karki bari Mommy ta sani, tom in dai kin yarda da haka ni kuma na fasa auran ta". Hassana ba tare da tunanin ko mai ba, ta ce, "Eh na yarda". Habib cikin jin dad'in abin da Hassana ta ce, ya tashi ya ce, "Tom tashi mu tafi kafin Mommy ta fito ". Hassana ta shi ta yi tana kama hannun Habib suka bar falon Hajiya Turai, suna zuwa Habib ya hangi wanda Hajiya Murja ta ce yana jiranta acikin mota. Shi ko mai jiran Habib ya na ganin Habib ya yo inda ya ke da sauri, hannu ya ba Habib suka gaisa, sannan ya ce, "Tun d'azu nake jiranka, gashi har nai ma limamin magana, yan zu haka kai suke jira". Habib kallan shi ya yi, ya ce, "sai zuwa gobe ma yi magana". Habib na fad'in haka ya shiga motar shi ya ja suka tafi suka bar Waliyin Farida tsaye". Habib na isa gida direct falon shi ya yi da Hassana suna zuwa Habib ya shiga wanka, ya yi alwallah. Habib bayan ya fito sanye da farar jallahbiya aji kin shi, kwance Habib ya iske Hassana, Habib hannun ya mik'a ma Hassana ya ce"Sanat zo in cud'aki". Hassana dariya ta yi, ta ce, "Bana so kai ma kai kai ma kanka, ni ma ni zanma kai na". "Ok, kina sha'awar yi min ne? ". Habib ya tambayi Hassana ". Hassana ta shi ta yi tana ba Habib amsa ta ce, "Uhm lokacin da baka da lafiya dai nai m.... ". Habib bud'e baki ya yi yana kallan Hassana ya ce, "Kin me? ". Hassana da sauri ta nufi hanayar Toilet, Habib ya ja wo ta ya yi yana kallan ta, ya ce, "Serious kin tab'a min wanka? ". Hassana kai ta juya ta ce, "Ni dai ka sakan in je in yi wanka na". "Nak'i d'in sai kin ban amsa, kin tab'a? ". Habib ya tambayi Hassana". Shiru Hassana ta yi, sannan ta ce, "Ni fa bani kema ba, kai ne ke shiga da kanka idan ina wanka, duk yadda nayi ka yi da kanka kake ma kanka". Habib kallan Hassana ya yi ganin ta fad'i maganar tana b'oye dariya , ya ce, "Da kaya jikina ko ko? ". "Tom ni dai na ma manta kamar akwai kamar babu". Hassana ta ba Habib amsa still tana son yin dariya ". Habib jan hanun Hassana ya yi juwa toilet d'in ya ce, "Muje nima yau ni zan miki ". Hassana k'ara ta yi, ta ce, "Tsaya in fad'ama gaskiya, Allah da kaya jikin ki". "Uhm nima muje in miki da kaya jikinki". Habib ya ce ma Hassana ". Hassana tsayawa ta yi tana kallan Habib ta ce, "Tom inda haka ne ma na fasa wankan". Murmushi Habib ya yi, ya ce, "Aiko yau dole ki wanka". Habib da k'arfi yaja Hasssana ya kai ta toilet d'in". Hassana cikin sakin k'ara da ya ke ita mai katsaniya ce, ta ce, "Tom Oga Habib tsaya, Allah da kaya nake ma, nima ba sai na cire ba". Habib ko sauraran Hassana bai ba, ya zage zip d'in doguwar rigar jikinta. A haka akai wankan daga ita sai bra sai pant d'in jikinta. Hassana ganin wankan ya k'i k'arewa jawo towel ta yi ta d'aura tana turo baki, ta fita tana cewa, "Duk an bi an wani kalle mutum". Habib dai murmushi kawai ya yi ma Hassana. Hassana na zaune tana shafa lotion d'in Habib, wayar Habib ta yi, ringing, Habib ganin number Hajiya Turai sai da gaban shi ya fad'i, aiko yana d'agawa Hajiya Turai ta ce, "Habib ina Hassana!? ". Habib kallan Hassana ya yi da ke zau ne tana shafa, sannan ya ce, "Mommy ga ta nan muna tare". daga can b'angaran Hajiya Turai ta ce, "Duk abin da ka ke ka bari ina son inga Daughter yan zun nan!? ". Hajiya Turai na fad'in haka ta kashe wayarta, tana mai ganin sakarcin Hassana ". Habib ko tashi ya yi ya tada sallah, yana idarwa ya kalli Hassana ya ce, "kin yi Sallah ne? ". Kai Hassana ta d'aga ma Habib". Habib ko gudin kar Hajiyarsa ta sake kira kashe wayar shi ya yi, acewar shi gobe ya mai da mata Hassanar. Habib kwanciya ya yi yana tunanin yadda zai yi da Mahaifiyar Farida, Hassana ko bayan ta gama shafarta da d'an k'aramin towel d'in da ke jikinta ta nufo wajan Habib, dan Hassana ta kan manta sabon da su kai da Habib kafin ya samu lafiya ne. Habib na kwance Hassana ta zo ta kwanta gefan shi. Habib juyo wa ya yi yana kallan Hassana, Habib jawo Hassana ya yi kusa da shi ya ce, "Mommy na nai manki, gashi ni kuma ba zan iya komawa yan zu ba sai dai gobe"."A'a ni dai ka tashi ka kai ni yan zu". Habib kuma jan Hassana ya yi ya ce kwanta mu yi bacci da sassafe zan kai ki". Hassana da dama bacci ta ke ji tana kwanciya bacci ya kwasheta, Habib kuma ga ba d'aya ya kasa bacci, d'an k'aramin lips d'in Hassana ya k'ura ma ido, can dai ya kama lips d'in yana kissing. Hassana cikin bacci taji an rik'e bakin ta. Ta shi ta yi da sauri zata zauna, Habib ya yi saurin rik'ota ya ce, "Sanat please ki yarda yau mu zama d'aya mana ". Hassana ciku-cikun kwace kanta ta ke, amma ina abun ya ci tura". Atak'aice acikin daran Habib ya mai da Hassana ci kakar mace". Asubar fari Habib ya tashi ya watsa ruwa, ya yi alwallah ya yi sallah, yana nan zau ne har aka kira Sallah, sai da gari ya yi haske sannan Habib ya tada Hassana, da kan shi ya tai maka mata ta kin tsa kanta". Hassana na yin Sallah ta koma ta kwanta in da Habib ma ya kwanta rungume da Hassana suka koma wani baccin". Kiran wayar Habib ce ta sa Habib ya tashi, Habib na d'agawa Hajiya Murja ta ce, "Habib kazo yan zu dan Allah ". Hajiya Murja ta fad'i maganar tana kuka". Habib ta shi ya yi ya shirya yana cikin shirin Hassana ta tashi tana son yi ma Habib magana ta kasa, dan ta ji wayar da ya yi da Hajiya Murja. Hassana ta shi ta yi ta nufi side d'in ta, tana zuwa da sauri ta shirya ta zauna Falo tana jiran Habib". Habib zau ne ya iske Hassana a falo, Hassana ta shi ta yi ta rik'e hannun Habib tana mai kauda idonta, da kallan shi, dan sosai ta ji tana jin nau yin had'a ido da Habib d'in". Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "Sanat zaki bi ni ne? ". Hassana kai ta d'aga ma Habib". Habib kama hannun Hassana ya yi suka nufi asibitin da aka kwantar da Farida...... ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment Sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB 📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy baby). Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kammala Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i. Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌👌 VIP group 300 Only👌 , normal kuma 200 ne, zaki yi transfer ta account d'in nan 2111619333. Account name Fadila Sani. Bank Name Zenith bank. Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828 Shafi na 90&91. Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Sanat za ki bi ni ne? ". Hassana kai ta d'aga ma Habib. Habib kama hannun Hassana ya yi suka nufi asibitin da aka kwantar da Farida". Habib na rik'e da hannun Hassana su shiga d'akin da aka kwantar da Farida. Lokacin Hajiya Turai bata nan ta ta fi kiran likita ya duba Farida ganin yadda ta ke ta aman jini, Habib da Hassana da sauri suka k'arasa in da Farida ta ke. Habib cikin tausayin Farida ya ce, "Sannu Farida". Farida ko da ta ji Muryar Habib kamar a mafarki, cikin rauni irin na marasa lafiya Farida ta rik'a lalibar Habib. Hassana ganin haka da sauri ta rik'o hannun Farida. Farida ko a tunaninta Habib ne ya rik'e ma ta hannu". Farida cikin dauriya da jarumta ta fara magana kamar haka, "Oga Habib ko da Mommy'na ta ce min zaka auran ban yarda ba, duk da ka fad'a aga bana, tabbas kai d'in raban Hassana ce, Hassana ta kasan ce mai sa'a arayuwa, Oga Habib ina ji ajikina mutuwa zan yi sonka shi zai zama sanadin ajalina, zan sanar da kai abin da baka sani ba ayau. Oga Habib ni ce nai silar auran ka da Hassana, na yi abubuwa da dama dan ganin ka zama miji agareni, amma ina abin bai yuwu ba". Farida shiru ta yi sabo da yadda taji numfashinta na fusgar mata, Farida sai da ta share wasu hawaye masu d'imi da ke zubar mata, sannan ta dafe gefan zuciyarta ta ci gaba da magana cikin kuka-kuka kamar haka, "Oga Habib ni ce sanadin haukarka, na yi haka ne ko zaka zama miji a wajena, amma da ya ke kai d'in ba rabo na bane, sai abin ya fad'a ma Hassana, mai makon karik'a yaddar da ni ni ka d'ai kamar yadda naso, sai ya zama mana da Hassana ka d'ai ka ke yadda, Inda tunanina ya bani, idan ya kasan ce dani ka d'ai ka ke yarda na san kowa zai yi tunanin had'a ni aure da kai, tom abin sai ya fad'a akan Hassana". Nan ma Farida shiru ta yi sannan ta ci gaba da cewa, "Oga Habib duk da Mommy ta had'a auranka da Hassana ban yi hak'uri ba nayi abubuwa da yawa ganin na raba auranka da Hassana, shima bai yuwu ba, na tura b'arayi akan su d'auke Hassana shima bai yuwu ba. Shi ne nayi tunanin fara aiki a Sanat ko zan ja hankalinka".kukan da ya k'wace ma Farida ne ya sa tai shiru, sai da tai kukanta ta gama sannan, ta ci gaba da cewa, nayi k'ok'ari sosai ganin na ta kurama Hassana". Farida kuma rik'e hannun Hassana ta yi d'ayan kuma ta dafe saitin zuciyar ta, da ta ke tunanin hannun Habib ne ta ci gaba da cewa, " Oga Habib kai da Hassana ku yafe min dan.....". Tarin da Farida ke yi ne, mai tattare da aman jini ya hana ta fad'in abin da ta ke so". Allah sarki Hassana da tausan Farida ya kamata kuka ta kama, dai-dai lokacin kuma Hajiya Murja ta shigo da likita". Wata doguwar Hajiyar zuciya Farida ta ja, daga nan tarin ya lafa. Likitan duba Farida ya yi, sannan ya kalli Hajiya Murja ya ce, "Hajiya Allah ya yi ma mata rasuwa!? Ihu d'aya Hajiya Murja ta yi ta yanke jiki ta fad'i". Ita kanta Hassana kuka ta fasa,cikin rud'ewa ta ke "Innalilahi'wa inna ilaihirraju'un! ". Habib rasa yadda zai yi da Hassana ya yi, ganin ta rud'e da yawa, ga kuma Hajiya Murja a sume". Habib waya ya ciro ya kira Hajiya Turai, tana d'agawa Habib ya sanar da ita mutuwar Farida yan zu haka suna asibitin. Ai Hajiya Turai bata gama saurara ba ta kashe wayar". Cikin minti goma Hajiya Turai ta iso asibitin, tana zuwa lokacin kuma dai-dai za atai da gawar Farida gida, haka aka tafi da gawar Farida gida, da Hajiya Murja keta rusa kuka tana kiran ta bani ta shiga uku, wa'iyazubiiya, Innalmaiyata layu'azibi bibika'ilhai, lallai mamaci ina masa azaba da kukan Wanda ya ke da rai. Allah ka ki ya ye mu kasa mu dace". Haka akai zana'idar Farida aka kaita gidan ta na gaskiya. Sai da aka gama komai sannan Habib ya d'auki Hajiya Turai da Hassana suka koma gidan Hajiya Turai ". Hassana da zazzab'i ke damunta tun acan daurewa ka wai ta ke, suna zuwa ta kwanta kan Three seater Falon Hajiya Turai, Habib kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Mommy Sanat fa bata ci komai ba".Hajiya Turai kallan Hassana ta yi, ta ce, "Daughter me zaki ci? "."Mommy tea ". Hajiya Turai Maimuna tasa ta had'ama Hassana tea ta kawo mata. Habib buga k'afar Hassana ya yi kad'an ya ce, "Tashi ki sha tea d'in ". Hassana tashi tai dama kuma yunwa ta ke ji, dan ma d'azu Habib ya kaita wani restaurant ta ci abinci. Hassana amsar tea d'in ta yi ahankaki-ahankali ta samu ta shanye tea d'in". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Habib ina son ka yafe ma Farida dan ta aikaita abubuwa masu girma gareka, ban yi niyyar sanar da kai ba, amma zan fad'a maka sabo da nai man mata yafiya da zan yi". Habib kallan Hajiya Turai ya yi ya ce, "Mommy duk abin da kike son sanar da ni Farida ta sanar da ni da kan ta, shine ma maganar ta ta k'arshe. Tabbas alokacin da take sanar da ni abin da tai min raina ya b'ace sosai, amma kuma bayan mutuwar ta sai naji tausan ta, na yafe mata Mommy Allah ya yafe mana baki d'aya ". 'Ameen". Hajiya Turai ta ce". Hajiya Turai ta shi ta yi ta nufi ciki ta watsa ruwa. Habib ko naganin Hajiya Turai ta tashi ya bubbuga Hassana ya ce, "Sanat tashi mu tafi kafin Mommy tazo please ". Hassana kafad'a ta mak'ema Habib ta ce, "Naki d'in, Habib tada Hassana ya yi zau ne, ya ce, "Sanat dan Allah kin san tun jiya Mommy ta so in dawo da ke, tom yan zu idan ta fito ta kangi Allah na san ba zata bari ba mu tafi". Hassana kwanciya ta yi kan kafad'ar Habib ta ce, " Ni kam yau ba zan bika ba". Habib da ke jin tsoran kar Hajiya Turai ta fito, tashi ya yi yana tada Hassana ya ce, "Sanat ki tashi mana, kar Mommy ta zo".Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Ni fa ba zan bika ba". Habib da fe kai ya yi, ya ce, "Sanat kizo muje ina son muyi maganar tafiyar ki garin ku ne". Hassana cikin jin dad'i ta kalli Habib ta ce, "Allah da gaske kake? ". Kai Habib ya d'aga ma Hassana. Hassana tashi tai suka tafi". Bayan su Hassana sun tafi ne Hajiya Turai ta fito falon tan bayar Habib shi mai zai ci. Amma abin mamaki Hajiya Turai bata ga kowa ba. Dariya Hajiya Turai ta yi, ta ce, "Allah sarki Habib wai guduwa ka yi da matar taka ba Sallama, in banda abin ka ai tun da naga Hassana ta kwaremin baya na hak'ura, Allah ya baku zaman lafiya". Hajiya Turai kiran Habib tai awaya, yana d'agawa ta ce, "Habib tafiya kuma babu sallama". Habib da ga can, sosa kai ya yi, ya ce, "Mommy na zaci kin kwanta ne, shine wai kar in tada ki". Hajiya Turai dai dariya kawai ta yi, ta kashe wayarta". Habib sai da suka biya ta Alheri suya ya sai masu gasassar kaza sannan suka tafi gida". Suna zuwa Habib ya kamo hannun Hassan ya ce, "zo ki wanka , mun yi bacci da wuri, yau kin gaji da yawa". "Uhm ni ban gaji ba, zan yi da kai na ma". Cewar Hassana ". Habib hannun Hassana ya kamo ya ce, "Haba 'yan matana, zan hutashshe ki ne, bazan kalli ko mai ". Habib haka ya shigar da Hassana toilet d'in ya taya ta tai wankan, tun tana nok'ewa har ta hak'ura Habib ya jajjagulata ahaka dai aka yi wankan aka gama". Hassana na fitowa ta kalli Habib ta ce, "Oga Habib sai da safe".Hassana ta juya ta nufi side d'in ta. Habib bai tan ka ma Hassana ba, rabuwa ya yi da ita sai da ya yi sallar issha'i ya gama duk abin da zai yi sannan ya nufi side d'in Hassana. Hassana ko lokacin har ta kwanta,ta fara bacci. Habib bai tada Hassana ba gefanta ya je ya kwanta ya rungumota ta gefe gudin karta farka". Hassana ko sai asuba da Habib ya ta data yin Sallah sanan ta san d'akinta ya kwana, Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib yau she ka shigo". "Kina can kina bacci". Habib ya ba Hassana amsa". Hassana ko bayan ta yi sallah batare da Habib ya sani ba, ta fita ta shiga kitchen ta dama mai kunun gyad'a. Lokacin da Hassana ta shiga bedroom d'in ta bata iske Habib, wanka ta shiga, tana fitowa ta zauna ta yi shafa, yau Hassana har da su safa powder da lipstick, sannan ta d'akko cikin atamfofin da Hajiya Turai ta d'inka mata tasa wata,ta d'au aribian perfume ta feshe jikinta da shi, Hassana na fitowa da Cup d'in kunun Habib ta ci karo da Habib ya fito. Kallan kallo aka tsaya yi, Habib ringumo Hassana ya yi ya had'e bakin sa da nata yana tsotsa sannan ya rad'a mata cikin kunnan ta ahankali ya ce, "Nayi missing d'in sweet lips d'inki, anya ko zan iya fita". Hassana murmushi ta yi ta ce, "Uhm Oga Habib ina zaka da wuri haka? ". "Zan je Company ne, yan zu zan dawo". Habib ya ba Hassana amsa ". Hassana hannun Habib ta kama ta ce, "Oga Habib na dama ma kunu, kasha tukun, nima zan rakaka". Habib jama ya yi Hassana ta mik'a mai kunun ya amsa yana sha, ya kai Cup d'in kunun bakin Hassana. Hassana kauda kai tayi ta ce, "Nasha ".Habib sha ya yi yabar Hassana dan ya lura ita kunun bai da meta ba. Hassana kallan Habib ta yi, ta ce, "Oga Habib manager ya dawo aiki? ". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "Yauwa kin tuna min, bai dawo ba, na ce sai kin yarda". Hassana turo baki ta yi, ta ce, "Ni fa ban wani ji haushin manager , haushin Billy naji ai ita ce tasa ya maran". Habib da bai son Hassana ta je Sanat, kallan ta ya yi ya ce, "Sanat ki bari ba yau ba zaki je". Hassana mak'ema Habib kafad'a ta yi, ta ce, "Ni dai yau nake son zuwa, dan Allah, akwai abin da zan yi acan". Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "Me zaki yi acan? ". "Mu je zaka gani". Habib ba dan yaso ba ya tafi da Hassana Sanat Yoghurt". Hasana bayan sun je, Habib ya nufi Office d'in shi, zai shiga Hassana ta yi saurin kamo hannun Habib ta ce, "Muje karaka ni in ga ya gurin ya yi, ka ga na rabu da zuwa ". Habib bin Hassana ya yi dan shima ya rabu da duba cikin Company yaga yadda ya yi. Duk in da su kai staff d'in gurin kallan su ka wai ake, inda duk in aka gaida Habib sai an gaida Hassana, Hassana da fara'arta ta ke amsawa.Dan yan zu kowa ya san matsayin Hasssana a Sanat. Billy tun daga nesa ta hango Hassana da Habib na zuwa. Hassana dai-dai saitin Billy ta tsaya ta kalli Habib ta ce, " Uhm Sweetheart yama sunan wannan? ". Hassana ta fad'i maganar tana nuna Billy. Habib ko sai da ya rintse ido dan jin dad'in su nan da Hassana ta kira shi da shi. Habib batare da tunanin komai ba, dan shi ya za ci Hassana da gaske ne ta manta sunan Billy, ya ce, "Billy ". Hassana kallan Billy ta yi, da fara'arta ta ce, "Sannu da aiki Billy gaskiya kina k'ok'ari, Ina manager fa? ". Billy bacin agaban Habib ne tabbas da babu abin zai sa taba Hassana amsa, amma babu yadda za tai dole ta ba Hassana amsa". Billy d'agowa ta yi tana kalli Hassana ta ce, "Bai zo aiki ba". Hassana cikin sakin fuska ta kuma cewa, " Lafiya bai zo aiki ba". Billy kallan Habib ta yi taga hankalin shi yana kan waya, ta harari Hassana ta ce, " an dakar da shine". "Ok, ki kira shi awaya yazo yan zu, idan ya zo ku zo tare". Hassana na fad'in haka ta kamo hannun Habib ta ce, "Wayyo Sweetheart wannan tafiyar da nai har nagaji Allah, mu koma Office d'in ka". Habib kama hannun Hassana ya yi suka koma ya ce, "Dama ke kika matsa sai kin biyoni ai". Billy kamar zuciyarta zata fashe haka taji. Da harara tabi bayan Hassana da shi, sannan ta tura ma manager text massage akan yazo yan zu". Hassana ko suna zuwa ta zauna kan chair d'in da Habib ya ke zama ta ce, "Oga Habib yau zan futassheka zan yi duk aikin da za kai". Murmushi Habib ya yi, ya ce, "Wane ke yarinya". Habib suna nan zau ne suna fira da Hassana Manager da Billy su kai nocking k'ofar. Habib izinin shiga ya basu". Manager cikin girmama Habib kamar yadda ya saba ya gaida shi. Habib babu yabo babu fallasa ya amsa ma manager. Manager kallan Hassana ya yi, ya ce, "Barka da hutawa ranki shi dad'e". Hassana ma ta b'angaran ta babu ya bo ba sallasa ta amsa ma manager ". Billy ko sosai taji ta kaicin gaida Hassanar da manager ya yi. Manager mai da kallan shi ga Habib ya yi, ya ce, "M.D, ance kana kirana? ". Habib nuna Hassana ya yi, ya ce, "Ga mai nai manka nan". Manager mai da kallan shi ga Hassana ya yi ya na jiran abin da zata ce". Hassana kallan Billy ta yi ta ce, "Billy kawo min Yoghurt mai sanyi". Billy kamar ta ce bazata ba amma kuma babu damar haka ga Habib kusa, hakan yasa kamar zata sa ihu ta fita ta je kawo ma Hassana". Hassana kuma bata cema manager ko mai ba har sai da Billy ta dawo sannan ta kalli manager ta ce, "manager ka dawo kaci gaba da aikin ka, babu komai, ko mai ya wuce"."Godiya na ke ranki shi dad'e ". Cewar manager ". Hassana kallan Billy ta yi da ke tsaye ta ce, "Ke fa lafiya? ". Billy cikin daurewa da yadda ta ke ji ta kalli Hassana ta ce, "ke ki ka ce in zo". Hassana kallanta ta yi sannan ta ce, "Babu da muwa zaki iya tafiya ki ci gaba da aikin ki". Billy fita ta yi tana mai jin zafin Hassana, sai dai ta san Hassana tai mata nisa nesa ba kusa ba, kuma tabbas yan zu Hassana duk wanda ta kora aiki ya koru". Billy Office d'in ta ta koma tana kuka, Billy na nan tana kuka ta ga Manager ya shigo Office d'in. Manager cikin damuwa ya k'arasa gun Billy, manager kallan Billy ya yi ya ce, "Nasan abin da ya saki kuka, Billy hak'ik'a na soki kuma har yan zu ina son ki, tom amma wannan ita ce magana ta k'arshe da ke, ya maganar aure na da ke? ". Billy d'agowa ta yi tana kallan Manager ta ce, " Nayarda duk lokacin da ka shirya, zaka iya zuwa wajan kawuna". Manager cikin jin dad'i ya ce ma Billy, "zan je gobe". Billy kai ta d'aga ma Manager ". Hassana ko sai 4:00Pm suka bar Sanat ita da Habib..... . ✍️ Idan kin karanta daure ki Comment sister 🤝 Share & Comment please 🙏. 📚 OGA HABIB📚 💫💫 *🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️* https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl _*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_ *💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫* TSARAWA DA RUBUTAWA FADILA SANI BAKORI (Faddy Baby). 🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚 Albishirin ku masu bibiyar littafin Fadila Sani Bakori. Yau gani da daddad'an albishir gare ku, insha Allah daga na kammala Oga Habib, zan nisha d'an tar da ku da sabon littafina wanda na baje basirata acikin shi. Anyi amfani da salo na birgewa acikin littafin. Labari ne wanda ya ke d'auke da madarar Soyayya, mai d'auke da ban al'ajabi. Inda ta wani b'angaran labarin ke d'auke da ban tausayi mai tsayawa a zuciyar makaranci. Duk yadda zan sanar daku ba zaku fahimta ba, ke dai karki bari abaki labari. Zaki samu littafin akan farashi mai sauk'i da rahusa👌👌. Summary. Abba tin ina yaro kana yawan fad'a min, duk abinda ya yi tsanani yana tare da sauk'i. Shin ni sai yau she sauk'i na zai zo! ?. Abba me yasa muta ne basa ganina, maganata kawai su ke ji!?.Abba me yasa muke rayuwa a daji mai makon cikin gari cikin mutane !?. Abba kana gani Husna zata aure ni, duk da halin da nake ci!?. Abba me yasa Husna ta kasan ce ita kad'ai ke ganina!?. Abba kace kai ba Mahaifinsa bane, tom waye Mahaifina, kuma me yasa muke rayuwa a jeji!?, Sannan me yasa Abdussalam kad'ai ke zuwa gurin mu, sannan Abba waye Abdussalam ?. Haidar duk banda amso shin tambayoyin ka, nima ban san kai na ba Haidar, ban san waye ni ba, bare kuma kai!. Labari mai tab'a zuciyar mai karatu. Paid book Akan farashi mai sauk'i da rahusa 👌👌 VIP group 300 Only👌 , normal kuma 200 ne, zaki yi transfer ta account d'in nan 2111619333. Account name Fadila Sani. Bank Name Zenith bank. Dan nai man k'arin bayani zaki iya managa ta wannan Number👉 08063830828 Shafi na 92&93. Hassana ko sai 4:00 PM suka bar Sanat ita da Habib. Suna komawa gida Hassana ta shiga kitchen tai jolop rice. Habib na zaune Falon Hassana, Hassana ta fi ta nifo wajan Habib, Hassana zama ta yi, gefan Habib tana kallan shi, ta ce, "Oga Habib Yau ban ma kunu ba, jolop rice nai ma, zaka ci? ". Kai Habib ya girgiza ma Hassana alamun ba zai ci ba. Hassana turo baki ta yi, ta ce, "Ai ko yau gidan Mommy zan tafi in dai baka ci ba".Murmushi Habib ya yi yana sa hannu ya shafo lips d'in Hassana da ta turo ya ce, "Sorry Sanat mai da lips d'in ki, kar ya yi tsini, yafi dad'in Kiss ahaka". Hassana kuma turo lips d'in ta ta yi, Habib kai baki ya yi dai-dai kan lips d'in ta, ya d'an cizi lips d'in ka d'an, ya ce, "Ki mai da su karsu yi tsini, suna d'aya daga cikin abin da ke min kyau". Hassana sake turo bakin ta yi, ta ce, "Uhm dama du kana baki d'aya lips d'ina ne ka wai ya ke da kyau? ". Hassana ta fad'i maganar kamar za tai kuka. Habib kai ya d'aga ma Hassana alamun haka ne". Hassana ta shi ta yi da sauri zata tafi, ta ce, "Aiko shima kabar ganin shi daga yau, gidan Mommy ma zan koma, inda duka na lips d'ina kad'ai kema kyau ". Habib da sauri ya jawo Hassana ya zaunar da ita kan cinyar shi suna fuskantar juna, ya ce, "Sanat ko mai naki mai kyau ne". "Uhm". Hassana ta ce, ta ce, "tom Dame-dame nau ke ma kyau? ". Habib hannu yasa yana shafa lisp d'in Hassana dan shi sosai shape d'in lips d'inta ke mai kyau, ya ce, "lips d'in ki, eyeliner, Breast d'in ki girman su dai-da, hips d'inki gir mansu ya yi min dai-dai, tsayin ki dai-dai, Uwa uba Babyna lips d'inki yan kar kiss ne, ke fa mai zafi ce, na yi ma missing d'in ki d'an bari in.... ". Hassana ta shi tai zata gudu Habib ya yi sauri ya rik'ota, ya had'e bakinsu guri guda. Ganin abin ya yi nisa na tafi zuwa dubo ma Hassana girkinta gudin karya k'one". lokacin da na dawo a toilet najiyo Su Hassana, suna wanka. Habib da kan shi ya yi ma Hassana shafa sannan ya d'akko mata wasu kaya marasa nauyi tasa. Hassana bayan Habib ya gama shiryata ita ma tai maka mai ta yi ya shirya, sannan ta zibo masu abinci suka ci ". B"angaran Manager ko har yaje gidan su Billy nai man auranta an bashi, dan yanzu Billy ta watsar da komai ta ringumu Manager hannu biyu, gudin kar tai biyu babu. Wata Uku aka tsaida auran Billy da Manager ". akwana atashi babu wuya awajan Allah, Yau saura sati d'aya bikin manager da Billy". B'angaran su Hassana ko fad'in irin soyyayar da suke, ina sai dai wanda ya gani, ko ya hasaso,Hassana zaman Soyayya sosai suke da Habib in da kowa ke k'ok'arin faranta ma d'an uwan sa. Hassana ta sake haske sosai fatar jikinta ta yi smooth ta ti clear, sai dai kwana biyun nan Hassana sun d'an samu matsala da Habib, in da har Hassan ta d'auki fushi da Habib, inda shi ma kuma Habib ya ke ganin dan yana nuna damuwar shi da Hassana ne ta ke mai haka, Shi yasa ya daure zuciyar shi ya fita lamuranta". Yau kwana biyu kenan, gaisuwa kad'ai ke had'a Hassana da Habib. Idan abin ya damu dukan su. Hassana da ke zaune ta rasa tudun dafawa, tunanin kiran Hajiya Turai ta yi, tana kiranta ko kira d'aya ta d'aga. Hajiya Turai na d'agawa Hassana ta sa mata kuka, Hajiya Turai cikin rud'ewa ta ke tambayar Hassana mai ya faru. Hassana da kyar ta samu ta tsaida kukan ta ta fara yi ma Hajiya Turai ba yani kamar haka, "Mommy Oga Habib ya dad'e yana min alk'awarin zai kai ne garinmu amma yak'i, kullum nai mai managa sai ya ce in bari sai sati mai zuwa, kuma shine yan zu ya ke fushi dani! ". Hajiya Turai lallan shi Hassana ta yi sosai sannan ta ce, "Ki hak'uri ki bar kukan daughter bari in kira shi ". Hajiya Turai na kashe wayar ta kira Habib, lokacin Habib na zaune Office d'in shi yana aiki, kiran Hajiya Turai ya shigo wayar shi". Habib picking call d'in ya yi, bayan sun gaisa da Hajiya Turai ne, Hajiya Turai ta ce, "Habib kasan abin da kai bai da ce ba ko?, yan zu nakira daughter mu gaisa naji voice d'inta alamun tana cikin damuwa. Haba Habib yan zu ni bannan bare daughter ko gurina tazo taji sanyin, kai kad'ai ke gareta amma kuma kai har ka bar ta cikin damuwa, me yasa ne haka Habib? ". Habib cikin damuwa ya fara magana kamar haka, "Tom Mommy ni ban san ya zan mata ba, ta matsa ita tana son zuwa garinsu, ni ba wai nak'i ma ta ba ne, in da ko ni ban da lokaci zan iya sa Bilya ya kaita, tom amma bata da lafiya kwanannan, kullum da zazzab'in dare ta ke bacci, nakira litama ya dubata ashe ciki ne". Habib ya fad'i maganar yana sosa kai sai kace Hajiya Turai na kusa da shi". Allah sarki Hajiya Turai gaba d'aya wutarta d'aukewa ta yi na wani lokaci, sannan ta ce, "Habib amma shine baka kira kai min albishir ba, kuma waya cema ana barin bai ciki k'arami irin haka cikin damuwa!? ". "Wallahi Mommy ita ke fushi dani amma ni bana fushi da ita, na bata hak'uri ta bari sai ta haihu amma tak'i ji, tom ya zan mata? ". Habib ya fad'i maganar cikin damuwa ". Shiru Hajiya Turai ta yi sannan ta ce, "Habib inda ta sa ranta akan zuwa gidan ka yi hak'uri ka kaita sai ta yi sati ka koma ka d'akko ta, in ba haka ba za fa a iya rasa cikin jikinta, bafa aso mai ciki tana zama da damuwa ko mai zai iya faruwa da ita, nima zan dawo Next week insha Allah ". "Tom Mommy Allah ya kawo ki lafiya". Habib na fad'in haka ya kashe wayar ". Habib tashi ya yi ya rufe Office d'in shi ya nufi gida. Kwance ya iske Hassana akan Three seater tana zibba hawaye. Habib zama ya yi kusa da Hassana yana ka mota ya zaunar da ita kan cinyar shi, Habib handkerchief d'in shi yasa ya goge ma Hassana hawayanta, sannan ya ce, "Haba Sanat ni fa bawai na hanaki tafiya bane dan wani abu, kawai dan naga baki da lafiya ne, dan Allah ki yi hak'uri ki goge hawayanki Allah alk'awari na d'auka daga kin haihu zan kai ki". Hassana kallan Habibb ta yi hawaye ya na mai ci gaba da zubar mata, ta ce, "Ni fa ba wai nak'i bane, ni bana son basu san nayi aure ba kawai sai dai in je musu da yaro, sai dai in haka ne azubar da cikin dan ni ba zan iya zuwa musu da yaro ba". Habib shiru ya yi yana kallan Hassana, sannan ya ce, "Kin yarda in kaiki gobe amma kwana d'aya zaki mu dawo? ". "Hassana kai ta d'aga ma Habib ta ce mai ta yarda". Washe gari da wuri Habib suka yi shirin tafiya Kano, kasan cewar da wuri suka fita hakan yasa k'arfe 1:00Pm suka sauka, inda Hassana ita ke nuna ma Habib hanya har izuwa local government d'in da suke akano". Hassana wani irin sanyi ta ke jin yana ratsata lokacin da suka iso k'ofar gidansu, sai dai ta wani b'angaran tana daurewa ne kawai kar tai kuka ta tada ma Habib hankali, amma idan ta tuna zata gidan su babu Mahaifinta mai sonta, ji tai kamar tai ihu, dan sai mutuwar Mahaifinta ta dawo mata farko. Duk yadda Hassana ke danne kukanta abin ya ci tura, sai ta ta sa kuka, Habib da ya yi parking a lalataccan gidan da Hassana ta nuna mai ta ce nasu ne, jira ya ke ta ce su sauka, amma sai yaji kukanta, Habib cikin damuwa ya kalli Hassana ya ce, "Sanat ko mai narayuwa d'an hak'uri ne, dan Allah ki yi hak'uri ki goge hawayanki, in ba so ki ke ki sa ni damuwa ba ". Hassana da sauri ta share hawayan ta , ta ce, "Natuna da Mahaifina ne mai sona , mai tausaina, sanadin rashin shi yasa na gudu na bar ma haifata". Habib lallashin Hassana ya yi sosai sannan ya ce, "ki shiga ciki mana, ko kin manta gidan ne? ". "A'a nan ne". Cewar Hassana ". Hassana fita ta yi daga Motar ta nufi cikin gidan. Zaune Hassana ta iske Mahaifiyar Usaina 'yar uwarta, da Usaina, Hassana sallama ta yi tana mai k'arasawa inda suke". Dukan su da kallo suka bi Hassana, dan basu gane ta ba. Hassana ko da fara'arta ta k'arasa inda suke ta ce, "Umma bugu gane ni ba ne, ?, yan zu kema Usaina bi ki gane ni ba? ". Usaina da taji Muryar Hassana zin bur tai ta mik'e tana kallan Hassana, ta ruga ta rungume Hassana ta ce, "Umma Wallahi Hassana ce!, Hassana ce ta dawo gare mu Umma!!! ". Usaina ta fad'i maganar da k'arfi tana fad'awa jikin Hassana". Hassana ma rungume Usaina ta yi tana kuka, Allah sarki Usaina ma kukan tasa, sai da su kai sukan su sannan su kai shiru, ita dai Umma kallansu kawai ta ke tana share hawayanta ita ma ". Usaina da katawa ta yi da kukan ta jawo hannun Hassana suka zauna. Umma cikin mamaki ta kuma kallan Hassana ta ce, "Hassana ke ce?, dama kina raye Hassana?, ina kika shiga ke ko?, Hassana kin tafi kin bar mu cikin damuwa ". Umma ta fad'i maganar tana share hawayan ta. Hassana ma goge nata hawayan ta yi, sannan ta ce, "Umma ku yafe min na gudu na barku, dan Allah Umma ki yafe min? ". "Hassana ai dole ki gudu, mun ta kura ma rayuwarki mun rabaki da abin da kike so, bakin cikin haka ya kashe mahaifinku, Hassana dole ki gudu ki bar mu, mu zamu rok'e ki yafiya, ki yafe mana Hassana, amma ke biki mana ko mai ba". Umma kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana inji dai ba karuwanci ki ka je ba? ". Hassana kuma goge hawanta ta yi sannan ta ce, "Umma banyi karuwanci ba, na bar nan da wata uku nayi aure, yan zu haka muna tare da wanda na aura". Umma bud'e baki ta yi tana kallan Hassana, ta ce, aure Hassana, amma naji dad'i da ba yawan banza ki ka yi ba, je ki shigo dashi, ya zaki bar shi waje ". Hassana zuwa ta yi suka shigo da Habib. Umma sosai ta cika da al'ajabi da ganin Mijin da Hassana ta aura, lallai wanan shine ake kira da kyakkyawar k'addara". Dama tun kafin Habib ya shigo an mai shim fid'a, Habib zama ya yi, sannan ya gaida Umma, suka gaisa da Usaina". Umma kallan Habib ta yi, ta ce, "bawan Allah taya kuka had'u da Hassana? ". Habib zayyane ma Umma ya yi kaf yadda suka had'u da Hassana, da yadda akai auran su da Hassana". Umma sosai ta yi murna, dan ta yi nadama sosai bayan tafiyar Hassana. Bayan Habib ya gama ba Umma labari ne, Umma ta kalli Habib ta ce, "Na san Hassana ta baka labarin halin da muka sata, wato Hassana bayan auran Kabir da Usaina, ina jin basu zaman wata uku cikakku ba, sai fad'a wulak'ancin yau da ban na gobe da ban. Hassana nayi nadamar rabaki da Kabir, amma kuma na godema Allah da na rabaki da Kabir in da sanadin haka ne yasa kika gudu, har Allah ya had'aki da bawan Allah nan, wato Hassana yan zu haka maganar nan da nake miki Usaina ta dad'e agida, da ta gaji da wulak'an ci da Kabir ya ke mata ta dawo gida, har yan zu ko zuwa bai yi ba, k'arshe ma munji labarin ya yi aure, jiya jiyan nan ya aiko mata da takardar ta". Hassana sosai ta tausayama 'yar'uwarta halin da ta shiga". Sun dad'e suna hira sannan Habib ya ne mi Masallaci ya tafi yin sallah. Bayan Habib ya fita ne, Umma ta kalli Hassana ta ce, "Hassana kinga gidan ko girki ba muyi ba, me zaku ci Usaina ta tashi ta siyo miku? ". "A'a Umma Allah bana jin yunwa sai da muka ci abin ci a hanya ". Habib na dawowa ya d'auki Hassana ya suka nufi dan gin mamarta da babanta, duk inda suka je ba wani dad'ewa suke ba, dama kuma ba wani damuwa da Hassanar su kai ba, garama yan zu da suka ga waye mijinta tom sun nuna damuwar su da ita". Da daddare Habib cikin gari ya shiga ya siyo abin da zasu ci. D'akin Mahaifinsu Hassana aka gyarama Habib ya kwanta, ya so ya nemi hotel ya kwana Hassana ta hana shi". Washe gari : Duk in da ya kamata Hassana su je, sun je, k'arfe 10:00Am Habib ya kalli Hassana ya ce, "Sanat ki shirya yan zu zamu wuce? ". Hassana dafa Habib ta yi kamar za tai kuka ta ce, "Dan Allah Oga Habib ka bari sai gobe mana". Habib da sosai ya daurema ya yi kwana d'a yan da ya yi, kallan Hassana ya yi, ya ce, " Dama nayi tunanin mu tafi da su Umma ne da Usaina suga in da kike, Allah basshi sai su zauna wajan Mommy har uzuwa lokacin da zaki haihu". Hassana da itama ta yi tunanin hakan, amma kuma ta kasa fad'ama Habib, Hassana cikin jin dad'i ta rungume Habib ta ce, "Sweetheart kamar ka shiga zuciyata nima nayi tunanin haka". Habib kallan Hassana ya yi, ya ce, "tom muje asanar da su sai su shirya mu tai da wuri". Habib zaune gaban Umma, ya ce, "Umma dama cewa nayi keda Usaina ko zaku shirya mu tafi tare kuga inda Hassana ta ke". Allah sarki itama dama ta yi tunanin hakan, hakan yasa batare da ja ba tace, "Tom ai shikenan sai mu shirya ". Cikin k'ank'anin lokaci su Umma suka shirya, in da Hassana ta hana Usaina d'aukar kayan sawa ko d'aya ta ce ta bari ta rik'a sa nata, haka ko akai Usaina ban da kayan jikinta bata d'au ko d'aya ba". K'arfe Biyar na yamma suka sauka. Wato su Umma mutuwar tsaye su kayi lokacin da suka ga gidan da Habib ya shigar da su". Haka suka shiga Falon Hassana,Habib kuma ya shige ciki. Usaina da ta kasa daurewa kallan Hassana ta yi, ta ce, "Hassana dama a irin gidan nan kike rayuwa?, gaskiya Hassana kin ji dad'i, kin ga ni son zuciya ya ja min na zama k'aramar bazawara". "Kibar tuna abin da ya wuce Usaina haka Allah ya k'addara". Cewar Hassana". Habib hajiyar sa ya kira ya ce ta turomai Maimuna tai masu girki dan Hassana bata iyawa ta gaji. Aiko haka akai Maimuna ce ta zo tai masu girki. Suna nan zaune suna hira Maimuna ta zo ta Sanar da Hassana ta gama. Hassana kallan Umma ta yi, ta ce, "Umma muje muci abinci". Haka suka ci abincin su suka gama. Koda lokacin kwanciya ya yi Hassana side d'in ta ta bar masu ta tafi wajan Habib ta kwana". Yau kwana nan su Umma uku kenan da zuwa. Habib ya zo zai gaida Umma, bayan sun gama gaisawa Umma ta kallai ta ce, "Yau she zamu tafi ne? ". Habib cikin girmama Umma dan shi ya na mata Kallan mahaifiyar Hassana ne, inda ita ta shayar da Hassana, ya ce, "Umma dama yau Mahaifiyata zata dawo, idan ta dawo zaki koma wajan ta da zama ne, idan Hassana ta haihu sai ku tafi". Umma k'in yarda da haka tai da kyar dai Habib ya samu ta yarda, dama Umma tana ma Hassana kallan kamar mai ciki, ashe ko haka ne". Hajiya Turai na dawowa Habib ya d'auki Umma da su Hassana ma baki d'aya suka je. Wajan dawowa ne suka dawo suka bar Umma, inda suka dawo da Usaina, dan Hassana ta ce bata yarda ba sai dai Usaina ta dawo wajanta". Billy ko tare da Manager suka zo har gidan Habib kawo ma Hassana invitation na biki. Hassana sosai ta yi mamakin ganin Billy amma kuma sai ta wuske, bayan manager ya ba Hassana Invitation card d'in, ya ce, "Madam dan Allah karfa kik'i zuwa". Hassana murmushi ta yi, ta ce, "insha Allah zan zo ".Billy kuma cikin kunya ta ce, "Dan Allah amaryar Oga Habib duk abin da ya faru ki yi hak'uri ki yafe min, Wallahi har da zigar Farida abubuwa da dama da nai miki". Hassana cikin nuna ba komai ta ce, "laa ni har nama manta karki ji koma Babu komai Wallahi". Billy Sallama su kaima Hassana suka tafi". Akwana atashi babu wuya awajan Allah cikin Hassana ya shiga watan haihu, amma cikin babu wani girman kirki. Yau tunda Hassana ta tashi ta ke jin ciwo ka d'an -kad'an tun tana daurewa har tasa Usaina ta kira mata Hajiya Turai". Hajiya Turai ko najin kira wai Hassana bata da lafiya, suka tafi ita da Umma in sa suka biya ta wata private hospital suka tafi da wata nursing". Cikin k'ank'anin lokaci Allah ya sauki Hassana ya bata yarinyar mace. Duk abin da ake Habib bai sani ba, har sai da Hassana ta haihu aka gyarata aka gyara jaririyar, sannan Hajiya Turai ta kira shi, yana d'agawa ta ce, "Habib gani agidan ka kazo yan zu, zamu yi magana". Habib ko batare da tunanin ko mai ba, ya taho, yana zuwa Hajiya Turai ta tare da Baby a hannun ta, ta mik'a Habib, Habib ko kamar sakare ya amshi Baby yana kallanta yana kallan Hajiya Turai ya ce, "Mommy dan Allah ki min bayani ban gane ba, ina kika samu Baby? ". Hajiya Turai kallan Habib ta yi, ta ce, "Nima ban santa ba". Habib da tunanin shi ya bashi Babyn shi ce, barin Hajiya Turai ya yi ya nufi bedroom d'in Hassana ". Habib zau ne ya iske Hassana tana shan tea, ga Usaina kusa da ita. Habib kallan Usaina ya yi ya ce, "Usaina Mun samu Baby kenan? ". Usaina dariya ta yi, ta ce, Aikam dai Na samu Baby". Habib zama ya yi kusa da Hassana ya na kallanta ya ce, "Sanu ". Hassana turo baki ta yi ta ce, "ka yi lattin zuwa". Habib murmushi ya yi ya ce, "Ban sani na Wallahi Mommy ce ta kirani wai za muyi magana, ashe Baby na samu Mommy ta b'oye min". Hassana Murmushi ta yi sannan ta lek'a tana kallan fuskar Baby'n. Dan sai yan zu taga yarinyar". Kwana atashi babu wuya yau kwana nan Hassana hud'u kenan da haihuwa. Billy ko tuni an amarce dan har tazo Barka, duk masu aiki Sanat Yoghurt babu wanda bai zo barka ba". Hassana tana zaune fitowarta daga wanka kenan, Umma ce ke mata wanka. Hassana na nan zaune tana ba yarinyar mama Habib ya shigo. Habib zama ya yi yana amsar Yarinyar, kuka yarinyar ta yi jin ancire bakinta Maman. Habib mai da ta ya yi yana zare ido, ya ce"ki ce Baby'n ci gareta kamar Mommy'n ta". Hassana harara Habib ta yi, sannan ta mik'a mai yarinyar. Habib kallan Hassana ya yi ya ce, "Sanat dama cewa nayi ina son in sa ma Baby sunan Farida, amma kuma ban san yadda zaki d'auki abin ba". Hassana da ita burinta asama yarinyar sunan mamanta shiru ta yi, bata ce komai ba, Habib jin tayi shiru yasan hakan bai mata dad'i ba, hakan yasa ya ce, "Kin yi shiru Sanat? ". "Kasa mata". Hassana ta ba Habib amsa". Habib tashi ya yi, ya bar Hassana nan". Akwana atashi babu wuya yau ne suna. Duk su Hajiya Turai babu wanda ya san sunan da Habib ya sama yarinyar, kuma Habib ya hana su Bilya su gad'a dan sai da ya jama Bilya ma kunne ya ce, "Saura ka fad'i ma Usaina, dan yanzu Usaina da Bilya soyayya ake sosai dan babu wanda bai sani ba, har anyi ko mai ma, yan zu haka k'arshen watan nan ne bikin, Umma ko Habib ya bata side d'in shi na ki gidan Hajiya Turai ya ce taci gaba da zama anan. Hassana na haihuwa Umma da kanta taje kano ta fad'a ma 'Yan'uwan Hassana, hakan yasa yau gidan yake cike, dan duk kusan sun zo sunan". Hassana ko dama tasan Farida Habib zai sa hakan yasa bata matsu da ta ji ba. Su Hajiya Turai na zaune har da Hassana Habib ya shigo. Hajiya Turai harara shi ta yi ta ce, "shine ka hana kowa ya fad'i sunan Baby ko, tom kai da kake son fad'a da kanka ai sai ka fad'a d'in". Habib kallan Hajiya Turai ya yi, ya ce, "Mommy nasa ma Baby Hassana, Saboda dalili uku, na farko saboda sunan late Hassana Sister na, na biyu sabo da sunan Company'na, na uku Sabo da Sanat". Habib ya nuna Hassana da ke gefan Hajiya Turai". Hajiya Turai cikin jin dad'in sunan da Habib ya sa ma Baby, ta ce, "Habib ka sama Baby nan sunan da nima shi nake buri in ce kasa". "Mommy na san burinki kenan shi yasa banyi tunanin shawara dake ba, nasan kema shine zab'in ki". Cewar Habib". Hajiya Turai cikin jin dad'i ta d'aga hannunta sama ta ce, "Ya Allah ka albarkaci auran Habib da Hassana, Allah ka raya masu Hassana ka k'aro mu zuri'a masu albarka, Ya Allah ka k'aro mai bud'i mai yawa mai albarka, Ya Allah ka albarkaci Company shi SANAT YOGHURT". Dukan su da "Ameen ". suka amsa. Hajiya Turai wayarta ta ciro tai ta masu pics kala-kala, tun Umma najin kunya har ta daure ta tsaya itama aka ci gaba da d'auka da ita. Hajiya Turai Habib da Hassana da Baby ta shiga tsakiyar su ta sa Usaina ta d'auke su✍️. ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!! Ya Allah nagode maka da kaban iko na gama Oga Habib lafiya. Ya Allah kuraran da ke cikin wannan littafi ya hurarrahman ya Allah ka yafe min ba dan halina ba, dan alfarmar anbi Muhammad (S. A. W). Masu Comment's akan Oga Habib na gani kuma Wallahi naji dad'i, nagode sosai Allah yabar zuminci. Comment d'in ku ke k'aramin k'warin gwiywa. Kuna da yawa lissafo sunan ku ba zai yuwu ba, amma Wallahi duk wanda ya yi nagani nagode na kuma ji dad'i sosa. Masu taya ni sharing na Oga Habib, nagani na kuma godee, kuma kuna da yawa sunan ku ba zai lissafu ba, amma ku sani nasan kunyi nakuma ji dad'i sosai Allah, nagode sosai Allah ya bar zuminci. Sai mun had'u asabon book d'ina mai sun RAYUWAR HAIDAR. Ku nuna min k'auna ta hanyar shiyan RAYUWAR HAIDAR. Dan Allah duk wanda na fad'ama rai ta hanyar rubuta Oga Habib ya yafe min. na yafe ma kowa. Ina alfahari da ku masoyana aduk inda kuke, Allah kairin Allah ya isa GAREKU ✍️ . Fadila Sani Bakori ce 08063830828