[5/23, 15:04] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN*🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* ~Marubuciyar~ Komai mukaddari ne K'addarar soyayya ta Najmat Abiy And now *NI DA YAYA ARMAN* 📚 *JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION* 📚 *GODIYA* godiya ta tabbata ga Allah (S W T) tsira da Amincin Allah su tabbata ga Annabi Muhammad(S A W) da ahalinsa da sahabbansa ina Godiya Ga Allah (SWT) da ya k'ara bani ikon fara rubuta littafin nan yanda na farashi lafiya ya sa na gama lafiya cikin yarda da amincewarshi. *GARGAD’i* ban yarda wata ko wani ba su juyamun Littafi ta kowace sigaba muddin Hakan ta faru zan d'auki mummunan mataki. Littafin nan NI DA YAYA ARMAN k'irk'irarren Labari ne Idan yazo daidai ko yayi shige da labarinki kiyi hakuri arashi ne. *DEDICATED TO SISTER LEMART L SADEQ* Y'ar uwa,Masoyiyata,Aminiya,Besty love Bazan tab'a iya misalta soyayyarki a cikin zuciyata ba Allah ya barmu tare my y'ar uwa Rabin jiki littafin nan gabaki d'ayanshi sadaukarwace gareki ki kiyi yanda kikeso dashi 💃💃💃💃 23/May/2022 بسم الله الرحمن الر حىم *BOOK ONE*📔 🅿️.........1&2 ```Kano state``` ~Nasarawa Quaters~ Tsit kakejin unguwar tayi shiru kasancewar ranar da ake gallawa kowa ya na gidajensu Unguwace ta y'an gayu yawaicin masu kudi sunfi zama unguwar gidaje ne na alfarma Chan na Hango wani tafkeken gida mai matuk'ar kyau da tsaruwa da kuma girma na ban mamaki Dan gate din gidan kanshi zai d'auki sama da mota sha biyar gidan gida biyu ne na kusa dashi Shima yana da kyau daidai misali Shima da gate d'inshi amma kuma akwai kofa wacce daga cikin gidan zaka bulla d'ayan gidan ba tare da kasha wahalar zagayawa ba cikin gidan ya hadu komai cikin tsari. Zaune take ta na guga ta na yi ta na Jan tsaki Inna dake zaune ta na taunar goro ta ce "da yake uban wani ya sanyaki gugar da zaki zauna tun d'azu kina yiwa mutane tsaki aikin b'urut inji tusa" Aira da a cike take daman cike da jaraba ta juyo ta ce "waike inna ina ruwanki dani ne,dandai neman tashin hankali irin naki magana nayi maki ne Dan ayi maki magana ki ce anyi maki Rashin kunya kije ki hada mutum da Abba ni kibarni da gajiya ta ma ta isheni"da ruwana dan ubanki shegiya mai kama da Aljannu figai figai kamar kaza amma sai Rashin arziki cike da ciki" tsaki taja tare da cire gugar ta mik'e tana hada kayan gugar ta ce . "Kindai kusa mutuwa mu huta " Inna cike da masifa ta dauki pillow dake kusa da ita ta jefa mata tace "uwarkice Rahama zata mutu Dan ubanki Da gudu Aira ta yi waje ta na Dariya Dan tasan yau ta tabo inna Dan ba abunda ta tsana irin kace za ta mutu. Ta na fitowa ta na Dariya sai sannan na k'are mata kallo Fara ce Sol farin nata har wani yellow yellow yake doguwace daidai misali sannan bata da k'iba siririyace amma ba Chan ba Dan tsawonta ne ma yasa za akirata da siririya badan haka ba ta na da kibar ta daidai gwargwado,ta na da shape sosai Musamman Hips Dan koya tayi tafiya saisun juya zaka iya kiranta da mai shape din cocacola bata da breast sosai Amma kuma bazaka kirata da kwaila ba Ta na da y'ar doguwar fuska ta na da dogon hanci da kuma k'aramun bakinta da yayi das da kyakyawar fuskarta lips d'inta jawur kamar ta shafa janbaki sanye take cikin wasu English wears Riga da wando ba kallabi kanta bak'in gashinta ne tayi parking Wanda ya dirar mata har gadon baya kyakykyawace sosai ta Bugawa a jarida Saidai daga kaga fuskarta kasan yarinyace girman jikine kawai Allah ya bata amma bazata wuce 17 years ba. Ta d'ayar kofar ta bi ta shiga cikin gidansu ta na shiga ta Hango Abba akan farar kujera sanye da glass yana karanta jarida kai tsaye wajenshi ta nufa ta na murmushi ta ce " Abba Sannu da hutawa"Cikin muryar girma da dattako ya d'ago ya Kalleta da murmushi a fuskarsa ya ce "Yawwa y'ar gidan Inna " sannan ya maida kanshi ga abunda yake hakan yasa ta tafi ta shiga cikin gida.saida na K'are mashi kallo naga kamarshi d'aya da ita sak kawai Haskene ta fishi. Tana shiga palourn ta tarar da duk y'an gidansu suna zaune yaran na shirin tahfex iyayen kuma na zaune suna hira ta na shiga Mamy ta ce "gwara da Allah ya kawoki yanzu nake. Cewa Aje a kiraki Kuyi shirin Tahfex"Mamy Fara ce itama sosai kamar Aira Saidai basa kama sosai ita Aira ta d'auko farin mahaifiyarta ne Amma sak Kamar Abbanta ta yo. Turo baki gaba ta yi ta ce Daman banzoba wlh ni na gaji Duka yaushe na dawo daga school bama wannnan ba sanin kanku Waec muke Ni nadauki hutun Tahfex d'innan gsky saimun gama jarabawa" Salati Mamy tayi tace "Aiko baki isa ba wlh ko ki tashi ki shirya ko yanzu nakira Abbanki na fad'a mashi" wara idanu tayi Dan a rayuwa ba Wanda take shakka irin Abba bayason wasa da Ilimi musamman Na Arabi hakan yasata jin Haushi kamar zatayi kuka Mama ce ta ce "Kiyi Sauri Kinga y'an uwanki harsun shirya ai ba a wasa da Ilimi a zamanin nan Daughter bare kuda har kunyi sauka hardace kuke had'ewa kinaga itama harkun tafi Hizif Arba'in ai kamar yaune zakiga kun hade" To Mama bari naje na saka kayan Amma Dan bazan koma ba na tab'o inna tafada ta na Dariya "Murmushi Mama ta yi ta ce " Ai keda Inna ba a shiga Mamy ko tuni harta tashi ta shiga ciki. Ta na shiga d'akin ta tarar da Su Amma harsun shirya ta ce "Sister Dan Allah aramun Kayanki insa''tana saka hijab ta ce " ke ina taki "cikin masifa ta ce " to ina ruwanki da ina tawa ko Dan nace ki aramun kayan ki shine zaki fad'amun magana "Amma ta ce" To Allah huci zuciyarki kidaga locker ki dauka kinci sa a An goge"Ummy dake gefe ta na chat taja tsaki ta ce "Kede Anyi sokuwa wlh idan nice Saidai ta mutu Amma bazan ba ta ba ta na kanwarki amma duk tabi ta rainaki" Tsaki Aira taja jin Abunda Ummy tace ta ce Ke ina ruwanki shigar shugula kawai ke har kin isa ki shiga tsakanina da Amma kidaina shiga sabgarmu dalla tafada ta na sanya kayan da ta dauko, dariya itama amma tayi ta ce"Ai shine ko ina ruwanta da shiga tsakaninmu" tabe baki ummy dan daman tasan ba a shiga tsakaninsu sanin ta biyewa Aira tsaf zatayi mata Rashin kunya ya sanya Ummy Jan bakinta tayi shiru ta ci gaba da chat d'inta. Bayan sun dawo da daddare D'akin Inna ta shiga ta na shiga ta fara balbaleta Tayi banza ta kyaleta ganin abun ya fara yawa ya sanyata tashi ta shiga bedroom d'inta ta d'auko wasu manya-Manyan chocolate guda biyu ta kalli inna ta ce "indai kina so in baki to wlh sai kinbar fad'an nan" tuni inna ta fara washe baki ta ce "Ah too Y'ar lele na daman akwai Zumar turawan nan a gidan nan.” " Dariya Aira tayi tare da mik'a mata tace "Ai fad'an ki yasa bana baki " amsa inna tayi ta na washe baki ta daga ta fara sha har wani lumshe ido take Aira tayi kasa da murya tace "Ai Hajiya inna sai kinyi shekaru irin na Dabino keda mutuwa ta yi nan kinyi Chan Yanzu Dan Allah My Inna wayarki zaki aromun yanzu zan maido maki " kai kede Allah yayi miki albarka yarinyar nan Duk a d'iyan Habubakar ke kika fita zakka duk kinfisu hali me kyau bakisan in mutu Sannan ta ciro wayar a d'an tofin ta ta ta mik'a mata ,itadai Aira Dariya kawai take jin yabon da inna ke mata kamar ba itace ta gama balbaleta ba tasan daman tunda ta bata choculate ta kashe bakin. Itako tashi tayi ta shiga bedroom d'inta ta haye kan Gado tare da Rungume pillow jujjuya nokiar inna tayi tare da dialing number daman tana kanta tana kira taji a kashe ta sake kira yakai goma amma abunda ake cemata kenan kuka ta fashe dashi ta ce "Yaya ina ka shiga tun jiya wayarka kashe na shiga ukku Kardai wani Abu ya sameka, ta jima ta na kuka ta na sabbatu tana kiran number a kashe Dan tab'a saba da missing d'inshi daidai da yini daya ba hakan yasa ta k'ara shiga damuwa da kyal ta samu wajen 1 bacci ya dauketa. Washegari sukuku ta tashi duk hankalinta ba kwance ba haka dai har taje school tayi jarabawa amma hankalinta ya na wani wajen daban. ©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️©️ *Government House* Ko ban fad'a ba kunsadai yanda gov house yake ba sai na bata bakiba wajen fad'an tsaruwarta da kyanta ba duk yanda zan kwatanta kunsan tafi haka. Yau duk gidan aikace aikace kawai ake da shirye shiryen Abinciccika kala kala Dan tarbar tilon d'an governor mai ci yanzu da zai dawo daga London Mahaifiyarshi Hajiya Fatima yau cikin farinciki take marar musaltuwa Dan sosai tayi missing d'an nata Da misalin k'arfe Shida ya yamma jirginsu ya Sauka a Nigeria Mahaifiyarshi da kanta suka tafi domin tarbarshi . A hankali yake Saukowa daga matattakalar benen jirgi cikin Tafiyarshi ta k'asaita sanye yake cikin K'anan an kaya da sukayi mugun Karbarshi Fari ne amma ba wai fari Chan ba dogo mai murdaddan jiki yana da saje Wanda shine Babban abunda yake rikita y'an mata lips d'inshi ko har wani ja yake kamar ya shafa wani abu Kyakkyawa ne na Bugawa a jarida daga ganin fatarshi kasan Hutu ya zauna mutum ne Mai ji da gayu Shima kallo d'aya zakayi mashi kasan ya na cikin tsananin farinciki hug din juna sukayi shida mahaifiyarshi cike da son juna da kewar juna suka koma gida suna hirarsu ta y'a da uwa koda suka isa gida baiyi mamakin tarbar da ya samu ba Dan ko da kwana daya ne yayi tafiya haka ake mashi. Bayan yayi wanka ya sake shiri ya huta mahaifiyarshi da kanta ta dinga feeding d'an nata kamar wani yaro shi kuma sai shagwaba yake mata kamar zaiyi kuka ya ce "Uhm mummy na k'oshi please ki barni haka cikina ya cike"mummy na k'ara d'auko wani spoon din ta ce " Haba son Bafa kaci da yawa ba nasan a can ba wani cin abinci kake sosaiba ha a d'aga bakin saika cinye na plate d'innan". "Murmushi kawai yayi a haka dak'yal har ya ida cinyewa Dan shi ba mutum bane mai fiyason cin abinci ba ya na gamawa ya Mike tare da kallon Mummy ya ce Mummy zan d'an fita please karki hana" Haba son ko fa hutawa bakai ba daga dawowarka ka ce zaka fita "cikin shagwaba ya ce Mummy ba jimawa zanyiba yanzu zan dawo " To bazaka bari sai ka kara huta wanna"Mummy please" yafada yana hade hannaye,To shikenan Allah ya kiyaye ka kulamun da kanka kuma karka jima"Hug d'inta yayi ya ce "Don't mention my dear mom saina dawo. Driver kadai ya tuk'ashi Dan bayason yawo da Security wannan Karin ma yayi kyau sai baza k'amshi yake Dan shigar da yayi ta yanzu ma tafi ta d'azu kyau murmushi kawai yake shi d'aya. Aira suna zazzaune a palourn inna Ita da su Amma,Haidar sai Ummy duk suna shan labari wajen inna sai kwasar Dariya suke banda Aira da tayi jugum Dan yau ko abincin kirki bataci ba Suka jiyo knocking Haidar ne ya tashi ya je ya bud'e Aira da hankalinta na kan k'ofa ganin mai shigowarne ya sanyata mik'ewa a matuk'ar rud'e ba k'aramun surprise d'inta yayi ba shima tsaye yayi ya na K'are mata kallo sanye take cikin wasu English wears Riga da wando red and black kanta bako kallabi sai gashinta da yake a parke Sosai yaga ta k'ara yimashi kyau da girma A d'an kwanakin da yayi bai ganta ba murmushinshi kawai mai tsada yake sakar mata Ai bata San Lokacin da ta Ruga a guje ba tare da Rungumeshi Farincikin da take ciki tama kasa musaltashi da komai Kuka ta fashe dashi cikin muryar kuka ta ce ..........✍🏿 ```Hmmmm ya kukaji salon Fans kudai muje zuwa ai ba afara komai ba salon na musamman ne Kudai kawai Had'in kanku nake buk'ata ta hanyar comment da zazzafan sharhi ni kuma zan datse damtse wannan Karin ba wasa a zafafe na dawo kamar yanda littafin yake zazzafa Idan Naji comment da sharhi zaku jini idan kuma Naji shiru nima zaku jini shiru ta hanyar yawan comment ne zan gane labarin zai muku dadi ko akasin haka more comment more typing ``` 💪🏼🤷🏼‍♀️🙅🏻‍♀️ _*Miss Hajo ce*_ [5/23, 18:16] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............3&4 “My Yaya why did you turn off your phone for two days i could not find you’’ dad dab’a bayanta yafara cikin sigar lallashi ya ce “ I’m sorry my cutie Babe bansan zaki tashi hankalinki haka ba I did this to surprise you shiyasa “sakinshi tayi tare da turo baki ta ce ‘’uhm My Yaya ni nayi fushi ma tunda da gangan kayimun haka ‘’ta turo baki ta koma kan Kujera ta Zauna ta na turo baki ita ala dole anyi mata laifi”Murmushi yayi tare da binta dan yasan ya tab’o y’ar rigimar tashi kamar zaiyi mata rad’a ya ce. “Sorry my cutie bazan sakeba kinsan fa duk saboda naganki na dawo kiyi hakuri ki janye fushin kinji little sis”Turo baki gaba tayi ta ce “Ni bazan hak’ura ba “kamar zaiyi kuka ya ce “Too na koma chan kenan “juyowa tayi cikin sigar shagwab’a tace “nayi missing din naka shine zakace zaka koma “ta fad’a ta na aika mashi da hararar wasa lakutar kumatunta yayi yace “Nima kewarki ce ta dawo dani I was joking dan ki hakura “To ai nahakura karka sake “murmushinshi mai tsada ya sakar mata ya ce insha Allah bazan sakeba smile mana kinsan kinfi kyau da murmushi “Dariya tayi tare da rufe fuska ta kwance kanta saman kafadarshi sai sannan yayi ajiyar zuciya yace”fatan dai na sameki lfy”gyada mashi kai ta yi tace “Alhmdllh saidai rashin lafiyar kewarka kuma yanzu na warke hope kazo lafiya ya hanya “murmushi yayi yace Nima lfy nadawo sai dai cutar kewarki kuma yanzu na warke ya fada yana shafar kanta ya ce “kinga yanda kika kara girma kuwa cutie Meye sirrin ko dai inna wani abun take baki “. Dariya tayi tare da rufe fuska tace “Kai yaya ai kaine ma ka kara girma “Tsinkayi murnar inna sukayi “To fa jarabar ta dawo yanzu za a faramun manne manne da tab’e-tab’e a daki ta karasa fada ta na jan tsaki “Dariya duka sukayi Banda Arman da baifiya dariyaba murmusawa kawai yayi ya ce . “Haba y’ar tsohuwas daga zuwana bako sannu da zuwa bakiyiwa angon naki ba zaki fara halin “tabe baki tayi ta ce “Akai kasuwa indai kaine sannan daka shigo ko gaisheni bakayiba bama ka ganni a wajenba ka tafi wajen fitsararriyar y’ar lelen naka “murmushi yayi yana kallon Aira yanda take aikawa da inna harara yace “afuwan hajjaju Nina isa na kyale uwar gida ran gida Allah huci zuciyarki ran ki ya dad’e kiyi shekaru irin na dabino “lokaci guda inna ta saki rai ta ce “sannu da zuwa Mujahid ya kasar turawan andawo lafiya “lafiya qlau inna fatan kuma mun sameku lafiya “su Amma ne da Haidar suka gaisheshi ya amsa a tak’aice basu damuba saboda daman sunsan duk gidan nan ba wanda yake sakewa ko doguwar magana ta hadasu sai Aira. Aira ce ta ce “Yaya ka rabu da inna Neman fitina ne kawai irin nata kaga tashi ma mu fita na baka labarin abubuwan da Akayi Baka nan ta fada ta na mikewa tare da kama hannunshi sukayi farfajiyar gidan Sunajin inna na sababi suka kyaleta. Sun jima a waje suna ta Hira ta bashi labari na dariya yayi itama haka har akai margriba suna nan saida Mummy ta kirashi ya Sanyashi tunawa da ta ce kar ya jima yace mata yanzu zai dawo kallon Aira yayi ya ce “Baby zanwuce Gida Mummy na kirana “nan ta fara shagwaba ita bata gaji da ganinshi ba dakyal ya samu ya lallabata ya tafi gida da niyyar washegari zai dawo yakaita shan ice cream kuma zai taho mata da tsarabarta. Daren ranar kowannensu Kwanan farinciki yayi Washegari Aira koda ta dawo daga school Lokacin Tahfex nayi langwabewa tayi tace batada lafiya bazataje ba saboda kar Yaya Arman yazo ta tafi. Da misalin karfe biyar na yamma ya shigo gidan sosai yayi mata kyau cikin riga ash da black din jeans itama tayi kyau cikin atamfarta doguwar riga ta sa malha tayi daurin dankwalinta tare da fito da gashinta baya sosai tayi kyau Arman ko kasa daina kallonta yayi dan ba karamun kyau tayi mashi ba bayan ta shigo gaban Motar ta ce “Yaya na shirya muje ko”Harararta yayi yace a haka zakije gashin kanki duk waje kuma wannan miririn mayafin zaki yafa jeki ki sanyo hijab “kamar zatayi kuka tace “Dan Allah yaya ka bari muje harfa na shirya kuma idan na koma inna ganewa zatai da inda zamu bakaga gyalenma a jaka na sanyashiba “zakija a fasa fitar wlh muddin haka zaki fita gardawa na gane maki gashi ke ko kishin kanki bakyayi “Yafa gyalan tayi ta saman ka tace “to yaya na rufe kan please karka kara cewa wani abu “badan ranshi yasoba suka tafi dan yana bakin cikin mutane su dinga ganemishi surar Airar shi ba danshi kad’ai yasan kalar so da kishinta da yake “. Wuraren shakatawa sosai yakaita sai murna da farinciki take tabbas farincikinta yadawo rabon da tashiga farinciki haka tun tafiyarshi london kimanin wata biyu kenan. A hanyar su ta dawowa a mota ya bata kyautar hadaddiyar zoben gold din daya sayo mata sosai tayi farinciki da murna sai godiya takemai shidai murmushi kawai yake yana kare mata kallo. Suna isa suka fito Hannunsu makale da na juna sai Dariya take ta farinciki tana zabgamai godiya daidai zasu shiga palourn inna Abba na fitowa Sosai gabanta ya fadi cikin dabarbarcewa ta fara kokarin kwace hannunta ya rike gam tare da galla mata harara kamar zatai kuka tace ka sakeni kara rike hannunta yayi ma . kallon zaki gane kuranta Abba yayi mata tare da wucewarshi sosai nayi mamakin ganin Arman baiko gaishe da Abba ba saima kauda kai da yayi Abba na wucewa Arman ya gallawa Aira harara yace “ita kuma wannan rikicewar da kikayi ta mecece kamar kinga mala’ikan mutuwa “cikin muryar in ina tace yaya ab ba tsaki yaja tare da sakin hannunta ya wuce ya fasa shiga gidan inna durkushewa tayi ta fashe da kuka tasan ba karamun hukunci zata fuskanta a wajen Abba ba ga kuma shima yaya Arman din yatafi kamar fushi ma yayi da ita tana cikin kuka haidar yazo tare da daddabata ya ce “ya Aira Abba yace kizo yanzu yanzunnan ki sameshi a babban palour kika wuce minti biyar kinsan sauran..........✍🏿 Tofa meye dalilin da yasa Aira ta rikice ganin Abba ya ganta tare da Arman ???? Meye dalilin da yasa Arman bai gaishe da Abba ba???? Tukunnama wace Alakace ke tsakaninsu???? Zaku samu amsarkune ta hanyar bibiyata cikin wannan zazzafan labari * Ta hanyar comment da sharhi tare da sharing shine abunda zaisa na gane labarin yana muku dadi ko akasin haka kuma shine babbar kwarin gwiwar da zaku bani idan kun karanta ku dinga comment tare da sharing sauran grps masoyan asali* 🤗 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [5/25, 00:17] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE* 📔 🅿️...............5&6 Cikin ta ne ya d'uri ruwa jin Abba na kiranta Cikin kuka ta kalli Haidar ta ce "Na shiga Ukku Haidar Abba Duka na zaiyi ko" Sai yaji yayar tashi ta bashi tausayi girgiza mata kai yayi ya ce "A a ya Aira nidai kawai cewa yayi kizo kuma kinsan Abba bayason yayi kira a bata mai lokaci ki taho muje " shahada tayi ta mik'e tare da Jan kafafunta Wanda dak'yal suke daukarta tsabar tsoro. Sosai ta tsorata ganin Abba na safa da marwa a palour tana shiga gabanta ba abunda yake sai fad'uwa juyowar da zatayi taji Abba ya d'auke ta wani gigitaccen mari da saida hankalinta ya gushe na d'an wani lokaci kafin ta d'ago ya k'ara kifa mata mari wani irin ihu ta fasa tare da durk'ushewa ta na kuka. Cable d'in wayar wuta ya d'auko ya nufeta tare da lafta mata daya azabar da taji ce ta saka Kara sakin wani karan "Na shiga ukku zan mutu" Mama ce ta taso hankali tashe ta rik'e cable d'in ta ce "Dan girman Allah Alhaji kayi hakuri karka daketa DA Wannan Abun" Abba ya juyo ya Kalleta ya ce "Zainab ki rabu dani wannan yarinyar bata jin magana ki barni na koya mata hankali" . "A a Alhaji Dan girman Allah kayi hakuri ka zauna Tukunnama me tayi Abba na huci ya zauna ya dubi Aira da ta ke kuka wiwi ya ce "Had'iye kukan nan yanzu yanzu nan Dan gidanku " Cikin Sauri ta Had'iye kukan sai shshsheka da take cikin tsawa ya ce. "D'ago ki kalleni Munafuka " Idonta jab'e jab'e da hawaye ta Kalleshi ya ce "Sau nawa Zan rabaki da d'an iskan yaron nan,ban rabaki dashi ba?tana shasheka ta d'aga kai " Bud'e baki zakiyi kimun magana "k a ra ba mu " ta fad'a a rarrabe "Fine Kinsan da haka kuma shine kika cigaba da mu'amula dashi ko Watau bakijin magana ta ko rainani ne kika yi?" Cikin kuka ta fara girgiza kai ta ce "Dan Allah Abba kayi hakuri Bazan sakeba". " wannan ya zama.last warning da zan k'ara ganinki da yaron can duk irin hukuncin da na yanke maki ki kuka da kanki kina jina"cikin Sauri ta d'ago ta ce "Naji Abba"ki tashi kiban wuri sakarai wacce batasan ciwon kanta ba "hada gudunta Aira ta Ruga tayi dakinsu ta na zuwa ta baje a gado taci gaba da rera kuka Amma Da Ummy su sukayi ta Lallashinta anma kamar k’ara zugata suke. Mama ko da Mamy sosai basajin dadin wannan al'amarin nasu musamman Abba da ya fi d'aukar zafi , ba Wanda ya kumayin magana cikin su Mamy ta tashi da tsohon cikinta ta tayi d'akinta ta jima ta na hawaye tasan Duka itace silar raba wannan y'an uwa Gashi kuma batajin dad'in yanda Kullum y'arta ta zama kamar jakka akan Arman kullum Abba cikin dukanta yake amma kamarma Kara tunzurata yake Haidar ne ya shigo maza tayi ta Goge hawayen ta Kalleshi ta ce. " Haidar jeka kiramun Hajara"to Mamy yafada yaje ya samu Aira na Kuka Amma na Lallashinta yace "ya Aira Mamy na Kiranki a d'akinta Gyada mai kai tayi ta tashi ta na Goge hawaye ta bishi ta na zuwa ta zaune gefen Gado Mamy ta kalli Haidar ta ce " Bamu wuri zamuyi magana "Yana fita ta kalli Aira ta ce " ke yanzu Hajara Haka zakiyi ta zama kin maida kanki jaka a gida ko,?kowa ya na zaune lafiya amma banda ke,tunda kika San mahaifinki bayason tarenki da shi meye na likemai Ubanki ne shi da bazaki iya rabuwa dashi ba ko kullum kinfison ke kad'ai ake jinki da mahaifinki na rasa uban me yake baki duk kinbi kin lik'emai sakarai Saikije kiyi tayi ai tunda bakison ciwon kankiba"Aira Abu dukya chunkushe mata ga Abba ya gama laftarta ga Mamy ta hauta da fad'a tashi tayi ta na kuka ta fita tayi waje ta ma bar part din gaba d'aya ta koma part din inna. Gadon ta ta hayaye a abunda take inbanda kuka shin ya zatayi da rayuwarta ,meye laifin ta ida da Arman akan gabar dake tsakanin iyayensu ga Abba ya gama jibgarta itama Mamy zata hauta da fad'a saida ta gama kukanta harta gode Allah tace "Gashi Shima Ya Arman din yayi fushi dani ya kukeso nayi da rayuwata tafada tana wulli da pillow Ta Kara fashewa da kuka ta ce. " Tun bansan kaina ba na shak’u da kai yaya ARMAN wacce bazan tab'a iya misalta ta da komai ba ,tun bansan kaina ba ,shakuwar dake tsakaninmu babu wanda zai isa ya rabamu koda za a dinga tsaga naman jikina ana barbada attarugu da barkono bazan tab'a iya rabuwa dakai ba " kuka ta k'ara fashewa dashi ita wai yazatayi da rayuwarta Daren ranar bacci kauracewa idanunta yayi banda kuka ba abunda take sai wajen Asuba bacci ya d'auketa. ©©©©©©©©©©©©©©© Arman kai tsaye guest house d'inshi ya nufa kwance yake kan makeken gadonshi da komai na d'akin pink ne dakin gabaki dayanshi manne yake da hotunan Aira wasu tun tana yarinya wasu kuma da girmanta wasu tare suka dauka daga shi sai T-shirt da gajeran wando banda tsaki ba abunda yakeja ya ce "Wannan tsoron na mahaifinta da nagani k'arara a kwayar idanunta Tabbas wataran zata iya ruguza alak'armu abunda bazan tab'a jura ba kenan ko sama da k'asa zata had'e ana ruguguwar tashin k'iyama bazan tab'a yarda a rabamu ba my cutie Aira I love her so much,ina jinta har cikin kokon zuciya ta ,i can't live without her inajinta a jinin jikina,tunaninta bai tab'a barin kwakwalwata ba daidai da second d'aya why Abba yakeson rabamu me mukai musu,ina ruwan mu da rigimarsu" Chan ya numfasa saboda bai saba doguwar magana ba ya ce. " Karfa Aje kuma ita Har yanzu Kallon yaya kawai takemun kartace kuma bata sona wulli yayi da laptop d'in dake gabanshi ya ce "Inaaaaa bazaiyuba haka yayi ta zirga zirga ya k'ulla can ya since can ganin kanshi ya fara kullewa ya tashi tare da daura alwala ya fara jera salloli duk adduarshi akan Allah ya bashi Aira Dan shi kanshi ya kasa gane wannan wace irin jarabtar so ce Allah ya d'ora mishi ta yarinyar nan........✍🏿 Hmm muje zuwa A gaskiya ina Jin dadin comment dinku sosai masoyan asali kuma ina godiya kwarai da gaske 💃🏾💃🏾💃🏾 *Comment* *vote* *Share fisabilillah*# *_Miss Hajo ce*_🤙🏿 [5/25, 23:13] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION* 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............7&8 Washe gari kasancewar weekend kuma basu da jarabawa yasanya bataje ko ina ba a d'aki ta yini tun Inna na tambayar me akai mata har ta rabu da ita sosai take baza ido ganin ko yaya ARMAN zaizo amma shiru hawaye ne ke zarya daga idanunta ta ce "Yaya kai kuma me nayi maka da zakayi fushi dani". ©©©©©©©©© Zaune suke a makeken palour shida mahaifiyarshi Magana take mai amma kwata-kwata hankalinshi baya gurin saida ta dafoshi ta ce " Arman dakai fa nake magana tunaninme kake"Nothing Mummy ina jinki "Hmmm kawai ta ce sannan ta d'ora da cewa. " Son maganar da na saba fad'a ce dai zan kuma maimaitawa Ka duba kaga ARMAN sa'anninka duk sunyi Aure wasu hada y'ay'a amma kai baka da ma niyyar yi shekararu fa ja suke Son ka duba 33years amma har yanzu baka da iyali ,ina son nima naga Aurenka naga Y'ay'anka karfa ka manta kai kad'ai ne d'ana a duniya kai kad'ai nake dashi Wanda zansamu jikoki daga gareshi ka tausaya mun ko Dan ni Arman plx". Numfasawa yayi a ranshi ya ce "Ina wata matsalar ita ma Mummy zatazo da wata a fili kuma cewa yayi " Mummy karki damu Aure lokaci ne Idan lokacin yayi za ayi"Kullum maganar ka kenan Aure lokacine eh Aure lokaci ne amma anasa niya kaikuwa kwata kwata baka ma da niyyar ma sau nawa ina turaka kaje kaga y'ay'an y'an uwa da Abokaina karshema ka kunyatani kayiwa yaran wulakanci " . calm down Mummynah Insha Allahu soon zanyi Aure ina da wacce nake so ita nake jira ne shiyasa" Hararar wasa ta gallamai ta ce "Kullum maganar kenan ka na da wacce kake so ,kuma kak'i fadarta mu Santa,yaushema kake kula y'an matan da har zakaso wata son kodai aljanna ta Aure ka bamu sani ba " . Dariya maganar Mummy ta bashi sosai saida ya d'an Dara ya ce "yawwa Mummy ashe kingane aljanarce ta Aure ni shiyasa na mutu a kanta to Kinga sha'anin Aljannu sai a hankali zata rabu dani ku tayani da addua kawai Allah bani ita amma kidaina mun maganar Auren nan kinsan Aljannu da kishi karta kullaceki fa mummy". pillow Mummy ta tillamai jin shirman na d'an ta ce " Watau Arman kadai maidani kaka ko zaka gamu dani ja iri kawai"Dariya yayi tare da gocewa pillown da Mummy ke jefamai yayi Hanyar fita yana cewa "Good bye mom saina dawo "yana fita guyd's d'inshi sukayo wajenshi dakatar dasu yayi Dan bai fiyason yawo da su ba Motarshi Fara Sol kirar Benz yahau kai tsaye gidan Inna ya nufa ya na shiga mai gadi ya bud'e mashi ya shiga A lokacin Aira na kwance saman sofa ba bacci take ba amma kallo d'aya zaka mata kasan ta na cikin damuwa. Dagowar da zatayi idonuwansu suka sarke cikin na juna ganin yanda ya hade rai ya basar ya yasanya maida idanunta kasa gabanta na fad'uwa tayi Sauri ta maida hawayen da suka zubo mata Arman na zama ya gaishe da Inna ta amsa tare da cewa "Wai ni Mujahid ina mahaifinka yaje kwana biyu bai lek'o ya gaishe niba " Baya gari ne Naji Mummy tace yaje Ghana wani metting nima tunda nashigo k'asar bamu had'u dashiba"yana maganar ya na satar kallon Aira ta maida idanunta ta rufe. "Inna ce ta ce " To Allah ya maido shi lafiya nikadai a raina nace lafiya Kabir zai kwana biyu baizo ba "shidai Arman baice komai ba sai satar kallon Aira yake inna ce ta tashi ta ce " Nidai na gaji da zafin nan bari na fita waje nasha iska tafada tare da ficewa farfajiyar wajen kamar jiran fitarta yake ya taso tare da zama kujerar da Aira take a hankali ya ce "My cutie" Shiru tayi kamar bacci take nanko ta na jinshi "Hmmmm nasan kina jina dan idonki biyu wake up zamuyi magana" badan taso ba ta tashi Dan sai yanzu take ganin me tayi mishi da zaiyi fushi da ita. "kallon ta ya tsayayi yanda idanunta sukayi jawur ga alamar Tasha kuka cike da damuwa ya ce "Kuka kikayi ko Cutie" Kamar jira take nan take ta fashe da wani sabon kukan jin kukanta yake har cikin ranshi rungumeta yayi yana Lallashinta dak'yal ya samu tayi shiru cike da damuwa yace "wa ya tab'amun ke" Shiru tayi ta na shashsheka "ganin shaftun bulala a hannunta yayi ja abunka ga farar fata cike da damuwa ya rik'e hannun ya ce. " Cutie Abba ya dake ki ko"Gyada mai kayi tana hawaye "sosai ranshi ya b'aci Dan a duniya ba abunda ya tsana sama da b'acin ran airanshi Har takai ga an tab'a lafiyarta wlh ba Dan shi ya haifeta ba da nikadai nasan matakin da zan d'auka cikin zuciyarshi yake maganar nan amma a fili cewa yayi "cewa yayi ki rabu da ni ko" gyada mishi kai tayi ta na hawaye "Dan son gwadata ko tsoro zaisa ta iya rabuwa da shi din yasanyashi cewa" Cutie Tunda Abba bayason mu'amularmu zan hakura na daina zuwa "wata irin zabura tayi tare da Rungumeshi tsam ta gefenshi ta zagayar da hannayenta cikinshi kamar wacce akace za a kwace mata shi tana kuka ta ce . " kadaina cewa haka Dan Allah ni babu mai rabani dakai ko mutuwa ma tare Zata daukemu "sosai yaji dadin kalamanta cikin zuciyarshi amma Dan son Kara latsata ya sashi cewa" Bakya tsoron irin dukan da Abba yake maki banason Ana tab'amun lafiyarki shiyasa "Ni dukanshi baya mun komai nidai ka daina cewa zamu rabu daman zaka iya rabuwa dani ni bazan iya juran missing dinka ba ko Abba zai kasheni nidai ina son ganinka " ta fada tana shasheka sosai yaji dadin kalamanta A ranshi "bubbuga bayanta ya fara tare da fara Lallashinta yace. " Sorry my cutie nima bazan tab'a iya rabuwa dakeba Kisa wannan a ranki babu mai rabamu sai mutuwa kibar kukan nan kinsan kukanki yana tab'amun Zuciya "Lokaci guda ta Had'iye kukan tayi luf jikinshi tana sauke ajiyar Zuciya kokarin Bambareta daga jikinshi yake amma ta kiya saima Kara Lafewa da tayi jikinshi tana shak'ar daddad'an k'amshin turarenshi har wani bacci bacci yake kokarin daukarta shiko bayason Yanda Aira ke rungumarshi Dan yana cutuwa amma ba yanda ya iya " A hankali ya ce "Cutie son jikinki yayi yawa " Murmushi kawai tayi ta na lumshe ido ta ce "Turarenka yanamun dad'i yaya" Ko kina so na kawo maki shi"cikin shagwaba ta ce "kamanta ka tab'a kawomun Amma ni idan na shafa banajin dad'in kamshinshi kamar ma ba shiba a jikin ka ne yake k'amshi me dadi" Murmushi kawai yayi ya ce. "Ya Exam din fatan kina maida hankali" Alhmdllh yaya ina karatu sosai ai "yaya aramun wayarka nayi game" Ciro wayar yayi tare da mik'a mata "gyarawa tayi tare da d'ora kanta a kafad'arshi ta na game din da ta fad'i yayi mata Dariya ganin haka yasa suka fara yi tare yayi ci daya tayi daya idan ta fad'i yayi mata Dariya Shima idan ya fad'i tayi mishi Dariya idan kuma taci tayi ta mashi gwalo Sosai suka shagala Aira harta manta da wani abu waishi damuwa Dan ita daman b'acin rai bai zama cikin zuciyarta. "Ummy ce ta shigo ita da Amma Duk.kallon Mamaki suka dinga kallonsu dashi Ummy dai tab'e baki tayi ta zauna Amma ko mamakin irin taurin kai iri. Na Aira take " Amma ce ta gaisheshi ya amsa yana mata dariyar ya fad'i Inna ce Ta shigo tsaki taja ta ce "Ohni Halima ina ganin rayuwa yaran zamanin nan baku San ta ido ba wlh ayi yara baku da aiki sai Rungume Rungume da tab'e tab'e kai nidai Na kusa korarku wlh a daina shigomun Bangare ehe akanme" ta k'arasa fad'a tana zama tare da Mike kafa "yi sukayi kamar bada su take ba saima cigaba da game d'insu sukayi " inna Haushi ya cikata ta tashi tace "ku tashi ku fita tare da nuna musu hanya turo baki Aira tayi ta ce " kedai tsohuwar nan baki son zaman lafiya me aka miki kuma"Ubanki akamun ku tashi ku fita nace "Bazamu fita dinba ki daukemu ki fiddamu ta fad'a tana murguda baki " Salati inna tayi tare da Goge hawaye ta ce "Ni kike zagi Hajara kai albasa batai halin ruwa ba baki biyo halin mai sunan ki ba Y'ar uwata ba haka take ba kai amma ma wlh an cuceta da aka saka mata sunanki kaico Adda Jaru Allah ya jikanki yasa kina cikin rahama ke kuma bari inje nafadawa ubanki kina zagina " Jin hakan ya sanya Aira saurin tashi tare da ruko hannun Inna Dan tasan ta kaita wajen Abba ta kade Ta ce . "Haba my lovely grandy wasan jika da kaka ne fa ni ina ni ina maki Rashin kunya waya haifeni a garin nan" Inna ta tsuke baki tace "ba wani dad'in baki da zakimun " ta kama hanyar fita tayi Sauri ta bita Tare da ruko ta ta ce "Inna dawo zan baki Zumar turawa wlh ai kina so ko" Lokaci guda Inna ta saki fuska ta ce "da gaske kike y'ar nan " Eh mana inna da gaske Amma saikin dawo saikin fasa zuwa"juyowa inna tayi tana washe baki ta ce "Daman ai wasa nake maki y'ar albarka ai duk cikin d'iyan Habu ke kika fita zakka ba kamar waccen Zakalkalar bata da aiki sai latsa waya Ko y'ar halawa bata tab'a kawomun ba . " ta fad'a ta na kallon Ummy Aira ko Dariya hada rik'e cike jin an tabo ummy itako Ko kallon Inda inna take bataiba saima cigaba da chat d'inta da tayi Arman dukda bai fiya Dariya ba saida ya d'an dara jin irin dramar da inna da Aira sukesha Bayan Aira ta kawowa inna coculate din Arman ya tashi ya ce "Cutie zan wuce " Kamar zatayi kuka ta ce "Yanzu kazo fa " wara idanu yayi ya ce "Kai cutie nafa jima" Cikin shagwaba ta ce Ni ban gaji da ganinka ba"Durkusawa yayi tare da rada mata wani Abu Wanda koni banjishi ba sainaji ta dago ta na Dariya ta ce. "promise fa yaya" Dage mata gira yayi ya ce "Gaske" tsalle tayi ta ce "Thnks you my yaya Goodbye sai gobe" Tare suka fita saida taga shigarshi mota tana mishi bye bye tukwana ta koma ciki ta na shiga lokacin Inna ta shige ciki Ummy ta wurga mata harara ta ce . "kedai wlh kin zama jaka Jiya Abba ya gama jibgarki akanshi yanzu kuma a ganku tare keda bakison ciwon jikinki ba" Turo baki gaba tayi ta ce "To ina ruwanki " Babu ruwana Jiki ma magayine ta fad'a ta na cigaba da latsa wayarta "Tsaki Aira ta ja kasa kasa ammako kallon y'ar uwar tata take kallon tausayi Dan sosai ta jima da ganewa Aira da Arman sunjima da Fara son junansu so ma ba na wasa Dan wannan abun nasu yafi k'arfin a kirashi shakuwa.......✍🏿 *Share fisabilillah* _*Miss Hajo ce_*🤙🏿 [5/27, 21:33] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION* 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............9&10 Washe gari Aira basu da Exams sungama Waec suna Dan hutun kwana Biyu kafin a fara neco hakan yasa bataje ko ina ba wajen 2 ta lek'a bangarensu Wanda rabon da ta shiga tun sanda Abba ya daketa Bayan ta gaishe da Mama dake palour ta wuje bedroom d'in Mamy "Kwance ta tarar da ita Alamar batajin dadi cike da damuwa tace. " Mamy meya sameki"Cikin k'arfin hali tace bakomai da sauki bandanjin dad'i ne amma na samu sauki"Zama tayi bakin gadon tare da cewa "Allah Kara sauki kema Mamy kidaina haihuwar nan Gaskiya ni kunya ma nakeji ace uwata zata haihu gashi sai wahala kikesha " idan na haihu kice d'an ko d'iyar ba k'aninki bane ba shikenan ba marar kunya ku biyun ne harzaki dinga mun complain masu y'ay'a goma suce me ke inaga ke d'aya kikaso a haifeki ma ko Dan ki juya ni yanda kike so ". Dariya Aira tayi ta ce "Sorry Mamy na Ba haka nake nufi ba wahalar da kikesha ce banso" Ummm Naji dai ya exams din "Mamy yau bamuyi ba Sai next week amma alhmdll" Masha Allah Allah ya taimaka ki dage Aira sosai Kinga kinci Jamb 230 yanda akeso ki dage kici Waec and neco yanda next year makaranta kawai zaku tafi banson shiriritar nan da kika fara koya Aira Kinga dai Mahaifinku Karatu yake so Kuyi tun daga kan Yayyunki kina gani da idonki saida suka kammala degree d'insu aka musu Aure Batare da sunba iyayensu matsala ba inma Akwai soyayya a ranki ki cireta Aira kin tabbatar Mahaifinku bayason Kule kulen samari Karkija ki samu matsala dashi kinsanshi mutum ne mai ak'ida Dan haka ki nutsu ki maida hankalinki ga karatu kinji y'ata karki bani kunya". Tunda Mamy ta fara maganar Aira take sauraranta saida ta gama ta ce "Insha Allah Mamy bazaki sameni da matsala ba " Sannan ta tashi ta ce "Bari naje nayi sallah naga ana kiran Sallar la'asr " Koda ta fita da Kallo Mamy ta bita Tayi mata maganar nan ne badan komai ba "Saidan zargin da take na Aira Soyayya suke da Arman a zuciyarta ta ce " Allah yasa ma tunanina karya zama Gaskiya muddin Aira da Arman soyayya suke akwai matsala batason yanda ta zama farin silar raba wannan y'an uwan y'arta ma tazo ta k'ara zama silar k'ara rugujewar zumuncin iyayensu tasan Arman baida wani Aibu amma kuma soyayyarsu da Aira k'ara ruguza abubuwa zatayi da dama ta jima ta na tunanin AL amarin nan kafin ta tashi ta shiga toilet Dan dauro tata alwalar. Aira Bayan tayi salla Kwanciya ta yi palourn inna tana kallon wani series inna ta fito daga d'akinta kare da waya a hannunta ta mik'awa Aira ta ce "Amshi inji Mujahid " Cikin Sauri ta Amsa ta gaisheshi ya amsa tare da tambayar ya take"tukwana ya ce ki shirya nan da 30 minutes ina nan zuwa zamu fita amma Bazan shigo ba Dan sauri nake Zan kiraki wayar Inna zaiki fito" To yaya ta fad'a cikin Sauri kafin ta kalli inna ta ce "Inna fa kasan Abba ya fad'a mata ta daina bari na fita " Lost phone" yafad’a mik'awa inna wayar Tai daga bangarenshi ya cewa inna "Inna Dan Allah Anjima zanzo mu fita da Aira zan yo maki sayayyar kayan marmari ta kawo maki " Washe baki Inna tayi ta ce "To d'an albarka Saikazo kai nidai nayi sa ar jikoki wlh " Dariya Aira Tai Dan ita da Arman sunsan logar kashe bakin inna Dan tana da saukin kai indai akwai kayan makulesshe. Kafin lokacin da yace harta shirya sosai tayi kyau cikin blue din Abaya Jikinta duk stones ne Sosai tayi mata kyau kunsan yanda blue din abun ke karb'ar farar fata flat takalmi tasa batai make up ba sai hoda da kwalli kawai da tasa Sosai tayi kyau ta fito kamar wata balarabiya Tana gama shiri inna ta kawo mata waya ya kira ta amsa mai da gata nan fitowa. Ta na fita ta Hango motarshi Dan nesa da gidan ta na zuwa ta bud'e front sit ta shiga a hankali ya ce "wow my cutie kece kuwa" Murmushi ta yi tare da rufe fuska "Yau kuma ni akejin kunya " cikin Sweet voice d'inta ta ce "Yaya ai Kaine kamar yau kafara gani na " Murmushi yayi ya ce "kinyi kyau ne shiyasa" Kallonshi tayi Sosai yayi kyau cikin Dakakkiyar shaddarshi milk Tasha aikin da shi kanshi abun kallone hularshi ya hada matching colour ga Agogon gold d'inshi da take ta walkiya sosai yayi mata kyau kamar wani ango "A hankali ta ce " Wow Yaya kaima Kayi kyau Kamar Wanda zaije Zance . "murmushi yayi ya ce " Ai zancen nazo ki rakani"yafada ya na tada mota"lokaci guda ta chanza fuska Tare da cewa hmmm"Dadi yaji a zuciyarshi na ganin kishinshi a kwayar idonta dukansu sukayi shiru na d'an wani lokaci kafin ya juyo ya Kalleta ya ce "My cutie ya kikayi shiru ko bazaki rakani zancen ba " Kallonshi tayi tare da turo baki ta ce "Ni bazanje ba Daman kasan wajen budurwarka zakaje shine kacemun shan ice cream za ka kaini" cike da so da k'auna yake kallonta Dan sosai kuruciyarta take burgeshi ya ce "To saboda me bazaki rakaniba" Saboda bana sonta"Dariya yayi sosai kamar bashi ba ya ce "Ina kika Santa da zakice bakya sonta" turo baki tayi ta kauda kai gefe Sosai ta bashi Dariya ganin yanda take kishin ido bud'e ko wannan alamar kadai ta tabbatar mai da Airanshi itama tana sonshi. Wuraren shakatawa sosai ya kaita saida ya fara kaita Tasha Ice cream Sukasha hotuna a Wayarshi mutanen da suka sanshi sai mamakin ganinshi da budurwa suke Dan sunsa Arman mutum ne mai kamun kai ba kowace mace ce zata iya tunkararshima ta ce ta na sonshi bare shi karan kanshi yace yana sonta sosai Arman yake burge mutane saboda bashi da girman kai inba saninshi kayi ba baka tab'a cewa d'an Governor ne Dan ko Security bai fiya yawo dasu ba. Saida ya kaita wuraren shakatawa da shan iska sosai ya kashe mata kudi Inda ya kaita shopping mall ta zaba abunda takeso yawaici duk turarruka ta zab'a da choculate da ta jibgo kamar ba gobe shiko sai karo mata yake inbata ga wata ba ya ce "Cutie ga wata Bayan sun gama ya wuce da ita wani makaken Shagon saida iPhone's lokacin har Angama kiran Sallar magrib suna shiga masu shagon suka gaisheshi cikin mutuntawa ya amsa " Kallon Aira yayi ya ce "Baby tayani zab'e Waya zan chanza wacce kikaga ta dace dani"murmushi tayi ta ce . " Tohm yaya "Nan suka fiddo mata wayoyin tundaga 5× har zuwa iphone13 Ana dauko 13 Din tace yaya wannan tayi kaga itace ake yayi yanzu"tambayarsu yayi kudinta suka fadamashi 720k nan take yayi musu transfer yasa aka sanya mata cover mai kyau tare da Yin register sabon layi tukwana suka fito a hanya sai zud'in wayar take har suka iso bakin gate " ganin bai fito ba yasanya ta cewa "Bazaka shiga ba" Eh cutie Sauri nake"Kindai iya d'aukar kayan naki ko na shigar miki dasu"Murmushi tayi ta ce. "Haba yaya kamar wasu da yawa zan iya " to shikenan "tana niyyar fita yace " Zaki mance wayarki"Zaro idanu tayi ta ce "waya ta kuma?nida banda waya yaya ka manta" Wadda muka sayo nake nufi takice "Yaya tawa kuma ta fad'a cikin nuna mamaki" mik'a mata yayi ya ce "zakiga number ta a ciki nayi miki save zan dinga Kiranki ta nan idan zamuyi waya" Farincikin da take ciki bai musaltuwa tazo rungumeshi ya kauce ya na Dariya Ya ce "Cutie kin girma fa" Cikin murna ta ce "Thnks you yaya bansan da wani irin baki zan gode Maka ba nagode Allah saka da alkhairi ya k'ara budi Sai jujjuya wayar take wai tata ce "ameen Cutie na bansan godiyar nan haka Kinfi k'arfin komai a wajena " . Murmshi ta sakar mashi kafin ta ce "Yaya to ya zan fad'awa y'an gida Kar Abba ya kwace kasan bai fara barinmu rik'e waya ba musamman Na yaji kai ka bani"Ashe baki da wayau Baby karki sake ko da wasa wani ya ganta bare har ma asan ni nasai maki nima nasai maki ita ne badan komai ba saidan nadinga jin muryarki koda na koma Wajen aiki amma kinsan nima banason Abunda zai dinga Zame maki matsala a gida ni zan wuce yanzu sai gobe Idan na leko" . Thnks yaya insha Allah ba Wanda zai ganta ta fad'a cikin murna tukwana ta dauki sayayyar da sukayi tayi cikin gida sai murna take wai yau itace da waya wayarma y'ar yayi Koda tashiga tayi sa a ba kowa Sai inna Nan ta bawa inna Sayayyar da Arman yayi mata tukwana tayi ciki Sai tsallen murna take nan take ta jona ta chaji saida ta cika tukwana ta bud'e tana budeta taga ya turo mata 10gb cikin zumudi ta shiga Ta dinga d'akko apps har su what's app da Instagrams su tiktok saida ta d'auko a ranar ta fara setting d'in komai a Daren ranar ma saida suka kusan raba dare suna shan hira da Arman Saida yaga ta fara jin bacci tukwana yayi mata saida safe . Washegari tunda safe Bayan tayi Sallar asuba harta koma saiga kiranshi saida ya tambaya lafiyarta Daga nan bata koma ba da d'auko numbobin class mates d'inta Wanda take dasu a Littafi duk ta Kwafe ta bud'e what's App duk tayi musu sallama zumudin wayar ya hanata komawa bacci ta shiga nan ta shiga Chan sai wajen 12 ta fito Bayan tayi wanka ta saka Riga marar nauyi gaishe da Inna taje tayi tukwana ta wuce bangarensu. A Babban palour ta tarar da Abba ta duk'ursa ta gaishe da shi ya amsa mata cikin sakin fuska taa cewa "lafiya qalau Mamana ya exams din yau bakuyi ko?" Alhmdllh Abba sai gobe zamu fara neco din "Masha Allah Allah taimaka ku dage kinji Allah muku Albarka" Cikin jin dad'in Addu'ar Abba ta amsa da Ameen tukwana ta wuce cikin bedroom d'in Mamy ta gaisheta tare da yi mata ya jiki ta amsa da sauki. "Mamy ba abunda za a miki bakya buk'atar komai? Eh Aira ba abunda nake buk'ata mai aiki tagama komai Saidai zan aikeki gidan Maman Zarah kawar tau nan dake d'orayi kingane gidan ko?Eh Mamy na gane ta Ai muna zuwa tare " yawwa to Chan zaki da kinje kice Nina aikoki ta baki sak'on ki kawomun ki gaisheta "Sannan ta zaro dubu d'aya a Jakarta tace " gashi kihau napep "to Mamy saina dawo ta fad'a saida taje ta d'auko doguwar Hijab d'inta har k'asa tukwana ta tafi. Ta na zuwa bata jima sosai ba ta amsowa Mamy sak'on ta fito ta na tsaye ta na jiran mai napep wata dalleliyar mota ta faka a gabanta Gaba tayi mai motar ya bita yana mata magiya Dan girman Allah ta tsaya ta saurareshi jin ya had'ata da girman Allah ya sanyata ta tsaya saida ta k'are mai kallo ta ganshi baida laifi dogone baki cike da magiya ya ce " ki shigo na rage maki hanya bai kamata mace kyakyawa kamarki rana na gallarta ba. "Yi tayi kamar bada ita yakeba " Saida ta yi ta had'ata da Allah tukwana ta shiga Dan ta lura zatasha wahalar samun abun hawa nan tayi mai kwatancen Inda zai kaita har kofar gida ya kaita ta fito ta ce Nagode "Me kyau baki bani number ki kuma ba?Kamar ta shakeshi Dan Haushi ta ce. " Bani da waya"Ta juya kenan ta Hango Motar Arman yayi tsaye jikin mota Rungume da hannayensu ya na kallonta "Cikinta ne ya duri ruwa Dan idan bata mance ba yaya Arman ya jima da mata kashedin akan karta yarda ta kula samari ko ya ganta da wani Wanda hartayi mashi alkawarin bazata kula kowa ba gashi idan ma tayi mashi bayanin rage mata hanya kawai yayi ba fahimtar ta xaiyiba . Taku Biyu Arman yayi kamar wani Zaki haka ya nufosu Fuskarnan tashi murtuke kamar bai tab'a Dariya ba ita kanta saida ta tsorata da ganinshi haka wani irin kallo ya watsa mata tare da data mata tsawa ya ce wuce ciki" A firgice ta wuce hada gudunta Dan sosai ta tsorata da yanayinshi "Arman ko kallon saurayin yayi ya ce.............✍🏿 *Share fisabilillah * *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [5/28, 21:04] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............11&12 ....." Malam wa ya baka izinin d'aukar yarinyar Chan a mota?cikin gaskiyarshi saurayin ya ce "Kayi hakuri na ganta ne a hanya ta rasa abun hawa shine na rage mata hanya kuma sonta nake ba son yaudara ba so na Aure Dan tunda na ganta Naji ta tafi da imani na " Wani irin wawan kallo ARMAN ya gallamai ji yake kamar ya shakeshi ta maza kawai yayi ya ce "Matar Aure ce Dan haka karka k'ara bibiyarta ko kaji a ranka kana sonta Wata alaka ta k'ara shiga tsakaninku zan kulleka hope ka gane ya na gama fad'ar haka ya juya ya shige ciki shiko saurayin sosai yayi mamakin jin cewar Matar Aure ce har yana murna yayi Babban kamu cike da jin haushi ya juya. Aira ko ta na shiga Bangaren inna ta yi sai rarraba idanu take kamar wata marar Gaskiya Daga Amma sai inna a palourn Amma nayiwa Inna Karin karatu tsaye tayi jikin Bango ta kasa ko motsawa ta na haka ARMAN ya shigo daga ganinshi.kasan ranshi yayi mugun b'aci kanta yayi gadan gadan kafin ta juya ya chafkota Cikin zafin nama ya murde mata kunne k'ara ta saki Dan taji zafi sosai Karanta ta jawo da hankalinsu Amma cike da masifa ya ce " Uban waye wancen d'in Wanda ya saukeki a mota "Cikin kuka Aira ta ce " Yaya nima bansanshiba Dan Allah kayi hakuri Bazan sakeba ka sakarmun kunne da zafi" "ke harkinyi girman da zakishiga motar wani k'ato ko ?ina alkawarinmu dake daman idan bana nan irin abunda kike ko?k'ara fashewa tayi da kuka ta ce "a a yaya wlh yau dinma tsautsayine" Sakin murdewar yayi tare da wurgata ta durkushe ta fasa kuka mai tab'a zuciya har cikin ranshi yake jin kukan nata ganin irin kukan da take ya sanyashi sanyaya zuciyarshi dan ba abunda ya tsana sama da kukan Aira Shima durkusawar yayi cikin kwantar da murya ya ruko hannunta ya ce "Sorry " Bama ta saurareshi ba saici gaba da kukanta da tayi murza hannayenta ya fara ya ce "Sorry my cutie bazan sakeba kema karki sake kinji kinsan banason ganinki da kowani d'a namiji shiyasa na kasa control d'in zcyta please karki sake in baso kike zuciyata ta tarwatse ba " Rungumeshi tayi cikin kuka ta ce "Bazan sake ba yaya kayi hakuri " Shafa bayanta yafara nan ya fara Lallashinta kamar ba shine ya gama zafutartaba. Inna ko da Amma suna nan suna kallon Ikon Allah "Murmushin jin dad'i inna ta yi ta ce " Allah nagode maka Tabbas mafarkina ya kusa zama Gaskiya Allah cikamun burina na ganin Auren Hajara da Muhajid Tabbas nasan ta silar hakan ne kad'ai za a iya samun sulhu tsakanin iyayensu. Da misalin k'arfe 10 na dare Aira sanye take cikin kayan bacci Nan ta d'auko wayarta ta ta boye cikin locker ta fiddota ta bud'e data nan tayi ta ganin message d'in mutane na shigowa frnds d'inta na mata congrats Number yaya Arman da tayi save da "My yaya ta shiga taga rabonshi da online one.week kenan Hakanan kawai tayi mai slm Dan daman ya fad'a mata shi chat bai dameshiba gwarama Twitter yana shiga yaga labarai. Amma ce ta shigo d'akin Aira bata lura ba maza tayi zata boye wayar da sosai ta tsorata Ta ce " Amma Me kikazo yi"Cikin in ina take maganar murmushi kawai amma tayi ta zauna ta ce "hmm Aira kenan ni bantaba tunanin akwai abunda zaki iya b'oye munba Kinsan tun muna yara bama boyewa junanmu komai kuma muna rik'ewa junanmu sirrikanmu to me yasa kwanannan kike neman chanzamun kinsan dai ko mutum muka kashe bamaiji" Ajiyar zuciya Aira ta sauke tasan hakane tun suna yara basa b'oyewa junansu komai a hankali ta ce "Sorry sis "ya wuce amma ta ce sannan ta Amsa wayar hannun Aira ta ce " Wow Sis 13 ce fa "Dariya Aira tayi ta ce " Kina mamaki ne "Sannan taje ta rufo kofar Dan kar Wanda ya shigo " Amma ta ce wa ya baki 13 Aira "yaya Arman ta bata amsa kai tsare dare da dawowa ta zauna" Arman "Amma ta fada sannan ta ce "Kai amma Allah yiwa Yaya Arman albarka Gaskiya Yaya ARMAN ba k'aramun sonki yake ba Aira" wara idanu Aira tayi ta ce "So fa kikace sis" So kuwa sis Arman ya jima da fara sonki fahimta ce kawai bakiyiba amma Arman ba k'aramun so yake maki ba ko ince kuke yiwa junanku. "kamo hannunta Aira ta yi ta ce " sis kina nufin yaya Arman sona yake"kwarai kuwa Ke wace irice Aira da baki gane so ,baki ganin kishinki b'arob'aro a idanunshi Abunda ya faru dazu ma Kad'ai ya isa ya k'ara tabbatar maki da irin son da Arman yake maki Bayan nan ma alamomin soyayyarki da yake gwada maki a fili suke ba a boye ba Aira ko k'aramun yaro zai iya fahimtar soyayyar dake tsakaninku ni a zato na kinjima da ganewa kiyi tunani ki gani". Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da lulawa duniyar tunani tun daga rayuwarsu ta baya har zuwa yanzu ,me yasa a cikin gidan ita kadai yake sakewa,me yasa ita kadai yake farantawa,ita kadai ya damu da ita,ita kadai yake kishinta ita kadai da dama Tabbas sai yanzu ta gane Yaya Arman sonta yake sosai gabanta ya fad'i kallon Amma tayi tace "To sis ni kuma ina sonshi? Ta k'arasa fad'a cikin sigar shagwaba Dariya Amma tayi sosai ta ce . " ke sis wlh baki rabo da abun Dariya ni zaki tambaya ai zuciyarki zaki tambaya"Turo baki tayi ta ce "To fad'amun menene alamomin so?Alamomin so suna da yawa Aira Amma zanfada maki Kad'an daga cikinsu saiki duba kiga idan kina daga cikinsu " Shak'uwa tayi yawa tana daga cikin Alamun so,damuwa da halin da dayan ku yake ciki "Damuwa da rashinshi a kusa dake koda kuwa na y'an dak'ik'a ne,kishi,shine babbar alamar Zurmiya a cikin soyayya,kyautatawa,ko da yaushe idan kika kalleshi kiji farinciki ya mamaye zuciyarki koda kuwa a waya Ne,jin bazaki iya rabuwa dashi ba duk rintsi duk wuya " ga sunan da yawa Aira kiyi tunani. Shiru tayi tare da Zurmiyawa duniyar tunani Tabbas inko hakane so ta jima da afkawa kogin soyayyar yaya Arman soyayyarma ba ta wasaba cike da damuwa ta ce "Tabbas sis najima da Fara son yaya Arman koma Ince da soyayyarshi na ginu tun bansan kaina ba nakejin Duka abubuwan nan da kika lissafo game dashi ina tsananin sonshi son ma bana wasa ba a da haukana na d'auka duk wannan din shakuwa ce saida kika lissafo nagane Abunda ake nufi da so da Chan shirmen banza na kawai nake sannan ta kamo hannun ta tace. " Sis ya zanyi help me please ina sonshi sosai ya zanyi kin tabbata shima yana sona"Cike da tausayin y'ar uwar tata ta ce "Karki damu sis son da yake maki ya linka son da kike mashi Wanda na gani a idanuna kedai kawai ki bari har zuwa lokacin da zai furta miki" Hakika indai kika samu Yaya Arman sis kingama samun wani jin dad'i a duniya Dan nasan zaiyi wuya a samu Wanda zai kula dake ya nuna maki tsantsar k'auna da soyayya Bayan yaya Arman Dan Arman mutum ne da kowace mace ta sameshi ta more ,Abu d'aya kawai nake Tsoro kuma nake jiye muku Iyayenmu na tabbata Abba Da Daddy bazasu tab'a yarda Kuyi Aure ba inba wani ikon na ubangiji ba shine Babban abunda yake tsoratani"Hawaye sosai Aira take ta ce "Ina sonshi sis Bazan yarda a rabamu dashi ba Abba bazai iya rabamu ba Inajin da sonshi aka halicceni a yanzu bana jin tsoro ko shakkun komai da zan tunkara indai akan a rabamu da yaya Arman ne na gwammace Ranar na mutu". ta fad'a tana fashewa da kuka " Sosai Amma ta tausayawa y'ar uwar tata Rungumeta tayi ta ce "Insha Allahu sis babu mai rabaku sai mutuwa nan tayi ta Lallashinta ranar daki daya suka kwana Wanda Aira baccci kauracewa idanunta yayi sakat tunanin Arman ya hanata bacci da kalaman y'ar uwarta Tabbas tasan indai hakane so to baiyi mata kamun wasa ba yayi mata kamun da ita kanta bazata iya control d'in zuciyarta ba sai Bayan asuba bacci ya d'auketa hakan yasa washegari tayi ranar bacci sai 12 ta tashi. ©©©©©©©©©©©©© B'angaren Arman Shima hakan ta kasance Dan Sosai yakejin son Aira a ranshi Wanda shi kanshi bazai iya kwatanta shi da komai ba Sosai yakejin Haushi idan ya tuno ganinta da yayi da wani a tsaye tunani yake akan ya fito ya furtawa Aira abunda ke ranshi koko ?zata amince dani ko akasin haka? Ta na sona kamar yanda nake sonta ko har yanzu Kallon yaya takemun?Daren ranar bacci kauracewa Idanunshi yayi Yasan son Da yakewa Aira daga Allah ne Dan koda bai shiga zuciyar zukatan masoya ba yaji yanda sukejiba ya tabbata son da yake yiwa Airanshi babu wani mahaluk'in masoyin da zai iya yiwa masoyiyarshi kalarshi ba. Washegari jiki ba kwari ya tashi koda mumy ta tambayeshi lafiyanshi qlau kawai yace mata nan take fad'a mashi Daddynshi jirginsu ya taso tun d'azu sun kusa isowa sai sannan ya d'anji sanyi sanyi a ranshi Dan sosai yakeson ganin Daddy Mummy tace yaje ya shirya nan da 30 minutes zai k'arasa. Arman da kanshi shida Mummy suka taryo Daddy daga Airport Hannun Daddy rik'e da na Arman Dan ko Wanda bai saniba yasan irin tsananin son da Daddy ke yiwa Arman kasancewarshi shi d'aya tilon d'anshi a duniya. Bayan Daddy ya huta yaci abinci Mummy sai Nan nan take da mijin nata Kallon Arman yayi ya ce "Son ya London d'in Fatan ka dawo lafiya" Lfyqlau Daddy "Masha Allah yaushe kuma zaka koma wajen Aikin naka" ran Monday sukace Daddy nama zata zasu d'an bani Hutu tunda kaga su suka turani London d'in nadawo na zata sunbani ko hutun 2weeks ne amma jiya sun kirani suke ceman Monday suke Son na koma"Dafa kanshi Dady yayi ya ce "Toh nan kusa kenan Kaga yau muna Friday to Allah ya kaimu Monday din Ai nasan d'ana jarumine Shiyasa basason suyi missing d'in aikishi ". Murmushi Arman yayi Dan sosai yakejin dad'in yanda Daddy kullum ke kod'ashi shi d'anshi jarumine jajirtaccene tun yana yaro haka yake cemashi shi jarumine Ranar Yini sukayi suna Hira da Daddy Dan ko gidan Inna bai lek'a ba Yau cikin hirar ne yake cewa "Daddy Inna na ta nemanka" murmushi yayi ya ce "Insha Allahu gobe idan na huta zanje na gaisheta. Washegari Daddy da Arman su kaje ya gaishe da Inna shida Security d'inshi Wanda koda yaushe suna biye dashi Arman bai samu ganin Aira ba dan Inna tace mai suna makaranta kasancewar da safe sukaje daga Chan suka wuce asibitoci Dan duba marassa lafiya sannan yayi musu alheri sosai wannan na Daga cikin abunda yasa mutanen jahar suke tsananin sonshi da son mulkinshi danshi mutum ne mai kirki da kuma tausayi ga Gaskiya da rukon amana. Ran Sunday da dare Arman ya je gidan Inna Dan bankwana da Airanshi koda ya fad'a mata zai koma wajen Aiki kuka ta sanya mashi ita batason yake nesa da ita dak'yal ya lallab'ata yace zasu dinga Video call kullum kuma suna waya duk saiyaji bayason ma Tafiyar Dan dai ya zama dole Amma shi Zama da Airan shi ya fiye da mashi komai. Tunda Arman ya tafi kullum cikin waya suke da video call kamar ma suna tare Aira suncigaba da Jarabawarsu ta neco ita da Amma sosai suka maida hankalinsu ga karatunsu har yanzu babu Wanda yasan da wayar Aira a cikin gidan Bayan Amma koda yaushe son Arman Kara ninkuwa yake a cikin Zuciyarta. Ranar da Arman ya cika sati Biyu da tafiya Ranar Su Aira suka gama neco d'insu sai farinciki suke suda class mate d'insu ana tashan hotuna a wayar Aira nan Duk wasu suka amshi numbobinta ranar ji suke kamar karsu rabu daga karshe suka sha kuka musamman Aira ita da frnds d'inta Khady bestynta sosai suka shaku koda yaushe a school tare suke yawo nan sukayiwa juna Alk'awarin ziyartar juna akai akai Sai wajejen 6 suka gama hotuna da bankwana suka fito Bakin gate domin tafiya gida Suna fitowa Wata wulfefiyar Mota Fara me masifar kyau Aira ta gani parke . Ganin mai fitowar ne ya sanyata wara idanu sosai yayi cikin sky blue din shadda ta tasha Aiki hular kanshi hadaddiya wadda a k'alla zata kai 100k Rungume yake da hannayenshi da suke sanye da Wrist din zinare kara wara idanu tayi Dan tabbatarwa da shi d'inne koko Gizau ne shiko kafeta yayi da idanu murmushi kawai yake sakar mata sosai tayi mashi kyau cikin unifoam dinta Light blue Hijab da Dark blue din wando y'ar k'aramar hijab dinta tare da rafar rigarta da ta sauko har gwuiya anyi mata hular hijab d'in da yadin wandon jelar rigarma haka ji yake Kamar ya je ya rungumota Aira ganin da gaske shi d'inne de gabanta ai batasan lokacin da ta saki Hannun Khady ba ta ruga a guje tayi wajenshi tare da Rungumeshi tama mance ta tsiraran mutanen class d'insu dake wajen Cike da murna da farincikin ganinshi ta ce My yaya........✍🏿 *Share fisabilillah* *_Miss Hajo ce*_🤙🏿 [5/30, 23:01] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............13&14 Cikin zazzak'ar muryarshi Mai cike da kassala a hankali ya ce "My Cutie baki girma har yanzu ko kin manta gaban mutane muke kike rungumeni " ya fada kamar bashi yayi maganar ba murmushi tayi tare da sakinshi ta ce "Sorry yaya murnar ganin kace ta sa na ma manta da mutane a gurin" Aike gimbiyace bakya laifi my cutie "Uhm My yaya ammafa Gaskiya kayi surprise Dina da yawa bantab'a tunanin zaka zoba" Ranar graduation d'in Cutie na guda ace banzoba ai Abu baiyi dad'iba yanzu dai ki shigo mu tafi gida ma ida maganar a hanya ko"to my yaya bari naje nakira Amma Tana barin wajen ya zagaya ya shiga mota. Aira na komawa khady tayi mata Dariya tace “ummm kwt har anfara love kenan kice mu fara shiri kece bikin farko a mate “harara ta galla mata tace “sa’idinawa kawai yaya nane to sannan tace muntafi sai mun had’e online “tukwana sukayi hug din juna suka rabu Amma na baya Aira na gaba haka suka tafi a hanya sai satar kallonta yake harsuka isa ba mai cewa uffan sunzo daidai bakin gate din inna sukaga fitowar motar Abba ta gate d’in gidansu cikin faduwar gaba Aira tayi k’asa da kanta dan kar Abba yaganta abunda bata saniba tuni yaganta saida taga wucewarsu tukwana ta dago tana sauke ajiyar zuciya Shidai Arman girgiza kai kawai nan ya gyara parking a waje Amma ta fita tare da cewa thnks Aira zata bude motar taji kulle juyowa tayi ta kalleshi saita sakar mai murmushi shima ya mayar mata tare da cewa. “Ina kika saka wayarki jiya nayi ta kira a kashe”uhm yaya wlh wayarce kasan boyeta nake bana yawo da ita ko tsakar gida dan kar wani yagani shiyasa tana locker d’ita tun jiya sai da zamu sch nadaukota dan muyi hotuna “. “Ajiyar zuciya ya sauke ya ce “nazata ba lafiya shiyasa na taho saida nazo nan nake tambayar haidar a bangaren inna yacemun kuna sch yau kuke last paper “wayyo yaya wai saboda baka sameni ba a waya kawai ka taho i’m sorry “ta fad’a ta na langabar da kai”Shitttt Kin manta bakya laifi komai kikayi daidaine my cutie “sannan ya dauko wata karamar waya daga cikin kwali tana gani ya daga ya saka wani sabon sim card tukwana ya bude ta yace “amshi wannan karamace saikidinga yawo da ita yanda duk sanda na kira zan sameki “murmushin jin dadi tayi tace Thnks my yaya”banson godiyarnan fa daman kinsan yau kuke graduation shine baki sanar daniba “uhm yaya na manta shiyasa “Allah bada sa a Ya fitar da sakamako me kyau kawai yace sannan yace “zan wuce dear baki bukatar komai”Eh yaya bana bukatar komai ganinka ma ya wayadas Bazaka shiga ku gaisa da inna ba “dazu mungaisa ai zanje na hutane kafin gobe na wuce “kamar zatai kuka tace “yaya gobe kuma yayi kusa ai”Zandawo soon yanzun akwai aikin da na baro shiyasa I am sorry gobe idan ba jirgin Safe zanhau ba zanbiyo muyi bankwana idan kuma na samu na safe na wuce kawai “hawaye ne suka fara zubar mata tace “shikenan yaya Allah ya kiyaye ya tsaremun kai “handkerchief ya d’auko ya fara share mata hawayen ya ce “Idan nazo kinamun kuka idan zan koma zandaina yawan zuwa dan bakisan yanda nakejin kukanki a cikin zuciyata ba “cikin sauri ta had’iye kukanta da take shirin cashews’ “sorry yaya bazan sakeba banson kana nesa dani ne shiyasa idan ka tafi yaushe zaka dawo “shima ji yake kamar yayi kukan yace “nafi kowa bukatarki a kusa dani dan bayanda zanyine next week insha Allah zanshigo na kwana biyu “to my yaya Allah ya maidoka lafiya “ki kulamun da kanki kinji my cutie “murmushi tayi tace “kaima ka kulamun da kanka sun dan taba hira kadan tukwana yayi mata bankwana ya wuce ji suke kamar karsu rabu da juna. Aira koda ta shiga gida bata iske kowaba sai Ummy da Haidar da amma da suka dawo tare “Ya Ummy ina y’an gidan naga ba kowa bangaren inna ma bata nan”ta fad’a tana Waige waige “Suntafi kai Mamy asibiti “wara idanu tayi tace “Asibiti kuma me ya sameta “Haihuwa zatai “langabar dakai tai tace “wayyo Allah sauketa lafiya ranar bangarensu ta kwana sai addua take Allah sauke mamy lafiya dakyal bacci b’arawo yayi awon gaba da ita. ************ Arman kai tsaye guest house dinshi ya wuce dan yasan ya biya ta gida Mummy saisunji dalilin da yazo to yace musu saboda Aira ko me hakan yasa ya wuce chan bayan yayi wanka t-shirt kawai ya sanya da gajeran wando fresh milk kad’ai yasha tukwana yabi lafiyar gado dan akwai gajiya sosai tattare dashi yau jinshi yake cikin farinciki saboda ya hadu da Airanshi lumshe ido yayi a hankali ya ce “I love her so much Cox she’s beautiful “tunowa lokacin da yaganta cikin unifoam yake kyakkyawar fuskarta kawai yake ta hangowa da yanda take sakar mai murmushinta mai narkar da zuciya tuno lokacin da ta rungumeshi yayi ji yayi tsikar jikinshi ta tashi kamar wanda aka tsunkula haka ya zabura rumtse idonshi yayi sosai kafin ya bude su mikewa yayi ya dauko wani hotonta sosai tayi kyau cikin Wata black laffaya daga gani hoton bai jima ba kafe hoton yayi da idanu bako kiftawa kafin ya fara shafa hoton yana murmushi shi kad’ai yace “I love you my Aira ina sonki sosai Airata ki soni please ko kadan ne yafada yana marairaicewa (🤣nikam nace Arman karfa ka haukace)rungume hoton yayi a haka baccci me dad’i ya daukeshi cike da mafarkin Airanshi. ********* Washegari Su Aira su na bacci Ummy ta tashesu cikin murna tace ku tashi yanzu mama ta kira Mamy ta haihu “Aira kamar an tsikareta haka ta tashi tace “da gaske Ya Ummy me ta Haifa”nima ban tambaya ba yanzu dai Mama ta kira tace da asuba ta haihu mu gyara gidan tare da Laure(yar aikin su)ba jimawa zasu dawo. Cikin murna Aira ta tashi da dinga murna nan suka gyara gidan wajejen 12 su Mamy suka dawo gida inna dauke da jaririn mamy ko duk tayi lakwas Aira sai murna take ganin k’anin nata shima fari me kyau dan duka d’iyan Mamy su ukkun fararene Haidar ne ma baiyo hasken mamy sosai ba nan yan barka da yan uwa suka fara shigowa. Aira ko bayan flowers ta koma domin kiran Arman taji ya tafi ko zaizo dan taga har anyi la’asr tana sand’o ta ciro k’aramar wayar da ya bata daman ta hardace number dannawa kawai tayi saitaga yamayi mata save da My yaya murmushi tayi tanajin karason Arman na ratsa kowani sassa na jikinta saida kiran ya katse kafin ta kara kira taji kiranshi ya shigo murmushi jin dadi tayi tare da kissing d’in wayar tace I love you my yaya tukwana tayi picking..........✍🏿 Manage ba yawa 😊 Share saboda Allah 👏 _*Miss Hajo ce_*🤙🏿 [5/30, 23:01] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............15&16 Daga dayan bangaren Arman ya ce "Hello Cutie ykk " lfyqlau yaya harka tafi ko"ta fad'a cikin sigar shagwaba "Yanzu haka ina Abuja my cutie jirgin 9 nabi shiyasa bansamu nazo nayi maki bankwana ba". "Ayya to Sannu ya gajiyar hanya "Alhmdllh ya fad'a yace Yadai Naji kamar kina cikin farinciki my cutie Shakomun " Dariya tayi jin ya ce Wai shak'omun ta ce "Yaya Mamy ta haihu fa ". Daga bangarenshi kamar tana ganinshi ya zaro ido ya ce "da gaske cutie Ah dole muyi farinciki me muka samu" Namiji ni nama zaci mace zata Haifa na samu y'ar uwa kawai sai ta haifi namiji"ta fada tana turo baki . Dariya yayi har tana jiyowashi cikin waya sosai k'uruciyarta ke burgeshi komai ya fito daga bakinta fad'a kawai take cikin shagwaba ta ce " Dariya ma kakemun ko"Sorry my Beauty Kece kikaban Dariya kince ke mace kikeso ko?"Eh yaya ni mace nakeso " To yanzu shikenan tunda Mai faruwa ta faru saimuyi addu'ar idan Kikayi Aure Haihuwarki ta farko ki haifo mana mace mai kama da ke ko?wara idanu tayi kamar yana gabanta kunya duk tabi ta lullubeta ga yanda yayi maganar ya d'an kulle mata kai "Ki haifo mana?sai muyi addua?Aranta take maimaitawa me yake nufi ? tsinkayar muryarshi tayi da cewa " Yadai cutie kikayi shiru"Uhm "kawai tace duk kunyarshi ma takeji" Shiko bangarenshi da gangan yayi mata har yanzu yana so ya furta mata Kalmar so amma ya kasa hakan yasa ya yanke shawarar nuna mata k'arara yanda zata gane ko baice yana sonta ba ta d'auko hanya. Jin tayi shiru ya sanyashi sauya maganar da cewa"Ki d'auko mun hoton kanan namu ki turoman"Ajiyar zuciya ta sauke jin ya sauya maganar ta ce "To yaya Anjima zand'aukarma" Hango Ummy tayi na nufo wajen cikin Sauri ta ce "Yaya sai anjima Ga ya ummy nan ta maza ta katse wayar ta boye bayanta. " Ummy ko tab'e baki tayi Dan ta ganta sarai ta ce "Kidaibi A Sannu rawar kan nan taki karta kaiki ta baroki Manya ma Abba ya bida bare ke tsirit" Aira ko kauda kai tayi ta na gunguni Saida taga wucewarta tukwana ta mik'e ta sanya k'aramar wayar a jikinta tayi bedroom d'in Mamy ta k'ara yimata ya jiki ganin d'akin da mutane ya sanya ta juya ranar duk sanda taso ta dauki jaririn hoto a wayarta ta turamai gagara tayi. Sai washe gari wajen 11am taje gaishe da Mamy ta tarar da Ita ta na Toilet ga Alamun wanka take kuma jaririn na kan Bed shi kadai cikin Sauri ta Ruga part din inna ta ciro wayarta dake locker ta boyeta a jikinta koda ta koma tayi sa a har lokacin Mamy wanka take cikin Sauri ta fiddo wayar ta shiga d'aukar babyn hoto a snap sosai yake yin kyau. Cikin Sauri ta bud'e data ta shiga ta turama Arman hotunan Sannan ta shiga status tayi status daman bata d'auki number kowa na gidansu ba Dan haka ba Wanda yasanma tana da waya bare har Susan tana chat tana gama dorawa ta sauka ta maza ta kira Arman tana lek'awa Kar wani ya shigo ta na kara wayar a kunne yana d'auka cikin Sauri ta ce . "Na tura maka hoton ka hau ka gani " rikicewa tayi ganin Fitowar Mamy tayi tsaye bakin bathroom d'in ta na kallonta maza tayi cikin Rashin gaskiya ta kashe kiran Tare da Boye wayar a bayanta "Wace waya ce na gani a hannunki?ta tsinkayi muryar Mamy " . kafin kace me idonta sun cika da hawaye ta fara in ina karya ma take so tayi abun bata saba ba ta kasa "Mamy ta daka mata tsawa ta ce " nace wayar uba waye na gani hannunki mik'omun wayar Mamy ta fad'a ta na nufota Tashi tayi tana ja da baya ta ce"I m sorry Mamy bazan Sake ba"me nace kinyi da zakice bazaki sakeba kuma wlh na k'ara magana baki mik'omun wayar nan ba zanmiki abunda baki tunani"Tuni Aira ta fara Kuka. tsawa Mamy ta k'ara daka mata ba arziki ta mik'a mata wayar ta na yayyarfa hannu kamar wacce aka daka "jujjuya wayar Mamy ta fara cike da mamakin ganin wannan tstsadar wayar Dan taga a Instagrams ana tallarta kudinta sun haura 700k " Kallon tuhuma ta kalli Aira dashi ta ce "Wayar wacece?Tawace Mamy Dan Allah kiyi hakuri kar Abba yaji " . ta fad'a cikin kuka "Salati Mamy ta rafka ta salamce ta ce " Na shiga Ukku ni Rahama Aira lalacemun kikeso kiyi Ki rik'e har wayar kusan 1 million a gidan nan batare da sanin kowaba Aira kunyata ni kikeson kiyi uban wa ya baki wayar wannan me tsada kuma banason kimun k'arya wlh kika kuskura kikamun k'arya saina lillisaki kuma na kira babanki na fad'a mashi maza fad'amun ubanwa ya baki yanzunnan " Tuni cikin Aira ya fara d'urar ruwa kuka ta k'ara fashewa dashi to ita me za tacewa Mamy Arman zatace ya sai mata kowa ..........✍🏿 *Tofa Fans ku taimaka ku bawa Aira shawara ta shiga matsala wa zatace ya saya mata waya 😰😢gaskiya ni harta bani tausayi* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/1, 18:30] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION* 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............17&18 ......Bazaki d'aga baki kimun magana ba dukanki nayi da zakumun kuka"Mamy ta fad'a cikin b'acin rai" Aira ko kuka kawai take ta na yarfe hannu Dan tasan Mamy bata fiya mata haka ba Dan bata iya b'acin raiba. "Okay bazaki fad'amun ba kenan tunda ni kin rainani bari na kira Abbanku saiki yi mishi bayani ta fad'a tana d'auko wayarta" Aira kamar wacce aka zabura haka ta zabura tareda Rugawa wajen Mamy ta rik'e hannunta ta na kuka ta ce "Mamy Dan Allah karki fadamashi zan fad'a maki wlh y'anzu Yaya Arman ya sayamun" ta k'arasa fad'a ta na hawaye" Arman?Mamy ta maimaita tana mata wani irin kallo,Saurin sakin hannun Mamy tayi tare da ja da baya ta ce "Dan Allah Mamy karki dakeni bazan sakeba" Arman Mamy ta k'ara maimaitawa zaunawa bakin gadon tayi tana jujjuya wayar na y'an sakanni kafin da d'ago ka kalli Aira dake tsaye tana kuka ta ce "Shi Arman d'inne zai sai maki wannan wayar a wani dalili?Wlh Mamy shi ya sayamun". " chabd'i Mamy tafada tukwana ta ce "Fad'amun yanzunnan wace alak'ace ke tsakaninki dashi Dan ubanki ,meye ke tsakaninku " Mamy wlh ba komai kawai zumunci muke dashi Mamy kin mance Yaya na ne fa"Ubanki ke da yayan Duka su sauran y'an gidan ba y'an uwanshi bane ko ke kad'aice y'ar uwarshi alak'ar dake tsakaninki dashi suma haka take su me yasa bai saya musu wayar ba saike kad'ai ya zab'a ya sayawa". kasa tayi ta kanta tana hawaye ta ma rasa wace amsa zata ba Mamy "koma meye ke tsakaninku ai zamuji sannan ki gaggauta mayar mashi da Wayarshi muddin kina gujin b'acin raina marar jin magana kullum kinfison ki dinga jawomun magana yanzu da Abbankune yaga wayar nan da ni kaina basaikinjamun ba ki mayar mashi da Wayarshi ko ki kiramunshi ni nafada masa yazo ya Anshi abunshi bansan d'iyan iskanci idan kuma ba haka ba sainayi kwatsakwatsa da wayar". cikin Sauri ta d'ago ta ce "a a a Mamy wlh bama saikin kirashi ba zan mayar masa da yadawo insha Allahu nagode da bazaki fad'awa Abba ba " Tsaki Mamy taja ta mika mata wayar tare da d'aukar jaririnta da ya fara tsala kuka Aira ko cikin Sauri ta amshi wayar ta sakata A siket ta fice daga bedroom d'in ta na fitowa palour ta tarar da Ya Umar da matarshi (Babban yayansu ss ne ya na aikine a Kebbi tare yake tafiya da matarshi khadija sai idan sunzo su sauka gidansu))cikin murna tace Lah ya yaushe kukazo"Murmushi yayi ya ce "Yanzu muka Iso little sis " sannunku da zuwa yaya Anzo lafiya ya hanya "Alhmdllh ya Rashin ji ya na nan ko yayi sauk'i " Dariya tayi ta ce "Yaya ai ni bana Rashin ji " Zadai kidaina y'ar gidan Inna "kallon Khadija tayi ta ce " . Ina yini Aunty"Lafiya qalau "ta fada a takaice tab'e baki tayi Dan daman Chan haka halin Matar Yayan nasu take ba mutuncin kirki ya isheta ba shiyasa ma ko gidanta basa zuwa " Bari naje na fad'awa su Mama kunzo ". "Aira tafada ta na nufar d'akin Mama da Mamy duk ta fad'a musu zuwan su ya Umar a tare suka fito su Mamy na musu barka da zuwa Suka amsa cikin sakin fuska har khadija Dan Duk iskancinta bata fiya yiwa su Mama da Mamy ba khadija ce Ta amshi jaririn hannun Mamy tare da yiwa Mamy barka tace " Allah raya "nan Shima ya Umar yayima Mamy barka Daman sunji haihuwar ne yasa suka taho Aira ganin Mamy da Mama sun d'auki hankalinsu ya Umar yasa tayi saurin fita ta nufi part d'in Inna. bedroom d'inta ta shige tare da rufewa ajiyar zuciya ta sauke ta ce " yau na tsallake rijiya da baibai da Mamy ta fad'awa Abba Aida na shiga ukku"kiran Yaya Arman tayi kamar zatayi kuka ta fad'a mashi komai kuma Mamy ta ce Wai na maido maka wayar ta fad'a kamar zatayi kuka". Daga bangarenshi ya ce "bana kyauta a maido mun Kuma bana kyauta na amsa ko wani nayiwa bare ke Dan haka karma ki maidomun " To yaya ta ce fa Ta Kara ganinta Fasa ta zatayi kuma ina tsoron karta Fad'awa Abba "Arman duk Haushi ya isheshi yana jin haushin yanda iyayen Aira ke nuna mai kamar ba Wanda bai had'a komai da ita ba kamar ba kanwarshi ba Mamyn ma da yake ganin dama dama a Wajenta itama nema take ta kwatsa" . Ya fada cikin ranshi a fili ko tsaki yaja baimasan yayi ba ya ce "Kinji dai abunda na fad'a sanin kanki ne bana magana biyu ta rage ruwanki ko ki yadda ita ko kiyi sadaka da ita ko ki fasata komai kikayi taki ce Dan haka karki k'aramun magana akan dukkan wani abu da zan baki ko na baki hope kinfahimta " Cikin sanyi Aira ta ce "Na gane Yaya yi hakuri Bazan sake ba nasan ranka ya b'aci Naji kamar kana fad'a "saiyaji ta d'an bashi tausayi yasan halinta Sarai akan wannan D'an abun saita yini ta na kuka hakan ya sashi kwantar da murya ya ce . " raina bai b'aci ba my cutie yaya za ayi my Aira ta ta b'atamun rai Y'ar lele na ai bakya laifi "Ajiyar zuciya ta sauke ta ce " Uhm "Shima Uhm" din ya mayar mata yana mata Dariya ita ma dariyar tayi tanajin sanyi Cikin zuciyarta "ARMAN ne ya ce " Naga hoton k'ananmu yayi kyau naga ma kamar yaso ya sato kamannin my cutie d'ina kodan ya samu ya d'anyi farinjini wajen y'an mata ammafa my Cutie d'ina ta fishi kyau nesa ba kusa ba . "Dariya Aira tayi sosai ta ce " Allah my yaya kace na fishi kyau"Eh mana ki daina hadamun kanki dashi ma "Dariya tayi ta ce " kai yaya Shima fa yana da kyau sosai"idan babu ke ba amma idan Dake musamman kuka Kara fuska mummuna zakiga ya koma kin manta Kyanki dishe kyan wasu yake "Dariya tayi sosai ta ce " to ni da kai kuma wa yafi kyau"Shima murmushi yayi ya ce "Ni mana Aini na taimaka maki da har kyan naki ya fito idan ba haka ba Ai kema kyan naki da baikai haka ba nine na taimaka maki" Cikin shagwaba ta ce "Kai yaya wlh nafika kyau" Dariya yayi sosai take burgeshi idan tana shagwaba hakan yasa ya biyeta sukayi ta gardama yana mata Dariya saida suka kwashe kusan awa Ukku suna waya batare da sun gaji da Hira ba daga karshe ma Video call suka koma Dan yau Arman baida aiki yana gida Nan Aira tayi tamai labari Dan rufo d'akin ma tayi Dan kar wani ya shigo ko da zasuyi salla kin kashewa sukayi kamar suna tare Ranar haka suka yini Dukansu sai farinciki suke Dan Aira harta manta ma da Maganarta da Mamy koda zasuci abincin dinner tare sukaci Shima ya zubo nashi ita ma ta zubo nata suna ci suna kirga spoon Din da kowa yayi ta waya dukda basu da cin abinci sosai ranar saida sukaci sosai. har wajen 11pm suna video call idan zatayi wani abun taje tayi ta dawo Shima haka Saida yaga bacci ya d'auketa murmushi yayi yana kallonta ta waya Yajima yana kallon yanda take baccin yana karajin sonta na ratsa kowani sassa na jikinshi saida yaga wayar ta birgima Alamun baccin nata yayi nisa tukwana ya kashe ganin baya ganinta ranar dukansu kwanan farinciki sukayi batare da tunanin wata damuwa ba. Ana jibi suna Aira na bangaren Inna wajen la asr ta fito ta nufi bangarensu tana shiga taga Yaya Aysha na fitowa daga mota driver na fito mata da akwatinta Aida gudu Aira ta Ruga ta Rungumeta Itama Aysha Rungume kanwar tata tayi cikin muryarta mai cike da iyayi ta ce "I really miss you my Fav sis " Itama cikin murna Aira ta ce Miss uh 2 my Fav Aunty da bakinan gidan ba dad'i nafi kowa rashinki "Murmushi Aysha tayi ta ce " Ai yanzu nadawo Sis mundaina Rashin juna ko"Gyada mata kai tayi ta na amsar hand bag d'inta ta rik'e mata Aysha tabs driver umarni ya shiga da akwatinta ciki tana dafe da Aira suka nufi haryar ciki Sai murnar ganin y'ar uwar tata ta ke Aira ta ce "Aunty Ya malesia d'in wai kina nufin harkun gama karatun gaba d'aya " Alhmdllh sis karatu kam mun kammala sai Kuma bautar Kasa burin Abba yau ya cika "Cikin murna Aira ta ce " Wow congratulations sis ta fad'a tana Kara Rungumeta Itama Rungumeta tayi ta ce "Thnks my sis yanzu kuma saura ku munyi waya da Ummy ai kwanaki take fad'amun kun kammala s s c e d'inku sai jiran result. " Wlhko Aunty mungama kai wlh Aunty Ummy bata da kirki duk lokacin da nace mata ta had'ani dake ko a waya Ne wlh kiyawa take Dana dame ta ma cewa tayi "karna k'ara damunta tunda ba waya ta bace nima nayi zuciya nasayi wayar kuma wai kinma sauya layi itama bata dashi" Dariya Aysha tayi ta ce "Kai Ummy ta na nan da halin nan nata kenan Wai har yanzu Abba bai baku waya ba ki ce dai har yanzu tsautsatsauran ra ayin nan na Abba na nan na Sai an Je university idan yanzu baku fara rik'e waya ba fisabilillah yaushe zaku rik'e Baku sanin halin da duniya ke ciki Gaskiya Abba yanzu An waye y'an 10 years ma suna rik'e waya bareku ". murmushi kawai Aira tayi batace komai ba shiyasa duk yayyinta tafi son Aunty Aysha jininsu yazo d'aya sosai ga tana mugun sonta tana tunanin yanda Aysha ta k'ara wayewa Dukda daman a waye ta tafi amma k'asar wajen nan da taje karatu ka k'ara kilewa....✍🏿 *Share plx* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/1, 22:52] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............19&20 Suna isa a palour suka tarar dasu Mamy da gudu Aysha taje tayi hug d'in Mamy da Mummy tana musu iyayin tayi missing d'insu Mamy na murna tana mata oyoyo" Sai sannan Aysha ta lura da mutanen dake palourn wasu baki ta gaishe su Ganin jariri a hannun wata ya sanya ta kalli Aira ta ce "Sis wa ya haihu" . Mamy Airata bata amsa "wow Kice nazo A daidai Allahsa dai ba ayi suna ba Kuma shine ko a fad'amun sannan taje ta amshi jaririn tace " wow ammafa yaso yayi kama da sis Aira "Haka kowa yakecewa Cewar Mamy Mama ko Kallon Aysha kawai take da shigar dake cikinta K'ank'anin kaya ne jiens da Riga danma bata da jiki hakan yasa basu d'ame ta ba ga wani uban glass da ta dageshi saman goshinta . Aysha black beauty ce tana da kyau ba fara ba ce Amma bata da bak'i sosai irin choculate colour d'innan amma daga ganinta kasan akwai iyayi da malle " ita Mama duksai kunya ma ta kamata Ganin da mutane itako Aysharma ko a jikinta hakan yasa Mama ta fara aika mata da Harara ganin batasan da ita ba yakeba ya sanya Mama kyaleta saida tagama iyayinta tukwana taja Aira sukayi Bedroom d'insu . koda su Ummy da Amma suka ganta suma sai murna suke suna daka tsalle suna murnar ganinta Aira tace "Su daina karsu b'alla mata yaya" suna haka Mama ta shigo ta kalli Aysha ta ce "Ke yanzu Aysha ba kunya haka kika ketaro tundaga wata k'asa kikataho a haka kamar ba y'ar musulmi ba " Aysha na tubure fuska ta ce "Haba Mama daga dawowata Ko Sannu da zuwan kirki fa bakimun ba zaki fara mun fad'a me shigar nan tayi kuma" . Mama ta girgiza kai ta ce "Ai daman Nasan sai Abunda yayi gaba a nan ma ya aka k'are bare anturaki wata k'asar da ba uwa ba uba ba mai tsawatar maki dole likkafa taci gaba shiyasa tun farko banso Alhaji ya tura ki wata k'asa karatu ba to wlh mu nan ba Chan bane Dan haka kar in Kara ganin kinyi wannan shigar kinfito wannan shigar ko tsakar gida Inda kunya kinyita bare waje idan kin gama hutawa kije abincinki na dining Mama ta fad'a tare da barin d'akin. Aysha gunguni tayi kasa_kasa saida Mama ta fita ta ce " Aifa nadawo wlh su har yanzu sunk'i su waye mu Chan ba ruwan wani da wani ina laifin wannan shigar ta fad'a tana tab'e baki "(nikam hajjo nace ikon Allah Ayshar nan za Aje da ita ). Bayan ta fito daga wanka ta shirya cikin Wata doguwar Riga (Abaya)mai shegen kyau maron kallonta Aira tayi ta ce " Wow My Aunty kinyi kyau"Lakutar kumatunta tayi ta ce "Thnks kanwa Sannan ta fiddo wata irinta ta mik'awa Aira ta ce " ga taki nan daman tare nayi mana Anko ki shirya kafin na gama cin abinci zamu fita outing ". Tsalle Aira ta daka tare da Rungumeta ta ce " Thnks Aunty shiyasa nake sonki da yawa tukwana ta maza ta cire kaya ta d'aura towel tayi bathroom danyi wanka Amma ce da Ummy suka hade baki wajen cewa "mu ina namu" Bansayo da kuba da gani sai Besty na zamuyi ankon"Amma tace "Aifa kindawo yanzu za a fara gwada mana wariyar da aka saba Ummy ko taja k'aramun tsaki ta ce " ko kunya wai wani bestynta k'anwarta ta Ukku amma kamar wata sa arta duk saisun rainaki". murmushi Aysha tayi ta ce "Kede kina nan da halin nan naki na shegen son girma to meye a ciki kanwar tau ta ukkun saime ke nan gani kike kinma girmi kowa To nidai karkimun Rashin kunya tunda ba a girmanba " Tab'e baki Umny ta yi ta ce "Ni mancewa ma nake kingirmeni Duka shekara biyun da wani Abu sannan ked'in mate Dina ce Ke bare kice kinfini aji nima dai yanda kika gama Degree d'innan nan da sati Ukku zan kammala saime banbancin kinje Malesia ne ni kuma ina B U K saime a ciki". Dariya kawai aysha tayi ta wuce parlou ta ce "Kanki akeji ta na fita ta tarar da bak'in duk sun tafi kai tsaye dining ta nufa taci abinci me rai da lafiya Aira ko cikin Sauri ta fito daga wanka ta shirya cikin doguwar Riga irin ta Aysha sosai tayi mata kyau ta fito kamar wata balarabiya sai baza k'amshi take hoda da kwalli kawai ta shafa sai lipstick sosai tayi kyau ta dansa madaidaicin takalmi marar tsawo ta yafa k'aramun belt din Rigar kwantaccen gaban gashinta ya fito wa iya zubillahi zo kuga yanda Aira tayi kamar wata balarabiya Tana fitowa ta tarar da Aunty Aysha ta kammala cin abincin kallonta tayi ta ce ". wow my kanwa kinganki kuwa "Sai sannan su Mamy suka Kalleta Suma sunga tayi kyau Mama tace "wannan gayu haka sai ina kuma" Murmushi tayi ta ce "Mama Aunty Aysha zan raka Unguwa" Mama tace "Tofa daga dawowa bako hutawa k'afar yawo" Mama ganin gari ne fa kawai zanyi"ta fad'a ta na ruko Aira ta gyara mata yafa Belt din nata ta ce "Yau akwai kashe hotuna sis ta fad'a suna Tafawa" Mamy ce ta ce "Aifa K'auna ta dawo Aysha da Aira tsohuwar zuma" Dariya Aysha tayi ta ce "Fad'i da k'ari Mamy Aini duk ita kadai nafi missing" . Mama ko ta ce "Ai Halin ne yazo d'aya shiyasa " dariya Mamy ta ce "Kuma Hakane yaya Halin Aira da Aysha duka d'ayane ba abunda Aira ta rago na Aysha Dariya Aysha da Aira sukayi. suna haka Abba ya shigo palourn Bayan ya zauna har k'asa ta duk'ursa ta gaishe da Abba ya amsa sai farinciki yake ya ce " An kammala karatu ko Aisha Allah ya miki albarka Allah baki abunda kike nema duniya da lahira yanda kika farantamun Allah baki masu farantamun miki nagode da yanda kikayi mun biyayya akan komai baki bani matsala ba karatun da na turashi shi kikayi ba tare da kin bak'antamun ko an tab'a kawomun koken ki ba Ko ki biyewa samari dukda dai ba yawo nake dake ba Naji dadi sosai Allah maki albarka" "Ameeen Aisha ta amsa sosai tayi farinciki da Addu'ar mahaifin nata sannan ya ce " Kamar yadda Yayyunki Maryam da umar Bayan kammala Degree d'insu na kaisu Aikin Hajji da umrah insha Allahu kema ki shirya zaki Fara zuwa umrah kafin lokacin aikin Hajji yayi Allah maki albarka sosai Aysha tayi farinciki marar musaltuwa ta ce "Abba nagode nagode Allah saka da alkhairi Allah ya k'ara budi" Aira ko tana tsaye duk tayi sanyi tasan Abba da ita ya ke na cewa "aysha bata bashi matsala ba Dan haka yakece ma Aira idan yana mata fada yace " ita ce Ke neman bashi matsala cikin y'ay'anshi . Amma hakan bai hanata taya y'ar uwarta ta farinciki ba jita ke Daman Ita "Saida Abba ya gama sanyawa Aysha albarka tukwana ya tashi zai shige ciki A hankali Aira ta ce " Ina yini Abba"ba tare da ya Kalleta ba yace "Lafiya" Dan tun sanda yaganta motar Arman Bayan dukan da yayi mata amma ta raina shi bata daddara ba yanzu ya tsaya yana tarasu ita da shi ya ga gudun ruwansu. .sosai Aira bataji dad'in yanda Abba ya amsa mata ba saida ta Goge hawaye Aysha ma saida tayi mamaki Dan tasan yanda Abba keson Aira dukda Abba bai gwada banbanci tsakanin y'ay'anshi Amma a yanda tasani yafi nunawa Aira so saisuka Alak'anta hakan Da sunan mamansu ne da take dashi "Saida suka fito Aysha ta ce " sis ya naga Abba bai kulaki ba "Wlh nima bansaniba Aunty " . tafada tana Goge hawayenta "makullin key Aysha ta amsa hannun driver ta tuk'a su suka tafi Aira na front seat gidan kawar Aysha suka fara zuwa basu jima ba Suka fito tukwana Suka wuce Wurin wani shak'atawa sosai Aysha tayi ta kashe musu selfie da wayarta iPhone 12 pro ita da Aira sosai suke kyau kamar wasu twins saidai kowa ya gansu yasan Aysha ta girmi Aira a shekaru Bayan nan su shiga wajen shan ice cream suna cikin sha wayar Aysha tayi ringing. ta d'auka ita dai Aira bataji me Dayan bangaren aka ceba saiji tayi Aysha ta ce " Okay Baby ka shigo zaka ganmu da marun Abaya"bata katse wayarba suka hangoshi yana nufo su aysha murmushi ya kasa barin fuskarta harya karaso ya zauna chair din kusa da ita. "Aira dai na kallonsu kawai take Shima ba laifin yana da kyau gashi Daga gani kamar akwai Naira Aysha cikin farinciki tace" Nayi missing naka my baby Tunfa sanda ka kawomun ziyara rabon da muga juna kusan 5months ta fad'a tana shagwaba "Shima cikin so da k'auna ya Ce " Miss you too my prince's kinsan yau ba cikin k'aramun farinciki nake ba na ganinki sannan ya kalli Aira da take kallonsu ya ce . "Dear ko ita ce k'anwar tamu da ake ji da ita " Aysha tace "Eh baby itace " Aira ko "yafada yana kallon Aira murmushi tayi ta ce " Eh ina yini "Lafiya qalau kanwarmu y school gsky yayarki Naji dake fa kusan kullum saitayimun maganarki" murmushi Aira tayi ta ce "Ai nima ina ji da ita sosai " Aira najin Aysha da Saurayinta na zuba love ita dai cikin ranta mamaki take daga karshema barin wajen sukayi suka koma Dan nesa da ita tana nan zaune rik'e da wayar Aysha taji wani yayi mata sallama ba tare da ta d'ago ba ta amsa . "zan iya zama Hajiya" Ba matsala ta fad'a ta na kauda kai"y'an mata bazaki kalleni ba "yafada yana murmushi kamar bazata d'ago ba sai kuma ta d'ago ta ganshi wani dogo mai matsakaicin jiki ya sha shaddarshi me kyau. kauda kai tayi yana b'ata rai Dan bata son takura " ina yini Hajiya Sannu da hutawa"Lafiya "ta fad'a ta na kauda kai" Kamar bazai magana ba saikuma ya ce "Tun d'azu na hangoki ina son nayi maki magana kikamun kwarjini na kasa Sai yanzu dak'yal nayi shahada na taho Dan na fad'a maki abunda ke cikin zuciyata Gaskiya tunda nake bantab'a ganin macen da ta burgeni ba sama dake nayi yawo wurare da dama Amma bantab'a cin karo da macen da sace zuciyata kai tsaye ba idan ba ke ba fatan baza a watsamun ruwa a k'asa ba za a amshi tayi na hannu bibbiyu" . Aira ji tayi kamar ta shakeshi Dan Haushi tace "d'an naci a zuciyarta amma a fili cewa ta yi" Kayi hakuri ni bana soyayya a gida an hanani"Saiki fara a kaina na tabbatar zan sanyaki farinciki "tsaki taja cikin ranta ta ce " maye "Nan yayi ta mata magana da magiya tayi banza ta Kyaleshi Suna Haka Aysha ta dawo ita kad'ai ga Alamun saurayin nata ya tafi Tana ganinta Aira ta mik'e ta ce " Aunty Aysha mu tafii". Kallon Aysha saurayin yayi ya ce "Auntynmu ina yini" murmushi Aysha tayi ta ce "lafiya qlau brk da hutawa" yawwa Aunty gwarama da Allah ya kawomun ke nasan zaki taimakamun ki shawomun kanta tun d'azu nake nan amma ank'i bani dama gimbiyar tawa dai ga alama akwai mulki "Dariya Aysha tayi ta ce " karka damu Insha Allahu zanmata magana haka take "kai amma nagode Wlh Aunty kinyi taimako amma ya sunan gimbiyar tawa" Hajara Amma ana ce mata Aira"wow so sweet name "nikuma suna na ABUBAKAR YUSUF MADUGU”ni D’an sokoto ne nazo bikin aboki na ne ni bakone a garin nan. Ah Babban suna sunan Abbanmu"cewar Aysha " kice ina da manyan y'ay'a to yanzu Aunty yaza ayi naga kamar Sauri kuke zaku wuce ko zaki taimakamun da number ta"wlh bata da waya yanzu kam"to Dan Allah kozaki taimakamun da taki saimuyi magana"ba matsala Aysha ta fad'a tare da karantomai number ta. rafar y'an 500 ya Aje musu Aysha taki amsa dak'yal ya samu ta amsa tare da mashi Godiya ya wuce "Aira ko duk Haushi ya isheta saitajima mutumin duk ya bata Haushi ga haushin Aunty Aysha da ta biye mai. A mota Aira ta kalli Aysha ta ce " Aunty wannan Wanda yazo wajenki d'azu waye"baby Abdulkarim kenan Boy friend d'ina ne kuma mijina insha Allah tafada tana murmushi wara idanu Aira tayi cike da mamaki ta ce "To Aunty yaushe har kuka hadu keda kika tafi karatu kuma nasan kafin ki tafi Abba baya barin kowa zance " Dariya Aysha tayi ta ce "Aira kenan kede kawai ayi sha ani amma ni tun ina s. S three nake soyayya ta a b'oye kawai dai ina nunawa Abba ne amma soyayya ta nake ke yanzu fa kai ya waye akanme ace Y'an mata gand'ama gand'ama damu ace ba samari yaushe garin zai waye my Abdul a Airport muka had'u dashi tun lokacin tafiyata karatu ta farko tun daga lokacin muke soyayya ina sonshi sosai Shima haka yana ziyarta ta chan akai akai munshaku sosai Dan tun bayanzu ba yakeson muyi aure na ce yayi hakuri ya jira lokacin da Na gama karatu gashi yanzu kuma alhmdllh yanzunma maganar ce mukayi nace ya samu Abba yanzu ba wannan maganar ba Wannan Sadiq din yana da hankali wlh sosai ga nutsuwa ki nutsu Kuyi soyayyarku saina dinga had'aku kinji kanwata baki da matsala dani ba meji". Turo baki Aira tayi ta ce "Ni Gaskiya Aunty kibar zancenshi ni baimun ba bama wannan ba kinsan Abba ya hanamu nikuma bazanyi Abunda ya hanaba Gaskiya gwara Na hakura nayi karatuna kawai yanda yakeso din"galala Aysha tayi tana kallonta tana tuki ta ce "Amma wlh Aira baki da wayo to maza kiyi sakakka irin na Aunty Maryam ta biye Dokar Abba harta gama Karatu bata da saurayi Abba ya had'ata da d'an Abokinshi dukda ba wani sonshi sosai take ba ta hakura danma yanzu suna son juna Amma ai Kinga batayi mata dad'i ba b'ata auri Wanda takeso ba To wlh kika biye kema haka zakuyi nidai ba ruwana tunda na kama My Abdul Dina" . Tab'e baki Aira tayi ta ce "Uhm Aunty yaya Arman fa Yama hanani kula samari fa kuma nayi mashi alkawari bazan kula kowa ba " galala aysha tayi ta na kallonta ta ce "Ke amma sakaraice ma Hajara har wani Arman ne zai hanaki kula samari to idan baki kula samari ba ubanwa zai Aure ki ko Shi Arman d'inne zai Aureki iyeeeeee kujimun ikon Allah " Aira daram Gabanta yayi irin mummunan fad'uwa jin Kalmar Aunty Aysha ta k'arshe "Ko shi Arman d'inne zai Aure ki?????!!!!!..............✍🏿 *Ni da Yaya Arman Book1 ne Free Book2 Ba free book ba ne Na kud’ine Book one zai k’are ne daga Page 30 daga nan za mu shiga Book two kai tsaye Ba tare da Gargada ba zaku iya fara biya tun kafin a k’are Book one zaku turo katin MTN #200 ta wannan number 07026166536 tare da shaidar biyanku ta 07026166536 y’an niger kuma ku bini pc ta number nan dana d’ora +2347026166536 zan turo muku number da zaku tura katin zain a ciki* _Normal group = #200_ _PC = # 300_ _V t u # 300_ *Sainajiku masoyan asali na tabbata bazaku tab’a nadamar sayan littafin nan ba darajarshi tafi ta #200 kachal na barshi ne hakan kawai saboda kauna da soyayya ga masu buk’atar a tallata musu hajarsu su tuntub’eni kai tsaye a number wayata kamar haka 07026166536 zamuyi ciniki cikin sauk’i insha Allahu sainajiku Masoyan asali na tabbata bazakuso ayi zazzafar doguwar tafiyar nan babu ku ba*👯‍♀️🙇🏽‍♀️🙇🏽‍♀️🙇🏽‍♀️ *Share fisabilillah* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/2, 09:31] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............21&22 Sosai gabanta ya fad'i sai yanzu ma ta tuna da Dan ayi Aure ake soyayya Shiru tayi ta na ta sak'e sak'en a ranta Tanajin Aysha nayi mata fad'a tayi mata banza ta kyaleta Har suka isa gida Suna isa Aira kai tsaye Part din Inna ta nufa Dan lokacin har Angama kiran magriba. "Bayan tayi salla a palourn zaune tayi tana lazumi kafin ta tashi innace ta shigo ta na fad'a tana cewa " Haba nidai wlh ana wahalshe dani ace Dan kinibibi Kamar Rahama god'ai god'ai da ita Bata iya wankan jariri ba koma ta iya Dan iskanci batayiwa d'anta wanka ba saini to zanga Ranar da babuni ubanda zai dinga musu ai duk gani na ne ya kawo hakan malalata kawai tun daga zamaninmu aka dena haifo mutanen kwarai Wai kamar Rahama da in Auren k'auye ake y'arta ma saita Aurar da Y'a Amma tsabar iskanci sai an wahalshe dani ". Aira na jinta tayi mata banza Dan ba kowani fad'an inna take tankawa ba " Tsaki Inna taja ta kalli Aira Dan ta tsani tana fad'a a mata banza in ba a bata hakuri ba gwara ko tankawa kayi ta ce "Ke kuma y'ar gidan malalaciya Daga gidan ubanwa Kike Rabonki da nan tun azahar ina kikaje " Tsaki Aira taja tare da tashi tayi bedroom d'inta ta na jin Inna na cewa "Uwarki da ubanki kikayiwa tsaki ba niba fitsararriya mai ido a tsakar ka " Murmushi kawai tayi dan yau ba y'an fad'an take ba shiyasa bazata biyewa inna ba ta na shiga d'akin ta kulle Dan yau batajin ko dinner zata iyayi sbd ciye ciyen da sukayi a waje. Ta na zuwa Sauri tayi ta cire kaya ta fad'a toilet ta yi wanka tana fitowa tasa kayan bacci ana kiran isha I nan ta tada salla saida ta gama ta tashi ta ninke hijab ta d'auko k'aramar wayarta da babba ta baje kan Gado wara idanu tayi ganin missed call d'in Arman rututu a k'aramar wayarta cikin Sauri ta Danna mashi kira saida ta katse tukwana ya kira cikin Sauri ta d'aga ta ce "Hello my Yaya ina yini" Ajiyar zuciya taji ya sauke daga bangarenshi ya ce "Nayi ta kira Baki d'auka ba ina kika shige" Sorry yaya wlh Aunty Aysha ce tazo shine na rakata unguwa"Yaushe tazo?Dazu "da ina da ina kikaje" gidan kawarta muka fara zuwa daga Chan muka wuce wajajen shakatawa amma waje biyu kawai mukaje muka dawo"Ita Aysharce daga dawowarta zata d'aukanmunke ku tafi yawo me yasa da zaku tafi baki fad'amun ba kafin nan ma wasu kaya kika fita da su? "sorry yaya na manta ban fad'a maka ba Bansa matsatsun kaya ba wlh doguwar Riga ce a ma baje take Aunty Aysha ta sayo mana Nida ita idan kana soma saina turo maka hoton ka gani"ba sai kituroman ba na yarda Amma fad'amun Gaskiya akwai saurayin da yace ya na sonki?gabanta ne ya fad'i sai sannan ta tuna da Sadiq cikin y'ar in ina ta ce "ya ya ba kowa" Aira kenan a tunaninki Idan kikayimun k'arya bazan gane ba baki saba karya ba Dan haka duk sanda kikayi ganewa nake oya fad'amun Gaskiya"Kamar zatayi kuka ta ce "To yaya bazakayi fad'a ba " Eh bazanyi ba gsky kawai nakeson ki fad'amun" Ajiyar zuciya ta sauke nan ta bashi labarin had'uwarsu da maganarsu da Aunty Aysha bata b'oye mashi komai ba "Sosai ranshi yayi mugun b'aci cikin fad'a da masifa ya ce " Ita Aysharce daga zuwanta har zata fara koya miki biye-Biyen Samari," "yaya Dan Allah kayi hakuri "Tafada kamar zatayi kuka " Cutie bakiyimun komai ba Amma Aysha tayi mugun bani mamaki Yazama dole gobe na shigo garin na kad'e mata warning Sannan duk sanda ya kirata ta baki ko kika bashi number ki kukayi mu'amula ko soyayya Allah ya isa ban yafe miki ba kinsan dai Mahimmancin Allah ya isa sarai(😆😂oh ni Arman hada Allah ya isa sai kace ubanta). Sosai Aira tayi mamakin kalaman Arman wai Allah ya isa Amma dayake tasan idan ranshi ya b'aci saida lallab'o tafi kowa iya zama dashi shiyasa ta ce "To Yaya Bazanyiba Goben da gaske zaka zo" ta fad'a ta na son sauya maganar "Eh cutie zanzo Amma kwana biyu zanyi na juya" Cikin murna Aira ta ce "Amma Naji dad'i my yaya Allah ya kawomun kai lafiya" Ameeen my Cutie ya fad'a tare da cewa Good night kiyi bacci yanzu nasan kingaji"murmushi tayi mai cike da so da k'auna ta ce "Have a nice dream yaya saida Safe". Tana kwanciya bacci yayi awon gaba da ita washegari Suna Yaro yaci suna Abdullahi za ana cemai Ameer sosai gidan ya cika ranar da mutanen Arziki Kanwar Abbansu Aira ma dake Aure a Kaduna Mama Halima tazo tare da y'arta Hafsat sa'ar Aira ce kuma kawarta ce sosai Ranar Aira jinta take cikin Farinciki duk inda tayi Hafsat na biye da Ita Da misalin k'arfe biyar na yamma sosai Aira tayi kyau cikin Wani tsadaddan lace black and blue sai ratsin pink sosai ya amshi farar fatarta batayi wata make up kamar koda yaushe hoda da kwalli kawai ta shafa Sosai tayi kyau kamar ka saceta ka Ruga a lokacin ta na bedroom d'inta dake d'akin inna Bayan ta gama shiryawa ta feshe jikinta da turarruka masu k'amshi drawer gefen gadon ta ta bud'e cike yake choculate kala kala kamar kaje Kanti duk Wanda yaya Arman yake saya mata ne manya biyu kawai ta d'auko ta fara sha Dan yunwa takeji sosai tunda safe rabonta da abinci Dan ita daman haka take batacin abincin sabga Nan Tasha hotunan ta sosai tana gamawa tayi status a what's app tana ganin amfara comment akan hoton ta maza ta kashe datar ta sauka wayarta ce k'arama tayi ringing ganin Yaya Arman ne ya sanyata picking cikin Sauri ta ce "Yaya Badai har kazo ba " Daga bangarenshi ya ce "Yanzu haka ina bakin gate d'in gidan Inna " Tsalle ta daka ta safko daga Gado ta ce "Wow Sannu da zuwa yaya ka shigo mana" bazan shigo ba cutie Naga akwai mutane a wajen kinfi kowa sanin ban fiya son taron mutane ba Kidai fito Kawai " "to yaya ga ni nan "ta fad'a ta na saurin Saukowa daga gadon cikin Sauri ta boye babbar wayarta a locker ta rik'e k'aramar takalmi da gyale ta zira tayi Sauri ta fito a palour ta tarar da mutane gaishesu tayi ta fita A farfajiyar gidan ta gamu da Hafsat Hafsat ta ce " Aira ina zuwa naga kina shirin fita"Taho ki rakani wajen YAya Arman zani" Dariya hafsa tayi ta ce "Ah koda nace wannan show d'in kice love za a sha wannan k'auna keda Yaya Arman har yanzu akwaita kenan" Murmushi Aira tayi tanajin dadi har cikin ranta ta kama hannun Hafsa ta ce "Ai kauna ta na nan Hafsa *NI DA YAYA ARMAN* Mutu ka raba Dariya Hafsa tayi ta ce " Allah yarda ni daman najima da sanin soyayya kuke wlh"wara idanu Aira tayi ta ce "Rufamun Asiri waya fad'a maki soyayya muke kawai dai k'auna ce muke " Uhm idan tayi tsami dai maji cewar Hafsa suna fita suka tarar dashi a cikin mota back seat driver na gaba Zage glass din motar yayi ya tsaya kallonta sosai ta tafi dashi ba k'aramun masifar kyau tayi mashi ba baisan lokacin da ya sakar mata murmushi ba Itama mayar mashi tayi Dan sosai yayi mata kyau cikin Dakakkiyar shaddarshi da Tasha aiki fara Hafsa ce ta ce "Ina yini Yaya" Lafiya qlau Hafsa yau a gari"murmushi tayi ta ce "Wlhko Yaya Suna mukazo tare ma muke da Mama " Aira ce ta shagwabe ta ce "Yaya bazaka fito ba wai ka hakimce a cikin mota" Dan murmushi yayi ya ce "So kike na fito a gama kalle maki ni wannan wankan nakine ke kad'ai" Dariya tayi ta ce "Wayau dai kawai cikin shagwaba ta ce " ni fa yunwa nakeji ba abunda naci tun dazu"wara idanu yayi ya ce "Subhanallahi garinya aka barmunke da yuwa" Yaya ban iyacin abincin Taro shiyasa"ai zama bai ganmu ba maza-maza shigo muje restaurant yanzunnan" ya fad'a yana bud'e mata Kofar da yake ciki Kallon Hafsa tayi ta ce "Sis taho muje" Girgiza kai Hafsa tayi ta ce "A a kije kawai Sis Mama ta ce Zan rakata gidan Daddy su gaisa Dan muna sa ran gobe zamu koma " To shknan saimun dawo Aira ta fad'a tana shigewa batare da shakkar komai ba Restaurant mafi kusa ya kaita saida ta tabbatar da ta koshi tukwana suka fito Suna shiga mota Yaji kiran daddy yana d'agawa nan Daddy ke shaidamai akwai Wani metting da za ayi karfe Tara a Zaria kome yake ya maza ya tafi Zaria yanzu yaje ya wakilceshi da to Arman ya amsa mashi Kallon Aira yayi da take latsa Wayarshi ya ce. "Cutie zamuje mu saukeki a gida yanzu Tafiya ta kamani zanje zaria zan wakilci Daddy wani metting " Yaya Dan Allah ka tafi dani Daman bantab'a zuwa Zaria ba Saidai mu wuce ta cikinta in zamu wuce Dan Allah kaje dani"tafada ta na marairaicewa "Rik'e hannunta tayi ya ce " Kiyi Hakuri my cutie Amma bazaiyu na tafi dake Zaria da Daren nan ba Kuma idan munje dinma bamusan tsawon lokacin da za a d'auka ba kiyi hakuri next time idan nazo zan daukeki da kaina na kaiki kiga ko ina da rana " "nidai Allah yaya ban yarda ba katafi dani kawai " Dafe kanshi yayi ya ce "Aira case Ce " to so kike na tafi dake na ja maki fad'a a gida Kin manta dare ne Zaiyi"Yaya wlh har muje mu dawo ba maiji ni daman b'angaren Inna nake kuma bamai sanin ma Inda naje"Ba yanda Arman baiyi ba Dan kar ya tafi da ita amma ta nace daga karshe ma kuka tasa mai hakan yasa ba yanda ya iya dole suka tafi tare tana ganin an tafi ta sauke ajiyar zuciya sai murna take daman ita tanason tafiyar mota a rayuwarta karfe takwas da wani Abu tayi musu a Zaria Rasa Inda ma zaikaita yayi hakan yasa ya yanke shawarar kaita gidansu Wani abokinshi kafin su gama metting d'in Abokin nashi ma bai gari mamanshi ta amshesu hannu bibbiyu Daga nan Arman ya wuce wajen metting d'inshi Hankali kwance nan Aira taci abinci sai nan nan y'an gidan suke da ita Dan Arman ya ce Musu kanwar sa ce Aira ganin Har 10Arman baizoba tana ta jiranshi Har bacci yayi awon gaba da ita. Arman ko metting d'in saida ya jasu Har 11:30 hankalinshi duk ya rabu gida biyu ga tunanin Aira daya baro. Koda ya koma maman su abokinshi hanashi daukarta yayi ta ce su barwa safiya ba irin yanda bai yiba amma ta hana tace bazasu tunkari hanya da Daren nan ba ga kidnappers da sukayi yawa suyi hakuri su barwa safiya ba yanda Arman ya iya sai hakura yayi yaje ya kama hotel ya kwana Aira ko tana baccinta bata San wainar da ake toyawa ba saida ta farka da asuba Ta ganta a wannan gidan Kan Gado Sosai gabanta ya fad'i ta ce. "Na shiga ukku ba dai a gidan nan na kwana ba " Sai sannan ta tuno da gida ba Wanda yasan Inda take Cikin firgice ta tashin hankali ta tashi Kanwar Abokinshice ta shigo Dan tada ta tayi salla Tazo ta isketa harta tashi Wanka Aira taje tayi ta mayar da kayan jikinta ta fito suka bata break fast mai rai da lafiya taci tana gamawa Arman yazo Godiya sosai Arman yayi musu tare da alheri Aira ma Godiya tayi musu dukda firgicin da take ciki. B'angaren gidan su Aira basu lura da Aira bata gida ba sai wajen 11pm Inna ta rikice ta nufi part din su Mamy ta fad'a musu Aira da bata gida Nan aka shiga nemanta lungu da sak'o ba a ganta ba Sosai suka shiga tashin hankali musamman Mamy hada kukanta Har 1 ana neman Aira ba a ganta ba ranar kwanan zaune sukayi Bcci saidai barawo. Hafsat ce da tasha baccin ta wajen Asuba ta farka Taji kamar ana neman Aira lokacin duk suna palourn Inna sunyi jugum Hankali tashe har Abba daya kasa zaune ya kasa tsaye inna ko inbanda kuka ba abunda take Hafsa dake bacci jikin mamanta ta ce "Mama Wai Aira ce bata dawo ba kowa" Duk kallonta mutanen dake palourn sukayi a tare sukace "ko kinsan Inda take ne Hafsa" Tashi tayi ta ce "Eh jiya dai da Yamma wajen magriba Yaya Arman yazo Nina rakata wajenshi tace yunwa takeji zaikaita joint taci abinci da tare zamuje saina ce Zan raka mama gidan Daddy shiyasa lokacin da muka dawo ni nazaci ma harta dawo" "Salati dukansu sukasa musamman Mamy kuka ta fashe ta ce " Na shiga ukku Airance tabi Arman suka kwana waje"Abba ko Shi kadai yasan yanda yaji a cikin ranshi safa da marwa kawai yake yama rasa wani irin hukunci zai yanke mata "Inna ko Salati ta rafka ta ce " ku bari sudawo muji dalili Dan nasan Tarbiyar Mujahed da Hajara sarai bazasuyi wani abunda bai kamata ba ni har hankali na ma ya kwanta tunda tare take da d'an uwanta"duk kallon mamaki suka bi inna dashi saikuma suka Jinjina kai Abba ko ya kasa magana sai safa da marwa da yake "Mama Halima ce ta ce " Dan Allah yaya ka kwantar da hankalinka Tunda dai anji Inda take sai a jirari dawowarta"Cikinsu ba Wanda Abba ya tankawa shi kadai yasan Zafin da yakeji cikin ranshi. Aira ko tun a mota take yiwa Arman kuka tasan yau Abba yasan bata kwana gida ba ta shiga ukku kasheta zaiyi tun yana Lallashinta har ya rabu da ita 7:20 tayi musu a Kano Kai tsaye gidan Inna suka isa Ba yanda Arman baiyi da ita ta fita ba amma taki sai kuka ta ke "tausasa murya yayi ya ce " "Kinga irin haka nake guje miki shiyasa Banso kika Bini ba Amma kika dage yanzu ki kwantar da hankalinki ki shiga nasan ma bazasu Gane ba Tunda Bangaren inna kike kuma inna ba d'akinki take shiga ba shiru Aira tayi ta na tunanin kuma hakane k'ilama Allah ya rufa mata asiri basu sani ba Kallonshi tayi cikin sigar shagwaba ta ce. "To bazaka rakani ba yaya" Idan na rakaki wani zai iya ganinmu Amma idan kikashiga ke kad'ai ba mai ganewa zaisu zaci ma kinfita ne sayan wani Abu Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Hakane Yaya to sai Anjima " Murmushi yayi mata ya ce "kije ki k'ara hutawa saimunyi waya Ko na shigo" gyad'a mai kai tayi bata samu damar ma mayar mai da murmushinba ta nufi bakin gate a hankali ta kwankwasa mai gadi ya fito ya bud'e yana mata kallon mamaki. Ajiyar zuciya Aira ta sauke ganin farfajiyar gidan ba kowa Arman ko yana ganin shigarta ya sauke ajiyar zuciya driver ya jashi suka tafi Aira ko gabanta na fad'uwa haka ta tinkari k'ofar d'akin. saida ta tofa addu'oi tukwana ta yi bismillah ta tura kofar a hankali kamar Munafuka tana bud'ewa tayi turus ganin Duka mutanen Gidansu a palour zata iya cewa a rayuwarta bata tab'a shiga tashin hankali irin na ranar ba baya tayi da Sauri tare da Niyyar Rugawa Kafin tayi taku d'aya Abba ya chafkota cikin zafin nama da b'acin rai yayi mata wani irin Mahaukacin ruk'o tare da d'auketa da wani gigitaccen mari..............✍🏿 *Kamar yanda na fad’a a page 30 In-Sha-Allah zamu gama book one ma ana free page kenan ku hanzarta biya tun kafin a kammala book one if you want to subscribe pay #200 katin MTN to 07026166536 hoton katin ko transfer masu Vtu suma zasu tura ta number tare da shaidar turowan amma su #300 wanda basu da buk’atar group ma ana ta pc za a tura musu suma #300 zasu biya ta number da na d’ora zasu tura y’an Niger kuma kumin magana ta wannan number +234-7026166536 zan turo muku number da zaku tura katin zain na 200 sai a saka ku Group karku manta book d’innan garab’asa ce babba da na sakeshi a 200 kachal Darajarshi tafi ta 1k Ni da Yaya Arman ba a fara komai ba bama a shiga wasan ba wannan duk somin tab’i ne hmmmmm wasan na nan gaba wannan shi ake kira koda kud’inka saida rabonka wannan salon na musamman ne masoyan asali ku harzarta ku biya nasan babu wanda zaizo ayi doguwar tafiyar nan batare da shiba saina jiku*💃🏾💃🏾💃🏾💃🏾💃🏾💃🏾💃🏾 *Share fisabilillah* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/4, 22:40] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............23&24 Aira jinta tayi cikin Wata duniyar ta daban kafin tayi ihu ya k'ara kifeta da wani marin da yafi na d'azu k'ara ta fasa cikin gigicewa Abba ko ranshi yayi kololuwar b'aci Wayar dutsin guga ya ciro Tare da wullata kanta ya bugi da Bango Nan ya hau lafta mata ta ko ina ihu take tana neman d'auki Abba ko baimasan tanayiba Dukanta kawai yake kamar baitab'a saninta ba. Duka mutanen dake d'akin saida suka tausaya mata Dan ko jakki aka yiwa dukan nan Yagamu da azaba dukda haushin Aira da Mamy keji Amma saida ta tausaya mata Cikin kuka taje ta rik'e Abba ta ce "Dan Allah kayi hakuri Abbansu Karka kasheta" . Bankad'eta Abba yayi Kad'an Ya hana ta fad'i cike da masifa ya ce "Ai gwara ta mutu Da ta d'auko mun magana mutuwar ta ta fiyemun rayuwarta " Cigaba da laftarta yayi Aira ko suma ce kawai batayi ba Inna ma Tana kuka ta taso ta dinga ba Abba hakuri ya kyaleta Baimasan ta nayi ba. Dak'yal dai Mama Halima ta rik'e Hannun Abba ta ce "Dan Girman Allah Yaya ka rabu da ita wlh ta daku karka mata illa nasan bata kyauta ba da ciwo amma kayi hakuri ka zauna " Dak'yal ta samu Abba ya zauna yana huci Aira ko Wajen Aunty Aysha ta ruga da gudu ta Rungumeta ta na kuka itama Rungumeta Ayshar tayi tana kuka Dan Duk wani mai imani saiya tausayawa Aira irin bugun da Tasha. Cikin tsawa Abba ya ce "Munafuka K'aramar karuwa Har kinyi girman da zakibi namiji kuje ku kwana waje ni zaki tozarta ki kunyata a idon al'umma ni da daraja da kimata da komai "Abba ya fad'a yana nuna kanshi" Aira ko sosai Kalmar k'aramar karuwar tayi mata ciwo Kara fashewa tayi da kuka magana ma ba kasa Mamy ma kanta saida Kalmar Tayi mata ciwo "Fad'a sosai Abba ya shigayi Inda ya shiga ba ta nan yake fita ba yana cewa . " Duk cikin y'ay'ana ban haifi y'ar iskaba tun daga kan Yayyunki saike y'ar karshe_Karshe Zaki gagareni ki bani matsala Tun yaushe na rabaki da d'an iskan yaron nan baki rabu dashi ba Abu har yayi k'amari kun Fara kwanan hotel hotel k'aramar yarinya dake ni zaki daukowa magana to baku isa ba Dagake har shi har ubanshi nafi k'arfinku wlh idan kuma da kene aka had'u aga bayana to ta Allah ba takuba kinja kin fita daga raina harna Fara tantamar ma Anya Nina Haifeki kuwa". Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Mama Da Mama Halima suka fad'a a tare Mama ta ce "Haba Alhaji wannan wace irin magana ce Kai da ranka ya b'aci baka iya control d'in bakinka wannan Maganar Ba Abun yi bace " Mama Halima kuka ta sa ta ce "Haba Yaya Wannan wace irin rayuwace kaida d'an uwanka Amma kun zama kamar Annabi da kafiri kawai kun biyewa shaid'an yayi tasiri a cikin zuciyar ku Wlh saboda ku yasa ko garin nan Banason zuwa kun Riga kun b'ata mana zumunci Kun b'ata zumuncin y'ay'anmu ". Mamy ko Itama kukan take sosai Maganar Abba ta k'ona mata rai cike da b'acin rai Ta tashi ta sab'i d'anta ta ce "Idan ba kai bane ubanta saika fad'i uban nata kokuma da ita nazo daga gidanmu Abun kuma ya tashi daga kanta ya koma kaina sharrima Ake neman K'ullamun kenan saikaje asibiti a Auna jininka da nata idan ba y'arka bace saika nemi ubanta ka maida mai" sannan ta kalli Aira tace " Ke kuma hankalinki ya kwanta saiki zubda ruwa a k'asa kisha kinja Anyimun wulakanci burinki yau ya cika"Ta k'arasa fad'a cikin kuka tare da barin Palourn.duk saida sukaji ba dad'i musamman Aira da ta k'arawa kukanta Volume inna ko tsaki taja ta ce “munafuka duk ba kece silar komai ba “. Abba baiko kula mamy ba saima ya tashi ya ce zanje wajen ubanshi na Mashi warning Rikeshi Mama Halima tayi ta ce Dan Allah kayi kayi hakuri kar kaje Bari a kirashi yaya Kabir d'in yazo a sasinta tunda haka kakeso wannan Maganar Ba ta waje ba ce tukwana ya zauna yana huci. Aunty Halima ta kira Abbansu Arman Bayan sun gaisa ta ce "Yaya Dan Allah kazo gidan Inna yanzu tana son ganinka da Sauri" Subhanalla innarce ba lfy ko wa cewar Daddy"Lafiya qalu yaya kaidai kawai kazo "To gani nan yanzunnan" Cikin Sauri Daddy Ya taho Dan a tunaninshi Inna ce ba lafiya Kafin minti Ashirin Ya Iso gidan. Suna zazzaune Kamar y'an zaman makoki Daddy Ya shigo Security d'inshi Ya umarta su tsaya a waje Har PA d'inshi Yana shigowa ganin Inna ya sauke ajiyar zuciya ya ce "Ai nama zaci Inna ce ba lfy hankali na harya tashi" . Lafiya qlau Yaya ka zauna "Bayan Daddy Ya zauna Mama Halima na kuka ta ce " Yaya Dan Allah Dan Girma Allah ku taimakemu ko ba Dan mu ba Dan Allah Kuyi hakuri ku janye wannan gabar Dake tsakaninku da tashin hankalin nan kamar Ba y'an uwa ba karku manta yaya ciki d'aya ba wasa ba ne Wlh kullum Da Bakin cikin wannan abun nake kwana nake tashi Ku taimakemu ku fahimci Juna na tabbata hatta ran iyayenmu dake k'asa basajin dad'in abun nan na tabbatar da suna raye da bazaku mana haka ba ". Abba ne Ya tashi cikin fad'a ya ce "Daman Halima dalilin da yasa kika kirashi kenan to babu wani saurin shiri tsakani na da mutumin nan Sannan ya kalli Daddy Ya nunashi da yatsa ya ce . " Kashe ne zan maka Akan Lalataccen d'anka Jiya ya d'aukar mun y'a sun kwana waje Dan haka kajawa Dan iskan d'anka kunne ya rabu da y'ata na rabasu sunk'i rabuwa nan gaba na k'ara ganinshi da ita Zan d'auki mummunan matakin da kowa saiya koka Dan wlh ka sake d'anka ya lalatamun tarbiyar y'a ko yayi mata ciki Kotu ce Zata rabani dakai". Cikin b'acin rai Shima Daddy Ya tashi cikin masifa ya ce "Daman saboda wannan dalilin ne kuka kirani sannan Shima ya nunashi da yatsa ya ce " Karka k'ara kiran d'ana da lalatacce y'arka ce lalatatta tunda har ka kasa bata tarbiyar da har ta bishi ta kwana Sannan kai zakayiwa y'arka kashe ba ni ba Idan ka isa da ita Kai zaka rabata dashi ba ni ba bazan rabasu d'inba Kuma da kake maganar abun Kunya ,y'a mace ke abun Kunya ba d'a namiji ba Dan haka idan ma yayi mata cikin kai da y'arka kukayi abun Kunya ba ni da d'ana ba Hope ka gane " Yana gama Fad'ar Hakan Fuuu yayi waje Duka Wanda ke Palourn Babu Wanda bai koka ba Musamman Mama Halima da take ganin tazo kiran gyara gashi an k'ara b'arna Shima Abba cikin b'acin rai da k'unar rai ya tashi ya fice daga palourn Tabbas yau Aira ta Ja Amfad'a mashi magana masu ciwo Aira ko Sosai take kuka ita kam ta shiga Ukkunta ya zatayi da rayuwarta da gudu tayi d'aki ta haye Gado ta na kuka mai tab'a zuciya. Yinin ranar Kowa sukuku ya yishi Haka dai akayi soye Rai duk babu dad'i musamman Mamy da zata iya cewa ranta yafi na kowa b'aci Aira ko ranar yinin D'aki tayi ko abinci bata iya ciba Tasha kukanta Har ta gode Allah ga shaftun bulalun Abba da suke mata mugun rad'ad'i. Daddy ko cikin b'acin rai ya nufi gida yana zuwa Ya d'auke Arman da Mari Arman da jin Marin kawai yayi a sama dafe kumcinshi yayi ya tsaya yana kallon Daddy karo na farko kenan a tsawon Rayuwarshi da Daddy Ya tab'a daga hannu ya dakeshi cikin fad'a Daddy Ya ce. "Ubanme yasa ka d'aukar musu y'a ina ka kaita har kuka kwana Waje Kaja yau an fad'amun maganganu masu zafi a saboda kai To daga yau bakai ba y'arsu na Rabaka da ita indai nine mahaifinka bakai ba ita tunda ba kanwar uwarka ba ce "Arman sosai ranshi ya b'aci Daman shi bai iya b'acin raiba " yace "Daddy daman A saboda Aira ne ka dakeni?Cikin fad'a Daddy Ya ce " A saboda ita d'in zan iya k'aramaka fiye da Wanda na maka Tukunnama fad'amun wata alak'ar ce Ke tsakaninku da bazaka iya rabuwa da ita ba " "Daddy sonta Nake Kuma Auranta zanyi itace matata bazan rabu da ita ba kome zakuyi Saidai Kuyi Amma bazamu tab'a rabuwa da junan mu ba Fad'anku bazai shafemu ba " So Mummy da Daddy suka fad'a a tare Bai jira sun Sake cewa wani Abu ba cikin b'acin rai yayi Hanyar waje Mummy na kirashi ta na cewa "Son dawo ina zaka kuma" Dan tasan Halin d'anta bai iya b'acin raiba musamman da har daddy ya mareshi shiyasa basusan b'ata mai rai Dan Duk maganar da tazo bakinshi fad'a yake "Amma ko juyowa Arman baiyiba Mumy zata bishi Daddy cikin fad'a ya ce " ke kuma ina zaki bishi ki rabu dashi mana yaje duk inda zaije yaro ne" "Cikin marairaicewa Mummy ta ce "Alhaji kasan halin Arman Da zuciya ka bari na bashi hakuri" Tsaki Daddy yaja Ya wuce yabar mata palourn Mummy bin ARMAN tayi lokacin da ta fita harya ja mota yabar Harabar gidan ba yanda ta iya ta koma ciki cike da tunanin Arman d'in Daman Aira ce yake so shiyasa duk lokacin da ta yi mashi maganar Aure yake cemata yana da wadda yakeso cikin ranta ta ce . "Kaikam son Soyayya batazo maka cikin Sauk'i ba ka kamu da son wacce iyayenku bazasu bari ku mallaki juna ba Sosai tashiga damuwar halin da D'an nata zai shiga Dan tasan Arman ba k'aramun so ne yake yiwa Aira ba Tunda har ya iya furtawa iyayenshi kai tsaye. Arman kai tsaye Airport ya nufa Yana zuwa ya yanki ticket na zuwa Abuja Allah ya taimakeshi akwai jirgin da zai tashi Kafin 1 hour jirginsu ya d'aga Abuja. B'angaren Aira har 6 tana daki ga wani zazzafan zazzabi da ya zubar mata Aysha ce ta je ta sameta Da kyal ta lallab'ata ta fito tana rik'e da hannunta a palour ta zaunar da ita ta na mata Sannu tukwana ta d'auko abinci ta dinga bata a baki dak'yal ta samu take karb'a kadan taci tace ta k'oshi. Man zafi Aysha ta d'auko ta dinga shafa mata tukwana ta b'alla mata magani dak'yal ta samu ta Had'iye kallon Aunty Aysha tayi ta ce " Thnks Aunty"Amma ce dake zaune ta ce "Sannu Aira" tsaki Aira taja tare da kauda kai Dan Duk haushin mutane take ji". jan bakinta amma tayi shiru dan tasan Aira akwai huce haushi,Hafsa ma dake gefen Inna ta ce "Ko baki lafiya Sis" Itama banza Aira tayi mata ,Aiysha ce ta ce "Kwanta Kan kujera ki huta kinji kanwata" gyada mata kai tayi tare kwanciya ta kalli sama ta rufe idanunta Tunanin yaya Arman ne kawai yazo mata a kwalwa taya ma zaiyu ace su rabu da juna duk wannan dukan da tasha batajin zata iya rabuwa dashi ga haushinta na zarginsu da Abba sukayi Abba hada cemata karuwa sosai ranta ke mata k'una gashi tasan Momy ba k'aramun fushi tayi da ita ba . Hafsat ce ta kalli inna ta ce "Inna Dan Allah Na tambayeki Allahsa ki fad'amun" Inajin Hafsatu fad'amun tambayarki"Inna wai me ya had'a Daddy da Abba basa jituwo nidai tsawon Rayuwata tunda na tashi a haka na sansu Kuma Idan Na tambayi Mama dalili saitak'i fad'amun ta ce Wai Family issue d'insu ne basainajiba Abun Yajima yana d'auremun kai Dan Allah Inna fad'amun" "Gyara Zama Inna tayi tare da cewa "Aiko yau zakiji labari tiryan tiryan y'ar nan ki gyara zama kisha labari inbanda abun Halima meye abun boye a Lamarin nan da duniya ma ta sani sannan ta fara da cewa..........✍🏿 *Tofa Abu ya rikice ya kuke tunanin Abba da Daddy zasu d'auki al'amarin nan kowannansu yad'au zafi* *Ya makomar soyayyar ARMAN da AIRA zata kasance nan gaba Bayan al'amari ya k'ara rikicewa* *Tofa ga wata sabuwa Hafsa tayi tambayar da kowannenku ke jiran Amsarta bari mu gyara zama Dan shan labari wajen Inna Dan nasan harkun k'agu kuji dalilin wannan gabar*😂 Share fisabilillah *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/5, 18:30] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️..............25&26 .....Kabir Da Abubakar y'an uwane Wanda suka fito ciki d'aya ma'ana uwa d'aya uba d'aya su Ukku ne a wajen iyayensu Abubakar ne Babba Sai Kabir da Abubakar ya bashi shekaru Ukku a duniya sannan Autar su Halima da har an cire ran Haihuwarta. Saida khabir ya bata sama da shekaru sha biyu Halima Nada wata Ukku Allah yayiwa mahaifinsu Malam Umar rasuwa Mahaifiyarsu Hajara ita taci gaba da kula da su Iliminsu,cinsu,shansu,suturarsu da koman su Tasha wahala sosai akansu Dan dangin ubansu Tunda mahaifinsu ya rasu basu tab'a taimaka musu da komai ba . Nida Hajara uwammu daya ubanmu ubanmu daya mu biyu kenan a wajen Iyayenmu Koda Allah yayiwa mijin ta rasuwa Saina dawo Wajenta daman mijina ya jima da rasuwa bantab'a haihuwa ba na d'auki y'ay'an Hajara tamkar nawa suma haka suka daukeni tare muka cigaba da kula dasu har Allah ya kawo girmansu. Sun taso cikin Had'in kai da son juna Abubakar tun yana Yaro yake da sha'awar siyasa yayinda shi kuma Kabir yake da sha'awar kasuwanci Koda Abubakar ya gama jami'a ya fad'a kasuwanci Sosai ya habaka Inda Har yayi Aure ya auri Zainab y'ar nan kano ce mace mai hakuri Shima Kabir yana kammala karatunshi ya fad'a harkar kasuwanci kafin kace me sun Tara arziki me yawa Su suka dinga kula da ni da Mahaifiyarsu tare da kanwarsu da suke ji da ita. Shima Kabir yayi Aure ya Auri Fatima y'ar gidan Wazirin Adamawa a Chan ya ganta ya aurota itama mace ce y'ar gidan mutumci ana haka ne Abubakar ya fad'a harkar siyasa yayinda shi kuma Kabir yake cigaba da kasuwancinshi Dan harkokinshima yawaici a waje yake yinsu. Kabir d'anshi d'aya a duniya Muhajed (Arman )tundaga kanshi bai sake haihuwa ba Abubakar ya rik'e mik'amai da dama a cikin wannan jahar tamu A siyasa kuma ya tab'a Senator A shekarun Baya . Zainab ta haifamai Yara Biyar Umar,Maryam,Aisha,Fauziya(Ummy),sai autarta Halimatu da aka sanya mata suna na" ana haka ne Allah yayiwa Mahaifiyarsu Rasuwa mutuwar da ta girgiza Al'umma musamman ni da Y'ay'anta munshiga damuwa sosai daga karshe kuma mukayi tawakkali ga Allah Yaranta suncigaba da daukata tamkar uwa Inda Abubakar lokacin da ya Gina wannan gidan Da muke ciki ya waremun bangarena guda Sosai suke kula.dani shida Kabir. Ana hakane k'watsam Kabir Ya had'u Da Rahama y'ar asalin Garin Agadez Bayan rasuwar iyayenta take zaune wajen Babban Yayanta tare da matarshi dake zaune a nan kano yake kasuwancinshi Fara ce sosai ga kyau irin jajayen buzayen nan masu masifar kyau Tunda ya ganta Kabir ya rud'e ba k'aramun so yake mata ba Nan ya samu suka sasinta ita ma har ta Fara sonshi . Wasa wasa magana ta fara k'arfi Wanda har iyaye suka shiga Aka kai kud'in gaisuwa wajen yayanta ganin yanda Kabir ya rud'e kullum zancenshi Rahama Ya sanya Abubakar cewa shikam ya kaishi yaga wannan rahamar da zata haukata mai k'ani Nan Kabir ya jashi ya rakashi Har gidansu Rahama Koda ta fito Abubakar ya d'ora ido a kanta Yaji duk duniya baitab'a ganin macen da tayi mishi a rayuwa ba sama da ita Lokaci guda ya kamu da matsanancin sonta Dak'yal ya iya daidaita kanshi suka gaisa tare da musu fatan Alkhairi Kabir yayi mata bayanin yanda suke da Abubakar ta gaidashi cikin girmamawa Har lokacin ya kasa Daina kallon ta . ita kanta saida ta tsargu tunda Abubakar ya ganta kullum da tunaninta yake kwana yake tashi Ana Hakane Tafiya Ta kama kabir China akan kasuwancinshi Nan ya mik'awa Yayan nashi ragamar komai game da rahama tare da cemai Dan Allah ya dinga kula mai da ita har ya dawo sannan duk abunda take buk'ata ya dinga zuwa yanaji Dan a lokacin waya bata wadata ba. Tunda Kabir yayi Tafiya Abubakar ya dinga zarya gidan su Rahama Kulawa ta musamman yake bata fiye da wadda Kabir ke bata Tun bata sakewa dashi har tazo ta sake dashi Cikin Dabara Abubakar yayi yanda yayi ya sace zuciyar Rahama A lokacin taji ba Wanda take so saishi. nan suka k'ulla soyayya mai karfi wanda har akazo ga maganar Aure dukda yayanta da farko ya hana saida ya lura Rahamar na mugun so shiyasa ya hakura ya ce abubakar ya turo iyayenshi Koda yaxomun da maganar korarshi nayi na shiga f'ada Inda na shiga ba tanan nake fitaba Ba yanda baiyi ya shawo kainaba amma naki Nace ba ruwana a maganar Auren cin amana . Dangin mahaifinshi ya sama ya saye su da kudi su sukaje suka nema mai Auran Rahama cikin k'ank'anin Lokaci ba ayi wata guda ba aka d'aura musu Aure har lokacin Kabir na China Ranar Da aka daura Auren Ranar ya dawo garin Inda ya tarar da wannnan tashin hankalin Wanda ya girmi tunaninshi Yayanshi uwa d'aya uba d'aya ya ci amanarshi ya Aure mai Matar da zai Aura . Ranar munga tashin hankalin da bamu tab'a gani ba Dan Kabir dukansu shida Abubakar daman suna da zafin kai Shak'e Yayanshi Kabir yayi Ya hau zaginshi da Tsine mashi Wanda dak'yal na samu maza suka rabasu Tofa tun daga lokacin nan suka k'ulla D'aurarriyar gaba da k'iyayya a lokacin Kabir yafi d'aukar abun Da zafi Inda Yayi Aniyar saiya yi mashi ramuwar gayyar abunda yayi mai. Rahama da Zainab sun had'e kansu sosai dukansu basu da tashin hankali sosai Rahama ke girmama Zainab haka d'iyan Zainab suna girmama Rahama sosai baka tab'a cewa kishiya da kishiya ne dukda kuwa lokacin Mijinsu Yana rid'in Rahama Dan yaso ya nuna yafi sonta a fili amma rahamar Ta k'iya ta nuna batason gwara ya dinga musu adalci kar ya rikita musu Zama . Ana Hakane Rahama ta samu ciki Sosai Ya d'ora son duniya akan cikin saikace lokacin ne za a fara Mashi Haihuwa Haka Rahama tayi ta rainon cikinta sosai take samun kulawa daga wajen mijinta da kuma Zainab Dan ni haushinta nake ji tunda ta zama silar had'a y'ay'ana fad'a har cikinta ya isa haihuwa ranar wata Juma a ta haifi y'arta kyakyawa Fara Sol wacce ta dameta fari da kyau Tunda aka haife yarinyar kowa ke sonta yayyinta kamar su cinyeta musamman Aysha . Ranar suna Yarinya taci suna "Hajara sunan Mahaifiyarsu kenan " A lokacin da Aka haifeta Mujahid duk Juma a yana kawomun ziyara Da mahaifinshi ya hanashi zuwa kwata_kwata dak'yal da kuka da kuma na nuna mashi Ya daukeni ba uwa ba hakan yasa Kabir ke barin d'anshi zuwa wajena sosai nakeson Mujahid kamar yanda Tunda aka Haifi Hajara nake sonta Dukda dai bana son uwarta data hadamun y'ay'a fad'a. Koda yaushe Hajara na bangarena inba kuka tayiba akaita wajen uwar sosai Mujahed ke sonta tun tana jaririya Danshi ya sanya mata Sunan Aira daga nan sunan ya bita a lokacin Mahaifin Aira baya hana Mujahid mu'amula da Aira Dan har lokacin yana jin nauyin K'anan nashi yasan shi yayi mashi laifi hakan yasa bai d'auki abun da zafi ba Dan koda Aira ta girma Har fita Mujahid yake da Ita Yayo mata sayayya a saboda Aira Mujahid Koda yaushe da ya dawo daga Makaranta ya na gida na yana like da ita harta girma. itama kuma sosai ta shaku dashi koda yaushe tana lik'e dashi Dan idan baizoba Haka zatayi ta kuka Ta rikice sai in yazo ake samun Lafiyarta Bayan Haihuwar Hajara da shekaru Hud'u Rahama ta sake haihuwar d'anta Namiji Aliyu Haidar tun daga kanshi kuma haihuwar ta tsaya mata Chak sai yanzu kusan Bayan shekara goma ta sake haihuwar wannan yaron Koda Mujahid Yaje Karatu k'asar Misra duk hutun da suka samu saiya taho Dan Ganin Aira Haka har ya kammala karatunshi Inda yana gamawa ya samu aiki a CBN Abuja Dan abunda ya karanta kenan har lokacin Mahaifin Aira bai damu da Taren Aira da Arman ba Dan ko da ya samu aiki Abuja tofa duk karshen mako saiya taho yaganta. Ana Hakane shekaru Biyu da suka wuce Abubakar ya fito takarar gwamnan wannan jahar ganin haka ya sanya Kabir cewa Shima ya samu damar da zai rama Abunda Yayan nashi yayi mashi Shima ya fito takarar gwamna a wata jam'iyar Wanda Duka su biyun aka tsaida y'an takarar gwamna. Sosai Abun ya bak'antawa Abubakar Nan aka shiga siyasa ba kama hannun yaro dukansu kamar ba y'an uwaba Dan yanda mabiyar kowannensu ke sukar d'ayansu musamman mabiyar Kabir wakoki da maganganu na habaice habaice na y'an siyasa aka shiga yiwa Abubakar ba yanda banyi dasu ba akan cikinsu wani ya janye amma sukak'iya Hatta kanwarsu Halima da tayi Aure ta auri wani soja a Kaduna Inda ta haifi hafsat kusan sa annin Aira ce kwana ashirin Aira ta bata Dan kusan tattare akayi Auren Halima da Rahama Halima yaranta biyu Hafsa itace babba sai kaninta Sadiq ita kanta ba irin tashin hankalin da bata shiga ba akan siyasar da y'an uwan nata suka fito Dan tuni zance ya baza duniya . zancen Cin Amanar da Abubakar yayiwa Kabir Y'an siyasa sukayi Amfani dashi dukda ba kowa yasan maganar ba amma suka yayata maganar ko ina Wanda da wannan ne suka samu damar kayar da Abubakar siyasa Dan Sun sokeshi da cewa tunda yaci Amanar d'an uwanshi suma talakkawa zai iyacin Amanarsu Inda suka zab'i Kabir a matsayin gwamnan wannan Jahar yanzu. Abubakar ya shiga tashin hankali ba Kad'an ba akan wannan Abun da d'an uwanshi yayi mashi wannan ya k'ara rura wutar k'iyayyar junansu Wanda Abubakar yakejin tsabar kiyayyar Kabir fiye da wacce kabir yake mashi Tun daga lokacin Abubakar ya raba Mujahid da y'arshi amma sukaki rabuwa kullum yaganta tare dashi saiya daketa Amma washegari sai ka gansu tare . daman Hajara wajena take tun tana yarinya to anan suke haduwa da mujahid dan baya shiga gidan su Abubakar ya daina yiwa Mujahid magana ya daina Amsa gaisuwarshi Dan k'iyayyar Mahaifinshi Ta shafeshi Mujahid ganin Idan ya gaishe dashi baya amsawa ya sanya ya daina gaisheshi kwata_kwata Duk yanda Abubakar yaso Raba Mujahid da Hajara gagara abun yayi shakuwarsu sai abunda yayi gaba har zuwa yanzu dai ya kasa rabasu. To Yau dai kinji Dalilin wannan Gabar da k'iyayyar Duka akan mace macen ma Rahama shiyasa kikaga bana son Rahama inbanda ma ina son d'iyarta da me zanyi da Rahama Mayaudariyar da ta raba mana Kan iyalai Duka fa itace munafukar da ta had'a abun nan da batace tana son Abubakar d'inba da duk haka ta faru ba" " amma Munafukar Mayaudariyar ta tashi daga kan k'ani ta koma Yayanshi ku yanzu duk a tarihi da kuka taba ji ina kuka tab'a ganin Anyi haka "Inna ta k'arasa fad'a tana hawaye Tare da murje ido ta ce " Ai Tsakani na da Rahama sai Allah ya isa Nasan da Adda Hajara na raye da bazata yarda A auro mata wannan annobar Rahamar ba "Inna takarasa fad'a ta na shaftar Majina". Hafsat ce da aka gama bata labari saida tayi hawaye jin wannan sark'ak'k'kiyar ta ce Daman ashe wannan dalilin ne ya had'a Daddy da Abba Jin Inna na shiruftu Daga karshe tana zagin Mamy ya sanyata B'ata rai ta ce " haba Inna Daga cewa ki bani labari kuma sai kihau kuka da Zage_Zagen Mamy nidai shikenan labarin ya isa Haka " "Yoke y'ar nan ba dole na zagi Rahama ba Dole kiga nayi kuka idan na tuna da Abun nan " Aira da tunda Inna ta fara labarin tana jinta tayi shiru sosai surutun ya dameta saida taga ta fara zagar mata uwa ya sanyata tashi cike da Masifa tana hawaye ta kalli inna ta ce. "Karki sake zagarmun uwa me tayi maki da zaki hau zaginta tun d'azu fa ina jinki na kyaleki" Cikin masifa Inna ta ce "to Mai ido a tsakar ka ai bansan kin damu da uwar taki ba Sai kin rama mata An Zage ta d'in"To wlh karki sake zagarmun uwa tunda uwa ba fin uwa tayi ba kowa son uwarshi Yake ke da dadi a zagar maki taki uwar" Aira ta fad'a tana gallawa Inna harara"Kuka Inna ta fashe dashi ta ce "Shikenan yau Hajara kin zageni amma kedai ba y'ar arziki bace tun kina yarinya nake wahala dake naci kashinki naci fitsarinki uwarki Haihuwarki kawai zata gwadamun amma badai wahala dake ba shine yau Kika saka mun da Zagi " Mama Halima da ta shigo lokacin taji abunda Aira ke cewa Inna "Tsawa ta dakawa Aira ta ce " Dan Ubanki Aira Inna sa'arkice da zaki fad'awa wannan maganar kin manta uwarmuce itad'in zaginta kike shirin yi ko me koma Ince zagin nata kikayi "kuka Aira ta fashe dashi ta ce "Mama fa tun d'azu take zagarmun uwa na kyaleta Kuma ni ba zaginta Nayi ba Daman Kullum idan ta tashi gidan nan bata zagin uwar kowa sai tawa " . ta k'arasa fad'a tana kuka Tsaki Mama Halima tayi ta ce "Ta zagi uwar taki ko Dukanta tayi kin mata wannan Rashin kunyar Dan baki da ta ido" Inna ko kuka take tana cewa "Rabu da Ita Halima ta haifu ai Tsautsayi ne ya kaini na tab'a jinin Rahama sakayyace tamun dan haka yau yau d'innan saikin barmun b'angare ki koma chan gidanku inma kasheki uban naki zaiyi ya kasheki daman ni nake Daure maki gindi yau ko ya k'are bani ba ke maza_maza fitarmun daga gida" ''Inna tafada tare da mikewa ta rike k'ugu "Kuka Aira ta fashe dashi tare da tashi Tayi d'akinta Da gudu tana kuka ta fiddo duk wani abunda take buk'ata a akwati Ta janyota Ta fito Mama Halima ta Kalleta ta ce " Ke ina zaki"Gidanmu zan koma sannan ta kalli inna tace "Daga yau idan kin k'ara gani na wajenki duk abunda kikaga dama kimun" ta fad'a tare da ficewa tana hawaye". "Ikon Allah " Mama Halima ta fad'a tare da tab'e baki Hafsa ce ta ce "Ni wlh Mama Aira har ta bani tausayi dama baki mata fad'a ba ga Abba ya daketa da safe yanzu sun b'ata da Inna kuma fa Mama innar ita ta dinga zagin Mamy wlh konice Aka zagi uwata haka zanyi " Harararta Mama Halima tayi mata ta ce "To kema zagarta Dan ubanki Da yake sa'arkuce" Cikin Sauri Hafsa ta tashi tana Dariya ta bi Bayan Aira Dan tasan itama maman tata gwanace wajen fad'a yanzu ta gane ashe Duka ukkun Mama da Daddy da Abba Duka halinsu d'aya na fad'a Dan yanda taga yanda Daddy da Abba sukayi fad'an nan da safe har sunfi ma mamanta fad'a . Suna fita Aysha ma ta tashi Dan ita daman ba gwanar zama bangaren Inna bace "Mama Halima tayi ta Lallashin Inna ta ce " Dan Allah Inna ki daina zagin mamanta inma zakiyi kidainayi a gabanta Kinga ba dad'i"Tsaki Inna taja ta ce an zageta d'in ko kema bayansu d'in zaki shiga ko gobe saina zageta"Shiru mama Halima tayi Dan tasan Halin Inna ta rikice sai da lallab'o. Aira kai tsaye gidansu ta nufa ta na kuka Mama kad'ai ta tarar a palour Mama ta ce "Lafiya Aira ya na ganki da akwati kina kuka kuma" Gidanmu na dawo ta fad'a tana kuka tare da shigewa Dakinsu na y'an matan gidan tana shiga ta saki akwatin Tare da Fad'awa Gado ta saki kuka mai ciwo............✍🏿 *NI DA YAYA ARMAN book 2 it’s not Free it’s for sale if you wan’t subscribe pay 200 only katin M t n hoton katin ko transfer #200 Naira to 07026166536 Vtu #300 Pc wanda basa bukatar a Sakasu grps suma #300 y’an niger zaku iyamun magana ta wannan number +234-7026166536* *Share fisabilillah* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/7, 10:24] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION* 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............27&28 ....Sosai take kuka ta ma rasa Inda zata tsoma ranta taji sanyi yayyinta ba irin Lallashin da basu mata ba amma tak'iya saida ta gaji Dan kanta tukwana ranar ma da mugun zazzab'in ta kwana Wanda zazzab'in duk na tunanin Arman ne . Washegari koda ta tashi bata lafiya sosai dak'yal ta samu tayi salla ta koma Ta lullub'e da bargo dukda zafin da ake Ba yanda su Ummy basuyi ba akan ta fito ko tea ne Tasha amma tak'iya har Ayshar mutuniyartata ba yanda batayi ba amma ta kiya. Ganin sosai jikinta yayi zafi ya sanya su tsorata Amma ce ta je ta samu Mamy ta ce "Mamy Aira bata lafiya fa kixo kiga jikinta yayi zafi sosai" Cike da b'acin rai Mamy ta ce "me zanyi mata taje tayi ta ciwon ina ruwana" Ganin ran Mamy bace ya sanya Amma Zuwa ta fad'awa Mama Taje ta dubata taga har yanzu zafi jikinta. Wajen Abba Mama Taje ta lallabashi akan ya fiddo mota akai Aira Asibiti Dak'yal ta lallabashi ya kira Family doctor d'insu ba ayi minti Talatin ba saiga Dr Bashir yazo tare da Abba suka shiga Mamy ta rakasu har d'akin da Aira take Haidar na gefenta Aysha na Jik'a ruwa tana shafa mata a ka dr yace meke damunta Amma tayi mai bayani dan har lokacin Aira ta kasa tashi kanta ji take kamar zai rabe gida biyu. Kallon Dr Bashir Abba yayi ya ce "idan ka duba ta ka auni jininta Kayi mata har awon Ciki" Ciki kuma Alhaji "Mama ta fad'a cikin mamaki Duka saida sukayi mamakin maganar Abba Aira ko hawaye kawai take tasan shikenan yanzu Abba ya daina yarda dani ta fad'a cikin zuciyarta hawaye na zarya daga idanunta. " Okay to Alhaji"Doctor ya fad'a Abba ko baiba Mama amsa ba ya fita cikin k'ank'anin lokaci Dr ya duba ta ya dauki jininta ya tafi dashi da niyyar zaije ya Auna Haidar ne yaje wajen Mamy ya ce . "Mamy Dan Allah Kije ki duba Ya Aira wlh bata da Lafiya yanzu ma Dr yazo ya duba ta Hada Awon ciki wai Abba yace ayi mata"Cike da tashin hankali Mamy ta ce " Shi Abban naku ne ya kira Dr yace ya mata awon"Eh Mamy wlh y'anzu ma Dr ya d'auki jininta ya tafi kuma sai kuka take"Sosai ran Mamy ya b'aci fitowa Palour tayi. Mama Halima ce da Hafsa tare da Inna dayake Chan suka kwana suka shigowa yi musu bankwana zasu wuce suna zaune suna Gaisawa da Abba Mamy ta shigo ranta matuk'ar b'ace ta nufi wajen Abba tare da kama k'ugu ta ce. "Shine har da kiran Doctor kace yayiwa y'ata awon ciki inbanda tsabar wulakanci da tonon asiri wannan ai sharri ne ma kake shirin yiwa y'arka Shi doctor d'in da ka kira Me zai d'auketa kasan abunda zaije ya k'ara ya fad'a nan gaba to Ta Allah bata mutum ba insha Allahu y'ata bazata tab'a abun kunyar da ake so tayi ba Tunda uwarta banyi ba Itama bazata tab'ayi ba" " Cikin fad'a Abba ya ce "Wlh Rahama zanyi mugun sab'a miki karkiga kina wani zafuce zafuce ina kyaleki ba tsoronki nake jiba Ina kyaleki ne darajar Y'ay'anki inba hakaba baki isa kizo ki dinga fad'amun maganganun banza ina kyaleki ba " Tsaki Mamy taja ta ce "Karka k'ara ragamun d'in daga yau " Mama Halima ce ta ce "Haba Rahama da hankalinki da komai ki dinga yiwa mijinki Haka Ku sanyawa zuciyarku ruwan sanyi kar k'aramar matsala ta zama babba mana Kaima yaya baka kyauta ba Akan me zaka kira doctor ayi mata awon wani ciki me ya had'a Aira da ciki " dukanku kunfini sanin abunda nakeyi ne Dan haka kar Wanda ya k'ara mun magana akan Abunda zan aikata ko na Aikata "Inna ce cikin Masifa ta ce " Kede Rahama baki da mutunci wlh Ko baki girma mashi matsayin mijinki ba Ai kin Yi karar ina wajen Y'arki d'in banza zakizo kina fafatu akanta y'ar da wahalar ta ma bakisaniba Sai in k'irga so nawa kika tab'a wanke mata kashi harta girma ke inkina da kunya kin d'aga baki kiyi magana Akan Y'arki y'arma ta fari in banda lalacewar zamani hada cewa wani y'arki Inajinma kece kika zugota jiya ta zageni Ai tunda ga Kanmu aka daina haifo mutanen kwarai wlh" "Inna ta k'arasa fad'a cikin Masifa "Mamy bata tanka mata ba sai zama da tayi ta na girgiza k'afa Masifa sosai Inna ta shiga surfa Masifa Inda ta shiga ba tanan take fita ba ana haka Doctor Ya shigo Samun wuri yayi ya zauna Dr yace " Alhaji mungama awon ba komai ke damunta ba Maleria ce sai tunani da ya fara mata yawa Awon cikin ma ba komai Duka Maleria ce ta sanyata ciwon sannan ya mik'awa Abba result d'in da leda ya ce "ga magungunan da za adinga bata kuma yanzu zanyi mata allura insha Allahu Zata samu sauk'i" Tashi Mamy tayi ta ce "Alhamdulilla Abunda ake son dai baifaruba akan y'ata kuma sai a tari wani sarkin" ta fad'a tare da wucewarta d'akinta duk da Kallo suka bita Girgiza kai Mama Halima tayi a ranta ta ce "Lallai Yaya Inbanda Rahama wa ya isa ya fad'a mashi maganganun nan a kwana lfy" Dr ko tashi yayi yaje Dan yiwa Aira Allurar "Inna ce taja tsaki ta ce . " Aikin banza Ai shiyasa Tun farko na hanaka Auran Yarinyar Chan kuka dage sai ita farin ne kawai ya d'ebeku amma ni daman Nasan ba mutuncin kirki zatayi ba yanzu wa gari ya waya shidai Kabir Allah ya taimakeshi kaikuma da ka jajib'o saikaji dashi Dukta salamceka ta asirceka inaga tsoronta kakeji ma ko to ni ba kai bane ni bata salamceni ba Ai naso wlh ta Tankamun yau da taga yanda tsaffi ke Rashin mutunci Yau da saitabar gidannan dukda d'anyen jegon tunda ba gidan ubanta bane wai nan gani take ta haifi maza biyu zatawa mutane iskanci to ko Nigeria ta haife ni sai in koreta tunda bata da mutunci". Shidai Abba baice komai ba Dan yasan Inna sarai inta rikice hakan yasa ya dinga lallab'ata Nan Dr ya fito yayiwa Abba sallama Mama Halima ce ta shiga d'akin da Aira ke ciki lokacin Ta tashi tana rama Sallar da batai ba "Koda ta gama sosai Mama Halima ta shiga yi mata nasiha cikin nutsuwa Akan ta yiwa iyayenta biyayya ta daina abunda basaso " Insha Allahu Mama bazan sakeba "yawwa Mamana Allah miki albarka idan iyayenki sun huce kije ki basu hakuri kinsan yanzu cikin fushi suke " tana hawaye tace "Insha Allahu Mama zan basu hakuri" Mama ta ce "To mudai zamu wuce ai zakizomun Hutu ko tunda kun gama karatu bare kice makaranta Dan nasan halinki sarai bakison zuwa kinamun hutu" Insha Allah Mama indai Abba ya yarda zanzo". Ranar su Mama Halima da Hafsa suka juya Aira ji take kamar ta bisu Dan gidan baya mata dadi . Aira ita ciwon biyu yayi mata ga na Rashin jin muryar Arman kwana biyu Dan wayarta tayi mata mugun b'oye daga babbar har k'aramar. Cikin kwana biyu Aira taji sauk'i ta warware sosai yanzu sai damuwar fushi da Iyayenta keyi da ita Dan Mamy ko magana bata mata sosai Abun yake damunta Yau tana zaune a dakinsu ganin ba kowa ya sanyata saurin d'auko wayarta Karama ta kunna ta maza ta shige toilet Dan karma wani ya shigo ta dannawa Arman Kira Saida ta gama ringing tukwana ya kira. Muryarta cike da damuwa kamar zatayi kuka ta ce "Yaya ina ka shige kwana biyu" Bangaren ARMAN Ajiyar zuciya ya sauke Dan tun ranar da ya koma Abuja Yake cikin damuwa yasan tunda Daddy yayi wannan fushin to yasan Abban Aira ne yayi mashi Rashin mutunci yasan ba k'aramun Duka Tasha ba tsoronshi d'aya Kada Ta tsorata ta rabu dashi hakan yasa duk ya shiga damuwa gashi yayi ta Kiran layin Ta kashe "Aira kina Lafiya ya fad'a cikin sanyi" Kamar zatayi kuka ta ce "Lfyqlau yaya sai kewarka da tamun yawa" Nima Ina nan kewarki ta addabeni My Aira Please kuyimun Alk'awarin duk wuya duk rintsi bazaki rabu dani ba idan kika rabu dani zan shiga mawuyacin hali please my Cutie"Kuka Aira ta fashe dashi cikin kuka ta ce "Yaya bazan tab'a rabuwa dakai ba Abunda ban tab'a kawowa a kwalwata ba Dan Allah kar Daddy yasa ka rabu dani nasan Shima yanzu bayason alak'armu tunda suka sake rigima da Abba" Karki damu my cutie Daddy bazai iya rabamu ba "Bai tambayeta Abunda ya faru ba Dan bayason k'arin b'acin rai sun tab'a Hira sosai Aira duk sai taji Kashi tamanin na damuwarta ya tafi haka Shima bangaren Arman din ta kasance Arman yace kina jina My cutie" yace Eh Yaya"Daga yanzu karki k'ara nuna muna tare karki sake wani ya lura da muna tare Ko garin nazo Bazan k'ara yarda nayi sakacin da har zai zame maki matsala banason yawan dukanki da ake Zamuyi Abotarmu cikin sirri kinji"Kamar yana gabanta ta gyad'a mai kai tace "to yaya " sannan kicewa su Abba da mamy kin rabu dani ko sun tambayeki kinji"To yaya tafada Sun Kara tab'a Hira Kad'an tukwana sukayi bankwana cike da Shauk'in k'aunar juna. Bayan kwana biyu Aira taje ta samu Abba a lambu ta dinga bashi hakuri tana kuka tun bai kulata ba haryazo yace ya hakura amma da sharad'i saita rabu da Mujahid Goge hawayenta tayi ta ce "Abba insha Allahu mun rabu bazan k'ara mu'amula dashi ba " Ajiyar zuciya Abba ya sauke ya ce "da ko kikayi hakan da kin taimaki kanki kuma kin nemu hanyar da zamu samu Masalaha a tsakaninmu Allah yayi miki albarka" Cike da farinciki Aira ta ce "Ameen Abba nagode". Daga nan d'akin Mamy ta nufa ta isketa tana Bawa Amer madara durkusawa tayi ta bata hakuri tayi banza ta kyaleta " Kuka ta fashe dashi tare da rik'e k'asar zanin Mamy ta ce "Dan girman Allah Mamy kiyi hakuri ki yafemun bazan sakeba Mamy na tuba"Shiru Mamy tayi saikuma ta ce " "Haba Aira tuban ki wannene bansaniba sau nawa zakiyi Abu kice bazaki sakeba karshe kizo kiyi Wanda ya linka na baya ai yanzu ni kinfi k'arfina kuma ba ruwana dake"Mamy wlh yanzu na tuba Allah nadaina bazan sakeba Ajiyar zuciya Mamy ta sauke ta ce "Tashi muyi magana indai da gaske kike bar kukan" cikin Sauri Aira ta tashi ta zauna gefen Mamy Kallonta tayi in serious talking ta ce "kin yarda kin rabu da Arman d'in koko?cikin Sauri tace.............✍🏿 *Share fisabillah* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/8, 22:32] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION* 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............29&30 " Mamy na rabu dashi Shima kuma nasan Daddynshi ya rabashi dani tunda bakusan mu amulata dashi"Yawwa ko kefa Aira ki taimakamun ki fiddani kunya ki rabu dashi sannan ki daina abunda zaidinga jamun Zagi kinji"Gyada kai tayi tace "Insha Allahu Mamy Na daina" Allah sa da gaske kike na yafe maki duniya da Lahira Allah maki Albarka " "Sosai Aira taji sanyi a ranta tace " Ameen Mamy nagode sosai"sosai Mamy ta saki jiki da Aira ta dinga janta cikin dabara ta Tambayeta ta ce " ranar da kuka tafi ina kikaje kuka kwana badai abunda yayi maki ko idan da Abunda ya faru fad'amun wlh ba maiji kuma bazan dake kiba kinji na rantse " Nan Aira ta bawa Mamy Labarin komai Da ya faru daga karshe ta ce " Allah Mamy Gaskiya na fad'a maki ba abunda yamun ni yaya baitab'amun maganar banza ba kawai zargine kuke amma shi ba haka yake ba"wata nauyayyar Ajiyar zuciya Mamy ta sauke ta tabbata Aira idan ta fad'i magana haka take Dan bata karya Sai sannan taji sanyi a ranta ta cire zargin dake ranta daman duk wannan Abun da tayiwa Abba itama akwai zargin a ranta kawai Dai abunka ga d'a da uwa ne "to yanzu shikenan komai ya wuce na yarda ki kiyaye nan gaba Dan Allah" to Mamy "sannan tace " Mamy banishi na rik'e maki ta fad'a tana mik'a hannu ta amshi Ameer tare da pidarshi ta sab'eshi a kafad'a ta fito palour Sai murna take yanzu Hankalinta kwance ta sasinta da Iyayenta. Haka rayuwa taci gaba Aira na shan wayarta da Arman a b'oye babu Wanda ya fahimta Kullum idan Sadiq ya kira Aysha idan ta bata wayar kin amsa take ba yanda Aysha batayi da itaba amma saita k'iya tun yana kira har ya hakura ya daina kira Wanda hakan sosai yayiwa Aira dad'i. Amma ta koma bangaren Inna kullum Inna da kewar Aira take kwana take yini Dan tayi mugun Shak'uwa da ita gashi taga Airar tayi zuciya ko bangarenta bata k'ara shigowa dak'yal a daddafe Inna ta daure tayi sati biyu ba Aira sosai kewarta ta dameta gashi Shima Arman bai sake zuwaba duk Abu ya dameta. Yau Aira y'an gidan su duk suna zaune a palour ana hira da misalin Tara na dare har Abba da su Mamy Amer na Bayan Aysha ta goyashi Inna ta shigo Aira na ganin shigowarta ta kauda kai Wajenta Inna ta nufa ta ce "Haba y'ar lelena daman zaki iya fushi dani Duka ina duniyar take bare mu dake cikinta biko nazo ki taho mu koma gidan duk bayamun dad'i da kika tafi" Turo baki Aira tana zunbura Baki ta ce "Keda kika koreni ni ba Inda zani kije Chan takwarartaki ta dinga tayaki kwanan ni bazan koma ba"Inna ta Goge hawaye ta ce " Haba Hajara Dan Kinga ina sonki shiyasa kikemun wulakanci to wai ba na baki hakuri ba ki taho mu tafi "ba Inda zani ni ki tafi " Sudai su Mama suna gefe suna Dariya kasa kasa Dan Inna da Aira sai Allah haka zasuyi fad'an kuma inna tadawo tana bata hakuri"cike da Masifa Inna ta juya ta kalli su Mamy ta ce "ku yanzu cikinku ba mai bata hakuri Kunajina kukayi banza dani Dan kun rainani ke Rahama ba y'arki bace Baki isa kice tayi hakuri kodan daman Nasan ai ke kike zugata shiyasa yanzu ta gujeni kiwon d'an makwarwa ne nayi " tafada tana Goge hawaye "Cikin ladabi Mamy ta ce " kiyi hakuri Inna ni wlh banzugata ba Dan kar nayi magana kuma kice ina ruwana shiyasa amma kiyi hakuri sannan ta harari Aira ta ce "Tashi ku tafi" Turo baki Aira tayi ta ce "Mamy itafa da kanta ta koreni har cewa tayi karna k'ara zuwan mata" Inna tace "Kai Hajara banda sharri a ina na koreki " Abba ne ya ce "Mamana tashi ku tafi banson doguwar magana" Tashi Aira tayi ta ce "To Abba a ranta sosai taji dad'i Dan daman kamar a k'aya take bata samun damar shan waya da Arman Yanzo ko gidan Inna ko kwana zatayi tana waya dashi ba mai sani d'akinta ita kad'aice kawai ta gwada batasone Dan inna tasan Taji Haushi Akwatinta ta d'auko wayoyinta daman suna ciki ta fito ta harari Inna ta ce . " To muje kuma wlh kika k'ara korata ko kika zagi Mamy na taho har abada bazan koma ba"To y'ar lelena Inani ina Kara korarki ni daman Chan ban zagar maki uwa ba Rahama ai y'ar kirkice bakiji sunan ba Rahama duk Inda kikaji an ambaci Rahama ai andace bakiga ba ko mutum mutuwa yayi ba Rahama ake nema mashi "Dariya Aira tayi sosai hada rik'e cike tace " To shikenan My Inna muje suma su Abba Dariya sukayi sosai Har Mamy wai yau itace Inna ke yabo . Su Aira na fita Mamy ta tashi ta cewa Mama"Yaya saida safe "To Auntynsu Allah tasheni lafiya Mama ta fad'a " Mamy ta kalli Aysha da murmushi fuskarta ta ce "Yau ko tayin bacci zai miki" Dariya Aysha tayi ta ce "Mamy muje saina kwantar dashi Dan karya tashi suna zuwa d'akin Aysha kwantar da Amer Sannan ta kalli Mamy ta na Sosa kai ta ce " Uhm Mamy Dan Allah wani taimako zakiyimun"Mamy tace "inajinki Aysha fad'a kai tsaye insha Allahu indai zan iya zan maki shi" Cike da kunya Aysha ta bawa Mamy labarin Saurayinta Abdulkharim da hadu Airport daga karshe ta ce "Shine yanzu yace yanason yazo ya gaishe da Abba shine nake tsoron yiwa Abba magana Dan Allah Mamy ko zaki fad'a masa nasan ke zai fahimce ki " Murmushi d'auke da fuskar Mamy ta ce "Ah masha Allah kice munkusa shan biki amma gsky Naji dadi karki damu Insha Allahu zanyi mashi magana ba matsala" Godiya sosai Aysha tayiwa Mamy Dan tasan daman itace zata fad'awa Abba direct yayi na'am. Mamy Bayan ta fito daga wanka jikinta daure ta towel ta dauki amer tana cikin sauyamai kaya Abba ya shigo kauda kai tayi kamar batasan yashigo ba Dan tun sanda sukayi rigima ta ke fushi dashi cikin kwantar da murya Abba ya ce "Haba sarauniyar mata Farar mace alkyabbar mata wai har yanzu baki huce ba Fushin nan ya isa Haka kinsan bazan jureba Airar ma data had'amu na yafe mata". " hmmm kawai mamy tace taci gaba da abunda Take Abba ya ce "To wai ba nace kiyi hakuri ba Haba my rahama bansanki da rashin yafiya ba "cike da kissa Mamy ta ce "hmm ya wuce Abban Aira amma karka sake irin haka gaskiya" Cike da farinciki Abba ya ce "Bazan sakeba Amma kema ki daina fad'amun magana son ranki gaban kowa" Murmushi kawai tayi a take suka shirya kamar basu tab'a fadaba(Su Abba da Mamy Daman ba a hakura da love ba😂🙈) cikin hikima Mamy ta fad'awa Abba sak'on Aysha sosai yayi farinciki daman yanzu kuma burinshi tunda ta gama karatu Aure kuma alhmdllh tunda ta samu cikin Sauk'i. Haka rayuwa taci gaba Aira komawarta gidan Inna sosai tayi mata dadi Dan tana samun damar shan wayarta da Arman da vedio call tarayyarsu taci gaba saima shakuwa da suka k'ara An sanya bikin Aysha Da Abdulkharim wata hud'u masu zuwa Wanda aka had'e da na Ummy itama Bayan gama karatunta Saurayinta ya turo Wanda dukansu cikin garin suke sosai hakan yayiwa iyayensu dadi. Su Abba ganin Aira ta nutsu ya sanya suka saki jiki da ita suke hamdalar ta rabu da Arman musamman mamy Arman saida Yayi wata biyu baizo garin ba Dan tunda Abba ya dakeshin nan bai sake zuwaba kullum Mummy cikin lallabashi take akan yazo tayi kewarshi Dan Arman ko sati biyu bayayi baizoba amma wannan tafiyar har wata biyu baizo tasan fushi yayi dak'yal ta samu ta shawo kanshi ya ce zaizo. Ranar da zaizo Aira sai Farinciki take Dan ya sanar mata ji take kamar ran sallah Tunaninta d'aya Inda zasu had'u Dan yace mata ko gidan Inna bazai dinga zuwa ba Dan kar a dinga samun matsala tana cikin tunani Dan tun d'azu yace mata jirginsu zai tashi wata dabara ce ta fad'o murmushin jin dad'i tayi Tabbas wannan shawarar ita ce kawai mafita cikin Sauk'i...........✍🏿 😱tofa wata shawara ce Aira ta yanke ????? _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/8, 22:36] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION* 📚 بسم الله الر حمن الر حين *BOOK ONE*📔 🅿️...............31&32 ......Cikin Sauri taje tayi wanka ta yi shirin Tahfex cikin ash din kaya da doguwar hijabinta jakar ta ta d'auka ta saka k'aramar wayarta Arman yana kiranta ya shaida mata yashigo garin kwatancen tahfex dinsu tayi mai ta ce a chan zai sameta da to ya amsa mata dan daman yasan Tahfex din. tana zuwa part d'insu Amma harta shirya napep suka Tara suka tafi suna gab da zuwa bakin get d'in makarantar Aira tace me napep din ya ajesu "Suna fitowa cikin marairaicewa Aira ta kalli Amma ta ce " Dan Allah taimako d'aya zakiyimun Yaya Arman ne zaizo mu gaisa bazanje makaranta ba Dan Allah ki Rufamun asiri kicewa Malam banda lafiya". "girgiza kai Amma tayi ya ce " Aira kenan Allah shiryeki Kardai kuje wani wajen daga nan a ina zan ganki idan antashi "ba Inda zamu sis ngd sosai Basu ida maganar ba ta Hango motarshi hug din amma tayi ta ce idan antashi zaki ganni " Amma ta wuce ciki itakuma Aira tayi baya cikin Sauri har taje Inda motar take back sit ya bud'e mata Inda yake ta shiga juna suka sakarwa murmushi Dukansu sunajin shauk'in k'aunar junansu Arman ya ce " I really miss you my cutie "Cikin shagwaba ta ce " Miss you too my yaya Ya hanya"Alhamdulilla fatan na sameki lfy . "Sosai suka dinga hira cikin nishad'i da Annashuwa har lokacin tashinsu yayi ganin anfara fiffitowa yasanya Aira Kallonshi ta ce " My yaya antashi Kar malamin mu ya ganni"To my cutie sai gobe Ai zamu had'u ko "murmushi tayi ta ce " Insha Allahu "wasu manyan ledoji ya mik'o mata guda biyu d'aya kayan makuleshene su choculate, biscuit'juice kala kala d'ayar kuma Kaza ce gashin oven guda biyu " . Kallonshi tayi a hankali ta ce "Thnks Yaya " Harararta yayi ya ce "ban hanaki yimun Godiya ba" Cikin shagwaba ta ce "Yaya aidole na maka Godiya ko Allah idan muka gode masa dad'i yakeji ya k'ara mana fiye da Wanda ya bamu a baya" Murmushi yayi ya ce "na manta fa mutuniyar tawa ustaziya ce " Dariya tayi tare da rufe fuska Rafar y'an dubu d'aid'ai ya mik'o mata cike da tsoro ta ce. "Dan Allah yaya kayi hakuri amma Bazan karba ba inma na karba Allah bansan Abunda zanyi dashi ba" Lokaci guda taga ya murtuke ya ce "Na k'ara magana baki amsa ba ranki zaiyi mugun b'aci kinsan dai banason gardama kuma bana kyauta a maidomun ko a k'i Amsa" Badan Aira ta so ba ta amsa ta ce "Nagode Yaya " lokacin da Arman ya tafi amma ta Iso Suka jera Suka tafi gida a k'asa Nan Aira ta nunawa Amma abunda Arman ga bata sosai Amma tayi mamaki ta ce. "Chab Kedai Kibi A hankali wlh kuma karki k'ara Amsar kudinshi ko ran nashi zai b'aci karki amsa ai dole ya huce " To Sister Aira ta ce "Sannan ta mik'awa Amma dubu Ashirin ta ce " ga naki sis"kin Amsa amma tayi Aira tayi ta mata magiya ta ce "Dan Allah ki amsa wlh ni Banmasan ta yanda zan kashesu ba " Amsa Amma tayi ta ce "Nima d'in bansan tayanda zan kashesu ba bari dai kawai na amsa" Suna isa gida Aira tayiwa kudinta mugun boyo kayan da ya kawo mata kuma ta ba Inna wasu Inna sai sa mata albarka take taci Wanda ta iyaci sauran ta kaiwa su Amma. Washegari da Yamma Aira ta shirya cikin hijab d'inta ta gida blue kasancewar Alhamis basa Tahfex a d'aki ta samu Mamy na linki Bayan ta gaisheta ta ce "Mamy Dan Allah gidan su Khady nake son naje idan kin barni zan duba ta bata da lafiya" "Ke ya akayi kikasan bata da lafiya"jiya da naje islamiya k'anwarta take fadawa Malam kinsan Tahfex d'inmu d'aya "To shikenan kije amma karki jima Dan Allah sannan ta mik'a mata dubu d'aya ta ce " Kiyi kudin transport A a Mamy ki barshi ina da kud'in da Abba ya bani jiya da zani Tahfex "Maida kudinta Mamy tayi batare da ta ce komai ba. Aira ko tasan wannan karyarce kadai zatayi mamy ta barta ta fita Aira tana zuwa gidansu Khady sun dan taba hira ba ajima sosai ba Arman ya kira ta ba Khady tayima Arman kwatancen gidan ba ayi minti sha ba sai gashi Nan Aira tayiwa Khady bankwana " Khady ta ce "haba kwt daga zuwanki daman Nasan zuwan nan naki ba banza ba " Dariya Aira tayi ta ce "Karki damu Besty zandawo nayi maki yini akwai labari" Har bakin get Khady ta rakata ganin ta shiga motar Arman ya sanyata Juyawa Aira ko da Arman yawo sukasha waje waje cikin nishad'i da Annashuwa Ganin magriba ta gabato ya sanya Aira cewa . "Yaya ka maidani gida Mamy ta ce kar nayi dare " Okay nima gobe zanwuce ki kulamun da kanki kinji kyakyawata"B'ata fuska tayi cikin shagwaba ta ce "Yaya jiya kazo ka ce kuma gobe zaka wuce" Kinsan yanayin Aikin namune bamuda Hutu sosai Amma ai kinsan bazan jima ba zanzo na k'ara ganinki"Cikin shagwaba ta ce "Yaya daman fa waccen tafiyar saida kayi wata kusan biyu bakazoba" " yanzu bazan sake dadewaba tunda my prince's bataso kamar karsu rabu da juna Arman ya tsaida mata napep ya bashi 10k mai napep sai Godiya yake saida yaga tafiyarta tukwana ya juya cike da kewarta a duniya shidai ya kasa gane wani irin sone Allah ya jarabceshi dashi na Aira Kwata_Kwata Ko wajen Aiki yaje Allah_Allah yake yazo ya ganta daidai da second d'aya da zai samu dama bazaiso yayi batare da Airanshi ba cike da so da kewarta ya koma gida washegari ya koma Abuja. Aira sosai take fachaka da kudi Dan ko Abincin gidan ta daina ci saidai ta aiki mai gadi ya sayo mata abunda take so Ummy da Aysha sunyi da ita ta fad'a musu Inda Take samun kud'i amma taki fadamusu . Yau Aira ta shigo d'akin Mamy kenan ta tarar da Haidar yana yiwa Amer wasa "K'arasa shigowa tayi ta ce " yau kuma Kaine d'an rainon kuma fa kayi kyau da rainon"Hararta yayi ya ce "Mamy ce tace na rik'e mata shi nayi maki kama da d'an Reno matsala ta dake wulakanci wlh ya Aira"Dariya tayi ta ce " Kardai kamun Rashin kunya kayiwa Arziki kulli Yaro "Naji ya fad'a tare da mika mata Amer amsarshi tayi ta ce . " Ina mamyn take"Tana Part d'in Abba "yawwa nasan ba yanzu zata dawo ba Aikenka zanyi yi Sauri kaje ka sayo mana Kaza da ice cream da shawarma ta fad'a tana fiddo kudi cikin siket d'inta" wara idanu Haidar yayi ya ce "Kam ya Aira ina kika samu kudi dubu goma ce fa kika bani ''ya fad'a yana juya kudin da ta bashi" Hararshi tayi ta ce "Dan kaci sa a zanci dakai shine Zakawa kanka inbazaka sayoba ban kudina" washe baki Haidar yayi ya ce "Chab wa yaga banza ya bari" Dariya Aira tayi ta ce "Uban son banza". Tana nan zaune tanayiwa Amer wasa sai Dariya yake Ba ayi minti sha biyar ba Haidar ya dawo da leda hannunshi plate suka d'auko suka baje kazar suka fara ci Haidar sai sawa Aira albarka yake tana Dariya ta ce " shegena banza ta samu"Dariya yayi ya ce "Aiko banza ta samu Allah karo na banzar muci mu nare. basu ida cinye kazarba kowa ya d'auki robar ice cream suka fara sha basusan ba Mamy ta shigo saida sukaji ta ce " Ubanme Kuke ci "cikin rud'u Aira ta tashi tare da ja baya Shima Haidar tashi yayi Kallon kayayyakin dake gadon tayi ta kalli Haidar ta ce " wa ya baku"Nuna Aira Haidar yayi cikin tsoro ya ce "ita ta bani na sayo mana" Kallon Aira Mamy tayi cikin b'acin rai Ta ce "Waya baki kud'i Dan ubanki harkika bada akayo wannan uwar sayayyar" . yarfe hannu Aira ta fara tare da mik'ewa kan gadon ta fara hawaye ta ce "Dan Allah Mamy Kiyi Hakuri bazan sakeba" Ubanki keda hakurin tambayarki nayi ko hakuri nace ki bani Munafuka sai anyi magana ta dinga yarfewa mutane hannu tana bada hakurin munafurci cewa nayi wa ya baki kud'i"Haidar yayi saurin cewa "Mamy saurayin Aunty Aysha ya bata ". Kallonta Mamy tayi ta ce "Na tambayi Aishar gyada mata kai tayi ta ce " Eh"Dannawa Aisha kira Mamy tayi tana zuwa ta Kalleta ta ce "Wai saurayinki Aysha ya ba Aira kud'i" Kallon mamaki Aisha tayiwa Aira ta ido Aira ta dinga nuna mata ta rufa mata asiri ta ce Eh "Eh Mamy shi ya bata " jin Abunda Aisha ta fad'a ya sanya Aira sauke ajiyar zuciya Gaskiya Haidar ya taimaketa har ya fita tunanin wannan mafutar Dukda baisan wa ya bani ba . "Itama Mamyn Ajiyar zuciya ta sauke ta ce " To angode sannan ta kalli Aira ta ce "Shine ko ki fadamun" nazata fad'a zakiyi shiyasa banfad'a maki ba "kede kika sani cewar Mamy Aira da Aisha suna fita suna Shiga Dakinsu Aisha ta tsare Aira da Tambayoyi akan saita fad'a mata Inda ta samu kudi badan Aira taso ba ta fad'awa Aisha Arman ne ya bata har wayar da ya bata saida ta fad'a mata " cike da mamaki aysha ta ce "Chabd'i amma Aira wlh kunfini rawar kai har ki rik'e har iPhone 13 ba tare da sanin kowaba''turo baki Aira tayi ta ce. " to Karki fad'awa kowa"Ba Wanda zaisani sister Amma ki fad'amun soyayya kuke da Arman koko ki fad'amun Gaskiya insha Allahu zan taimaka maki da shawarwari"k'asa da kanta Aira tayi wasu zafaffan hawaye na zubo mata ta ce "Aunty ina sonshi sosai nima bansan tun yaushe na fara sonshi ba amma dai na sani ina matuk'ar sonshi son da bazan iya rabuwa dashi ba " Cike da tausayin y'ar uwar tata Aysha ta ce "Nasan Hakan zata faru Aira banyi mamaki ba najima da zargin kuna son junanku keda Arman Amma shi ya tab'a fad'a maki yana sonki". Girgiza mata kai Tayi ta ce "A a a a" Karki damu sis komai zaizo da sauki insha Allahu nima zanbada gudummawata d'ari bisa d'ari Dan Gaskiya Arman dake ya dace haka kema dashi kika dace Allah dai ya sa iyayenmu su yarda Ku auri juna"Sosai Aira taji dad'in yanda Aysha ta nuna tanason tarenta da Arman Ranar sun jima suna Hirarraki. Haka Rayuwa taci gaba Aira sosai ita da Arman suke shan wayarsu Idan yazo kuma tasan dabarar da zatayi ta fita ba Wanda cikin iyayensu ya k'ara gane tare take da Arman sosai hankalinsu ya kwanta musamman Abba yana murnar Aira ta rabu da Arman baisaniba saima gaba da yayi. Komai aka sakawa Rana sai yazo ya rage saura sati Ukku biki Aysha Da Ummy suka tafi Umrah sai ana jibi za a fara event d'in suka dawo sosai suka k'ara kyau dan sunsha gyara a Chan baki na nesa da na kurkusa duk sunzo Har Yayarsu Aunty Maryam da ke Aure a Lagos tazo tare da yaranta Zainab(Yasmeen) Ahmad,Sadiq Aunty Halima ma da Hafsa duk sunzo. Haka aka fara hidimar biki sosai amaren sukeyin kyau ranar farko akai Friend evening rana da biyu walima rana ta Ukku Aka d'aura Auren Bayan kowacce an kaita gidan mijinta sosai Aira suka sha kuka musamman ita da Aysha Da dare aka shirya Dinner sosai amaren da angwayen sukayi kyau Wajen da ake dinner ma an kawatashi Aira ma ba abarta a baya ba Sosai Tasha kyau cikin wani tsadadden lace d'inta purple Anko anyi mata Riga da siket rigar mai dagewar nan sosai kayan suka amsheta ga make up d'inta da tayi bala'in mata kyau ko gyale bata yafe ba. haka aka fara gudanar da programs d'in cikin tsari Bayan anyi hotuna aka fara rawa sosai Aira ta saki jiki take rawa saboda ansa wak'ar da take mugun so kuma daman tace a bikin yayyin nata saita chashe Sosai ta burge mutanen dake wajen sai lik'i maza ke mata ganin haka ya sanyata saurin Zamewa ta fita daga filin rawar Taje ta zauna a kan chair tana zama wani ya biyoto ya zauna kusa ta isa Tare da cewa "Y'an mata yakike Gaskiya kin hadu ba k'arya kin burgeni sosai Dan Allah zan iya samun number wayarki" D'agowa Aira tayi ta Kalleshi daga k'asa har sama sannan taja tsoki,. wayarta babbar ta fiddo zaro ido tayi ganin missed call d'in Arman rututu cikin Sauri ta Danna mai kira Abun mamaki sai taji ringing d'in daga bayanta juyawar da zatayi idanunsu suka sartse cikin na juna Fuskarnan tashi a murtuke Kamar bai tab'a Dariya ba ya sanya hannuwanshi cikin Aljihu sosai Aira tayi mamakin ganinshi ko dai gizau ne yake mata amma ai da Yamma ma sunyi waya yake ce mata yana Abuja Bata gama wannan tunanin ba Taji ya........✍🏿 *Kamar yanda na fad'a a page 30 zamu gama book one ma ana free page to na k'ara muku page biyu wannan shine page din biyun karshe da zamu gama freee Wanda suka sayane kad'ai suke da damar cigaba da karanta wannan littafin ga mai buk'atar saya ya tuntub'eni ta wannan number 07026166536 haka zalika masu buk'atar a tallata musu hajarsu suma su tuntub'eni kan number wayata* *NORMAL GROUP #200* *V T U #300* *PC #300* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/9, 12:56] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* 📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚 بسم الله الر حمن الر حين _Last Free Page_ *BOOK ONE*📔 🅿️...............33&34 ........Ya Janyo hannunta janta ya fara yi tun tana tirjewa harta hakura Dan sosai ta tsorata suna fita farfajiyar wajen Hall din Ya wullata Ta fad'i dafe kanta tayi Wanda da kyal ya hana ya buge kuka ta fashe dashi ta ce. "Yaya Airanka ce fa da kajimun ciwo fa" Cike da b'acin rai Arman ya nunata da yatsa ya ce "Daman irin abunda kike bana nan,ki shiga filin rawa kina karkada jikinki ko wani k'are da doki yana karewa halittarki kallo kega mahaukaciya,ko gyale babu ga wannan tsinannun kayan da suka matseki ya mukayi dake kwanaki ban hanaki rawa ba sannan ban hanaki saka matsatsun kaya ba ,ban hanaki mu'amula da maza ba ,Duka abubuwan da na hanaki yau na kamaki da kaifinsu daman irin abunda kike bana nan" ya k'arasa fad'a cikin d'aga murya . Aira sosai tashiga tashin hankali tasan Idan ran Arman ya b'aci bai iya fushi ba Batasan lokacin da ta tashi ba ta fad'a jikinshi tare da sakin kuka ta ce "I'm so sorry yaya Bazan sakeba forgive me please kayi hakuri " Ajiyar zuciya Arman ya sauke sai yaji zuciyarshi tayi sanyi yana daga cikin abunda yake k'ara mishi k'aunar Aira da idan tayi laifi zata bashi hakuri koda kuwa itace mai Gaskiya bata da girman kan bada hakuri. daddab'a bayanta ya fara cikin kwantar da murya ya ce "yi shiru daina kukan is okay na hakura Amma karki sake kinji my cutie idan ba so kike zuciyata ta buga ba " Sosai Aira taji dad'i k'ara Rungumeshi tayi tare da Murmushi ta ce "Thnks yaya shiyasa nake sonka kana da saurin yafiya" Sai kuma ta rufe bakinta sai yanzu ta tuna b'aram b'aramar da tayi murmushi Kad'an Arman yayi sannan ya janyeta daga jikinshi kama hannunta yayi ya bud'e mata mota suka shiga ta na Front sit shi kuma yana mazaunar driver A hanya Aira ta ce "Amma Yaya ya akayi kazo wajennan Bayan nasan baka gari kuma bakasan Wajenba" Cutie kenan Kin manta yanzu kiwon mutum ake ba dabba ba"Cike da mamaki Aira ta ce "Yaya kiwon mutum kuma me kake nufi" Ina nufin kome mutum yake a idon mutane yanda akai nazo wajennan a isha'i ma ina Abuja Wajen 9:45 haka Wani Abokina Dake nan kano ya kirani yake Cemun yaga kanwata wajen wata dinner. Sosai nayi mamaki nace wace kanwartau sai yake Cemun nahau what's app zai turomun videon ta na gani idan ita ce "Ina hawa ya turomun videon ki kina rawa wasu tsinannun y'an iska na miki lik'i karkiga yanda hankalina ya tashi ban k'arasa Kalla ba na tashi na tafi Airport na yanki ticket na taho Ina zuwa na kirashi yayimun kwatancen wajen shi kanshi saida yayi mamakin cewa Na shigo garin" Cike da mamaki Aira ta ce "Chab Amma abokin nan naka anyi Dan sa ido to shi a ina ya sanni" A Hoto"Hoto kuma yaya a ina kenan Nida ba post din hotona nake social media ba "Hararta yayi ya ce " kima fara mana ki gani" Dariya tayi ganin yanda yayi maganar ta ce "wace ni wa ya haifeni a garin nan " Dariya yayi Kad'an sosai Komai Aira tayi take burgeshi ya ce "a d'akina da ya tab'a shiga Yaga hotunanki a lokacin ya nuna mun yana sonki na cemai kanwata ce kuma anyi mata miji Sai ya hakura " murmushi Aira tayi ta ce "Me ma zanyi da d'an sa ido gwara da kace mashi haka dukda dai ba ayimun mijinba". Harar wasa yayi mata yace "wa ya fad'a maki ba ayi miki miji ba Ai nariga da zab'a miki mijin da ya dace dake ko bazaki amince da zab'in yayanki ba" Murmushi tayi tare da Kauda kai ta kalli gefen titi Dan batason maganar"Baikara cewa komai ba harsuka isa gida lokacin 12pm danma Allah yasa a gida Ansan Dinner sukaje kuma a motar gida sukaje A ita za a maidosu saitaje ita gaba tayo, Bye bye tayiwa Arman Ta ce "Sai gobe yaya daan Allah gobe ka shigo Inna fa na nemanka" karki damu cutie zanshigo goben "Thnks my yaya bye bye ta fad'a tana daga mai hannu saida yaga shigarta tukwana ya wuce guest house d'inshi Dan yanzu yaje government house Mummy cewa zatayi ba Lafiya ba gwara ya bari sai gobe yaje ba . Washegari Aira da Amma sukaje suka gygyarawa yayun nasu gida saida yamma suka nufo gida kamar karsu rabu A Hanya Aira ta ce " Amma bakiga Aunty Aysha iyayin nan yau duk tayi lakwas ko bata lafiya dai bakiga ba a sanyaye take ba Yau shikuma Yaya Abdul sai wani lillike mata yake ba ko kunya a gabanmufa dazu yayi mata kiss". Dariya Amma tayi ta ce "Kikak'i tambayarta kafin mu taho kema da kukafi kusa baki saniba bareni y'ar karoro ko mu koma ki tambaya" Waro idanu Aira tayi ta ce "Rufamun Asirin Har ya koro mu" Dariya Amma tayi sosai ta ce "Nikuma ya Ummy ce ta ban Mamaki ji fa yau hada cewa Dan Allah karmu tafi mu bari sai Bayan Isha'i Yaya Usman ya maidamu yau ko jarabar babu "Dariya Aira tayi ta ce " Ba dole taso muk'i tafiya ba Barin gida ai saidole Ni ko tausayi bata banba yanzu dai shikenan mune manya a gida Aira ta fad'a tana murna Dariya Amma tayi ta ce "Wlhko muci karanmu ba babbaka Har suka isa gida Suna gulmar yayyin nasu. Bayan kwana biyu Arman ya koma Wanda dak'yal Ya shawo kan Aira saida ya shaida mata nan da two weeks zaidawo yayi hutun One months sosai Aira tayi farinciki haka ko akayi baiyi sati biyu ba ya dawo Aira jinta take cikin Farinciki Marar musaltuwa Tunda yazo Aira ta tarki k'aryar fita Wanda Aysha ce ta d'aure mata gindi saita kira Mamy ta ce " Dan Allah Aira tazo ta tayata Aiki haka Mamy zata barta batare da kokontoba Dan yanzu Hankalinta ya kwanta a tunaninta Aira harta mance da ARMAN. A palourn Aysha suke zauniya su sha Hirarsu Saisu shafe awa Hud'u suna Hira Yauma yazo Aysha ta sa Aira ta kawo mashi snacks Kad'an yaci Shima Dan Aisha ta nuna bazataji dadi ba Sosai Aira da Arman suke shan hira Sai wajen magriba Arman ya tashi yace zasu wuce " "tashi Aira tayi ta ce " bari naje nayi mata bankwana saimu tafi "ta fad'a ta na Zuwa Palourn Chan ciki Inda Aysha take da mijinta " Abdul ya ce su Aira manya Angama Shan Love din"Dariya tayi tare da rufe fuska ta ce "Kai yaya kaima haka zakace Nasan Aunty zata fad'a maka " Aysha dake jikin mijinta kallon Aira tayi ta ce "Ai yanzu ba wani rufe rufe y'an matan Abba yanzu kuma sai ina". Uhm gida zamu wuce"Okay to ki gaishe da mutanen gidan"To Aunty zasuji "Saikuma yaushe " Sai idan kuma an barni kinsan dazu dak'yal Mamy ta bari cewa tayi nafiya miki zarya"Dariya Aysha tayi ta ce "Lallaima Mamy Danma batasan ba ba saboda ni ake zuwaba Duka zuwan na Arman" Dariya tayi ta ce "Kai Aunty Nifa saboda ke nake zuwa Yanzu dai munwuce kar ya gaji da jira" Okay to Allah kiyaye Aira harta juya zata fita Aysha ta kira sunanta Juyowa tayi tashi Aysha ta kama hannunta ta ce "Sis karki bari wata matsala ta afku kidinga bi a hankali kinsan Abba yasan kuna had'uwa da Arman a gida na ni kaina na shiga ukku sannan ku daina yawo barkatai a gari Dan Allah saboda gudun zargi " k'asa tayi da kanta ta ce "Insha Allahu Aunty zan kiyaye " Hug din juna sukayi tukwana Aira ta tafi Bayan Aira ta tafi Mijin Aysha ya ce "My love abunda kike kina kyautawa kuwa?Cike da mamaki Aysha ta ce " Me Dia"Na barin Aira da Arman suna kebewa anan mana Bayan iyayenku a yanda kika fad'amun sun rabasu me zaisa ki basu shawarar su hakura da juna Ita kuma ki bata shawarar ta tunkari karatunta Amma wannan hanyar da kika bud'e musu ba mai bullewa bace yanda Abba keda burin y'ay'anshi suyi karatu banga Alamun ko Kad'an a idon Aira akwai wani karatu a ranta ba bakiga Duka Rayuwarta a soyayyar ARMAN take tafiya ki bata shawarar Ko bazata rabu da shi ba ki nuna mata karatu zatayi kafin inma auran ne ya biyo baya bakiganin yarinyace marar wayau"ya k'arasa fad'a yana Jan numfashi "Shiru Aysha tayi Tabbas hakane cike da damuwa ta ce " Baby bazaka gane bane Aira da Arman suna matuk'ar son junansu Wanda ni kaina bazan iya kwatanta maka kalarsa ba ta Riga ta mutu a kanshi tun kafin tasan kanta Shima kuma haka sauya musu ra'ayi Abu ne mai wahala dalilin da yasa kuma nake barinsu zuwa nan dole ne fa saisun had'u a koma ina ne gudun kaucewa hanya kasan ance duk Inda mace da namiji suka had'u na ukkunsu shaid'an ne dukda nasan ba halinsu bane amma kiyayewa na da kyau hakan yasa nace su dinga zuwa nan yafi kwanciyar hankali akan suje wani wajen daban Ina son y'ar uwata Abdul sosai bantaba Jin a raina ba wai ba ciki d'aya muka fito da Aira ba sonda nake mata yafi son da nake yiwa wanda muke uwa d'aya uba d'aya Dan haka bazanyi Abunda zai chutar da ita ba "hakane kuma baby da wata ya wannan Allah dai ya kawo musu mafita cikin Sauk'i " Ameen Aysha ta fad'a . Aira ko Arman har gida ya maida ita kullum saisun had'u idan basu hadu ba idan zata tahfex to sun hadu idan ta dawo Innace ta fito Cikin masifa Kallon Aira tayi tare da mik'a mata wayar ta ce " kiramun Mujahid laifin me nayi mishi da ya daina zuwa wajena "Aira ta kira mata Mujahid yana ganin kiran Inna murmushi yayi ya kira cikin Masifa Inna ta ce " Mujahid ko d'an fari na kashe maka ai sai haka watanka nawa rabonka da gidana "Hakuri Arman ya dinga bawa Inna tare da cewa gashinan zuwa yanzu Lokacin da yazo Aira na zaune akan sopa tana kallon wani series a Bollywood Hankalinta na wajen ya shigo tana ganinshi itama ita yake kallo kashe mata ido yayi girgiza kai tayi ta na murmushi inna ko washe baki tayi ta ce "" " Ko kaifa mai gidan Har hankali na ya kwanta ashe ma kana garin shine Ko kazo ka gaishe ni ko"To yanzu ba nazo ba y'ar tsohuwa sai a rufe chapter ya fad'a yana zama kan sopa K'asa Inna ta zauna Suka shiga gaisawa da Arman sai zolayanta yake dayake tana son ganinshi yau ko fad'an Babu Kallon Aira tayi da take kallo ta ce . "Hajara bakiga Mujahid ba ne Kika wani kauda kai" Juyowa Aira tayi ta ce "Na ganshi Inna ta fad'a tana kauda kai" Hakan da tayi duk cikin shirinsune "Salati Inna ta farka ta kalli Arman ta kalli Aira ta ce " Nashiga Ukku ni Halima ba dai Iyayenku sunyi nasarar raba ku ba. Kallon Inna Aira tayi ta kalli Arman dake satar kallonta tashi Inna tayi Ta kamo hannun Aira ta janyota ta had'a da na Arman ta fashe da kuka ta ce "Karku sake Iyayenku su zama sanadiyar lalacewar daddaddiyar Tarayyarku mai cike da Albarka Na tabbata Allah da abunda ya gani ya had'aku Karku sake ko dad'i ko wuya suyi nasarar rabaku koda bana numfashi Duk sanda alak'arku ta lalace to ina da tabbacin komai ya Riga da ya lalace Iyayenku bazasu tab'a Shiryuwa ba muddin bakwa tare da junanku Kune nake fatan ku zama silar Daidaituwar Iyayenku kuyimun Alkawari Dan Allah bazaku rabu ba kodan ni ko da bana raye" . Aira tunda Inna ta fara jawabin nan take kuka Rungume Inna tayi Cikin kuka Ta ce "Insha Allahu Inna munmuki Alkawari sannan ma kina raye insha Allahu" Arman ma Rungume Inna yayi cikin k'arfin hali ya ce "da yardar Allah Inna zamu sanyaki Farincikin da kike buk'ata da ranki insha Allahu" Allah yayi muku albarka Ya nunamun Ranar da nake ta tsumayen jira da raina da lafiya"Kallon juna Arman da Aira sukayi sai kuma Aira ta sadda kai. Washegari Aira na bangarensu ta na Wanki A washing machine Mamy ta lek'o ta ce "Aira idan kin gama ki shirya zaki rakani Gidan Safiya zanyi mata barka" To Mamy Ai na gama ma bari naje na shirya Cikin kankanin lokaci ta shirya a parking space ta tarar da Mamy "Mamy ta ce duk'ursa na goya maki shi " Cikin marairaicewa Aira ta ce "Goyo kuma Mamy ki bari na daukeshi wlh d'annan naki nauyi garai Yaro wata shidda ai Yama wuce goyo ni banma iya goyon ba" Hararta Mamy ta yi ta ce "To yau saiki koya idan dankine wazai goya miki " Dariya Aira tayi ya ce "Maid house mana Mamy yanzu Dan Allah taimaka ki bari na rikeshi a hannu" to Naji raguwa muje Motarta Mamy da dauko tayi mata key suka bar gidan Aira na gaba da Amer a hannunta. Suna isa gidan Safiya Mamy tayi mata barka Hjy Safiya ce ta ce "Wai Rahama y'armuce ta zama Haka Allah mai iko kice kin kusa Taramu" Dariya Mamy tayi ta ce "Aikodai ku iyaye saiku fara shiri Fita Aira tayi ta basu waje Arman ta kira tayi mashi kwatancen Inda Take cikin k'ank'anin lokaci ya kira ya shaida mata yazo. tsayuwar Hijab d'inta ta gyara tukwana ta fita A mota ta tarar dashi ciki ta shiga Arman ya ce " kindai maidani bita zaizai ko My cutie duk Inda kikayi ina binki"Dariya Aira tayi ta ce "Yaya kenan ni kuma a kirani da me da duk Inda naje ina kiranka" Sun tab'a Hira Kad'an cikin nishad'i Sun kwashi wajen minti Talatin Mamy koda suka gama fira da Hjy Safiya suka fito sosai tayi mamakin k'in ganin Aira da batayi ba Tana fitowa waje bata ganta ba Aira ko ta cikin mota ta Hango Mamy sosai gabanta ya fad'i ta ce "Na shiga ukku '" 'Kallon Inda take kallo ARMAN yayi ya ce " Daman tare kuke da Mamy"Eh wlh yaya wlh banzaci har zata fito yanzu ba"To yanzu yi Sauri ki fita danma Mamy ce Ai da sauki "Kamar wacce kwai ya fashewa haka Aira ta fito daga motar Sosai Mamy ta kafeta da idanu ganin Fitowarta daga mota Aira ko dukta tsure bin motar da Kallo Mamy tayi Bayan ya tafi Kallon Aira tayi da ta kasa motsi ta daka mata tsawa ta ce " Saikizo mu wuce gida ko" "Cike da tsoro Aira ta shiga Mota Mamy ta zagaya ta tada Ranta na matuk'ar k'una tama rasa ita ina zata saka ranta game da Lamarin Aira daman basu rabu ba kenan Aira ko duk ta tsure jira take taji zagi ko saukar dukan Mamy amma bataji ba harsuka isa Mamy Saidai ta Kalleta ta girgiza kai ta ma rasa abunda zatace " Suna isa Aira ta ce "Mamy Dan Allah kiyi hakuri" girgiza kai kawai Mamy ta yi ta ce "Allah ya shiryeki Allah ya shiryeki ita kad'aice Addu'ar da zan dinga maki ta fad'a tare da shigewa ciki Aira ko kamar wacce kwai ya fashewa Haka ta shiga part d'in Inna idan ta tuno kuma da karfafa gwuiwar da Inna tayi musu saitaji sanyi A ranta. Bayan Sati Biyu Da misalin k'arfe goma Na dare Aira na kwance wayarta tayi ringing d'auka tayi Dan tasan Arman ne kad'ai ke kiranta " ki shirya yanzu ina palourn inna zamuje wani wuri,Cike da mamaki Aira ta ce fita kuma Yaya ?ina zamuje a Daren nan "kede kiyi abunda nace kinsan dai bazanyi Abunda zai cutar dake ba Kuma kinfi kowa sanin bansan gardama " Badan Aira ta lamunta ba ta ce To yaya Doguwar Hijab Ta d'auko tare da sanya flat takalmi ta fesa turare d'an Kad'an ta fito a palour ta tarar dashi shida Inna tana fitowa Inna ta ce. "To kumaza kuje Allah kiyaye" Kallon Mamaki Aira takebin Inna Dashi to ina zasu a Daren nan Arman ko har yayi gaba binshi baya Aira tayi Tana zuwa harya tada Mota da yake ciki ya shigo da ita Aira na shiga suka ja suka bar gidan daman get man ya bud'e musu kofa. Aira dai zuciyarta cike take ta tunannika kala_Kala"A wani katoton shagon make up taga yayi parking Kallonshi tayi murmushi yayi mata ya ce "muje ko" Itama mayar mashi da murmushin tayi"Ta bishi suna shiga Shagon y'an mata biyu Aira ta tarar Duka sun girmeta Cikin girmamawa suka dinga gaishe da ARMAN ya amsa sama sama Mai kwalliyar ta ce . "yallab'ai ko ita ce " Gyad'a mata kai yayi ya ce "ita ce so nake kiyi mata kwalliyar da Baki tab'a yiwa wata irinta ba ko nawane zan biyaki" Dariya Zey tayi ta ce "Angama yallab'ai kai kanka dak'yal zaka ganeta" Haka nakeso Rafar y'an dubu ya bata guda biyu Zey sai Godiya take dan yau ta warke Kallonshi Aira tayi Shima ita yake kallo murmushi ya sakar mata bata samu damar mayar mashi ba saboda a tsorace take saikuma ta tuna Ai Arman bazai tab'a abunda zai chutar da ita ba hakan yasa ta saki jikinta. Fita Arman yayi ya ce zaije ya dawo itadai tana zaune mai make up ta sanyata tayi wanka a toilet d'in Shagon tana fitowa ta bata wata had'ad'd'iyar gown Fara ita kanta Aira saida ta tsorata da ganin rigar Dan bama zata iya kwatanta Misalin kud'inta ba irin rigunan Amaren nan ce Amaren ma sai d'an waye da wane Bayan Aira ta sanya rigar sosai tayi chif a jikinta kamar a jikinta aka d'inka rigar. Ba b'ata lokaci aka shiga tsansarawa Aira kwalliya ta ban Mamaki saida suka shafe sama da Awa d'aya tukwana aka gama ya subhanalla Ai Ni kaina kasa gane Aira nayi ta sani sauya kamar ba ita ba tayi wata irin masifar kyau Wanda ko mace ta ganta saita yaba da kyan da tayi mai make up cewa take masha Allah a Gaskiya bantaba make up mai kyan wannan ba kodan nayi a jikin me kyau ne kanwata ki godewa Allah Gaskiya yayi miki kyau da baiwa kala kala" "murmushi Aira tayi ta ce "Nagode hotuna Sosai Zey da abokiyar aikinta suka dinga wa Aira 11:30 Zey wayarta tayi ringing itadai Aira bataji me akace ba daga dayan bangaren Taji dai ita ta ce " Eh Angama Yallabai yanzu haka muna shirin Tahowa da ita ne bada jimawa ba "tana gama wayar itama ita da d'ayar suka shirya cikin wasu Riga da sicket pink rigar siket din bak'i rigar Anyi rubutu a jiki an rubuta *A & A* k'asar rubutun kuma anrubuta HBD MRS..sauran rubutun taga An rufe da wani Abu ita dai bata tambayesuba har suka gama shiryawa suka fito a wata dalleliyar mota suka shiga Aka jasu suka tafi Basuyi wata diguwar tafiya ba motar ta tsaya Alamun sunzo wajen da zasu Kallon Aira sukayi tare da kama hannunta Zey ta d'auko wani Farin kyalle sai kamshi yake Duka zanan heart ne jikinshi zagayawa sukai suka rufewa Aira idanu dashi itadai kawai binsu take taga ikon Allah. a haka suka dinga Jan hannunta idonta Rufe suna zuwa wani waje taga sun damk'a hannunta jikin na wani ko wata ita dai bata bambance ba tana nan tsaye anyi kusan 5 minutes tukwana taji Wanda yake rik'e da hannun nata ya fara since mata Kyallen da aka rufe mata Idanu Har ya isa sincewa yana gama sincewa Taji suka wajen ta d'auko satin wak'ar Love mai narkar da zuciya wara idanunta tayi Dan son ganin Da gaskene ko mafarki take Arman ta Kalla dake sakar mata murmushi sosai yayi kyau sanye yake cikin bak'ar coated Fuskarnan tashi Cike da annurin farinciki a cikinta. Juyawa tayi ta kalli wajen Bata San Lokacin da ta furta Kalmar wow ba "Duka wajen Anyi mai decoration na ban mamaki ko biki Sai y'ar gata zata samu wannan daular Duka wajen kuma robobine ga wasu danjoji da suke Rubuta Happy Birthday Aira Wasu na fita wasu na fitowa ga kuma mutane Sunkai 20 Sanye da Riga An rubuta *A A HBD MRS ARMAN* Photographer ko sunfi biyar hada Camerar gidan wasu gidajen television ta gani bama ta Tantance gidan television d'inba Juyawa tayi ta kalli wata k'atotuwar Laptop dake nuna duk abunda suke Alamun Live Kenan Kallon Arman tayi da ya ke ta kallonta Yasan dole tayi mamakin duk wannan Abun da ya shirya . Ai batasan lokacin da ta fad'a Jikinshi ba ta saki kuka " Tallabota yayi cikin rad'a ya ce "Kiyi shiru mana so kike ki b'ata make up d'inki ko so kike mutane suce Matar tawa saurin kuka gareta " Dagowa tayi ta Goge hawayenta saikuma ta zumb'uro mai baki Murmushi yayi ya kama hannunta . A wani makeken High Table suka Je K'atoton cake shake wajen zan iya cewa tunda nake ban tab'a ga cake mai girma da Kyanshi ba Ga wata had'ad'd'iyar agogo dake Juyawa a Gaban wajen Rik'e hannunta yayi Tare da wuk'a a hannunsu. Mutanen wajen ne suka hau lissaafi daidai lokacin da 12 ta kusa Bugawa 1,2,3,4,5,6,7,8,9,10 Arman ya kama hannunta suka Yanka cake Duka wajen tab'i ya d'auka tare da wakar Happy Birthday Aira sosai wak'ar tayi Bala'in dad'i Aira zata iya cewa cikin rayuwarta bata tab'a shiga farinciki irin wannan ba kwata kwata ta ma mance yau ne ranar birthday d'inta sai yanzu ta tuna . Ita ta fara bashi cake d'in a baki tukwana Shima ya bata ya na Gama bata Ya amshi Abun magana tare da kallonta duka camera na kanshi k'asa da kanta Aira Tayi Ya fara magana cikin zazzak'ar muryarshi kamar haka "Alhamdulilla Alhmdllh Alhamdulilla My Love sister she's +1 year God bless you for many more years Happy Birthday Lover for you is the real,real,real,a deal a really ,really really big deal You are my North Star and help me know my direction in life you make me happier and a better person Happy Birthday to you My cutie Aira I Love I Love I Love you so much My Cutie Please Love Me my Aira sannan ya durk'usar da gwuiwarshi har k'asar Inda take tare da kallonta ya had'e hannayenshi biyu Alamun rok'o ya ce " will you marry me?...........✍🏿 *Tofa ya kenan Arman ya k'ara ringimo wata rigimar ya kuke tunanin iyayensu zasuyi idan sukaga wannan birthday d'in a duniya*??? *Wani irin mataki kuke tunanin Abba Da Daddy zasu d'auka Kuna tunanin zasu bari wannan Abun ya tafi a banza kuwa*?? *Yau dai Arman ya fito ya bayyanawa Aira tare da duniya Kalar son yake mata tilon d’an governor guda ya dukursawa mace cikin bainar Jama’a* *Iyayensu zasu samu daman raba su kuwa*??? *ya makomar soyayyarsu zata kasance nan gaba Zasu mallaki juna ko akasin haka* *Idan iyayensu suka samu damar rabasu ya kuke tunanin halin da wannan masoyan zasu shiga yanda suke jin bazasu iya cigaba da rayuwa ba ba tare da d'ayansu ba* *Shin Abba da Daddy Zasu shirya kuwa*????? *Duka wannan Amsoshin zaku samesu ne kai tsaye idan kin biya 200 kachal zaku karanta cikin kwanciyar hankali karku bari kice sai an sata a kawo maki ki karanta ba girmanki bane Hajiya ki biya ki karanta cikin nutsuwa da kwanciyar hankali darajarshi tafi ta kudin na barshi hakane a saboda k'auna da soyayya Masoyan Asali*💃💃💃 *wannan shine last page na free page na wannan littafin kamar yanda na fad'a daga yanzu sai Wanda suka biya ne suke da damar ci gaba da karanta wannan k'ayattacen littafin mai cike da salon burgewa sannan duk Wanda zata saya ta saya da zuciya d'aya Karki saya ki fitar mun da Littafi kud'in karantawa kika biya ba na mallaka ba Kunsan dai mahimmanci hak'k'i Sarai bazanyi Allah ya isa ba Ammafa ban yafe ba akwai hak'k'i ni da yaya Arman koda kudinka saida rabonka nasan babu wacce zataso ayi tafiyar nan babu ita ga masu bukatar saya ga tsarin yanda biyan yake* *Normal group Transfer Ko hoton katin MTN #200 kachal* *PC Wanda basa buk'atar sakasu group ta PC zandinga tura musu zasu biya #300* *VTU 300* *Zaku turo ta wannan number 07026166536* _Saimun had'e a Paid group_ Taku har kullum 👇 *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/11, 16:49] Hajo hajo: 🅿️....*35&36* ........."Will you marry me??Aira da jin kalaman Arman kawai take tamkar a mafarki " Dagowa tayi ta Kalleshi batasan lokacin da wasu zafafan hawayen farinciki suka fara zirarowa daga idanunta ba "Cikin saurin Arman ya tashi tare da d'aukar handchiep ya fara Goge mata hawayen ya ce " Kinsan bansan kukanki My Love ki bari"d'agowa Aira tayi ta Kalleshi Shima itad'in yake kallo idanunsu suka sartse Cikin na juna Aira batasan lokacin da ta fad'a Jikinshi ba har yanzu ji take kamar mafarki yau Itace Arman ya bayyana mata kalar son da yake mata kuka ta fashe dashi Arman jin kukan nata Yake har cikin ranshi daddab'a bayanta ya fara cikin sigar lallashi ya ce "I m sorry cutie bansan ranki zai b'aci ba ko baki sona ?cikin muryarta mai kama da wacce ta sha kuka ta ce " I love you too yaya I love you so much I can never live without you yaya I love you more "Duka wajen tab'i ya dauka tare da sakin wak'ar love sosai suka burge mutane da dama dake wajen Ai Arman baisan lokacin da ya k'ara kankameta ba cike da farinciki ya ce " Thnks you thank you thank you so much My Love Bazan tab'a iya kwatanta maki farincikin da nake cikiba "Aira ko shiru tayi jikinshi tana shak'ar daddan k'amshin turarenshi Mai narkar da zuciya Sosai Akayi bishasha a birthday din kamar wani biki Wanda wadanda sukajema saida suka.shaida arziki daga k'arshe ARMAN yayiwa Aira kyautar Sark'ar gold tare da Dan kunnenta da zobenta wadda a k'alla ta haura sama da 3million A matsayin special gift d'inta na birthday Aira jinta take kamar a mafarki tama kasa kwatanta kalar farincikin da take ciki 12:40 aka tashi daga kayataccen birthday d'in a Mota d'aya Aira da Arman suka shiga Driver ya jasu tana baya ta lafe jikinshi Tayi shiru Arman ko yau jinshi yake kamar ya sauke wani katoton dutsi a kanshi ya fad'awa Aira abunda ke ranshi A mota sai zolayanta yake itadai tayi shiru Dan wata kunyarshi kuma take ji. B'angaren gidan Su Aira Mamy harsun kwanta Aunty Maryam ta kira Abba saida ta kusa Katsewa tukwana ya Dauka cikin rud'u Maryam ta ce " Abba kuna ganin abunda nake gani yanzu kuwa"Abba ya ce me kenan "ku kunnan tashar Haske Television(k'irk'irarrar Tasha ce )yanzunnan zakuga abunda nake gani Mamy ce ta tashi ta ce " Lafiya Abbansu "To kawai Abba ya cewa maryam sannan ya fad'awa Mamy abunda maryam ta ce mashi " A tare da Abba da Mamy suka fito palour suna shigowa sukaga Mama da su Amma suna kallo Duk a tsaitsaye Alamun abun al'ajabi suke kallo A sanyaye Abba da Mamy suka kai dubansu TV sosai hankalinsu ya tashi ganin abunda ake nunowa a tashar kuma Live tundaga lokacin da Aira da Arman suka Yanka cake har zuwa Maganganun da Arman yayiwa Aira na soyayya da Rungumeshin da Aira tayi Da ita ma Kalaman da ta mayar mashi komai saida suka gani har zuwa kyautar da yayi mata "d'ora hannu a ka Mamy tayi ta ce " na shiga Ukku Abbansu me nake gani kamar Aira "Abba da ranshi ya gama b'aci Zuciyar shi tafarfasa kawai take cikin tashin hankali ya kashe t v safa da marwa ya fara kafin ya bar palour cikin tashin hankali Mamy kuka ta dukurshe tanayi Mama ta lallasheta ta ce " Kiyi Hakuri Ni kaina nayi mamakin al'amarin nan garin Yama ta fita cikin Daren nan "Mamy cikin kuka ta tashi tabi Bayan Abba Bangaren inna Abba ya nufa cikin tashin hankali ya dinga buga mata k'ofa Inna cikin bacci ta fito ta na wanene " Abba yace nine "tana bud'ewa cikin tashin hankali Abba ya. Ce " Ina Aira??Sosai gaban Inna ya fad'i ta ce "basu dawoba" Cikin tashin hankali da zafin rai Abba ya ce "Daman da saninki ta fita" Kuka Inna ta fashe dashi ta ce "Kai amma yaran nan sun chucheni daman basudawo ba" Abba da ranshi ya gama b'aci yasan wata maganar ma ya kumayi ran Inna zai iya b'aci a yanda yakeji baice komai ba ya juya Mamy ko cikin kuka ta ce "Inna ina sukace maki zasu" Inna bata bada amsa ba sai sharb'ar hawaye take inna ganin Mamy ta dameta cike da borin kunya ta ce “to ni ina zan San inda take kema uwarta baki saniba bare ni ta fada tare da rufe dakinta ta koma ciki sai rarrabe ido take Itama Mamy Juyawa tayi cikin tashin hankali ta koma gida Mamy tun tana kukan har ta dawo tana zubda hawaye Abba wajen mai gadi yaje yayi ta surfamai masifa akan ubanwa ya bashi umarni budemai gida har wani ya fita shi kanshi mai gadin saida ya tsorata hakuri ya dinga bawa Abba Komawa ciki Abba yayi Wanda Da za a shiga zuciyarshi a fito da ita tofa da za aga tana ci da wuta tsabar bacin ran da yake ciki Safa da marwa kawai yake Mamy ko tayi tagumi sai hawaye take "Nikam ya Aira takeso dani mutuwata takeson gani kome" ta fad'a tana hawaye. B'angaren gidan su Arman ma haka ta kasance Duka abunda ya faru Mummy da Daddy sun Kalla sosai ran Daddynshi yayi kololuwar b'aci itadai Mummy hakuri kawai take bashi. Aira bata tsorata ba saida sukazo bakin get d'in gidansu Sai sannna ta tuna da tashin hankalin gida idan suka gani"Kallon Arman tayi cikin hawaye tace "Yaya tsoro nakeji" karki damu ba abunda zai faru "Shiya kama hannunta suka fito Sukayi knoking mai gadi yazo ya bud'e musu " Kallon Arman mai gadi yayi ya ce "yallab'ai da zakubi shawarata Karku shiga gidan nan ka kaita wani waje ta kwana dukda bansan abunda ya faru ba Amma muddin ta shiga komai zai iya faruwa Dan ran me gidan ya b'aci sosai'"Kuka Aira ta fashe dashi tace" ka gani ko yaya"kama hannunta Arman yayi suka juya suka shiga mota driver ya umarta da ya wuce government house har suka isa Aira kuka take shikuma sai aikin lallashinta yake a tare suka shiga makeken Babban palourn gidan Aira na baya tana hawaye tana biye dashi Mummy da Daddy suka gani tsaitsaye Sosai Aira ta tsorata Arman ko ajikinshi "Kanshi Daddy yayo cikin Masifa ya ce " Daman kalar tarbiyar da na baka kenan,hakan da kayi me kenan me kake nufi ka fa sani bamu kadai muka kalli abun nan ba duniya ce gaba d'aya me kake tunanin mutane zasu d'auki Lamarin nan Mujahid kana cikin hankalinka kuwa ka rasa wacce zaka durkusawa cikin bainar jama'a sai mace macen ma wacce bazaka tab'a Auranta ba har abada muddin ina numfashi"Sosai ran Arman ya b'aci jin Kalmar Daddy ta k'arshe ya ce "Daddy ina sane nayi hakan Dan na gwadawa duniya Kalar son da nake mata kuma duniya ta shaida kuma ku shaida idan kuna tunanin wasa ne ku daina tunani sannan kuma Aira ita ce Mata ta insha Allahu bazaku iya rabamu ba Tunda bamuda masaniya a rigimarku Dan haka bazata shafemu ba " sosai ran Daddy Ya b'aci ya d'aga hannu zai wankawa Arman mari Mummy ta rik'e ta ce "Haba Alhaji yaron nan da Gaskiya ya fad'a Akanme duk kukeso kubi ku rikitawa yara rayuwa Bayan suna son junansu Gaskiya ya fad'a babu ruwansu a rigimarku a kanme zai shafesu " Cikin fad'a Daddy ya ce "ke daman na Riga da sanin ke kike daurewa yaron nan gindi Bakijin irin maganganun da yake fad'amun bako d'a'a sannan ya kalli Aira da ke lab'e Bayan Arman ya ce " ita kuma da ka taho da ita ina zaka kaita ko so kake ka k'ara jamun wulakanci wurin mahaifinta kamar yanda ka jamun a kwanakin baya"Sai sannan Mummy ta kalli Aira Wajenta ta nufa tare da kamo hannunta ta ce "Taho y'ata " a sanyaye Aira tabi Mummy "Arman ko cewa yayi kwana zatayi kafin gobe " yana gama fad'ar hakan ya haye sama "Kallon Mummy Abba yayi ya ce " Fatima kina ganin abunda d'anki yayi ko ban fad'a maki irin wulakanci da mahaifinta yayimun ba a saboda shi shine yanzu zai kawo mana Ita gida to ba gida na ba ya maidata gidansu ko yaje ya nemu Inda zai kaita"Mummy ce ta ce "Haba Alhaji wai wannan wace irin rayuwace To babu Inda zataje da Daren nan haba wannan Abun da kuke kanku kuke wulakantawa wlh d'iyar d'an uwan naka uwa d'aya uba d'aya kake cewa ta bar maka gida idan mahaifinta yayi maka Abu ai ba ita tayi maka ko a lahira laifin wani bai shafar wani Dan haka ba Inda zata" cikin fushi Daddy Ya fice daga palourn bai kara cewa komai ba Mummy ko Aira ta Rungume tayi ta lallashi ganin kukan da take ta ce "Ki kwantar da hankalinki.kinji y'ata nid'in Tamkar uwa nake a wajenki muje kije kiyi wanka ki kwanta " makeken bedrom d'inta Mummy takai Aira Ta bata towel ta cire doguwar rigar jikinta Taje tayi wanka tana fitowa Mummy ta miko mata wata rigar bacci marar nauyi tasa Aira duk a kunyace take A Gado d'aya mummy da Aira suka kwana sosai Mummy ke k'aunar Aira har cikin ranta. B'angaren gidan su Aira Mamy da Abba cikinsu babu Wanda ya rintsa Mamy ga Karin tashin hankalinta na k'in dawowa da Aira tayi Inna ko tana Chan duk ta tsure. Washegari tunda Safe kiran Mama Halima ne ya tayar da Arman Cikin fad'a ta ce "Tun jiya nake kiranka bansameka ba abunda kukayi kun kyauta kenan Arman da hankalinka da komai Dan iskanci kuyi wani birthday a idon duniya to inbaka saniba tuni labari ya bazu ko ina har social media zancen da ake kenan tun jiya da daren " Murmushin gefen baki Arman yayi ya ce "Mama ai haka nakeso tunda su Daddy suna d'aukar abun wasa hakan yasa na bayyanawa duniya" Cikin fad'a Mama Halima ta ce "Mahaukatan banza ita ina Airar ta ke" Ta na d'akin Mummy,okay gidanku ta kwana kenan?Eh Mama "To Kada ka sake ka maida ita gidansu Ran Yaya ya b'aci sosai Dan na kirashi Yanzu Naji ranshi matuk'ar b'ace zai iya mata dukan da zata kasa tashi ka kawomun ita nan Kd anjima" Ajiyar zuciya Arman ya sauke Dan daman yanzu matsalarshi Hukuncin da Aira zata fuskanta Wanda bazai jurewa hakan ba "To big Mama saimunzo" ja'iri "Mama Halima ta fad'a murmushi yayi. Driver ya aika ya sayowa Aira rigar da zata saka ya ba da aka Aiko mata Bayan tayi Wanka ta shirya cikin kayan da ya Aiko mata sosai sukayi mata kyau sannan ta yafa Belt din rigar ko hoda bata shafa ba kallo d'aya zaka mata kasan tana cikin tashin hankali Mummy tazo ta ce " Daughter harkin tashi kenan "k'asa da kanta Aira tayi ta ce " Eh Mummy ina kwana"Lafiya qalau Kintashi lafiya "Alhmdllh ta fad'a a sanyaye kama hannunta Mummy tayi ta ce " kindaiki sakin jiki da ni ko Daughter keda gidanku amma sai bakunta kike"murmushin da bai kai ciki ba Aira tayi ta ce "Ba haka bane Mummy" to yaya ne"shiru tayi tama rasa abun cewa A dining suka tarar da Arman yana breakfast cikin kwanciyar hankali kallo d'aya Aira tayi mai tayi kasa da kanta Kujera taja ta zauna Mummy ma ta zauna Mummy tayi serving d'in Aira Kad'an taci ta ce ta k'oshi"Mamy ta ce "a a a baki isa ba saikin cinye wannan D'an dankalin da kikaci zakice kin koshi ha a d'aga bakin Mamy ta fad'a tana d'auka a spoon ta Saka mata a baki " murmushi Aira tayi sosai taji Mummy ta shiga ranta cikin shagwaba Arman ya ce "Mummy Nifa''Harararshi tayi ta ce " y'ar tawa zan fasa ba na baka d'an karere "b'ata fuska Arman yayi ya ce " Kai mummy "Sannan ya kalli Aira dake yar dariya cikin so da k'auna ya ce " My cutie bazakicewa Mummy nima ta bani ba "mak'e kafada Aira tayi ta na wurgamai Harara ta ce " kayi girma da yawa "Dariya Mummy tayi ta ce " Fad'a masa dai Shi inaga baisan ya girma ba "cikin raha har suka gama cin abincin Sosai Aira ta fara sakin jiki da Mummy Dan ta lura kwata kwata bata da wata matsala a rayuwa ga yanda take nuna mata so wannan ne lokaci na farko da ta tab'a ganin Mummy saboda Daddy baya barinta zuwa Chan suma kuma Abba baya barinsu zuwa nan shiyasa basu San juna ba sai a Hoto idan Arman ya nuna mata itama mummyn a Hoto take ganin Aira. Arman ya fad'awa Mummy yanda sukayi da Aunty Halima akan yakai Aira Chan " cewa ta yi "Me makon ka barmun ita nan" a a Mummy Chan din yafi kwanciyar hankali kafin komai ya lafa"jinjina kai tayi ta ce Hakane kuma Allah dai ya kyauta "Sosai ta had'a Aira da tsaraba Turamen atamfofi shida ta ce ta kaiwa Mama Halima biyu hud'u nata banda kayayyakin makuleshe da turarruka har Parking space Mummy ta rakasu Hug din juna Mummy da Aira suka yi tukwana Shima Arman yayi hug din Mummy ta shafa kansu ta ce " Allah ya kiyaye yayi muku Albarka "Da ameen suka Amsa har suka fice tana musu bye bye sosai Aira ta shiga ran Mummy Daman ita a rayuwarta tana son y'a mace sai taji Aira tamkar y'arta muddin Arman ya samu Aira a matsayin mata da saitafi kowa farinciki. Kai tsaye Airport suka nufa duk Inda suka gitta ana kallonsu wasu hada cewa" Wallahi su d'inne "wasu kuma suce " laila majnon kenan"wasu kuma na gardamar couple's ne wasu na cewa a a saurayi da budurwa ne "kowa na fad'ar albarkacin bakinshi Dan cikin k'ank'anin lokaci video d'insu ya baza duniya duk Inda suka wuce ana kallonsu (😂nikam nace Aira da Arman fa kunzama cele)Cikin kankanin lokaci Arman yayi musu clearing d'in komai jirginsu ya tashi Cikin kankanin lokaci suka isa Kaduna Aira daman ba wannan ne lokaci na farko hawan jirginta ba idan zasuje garin su Mamy ko zasuje lagos gidan Aunty maryam a jirgi suke zuwa Aunty Halima ya kira yace sun iso suna Airport ta ce " su jira ga driver nan zaizo ya d'aukesu sosai sukayi mamakin anan d'inma kaduna sai kallonsu ake Itadai Aira duk ta tsure ga tunanin Gida Dan batasan irin hukuncin da Abba zai yanke mata ba driver yazo ya d'aukesu A hanya Aira ta kalli Arman ta ce "Yaya Saboda me kayi haka kasan Abba bazai kyaleniba" karki damu cutie nayi hakan ne saboda na gwadawa su Daddy kalar son da mukeyiwa junanmu Susan Soyayyarmu tayi k'arfin da bazasu iya rabamu ba hakan zai iya sawa su hakura su barmu mu mallaki juna"Aira badan ta gamsu da maganarshi ba ta gyada kai ta ta ce "Amma ya akai Inna ta bari ka tafi dani hadafa yimana saimun dawo Murmushi yayi ya ce.........✍🏿 *littafin Ni da yaya Arman na kud'ine it's #200 via Katin MTN to 07026166536 v t u #300 PC #300* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/12, 17:01] Hajo hajo: 🅿️.......*37&38* .....Ya ce "Keda kikasan Inna saurin sayuwa gareta sayayya na had'o mata na rikita ta nace ta bani ke zaki rakani wani bikin best friend Dina kuma kowa da budurwarshi yake zuwa sannan na had'ata da 100k nace ko minti ashirin bazamuyi ba zamudawo "karkiga yanda ta rude hada cewa bari taje ta tadoman ke" Dariya sosai Aira tayi ta ce "Kai yaya amma wlh kasan logar Inna" shafa sajenshi yayi ya ce nid'in na wasa ne "cikin shagwaba tace" to baka tunanin Abba Da kowa zai gani me yasa kakira yan gidan television"Murmushin gefen baki Arman yayi ya ce "Saboda su shaida kalar son da nake maki" Uhm kawai ta ce "ta d'ora kanta a saman kafad'arshi Ta ce " My yaya wai tun yaushe ka fara sona haka"Tun ranar da kikazo duniya "ya fad'a yana murza lallausan hannunta sannan ya ce " kece ma zan tambaya yaushe kika fara sona haka kodan Kinga d'an beautiful ko"Hararar wasa tayi mashi ta ce "Kaine dai kaga y'ar beauty ka rud'e" Dariya Arman yayi ya ce "to oya nima fad'amun yaushe kika fara sona" Cikin k'asa da murya ta ce "Tun sanda ina zanin goyo" Dariya sosai maganarta Tabawa Arman saida ya dara Suna isowa Gidan Aunty Halima Har cikin get d'in gidan Mai gadi ya shiga dasu Shima had'adden gidane flat da ya tsaru da shuke shuke Saidai baida wani girma sosai Dan Parking space d’in bazai wuce ya d'auki mota Ukku ba Aira ta fara fita tukwana ARMAN Shima ya fito Hafsat ce ta rugo da gudu daga ciki ta Rungume AIRA ta ce "oyoyoy my Fav sis sannunku da zuwa Gaskiya i'm glad to see you” " Itama Rungumeta Aira tayi ta ce "Nima nayi farincikin ganinki sister Tukwana suka shige palour Arman ma yabiyosu Bayan sun zauna Hafsa ta ce " bari na kira Mama ta na ciki ta fad'a tare da shiga Tare suka fito Hafsat da Mama da harara Mama ta tare su da ita Arman ko murmushi yayi tare da cewa "Sannu da fitowa big Mom uwata ta kaina" Harara Mama ta aika mashi ta ce "marar mutunci nizakayiwa dad'in baki kai yanzu abunda kayi ko ince kukayi ganinku kun kyauta" Haba Mama ki bari mu gaisa mana sauran fad'a saiya biyo baya "Arman ya fad'a " Aira ko kasa tayi da kanta "Mama ta ce " baza a gaisa ba d'in wlh karkaja nayi maka shegen Duka a gidannan "Dariya Arman yayi tare da tashi yaje fridge ta d'auko ruwa ya ce " tunda ba ayi mana tayi ba bari mu d'auka da Kanmu ya fad'a tare da d'auko cup ya tsiyaya ya sha sannan ya k'ara tsiyayawa Ya mik'awa Aira ya ce "My cutie amshi kisha nasan kinajin kishi" Aira da duk kunya ta isheta ta lura Arman kwata kwata baisan meye kunya ba k'asa tayi da kanta Mama ta ce "Marar kunya kawai " Aira ta d'ago gabanta na faduwa ta ce "Ina kwana Mama "Lafiya qalau Mamana ke yanzu abunda kukayi kun kyauta kenan kuje ku jawa kanku bakin duniya bakin mutane ma aka barku dashi ya isheku dole saita hakane zaku bayyanawa duniya kuna son junanku Dan tsabar shak'iyanci" Aira tuni idonta ya ciko da k'walla cikin kuka ta ce "Mama kuyi hakuri bazamu sake ba" Haba Mama Kinga kin sanyamun ita Kuka Dan Allah abar fad'annnan haka shikenan "Arman ya fad'a yana mik'awa Aira Handchiep Girgiza kai kawai Mama tayi ta ce " Allah kyauta kai daman ai nasan ba kunya gareka ba Sannan ta kalli Hafsa ta ce "jeki hado musu breakfast" Aira da Arman sukayi rigen cewa "mun karya kafin mutaho" Hafsat ce taja Aira ta ce "Taho muje ciki sis Arman har suka wuce yana kallonta cikin so da k'auna " Mama ce ta sauke ajiyar zuciya Bayan su Aira sun wuce ta kalli Arman ta ce "Wai me ya kaika hada abun nan jiya maimakon kazo ka sameni ka fad'amun komai mubi komai a hankali har mu samu Iyayenku su Amince Amma kaje ka rikita Abu karkaga irin fad'an da Babanta ya dingayi dazu da na kirashi " Mama a tunanina hakan da mukayi shi zaisa su gane kalar son da mukeyiwa junanmu har su hakura su bari mu mallaki juna "girgiza kai Kawai Mama tayi ta ce " Allah ya kyauta Gaskiya zance nafi kowa jin dad'in wannan al'amarin Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya ida nufi"murmushi ARMAN yayi cikin jin dad'i yace "Ameen Mama yanzu kikayi magana wlh ina son Aira sosai Mama bazanso abunda zai raba mu ba Dan Allah kiyi mana kokari ki shawo mana kansu" ya fad'a kamar mai shirin yin kuka"Insha Allahu zanyi iya bakin kokarina "Daganan suka cigaba da hirar duniya sai wajen Azahar Arman yayi musu bankwana ya wuce Abuja. Aira ko suna Chan suna shan hira da Hafsa tana nuna mata hotunansu da vedio wadanda ta gani a social media sosai Aira tayi mamakin yanda abunsu ya bazu duniya cikin k'ank'anin lokaci. Mamy ce zaune gefen kujerar Abba ta na hawaye ta ce " Abban Aira Dan Allah ka taimakamun a nemo Inda Aira take harfa Azahar yanzu kayi hakuri mu nemeta karta b'ata"cike da b'acin rai Abba ya hayayyak'o mata ya ce "Ke ki tashi kije ki nemeta da yake ni na aiketa na rantse da Allah kika k'ara zuwamun da maganar nemanta ranki zaiyi mugun b'aci ki barni da abunda ke damuna Dan tsabar rainin hankali harma nemanta kike yarinya ce ita kuma ina nan ina sauraran zuwanta Saidai ki haifi wata y'ar badai ita ba" Kuka Mamy ta fashe dashi ta ce "Wlh ko ta dawo bazaka kashemun y'a ba duk ba kai kaja ba da baka raba suba da duk haka ta faru ina dalili tunda suna son junansu ku barsu mana Su auri juna kawai in banda ana son a samun y'a cikin wani hali nidai wlh na gaji kawai a nemu mafita" Abba ji yake kamar ya d'auke Mamy da Mari tsabar bacin rai da kyal ya iya control d'inshi ya tashi ya bar mata d'akin tare da barin gidan Gaba d'aya mamy ko durk'ushewa tayi ta na kuka mai tab'a zuciyar mai sauraro. Da misalin k'arfe Tara na dare Aira suna dinning suna dinner ita da Hafsat da Mama sai faruq Wanda Aira tsakular abincin kawai take hankalinta duk yana wurin Mamy "Mama ce ta lura da haka ta daddabata ta ce " Mamana Yadai ko bakyajin dad'i"girgiza kai Aira tayi ta ce "a a Mama " to menene"Mamy ta fad'a ta na hawaye "to shine kuma saikinyi kuka uwar y'an shagwaba Bari mu gama na kira maki ita " cikin murna Aira hada Dariya ta ce "thanks Mama" suna gama dinner Mama ta kira Mamy ringing Biyu ta d'auka Daga d'ayan b'angaren mamy tayi sallama Mama ta amsa Tare da cewa "Yadai Naji muryarki wani iri maman Aira" ba dole ba Halima tun jiya fa Aira bata dawo gida ba Gashi Abbansu yaki saurarena "Ajiyar zuciya Mama ta sauke ta ce " Aira fa ta na gidana Ni nasa ya kawomun ita saboda nasan halin yaya a lokacin nan zai iya illatata"Ajiyar zuciya Mamy ta sauke Wanda har saida Mama taji cikin waya ta ce "Alhamdulilla Halima kin taimakemu wlh kuwa da ta dawo din da illatatadin zaiyi gwara da take nan din daman tashin hankali na ba asan Inda take ba " Ai nasan hakan zata faru shiyasa idan komai ya lafa zanzo muyi zama Dan Gaskiya yaran nan nason junansu inba wani hali akeso ajefa rayuwarsu ba"Mamy ta ce "Wlh maman Hafsa nima tuni na hango hakan amma Abbansu yaki ganewa kamar ma Kara zugashi ake ni da sunbi ta tau kawai su barsu muga yanda Allah zaiyi" Hakane Allah dai ya shige mana gaba Mama ta fad'a sannan ta ce "ga Airar ku gaisa A tsorace Aira ta amshi wayar ta ce " Hello Mamy ina yini"Lafiya qalau ya kaduna d'in"Alhmdllh Mamy "Sosai Aira tayi mamakin Mamy yanda ta nuna mata kamar ma komai bai faru ba " To sai anjima "Mamy na fad'ar hakan ta kashe wayar Ajiyar zuciya Aira ta sauke Dan kashi Hamsin cikin d'ari na tashin hankalin da take ciki ya ragu yanzu kuma saura na Abba batasan Me zata tarar ba. Sosai Zaman Aira gidan Mama Halima yayi mata dadi Hankalinta ya d'an fara kwanciya kayan hafsat take sanyawa Arman ko ya maida kd kamar gida kusan kullum sai yazo sosai yake son fita da ita amma mama halima ta kasa ta tsare tace bazasuyi mata shiriritar yawon da suke a kano ba dan haka kome zasuyi suyi a gidanta yau ma Arman yazo Dagashi sai ita a palour suna zaune kujerar 2siter kamar zasu shige juna Aira sai shagwaba take mai akan ya tafi da ita Abuja shikuma yana biyeta sai Lallashinta yake " da Hira tayi dadi Aira ta ta d'ora kanta kan kafad'arshi tana shak'ar daddad'an k'amshin turarenshi har wani lumshe ido take shiko baiyi kokarin dagata ba dukda duk lokacin da jikinsu suka had'u Dana juna yana cutuwa "Mama Halima ce ta shigo d'akin Salati tayi ta ce " me zan gani haka Mamana"Cike da rud'u Aira ta tashi ita tama manta da d'akin Mama Halima suke "Hararta tayi ta ce " Wuce ciki"cikin sauri Aira ta wuce hada tuntub'e Mama ya zaki korata kuma saboda ita fa nazo ki bari mu gama hira mana "Arman ya fad'a" kai daman nayi maka Ittik'afin kanka marar kunya Kunzo kun wani manne kamar chumgum "Dan murmushi Arman yayi tare da tashi ya ce " Ai munmafi gum Mama chumgum ai yana fita cikin Sauk'i "Pillown kujera Mama Halima ta d'auko tare da wulla mai tace wuce kaban wuri marar kunya so kake ka fitsarar mun da y'a" Dariya yayi ya kauce tare da Yin hanyar fita ya ce "y'artakice dai take son ta fitsarar dani" ya fad'a yana barin d'akin "Ja'iri ai zaka dawo ka sameni Mama Halima ta fad'a tare da wucewa Dakin da Aira take ita da Hafsat kwance ta tarar dasu Suna kallo a wayar Hafsa cikin fad'a Mama ta ce " Ke yanzu Mamana Dan gidanku haka ake hira kije ki lik'e jikin namiji Ko kunya gaku fitsararru'cikin shagwaba Aira ta ce "Mama yaya Arman ne fa " Arman din dan gidanku to wlh daga yau ki kama kanki kar in karaga kina shigemai jiki da da yanzu ba d'aya bane ki shiga hankalinki "To Mama yi hakuri Bazan sakeba" Yawwa y'ar kirki Mama ta fad'a tare da cewa ku fito ku d'ora mana abincin Dinner kunsan dai inada zakad'a zakad'an y'an mata kamarku bana shiga kitchen ba Dariya Aira da Hafsa sukayi Aira ta ce "Gaskiya ne big Mama muje ta fad'a tana kama hannun Hafsa suka sauko kan gadon. Aira saida tayi sati biyu a Kaduna Tukwana Mama.Halima ta fara tunanin yanda zata kaita gida Mamy ta kira Bayan sun gaisa ta ce " ya ake ciki nan din Maman Aira Yaya ya huce kuwa"eh ko a a zance Dan Gaskiya bai sake maganar ta ba Kuma na fad'a masa tana wajenki baice komai ba "Ajiyar zuciya Mama Halima ta sauke ta ce " to kina ganin ba matsala gobe mu taho ko mu bari dai ya k'ara hucewa"Duk yanda kikace maman Hafsa Magana na wajenki "to bari muga gobe zamu shigo insha Allahu idan ya huce ni da sai ya bani ita ta zauna nan muga yanda hali zai bada" to Halima nagode sosai Allah dai ya bar Zumunci "ba komai ai yiwa Kaine ko na baki Airan ku gaisa" a a barta kawai sai anjima ngd "tukwana sukayi bankwana. Washegari da safe Mama da su Aira sukayi shirin Tahowa kano Aira duk Inda hankalinta yayi dubu ya tashi sosai take fargabar haduwarta da Abba Wajen 10 suka fito Suna shirin shiga mota su tafi Airport motar Arman da danno dakatawa sukayi saida ya Iso kallonsu yayi ya ce " ina zuwa kuma Mama na ganku hada kaya"Kano zamu"Mama ta bashi amsa "Kano kuma Mama da kun bari ba yanzu ba" Yau mukayi niyyar zuwa ko zaka hanamu"Allah huci zuciyar big Mom Allah kiyaye amma nifa Gaskiya anshiga hakkina nan yafimun kusa ina ganin my cutie kullum ya fad'a yana tsare Aira da idanu sosai tayimai kyau cikin goduwar Riga Atamfa ta yafa gyale matching da kayan fuskar nan fayau sai hasken annuri "Itama Airan shi take kallo bako kyaftawa sosai yayi mata kyau cikin Shaddarshi da tasha aikin manyan mutane Fuskarnan tashi fayau ba ko Alamun damuwa a cikinta kafe juna sukayi da kallo bako k'iftawa Saida Arman yace karki cinyeni" Tukwana ta dawo daga duniyar tunanin da ta Lula "Hararar wasa ta aikamai cikin shagwaba ta ce " ba Kaine ka fara kallona ba "Murmushi yayi ya ce " To laifi ne Dan na kalli mata ta "Nima laifine Dan na kalli yaya na ta fad'a tana tsatsareshi da idanu irin ba wasan nan" Dariya yayi sosai ya ce "Keidai ki fad'i abunda ke ranki so kike kice laifine Dan na kalli mijina" ai tun kafin ki fad'a na shiga zuciyarki Naji abunda takeson furtawa"Uhm to ni ai bance ba Kaine kace haka"Kuma hakane ba Dan zuciyarki bazatayimun karyaba"Mama Halima ce ta ce "To marassa kunya a gaban nawa ma nafa lura kwata_kwata ku bakwamajin kunya ta ko " Murmushi Arman yayi ya ce "Wlhko Mama kamar kinsani " Bugu a baya Mama ta kaimashi ya kauce tace "ja iri da ka tsaya mana sannan ta kalli Aira ta ce " Saikishiga muje "Kallon Arman Aira tayi ta ce " yaya zamu wuce "Ai tare zamu tafi yaza ayi ku barni" Mama Halima ce ta ce "Wallahi baka isa ba Bazaka bimuba ka bari ma naje na samu na kashe gagarumar wutar da ka tada ba Inda zaka bimu ka k'ara tada mana wani bomb din" Dariya sosai Arman yayi ya ce "please Mama bansan cutie tayi nesa dani" tsaki Mama Halima taja ta ce "Saikayi kuma amma bazaka bimu ba Dan haka kama maza ka wuce Inda ka fito" Badan Arman ya soba yaki binsu ba ya koma Abuja su kuma suka kama hanyar kano Dan sunje Airport jirgin zai jima bai tashi ba hakan yasa kawai driver ya wuce da su kano. K'arfe 12 da wani Abu tayi musu a Kano sosai Aira gabanta ya fad'i har suka isa gidansu addua take Dak'yal Mama Halima ta samu ta fito daga mota duk a tsorace take har suka isa Babban palourn gidan Mama da yaya Umar sai matarshi suka tarar a palour Ajiyar zuciya Aira ta sauke ganin basu tarar da Abba ba "Mama ce ta ce lale marhaban mutan kd sannunku da zuwa " Mama ta tarbesu Zaunawa sukayi aka gaggaisa Sannan ta kawo musu ruwa Aira duk ta rakube ta zama kamar wata bakuwa "Umar ne ya gaishe da Mama Sai kallon Hafsa yake khadija ko sai wani shashshan magani take a takaice ta gaida Mama Halima Aira ce ta ce " Yaya ina yini anzo lafiya "Lafiya qlau y'ar gidan Inna sannan ya kalli Hafsa ya ce " wai Mama Hafsa ce ta girma haka"Murmushi Mama tayi ta ce "Ai ka jima baka ganta ba shiyasa Mama Halima ta ce " Ai ganinka Babana wuya yake "Murmushi yayi ya ce " Mama yanayin Aiki ne sai a hankali yanzu ma Hutu ne muka Dan samu zuwanmu kenan"Allah ya taimaka yayi jagora "ameen " Hafsa ce ta ce "Ina yini ya Umar" Cike da Fara a ya ce "lafiya qlau Hafsa ya makarantar har Angama ko" Eh "to Allah ya taimaka " Ameen ta fada Sosai ta tsarugu da Kallon da ya Umar ke mata "Khady ko sai cika take tana batsewa tana Aika mata da harara Mamy ce ta shigo " zaunawa tayi suka gaisa da Mama Halima cikin mutuntawa Aira dai kanta a k'asa "dak'yal ta d'ago ta ce " Mamy ina yini"Lafiya qalau mutanen kd ke Kd dinma tafi amsarki harda k'iba"Murmushi Aira tayi Mama Halima ta ce "Nima haka nagani Ai shiyasa nazo mutafi da kayanta ni da kun bani ita ai sai Aure ya raba" Dariya Mamy tayi ta ce "nidai indai nice na baki halak malak sai ki hada kiyi twins Hankalina ma ni da yafi kwanciya" Dariya Mama Halima tayi ta ce "Kamar gaske " Sosai suka shiga hira cikin raha "Amma ce ta shigo Da gudu ta fad'a ta ta Rungume AIRA ta ce " oyoyoy sis Gaskiya nayi kewarki da yawa wlh gidan Duka baya yimun dadi da bakyanan"nima nayi kewarki sis daga ina kike"Amma bata kai ga Amsa mata ba Abba ya shigo sosai Aira ta tsure cikinta ya d'uri ruwa Cikin b'acin rai Abba ya nuna Aira da yatsa ya ce "........✍🏿 *Ni da yaya Arman na kud'ine ki biya #200 kachal to 07026166536 ki karanta cikin kwanciyar hankali karki fitarmun da Littafi kud'in karantawa kika biya ba na mallaka ba bazanyi Allah ya isa ba amma ki sani akwai hak'k'i* *_Miss Hajo ce*_ [6/13, 08:16] Hajo hajo: 🅿️.......*39&40* ......Ya ce "me ya kawo wannan gida na me take a gidana maza maza ki gaggauta barin gidannan kafin na sauya maki kamanni" Aira cikin tashin hankali ta tashi ta Ruga ta boye Bayan Mamy ta makalkaleta tare da sakin kuka ta ce "Dan Allah Abba kayi hakuri Bazan sake ba " Mama Halima ce ta ce "Kayi hakuri Dan Allah yaya bazata sake ba ka zauna muyi magana ta fahimta" Ba wata maganar fahimta Halima daman na lura yanzu dake kike d'aurewa yaran nan gindi me ya maidota gidana ta koma gidanki bani ba ita na hakura da ita ko ita kad'aice y'ar da na Haifa na hakura da ita ku gaggauta ta barmun gidana bansan ganinta"Aira kuka ta k'ara fashewa dashi ita kam ta shiga ukku dak'yal Mama da Mama Halima suka dinga bawa Abba hakuri suka samu ya zauna Mama Halima ta ce "Dan Allah yaya ka saurareni muyi magana munsan sunyi laifi amma kayi hakuri saika yanke mata hukunci cikin nutsuwa ai hannunka bai rub'ewa ka yanke shi ka yar" Abba na huci ya zauna ya ce "wani hannun tuni kake yardashi karya isheka da Wari ku maza ina Sauri ku fad'amun me ke tafe daku" Ajiyar zuciya Mama Halima ta sauke ta ce "Daman yaya akan maganar Mamana ce nazo mu baka hakuri Dan Allah kayi hakuri ka yafe mata Allah ma munayiwa laifi ya yafe mana " Ai babu wani zancen daidaitawa Nida wannan yarinyar tunda bazatabi umarni na ba to fa nima bazan sassauta mata ba Ai tunda har ta iya d'aukar kafa ta tafi har kaduna wajenki nikuma ai tafi k'arfi na ta koma wajenki da zama bani ba ita "cike da damuwa Mama Halima ta ce " wannan laifi na ne Yaya wlh ni na sanya Mujahid ya kaimun ita saboda nasan kayi fushi daman jira nayi ka huce amma kayi hakuri Dan Allah ina neman alfarma Dan Allah Dan darajar iyayenmu da suka haifemu suna k'asa ka taimakamun ka yafe mata wlh tayi nadama bazata sakeba "ta k'arasa fad'a tana hawaye " shiru Abba yayi yana daidaita nutsuwarshi na y'an sakanni.kafin ya d'ago ya ce "Wlh taci darajarki da kuma darajar iyayenmu da kika Ambata zan yafe mata ta zauna a gidana Amma saida sharuddan nan da zan lissafo guda hud'u kuma cikinsu ba d'aya da za a kuskure idan kun amince dasu to zata zauna a gidana idan kuma baku amince su ba to na hakura da ita ta koma gidanki ko kuma taje duk Inda zata na hakura da ita" Cikin Sauri Mama Halima tace "munyarda zamu amince insha Allahu wasu sharudda ne" Aira ko duk ta tsure tana like da Mamy sai kuka ta ke Itadai Mamy batace uffan ba Yaya Umar ma saurara kawai yake Dan baisan case d'inba daga Mama Halima sai Abba kadai suke magana "Abba ya ce " sharad'i na farko shine "zata zauna a gidannan bazata k'ara lek'a ko bakin get ba hatta ko Tahfex na cireta bazata k'ara zuwa ko ina ba sannan zata dawo nan part din ko bangaren Inna nayi mata iyakar shiga kun yarda da wannan?Ajiyar zuciya Mama halima ta sauke ta ce " Mun yarda,na biyu kuma "Babu zancen jonawarta Makaranta Kamar yanda ko wani d'ana nake tsaye musu harsu kammala Degree d'insu kuma shine Babban burina da tsarina tundaga kan yayyinta to banda ita ko Diploma bazatayi ba " Kallon Aira Mama Halima tayi ta ce "Kinaji kin yarda " gyad'a kai Tayi tana kuka Alamun ta yarda "Kallonshi Mama Halima tayi ta ce " Shima mun yarda " Na Ukku babu ita ba Yaron Chan Nayi mata katangar karfe dashi babu wace alaka ko a fili ko a boye da zata k'ara shiga tsakaninsu Shima kun yarda da shi?Mama Halima cikin damuwa ta ce "Haba yaya d'an uwanta ne fa " d'aga mata hannu Abba yayi ya ce "na fiki sanin hakan amsa kawai kun yarda eh ko a a " Kallon Aira Mama Halima tayi Ta ce "Kinaji abunda yace Amsa na wajenki kin yarda?Sosai Aira ta shiga tashin hankali amma kuma ba yanda zatayi muddin tanason zaman lafiya da mahaifinta dole ta amsa ta ce " Eh na yarda"Amma har cikin zuciyarta ba wai ta yarda zata rabu dashi d'inba ta amsa ne kawai Dan ta samu sassauci.Kallon Abba Mama Halima tayi ya ce "mun yarda " To hud'u kuma na k'arshe shine "Aure zanyi mata?Cikin tashin hankali Mamy ta mik'e ta ce " Aure kuma Alhaji Sadakarta kake nufin zaka bada ko me?Eh Aure Kamar yanda na fad'a Tunda shi take so kuma shi zanyi mata bazata daukomun magana ba sannan ko sadakar ta kama sai inbadata abunda ya dace da ita ai"Tashin hankali ba a gwada maka rana Aira ita bama zata iya cewa ga halin da take cikiba kuka kawai take " Mamy ce ta ce "Wlh Ba a isa ba Daman na lura duk cikin gidan nan ka tsani Y'ata Duka cikin Y'ay'anka wa kayiwa Aure a age d'inta sai ita Dan tsana me ta tsare maka a gidan shekarar sha 18 ma bata ida ba to Allah bazan yarda ba laifin me tayi ko cikin shege tayi ai sai haka Inbanda lalacewa akan d'an d'an uwanka ake wannan Abun laifine Dan sunyi soyayya dashi matsafine ko d'an giya ne ko kuma wani mashahurin boka ne da za a sanya mun y'a cikin wani hali dan tana sonshi ai ba sab'on ubangiji bane Ku barsu mana Suyi soyayyarsu inma Aure ta kama ni ina bada goyon baya d'ari bisa d'ari tunda suna son junansu amma wlh bazakayiwa y'ata Aure ba yanzu " ta k'arasa fad'a cike da masifa "Tashi Abba yayi ya nuna ta da yatsa ya ce " Sau nawa zan fad'a maki idan ina yanke hukunci akan y'ay'ana ki dainamun katsalandan Ke kike da iko akanta ko ni Na rantse da Allah idan ba so kike ranki yayi mugun b'aci ba na kowa ya b'aci ki k'ara shigarmun idan na yanke hukunci "ran nawan ya b'aci na kowama ya b'aci sai me ko me zakamun yau kamun a shirye nake wlh " Mama Halima ce ta kama hannun Mamy ta ce "Dan girman Allah Rahama kiyi shiru tun d'azu da muke magana bakisa bakiba yanzu ma kiyi shiru kiwa girman Allah da darajar iyayenki ki wuce d'aki "Dakyal Mama Halima ta samu Mamy ta wuce ciki " Mama Halima tace "Yaya ku rik'a sassauta zuciyarki Dan Allah kayi hakuri ka janye maganar ka ta k'arshe sauran Duka mun amince dasu na karshen ne yayi tsauri" Cikin fad'a Abba ya ce "to ku tashi ku bani wuri daman na ce muku ai d'aya bazan hakura cikin hudunnanba idan baiyi mukuba babu dole ku tashi ku barmun gida Aira da take shan kuka Muryarta harta dishe ta ce " Na amince Abba "ta fad'a tare da tashi tana kuka ta wuce Bedroom d'in Mamy tana Zuwa ta haye kanta ta fashe da kuka Kamar wacce akayiwa mutuwa " sosai kowa dake palourn saida ya tausayawa Aira sai sannan Yaya Omar yayi magana ya ce "Dan Allah Abba kayi hakuri ka janye na karshen" Na gama magana kuma babuja da baya Abba ya fad'a tare da tashi ya fice part d'inshi"Girgiza kai Mama Halima tayi ta ce "Nima Allah ya kawoni Allah ya kyauta tukwana ta wuce d'akin mamy ta samu Aira na kanta sai risgar kuka take Mamy ko tayi tagumi sai huci take " Zaunawa gefen gadon Mama Halima tayi ta ce " Kuyi hakuri Rahama Kalar tamu jarabawar kenan Allah ya bamu ikon cinyeta "Cikin hawaye Mamy ta ce " Yanzu Halima ki duba kiga Akwai adalci a maganganun Alhaji kuwa"numfasawa Mama Halima tayi tukwana ta ce "Ni fa a ganina duk wannan maganganun yayi su ne cikin fushi Amma bazai aiwatar ba tunani na kawai zai tsorata ta da haka ne amma sai nakega bazai mata Aure ba Ki duba kiga yayyinta Duka saida suka kammala Degree d'insu A kanta bazai karya akidarshi ba ku kwantar da hankalinku kawai tsoratarwa ce sannan ma idan yace zai mata Auren itada yanzu ya hanata fita ina ma zata fita bare har wani yace yana sonta " bakiji me yace Ba sadakarta zai bada Mamy ta fad'a tana hawaye "Duka fad'ine yayi Dan mu tsorata Amma bazaiyuba zai sauko nan kusa" Ajiyar zuciya Mamy ta sauke ta ce "kila kuma hakanne Allah dai ya shige mana gaba " Ameen Mama Halima ta fad'a Aira duk tanajinsu sai sannan hankalinta ya Dan fara kwanciya Dagowa tayi cikin kuka ta ce "Mama Dan Allah ki rok'eshi ya bari mu koma Kadunan tare" Chab Inani ina wannan Mamana kina ganin dak'yal ma muka samu ya amshemu idan nace xan koma dake ai rikicewa abun zaiyi ki bari idan aka kwana biyu Zan dawo nayi yanda nayi na shawo kanshi ya bani ke sannan ya huce sannan kuma ki kiyaye ki hakura da Mujahid na wani lokaci "Gyada kai Aira tayi tana Hawaye taje ta Rungume Mama tana kuka Dak'yal Mama ta lallasheta harta samu ta hakura. Wajen la asr tana kwance a d'akin mamy kanta sai ciwo yake mata Amma ta shigo ta ce " Aira kije ya Umar na Kiranki"to ta fad'a tare suka fita a palour ta sameshi shi kadai Alamun Khady ta fita daga ita saishi yace Amma ta wuce ta basu waje kusa dashi taje ta zauna "Cikin nutsuwa ya ce " Hajara Naji Duka abunda kikayi yanzu Halimatu ke bani labari bani da labari sai yanxu na samu labari Dan kyautawa baku kyautaba Amma Duka ya wuce sai a tari gaba ke yanzu fad'amun Gaskiya kina son Mujahid ko a a magana ce tsakani na dake"Dagowa Aira tayi ta kalli ya Umar daman tasan shi baya da matsala Dan halin Mama yayo yana da hakuri ga nutsuwa komai cikin kwanciyar hankali yake binshi k'asa tayi ta kanta batasan lokacin da wasu zafaffan hawaye suka zubo mata ba ta ce "Yaya ina sonshi sosai kuma Shima yana sona banason a rabamu " ta k'arasa fad'a tana hawaye "Girgiza Kai Umar yayi ya ce " Arman bashi da Aibu Aira da zance wai ki rabu dashi amma ina baki shawarar kisan yanda kikayi kika rage sonshi a cikin zuciyarki sannan duk yanda zakiyi ki hakura dashi na y'an wani lokaci ki samu Ki shawo kan Abba ya barki ki jona makaranta kinajina duk abunda Abba yace kiyi kidinga yi ki dinga barin abunda ya hana saboda Kinsan dai Halin Abba mu Kanmu da girman mu da komai kiyaye umarninshi muke bareke Duka yaushe kikazo duniyar"Goge hawayenta tayi ta ce "Insha Allahu Yaya zanyi duk abunda kace nagode " Yawwa ko kefa y'ar wajen Inna sannan bance ki tada hankalinki ba kiyi rayuwarki.kamar yanda kike a baya kidaina sa damuwa a ranki ko so kike y'ar k'aramar kanwarmu ace ta kamu da hawan jini so kike tsufa ya kamaki da wuri"Murmushi Aira tayi ta ce "A a ayaya nadaina daga yau " To shikenan ko kefa yanzu kije kici abinci kinji y'ar kanwata"To yaya ta fad'a tare da tashi sosai taji d'an sanyi a ranta a ranta ta ce "Nidai nayi sa'ar yayyu Duka suna sona Allah na gode Maka da ka bani y'an uwa masu sona Nidai bansan wani Abu wai y'an ubanci ba har mamaki take idan a makaranta ana firar y'an uba ko ana zaginsu itadai Duka d'aya suka d'auketa" da wannan tunanin ta koma dakinsu ta tarar da Hafsa Na salla itama alwallar tayi taje tayi salla suna gamawa Amma ta zubo musu abinci a d'akin sukaci abinci su Ukku plate d'aya suna ci suna Hira Aira ce ta ce "Wai dazu daga ina kike naga kamar tare kuke da Abba " Daga B U K muke Registration mukaje Abba yayimun Bayan tafiyarki Mukayi jarabawar PUMB kuma naci sa a naci harsun bani admissions sosai na damu da bamuyi tare ba Kuma Kinga tare mukayi apply ta Online'"girgiza Kai Aira tayi ta ce "Allah ya taimaka ya baki sa'a nikam yanzu ba karatu ne gaba na ba nama fara hakura dashi " Sosai Amma tayi mamakin jin Abunda Aira ta ce "tana mata wani irin kallo ta ce " kamarya ba karatu ne ke gabanki ba to meye gabanki........✍🏿 *Ni da yaya Arman it's not free na kudi ne it's #200 via katin Mtn to 07026166536 VTU OR PC #300 kada ku fitarmun da littafi kudin karantawa kuka biya ba na mallaka ba* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿🤙🏿 [6/13, 23:20] Hajo hajo: 🅿️........*41&42* Meye gabanki"Kawai haka nan ke Nifa karatun ma.ya fice a raina "Hafsa ce ta ce " Amma baki da hankali Aira to idan ba karatu ba zaman me zakiyi a gidan "Turo baki tayi ta ce " meye abun Rashin hankali ra'ayi ne kowa da nasa"to munji ra'yin ne amma me zakiyi banda karatu"Hmmm nifa wlh da so samu ne Kawai Ayi mana Aure *Nida Yaya Arman* wlh kwata kwata gaba d'aya hankalina baya kan komai yana kanshi kuma koma naje karatun Allah ba abun kirki zanyiba saboda tunaninshi ma bazai barni nayi karatu ba shiyasa ko a kaina da Abba ya ce bazanje karatu ba ni ya ma fa hutashsheni ai indai ba gani na nayi a d'akin yaya Arman ba matsayin matarshi to sannan ne hankali na zai kwanta har na samu damar yin karatu cikin kwanciyar hankali"sakato Amma da Hafsa sukayi suna kallonta Sosai ta basu mamaki Amma ta ce "Chabd'i lallai Aira waike kanki wani irin taurine dashi duk abun nan da akayi sabodake ba Aje ko ina bama Har kina tunanin wai Aure Aurenma da Arman kuma " Tsaki taja ta ce "To ina ruwanki ni bansan wani k'abli da ba Adi abar maganar" Hafsa ce ta ce "Ni banga laifinkiba Yanda Kuke baza wannan love d’in ai kawai gwara a shige daga ciki kowa ma ya huta" Dariya Aira tayi ta ce "Shiyasa nake mugun sonki sis " Dariya Hafsa tayi ta ce”Mudai a taimaka kar a samar mana D’an baba a waje a bari dai sai anshiga daga cikin dan naga dukanku ke da shi kan dancing yake “kulli a baya Aira ta kai mata ta kauce ta ce “ke dama yar iska ce wlh hafsa “Dariya hafsa tayi ta ce “Sorry uwar gida kuma Amarya a gidan Yaya Arman “insha Allah “Aira ta fada da karfi Amma ce ta ce "uhm sarkin tura turarre wannan ai ba a zuga ta" Dariya Aira tayi ta ce "da a zugani da kar a zugani duk abunda naso nake zugar bata hanani kuma bata sanyani indai akan yaya Arman ne " girgiza kai kawai Amma tayi dan kanwar tata ta riga da tayi nisa batajin kira Suna gama cin abincin Aira ta haye Gado ta kwanta Ta ce "Bacci zanyi kaina ke ciwo idan anyi magriba Dan Allah ku tasheni" kinsan dai baccin yamma ba kyau"Amma ta fad'a tana gyara Inda suka bata "ke kika San wannan Aira ta fad'a ta na jan blancket tayi kwanciyarta. Sai Bayan magriba suka tasheta tana tashi taji kanta ya daina ciwo sallah tayi ta fito palour Ta tarar da Inna cikin Sauri Inna ta tashi ta tarbeta ta ce " y'ar lelena Shine kika tafi kika barni duk nayi kewarki gidan bayamun dad'i sai yanzu da nake tambayar Zainab ke ban labarin Abunda ya faru wai ubanki ko gidana ya hanaki shiga rabamu yake so yayi"Inna tafada tana kwakuro hawaye "Dariya Aira tayi ta ce " Haba My Inna aikinsan ni Dake mutu karaba ki bari kawai ya huce nasan zai barni"yawwa y'ar kirki ai daman Nasan ke y'ar arziki ce Bazaki juyamun bayaba "Itadai Aira murmushi tayi tare da tashi tace bari na shiga wajen Mamy tashi Inna tayi ta ce " nima bari na wuce daman ganinki kawai nazo"Hug din inna Aira tayi tare da shigewa d'akin Mamy a Gado ta tarar da Mamy da Mama Halima saishan hira suke daman Chan tunda aka Auro Mamy k'awayene saboda sa'annine "Tsayawa tayi tare da gyaran murya kallonta sukayi Mamy ta ce " lafiya"sosa kai tayi ta ce "Lafiya Mamy sannan ta kalli Mama Halima ta ce " Mama Dan Allah wayarki zaki aramun"Mamy ce tayi karaf ta ce "Uban me zaki mata da waya" Bakomai Mamy "wayar Mama Halima ce tayi ringing duba mai kiran tayi saikuma tayi murmushi ta d'auka Daga d'ayan b'angaren ARMAN ya ce " Haba Mama tun d'azu nake kiranki bata shiga ina my cutie tun d'azu na kasa samun sukuni kwata_kwata banji muryarta ba Yau idan banji muryarta ba ban iya bacci wlh Mama please ki kai mata wayar"Kallon juna Mamy sukayi saboda wayar a hands free take girgiza kai Mamy tayi Mama ta ce "To sarkin y'an Rashin kunya aikama tambaya mun Iso lafiya" Kamar Wanda zaiyi shagwaba ya ce "Nasanma kunje lafiya insha Allahu nidai bani ita please" Aira duk tana tsaye jin muryar sahibin nata sai taji wani farinciki ya mamaye zuciyarta Mama ce ta ce "zo ki amsa Aira hada tuntub'enta taje ta amshi wayar Ta Kara a kunne kamar wadda zatai kuka ta ce " My yaya "Ajiyar zuciya bangaren Arman ya sauke ya ce " My cutie are you okay "gyada mai kai tayi kamar yana gabanta " Alhmdll kunje lafiya ya hanya fatan baki wahala ba ko?gyad'a mishi kai tayi ta ce "Alhamdulilla " kallonsu Mama tayi zata tashi ta tafi "Mamy ta ce " Dawo ba Inda zaki gama wayar a nan "ta fad'a ta na Harararta " Chan gefe Aira taja ta tsugunna ARMAN ne ya ce "Yadai naga kinyi sanyi ko Abba ya dake ki" a a a yaya baimun komai ba su Mamy na wajen shiyasa kaji haka"ta fad'a yanda bazasuji ba "wai kina nufin a gaban Mamy muke waya kenan yanzu itama ta hakura muyi tare" murmushi tayi ta ce "Abunda nake tunani kenan Dan ko fad'a batayimun ba" Alhamdulilla Arman ya fad'a sannan ya ce "Gaskiya nayi farinciki daman ba na fad'a maki ba Ai wannan Abun da mukayi zai iya sawa suyi sanyi" murmushi Aira tayi Arman ya ce "to ban labarin ya kukayi da Abba" Kallon su Mamy tayi taga hirarsu suke ta ce "Yaya zan fad'a maka amma ba yanzu ba sai basa wajen" to yanzu ina wayarki wai Duka biyun fa basa shiga"tana part d'in Inna dukansu Idan na samu ko zuwa gobe zansa a d'auko mun sainayi chajinsu nasan mutuwa sukayi ba chaji"okay ke bazakije ki daukoba yanzu kinsan bana jure Rashin jin muryarki "Zanfada maka duka yaya sai anjima" okay bye dia take care of yourself"murmushi tayi ta ce "Don't mention my yaya" I love you my cutie ya fad'a cikin kasalalliyar murya k'asa k'asa ta ce"I love you too "tukwana sukayi bankwana Mama ta mik'awa wayar ta ce " gashi Mama "Kallonta Mama tayi ta ce " ba kince zaki ara wayarba tafi da ita"Sosa kai tayi tana murmushi ta ce "Shikenan Mama" Daman shine zaki kira kuma ya kira ko?Mamy tafada tana Harararta b'ata rai Aira tayi tayi ta ce "Ai nidai bance ba sannan ta d'auko Ameer dake k'asa yana rarrafe ya Mike zai Fard'o kayan kwalliyar dake mirror ta ce " wannan D'an naki mab'annaci ne Wlh""Ai bai kai k'afar b'arnar da kikayi ba "inji Mamy " kai Mamy nidin kuma ta fad'a tare da barin d'akin tare da Amer suna fita Mama Halima ta kalli Mamy ta ce "Kidinga janta a jiki Dan Allah inba wajenki ba ba ina zataje taji sanyi " Girgiza kai kawai Mamy tayi ta ce "Ina bakin kokarina Halima wlh ni abunda yasa ma tun farko na nuna banason tarenta dashi karya lalatamun y'a shiyasa nidai tawa addu'a ce kawai Dan wlh yarinyar nan tayi nisa yanda baki tunani" ba abunda zai faru sai alkhairi insha Allahu addua zamuyi tayi Ai nice shaida wlh yaran nan ba k'aramun so sukeyiwa junansuba ranar sunjima suna tattaunawa akan Lamarin su Aira.washegari mama Halima suka shirya zasu tafi harsun fito da kayansu Aira sai magiya take abar Hafsat itama Hafsat din tana so a barta Mama ta ce "a a a ita takemun aiki wlh itace k'arfin aikin gida kunsanni ba maid house nake daukaba " Mamy ta ce "kedai kin k'iwace wlh Halima ki barta ta d'an huta ko sati biyu ne" Dariya Mama tayi ta ce "bazakiganeba wlh Ban iya aikin gidan nan ni kadai anma zatazo kwanannan"Yaya Umar ne sukayi sallama shida matarshi Kallon Mama yayi ya ce "Mama badai tafiya ba" wlhko babana wucewa zamuyi wai"Kallon Hafsat yayi ya ce "Amma ba da ita ba zaki tafi ko" Dariya tayi ta ce "Tare " haba Mama Ki barta mana ta kwana biyu wai meyasa bakyason barinta tana zumunci"Mamy ce ta ce "kaima dai ka fad'a " Hafsat ce ta ce "Dan Allah Mama ki barni ko 1week ne nayi" Mamy ce ta amshi Jakarta ta kaya ta ce "mun rinjayeki ba Inda zata " Dariya Mama tayi ta ce "Ai dole ma na barmuku ita Anyimun chaaa Hafsat sai murna take Ita da Aira Airace ta rad’a mata ta ce " wai Sis bakiga yanda yaya Umar ke kallonki matarshi sai Aiko miki harara take"Dariya Hafsa tayi ta ce "Kai Aira sharri Juyawa sukayi suka koma ciki Mama Halima ta tafi. Washegari Wajen la'asar kasancewar girkin Mama ne gashi Y'ar aikinsu batajin dad'in bata zoba Mama ta shiga kitchen tana girki Khady tana ganin yanda take aiki da zirga zirga ko Sannu batacewa Mama ba bare har ta tayata " Itako Mama bata damuba Dan ta saba Aira ce ta Hafsa suka fito palour suka zauna Sukace "Sannunku da hutawa Yaya" Yawwa Y'ar Inna Sosai Umar ya dinga Jan Hafsa da Hira Khady ta cika tayi Fam Airako Kad'an Ya hana tayi dariya hakan yasa take tsunkunin Hafsa akan ta k'ara chusa mata Haushi itama Hafsat da Jan magana tashi tayi taje kujerar kusa dashi ta ce "Yaya please ka kaini naga gari Dan na shaida nazo Hutu nima" Cike da farinciki Umar ya ce "Aiko yanzu zaki shiga gari kanwata jeki shirya" Khady ce ta mik'e cike da b'acin rai Ta ce "wannan wani irin iskanci ne to ba Inda zaka kaita wlh ta tari napep mana ta hau inbanda tsabar iskanci ka tashi mu tafi ni gida nake so muje mu huta da bakazoba da wa zai kaita " Bata fuska Umar yayi ya ce "Meye haka Khady banson iskanci gaban yara idan gidan zaki ga hanya nan ki tafi ko dole saidani" Aira me zatayi inba Dariya ba hada durk'ushewa Amma kasa kasa take yanda bamaiji Hafsat ko itama ji take kamar ta fashe da dariyar Aira Dan ta k'ara chusa mata Haushi ta ce "Haba Aunty ki bari mana ya kaita bakuwace kafin su dawo ma Kinga kin kara hutawa naga kamar gajiye kike" harara Khady ta gallawa Aira tare da Jan tsaki Hafsa ce ta tashi ta ce "Daman da wasa nake wlh " Tashi sukayi ita da Aira suka koma bedroom d'insu suna kwasar Dariya. Da dare Aira ta lallaba Amma ta ce "Dan Allah sis kaya na zaki daukomun a bangaren Inna wayoyina na cikin d'akin Dan Allah daukomun " Dak'yal ta samu Amma taje ta d'auko mata Allah yasa lokacin da wuta Aiko tasa wayoyinta Duka chaji k'aramar Kara d'aya tayi ta maza ta bud'e tana kiran shi saida ya katse ya kira Ajiyar zuciya ta sauke Suka shiga gaisawa cikin so da k'auna kwancewa gado Aira tayi rufda ciki tana jin farinciki ya mamaye zuciyarta Sunjima suna waya tukwana ARMAN ya tambayeta Ya sukayi da Abba Duka ta fad'amai amma bata fad'amai maganar karshe ba na Aure zaiyi mata Dan bata d'auki abun serious ba "Ajiyar zuciya Arman ya sauke ya ce " Ai wannan ni Abba ya taimaka bai sani ba ya hanaki fita bare wani ya ganemunke har yace yana so,makaranta ma hakan yayimun dad'i Daman ina kishin shigarki makaranta kowa ya dinga kallemunke a bilis"na Ukku kuma abunda bazai tab'a yiwa bane har abada Watau rabuwarmu Kinga ko ai Hukuncin mai sauki ne "Dariya Aira tayi ta ce " kai yaya kuma fa hakane sai kuma ta bata fuska ta ce "To idan munason mu hadu yazamuyi Bayan ya hanani fita" murmushi yayi ya ce "banida damuwa da wannan saboda duk sanda naso ganinki dole saina ganki ko ana ruwa ko ana iska Allah yana tare damu Insha Allahu" wani sanyi Aira taji a ranta kwata-kwata ma Arman ya kwantar mata hankali Sai takega Duka hukuncin ma da Abba ya yanke mai sauki ne sunjima suna shan hirarsu gwanin sha'awa cikin so da kaunar juna. Hafsa satinta guda Driver yazo daukarta a lokacin Su Yaya Umar sunzo sosai yayi mata tsaraba su Mamy ma sunyi mata tsaraba sosai Airako hada kuka duk saitakejin ba dadi itama Hafsa din Har zasu tafi Aira da Jan magana ta ce "Yaya ka amshi numberta kuwa" mik'a mata Wayarshi yayi ya ce "Amshi ki sanyamun ki sanya mata tawa mundinga gaisawa a waya tunda bata da zumunci " murmushi Hafsa tayi ta ce "Yaya aikai dinne ganinka ke wuyar gani" cike da gayya Aira ta sanya musu numbobin juna Khady ji take kamar ta shak'e Aira sai aika mata da harara take da abun ya isheta tsaki taja tare da ficewa tabar gidan Gaba d'aya "girgiza kai ya Umar yayi sannan ya kalli Aira ya ce " so kuke ku haukatamun mata ko"Dariya Aira da Hafsa sukayi suka tafa Hafsa ta ce "To me aka mata kawai kishidai yayiwa Matar ka yawa " Dariya Aira tayi hada rik'e ciki Mamy dake kallonsu girgiza kai tayi ta ce "Allah shiryeku" Mama ko Addua tayi ta ce "Allahsa Umar son Hafsa yake wannan Matar zamanta ita kadai gidan dana matsala ce " Hafsa Na tafiya Aira ta koma ciki duk batajin dad'i. Haka rayuwa taci gaba Aira bata zuwa ko ina Abba ya fad'awa me gadi kar asake a barta fita Amma tuni harta fara zuwa makaranta hakan ko Kad'an bai damu Aira ba Saboda tana shan wayarta da Arman kullum Daki take rufewa susha wayarsu da video call da dare ko raba dare suke suna shan love Harsai Amma tayi fafatu akan sun hanata bacci Daman Haidar ya koma bangaren Inna yake tayata kwana. A haka har akayi wata guda ranar wata juma'a Arman ya kirata ya ce ya shigo kano kuma yanason su hadu tasan yanda zatayi ta fito su hadu Sosai hankalin Aira ya tashi ta kasa zaune ta kasa tsaye Mamy taje ta samu tana hawaye ta ce "Mamy Dan Allah gidan Aunty Aisha nake so naje ki taimakamun naje kafin Abba ya dawo Allah na dawo" Wlh Aira ba ruwana Tunda Abbanki ya hanaki fita kawai ki hakura yanzu Abun na barki ki fita ne ni kaina matsala zaki jamun ba ruwana karkije ko ina idanma Aishar kikeso Kuyi magana amshi wayata ki kirata"Goge hawayenta Aira tayi ta ce "Shikenan Mamy ba sai na kira ta ba " ta fad'a tana barin d'akin saida Mamy ta tausaya mata Aira na komawa gado ta fad'a tare da kiran Arman yana kira ta fashe da kuka ta ce " Yaya mamynma ta hana "kuka kawai take Lallashinta yayi ya ce " jeki ki samu mai gadi ki lallabashi kiga zai bari ki fito "to Aira ta ce sannan ta fita tana zuwa ta samu Baba mai gadi najin radio har k'asa ta durkusa ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska Zaunawa tayi gefenshi ta ce " Baba Dan Allah fita nakeson nayi "Dayake baba suke cemai tsohone sun jima dashi " kallonta yayi ya ce "Kiyi hakuri Hajiya Alhaji yayimun kashedin na sake na barki kika fita a bakin aikina ni kuma aikin nan dashi nake sha nake ci shine rufin asiri na bazanso rasa shi ba Dan haka kiyi hakuri bazan bud'e miki k'ofa ba" Cikin tashin hankali Aira ta fara kuka ta ce "kayiwa Allah da girman manzon Allah S a w Baba ka bari in fita wlh ba zanja maka matsala ba yanzu zan dawo........✍🏿 *Ni da yaya arman Littafin kud'i ne ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali da nutsuwa #200 Katin MTN to 07026166536* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/14, 18:32] Hajo hajo: 🅿️........*43&44* Gaskiya kiyi hakuri Amma bazan bud'e maki ba idan har ba mai gidan bane da kansa ya ce na bud'e maki ba "jin abunda Baba mai gadi yace ya sanyata tashi ta Ruga ciki da gudu tana kuka tana zuwa ta fad'a kan Gado tare da fashewa da kuka saida tayi kukanta mai isarta Arman ne ya kira d'auka tayi cikin kuka ta ce " Yaya Baba mai gadi ya hanani fita wlh ba irin magiyar da ban mashi ba "daga dayan bangaren Arman sosai baiji dadi ba cewa yayi " ki kwantar da hankalinki kinsan bansan kukanki kuma ke baki tashi yi sai gabana"share hawayenta tayi tare da turo baki kamar yana gabanta ta ce "To ba dole nayi kuka ba kana gari amma anhanamu ganin juna" To sai kiyi shiru mu nemi mafita ko kukan shi zai zame mana mafita"a a yaya "Numfasawa yayi ya ce " matsala ta dake baki iya dabara ba ke a y'an farin ma shugabar faranta ce Wlh ko k'aramun yaro ya fiki wayau "ya fad'a da sigar zolaya " Kamar zatayi kuka ta ce "Ni wlh ba y'ar fari bace Kaine ma za a ce d'an fari kuma auta tunda baka da yaya baka da k'ani Niko ina da yayyu ina da k'anne" ta fad'a tana turo baki "Dariya Arman yayi ya ce " yau naja gori ko to ai ni bana abubuwan y'an fari keko ko maganarki ta y'an fari ce "Allah yaya ka bari zanyi kuka" ta fad'a cikin shagwaba "Dariya yayi ya ce " sorry my cutie kar ayi kuka ayi hakuri"turo baki tayi ta ce "Kai naga bama ka damu ba da Rashin haduwarmu ko" hmmm bazaki gane bane cutie wlh nafiki damuwa kawai taurin haline kinsan maza da dauriya"Uhm tace"kinsan me za ayi"a a saika fad'a "Yanzu bari zakiyi jibi saboda gobe idan Kikayi ganewa za ai kije ki kaiwa mai gadi kudi kice Mamy ta ce ya sayo mata wani abun kinsan dai abunda zakice ke kuma yana fita ki maza ki fito " tsalle Aira ta buga akan Gado ta ce "yesssssss wlh yaya wannan dabarar tayi kwata_kwata ni banma kawo hakan a kaina ba" Dariya yayi ya ce "to kindai yarda kece y'ar farin" Turo baki tayi ta ce "Uhm ban yarda ba Kaine dai Dan fari'" sun tab'a Hira cikin nishad'i tukwana suka kashe suna gama waya Hafsa ta kira tana d'auka ta zolayeta da "Matar yayaana" Dariya Hafsa tayi ta ce "Mrs Arman ake gaya muku" murmushi Aira tare da dafe saitin zuciyarta ta ce "wayyyyo har kinsa Naji wani sanyi a cikin zuciya kai Gaskiya kinci katin 1k " Dariya Hafsa tayi ta ce "Allah shiryeki" Ameeen indai akan Yaya Arman ne Kuyi tayimun Addu'ar ya ake ciki ne wai har yanzu yaya Umar na Kiranki"ke inaso na baki labari kullum fa sai yaya Umar ya kirani musha hira kawai jiya ingaya maki Matarshi ta kirani ta dinga surfamun zagi ta uwa ta uba hada cewa wai "na k'ara kira mata miji saita sa an sauyamun kamanni" Hafsa ta k'arasa fad'a tana fashewa da Dariya "Dariya Aira ta fashe da ita ta ce " wayyo Allah cikina amma Gaskiya abun nan ya bani nishad'i Ai daman Nasan Bazata barkiba shegiya y'ar wahala"Dariya tayi ta ce "Ai na dinga chusa mata Haushi kenan tunda mahaukaciya ce" cikin dariya Aira ta ce hhhh kici gaba da gasa mahaukaciya Wai yace yana sonki kuwa"Uhm ke wlh baice yana sona ba shifa kawai a zumunci yake kirana ita kuma ta d'auka sona yake"haba Hafsa Ai yaya Umar sonki yake kawai wlh kawai fad'a maki ne baiba"Uhm kawai Hafsa tace tukwana suka saki hirar suka koma wata sunjima suna waya tukwana sukayi bankwana.kamar yanda Arman ya fad'a ranar Da wajejen Ukku Aira ta shirya cikin doguwar Hijab d'inta purple me hannu sosai tayi mata kyau a palour ta tarar da Mamy tana kallo "Sannu da hutawa Mamy" ta fad'a tana zama kusa da ita"kallonta Mamy tayi ta ce "Yawwa " Mamy Dan Allah 1k zaki bani"me zakiyi da 1k"Sosa kai tayi tama rasa k'aryar da zatayi sai chan ta ce "Uhm Mamy awara zan bada a sayoman "hmm jeki jikin drawer kayan Amer akwai jakata ciki ki d'auka saiki maidoman chanjin" Cikin murna ta tashi ta ce "Thnks you my dear mom ta fad'a tare da shiga taje ta d'auko zata fita Mamy ta ce Ina kuma zaki keda Abbanki ya hanaki fita" kamar zatai kuka ta ce "Mamy Bafa wani waje ba zani Ba Bala mai bawa flower ruwa ne zanba ya sayoman"to dan Allah karkije ko ina" To Mamy ta fad'a tare da fita tana zuwa ta tarar da Baba me gadi zaune cewa tayi "ina yini Baba Sannu da hutawa " yawwa y'ar kirki "Baba gashi inji Mamy ta ce Ka amso mata kati Dan Allah " Amsa yayi yace "to bari a amso na nawa" na d'ari biyar "yana fita Aira tayi Sauri ta lek'a taga ya danyi nisa a guje ta fice tayi d'ayar center saida ta daina Hango gidansu tukwana ta tsaya tana hak'i kiran Arman tayi ta ce " yi Sauri yaya kazo ina daidai karshen layin gidanmu kwanar wannan ta biyu zaka ganni"To cutie ganinan "Huci kawai Aira take Dan tayi gudu ba ayi minti goma ba saiga Arman saboda gudu ya sharara tana ganin motarshi cikin Sauri tana waige ta shige gidan Gaba sai hak'i take" Ajiyar zuciya dukansu suka sauke a tare kallonta Arman yayi ya ce "Badai gudu kikai ba" haba yaya meye ma banba muje dai kar wani ya ganmu ta fad'a tana rufo kofa "Jan motar Arman yayi suka bar unguwar sai kallonta yake itama tana Kallonshi a hankali ya ce " kinyi missing Dina kuwa cutie"cikin shagwababbiyar murya ta ce "my yaya ai ko ban fad'a ba fuskata kanta ta isa ta shaida maka kalar missing dinka da nayi" murmushi yayi ya ce "kuma zuciyoyinmuma sun isa su shaidawa junansu kalar kewar juna da sukayi ko" Eh mana my yaya ai yau jina nake kamar salla fa"Dariya yayi ya ce "Nikuma ji nake kamar Anyimun Albishir an yafe mani Duka laifuka na" Dariya tayi ta ce "Yaya kenan "Shima cikin murmushi ya ce " cutie kenan ina sonki fa sosai"murmushi tayi ta ce "Nima ina sonka sosai yayana sonda bana kwatantashi da komai" d'ayan hannunshi ya mik'o ya kama lausassan hannunta kamar auduga murza hannun ta yake cikin wani irin salo ita kanta Aira jin sak'on nashi take Sunkai tsayin minti kusan Ukku ba Wanda yayi magana ji tayi Arman yayi parking tare da kallonta cikin Wace irin murya mai cike da kasala ya ce "Mu yiwa juna Alk'awarin bazamu rabu da juna ba duk rintsi duk wahala please cutie" Aira batasan lokacin da wasu ziraren hawaye suka fara zarya daga idanunta ba Cikin muryar dake shirin fashewa da kuka ta kalleshi ta ce "my yaya" juyowa yayi ya Kalleta idanunsu suka sartse Cikin na juna kafe juna sukayi da idanu bako k'iftawa kama d'ayan hannunshi tayi hawayen dake idanunta suka zubo a hannuwansu ta ce "Alk'awarin mu ya na nan yaya karkatab'a kawowa a ranka cewar zan manta dakai bazan tab'a iya rayuwa babu kai a tare dani ba kaid'in ka zamemun wani bangare na jikina kamar yanda mutum baya rayuwa ba tare da zuciya ba to kamar haka rayuwata take muddin idan babu kai a cikinta bata da amfani" ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka tare da Rungumeshi "daddab'a bayanta Arman ya fara tuni zuciyarshi ta karaya da jin kalamanta Shima jin yake da zai samu damar da yayi kuka cikin sigar lallashi ya ce " nima ta bangare na hakan take Aira kullum fad'a nake ina Kara fad'a. Sonki daga Allah ne na kasa iya misalta kalar son da nake maki a cikin raina Inajin a jikina duk ranar da su Abba sukayi sanadiyar rabamu to ranar ce ranar ajali na.."rufe mai baki Aira tayi cikin kuka ta ce "Ka daina fad'ar haka yaya bazasu iya rabamu ba banason kana maganar rabuwar nan tana tayarmun da hankali"daddab'a bayanta ya fara Dan son kwantar mata da hankali ya ce " Ai daman Nasan abunda bazai tab'a yiwa bane tashi ki yi shiru ki kalleni"kamar yanda ya fad'a tashi tayi daga kanshi tare da Kallonshi murmushinshi mai tsada ya sakar mata batasan lokacin da ta mayar mashi da kayataccen murmushin ta yake Kara mata kyau "mu yiwa juna alkawari" ya fad'a ya d'ora Hannunshi ya Aje itama ta d'ora nata a kan nashi tare suka ce " Alk'awarin mu na nan har abada"Goge hawayenta Aira tayi Ta ce "Yaya ina zamu" Gida kinsan Mummy ta dameni akan tana son ganinki"y'a fad'a yana tada mota"murmushi tayi ta ce "Allah sarki Mummy nah nima inason ganinta nayi kewarta" . b'angaren gidan su Aira Baba mai gadi yana dawowa yaga wayam ba Aira sallama yayi cikin gidan Dan a tunaninshi ciki ta koma Mamy ce ta lek'o ta ce "Lafiya Baba" kati ya mik'a mata tare da chanji ya ce "gashi sak'on da kika Aiko maman Alhaji da yake haka cewa Aira na sayo" Cike da mamaki Mamy ta amshi katin ta ce "Ita Airar ta ce Na aikota ina take ita d'in" sosai mamaki ya kama Baba mai gadi ya ce "Hajiya yanzu fa ba jimawa ta zo ta ce kince na amso maki kati nikuma na tafi na barta a nan" tab'a hannu Mamy tayi tare da salati ta ce "Aiko wlh Baba wayau kawai tayi maka ta fita ba wani Aikenta da nayi sannan ta jinjina kai ta ce " Allah ya shiryeki Aira har kin iya dabarar fita "Sosai Baba mai gadi yayi mamaki ya ce " lallai yaran zamanin nan a gansu a kyale karamar yarinya tayimun wayau "Dariya mamy tayi ta ce " Allah dai ya shirya mana zuri'a kawai za ace ka koma kan aikinka kawai Baba "itama ciki ta koma tana mamakin Fitsarewa irin ta Aira ashe kudin da ta amsa duk shirine girgiza kai kawai tayi taci gaba da Al'amuranta. suna isa Government house a tare suka fito security na Sara musu har suka isa Babban Palourn gidan Mummy ta taho da fara'arta ta ce "oyoyoyo ga y'ata ta fad'a tana Rungume Aira cike da farinciki ta kama hannunta ta ce " Sannu da zuwa tunda kika tafi kika barni da kewa"murmushi Aira tayi ta ce "Nima nayi kewarki sosai Mummy nah " Sosai Mummy ta dinga nan nan da Aira kamar zata maidata ciki sosai hakan yake yiwa Arman dadi yanda Mummy ke son Airanshi sai wajen magriba Aira ta fara tunanin Gida sai sannan ma ta tuna a yanda ta fito kallon Arman tayi ta ce "Yaya Mamy tace kar muyi magriba " ta fad'i hakane Dan Mummy tayi zaton da sanin Mamy ta fito "Mummy ce ta ce " Au har ina tunanin kwana zakimun "Murmushi Aira tayi ya ce " Mummy ai zandawo nayi maki kwana biyu"To shikenan Aiko da Naji dadi sannan ta tashi ta ce "jira ni ina fitowa Mummy na shiga Arman ya dawo kusa da ita ya ce " Yanzu sai yaushe zamu k'ara had'uwa"Turo baki tayi ta ce "Saina duba" Dariya yayi ya ce "irin wannan wulakancin na y'an mata ko" Dariya tayi ta ce "To me yafi son raina badai kace kana soba ai gwalaka ma fa zan fara"Dariya Arman yayi ya ce " Haba yarinya munga Wanda zai gwala wani cikinmu"ganin fitowar Mummy ya sanya Aira harararshi ta ce "To ka tashi sai Mummy ta ganmu" Meye Dan ta ganmu kefa har yanzu kink’ii ki waye saina wayar dake"harara Aira ta galla mai ta ce "Ai nice ma na wayar dakai ta fad'a tare da tsinkuninshi d'an Kara yayi tare da tashi yana Dariya " Mummy na isowa ta mik'awa Aira k'atuwar kwali bag mai d'auke da hoton Mummy da na Daddy ga alamu dai na siyasa ne ta ce "Amshi ki kaiwa maman naki kice ina gaishe ta sosai Dan Allah" Amsa Aira tayi ta ce "To Mummy zan fad'a mata nagode sosai " Tukwana sukayi bankwana lokacin da Suka isa unguwarsu Ana kiraye kirayen magriba a Inda ya d'auketa ya sauketa har ya wuce ta na Mashi bye bye saida taga wucewar motarshi tukwana ta nufi layinsu Tsit ba kowa unguwar Cikin Sauri take tafiya Harta isa gabanta na fad'uwa ta na zuwa Knoking tayi mai gadi ya fito ya na K'are mata kallo Aira bata Ko Kalleshi ba ta yi Sauri ta shige cikin Sauri har tuntube take ta nufi hanyar Part d'insu Daga bayanta taji muryar Abba na cewa "daga gidan uban wa kike"Shock Aira tayi a wajen ta kasa koda motsi gwalo idanu tayi ta ce " na shiga ukku "Abba ko tsawa ya k'ara daka mata daga Inda yake kan farar kujerar roba ya ce " ba dake nake ba".......✍🏿 *Ni da yaya Arman Littafin kud'ine akan Naira #200 kachal katin Mtn ta wannan number 07026166536* *Takun ce dai mai k'aunar farincikinku* _*Miss Hajo_*🤙🏿 [6/14, 20:47] Hajo hajo: 🅿️.......*45&46* Cike da firgici Aira ta juya ta saki jakar hannunta bin jakar Abba yayi da kallo Mamy ce daga palour tajiyosu cikin Sauri ta fito ta na fitowa kallon Aira tayi cikin basarwa ta ce "Harkin dawo kenan Kinko kyauta baki wuce magribar ba bani sak'on ta fad'a ta na amsa jakar hannunta kallon Abba tayi ta ce " Ni na aike ta" Ajiyar zuciya Aira ta sauke a zuciyarta ta ce "Amma Mamy ba k'aramun ceto na ba kikayi tayi saurin daidaita nutsuwarta ta ce "Eh Mamy na dawo" Abba ne ya kalli Mamy ya ce "Da izininwa kika aiketa ba gabanki na yanke hukuncin hana ta fita ba shine zaki aiketa Raini ne ko me" Danne zuciyarta Mamy tayi cikin ladabi ta ce "Kayi hakuri D'an aike na rasa ita kad'aice gidan shiyasa banjima da aikenta ba " Shiru Abba yayi saikuma ya ce "Daga wannan ya zama first and last ko kin rasa d'an aike duk Mahimmancin abun ki jira wani yazo ko ki kira driver kika sake Aikenta ranki zai b'aci" Ikon Allah Mamy ta fad'a a cikin zuciyarta a fili kuma cewa ta yi "To Allah huci zuciyarka" tana gama fad'a ta kama hannun Aira ta jata sukayi ciki suna Zuwa bedroom d'in Mamy ta saki hannunta Tare da d'aure fuska ta ce "Daga ina kike?" Gidan....saikuma tayi shiru"Bansan k'arya kinsan kikamun ganeki nake ki fad'amun Gaskiya kai tsaye Daga ina kike"Aira ba yanda ta iya tasan dole ta fad'awa Mamy tunda ma harta taimaketa a wajen Abba k'asa tayi da kanta ta ce "Mamy yaya Arman ne yazo shine.." shine me"Mamy ta fad'a a tsawace"Shine naje muka gaisa kuma wlh ba Inda mukaje gidansu kawai mukaje Kuma daga Chan ya maidoni wlh kingama abunda Mamanshi ta bada na kawo maki "ta fad'a tana nunawa Mamy jakar" shine ke har kin iya dabarar fita kiyi mana wayau ki fita kodan kinga na daina matsa maki shine kike nema ki rainani To yanzu da babanki ya kamaki kice Ubanme inbanda na taimakeki ke kinfison kullum ke kad'ai akejin kanki Da mahaifinki Aira"Cikin hawaye Aira ta ce "Bazan sake ba Allah Daga yau kiyi hakuri mamy Allah ban rainakiba " Hmmm ai hakurinki da bazan sake d'inki ba Inda sabo mun saba Allah ya shiryeki "Sannan ta d'aga jakar ta fiddo kayan ciki Turamen atamfofi ne Ukku sai Turare da sabululluka masu kyau " kallonta tayi ta ce "Ai da ina da number ta da nayi mata Godiya Angode" Murmushi Aira tayi ta ce "Wlhko mamy Ai tana da kirki sosai Mummy ba ruwanta kuma karkiga yanda take sona har cewa tayi na koma nayi mata kwana" hmmmm naga alamu ni da zan samu numberta ma akwai maganar da mukeso muyi"Cikin Sauri Aira ta ce "Ko nace yaya Ya turo maki" Ta ina zakice ya turo Makin keda ba waya kukeba sannan Mamy ta kama hab'a ta ce "Ke wai ko har yanzu wayar nan na cikin gidan nan taya ma akayi kikasan yazo har kika fita inba kuna communication ba " cikin tsurewa Aira ta ce "Na janyowa kaina garin ilata Cikin Sauri ta ce " a a wlh Mamy na mayar mashi da Wayarshi a wayar Inna yakirani shine fa dazu da tazo take fad'amun"kindai tabbata kin maidamai wayar"cikin basarwa tace "Haba Mamy tun yaushe idan baki yarda ba Kuma ki tambayi innar" a a ni ba saina tambayeta ba jeki"Ajiyar zuciya Aira ta sauke ta ce "Na sila" cikin Sauri ta bar d'akin a palour ta tarar da Amma na salla zama tayi Dan fashin Sallah take saida Amma ta gama ta tambayeta ta ce "Y'an makaranta kenan sai yanzu" Wlhko ai yau munsha wahala Kinsan sai six muke fitowa daga lecture to yau driver baizo da wuri ba shiyasa nakai magriba"Amma ta fad'a tana cire hijab tab'e baki Aira tayi ta ce "Tofa Allah takaita wahala" Kamarya Allah takaita wahala Amma ta fad'a tana Harararta "Dariya Aira tayi ta ce " To me zance inba Allah takaita wahala ba to Allah k'aro wahala shikenan"girgiza kai Amma tayi ta ce "Kede kika sani Ai zaki shiga University d'in zakiji yanda mukeji kema" Tab'e baki Aira tayi ta ce "Uhm Aiko kina ruwa inkinganni lahira kaini a kayi karatu ba shine gaba na ba" Mama ce da ta fito tayi charaf ta ce "To meye gaban naki" Rufe baki Aira tayi tare da zare idanu ta ce "Kai Mama waida kinajina Sannan ta tashi tayi dariya ta ce " Ina nufin ba yanzu ba sai Abba ya huce tukwana"girgiza kai Mama tayi ta ce "Ai nazata ko Aure kike nufi keda sahibin naki" Rufe fuska Aira tayi tare da rugawa bedroom d'insu tana Dariya Itama Mama Dariya tayi ta girgiza kai. Tana shiga Aira wanka tayi ta sauya kaya ta haye Gado Arman ne ya kirata tana d'auka ta fad'a mashi cewa "Mamy ta ce yayiwa Mummy Godiya sannan ta bashi labarin taimakonta da Mamy tayi a wurin Abba" cikin jin dad'i ya ce Allah sarki Mamynmu Allah mata albarka Gaskiya ta taimakemu yanzu dai Matsalarmu tayi sauki tunda Mamy ,Mummy, Mama Halima, Inna duk sun goya mana baya Saura Abba da Daddy kawai suma kuma muyi ta addu'a Insha Allahu Zasu amince kinsan ni fa harna k'agara Dan wlh bansan Aurenmu ya wuce nan da 3Months a k'agare nake "wara idanu Aira tayi kamar yana gabanta ta ce " 3months kuma yaya"Eh mana ai yamayi kusa ai kwanciyar hankali ace ranar da aka daura aranmu gani Gak.....cikin Sauri Aira ta katse wayar tana Dariya ta ce "Kai yaya wlh yanzu baida kunya yanzu da magana tayi nisa sai ya saki layi ta fad'a tare da yimai text da cewa " Good Night ka kwanta kayi bacci saida safe"tana turamai tayi saurin kashe wayar Dan karyayi ma ta kira Kwanciya tayi Bayan tayi Addua Dan bacci take ji Ba b'ata lokaci bacci mai dad'i yayi awon gaba da ita cike da mafarkin sahibin ta.washegari Bayan tayi Sallar asuba komawa bacci tayi Dan bai isheta ba ita ce bata tashi ba sai 10 da wata muguwar yunwa ta tashi da ita brush kawai tayi cikin Sauri ko wanka bata tarka ba ta fito palour bata tarar da kowa ba Alamun amma da Haidar suna School Dining ta nufa ta bud'e cooler soyayyar Doya da kwai ta gani a plate ta zuba da yaji ta fara ci dukda ta fara sanyi tadanji dad'in ta tana cikin ci taga fitowar Mamy da hijab Tare da Amer a hannunta "ina kwana Mamy ina zaki naga kinfito kamar kina shirin fita" Aira ta fad'a tana cin doyarta "Wlh ko wai Aysha ce suke Asibiti tun jiya da dare bamu saniba sai dazu mijin ya kira tayi miscarriage ne Wai harma anyi mata wankin ciki Su Mama sunyi gaba shine zan bisu " Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Aira ta fad'a tana hawaye sannan ta ce "Kaico Aunty Aysha Allah bata lafiya Mamy Dan Allah inzo mu tafi" Ta fad'a tana hawaye ganin yanda ta damu ya sanya Mamy cewa sanya hijab d'inki tare da Abbanku ai zamu idan ya yarda saimuje "cikin Sauri Aira taje ta sanyo hijab da takalmi suna fitowa farfajiyar gidan Abba na mota harsun fiddo mota Zagayawa Ta glass Mamy tayi ta ce " Abbansu wai Aira tace itama zataje ta dubata da naga a mota ne kuma tare zamu ta bimu ko ?Ba Inda zata ta koma tayi mata addu'a a gida ke kuma kiyi Sauri ki shigo mu tafi Sauri nake"Kallon ta Mamy tayi ta ce "Kinji abunda ya ce " ki koma"Goge hawayenta Aira tayi ta ce "To Mamy Allah bata lafiya barmun Amer Dan Allah ya tayani zama tunda ni kad'aice"Mik'a mata shi Mamy tayi ta ce " idan yaji yunwa ki had'a mashi abincinshi ki bashi saboda zamu jima"Amsarshi tayi daga hannun Mamy ta ce "To Allah kiyaye kice ina duba ta Dan Allah Mamy" Su Mamy na tafiya Aira ta koma ciki tare da Amer dake mata gwalamgwamtu sosai ta damu da Rashin lafiyar Aunty Aisha taso taje ta ganta Amma ba dama a gida tayi mata addu'a ta ce "Allah baki lafiya Aunty" tana komawa Aje Amer tayi da niyyar taje tayi wanka Amma fir ya k'iya ya fara kuka ba yanda ta iya sai daukarshi tayi ta fara jijjigashi Dabara tayi ta goyashi ba b'ata lokaci ko bacci ya daukeshi saukeshi tayi a hankali ta shinfid'ar dashi gadonta taje tayi wanka tana fitowa ta shirya cikin Doguwar Riga Atamfa ta d'aura kallabin atamfar Wayartace tayi ringing d'auka tayi Daga bangarenshi Arman ya ce "Shine jiya kika gudu kika barni ko" Dariya tayi ta ce "Ai kai dinne yaya Naji kana neman sako wata maganar yanxu dai ya kake ka tashi lafiya" Alhmdllh sai kewarki kawai"Zaro idanu tayi ta ce "Jiya fa muka rabu" Eh mana ai nafison koda yaushe muna tare da juna"Murmushi tayi ta ce "Nima da so samune hakan amma ya zamuyi" me kike Arman ya fad'a "Bakomai ni kad'aice ma a gidan sai Amer Duka sun tafi duba Aunty Aysha " Subhanalla Me ya sameta"miscarriage tayi"wayyo Allah ya bata lafiya ya musanya musu da mai amfani "Ameen yaya" kince ke kad'aice ko"Eh yaya"To ganinan zanzo mu gaisa "gabantane ya fad'i ta ce Yaya ai mai gadi bazai bari na fita ba" eh na sani lek'owa zanyi daga bakin gate ganinki kawai zanyi na koma"murmushi Aira tayi gabanta na fad'uwa ta ce To yaya saika zo"ganin ana kiran Sallar Azahar ya sanyata tashi taje kitchen ta dafa indomie Da egg cikin 30 minutes ta gama komi ta fito a palour ta Aje jiyo kukan Amer ya sanyata tashi tana zuwa Taga ya tashi yana shirin fadowa kasa ta tareshi tare da daddaukarshi ta jijjigashi ta ce "To yi shiru" Kuka ya cigaba dayi dafe kai tayi ta ce "Nima naga ta kaina fitowa tayi dashi palour dakin Mamy taje ta had'o mashi custard da madara cikin Sauri ta dawo palour Tana fara bashi yayi shiru Ajiyar zuciya ta sauke taci gaba da bashi saida ya koshi har yana kauda kai tukwana ta rabu dashi abun wasa ta Aje mishi nan yahau wasanshi yana dariya"(Nikam nace Aira ashe an iya raino😂) sai sannan ta samu damar cin nata abincin tana gamaci ta gyara wajen Wayarta ta d'auko ta hau what's app Ta fara chatting wajen la'asr Arman ya kirata ya ce " ki lek'o ina bakin gate"cikin Sauri Aira ta ce "To yaya ganin har yanzu y'an gidansu basu dawoba ya sanya hankalinta kwanciya ta ce " nasan kila ma ba yanxu ba zasu dawo"Fuskarta kawai ta gyara ta janyo doguwar Hijab d'inta tasa Tana fitowa Amir ya fara kuka yana mik'a mata hannu Alamun ta daukeshi tsaki taja tare da dungure mai kai ta ce "saikace cewa nayi zan barshi d'an rigima kawai" shiko shiru yayi tare da Lafewa jikinta yana tsotsar yatsa suna fitowa bakin gate ta nufa Baba mai gadi na zaune gaisheshi tayi ta ce "Baba zan gaisa da wani ba fita zanba ina bakin kofa yana waje " Baba mai gadi ya ce "To kiyi sauri dan Allah maman Alhaji karsu dawo su sameki" murmushi tayi ta ce "To Baba nagode" Tana lek'awa Ta Hango Arman a.mota yana hangota ya taho sosai yayi.mata kyau cikin shigar k'ana nan kaya Fuskarnan tashi sai shek'i take ga sajenshi lufluf dake zagaye da kyakyawar fuskarshi gashin kan nashi sai shek'i yake Dan yau baisa hula ba Alamun yana shan gyara"murmushi Aira tayi ta ce "Amma fa wankan nan ya tafi dani yaya" Haba my love ya fad'a yana karasowa bakin kofar"murmushi tayi ta ce "Ai.kaima ka sani sannan ta bata fuska ta ce " Allah sa wasu basu gama ganemun kai ba"Dariya yayi Kad'an dake k'ara mishi kyau cikin sigar zolaya ya ce "Ai kinsan babu wacce ta isa ma ta tsaya kalle miki miji kinsan kwarjini yake yiwa y'an mata basa iya kallona su k'ara "Uhm yaya kenan sarkin kod'a kai" Ai kema kinsan Gaskiya na fad'a "Sannan ya ce " Wai Amer ne ya girma haka masha Allah kawoshi mu gaisa"ya fad'a yana mik'a mata hannu "Mik'a mishi shi tayi daman Amer ba kiyiwa garai ba Sajen Arman ya kama ya dinga ja yana kyalkyalewa da dariya" Dariya Aira da Arman suma sukayi Arman ya ce "Ina son yara sosai my Aira nasan zaki Haifa mun yara kyawawa kamarki Allah yasa wataran d'anmu ne ni Dake na d'auka haka"Rufe fuska Aira tayi " Murmushi Arman yayi ya ce "bazakice Ameen ba" Dariya tayi ta ce "uhm To ameen my ya...muryartace ta sartse sakamakon Ganin motar su Abba da tayi a bakin gate din Alamun sun dawo suna Horn Cikin rudewa Aira ta amshe Ameer dake.hannun Arman ta Ruga ciki Kad'an Ya hana ta fad'i Arman ko Juyawa yayi yaga Inda take kallo" Girgiza kai yayi tare da Juyawa ya nufi Inda motarshi take Aira cikin tashin hankali ta shiga cikin gidan Tuni ta fara hawaye tace "Shikenan yau karyata ta k'are na shiga ukku " Batayi minti Ukku ba tsaye taji shigowar su Mamy Tare da su Mama hada Amma Cikin Sauri ta Aje Ameer Kasa tare da rugawa tayi cikin Dakinsu ta kulle sai hak'i take"Mamy ko d'anta ta d'auka tayi d'akinta Abba koda ya shigo bai tambayi Aira ba Kuma baice ina take ba bai nuna Alamun ko damuwa a fuskarshi ba Aira ko ta na Chan kulle Ranar bata fito ba Amma ma dak'yal ta bud'e mata ta shiga Washegari saida taga fitar Abba ta window tukwana ta sauke ajiyar zuciya ta fito palour Mamy ta tarar da Mama Gaishesu tayi suka Amsa Ya jikin na Aunty Aysha Mama"Aira ta fad'a tana kallon Mama"Aisha jiki da sauki Aira harma an sallamesu yanzu haka ta na gidan ta na maso nan sukayo da ita"Kamar zatayi kuka ta ce "Allah Kara sauki wlh inason ganinta Dan dai ba yanda zanyi ne" ita ma jiya ta na ta tambayarki idan taji sauk'i zatazo ai "To Allah Kara sauki " Satar kallon Mamy tayi taga harkarta take k'asa tayi da kanta ta ce "Mamy Dan Allah kiyi hakuri Allah bazan sakeba Jiyanma " juyowa Mamy tayi ta ce "Me kikamun " Shiru tayi saikuma ta ce "Jiya da Yaya Arman yazo Allah banzaci har zaku dawoba Nasan Abba ya k'ara fushi dani Dan Allah ki bashi hakuri" tsaki Mamy taja "Matsalarkice wannan tunda ke bazaki kiyaye umarninshi ba gashi gaki ba daidai yake dake ni ba ruwana " Abba ne ya shigo Sosai Aira ta tsorata sai kuma ta dake dak'yal ta iya d'aga baki ta gaisheshi ta ce "ina yini Abba"Lafiya" ya bata amsa sosai tayi mamakin ganin ko maganar Baiyi mata ba sannan ya amsa gaisuwarta Ajiyar zuciya ta sauke a ranta ta ce "Alhamdulilla k'ila Abba ya fara Saukowa " ta nan tsaye ta zaci zaiyi mata maganar amma shiru cike da murna ta koma Tare da cigaba da harkokinta.washegari wajen la'asr Arman ya koma Abuja basuyi bankwana ba da Aira sai a waya Bayan sati guda Ranar Juma'a Aira na palour ta na guga Mamy ta shigo kallonta tayi ta ce "Bar gugar nan Aira tashi mu shiga kitchen ki tayani Aiki Abbanku zaiyi bak'o sai yanzu yake fad'amun" bak'o kuma Mamy waye zaizo"Wai abokinshi ne tun suna secondary daga sokoto zaizo ni banma sanshiba amma Naji ance da yana zuwa kafin inzo gidan nice dai ban sanshiba badai wannan doguwar maganar ba yanzu tashi muje "to Mamy Aira ta fad'a tare da tashi a tare Mamy da Aira suka shirya duk wani Abu da ya kamata papper chicken, abinciccika, snacks karfe hud'u da wani Abu suka gama komai Aira duk ta gaji Dakinsu taje tayi wanka tana fitowa ta tada Sallah tana gamawa ta zira Atamfarfa blue da ratsin fari Riga da sicket sosai suka amsheta bata shafa komai a fuskarta ba Mamy ce ta shigo kallonta tayi ta ce " Bak'on Abbanku ya Iso kije ki d'auki kulolin ki kai palourn Abbanku saiki gaisheshi daga Chan kafin na shirya naje mu gaisa"Hakanan Aira batasan dalili ba Taji gabanta ya bada ras a hankali ta ce "To Mamy bari na kai gyale ta yafa ta fito taje kitchen ta dauki kulolin a basket ta tafi dasu da Sallama ta shiga palourn Abba zaune ta tarar dasu Suna fira sai Dariya suke a hankali ta k'arasa shiga kallon Bak'on Abba tayi dattijone bak'i mai kamala Wanda daga gani bazai wuce sa'annine Abba ba sanye yake cikin manyan kaya babbar Riga Tasha d'inkin manyan mutane k'atoto ne yana da k'iba sosai irin wannan manyan masu kud'in ne masu jiki da tumbi Aira saida taje gab dasu tukwana ta tsugunna cikin ladabi ta ce " Ina yini anzo lafiya"Tunda ta shigo Alhaji Yusuf madugu ya kafeta da idanu bako k'iftawa Wanda sosai kallon ya takura Aira baimaji gaisuwar da take mashi ba saida Abba ya ce "tana gaisheka fa" sai sannan ya dawo hayyacinshi cikin fara'a ya ce "Sorry banji ba lafiya qalau munsameku lafiya" Alhamdulilla "Aira ta fad'a har lokacin kanta kasa Aje basket d'in tayi ta ce " gashi Mamy ta ce a kawo maka"murmushi yayi ya ce "to nagode Beauty" Beauty Aira ta maimaita cikin ranta kallon Abba Alhaji Yusuf yayi ya ce "Yallab'ai y'arka ce ya akayi ban Santa ba" Eh ai ka daina zumunci shiyasa baka santa ba "haba ai zumunci ya na nan indai ba mutuwa akai ba ko y'ar Amarya ce dai naga bata kama da y'ay'an Zainab " Eh Abba ya bashi Amsa "Har lokaci Alhaji Yusuf idonshi na kan Aira ya ce"Masha Allah Ammafa tana da kyau sosai Alhaji Duka tafi Y'ay'anka kyau" Aira na jin Haka tayi saurin tashi duk saitaji mutumin Yama bata Haushi ta ce "Sai anjima " To ya sunanki y'an mata "Hajara ta bashi tare da Juyawa ta fice cikin Sauri ko sauraren me zaice batayi ba har ta isa part d'insu ta na Jan tsaki tana zuwa Mamy ta ce " ke kuma tsakin me kike "turo baki Aira tayi ta ce " nida wannan Bak'on na Abba mana karkiga irin kallon k'urullar da yakemun hada cewa wai wani beauty "tsaki Mamy ta ja ta ce " kede baki rabo da shirme me zai gani a jikinki zakizo kina wani famfamin yana kallon ki "Turo baki Aira tayi ta ce " Allah Mamy da gaske harna fito yana kallona kuma tunda na shiga yake kallona ni bansan kallo "hmm kede kika sani Mamy ta fad'a tana sanya hijab d'inta tare da ficewa taje su gaisa Aira ko zama tayi tana Jan tsaki ita kad'ai..........✍🏿 *ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali Naira 200 kachal katin Mtn ta wannan number 07026166536 karku fitarmun da littafi mu rikewa juna amana please* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/17, 10:08] Hajo hajo: 🅿️.......*47&48* Ta na Jan tsaki ita d'aya Ta na nan zaune har Mamy ta dawo kallonta Mamy tayi ta ce "har yanzu baki gama tsakin ba " Turo baki tayi ta ce Na gama Mamy Dan Allah ban d'ari biyu"Harararta Mamy tayi ta ce "me zakiyi da ita ko wayan da kikamun ne zaki sake" Dariya Aira tayi ya ce "a a wlh Mamy Choculate zanba Haidar ya sayomun " ke bazan bada ba sai shegen shan zak'i zafi duk ya cinyeki"Dariya tayi ta re da tashi ta ce "Ni bani da zafi Mamy bari naje Allah ban iya bacci bansha choculate ba Duka nawa sun k'are " Tana zuwa ta haye Gado ta janyo wayarta kiran yaya Arman tayi yana kira cikin shagwaba ta ce "Yaya choculate d'ina sun k'are " Ba ko gaisuwa cutie ya fad'a cikin husky voice d'inshi"Uhm ai mun gaisa dazu shiyasa to ina yini"Murmushi yayi ya ce "lafiya qlau uwar y'ar shan zak'i " cikin shagwaba ta ce "Kai yaya kaima haka zakace nidai Allah choculate d'ina sun k'are ka kawomun ko na sanya maka kuka" Dariya yayi ya ce "to yi kukan muji " Diddira kafa Aira ta fara ta fara kukan shagwaba na k'irk'ira "ARMAN me zaiyi inba Dariya ba ganin zatayi na gaske ya sanyashi cewa " sorrrry my cutie kiyi shiru yanzu zansa a kawo maki"lokaci guda tayi shiru tana Goge hawaye Dariya ta yi ta ce "da gaske my yaya" gaske mana idan yazo zan kiraki sai mai gadi ya lek'a ya amsa"tsalle ta daka ta ce "yeeeee my yaya thank you so much I love youuu so much I love you with All my heart my sweetheart" murmushi Arman yayi ya ce "I love you too my prince's you deserve more than that Amma ki daina shan zakin nan da yawa karkiga ina biye maki yana da illa Kinga kwanaki ya fara sanyaki ciwon ciki lokacin period "Uhm to yaya ta bashi amsa Yana kashewa ba ayi minti Talatin ba ya kirata ya ce ta lek'a ta amshi sakonta wajen mai gadi cikin Sauri ta mik'e tana murna ta fita palour lokacin Su Amma harsun dawo bata Ko saurare su ba ta fita tana zuwa Baba mai gadi ya mik'a mata k'atuwar Leda har rinjayar ta take tana komawa palour suka ganta da leda Mamy ta ce " wannan Ledar fa "Sosa kai tayi tace " kayan guga ne"dak'uwa Mamy tayi mata ta ce "wannan ne kayan gugar ban mugani" badan Aira taso ba ta mik'awa Mamy zata daga Aira tayi saurin zuwa ta amsa tace Dan Allah Mamy ba saikin daga ba "Saboda baki da Gaskiya ko" a a Mamy to kawo na Daga tana amsa ta shiga dagawa choculate ne manya manya masu tsada sai k'atuwar robar ice cream da juice kala kala gefe kuma an nannade Kaza hada zafinta "kallon tuhuma Mamy tayi mata ta ce " wannan daga gidan ubanwa Aira bansan Rashin ji wlh kodan Kinga ina maki lakwa lakwa "Sosa kai Aira tayi ta ce " Dan Allah Mamy ki bari anjima kinmun fadan Yaya Arman ne fa ya bada a kawoman"Duka a baya Mamy ta kai mata cikin Sauri Aira ta tashi ta kwashi kayanta tayi ciki Tana zuwa ta boye choculate d'inta Haidar ko na ganin Banza ta samu ya biyota shida amma a tare sukaci Wanda suka iya ci sauran Haidar taba ya kaiwa Mamy da Mama mamy ta ce " ta k'oshi"Mama ko ta amsa taci kayanta Ta ce "Ai wlh Rahama indai akan Yaran nan ne kingaji ki bari Koba Aira da Mujahid ba Ai kika bi ta tasu tuni jininki zai hau gwara kawai mu sawa sarautar Allah ido"Wlh yaya nima na sa musu idon ni tsoron Abbansu kawai nake idan ya juyo kanta wannan shirun nashi gani nake ba banza ba baki ganin duk ya zuba mata ido kuma ita sakaran bata sanma Annabi ya k'aura ba" Saidai muce kawai Allah ya kyauta Dan Alhaji bai shiru a banza amma kuma kila ya fara Saukowa"hmmm kawai Mamy tace tacigaba da tunani. Bayan magriba Har Aiport Abba ya raka amininshi Abba yaso ya kwana Amma alh Yusuf yaki ya ce "Karka damu Abokina ai zan dawo kusa insha Allahu" To shikenan nima zansamu na shigo"cewar Abba"murmushi Alh yusuf yayi ya ce "Allah da gaske abokina gaskiya fa y'arka ta na da kyau Alh Ta burgeni wlh " murmushi Abba yayi tare da girgiza kai ya ce "Madugu kenan Har Alh yusuf ya tafi yana yiwa Abba zancen Aira. Bayan Kwana biyu da tafiyar Alhaji Yusuf ya kira Abba Bayan sun gaisa Alhaji Yusuf ya ce " Maganace a bakina Abokina amma ta na da nauyin fad'a Inajin nauyi sosai kuma ina fargaba"Wace magana kenan Alh Madugu ka fad'a kawai kai tsaye "Abba ya fad'a " Alh Yusuf ya ce "A Gaskiya Alhaji bazan b'oye maka ba wallahi tun sanda naga y'arka Hajara Zuciyata ta kamu da sonta Mai tsananin gaske Tunda na koma gida wlh alh bana iya bacci da na kwanta ita nake gani kwata_kwata hankalina ya kasa kwanciya sainazo zankiraka na fad'a maka nauyin maganar tasa na kasa Dak'yal yanzu nayi jarumta har na iya fada maka abunda ke zuciyata a Gaskiya na gani Ina so Indai ba ayi mata miji ba ina ciki dukda dai nasan na manyanta shine na kira na nemi amincewarka Allah yasa ba ayi mata miji ba Kuma za a amsheni " Daga bangaren Abba sosai yayi mamakin maganar data fito daga bakin aminin nashi wata zuciyar kuma ta ce "Alhamdulilla wannan babbar dama ce ta zo maka cikin sauk'i " Ajiyar zuciya Abba ya sauke ya ce "To Alhaji maganar Gaskiya banyi mata miji ba Kuma kai ba mutum bane da za ace yana da wani aibu da baza a bashi Aure ba tare muka taso nasan halinka kasan nau maganar Gaskiya kai tsaye zan amsa maka ni mahaifinta na baka ita " Ajiyar zuciya Alhj Yusuf ya sauke sosai yayi mamakin amincewar aminin nashi cikin Sauk'i cike da farinciki ya ce "Nagode nagode Alhaji bansan da wani yare zanyi amfani wajen gode Maka ba Tabbas kayimun babbar kyauta ni kuma insha Allahu bazan baka kunya ba insha Allahu zanriketa da amana Saidai kuma wani hanzari ba gudu ba ka fara tuntub'ar yarinyar kaji ta bakinta Kasan yaran yanzu sai tace Nayi mata tsufa zanso na samu amincewarta tukwana " karka damu Alh Madugu bani da matsala da ita duk umarnin da na bada dashi ake amfani Dan haka indai da gaske kake kana son yarinya Magana ta k'are bayan anyi Aure ka nemi yardartata"Alhamdulilla to shikenan nagode sosai Alh ko ince Abba dan yanzu kuma ka zama uba Allah ya saka da alkhairi "Dariyarsu ta manya Abba yayi ya ce " Madugu kenan Yanzu nan da kwana biyu zanyi shawara sai na fada maka ranar da Zaka turo magabatanka Dan bansan abun ya dau kwanaki sosai Alh Madugu ya shiga Jerawa Abba Godiya shikan kakarshi ta yanke sak'a bai tab'a tunanin Abba zai amince mashi cikin Sauk'i haka ba Abba ko suna gama waya hamdala yayi ya ce "Allah na gode Maka da ka kawomun haryar rabuwa da yarinyar nan cikin Sauk'i bata daukomun magana ba".tundaga ranar Abba da Alh Yusuf suka shiga daidaita maganar ranar da magananta Alh Yusuf zasu turo Babu Wanda Abba ya sanarwa Cikin gidan Aira ko yanzu Hankalinta kwance yake Dan yanzu ba mai takura mata ko sa idon da Abba ke mata ya daina ga sako da Arman yake badawa a kawo mata kullum take amsowa a gurin mai gadi a haka har akai sati guda Ranar Asabar Aira na kwance sai shan love d'inta take da Arman Ta na shan choculate d'in da ya kawo mata Sun kwashi kusan awa Ukku suna waya Arman ne ya ce" Gaskiya cutie na gaji wlh Kawai zanzo na tinkari Abba da magana kai tsaye Ayi mana Aure wlh na gaji "Dariya Aira tayi ta ce " kai my yaya me kake ci na baka na zuba ka bari mana su k'ara hucewa Dan wlh Abba ya fara hucewa yanzu ya daina Takuramun kuma fa rannan har ganina yayi na amso sako amma baice uffan ba Kuma fa ranar nan ma da yaganmu tare ko uffan bai ceba "Allah my Love da gaske kike" wlhko yaya"To Alhmdllh Allahsa ya fara hucewar Dan kinsan ni nafijin Abba wlh Daddy banajinshi sosai yana Saukowa wani time din idan ya hau shikuwa Abba baya Saukowa"murmushi Aira tayi ta ce "Shima zai sauko " daga palour Aira ta jiyo y'an gidan su na oyoyoy ga aysha cikin Sauri ta mik'e ta ce "Yaya sai anjima Aunty Aysha tazo " tafada tana kashe wayar tare da ajeta a guje ta ruga palour Tana zuwa kuwa taga Ayshar ce Ai da gudu ta je ta d'are ta cike da farinciki ta ce "oyoyoyo my Aunty " Rungumeta Aysha tayi ta ce "oyoyoy sis nayi kewarki da yawa" Cike da farinciki Aira ta saketa ta kama hannunta ta ce "Nima nayi kewarki Aunty Gaskiya nayi farincikin ganinki sannan ta bata fuska ta ce " ya jikin naki Aunty Kinji sauki ba abunda ke maki ciwo dai ko"murmushi Aysha tayi tare da lakutar kumatunta ta ce "Na warke sis " Zaunawa sukayi kujera D'aya Aira tana Rungume da Aysha ta gefenta ta ce "Allah ya k'ara sauki Aunty ya kawo mana wani mai amfani Amma dai yini kikazo mana ko aunty" Ameen my Aira eh yau ina nan har magriba "yeyeyeye yawwa my love " Aira sai murna take sai nan nan take da Aysha ta kawo mata wannan ta kawo mata wancen"Mama tayi dariya ta ce "Ai yau kuma Aira ba zama" Mamy ta ce "Ah ina zata zauna K'auna guda na gida " Dariya Aysha tayi ta ce "Ai dole ai zuwan nata ne" Murmushi Aira tayi ta ce "Ai ina mugun sonki sosai wlh Aunty" Abba ne suka ga ya shigo da goro bayanshi Baba mai gadi d'auke da cartoons d'in biscuit da su halawa "a ajjewa sukayi a palourn Abba ya Sallami mai gadi ya fita neman kujera Abba yayi ya zauna tare da sauke ajiyar zuciya Duka d'akin Kallon abubuwan da Abba ya shigo da su suke cike da mamaki Mamy ce ta kasa shiru ta ce " Abbansu wadannan kayanfa naga su goro"Kayan sa Auren y'arki ne"Abba ya fad'a yana Danna waya"Cike da tashin hankali Mamy ta mik'e ta ce "Sa Aure kuma wace y'ar tawa" kina da wace y'ar ne da ta wuce waccen "ya fad'a yana nuna Aira" Cike da Tashin hankali Aira ta mik'e Aysha Da Mamy ne suka hada baki wajen cewa"sa Aure kuma?Aira ko kasa magana tayi sai kallon Abba ta ke jin maganar tashi take kamar a mafarki Mama ce ta ce "Alhaji ka sanyamu cikin duhu ka warware mana Dan Allah " Ai daman warwarewar nazo maku inason dukanku ku bud'e kunnanku ku saurareni da kyau"Wannan kayan da kuke gani na sa Auren Mamana ne Aira Tare da Amini na Alhaji Yusuf Madugu sokoto Tun sanda Yazo ya ganta yarinya tayi mai baiyi kwabron baki ba Ya fad'amun ni kuma na amsamai na bashi ku godewa Allah ma da da kanshi ya ce ya na sonta dan ina shirin bada ita sadaka Yau magabatanshi sukazo da kayan sa auransu da toshi An sanya Auren wata Guda Masu zuwa na fad'a muku ne yanzu Dan kar kuji daga sama Dan haka sai ku fara shirin biki "Kutumar Uban nan Suka tsinkayi Muryar Mamy daga sama cike da Masifa da tashin hankali ta mik'e ta ce........✍🏿 *Tofa ana wata ga wata tashin sense ta Inda Abba ya b'ullo kuma*🙆🏽‍♀️ *Ni da yaya Arman it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/17, 10:43] Hajo hajo: 🅿️.........*49&50* .....Ta ce "Wlh Alhaji baka isa Ba idan na yarda shegiya nake wannan Ai zalinci ne da nuna k'iyayya k'arara y'ar tawa yarinya k'arama zaka Aurawa Wannan tsohon Abokin ka ne fa sa'ankane to wlh ban yarda ba ai ba kai kad'ai kake da iko akanta ba Nima Ina da iko akanta tunda Nina haifeta " cikin nutsuwa Abba ya ce "Daga baya kenan duk wani hauka da zakiyi ihu Bayan hari ne hukunci ne na Riga na yanke kuma ba Wanda ya isa ya k'etareshi Abunda baki sani ba Duka keda y'artaki ido ne na zuba maku a tafin hannuna kuke yawo hukuncine na Riga na yanke Aure kuma ba fashi" kuka Aira ta fashe dashi cikin kid'imewa kwata kwata jin Abun take har yanzu kamar mafarki ihu ta fasa tare da kuka ta ce "Na shiga Ukku Abba tsohon nan fa kake nufi shikenan na mutu Abba ka temakeni kayiwa girman Allah karka Mun haka Wlh na nustu na shiryu nabi Allah na bika Abba karka Auramun Tsohon nan wlh duk hukuncin da ka yanke mun na yarda dashi amma ka janye wannan " ta karasa fad'a tare da durk'ushewa tana fashewa da kuka mai tab'a zuciya cikin tashin hankali Mama ta ce "Haba Alhaji wannan ai ba adalci bane taya zaka Aurawa y'arka tsohon nan " Aysha ko rik'e Aira tayi da ta haukace ta ke risgar kuka Ta kalli Abba ta ce "Abba Dan Allah Inda wasa kake ka fad'a mana" Mamy batasan lokacin da wani kuka ya Kufce mata ba cikin kuka ta ce "Daman nasan Ba kaunata kake ba Nida y'ata inbanda Rashin so da Rashin Adalci Duka cikin Y'ay'anka wa ka tab'a yiwa haka wak'a tab'a Aurawa tsoho Duka gatan da kakewa Y'ay'anka babu d'aya da kayiwa y'ata Wlh Alh nayi maka Allah ya isa saita bika chutata kawai kake ko ni uwarta a zamaninmu ma Anyimun Haka na yarda bare ita" Ta k'arasa fad'a cikin kuka Abba ne ya ce "Daman wannan ranar nake jiran zuwanta Duka kince cikin y'ay'ana babu wacce na tab'a yiwa haka bakiyi karya ba Amma ki duba kiga cikin y'ay'ana babu wacce ta tab'a yimun kwatar abunda y'arki tayimun Aira ta kwana A waje,ta fita cikin dare sunje sun had'a iskanci a idon duniya Wanda cikin y'ay'ana ko a cikin gida basu tab'a hadawa ba,na hanata Abu tayi" na rabata da Yaron Chan yafi a k'irga amma tak’i rabuwa dashi ,ido k'arara ta rainani zan fadi magana yanzu kafin a jima ta take ta a idonki ido na Bayan na k'ara rabasu muka gansu a kofar gida ,sannan ko ranar da ta fita Ke da kike d'aure mata gindi Kika kareta to a mota naje shan round na ganta ita dashi na kyaleku ne.kawai naga gudun ruwanku sannan duk sayayyar da take shigowa gidan nan akan idona Yarinyar Chan bama nema take ta kangare ba ta Riga da ta kangaremun ta lalace yaron Chan ya iskantata Dan haka wlh ba a gida na ba ban haifi d'an da zai kunyatani a idon duniya ba duk k'ok'arin da zanyi nabata tarbiya Inma ke kika koya mata Rashin tarbiya to ga k'arshen abun yau na kawo Idan Kinga Anfasa auran nan Saidai in bana numfashi kuma godewa Allah da zamu Aurar da ita Bata d'auko mana magana ba "Mamy sosai take kuka ta kasa maidawa ma Abba magana Aira ko tuni ta haukace fisgewa tayi daga hannun Aysha ta Ruga ta rik'e k'afar Abba ta ce "Wlh Allah bazan yarda ba ni Inma Auren ne Abba wlh ni Yaya Arman nakeso A Auramun inshine wlh ko yanzu na yarda Dan Allah karka Auramun tsohon najadun nan Wlh Abba bani ba ko Mamy ya Haifa " D'auketa da Mari Abba yayi ba arziki ta sakeshi tare da kama kumcinta Abba ko tsallaketa yayi ya fice daga d'akin Aira na mik'ewa Goron ta D'auka ta wullashi tare da warwareshi a d'akin da dinga watsi da kayan d'aurin Auren ta hau watsasu tana kuka tana sabbatu ruk'ota Aysha Da Amma sukayi da suma kuka suke "Rungume Aysha tayi ta ce " Aunty shikenan Abba ya kasheni wlh ni yaya Arman nakeso Allah idan suka rabamu mutuwa zamiyi Aunty ku taimakamun ku ce Abba ya fasa Dan Allah"Rungumeta Aysha tayi ta ce "Kiyi hakuri ki nutsu" Fisgewa Aira tayi taje ta fad'a kan Mamy dake kuka ta ce "Mamy ki taimakamun kar Abba ya auramun tsohon nan mamy wai Dan Allah Abba baida magaya da zanje na samesu Dan Allah idan kinsan wani Wanda yakejin tsoro ki fad'amun ko shi baida mafad'a"kasa daga baki Mamy tayi magana d'anji take zuciyarta kamar zata rabe gida biyu Kamar wacce aka tsunkula Aira Haka ta tashi tare da rugawa da gudu tayi waje Binta Aysha sukayi Amma ta ruga ko kallabi kanta babu haka ta fito ko Baba mai gadi bata saurara ba ta bud'e kofa ta fice a guje Binta Aysha Da Amma sukayi suna cewa" ina zaki Aira ki dawo wai baki da hankali"Tana fita Aira gudu kawai take Ganin su Aysha sun biyota ya sanyata tsaida napep Mai napep din kanshi saida ya tsorata da yanayin ta Amma Hakanan ya d'auke ta tunda ta shiga kuka kawai take mai napep ya ce "Hajiya ina za a kaiki cikin kuka ta ce Hotoro su Aysha ganin ta hau napep cikeda firgice suka koma suna zuwa Suka tarar da Inna gaban Abba sai surfa masifa ta ke ta na cewa"wannan Ai zaluncine Habubakar zakayiwa y'arka to wlh indai na isa dakai kaje ka mayar musu da kayan auran su kai dama ban isa da kai ba ka rainani kodan bani na haifeka ba " cikin girmamawa Abba ya lallab'ata Inna ya ce "to shikenan kiyi hakuri Inna za a mayar musu Dan Allah ki koma ki kwantar da hankalinki " Dak'yal Abba ya samu ya lallaba Inna ta koma part d'inta sai famfami take Su Aysha ne cike da damuwa ta ce "Abba Aira fa ta Ruga bako kallabi mun bita ta tari napep Dan Allah a fito da mota mu bita karta shiga wani halin" Tsawa Abba ya daka wa Aisha ya ce "wuce ku ban wuri " ba arziki Aysha suka koma ciki Sai kuka take da magriba mijinta yazo zai d'auketa ta ce "ba Inda zata ba yanda ya iya sai komawa yayi Dan tace sai gobe. Aira a napep ma sai kuka take mai napep ya dinga bata hakuri ya ce " sai hakuri baiwar Allah dukkan mai rai mamacine"Dan a tunaninshi mutuwace aka mata ita dai Aira bata tanka shiba har suka isa Hotoro suna zuwa inda zata ta ce ya isa tana sauka ta hau buga gidan da karfi ta na kuka a lokacin har ankira magriba mai napep kam girgiza kai yayi ya wuce Dan ko kudi bata bashiba Aira na cikin bubbugawa Khady ta fito ta bud'e kallon Aira tayi ta ce "Lafiya ke kuma" Aira ba ta ko saurareta ba ta bangajeta tayi ciki "yaya Umar yaya Umar kawai take fad'a harta isa palourn Tana zuwa ta sameshi yana shirin fita Sallah fad'awa jikinshi Aira tayi tareda sakin kuka cikin tashin hankali Umar ya ce " Lafiya Aira waye ya mutu ko ba lafiya "cikin kuka ta ce " Yaya Abba ne...Abba ne yayi me ya Umar ya fad'a cikin tashin hankali Dan a tunaninshi wani abun ne ya samu Abban Kuka ta k'ara fashewa dashi ta ce "Abba ne ya ce zai auramun Abokinshi wai har sun sanya Aure wlh yaya mutuwa zanyi karkaga tsohon ya haifi Mamy Dan Allah kaje ka hana shi Nasan kaikad'aine magayinshi" Daddab'a bayanta yaya Umar yayi ya ce "Subhanallahi kiyi shiru yanzu zauna naje nayi salla saimu tafi gidan insha Allahu bazai aura maki ba " zaunawa Aira tayi ta hade kanta da gwuiwa sai risgar kuka take yaya Umar fasa fitama masallacin yayi ciki ya koma Dan yayi Sallar a gida ya gama su tafi Dan ta rud'ashi Yana shiga ciki Khady dake tsaye taja tsaki ta ce "Allah ya k'ara aniyarki ce ta koma maki ni ai kikaso mijina yamun kishiya kika mak'alamai wata sai gashi Allah ya maida maki aniyarki saikije Chan Allah raka taki gona daman ai kun saba Auren tsaffi uwakkima Auren kud'i tayi waye bai saniba taga Abba yafi k'aninshi kud'i lokacin shiyasa ta aureshi ta had'a y'an uwa gaba Ai gashi nan Alhakine ke ta binku " Aira cike da masifa ta mik'e sosai taji zafin maganganun Khady cikin b'acin rai Ta ce "Alhamdulilla tunda uwata Auren kud'i tayi ke Ai naga uwarki ta samu Mai kudin da ta aura ince ubanki ba shi bane Salisu mai wankin hula a bakin titi Banza y'ar matsiyaciya da kika taso cikin tsiya kin samu wuri shine har zakiyiwa mutane iskanci banza juya wacce ko B'ari bata tab'a shekara Shida Da Aure juya kawai y'ar matsiyata" kasan abunda zaka fad'a bakasan abunda za a mayar maka ba Khady sosai Maganar Aira ta k'ona mata rai Kukan kura tayi ta Kama Aira da dambe ta ce "Yau zakisan ni kika zaga itama Aira Daman ranta a mugun b'ace yake Aiko ta chukunkume Khady suka hau Dambe dukda Aira ke cutuwa Dan Khady Nada jiki Amma k'arfin hali na Aira Farcenta tasa ta yage ta a fuska har saida jini ya fito Yaya Umar ne ya fito Cikin tashin hankali ya shiga rabasu ya ce " meye haka bansan iskanci ubanme ya had'aku.dak'yal ya samu ya rabasu dukansu sai huci suke Khady ta fashe da kukan munafurci ta ce "wai baby daga zuwanta ta hau mun gori wai juya bani haihuwa " Itama Aira kuka take ta ce "Karya take yaya ita ta fara zagi na da Mamy wai Mamy tayi Auren kud'i ta auri Abba Dan yafi Daddy kudi nima wai Allah Kara da za a auramun tsohon" ta fad'a tana Kara rushewa da kuka "D'auke Khady umar yayi da Mari Dan yasan kome akace zata aikata ya ce " Dan iskanci iyayena sa annin kine ina ruwanki da harkar gidanmu nasan kome akace zaki aikata fiye da haka"Rushewa tayi da kuka ta ce "Shine ka mareni gaban kanwarka ka goyi bayanta a kaina Umar" Tsaki Umar yaja sannan ya kalli Aira ya daka mata Tsawa ke kuma da yake sa'arkice har zakiyi dambe da ita wuce muje biyoni "ya fad'a yana bin hanyar fita"Cikin Sauri itama Aira ta bishi juyowa tayi tare da yiwa Khady gwalo zata taso ta Ruga" A motar yaya Umar Aira suka taho suna isowa gida Ya ce "wuce ki shiga ciki zanje na samu Abban" to yaya nagode "tafada tare da shiga ciki idonta duk yayi jawur taranta Aysha tayi ta ce " Alhmdllh ina kikaje duk kin tada mana Hankali "Goge hawayenta Aira tayi ta ce 'gidan yaya Umar tare muke dashi yana part din Abba ya bashi hakuri " Ajiyar zuciya Aisha ta sauke ta ce "Ai nazata wani wajen zaki " ina Mamy"Tana d'akinta "cikin Sauri Aira ta nufi d'akin tana zuwa ta sameta a Gado sai risgar kuka take Amer na kanta shima yana kuka ita har tafi Aira shiga tashin hankali " Fad'awa jikinta Aira tayi itama ta fashe da kukan cikinsu ba mai Lallashin wani "Mama ce ta shigo dak'yal ta rarrashesu ta ce " Haba Rahama kamar yarinya tun d'azu fa ake baki hakuri ko ita Airar batayi kukan da kikayi ba Kara tayar mata da hankali kike keda zaki kwantar mata da hankali"Haba Yaya wlh dole nayi kuka kawai Alh ya cuceni ya zalinceni Aure fa ya sanya mata da sa'anshi kwata kwata ya kashe rayuwar y'ata ta fad'a tana kuka"Cikin kuka Aira ta ce "Mamy wlh ni nasan abunnan bazai yuba Yanzu ma tare muke da yaya Umar yana wajen Abba yana bashi hakuri nasan kila ya hakura " Kallonta Mamy tayi ta ce "duk ba ke kika ja ba duk yanda nake nuna maki kika k'i ki gane shi umar d'in Gidanshi kikaje " Eh Mamy har mukayi fad'a da Matarshi ta fad'a tana saka kuka"Fad'a kuma Mama da Mamy suka fad'a nan Aira ta kwashe komai ta fad'a musu sosai ran Mamy ya b'aci amma ta Danne Mama ko fad'a ta shigayi sosai ta ce "zataci ubanta tunda ita y'ar gidan matsiyata ce zan nuna mata fushi na sannan kinyimun daidai da kika goranta mata tunda ita bata da hankali" Mamy ko cewa tayi "Ai Inda sabo na saba da jin maganganunan Su har yanzu mutane basa Duba Aure da haihuwa yafi gaban wasa wani baya haihuwar d'an wani Kome rubutaccene Amma bakomai Ai akwai Allah duk na barsu da Allah "Ba irin magiyar da yaya Umar baiyiwa Abba ba akan ya janye maganar nan amma yak'i yace ya gama yanke hukunci har Tara Umar na Abu d'aya daga karshe sai tafiya yayi ko ciki bai koma ba Dan baisan ya iskesu cikin tashin hankali Ranar Aira daki daya sukakwan da su Aysha kuka tayi ta risga musu suna Lallashinta Har karfe sha biyu tana kuka ga kanta dake mata ciwo Dak'yal Aysha ta Rungumeta ta dinga Lallashinta tana shafa bayanta a haka har wahalallen bacci ya kwasheta a hankali Aysha ta kwantar da ita tukwana itama ta kwanta gefenta cike da tausayin y'ar uwar tata Dan tasan Abba baya magana biyu"...........✍🏿 *Karki fitarmun da Littafi mu Rikewa juna amana y'an uwa duk maiso ta biya ta karanta cikin kwanciyar hankali* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/19, 10:19] Hajo hajo: 🅿️..........*51&52* .....Washegari haka Aira ta tashi sukuku kallo d'aya zaka mata ta baka tausayi lokaci guda harta rame Ba irin yanda ba ayi da ita ba akan taci abinci ba Amma takiya had d'ure Aysha tazo zata mata amma ta cije Haka.ta yini har dare bataci komai ba kwance ta yini a d'aki Tunanin Arman yaki barin kwalwarta Yama zaiji idan yaji wannan mummunan labarin shi yafi damunta saida dare Mamy taje har d'akin da take kamar zatayi kuka ta ce "ki tashi kici abinci Dan Allah Aira inba so kike hankalina ya k'ara tashi ba wani abun ya sameki ba " Aira da harta gaji da kukan tashi kanta dafe da kanta dake tsananin sarawa sai hawaye da take ta ce "Mamy bazan iya ci bane Dan Allah Mamy ku bawa Abba hakuri ya janye Auren nan Ji nake mutuwa zanyi kafin lokacin" Rungumeta Mamy tayi itama tana hawaye tayi Sauri ta Goge Dan son kwantar mata da hankali ta ce "ki kwantar da hankalinki yanzu haka Inna na wajenshi kuma Halima ma ta kirashi Suna Chan suna kokari zai janye insha Allahu Amma kici abinci kinji y'ar kirki" Goge hawayenta Aira tayi cikin muryar da ta gaji da kuka ta ce "Allah yasa ya yarda A baki Mamy ta dinga bata abinci har ta samu ta d'anci sai sannan hankalin Mamy ya Dan kwanta ita ta taimaka mata tayi salla har isha'i tukwana ta kwantar da ita Dan taji jikinta zafi ta ce " kiyi bacci Dan Allah "gyada mata kai Aira tayi ta ce " to Mamy "kallon aysha mamy tayi ta ce " ki shirya mijinki ya zo ku tafi" mamy bazan iya tafiya ba Aira na wannan halin please ku ce mashi ya bari sai gobe"a a a aysha ba za a yi haka ba shiryawa zakiyi ki tafi goben zaiki dawo tunda ba wani abu ake ba mijinki karya daukemu k'ananan mutane"Aysha ta Goge hawayen tausayin y'ar uwar tata ta tashi ta sanya hijab d'inta zuwa tayi ta Rungume AIRA ta ce "karkisa damuwa a ranki plz sis kiyi bacci gobe zandawo kinji kuyimun Alk'awarin" gyada mata kai Aira tayi daga kwance hawaye nabin gefen idonta Badan ta so ba Aysha ta koma gidanta cike da tunanin tausayin y'ar uwar tata Mamy ko tashi tayi ta nufi dakinta itama cike da tausayin y'artata Aira ko har 1 bacci bai d'auketa ba wajen karfe ukku kallon gefenta tayi taga amma ce kwance tana bacci tashi tayi tare da shiga toilet ta d'auro alwala Tana fitowa ta sanya hijab nan ta tada salloli ba abunda take sai rokon Allah akan ya lalata wannan Abun karo na farko kenan da Aira ta shiga tashin hankalin da har ta tashi cikin dare take k'iyamul laili inba da azumiba idan sunje tuhajji Har asuba tana salla Sai Bayan asuba bacci ya kwasheta akan sallaya bama tasani ba da safe Mamy ta shigo Dan ta bata break fast ta ganta kwance kasa kan sallaya da hijab amma data fito daga toilet ta tambaya tace ya na ganta kasa kwance "wlh mamy kwana tayi tana salla inad'anjinta cikin bacci to bayan tayi asuba ne bacci ya kwasheta shiyasa ban tashetaba Dan ta d'an samu baccin girgiza kai Mamy tayi ta ce "Allah mai iko kenan Wai Aira ce da Sallar dare Allah Amsa maki abunda kika roka Mamy ta fad'a tana barin d'akin ta na fita part din Abba ta nufa zaune ta sameshi yana Tasbihi saida ta jira ya gama ta gaisheshi " Bayan ya amsa "hawaye ta fara ta ce " Dan Allah Abbansu kayi hakuri ka janye maganar Auren nan wlh yarinyar nan zata shiga wani hali ka tausaya mata Dan Allah"bazaki gane bane Rahama nafiki Sanin abunda nake Idan na zubawa yarinyar nan ido wlh abun Kunya zata d'auko mana ke uwace kiyi mata addu'a kawai Allahsa hakan shi yafi alkhairi bawai ki rik'a zuga ta ba "Cikin muryar kuka Mamy ta ce " to tunda zarginsu kake Abbansu ka Bari su Auri juna mana Ita dashi tunda kana zargin sunsan juna a waje kaga Inma sunyi Auren Chan su karata asiri ya rufu amma Dan Allah karka Aura mata tsohon nan ka barta ta Auri Wanda takeso "tsaki Abba yaja ya ce " ki tashi kiban waje indai Akan maganar wannance Har abada indai Nina haifeta bazan tab'a Aura mata Mujahid ba akan idonki wace irin Maganace ubanshi bai fad'a mana ba Har cewa yayi indai na isa da y'ata na rabasu sannan y'a mace ke abun Kunya ba d'a namiji ba irin maganganu masu ciwo da baifadamunba akanta Shine kike zancen wai na barsu su Auri juna karki Kara zomun da wannan shashanci Aure ne an Riga ansanya gwarama ku fara shiri"tashi Mamy tayi cikin fad'a ta ce "To Dan kaga muna Binka lakwa lakwa karka fasa d'in mu zuba mu gani niko Allah banga Auran nan ba Allah kaimu lokacin Saimuga ta yanda za a daura Wannan ai zalinci ne kake kai ba a isa a baka hakuri ka hakura ba Allah baza ayi Auren ba Indai Nina haifi Aira aiba y'arka bace kai d'aya bare kayi ikonta kai d'aya nima y'ata ce kuma ni nasha wahalar Haihuwarta harda za adinga mun iko akanta" ta k'arasa fad'a cikin kuka" tsaki Abba yaja ya ce "Karki samun ciwon kai da safen nan mai k'aramar kwalwa kawai har yanzu kwalwar yara gareki wlh shirmen da zakiyi ko Haidar d'anki na biyu baya yiba Dan ta farkonma irin kanki tayo shiyasa take bani matsala duk maganar da tazo bakinki ki dinga fad'amun Kamar ba mijinkiba wlh in banda kece da babu wacce ta isa tamun abunda kikemun na kyaleta amma ke bakya gani ganinkima ke ake chuta yanzu wannan Abun da kike shi zaki koyawa y'arki taje tanayiwa miji" Tsaki Mamy taja ta ce "Ai daman ka saba Cemun mai k'aramar kwalwa to wannan Karin zakaga aikin k'aramar kwalwar tana gama fad'ar hakan fuuuu ta fice daga d'akin tana komawa d'akinta ta kira Mama Halima tana kuka ta ce " yanzu Halima haka zamu zuba ido Abun nan ya faru wlh yanzu haka daga wajenshi nake naje mai da lalumarma amma karshe ba arziki muka kwashe yanzu ya zamuyi halima"da yake Mama Halima Tabawa Mamy wannan shawarar numfasawa Mama Halima tayi ta ce "To ni yanzu wlh kaina ma ya kulle Banmasan ya zamu b'ullowa yaya ba Nima fa Dana kirashi ba irin magiyar da ban mashi ba Amma ya murje ido yanzu yanda za ayi kawai kiyi hakuri mu zubawa sarautar Allah ido sannan ita kuma Mamana ki lallabeta kice mata kunyi magana dashi ya ce ya janye Dan a kwantar mata da hankali karta shiga wani hali" goge hawayenta Mamy tayi ta ce "To shikenan Halima nagode Bari nace mata hakan " sai wajen Azahar Aira ta tashi tana tashi taji saukin ciwon kan wanka taje tayi tana fitowa Mamy ta shigo da abinci saida Mamy ta bata fuska tukwana ta yarda taci abincin cikin lallashi Mamy ta ce "ki kwantar da hankalinki Mamana Munyi magana dashi kuma yace zai hakura amma saiyaga nutsuwarki har zuwa lokacin ki kwantar da hankalinki kinji" cikin farinciki Aira ta d'ago ta ce "Mamy da gaske " gyada mata kai tayi ta ce Gaske mana"Alhamdulilla Aira ta fad'a tare da Rungume Mamy ta ce "Nagode Mamy Allah tsundumaki a aljanna nikuma insha Allahu zankiyaye nagode Gaskiya Mamy kincika uwa ta gari Allah saka miki da alkhairi " murmushi Mamy tayi ta ce "Ameen yanzu ki kwantar da hankalinki ki dinga bacci kina cin abinci kinji" gyada kai Aira tayi tana murmushi ta ce "Insha Allahu Mamy kai ashe addu'a ta ta amsu " murmushi kawai Mamy tayi a zuciyarta ta ce "tukunna dai" Tun daga ranar Aira ta d'an kwantar da hankalinta take cin abinci amma walwalarta taki dawowa Tana waya da Arman akai akai ta kasa fad'a masa abunda ke faruwa Abba ko dabara yayiwa inna ya tura ta umrah dan yasan halinta haka zatayi ta cewa dan ba ita ta haifeshi ba shiyasa bayajin maganarta Yaya Umar ko tuni ya koma wajen aikinshi tare da matarshi dan yace ko bikin bazaizo ba a haka har akayi sati Ukku Ranar Litinin Aira na baccin rana Haidar yazo cikin tashin hankali ya dinga Bugata ya ce "ya Aira ki tashi " tana tashi ta ce "ya akai haidar ina bacci kanamun wannan tashin hawaye haidar ya fara ya ce "ya Aira kije palour ki gani wlh ashe Abba da gaske yake Auren nan Lefenki ne aka kawo yanzu daga sokoto firgit Aira ta mik'e ai bata gama Jin Abunda Haidar zai fad'a ba tayi palour cikin tashin hankali tana zuwa ta tarar da Wasu mata tare da su Mama hada su Mama Halima Akwati Sunkai guda ashirin baje a palourn tashin hankalin da ta shiga bai misaltuwa tsaye tayi tare da kama k'ugu tana k'arewa y'an d'akin da akwatinan kallo Wata mata ce daga cikin Wanda suka kawo kayan ta ce " Ah masha Allah itace amaryar kenan ba shakka Allah Sanya alkhairi ya bada zaman lafiya"Ba Ameeen ba Aira ta fad'a tare da Jan tsaki cike da Rashin kunya tare da nuna yatsa ta ce "Na rantse da Allah kuka yarda Aka d'aura Auren nan kun saiwa kanku tashin hankali wlh tun wuri ku kwashi tsiyarku ku koma Inda kuka fito kunzo kun wani jugum jugum bako kunya tsaffin banza kawai uban Waye za a aurawa tsohon najadun nan ko nayi muku kama da kalar tsaffi kuje chan ku nema mishi tsohuwar zawara ko sa’anninku ne itace mate dinshi ba niba wlh ko ku fita da Kayan nan ko na zagi tsohuwa har uban tsoho da uwarsa zan zaga dan haka ku kwashi tsiyarku ko in sawa kayan fetur wlh “Lokaci guda Aira taji jinta da ganinta sun fara gushewa kwalwarta ta fara juya mata Duka matan da suka kawo kayan sororo sukayi suna mamaki wace mata ta ce " lallai yusuf yau ya kawomu inda za a wulakanta mu Daman yarinyar bataso kenan to Aiko da sake "Kanwar Alh Yusuf ce ta mik'e ta ce " Ku tashi mu tafi munfasa daman yasan yarinyar bata da tarbiya shine zaisa muzo ayi mana Rashin mutunci "Mama ce ta ce " Dan Allah Kuyi hakuri yarinta ce Mama Halima ko d'auke Aira tayi da Mari ta ce "Daman baki da mutunci Aira Rashin kunya zakiyiwa mutane Dan iskanci wadannan waye bai haifekiba" kuka Aira ta durkushe ta fashe dashi ta ce "Mama kuyimun rai wlh banason shi sannan ta Ruga wajen Mamy ta jijjigata kamar mahaukaciya ta ce " Daman Mamy k'arya kikamun kikacemun Amfasa Mamy dake za a had'a baki a kashemun Rayuwa"Tsawa Mama Halima ta daka mata ta ce "Wai baki da hankali Aira uwar taki kike cewa ta miki karya ki wuce kiba mutane wuri" Durk'ushewa Aira tayi kuka kawai take kamar ranta zai fita Wanda suka kawo kayan nan wata dattijiwar mata ta ce "ku bita a hankali Dan Allah mu bamusan yarinyar bataso ba Gaskiya a hakura da abun nan tunda Kunga halin da yarinya ke ciki" Abba ne ya shigo da ya samu labarin Abunda Aira tayi da belt ya shigo ya hau lafta mata ihu da kuka Aira take tana neman a kawo mata d'auki tashi Mamy tayi tabar d'akin gaba d'aya dak'yal matan da suka kawo Lefe suka kwaci Aira a hannun Abba su suka dinga bawa Abba hakuri Aira ko da gudu ta Ruga Dakinsu tana kuka Wayarta ta janyo cikin tashin hankali ta shiga kiran Arman. Arman yana kwance a kan sopa Idonshi bud'e amma ba bacci yake ba Hakanan kawai tun satin nan gabanshi ke fad'uwa jin Kiran Aira ya tasheshi kiranta yayi tana d'auka ya jiyo kukanta cikin tashin hankali ya mik'e tare da cewa "Lafiya cutie me ya sameki kukan me kike " shiru Aira tayi sai kuka ta ke "cikin tashin hankali ya ce " please cutie ki fad'amun abunda ke faruwa kin tayarmun da hankali ki fad'amun me yake faruwa"Cikin kuka Aira ta ce "Yaya nashiga Ukku shikenan mutuwa zanyi Aure Abba zaiyi mun cikin satin nan yaya har ankawo Lefe yau wlh bansaniba yaya sai yau na shiga ukku shikenan an kasheni " What Arman yafada cikin tsananin tashin hankali ya ce "Bansan irin wannan wasan kinfi kowa sani Aira ki fad'amun Gaskiya" Cikin kuka ta ce "Wallahi tallahi da gaske Yaya abokinshi zai auramun tsoho ne kuma" Ai Arman baisan lokacin da..........✍🏿 😂Team Aira and Arman how market 🤣yaudai Aira ta zage tsaffi 😅😭Arman yau zaiji mugunji 😭😭where is team Abba🙄 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/19, 22:52] Hajo hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏 Hot love story♥️🔐 *MALLAKAR* *Hajara L Sadeq* *BONUS PAGE*💃🏾💔😂 *This page is dedicated to all lovers of this book as much as they love this book I love them in my life I am so grateful for the way you show love to my book wanda sukayi paying da wanda basuyi ba duka ina godiya ina muku son fisabilillah shafin nan naku ne masoya a duk inda kuke I am very proud of you*♥️❤️♥️❤️❤️❤️❤️♥️♥️♥️♥️♥️♥️ 🅿️..........*53&54* Ai Arman baisan lokacin da wayar ta sulale a hannunshi ba Sakinta yayi Tim a k'asa "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un kawai yake maimaitawa dafe kanshi yayi kamar Wanda Aka tsikara haka ya tashi ya ce " no bazaiyu ba wlh impossible wlh duk abunda yake kusa dashi ya hau wullawa cikin tashin hankali ya kwashi wayoyinshi yayi waje yana zuwa ya kwalawa mai gadi kira ya ce "Ka maza second biyu na baka ka budemun get yana gama fad'ar haka ya tafi ya d'auki motarshi 360 ya jata yana zuwa bakin gate har mai gadi ya bud'e a guje ya figi motar ikon Allah ne kawai ya kaishi Airport lafiya cikin k'ank'anin lokaci ya yanki ticket zuciyarshi ba abunda take In banda zafi kamar zata fashe kowa ya Kalleshi lokacin zakasan yana cikin tsananin b'acin rai idanunshi sunyi jawur kamar garwashin wuta k'arfe bakwai da wani Abu jirginsu ya d'aga zuwa kano.Aira ko ganin Arman shiru tayi ta magana shiru ya sanyata fashewa da kuka jikin kofa ta durkushe kuka kawai take gwanin ban tausayi Bangarensu Abba ko sosai ranshi ya b'aci matan da suka kawo kaya suda aka batawa rai saiyadawo su sukebawa Abba hakuri sukace ai d'ane ka haifeshi baka haifi halinshi ba ba yanda ba suyiba akan a janye maganar Auren nan tunda bata so suka kira Alh Yusuf sukayi mashi bayani shi ko da yake Allah ya d'ora mai son Aira cewa yayi ba abunda za a fasa idan an d'aura Auren zata soshi Ai Abba ma ko haka yace shi da Mama Halima suka basu hakuri akan Abunda Aira tayi musu sukace ba komai sosai akayi musu sha Tara da arziki Da zasu tafi Mama Halima ce Bayan Tafiyarsu ta je ta samu Mamy Tagumi ta iske tayi ta na hawaye dafa ta Mama Halima tayi ta ce "a Gaskiya zan fad'a maki Rahama kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki ki fawwalawa Allah komai wannan damuwar da kike bata sa komai bata hana komai kila Allah ya nufa matarshi ce ba abunda za a fasa kiyi hakuri sannan kiba y'arki hakuri kiyi mata fatan Alkhairi kawai ki bari tayiwa mahaifinta biyayya tunda Kinga ya kafe idan kika nuna Rashin sonki kamar kina k'ara zuga tane ki mata fad'a ta nutsu ta rabu da mahaifinta lafiya sannan ta cire Mujahid a ranta tunda Allah ya nufa kila bashi bane mijin dukda dukanmu ba haka muka so ba ki saki jikinki ayi hidimar biki dake naga ko gayya bakiyiba dan Allah Rahama ki kwantar da hankalinki ki kwantar da na y'arki hakuri zamuyi mu barwa Allah sauran tunda munyi abunda zamu iya" Haba Halima taya zan kwantar da hankali na bama wannan ba yanzu abunda yafi tadamun hankali idan na tuna gidan kishiya za a kaita da y'ay'a ta yaya Aira a y'an shekarunta zata iya da kishiyar da ta haife tamayi kusan jika da ita ina zataji da d'iyan miji ki duba fa kiga nisan sokoto Halima nifa gani nake kamar sayarmun da y'a ne wannan Abun Sokoto fa ina zata iya kishi da sokkwatawa me ta sani game da kishi "Ajiyar zuciya Mama Halima ta sauke ta ce " ai akwai Allah shi zai tsareta insha Allahu ki daina damuwa da wannan nima Inajin wannan din amma Addua zamuyi tayi mata sannan muyi mata nasiha ta zauna da kowa lafiya"Sosai Mama Halima ta dinga bawa Mamy baki.Arman koda ya Iso kai tsaye Gida ya wuce cikin tashin hankali Mamy ta tareshi tace Lafiya son na ganka da dare tsaka Baka sanarmun kuma zaka zoba naga kamar ma baka cikin nutsuwa Arman bai iya magana ba Dan in yana irin cikin wannan tashin hankali bai iya magana lura da haka ya sanya mummy shiga damuwa kamo hannunshi tayi kamar yaro tare da zaunar dashi itama ta zauna kwantar dashi tayi saman cinyarta tare da Daddab'a bayanshi ta ce "Calm down my son yayyafawa zuciyarka ruwan sanyi " Dan haka take mashi idan ya shiga damuwa Arman huci kawai yake tare da lumshe ido yanason yayi control d'in zuciyarshi Sosai Mummy take Abu d'aya dukda batasan meya sanyashi cikin wannan halin ba ta kwashi kusan Awa guda yana kan cinyarta tana lallaashinshi sai Chan taji ya na sauke ajiyar zuciya hamdala tayi azuciyarta alamun ya dawo daidai kenan cike da damuwa ta ce "me yake damunka Arman ka fad'aman please" Arman yana daga kan cinyarta ya lumshe idanunshi tare da bud'esu a hankali kamar mai koyan magana ya ce "Mummy wai Aure zasuyi mata" Wacece za a yiwa Auren "Aira Mummy wlh Mummy inasonta sosai please karki bari a rabamu itad'in rayuwa ta ce Bazan iya cigaba da rayuwa babu itaba " Sosai gaban Mummy ya fad'i tasan abunda Arman yake fad'a Gaskiya Dan son da ya ke yiwa Aira ya zarce misali sosai ta shiga damuwa cikin damuwa ta ce "Aure kuma son Waza a aura mata Bayan sunsan kuna son junanku" Arman baisan lokacin da wasu zazzafan hawaye suka zubo mashi ba ya ce " wani ne Abokin Abbanta Ranar Friday Auren Mummy Dan Allah karki bari ayi Auren nan wlh ni nake sonta nasanke uwace ki tausaya mun nasan Daddy bazai saurareniba ammake zaki saurareni Yin Auren nan daidai yake da rasa rayuwata idan ba so kuke ku rasa ni ba to kusa a hana auran nan please ya k'arasa fad'a tare da mik'ewa ya rik'e hannayenta biyu "Rufe mashi baki Mummy tayi karo na farko kenan da ta tab'a ganin hawayen d'an nata da girmanshi Sosai itama ta shiga damuwa Dan a duniya ba abunda take so sama da Arman d'a daya tilo da Allah ya bata girgiza mashi kai tayi tare da Goge mashi hawaye ta ce " ka kwantar da hankalinka kaji Arman d'ina Insha Allahu Aira taka ce zansamu Daddynku yanzu yaje suyi magana da d'an uwanshi fatan mudai ya yarda"yawwa Mummy Dan Allah kuyimun kokarin wannan "Mummy duk yanda taso da Arman yaci abinci kasawa yayi har a baki ta bashi amma ya cije sosai ya bata tausayi lokaci guda ya zama wani so silent A Daren ta samu Daddy ba irin magiyar da batayimai ba akan yaje wajen Abba suyi magana Dan Allah a janye Auren nan Ya nemawa Arman Auren Aira amma Daddy fir yaki cikin hawaye Mummy ta ce " Ammafa kasan d'anmu zai shiga cikin wani hali me yasa kuke zafafa Abu ne ku bari yaran nan su Auri junansu tunda suna so za a sanya rayuwarsu cikin wani hali"ko zai mutu wlh bazanje ba akanshi wace irin Maganace mahaifinta bai fad'amun ba shine kukeso na je a k'ara fad'amun maganar da zan kwana ban rintsa ba to badaniba bazanje ba idan ke kin matsu kije "Daddy na gama maganar ya fice daga d'akin sosai Mummy ta shiga damuwa Mama Halima ce ta fad'o mata a rai ita ta kira ko zata samu ta taimaka mata amma maganar da taji daga bakin Halima ma ya sanyata Kara shiga damuwa Dan labarin komai Mama Halima ta bata akan ba yanda basuyi da Abba ba Amma ya kafe hatta Inna ta kasa tankwarashi Saidai kawai mu barwa Allah zab'i"washegari Arman har ya fad'a sosai ya shiga tashin hankali da Mummy ta fad'a mashi yanda sukayi da Daddy da kuma yanda sukayi da Mama Halima kamar wani zaki haka ya mik'e kamar Wanda aka zabura ya ce " impossible wlh Mummy bazaiyuba Aira tawace Dan ni kad'ai aka yita bazan tab'a zuba ido ta zama mallakin waniba itadin rayuwata ce munyiwa juna Alk'awarin bazamu tab'a rabuwa ba muddin na bari ta auri wani Tabbas munci Amanar soyayya Yana gama Fad'ar haka ya figi makullin mota kamar zai tashi sama ya fice Mummy ba binshi baiko saurare ta ba mota ya figa a tamanin a lokacin wajen karfe Takwas na dare ranar Aira a d'aki ta yini taci kuka kamar ba gobe masu Lallashinta harsun gaji ga Arman tayi ta kiranshi kashe Wayarshi tana kwance tana hawaye ga k'aramar wayarta dake hannunta taji tayi ringing cikin Sauri ta d'auka kuka ta fashe dashi ta ce "Yaya kai kadaine nakejin muryarshi a yanzu Naji sanyi a raina plx karkayi fushi dani wlh babu masaniyata " Daga bangaren Arman taji muryarshi ya ce "bana fushi dake Aira bantaba fushiba tashin hankalin da na shigane yasa ban waiwayi waya ba ki kwantar da hankalinki rabuwa ta dake abunda bazai yu bane kisa a ranki Auren nan babushi muddin ina numfashi alk'awarinmu bazai tafi a banza ba" Cikin kuka Aira tace "taya zan kwantar da hankalina yaya Bayan baka tare dani" kisa a ranki a ko ina ako wani hali ina tare dake my Aira ked'in jinin jikina ce taya za ayi na samu ganinki yanzu"Wlh yaya yanzu babu ta yanda zaka ganni Abba ya sanya mai gadi tsaro sosai babu ta yanda zan fito "Sosai Arman ya shiga damuwa cikin zuciyarshi Dan son kwantar da hankalinta ya ce " karki damu dole ne ki baro gidannan muddin munason cigaba da rayuwa kamar kowa Duk yanda zakiyi gobe kiyi ki gudo kina kub'utowa daga gidan ki fito da waya kiyi saurin Kirana "Goge hawayenta Aira tayi Dan tasan kaso ashirin na damuwarta ya ragu tunda Arman yana nan bazai bari Auren nan ya faru ba a tunaninta " To yaya zan kokarta na gani saurin kashe wayar tayi ganin Amma na nufowa k'ofar maza tayi ta boye wayar tare da kwanciya "Amma tace sis bazakije kici abinci ba " bazanciba ta fad'a tana juya mata baya.washegari ta kama laraba kuma ranar ne za a fara hidimar biki ba yanda ba ayi da Aira ba akan ayi mata lalle da saloon Amma fir tak'i su Ummy da sukazo ana musu lalle su sukace itama sai anyi mata taga zasu takura mata hauka tayi ta ce "Bazanyiba d'in nace Bazanyiba dole ne ku rabu dani mana wlh kuka Takuramun zanyiwa mutum abunda bai tunani ta fad'a tana girgiza kai " Allah baki hakuri Ummy ta fad'a Hafsa ce ta ce "kuma ku rabu da ita tunda bataso ai ba dole bane " tsaki Aira taja tare da komawa daki Ta dinga risgar kuka Aunty Maryam lokacin tazo da yaranta daga Lagos cewa tayi ina Airar akace mata tana daki tana sana'ar kukan d'akin ta nufa daman ita fad'a gareta nan ta hau Aira da fad'a ta ce "To saikiyi tayi hawan jini ya hauki kanki farau Auren dole Ni kaina ai ba Wanda nakeso aka auramunba kuma nayiwa Abba biyayya na zauna da mijina lafiya yanzu ba gashi munason junanmu ba harda zuri'a ke akanme bazakiyi hakuri ba baki da tawakkali kenan kuma Arman din da kika likewa ai gwara da Abba zai miki Auren Dan ubanki daman hak'e nake dake harkuje Kuyi birthday a idon duniya kuna Rungume_Rungume ke inkina da zuciya me zakiyi da Arman yaronda ubanshi ya tsaya takara da ubanki a gaban idonki wani irin wulakancin da cin mutunci ba ayiwa Abba ba dukda yana Dan uwanshi ya take shine ke Dan Rashin zuciya kika likewa d'anshi to ai yanzu ta k'are saikiyi hakuri ki tsaya a gyaraki ko kinje kiyi daraja gidan mijin naki"Aira ji tayi kamar ta shak'e Aunty Maryam tsaki taja da batasan tayi ba cikin kuka ta ce " Aike saurayine aka Aura miki Nifa sa'an ubana ne za a auramun ko kece ai nasan saikin damu Kuma yaya Arman da kike magana Nidashi mutu ka raba insha Allahu babu Wanda ya isa ya rabamu kuma ni shi nakeso sannan in kinga anyi Auren nan Saidai in baya numfashi ke daman Aunty Maryam ai nasan ba k'auna ta kike ba "Rik'e hab'a Aunty Maryam tayi ta ce " Eyye lallai Aira Tabbas na yarda yanda aka ban labarinki kin wuce nan Harni zaki d'aga baki kiyiwa Rashin kunya tare da tsaki to wlh ni ba Ummy da su Aysha bane sai in tsiinkeki da Mari ko inyi maki dukan tsiya "Aysha ce ta shigo ta ce " Haba Haba Aunty wai meye haka ki bartama da abunda ke damunta kinzo kin hauta da wani fad'an "ai daman ke da ita halinku d'aya" inji Aunty Maryam Rungume Aira Aysha tayi ta fara Lallashinta tacewa Aunty Maryam "eh munji mudai ki tashi ki tafi" Lallashi sosai Aysha ta shiga yiwa Aira harta samu tayi shiru wajen magriba Aira ta fito palour ganin kowa na harkar gabanshi masu salla nayi daga ita sai doguwar Riga da kallabin rigar hanyar fita tayi ba Wanda yayi mata magana Dan a tunaninsu alwala zatayo a tap din waje tana fitowa taga mai gadi na alwala hamdala tayi tare da basarwa taje tap ta fara alwala Tana ganin fitar Baba mai gadi tayi Sauri ta bar wajen Allah ya taimaketa farfajiyar gidan ba kowa a guje ta Ruga ta fice daga gidan gudu ta shigayi sosai kamar wacce aka biyo saida tayi nisa sosai tana hak'i ta kira Arman yana d'auka tace Yaya na gudo kayi Sauri ina daidai inda ka d'aukeni rannan kayi Sauri"Ai Arman na shirin shiga Salla fasawa yayi a sukwane ya d'auko mota ya nufi unguwar su Aira yana zuwa ya sameta a wajen sai waige waige take tana ganinshi aguje ta shige Motar Tana Shiga Arman ya ja motar a guje Dukansu Ajiyar zuciya kawai suke saukewa Kallonshi Aira tayi ta ce "Yanzu ina zamu yaya " shiru yayi itama shirun tayi Dan ta lura da yanayinshi sai huci yake a wani katafaran hotel yayi parking Bayan ya biya ya sai mata hijab tasa tare suka fito d'aki ya kama musu mai kyau da komai room45 itadai Aira Ajiyar zuciya kawai take tunda ta samu ta kub'utowa daga gida ai alhmdllh suna shiga d'akin ya Umartar Aira da tayi salla Shima anan sukayi Sallar har isha'i itadai Aira ta rakube kamar munafuka sai yanzu takejin tsoron idan gida aka nemeta aka rasa Danna belt din d'akin akai Arman ya lek'a ya amso plate din abinci d'aya gaban Aira ta Aje ya ce "oya ci" d'agowa tayi cikin hawaye ta ce "Yaya bazan iyaci ba" d'aure fuska yayi ya ce "ji yanda kika rame kamar bakeba d'aga bakin na baki" Arman shiya dinga bawa Aira abinci sosai kuma taci taji dad'inshi har saida ta k'oshi Kallonshi tayi ta ce "Yaya kai kaci mana kaimafa karkaga yanda ka rame" girgiza mata kai yayi ya ce "Bazan iyaciba " Ruwa Tasha a fridge din d'akin tare da zama bakin gadon ta cire hijab din jikinta Dan ta takura mata Kallonshi tayi tace "Yaya me yasa ka kawoni nan wani zai iya ganinmu yayi mana wata fassarar ko a zargemu daman gidan Mummy ka kaini" cike da yanayin b'acin rai Arman yace "Daman ai bamuyi ba suke zarginmu suke cewa munyi dukdai ba dalilin hakan bane yasa har zai miki Aure shiyasa na kawoki nan muyi abunda da bamuyi ba wlh bantaba sonki da wani Abu na jikinkikiba Aira Amma har Gobe kallon d'an iska mahaifinki yakemun why tunda nake bantab'a zina ba na tsaneta na tsani masu aikatata amma mahaifinki da laifin wannan yake dangantamu To Yau abun yazo karshe yau d'innan zan rabaki da virginity d'inki sai Inga ta yanda zasuyi miki Auren Tunda su basu tunanin halin da zamu shiga nan gaba ya k'arasa fad'a yana cire kayan jikinshi ya rage Dagashi sai singlet da gajeran wando sosai Aira ta tsorata da maganganun Arman sosai tashiga tashin hankali ja da baya ta fara tare da girgiza mai kai tana hawaye shiko tuni ya hayo gadon tare da chafketa yabi ya hau kanta ya danne sosai Aira ta shiga tashin hankali marar musaltuwa cikin hawaye ta ce " yaya karkamun hak.....bata k'arasa maganarba ya had'e bakinsu waje d'aya tare da Fara musu wata irin tsotsa kamar mayunwacin zaki a zafafe yake Aira ko tuni numfashinta taji ya fara d'aukewa fusfusgewa ta fara iya karfinta amma Arman ko motsi baiba daga kanta.................✍🏿 *NI DA YAYA ARMAN it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* *ki biya 200 d’inki kachal ki karanta cikin kwanciyar hankali da nutsuwa duk Mai buk’atar saya ya tuntub’e ni kan number wayata 07026166536* *_Miss Hajo ce_* [6/21, 19:23] Hajo hajo: 🅿️.........*55&56* ... .....Tashin hankalin da Aira ta shiga yafi Wanda ta shiga lokacin da Aka ce za ayi Auren ta da Alh yusuf Arman ko tuni ya fara fita daga hankalinshi Aira batasan lokacin da ta sume ba tsabar firgici Arman yad'au minti ashirin yana kissing d'inta jinta shiru ta daina hafre hafre ya dawo dashi cikin nutsuwarshi tashi yayi a matuk'ar firgice Rik'eta yayi yaga ta koma "Innalillahi meyake shirin faruwa da nine me nake shirin aikatawa " Arman ya fad'a yana kallon jikinshi cikin Sauri ya mayar da manyan kayan jikinshi tare da dauko ruwa a fridge a d'imauce ya shiga watsa mata Ajiyar zuciya yaji ta sauke Shima Ajiyar zuciyar ya sauke Aira na bud'e idonta Maganganun Arman da abunda ya mata suka shiga dawo mata tashi tayi a matuk'ar firgice tare da rugawa tayi hanyar fita girgiza k'ofar ta farayi taji a kulle Kuka kawai take Arman ko binta yayi ya ce 'please cutie ki saurareni"d'aga mishi hannu tayi ta ce "Babu abunda zaka Cemun yaya ka cuceni ka zalince ni banyi tunanin zaka yimun hakaba kaikad'aine na yarda dashi na bashi amana ashe kaimad'in zaka iya cin amana ta yaya me nayi maka tukuicin soyayyar da nake maka da haka zaka sakamun ashe Ta k'arasa fad'a tana durk'ushewa a wajen tare da sakin kukan takaici girgiza mata kai Arman ya fara tuni idanunshi sun chuko da k'walla duk'ursawa yayi gabanta ya ce " Kiyi Hakuri ki yafemun cutie shed'an ne yaso yayi galaba a kaina nayi tunanin wannan ce kurin mafitarmu ta k'arshe saida nadawo hayyacina na gane ba haka bane Dan Allah kiyi hakuri nasan ni mai laifi ne a gareki amma kiyi hakuri ki yafemun please "Cikin kuka da jaraba Aira ta ce " shed'an ko son zuciya Yaya kaban mamaki nayi tunanin kai mai tsareni da tsare mutunci na ne a ko ina amma da kanka zaka lalatamun rayuwa nayi danasanin biye maka da nayi yaya ka bud'e mun k'ofa na fita tunda burinka ya cika ka rabani da mutunci na ka bud'e mun nace "Wlh tallahi babu abunda nayi miki cutie na rantse da girman Allah banyi maki komai ba kiyi hakuri mu fahimci Juna ya fad'a yana ruko hannunta ta fusge hannun tayi ta ce " karka sake tab’ani ka bud'emun kofa nace ba abunda zaka Cemun na tsaneka na tsaneka yaya bansan ganinka I hate you "ta fad'a tana rumtse ido " Ai Arman jin Kalmar yayi kamar an d'iga mishi Darmar wuta "na tsaneka Na tsaneka" Ai baisan lokacin da ya fashe da wani matsanancin kuka ba da tunda uwar da ta haifai bai tab'ayi irinshi ba ita kanta Aira sosai Cike da mamaki take Kallonshi shiru tayi tana sauraren kukan shi sosai Arman yake kuka kamar Wanda aka cewa uwarshi ta mutu Mik'ewa yayi tare da d'auko wuk'a zai chakawa kanshi Aira ta maza a matuk'ar rud'e ta rikeshi tare da rik'e wukar ta ce "Meye haka yaya kashe kanka kake shirin yi kana hauka ne? cikin b'acin rai ya ce "ki saki ki rabu dani na kashe kaina rayuwata bata da amfani Aira tunda kema baki sona bani da wani amfani a duniya ki bari na mutu itace kawai tafi chanchanta dani meyasa bazaki fahimceniba Aira Duka abunda nayi na yine a saboda son da nake maki wlh banyi da wata manufa ba Kuma nayi nadamar abunda nayi shirinyi Meyasa bazaki fahimceniba kince baki sona kin tsaneni Aira bakin da ya furta mun so yau shine ya furtamun kalmar k'i da kanki yau Kika furtamun Kalmar tsana" kuka Aira ta fashe dashi ta ce "I love you yaya bazan tab'a daina sonka ba Ina sonka har yau har Gobe har jibi har abadan abada bazan tab'a iya daina sonka ba"Ai Arman baisan sanda wuk'ar ta sulale a hannunshi ba Ganin haka ya sanya Aira fad'awa jikinshi tare da fashewa da kuka ta ce "please yaya karka k'ara attempting kashe kanka Nima mutuwar zanyi ka daina banso ina sonka sosai yaya Amma me yasa zakace saita haka ne kawai mafita akwai mafita da yawa zamu iya guduwa muje a d'aura mana Aure a wani wajen " Daddab'a bayanta Arman ya fara ya ce "Kainane ya kulle Aira Bansan wani irin so ne nake maki ba har shed'an yaso galaba a kaina kiyi hakuri ki yafemun na mance da wannan mafitar ta mu gudu I love you so much Aira please karki gujeni duk rintsi duk wuya " Lafewa jikinshi Aira tana sauke ajiyar zuciya Dan sai yanzu ta fara dawowa daidai sosai Arman ya tsoratata a hankali ta ce "Nima karka gujeni duk rintsi mu rik'e alk'awarin juna yaya da gaske Bakayimun komai ba " Gani kawai tayi ya tashi tare da d'auko Quran hizif sittin dake gefen Gado ya rik'e ya ce "na rantse da Quran d'innan Mai girma babu abunda nayi maki" Saurin tashi Aira tayi tare da amshe Quran din ta ce "Ni bance ka Rantsemun ba na yarda " Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "kin hakura kenan" gyad'a mashi kai tayi tana zumburo baki"Murmushi yayi ya ce "Thnks you my cutie zaunawa Aira tayi tare da Yin tagumi" sai nakega kamar har yanzu baki hakura ba cutie please Dan Allah kiyi hakuri"murmushi ta kirkira ta ce "Na hakura yaya kawai tunanin mafitar da zamu samu nan gaba nake" Ajiyar zuciya ya sauke tare da zaunawa gefenta ya ce "mafita ta k'arshe itace kawai gobe muyi safko mu gudu" Kallonshi tayi ta ce "ba matsala kuma yaya" Ba wata matsala insha Allahu ita ce kawai damarmu ta k'arshe Ko zaki yarda Kinaji kina gani a aura miki wani banzan tsoho"girgiza kai Aira tayi tana hawaye ta ce "Alllah ya kaimu goben Yaya Amma please mu raba d'aki " murmushi yayi ya ce "to Prince's Angama ina zuwa " yana fita Aira ta sauke ajiyar zuciya tana hamdalar da Arman bai mata komai ba baijima ba ya dawo yace na kama wani d'akin ke ki kwanta anan kinji kiyi bacci sosai Dan Allah "murmushi tayi ta ce " Insha Allahu Yaya kaima kayi bacci"Murmushi yayi cike da so da k'auna ya ce "Good night" Arman tunda ya shiga d'akin inbanda salla ba abunda yake Airako bacci bai d'auketa ba sai wajen biyu da asuba tana tashi tayi sallah ta koma bacci saboda tsananin ciwo da kanta ke mata Arman ko Shima saida yayi Sallar asuba bacci ya daukeshi Bayan ya leko Aira yaga itama baccin take bacci mai mugun nauyi Duka ya d'aukesu kamar Wanda suka sha wani Abu saboda sunjima daman basu samu bacci ba. B'angaren gidan su Aira sosai suka shiga tashin hankali da suka lura ta gudu musamman Mamy Daman tasan hakan zai faru sosai Tasha kuka a d'aki Mama Halima ko cikin tashin hankali taje ta samu Abba ta fad'a mashi Aira fa ta gudu a lokacin goman dare sosai ran Abba ya b'aci cike da mamaki ya ce "What Guduwa garinyaya ta gudu Bayan nasa matakan tsaro a kanta aikinme me gadin yake " To wlh yaya ta gudu batanan "cikin b'acin rai Abba ya fito wajen mai gadi ya nufa ya dinga surfamai masifa akan garinya ya barta ta fita da rantsuwarshi Baba mai gadi yace "wlh nidai banga fitar ta ba Saidai idan lokacin da naje salla ta gudu Dan daman na hangota a pampo tana alwala bankawo komai a kaina ba saboda naga alwallace take shiyasama harna fita amma wlh banga fitartaba Alhaji kamun rai karka koreni a aikin nan dashi kawai na dogara " Cikin b'acin rai Abba ya nufi parking space ya d'auko mota ganin haka ya sanya Baba mai gadi rugawa yaje ya bud'e mai Abba kai tsaye police station ya nufa ya basu mak'udan kud'i akan duk Inda Aira take Su shiga su nemota tare da tura musu hotonta a wayarshi Tun Daren y'an sanda suka fara fafutukar nemanta duk sun turawa abokan aikinsu hotunanta akan duk Inda suka ganta su sanar Abba ko ranar Kad'an Ya hana jininshi ya hau sosai Aira ta k'ara chusamai bak'inciki Daren Ranar cikin gidansu Babu Wanda ya rintsa Musamman Mamy tsoronta kawai karta fad'a mugun hannu Bayan Sallar asuba Mama Halima da yake daki daya suka kwana da mamy wani tunani ne ya fad'o mata Mummyn Arman ta kira Bayan sun gaisa ta ce "Dan Allah Arman ya kwana gida kuwa" Sai sannan hankalin Mummy ya kawo ta ce "a a bai kwana gida ba rabo na dashi tun shekaranjiya lafiya kuwa Halima" da sauki dai za ace Aira ce ta gudu tun jiya da dare nasan duk Inda take suna Tare da Arman Dan Allah kid'an bincika mana nayita kiranshi Wayarshi kashe "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Mummy ta fad'a tace " Amma banji dadiba Gaskiya irin haka nake gujewa yasa tun farko naso abar yaran nan su Auri junansu tunda suna so Amma taurin hali na iyayensu sun kafe bari nayi Sauri na tura guest house d'inshi dake gra duk sanda bai gida to yana Chan nasan kila suna Chan"Wlhko Aunty kinga mamanta nan ma duk hankali tashe itama Ba irin gwagwarmayar da bata sha ba akan abun nan yafi karfinta"Ajiyar zuciya Mummy ta sauke ta ce "Allah shige mana gaba bani Rahamar mu gaisa" mik'awa mamy wayar tayi ta amsa Bayan sun gaisa da Mummy suka jajintawa juna abunda ya faru Mummy ta ce "To Allah ya kawo mafita bari na maza na tura can din zakujini " Ameen nagode "Mamy ta fad'a ba ayi minti Talatin ba Mummy ta kirasu hankali tashe ta ce " Wlh na sanya Duka anbincike cikin Chan din basanan mai gadin yace rabonshi da gidan tun Jiya da magriba "Mama Halima ta ce " ba kokontoma suna tare daidai lokacin ta gudu itama "Sosai Mummy suka shiga damuwa shawara mummy ta bada akan a sanya jami'an tsaro suje hotel_hotel d'in garin nan da kuma y’an sandan bakin hanya kila a dace Tsoronsu Kardai Aje guduwa sukayi hankali tashe Mama Halima taje ta fad'awa Abba tace Suna tare da Arman A sanya jami'an tsaro su tsaya bakin duk hotel d'in garin nan shi daman Abba baiyi mamaki ba Daman Chan yasan shi zaisa ta gudu cikin k'ank'anin lokaci Abba ya kira jami'an tsaro aiko ba b'ata lokaci Duka suka bazu duk hotel d'in da suka sani sannan Abba ya sa Mama Halima ta tura musu hoton Arman. Aira itace bata tashi ba sai karfe d'aya na rana sosai taji ta wartsake bayan tayi wanka Salla tayi kayan jikinta ta mayar zaunawa tayi bakin Gado tayi tagumi Ta na zaune taji shigowar Arman da harta tsorata tana ganin shine Ajiyar zuciya ta sauke a hankali ta ce " ina yini Yaya "Murmushi yayi ya ce " Alhmdllh cutie yau munsha bacci ko"murmushi tayi ta ce "Wlhko banzaci munkai haka ba" Ai nima banjima da tashi ba bari naje na Samo maki kayan da zaki sauya kafin mu tafi na so ace sauko mukayi "rik'e hannunshi tayi ta ce " Yaya zan mayar da na jikina plx kawai mu tafi banson a samu matsala nasan duk Inda y'an gidanmu suke nemana ake "a a ki bari na samo maki wasu kayan cutie babu wata matsalar da za a samu tunda kina nan ba tare zamu ba Kuma ma mota ta tinted ce bamai ganinmu daga Chan saina taho maki da abinci nasan yunwa kikeji ba Dan Aira ta so ba ta bar Arman ya tafi Arman yana fitowa daga farfajiyar hotel d'in kai tsaye motarshi ya nufa ya tada Y'an sanda ko suna ganinshi suka ganeshi Dan tunda aka turo musu hoton daman sunsanshi d'an Excellency ne Abba suka kira sukace " ranka ya dad'e munyi nasarar ganin shi Mujahid d'in yanzu a harabar Grand central hotel amma shi kad'ai muka gani yanzu haka ya tada mota ya bar hotel din amma ga alamu kamar bazaiyi nisa ba "" Abba tashi yayi daga zaunen da yake ya ce "Karku saki ya gudu Kuyi yanda kukayi kuka tsayar dashi suna Tare da ita Tabbas gani nan zuwa " to ranka ya dad'e kayi Sauri Dan Gaskiya bamu da power Kamashi D'an governor guda zamu iya ta aikinmu amma kai kazo "Suna cikin wayar suka ga dawowar Arman " ranka ya dad'e gama shinan ya dawo ka yo Sauri"Cikin hanzari Abba ya d'auko mota Dan zuwa Inda suke ya ce "kusan duk yanda zakuyi ku tsaidasu Karku bari su gudu kafin nazo" Angama y'an sanda suka Fad'a suna ganin Arman ya fito daga motar ya shiga ciki suka maza sukaje sukasa k'usa suka sace tayar motar Arman ko baisan wainar da ake toyawa ba yana shiga ciki ya samu Aira Inda ya barta "Sorry dia ya fad'a yana zama " murmushi tayi ta ce "Amma kayi Sauri yaya " murmushi yayi tare da fito da wata had'ad'd'iyar zoben gold ya matuk'ar tsada mai shegen kyau kama hannun Aira yayi tare da saka mata zoben yace ga zoben alk'awari murmushi Aira tayi tare da fito da zoben dake hannunta azurfartace tun tana Yarinya take jikinta dak'yal ta cirota itama k'aramar yatsar hannunshi ta kama tare da saka mashi tace "nima ga tawa ta alk'awarin" murmushi suka sakarwa juna tare Sosai Aira taci abinci saboda yanzu Hankalinta ya d'an fara kwanciya Arman Shima ya samu yaci Waje ya bata ya ce ta sauya kayan yana fita Aira cikin Sauri ta cire na jiya ta sanya doguwar rigar d'aya kawo mata bak'a tana gama sawa ta d'ora hijab d'inta pink ta jiya yana shigowa kallonta yayi yace"Koda yaushe Kyanki karuwa yake cutie "murmushi tayi ta ce " kamar kai kenan"A nan suka bar kayanta na jiya hannunsu mak'ale Dana juna suka fito Bayan Yaje ya saki d'akunan da suka kama Aira tunda suka fito kanta yake a k'asa saboda ganin yanda ake kallonsu ga kuma gabanta dake fad'uwa Suna isa Inda Arman yayi parking sosai yayi mamakin Ganin tayoyinshi Duka a sace cike da mamaki yace "yanzu fa lafiya qalau na bar motar nan cutie " Cike da tsoro Aira tace "ko wasu suka sacemaka su Yaya nidai tsoro nakeji muyi Sauri mubar wajen nan Tab'i suka jiyo daga bayansu raf RAF Raf saurin Juyawa sukayi a tare Wara idanu Aira tayi cike da firgice ganin...........✍🏿 *Ni da yaya Arman it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* *_Miss Hajo ce_* [6/23, 10:04] Hajo hajo: 🅿️........*57&58* ......Wara idanu Aira tayi cike da firgice ganin Abba tsaye bayansu yana tab'i tare da jami'an tsaro Sosai ta firgita ba itaba hatta Arman saida ya tsorata Rugawa Bayan Arman Zatayi Abba yayi Saurin Fard'o hannunta Tare da d'auketa da gigitaccen mari rumtse ido Arman yayi ji yayi kamarshi Aka Mara cike da b'acin rai Abba ya k'ara wanketa da wani Marin Wanda yafi na d'azu durk'ushewa a wajen tayi tare da fashewa da kuka Kamar Wanda aka tsunkula haka ARMAN ya zabura tare da Fard'o Aira ya boyeta bayanshi idanunshi harsun fara sauya launi tsabar masifa cike da b'acin rai Abba ya ce "Kai harka isa ina yiwa y'ata hukunci ka boyeta Dan ban waiwayo kankaba "cike da b'acin rai Arman yace " na b'oye ta d'in wannan ai zalinci ne Idan ka daketa a Bayan idona wannan ban ganiba amma gaban ido na baka isa ka daketa na zuba ido ina kallo ba "cike da b'acin rai Abba yace " Tabbas ka haifu kome kamun bazanji ciwo ba saboda baka da tarbiya bacin b'atawa y'ata tarbiya da kayi shine har zaka nuna mata hanyar da zaku gudu to Allah ya Toni asirinku y'an iskan banza y'an iskan hofi sannan ya nuna Aira dake mak'ale a bayan Arman ba abunda take inba kuka ba ya ce "Ke kuma zaki gani zakisan ja da iyaye ba Abu bane me kyau y'an sandan ya juya yace " ku kama mun ita "Daya daga cikinsu yazo Zai kama Aira dake Bayan Arman wani irin bak'inciki da ya tunkarowa Arman Ai baisan sanda ya d'aukeshi da Mari ba cike da masifa ya ce " zanga ubanda ya isa ya D'auketa wlh duk Wanda ya k'ara attempting tab'ata zaku San asalin waye ni stupid kawai mararsa Aikinyi"Sosai y'an sandan sukayi luk'ui ba Wanda ya k'ara yunkurin tab'ata cike da b'acin rai Abba ya nunashi da yatsa ya ce "Harni ubanta?Harkai d'in Arman ya fad'a cikin k'unar rai" D'aukeshi Da mari Abba yayi Dagowa Arman yayi tare da rik'e kumcinshi yace "Ni ka Mara?An mareka d'in marar mutunci ko ramawa zakayi" Suka tsinkayi Muryar Mummy"duk kallonta sukayi musamman Arman dake mamakin me ya kawota wajen nan "Abba ko sosai ranshi ya b'aci cike da b'acin rai Mummy ta ce " ka basu y'arsu Arman kafin ka fuskanci fushina"Mummy Auren dole fa yake shirin yi mata mutumin nan baida tausayi ki barmu Mummy babu ruwanku munason junanmu koma ina zamu babu ruwanku"cike da b'acin rai Mummy ta ce "Arman Yayan mahaifin naka kake fad'awa haka?Shima Arman d'in cikin b'acin rai ya ce " shi Mummy baisan da hakan ba baisan da wannan alak'arba abunda yakemun ko Wanda bamu had'a komai dashi ba bazaiyi ba me yasa bazaku ganeba Mummy munason junanmu amma mutumin nan ya tsaneni baku tunanin irin halin da zamu shiga rabamu ba alkhairi bane"Cikin b'acin rai Mummy ta ce "nace ka basu y'arsu kai wani irin mutum ne y'ar ko ta gwal ce baka hak'ura da ita ba na fad'a maka ka rabu da ita me yasa baka da zuciya Arman " Kallon Mummy Aira tayi cikin kuka ta ce "Mummy please karkice haka Allah inasonshi Karku rabamu" Hawaye ne suka zubowa Mummy tamaza ta Goge ta ce "Kiyi hakuri Kibi umarnin mahaifinki zakifi ganin da kyau Aira ku hakura Da juna sannan ta dakawa Arman Tsawa ta ce " bazaka saketa ba baka ganin hankalin mutane duk yana Kanmu ko so kake sai mutane sun fara daukarmu "Cikin b'acin rai Arman ya saki Aira tare da kama hannunta ya wullata wurin Abba ya ce " ga y'ar taka nan idan ka tashi ka kasheta Sannan baka burgeba idan baka Aura mata Duka mazan duniyar nan ba"Rik'e hannunshi Aira tayi tana kuka Ya fisge hannunshi tare da barin wajen kamar zai tashi sama cikin Sauri Mummy ta bishi Dan tasan halinshi idan yana cikin wannan halin kome zai iyayi ruk'oshi tayi dak'yal ta samu ya shiga motar da sukazo da ita tare da escort d'inta Suka bar wajen Aira ko cikin b'acin Rai Abba Shima ya kama hannunta Tare da wullata cikin mota ya zagaya ya shiga ya tada motar Mutane harsun fara taruwa wajen danma y'an sanda sun rufe ba kowa ya fahimci abunda ake ba Aira harsuka isa gida tana kuka kamar ranta zai fita suna isa Zagayowa Abba yayi tare da Fiddota ya wullota nan ya hau ball da ita tsakar gida cikin b'acin rai masifa kawai yake ya ce "kin nunamun ban isa dake ba ,ni zaki wulakanta a idon duniya Kibi namiji hotel ku shirya guduwa Y'ar iska wulak'antatta marar mutunci biye biyen maza ne kika fara hotel hotel koshi D’an iskan naki nafi karfinshi bare ke " Sosai Aira ke kuka y'an ciki ne duk suka fito Jin hayaniyar Abba da kukan Aira dak'yal manya suka kwaci Aira daga hannun Abba ba k'aramun Duka yayi mata ba Mummy ko ko lek'owa batayi ba tana ciki ta na kuka Yayyinta da d’iyan yayyinta da suka zo daga agadez su suka dinga Lallashinta akan tayi hakuri ta fawwalawa Allah komai Aira ko Bayan ankwaceta d'akinta Mama a kayi da ita ba abunda take In banda kuka tana cewa "Dan Allah ku barshi ya kasheni wlh bana k'aunar rayuwar nan mutuwa ta kawai nake buk'ata Duk Wanda yaganta saiyayi mata kuka Cikin kuka Aysha taje ta duk'ursa gaban Abba tace " Dan Allah Abba kayi hakuri ka janye Auren nan wlh Aira na cikin wani hali"D'auketa da Mari Abba yayi ya ce "kika Kara zomun da makamanciyar maganar nan sainayi miki lilis bar ganin kinyi aure cikin y'ay'ana babu Wanda yafi k'arfina" Cikin kuka Aysha ta koma ciki rik'e da kumcinta da tasha Mari wajen Aira ta nufa ta Rungumeta Itama ta fashe da kuka cikinsu bamai Lallashin wani itama amma rungumesu tayi tana kuka Dak'yal aka samu suma wata yayar Mamy ta rabasu Ta dinga basu hakuri a ranar za ayi walima walimar da ba ayita ba kenan Dan gidan ya koma kamar gidan makoki wajen isha'i Abba ya shigo ya cewa Aunty Maryam a palour maza na baki minti goma kije ki amsomun wayar da suke communication dashi idan ta Bari kuma naje na amsa da kaina tasan sauran" "To Abba" Aunty Maryam na zuwa tace "Aira ki kawo wayarki idan akwaita a kaiwa Abba yace ya shigo ranki zai b'aci " cikin kuka Aira tace tana d'akinmu cikin kayana dukansu ki kaimai"ta k'arasa fad'a tana kuka"Aunty Maryam na zuwa Inda Aira ta fad'a mata nan ta samu wayoyin tana zuwa a palour tace "ga su Abba" Kallon wayoyin Abba yayi tare da amsa ya kalli Mamy ya ce "kalli wayoyin da take rikewa a boye ke da kike d'aure mata dukanku harke zanyi maganinku" Sannan ya tarwatse wayoyin sukayi ratsa ratsa "Mummy ko tsaki taja batare da tayi magana ba abun duniya duk ya ishi Mamy Abba na fita ta tashi ta dauki mayafinta tare da ficewa ta dauki mota kai tsaye gidan Yayanta Wanda ya rik'eta ta nufa tana kuka ta ce "Dan Allah Yaya kaje ka samu Alhaji ka mashi magana kila kai yaji maganarka Dan Allah kar a d'aura Auren nan " Yayanta Alhaji Safiyanu dattijone Shima Dan zai wuce sa annin su Abba ba kamarsu daya da mamy shima dukda ya fara manyanta ya ce "Gaskiya zan fad'a maki Rahama kiyi hakuri mijinki ya dau zafi baki saniba ni kaina na sameshi munyi magana dashi ta fahimta Duka ya fad'amun abubuwan da take da kuma dalilinshi na Aurar da ita a Gaskiya ko nine iya hukuncin da zan yanke mata kenan Aurar da ita y'arki batajin magana Rahama Duka abubuwan da tayi bana kyalewa bane kawai dai Auren tsohon ne ba dad'i amma tunda shi mahaifinta ya yanke hukuncin da ya yanke me zaisa bazaku hakura ba Kuyi mashi biyayya tunda dai shine mahaifinta ku mata kuna da matsala wlh ku kuke d'aurewa y'ay'anku gindi suke lalacewa sai abu yazo yafi k'arfinku kuzo kuna kuka da idanunku kuna sharrin shed'anne bayan y'ay'annakune shaid'anun kuzo ana lik'awa k'addara tabbas akwai k'addara amma kaddara tana tarda hali Allah yace tashi in taimakeka ko saikije ki aje kud'inki a kasuwa ki tafi ki barsu kice Allah zai tsare to kamar hakane ku da kanku ya dace ku dinga tsawatarwa y'ay'anku idan sunyi ba daidai ba yana da kyau y'ay'anku ya kasance suna shakkarku to nidai indai na isa dake karki k'ara daga maganar nan ki sanyawa Auren nan Albarka kawai kinji abunda na fad'a maki" cikin kuka ta ce "Yaya ni ban d'aurewa y'ata gindi ba maganar gaskiya ce yaya tana da wanda takeso suna san junansu kuma d'an uwanta ne yaya kasan komai fa yanzu haka fa yau inbanda Allah ya taimaka dafa sun gudu wani hali kake tunanin zasu jefa kansu da ace sun gudu d'in" d'aga mata hannu yayi ya ce "duka nasan komai Ya fad'amun ba a hotel aka gansu ba ni kaina na so ace d’in wanda take so d’in aka bata amma tunda mahaifinta yace bayason alak'arta dashi me yasa bazasu hakuraba tayiwa mahaifinta biyayya kika sani kila sanadin biyayyar da tayi mashi Allah ya daidaita tsakaninshi da d'an uwanshi ko kuma ya sanya ya hakura kinsan dai ba ayiwa iyaye biyayya a tab'e Bansan ki k'aramun maganar komai Rahama y'arki bata da gaskiya abubuwan da take ba daidai bane ga al'adar mu mu hausawa harma a musulunce dan haka Aure shi yafi dacewa da ita Tsohonma idan yaro ya gagareka wanda ya fishima saika Auramai da dai d'a ya daukomun magana hukuncin mahaifinta yayimun daidai kawai inda bai Kyauta ba da baya bin komai a hankali fushi ne kawai matsalarshi ‘’Goge hawayenta Mamy tayi tare da tashi Ta ce " saida safe yaya " Kinji Haushi na dan na fad'a maki Gaskiya ko Rahama"girgiza kai tayi ta ce "a a yaya zantafi ne nabar bak'i "girgiza kai yayi ya ce" sannan itama Hajarar ki yi mata nasiha kinji gobe idan an d'aura Auren zanshigo na ganta"To"tafada tare da saurin ficewa daga palour duk Haushi ya kamata yayannata ma da take tunanin zai huce mata takaici shima ga abunda yake fad'a Cike da takaici Mamy ta koma gida sannan kuma tana nazarin maganganun Yayan nata. Arman har suka isa gida jin zuciyarshi yake kamar zata rabe gida biyu dak'yal Mummy ta samu ya shiga gida cikinsu babu Wanda ya kuma yiwa magana Ranar kamar wani zararre haka ya koma ba um ba um um ga wani zazzabi da ya rufeshi lokaci guda Sosai Mummy ta shiga tashin hankali Kwantar dashi tayi a d'akinshi lallashi da nasiha ba irin Wanda Mummy batayi ba Amma a banza ko tanka mata baiba wajen karfe goman dare ganin har yanzu Arman yaki magana ya sanya Mummy fashewa da kuka ta ce "ya kakeso nayi Arman karka sanya rayuwarka cikin wani hali please kaikad'ai nake dashi " Shima fashewa da kuka yayi tare da Rungume Mummy ya ce "Shikenan Mummy yanzu ya rabamu Mummy me yasa kikaje wajen me yasa zakice na bar mashi ita su tafi Mummy why ina sonta sosai itad'in rayuwata ce Mummy ko kema kin daina sona kamar Daddy duk Wanda ya rabani da Aira mak'iyina ne Mummy na tsani Abbanta bana kaunarshi ya rabamu.....ya k'arasa fad'a yana rushewa da matsanancin kuka Itama mummyn kuka take ta ce " ka nutsu son ina sonka sosai kawai Inajin takaicin irin wulakancin da ake makane a sabo da ita shiyasanya nace ka rabu da ita nafi kowa sonka tare da ita Arman Amma tunda mahaifinta bayaso ka hakura da ita shi yafi Allah zai musanyama da wacce ta fita Alkhairi a lokacin da naje wani D’an sanda ne ya kirani yace nazo ba lafiya shiyasama harka ganni “Mummy babu wacce tafi Aira a duniyar nan ki daina fad'ar haka ni ita kadai nakeso kuma ita kadai zan iya rayuwa da ita Mummy mutuwa zanyi ya k'arasa fad'a yana rushewa da kuka Mummy Lallashinshi sosai Mummy ta shigayi amma ya dinga mata sabbatu Daddynshi ta kira ta fad'a mashi halin da ake ciki tsaki yaja yace "ki rabu dashi indai akan mace ne yake wannan haukan ni kaina mahaifinka bazan tab'a yarda ka aureta ba baka isa ka aurarmun jinin Rahama ba duk na kyale kane ka gama haukan naka kuma yayimun daidai da ya rabaku kuma zai mata Aure Kamar yanda mahaifinta ya isa da ita zai mata Aure to haka nima indai na isa dakai Bazaka k'ara sati biyu ba batare da na maka Aure ba " yana gama fad'ar haka Daddy yayi waje Arman sosai ya k'ara burkicewa Mummy ya zame mata kamar wani Mahaukaci dak'yal ta samu ta kira family doctor d'insu yayi mishi allurar bacci Saida bacci ya daukeshi hankalin Mummy ya d'an kwanta gefenshi ta zauna tana hawaye tayi tagumi sosai ta tausaya halin da tilon d'an nata yake ciki. Daren ranar Aira bata rintsa ba kwana Tai tana kuka tana jin daman mutuwa tayi ta huta washegari koda ta tashi batayiwa kowa magana ba ko kukan ta daina Dan tuni ta sik'e duk yanda akayi da ita tayi magana takiyi kowa yazo Saidai tayi mishi banza wajen k'arfe Goma da wani Abu yayar mamanta Fadila ta shigo Tare da farfesun Kaza a plate da tasha had'i zaunawa tayi tare da Kallon Aira ta ce "maza maza y'ata ki cinye wannan kinji Wai Yama za ayi Ace Amarya ba gyara ba dilka ba komai har yau d'aurin Aure Amshi ki cinye wannan muje na had'o maki ruwan wanka " Wani irin banzan kallo Aira ta wulla mata Tare da Amsar Farfesun ta watsa mata shi a jiki dukanshi ga zafi"Fadila saida tayi ihu Dan sosai zafin ya shigeta cikin tashin hankali ta mik'e tana yarfe hannu Tace "Aira ni zaki k'ona koma nace kika k'ona tsaki Aira taja tare da tashi tayi hanyar waje Aunty Maryam ce dake d'akin tace " waike Baki da Hankali yayar mahaifiyartaki zaki yiwa wannan wulakancin"itama harara Aira ta galla mata tare da Jan tsaki tabar d'akin Fadila koda ta koma sosai yayyun Mamy suka shiga yi mata Dariya Aunty ramlat tace "daman wa ya kaiki in banda kinibibi irin naki" Dariya Mama Halima tayi ta ce"Ai saida nace ki rabu da ita wannan kiyi waje kawai ki ajeta Muma ido muka zuba mata Aira tana barin d'akin daman dakin Mama ne Chan ta kwana Dakinsu ta koma Tare da buga uban tagumi K'arfe d'aya da wani Abu aka d'aura Auren Hajara Abubakar tare da Angonta Alhaji Yusuf Madugu sokoto Wanda ya samu halartar manya_manyan mutane Dan Alh Yusuf Shima ba k'aramun attajiri bane haka Abba a masallacin Juma a aka D'aura Auren Arman na kwance Bayan ya tashi lokaci guda harya rame Mummy ta sanya mishi pillow a bayanshi tana bashi tea a baki Wanda dak'yal ta samu yakesha saida tayi kuka ta samu ya fara sha a plasma din dake manne a d'akinshi tashar da suke kallo suka ga An nuno D'aurin Auren Inda d'an jaridar yake cewa "Alhmdllh a yaune Ranar Juma a aka d'aura Auren Alhaji Yusuf Madugu Shahararren d'an kasuwar nan tare da Amaryarshi Hajara y'a ga Former Senate Alhaji Abubakar Umar.......ai Arman bai k'arasa jin sauran maganganun ba ya nemi numfashinshi ya rasa Mummy na bashi tea taji ya fara tari da wani irin Abu kuka ta fashe dashi tace " na shiga ukku me zan gani haka Arman "Kafin ta k'arasa maganar sai gani tayi jini yana fito mai ta hanci ta baki wani uban k'ara Mummy ta saki tare da rugawa tayi waje cikin tashin hankali ma aikatan gidan suka taryeta tare da Daddy da ya shigo ta kasa magana sai d'akin da Arman yake take nuna musu Cikin kid'imewa Daddy suka nufi d'akin sosai suka shiga tashin hankali ganin halin da Arman ke ciki gudajen jini kawai ke fitomai shi kanshi Daddy cikin rud'u dukda nauyin Arman haka ya sungumeshi cike da tashin hankali Mummy Da Abba sukayi waje Driver Ya fiddo mota tare da Security Aka nufi Asibitin Dr Aminu kano dashi Aira na kwance Wajen karfe biyu zuciyarta banda Bugawa babu abunda take ita kadaice a dakin Haidar ya shigo da shirinshi hada babbar Riga ya ce " ya Aira har an d'aura aurenki yanzu ma daga wajen d'aurin Auren muke kamar wacce aka zabura haka ta mik'e ta ce "whattttt ?ja baya Haidar yayi Dan sosai ya tsorata ganin yanda ta mik'e a zabure a matuk'ar tsawace ta ce " get out fita ka bani waje"Cikin sauri Haidar ya fice Dan sosai ya tsorata yanda tayi maganar saikace mai iska yana fita Aira ta mik'e tare da d'ora hannu aka ta ce "Shikenan na shiga ukku " sai kuma ta sauke hannunta Tare da Saukowa daga gadon dube duben fiya_fiyarsu da suke ajewa saboda kashe k'wari ta fara duk ta barbaza kayan d'akin Chan ta hangota k'ark'ashin Gado cikin Sauri ta d'auko tare da bud'e kwalbar ta kafa a bakinta Saida ta kusa Shanye Rabin kwalbar Haidar yana fita da gudu ya ruga d'akin Mamy yace Mamy ki taho kije kiga ya Aira kamar mai iska Da gudu Mama Halima da Mamy Tare da sauran mutanen dake d'akin suka fito a guje sukayi d'akin nata Mamy da Mama Halima suka fara shiga suna shiga suka sameta yashe a k'asa kumfa na fitowa daga bakinta A guje Mamy tayi kanta tare da fasa ihu tace "na shiga ukku Aira meye haka ki tashi karki mutu" Saurin duba kwalbar dake hannunta su Mamy sukayi Mama Halima cikin tashin hankali ta kwankwale kwalbar a hannunta dubawa tayi ta shinshina taga fiya fiya ce Salati tayi ta ce "Munshiga Ukku Ta kashe kanta fiya fiyace Tasha ku duba kwalba guda Kad'an ta rage warce kwalbar Mamy tayi cikin tashin hankali ta duba sakin kwalbar tayi tare da girgiza Aira kuka kawai take tace " Shikenan Alhaji hankalinshi ya kwanta ya kashe mun y'a ya ja ta kashe kanta ta mutuu"ta k'arasa fad'a tare da Rungume Aira da kumfa ke fita daga bakinta ta fashe da kuka Mama Halima ce cikin kid'imewa taje ta fiddo mota Dan Abba har lokacin suna wajen d'aurin Aure Mama ko cikin tashin hankali ta amshe Aira dake hannun Mummy ta sungumeta sukayi waje "ina zaku kaita kuma ku barmun ita tunda ta mutu hankalinshi ya kwanta ya kashemun y'a Mummy ta fad'a tare da bin Bayan su Mama Rikota yayarta Ramlat tayi ta ce " kiyi hakuri Asibiti za akaita a tabbatar da in mutuwarce tayi"Basuyi Aune ba sai ganin Mamy sukayi ta sulale a wajen summammiya Aira ko cikin tashin hankali Mama ta sanyata mota Ta shiga ta rik'eta Mama Halima tayiwa motar key kai tsaye asibitin doctor Aminu kano suka nufa da ita.........✍🏿 *NI DA YAYA ARMAN it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/23, 15:58] Hajo hajo: 🅿️..........*59&60* ......Kai tsaye asibitin doctor aminu kano suka nufa da ita suna isa emergency aka nufa da ita cikin k'ank'anin lokaci manyan likitoci suka duk'ufa a kanta Dan ceto rayuwarta Mama Halima waje suka tsaitsaye sai safa da marwa suke Mama Halima ce ta Hango Mummy tare da yayan nata cikin Sauri ta nufi wajensu tace "Yaya lafiya me ya kawoku asibitin nan" Cikin tashin hankali Daddy yace Arman ne ba lafiya yake aman jini yanzu haka yana emergency bamusan halin da yake ciki ba "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un " Mama Halima ta fad'a tana hawaye ta ce "Allah ya bashi lafiya Kunga dai irin halin da kuka jefa y'ay'anku sannan ta kalli Mummy dake zaune tana kuka ta ce " Sannu Aunty Allah bashi lafiya"Goge hawayenta Mummy tayi tayi ta ce "Amen Halima wa kuka kawo" Wlh Aira ce muka kawo Tasha fiya fiya zata kashe kanta koma ta mutu badai mu saniba sundai shiga ciki da ita "Cikin tashin hankali Mummy ta mik'e ta ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un kai mudai muna ganin kaddara sannan ta kalli Daddy tace hankalinku ya kwanta shikenan in suka mutu saiku zubda ruwa a k'asa kusha kun cucemu Alh d'ana d'aya tilo shikenan Kunmun sanadin mutuwarshi ga ta Chan itama Tasha fiya fiya duk sabodaku hankalinku saiya kwanta idan suka bar muku duniyar" ta k'arasa fad'a cikin kuka cikin b'aci rai Daddy yace "Ni da kike maganar nima ba shi kad'ai bane d'an nawa ko ina da wani d'an Bayanshi " Ai zaka iya k'ara Aure ka haifi wasu y'ay'an Nifa daga kanshi na gama haihuwa shi kadai garan kun kasheshi ai"Kallon Aunty Halima Daddy yayi ya ce"An d'aura Auren ne?"tana hawaye tace "Eh an d'aura labarin d'aurin Auren ne ma ya sanya ta yunkurin kashe kan nata" dafe goshinshi Daddy yayi sannan ya kalli Mummy yace "kinji an d'aura da ba a daura ba da sainaje musan yanda za ayi" Cikin kuka Mummy tace "ba tun kafin a d'aura ba nace kaje ka bashi hakuri ku bari su Auri juna kaki" kan Daddy gaba d'aya ya kulle ga Rashin lafiyar Arman da basusan halin da yake cikiba ga Mummy itama tana neman chazamai kai Rungumeta yayi tare da Fara Lallashinta yace "kiyi shiru bansan wannan kukan naki addua zamuyi ta musu Allah basu lafiya sannan zanyi magana da mahaifin nata tunda haka kike so kidaina kukan amma" Goge hawayenta Mummy tayi tare da gyada mashi kai kamar wata yarinya. Abba bayan ya dawo ya samu wannan labarin Tashin hankali Alh yusuf kawai ya fadawa halin da ake ciki cikin kankanin lokaci suka sallami mutanen da suka gayyata basu yarda kowa yaji wannan labarinba sosai alh yusuf ya shiga tashin hankali amaryarshi guda na asibiti halin mutuwa ko rayuwa Abba tashin hankali biyu ga na mamy dake sume a d'aki ruwa ya d'auko tare da yayyafa mata saida ya yayyafa mata sau Ukku tukwana ta fara sauke ajiyar zuciya Shima Abba Ajiyar zuciya ya sauke Dan sosai yakeson Mamy da kaunarta baisan wani Abu ya sameta Mamy na tashi Ganin Abba ya sanyata Fara kuka tace "Ka tafi banson ganin ka Alhaji ka kashemun y'a hankalin ya kwanta wlh yau saika sakeni wlh bazancigaba da zama da kaiba tunda baka da imani" Sosai Abba yayi sanyi Kallon Aunty fadila yayi dake yiwa Mamy firfito yace "wani Asibiti aka kai ta" Asibitin Dr aminu "ta bashi amsa Tashi Abba yayi ya ce " bari naje Chan Asibiti ita kuma ku kula da ita sosai "yana gama fad'ar haka ya fita tare da Alh Yusuf suka tafi asibitin suna zuwa Suka tarar da Su mama chirko chirko tare sukacigaba da zama jiran fitowar likitocin yayinda Abba da Daddy ko kallon juna basuyiba suna zaune wani likita ya fito ya ce " ina wad'anda suka kawo Hajara wacce Tasha fiya_fiya har rigen cewa ga munan su Mama ke "Kallonsu yayi ya ce " Ammafa Gaskiya yarinyar nan ta Auna arzik'i rabon kwana a gaba ne ya tayar da ita amma gubar da tasha mai kashewace nan take Yanzu munyi bakin kokorinmu wajen ganin mun bata agajin gaggawa alhmdll Munsamu mun daidaita abun saida bazata tashi yanzu ba zata iya kai gobe Gaskiya zaku iya shiga ku ganta"Alhmdllh duk suka Ambata tare da sauke ajiyar zuciya musamman Alh Yusuf Mummy ma sosai tayi hamdala dukda tashin hankalin ciwon Arman da suke ciki dukansu d'akin da Aira take suka nufa kwance suka tarar da ita saman gadon marassa lafiya bata Ko motsi drip daure ga tsintsiyar hannunta numfashine kawai zai tabbatarma da tana da rai Shima ba Sosai ba sai Wanda ke kusa da ita zaigane tana yinshi cike da tausayawa Mama Halima da Mama sukace Allah bata lafiya Abba ko sosai ya tsorata ganin har akan abun nan zata iya kashe kanta Shima addu'ar fatan samun lafiyar yayi mata Alh Yusuf bako kunya yaje ya zauna gadon da take tare da kama hannunta guda da babu komai ya ce "Allah ya baki lafiya my wife ya tashi kafadunki" Mama Halima da haushinshi takeji tsaki taja tare da fita itama Mama fitar tayi Dan haushinshi sukeji tace "me budurwar zuciya kawai wannan ritaten k'aton Alhaji zaiba figigiyar y'a ko ba ta mutu ba yanxu wannan ai sai ya kasheta inashi ina ita" Sai wajen 10pm tukwana Dr ya fito tare da cewa su Daddy su biyoshi office d'inshi cikin girmamawa binshi sukayi har office d'in hankalinsu duk tashe Bayan sun zauna kallonsu yayi ya ce "Alhaji munyi iya bakin kokarinmu wajen ganin mun shawo kan Lamarin d'anka alhmdllh mun d'anci nasara Kad'an zuciyarshi ce take gab da Bugawa Wanda idan ba ayi Sauri wajen ganin Anyi mashi abunda yakeso komai zai iya faruwa Sannan yanzu Egypt zamu turaku munyi magana da Babban likitan zuciya dake Chan gobe a shirya tafiyar kawai saimu tafi tare insha Allahu zai samu lafiya Allah ya bashi lafiya" cike da tashin hankali Mummy dake kuka ta ce "ciwon zuciya kuma Arman innalillahi Na shiga ukku" calm down Hajiya insha Allahu zai samu lafiya kiyi tayi mashi addu'a "Girgiza kai Mummy tayi tayi ta ce " to doctor mungode yanzu ashirya tafiyar goben harni saimu tafi"ba matsala Hajiya Daddy ko ya kasa magana kallon Dr yayi yace "ayi duk abunda ya kamata zanturo PA d'ina a shirya komai Dan Allah ka taimaka mana Dr karmu rasashi shi kadai garemu" Insha Allahu Excellency zai samu lafiya amma ayi kokari wajen ganin an bashi ko an mishi abunda yakeso Dan ciwon nashi na attack ne kamar yaji ko yaga abunda yafi k'arfin kwalwarshi"Girgiza Daddy yayi yace insha Allahu yanzu zamu iya ganinshi "ba matsala ranka ya dad'e zaku iya ganinshi amma kar ayi hayaniya a kanshi" A tare da Dr Mummy da Daddy sukaje sukaga Arman Mummy saida tayi kuka ganin d'an nata yashe kamar gawa Cikin kuka ta ce "Allah ya baka lafiya my son " Daddy ko ya jima yana zirga_zirga fitowa yayi Inda su Abba suke ya nufa Yana zuwa kallonsu yayi yace "zamu iya magana" Batare da Abba ya kalelleshiba ya ce "ba matsala" Kallon Alh Yusuf Daddy yayi yace "ko zaka bamu wuri" Dage kafada Alh Yusuf yayi tare da komawa d'akin da Aira take Dan Kara ganin jikin nata Kallon Abba Daddy yayi kamar bazaiyi magana ba saikuma yace "Daman Alfarmace nake son nema wajenka akan maganar yaran nan ni ta bangarena na hakura su Auri juna tunda dukansu Suna cikin wani hali kuma suna son junansu " "to ai anriga an baro magana a baya ko baka da labarin dazunnan aka daura Auren ta Saidai Kuyi magana da mijinta yanda yace yanzu bata hannu na" Daddy Danne zuciyarshi kawai yayi Dan sosai yakejin haushin Yayan nashi kamar bazai magana ba saikuma yace "OK had'ani da mijin nata" ta waya Abba ya kira Alh Yusuf yana zuwa Abba ya bar wajen tare da barin asibitin ma gaba d'aya kallon Alh Yusuf Daddy yayi ya ce "Kaine mijin mamana Hajara?eh nine lafiya" Ajiyar zuciya Abba ya sauke ya ce "Ina son ne ka saketa Saboda d'ana yana cikin wani hali a saboda da ita Sannan itama a saboda shi ta shiga halin da take ciki suna son junansu ka saketa ta auri wanda take so ni kuma daga million d'aya abunda yakai billion zan iya kashewa a saboda d'ana ka fad'i duk abunda ka kashe tundaga neman Auren har auranta zan linka maka sau gomanshi"Alhaji Yusuf jin maganar Daddy ma yake ya raina mashi wayau yanda yake maganar a gadara ga maganar da yazo da ita ko hauka yake ai bazai iya sakin Matar da tazomai allura cikin ruwa haukama yake zai saketa "cike da girmamawa Alh Yusuf ya ce " A Gaskiya excellency kayi hakuri amma Bazan iya sakinta ba ina sonta sosai nima zan iya shiga halin da d'an naka ya shiga koma fiye da nashi Allah ya bashi lafiya amma kayi hakuri Bazan saki mata ta ba "Yana gama fad'ar haka Shima yabar wajen tare da d'aukar motarshi ma ya bar asibitin Daddy sosai ranshi ya k'ara k'uluwa har ya sauke fushinshi shida akafiyima laifi ma ya nemu alfarma su hanashi cike da b'acin rai ya koma d'akin da Arman yake tare da d'aukar aniyar har abada bazai kara neman alfarma wajensu ba kallon Mummy yayi yace " Daman na fad'a maki mutumin Chan baida mutunci shiyasa Tun farko banje neman alfarma wajenshi ba nan ya kwashe yanda sukayi ya fad'awa Mummy cike da hawaye ta ce "Kayi hakuri sannan ta kalli Arman tare da murza hannunshi tace " Allah ya baka lafiya my son ya cire maka k'aunar yarinyar nan a cikin zuciyarka"Zanje mu cigaba da shirya tafiyar nan gobe Dan komai ya Zama cikin ready"gyada mashi kai Mummy tayi batare da tace komai ba Mummy ita ta kwana tare da Arman Wanda ko motsi bayayi Aira ko Mama Halima ta kwana da ita Washegari Wajen k'arfe Sha biyu na safe Aira ta Farka da sunan Arman ta farka a bakinta Su Mama Halima da Alh Yusuf da Aysha Da Aunty Ramlat yayar Mamy dukansu hankalinsu ya koma Wajenta cikin Sauri Aysha tayi gadon tare da kama hannunta ta ce "Alhmdllh sis kin tashi" Aira da takejinta kamar ba ita ba Bud'e idanunta tayi a hankali Sai kuma ta lumshe a hankali ta ce "Yaya Arman ku kaini wajenshi" Hawayen tausayin y'ar uwar tata ne suka zubo mata ta ce "kina lafiya ko sis ba abunda ke damunki" gyad'a mata kai Aira tayi"to ki bud'e idonki ki kalleni"bud'e idon tayi ta Kalleta abubuwan da suka farune suka dinga dawo mata a kwalwa "rufe idonta tayi ta ce " sis yaya Arman yana ina please ku kaini wajenshi"Hawaye kawai Aysha take tama rasa amsar da zata bata "Alh Yusuf ne ya dawo tare da Dr ya ce " duba ta Dr ta farka tare da Dr suka nufi Wajenta likitan ya ce "Tashi ki kalleni kinji " ba musu Aira ta bud'e idonta aysha ta kama ta ta zaunar da ita murmushi Dr yayi mata ya ce "Bakyajin komai kinajin jikin naki normal ko " gyad'a mishi kai Aira tayi ta ce "Ba komai please ku kaini wajen YAya Arman shi nakeson gani" Alh Yusuf sosai yake kishin sunan wani da take Ambata Hakanan ya Danne zuciyarshi kama hannunta yayi tare da cewa "Ya jikin naki baby" wani irin k'ududun bakin ciki ne ya tunkarowa Aira Fisge hannunta tayi tare da Jan tsaki Dan a duniya babu Wanda ta tsana takejin da tana da dama da zata iya kasheshi sama da wannan bak’in mutumin "Sosai Alh Yusuf yaji ba dadi amma kuma yasan dole yayi hakuri da hakan tunda bata sonshi harya samu ya shawo kanta " Kuka Aira ta fashe dashi Tare da Fad'awa jikin Aysha tace "Aunty ku kaini wajenshi please ku taimakeni ku kaini ko ganinshi nayi " Mama Halima ce ta taso Bayan ta Goge hawayenta ta kama hannun Aira tare da mik'ar da ita ta ce "muje ki ganshi sai Kuyi bankwana " Cikin Sauri Aira ta mik'e tana hawaye ta ce "Yawwa Mama Dan Allah ki kaini wajenshi yana ina " cike da b'acin rai Alh Yusuf ya kalli Mama Halima ya ce "da izininwa zaki kaita wajen wani kin manta da igiyar Auren na a kanta to ba Inda zata " Cike da b'acin rai Mama Halima taja tsaki tare da cewa"Wannan kuma baka isa ba D'an uwantane koba alak'ar soyayya tsakaninsu dole zankaita suyi bankwana "tana gama fad'ar haka ta figi hannun Aira sukayi waje suka nufi Inda Arman yake Arman Angama shirin komai har anfito dashi a kan gadon marassa lafiya har lokacin ko motsi bayayi Mummy na Bayan masu turashi sai kuka take dukda tare da ita zasu tafi Nan suka had'e dasu Aira ana shirin fita dashi daga asibitin Kallon Mummy Mama Halima tayi tace Kiyi Hakuri Insha Allahu zai samu lafiya sannan ta kalli Aira ta ce " ga shinan Saidai kiyimai fatan samun lafiya"Cikin rud'u Aira ta fisge hannunta daga na Mama Halima tare da rugawa ta fad'a kan Arman dake kwance ta fashe da wani irin kuka mai shiga rai Sosai take kuka kanta na k'irjinshi tace "Yaya Kaine cikin wannan halin yaya karkamun haka yaya bamuyi haka dakai ba munyiwa juna Alk'awarin rayuwa tare yaya ka mance alk'awarinmu kai da kanka fa kace Mu rik'e alk'awarin juna sannan ta nuna zoben hannunta ta ce " yaya da kanka fa ka bani zoben nan kace ta alkawarinmu ce Karka tafi ka barni karmuci Amanar soyayyar mu I love you yaya kai kad'aine nakeso kaikad'aine mijina ka tashi Airanka ce ba Aira kadai ba hatta mutanen dake wajen kukan tausayi suke sosai Mummy itama take kuka rungumo Aira tayi ta ce "Kiyi hakuri daughter Kiyi mai fatan samun lafiya kinji ke kuma Allah baki zaman lafiya da mijinki" kuka Aira ta fashe dashi tare da kankame Arman gam tace "Mummy ki rabu dani ni yaya Arman ne kad'ai mijina yaya ka tashi Airanka ce fa ta na fad'a tana girgiza shi Bambareta Mummy tasoyi amma ta kasa saboda ba rikon wasa ta mashi ba gashi Dr sai magana yake akan lokaci na kurewa jirgin ya kusa tashi Mama Halima da Mummy sukayi kokarin bambare Aira daga kanshi sai kuka take Dak'yal suka Bambareta suna Bambareta sukaga Arman na motsi cike da mamaki suke Kallonshi " Kungani daman nace maku zai tashi Yaya Ka bud'e idonka Airanka ce "Bud'e idonshi Arman yayi a hankali ya s'aukesu akan Aira Murmushi Aira ta sakar mashi dukda hawayen da yayi jab'e jab'e da fuskarta fad'awa jikinshi tayi tare da Rungumeshi tace " I love you yaya please Karka tafi ka barni ina tare dakai karka mance alk'awarinmu yaya ka manta kaid'in jinin jikina ne "lumshe idonshi Arman yayi dukda zafin ciwon da yakeji a cikin zuciyarshi a hankali ya d'aga hannunshi tare da rik'e hannunta ya murza hannunta daidai kunnanta ya saita bakinshi a hankali kamar mai koyon magana ya ce " My cutie "Cike da farinciki Aira ta ce " My yaya"Lumshe idonshi yayi saikuma ya bud'e a hankali ya rad’a mata ya ce "I Love you my cutie ki rik'emun Amanata Alk'awarinmu ya na nan karki ci Amanata ki rik'emun Amanar Komai dake tattare dake na baki Amanar kanki Da kanki ke tawace ni kad'ai kiyi hakuri kiyiwa mahaifinki biyayya kafin na dawo ina tare dake duk rintsi duk wuya alk'awarin mu na nan i love you .....Duka a hankali yake maganar cikin k'arfin hali Dan a rarrabe yake maganganun " Goge hawayenta Aira tayi tace "I love you too yaya kai nawa ne ni kad'ai nima takace kai d'aya plx ka tashi a ciwon nan meya sameka yaya" tari ne yazowa Arman Cikin Sauri Aira ta Dagashi cike da tashin hankali ta fashe da kuka ganin Arman na tari jini na zubowa daga bakinshi "Dr ne yace " ku maza ku turashi a sakashi mota ciwon yana worse "cikin Sauri aka tura Arman Dan a sakashi mota a tafi Airport Kuka Aira ta fashe dashi tare da Rik'e k'arfen gadon ta ce " ina zaku kaimun shi ku barmunshi zai tashi ba abunda ya sameshi yanzu muka gama magana dashi ku barmun miji na dak'yal wasu nurse tare da Mama Halima suka rik'eta tana fusgewa tana kallo har aka fitar da Arman daga asibitin Sulalewa a wajen Aira tayi summammiya.........✍🏿 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/23, 18:57] Hajo hajo: 🅿️.......*61&62* Sulalewa a wajen Aira tayi summammiya kuka sosai Mama Halima da su Aysha su Mama suke sosai suka tausaya musu Emergency aka k'ara wucewa da Aira Mama Halima ko cike da b'acin rai Ta fice daga asibitin Tana kuka tana zuwa gidansu Aira Cike da b'acin ran da tajima batayishi ba ta samu Abba ta ce "Hankalinka ya kwanta ka sanya su cikin wani hali Arman yana Chan rai hannu Allah daman haka kakeso yaya baku da imani baku da tausayi ba yanda bamuyi dakai ba kar ayi Auren nan amma ka dage sai anyi Daga yau na tafi bazaka k'ara gani na da idonku ba bazan k'ara zuwa garin nan ba Yau ina kukan rashinku iyayena amma kuma ina tayaku farincikin tafiya da kukayi ba tare da kun iske wannan bakin tashin hankalinba" tana gama fad'ar haka zata fice Abba yayi saurin janyo hannunta ya ce "Haba Halima yau kece kika fad'amun magana haka" cikin kuka ta ce "Yaya dole na fad'a maka bakuyi mana adalciba a rayuwa" Sosai Abba ya shiga Lallashin kanwar tashi dak'yal ya samu ta hakura ta fasa tafiyar amma da niyyar da tayi gida zata koma Daga wajen Abba kai tsaye wajen Mamy ta nufa Inda ta sameta sai hawaye take yayyinta sai Lallashinta suke Dan tunda akace Aira bata mutu ba hankalinta ya kwanta Saidai hawayen tausayinta da take ta so taje taga jikin nata amma ta kasa Dan zuciyarta zata karaya bangaren su Arman Cikin sauki akayi clearing d'in komai jirginsu ya d'aga Egypt koda suka isa sosai asibitin aka karbesu cikin girmamawa nan manyan likitoci suka shiga Duba lafiyar Arman Inda suka duba sukaga zuciyar tashi ta kumbura sosai Dan Kad'an Ya rage ta buga nan suka shiga bashi taimakon gaggawa cikin kwarewar aiki irin nasu.Aira ita ce bata farka ba sai wajen Tara na dare da sunan Arman ta farfado ba abunda take In banda kuka sosai Aysha Da Aunty Fadila yayar Mamy suka shiga Lallashinta Sannan Dr ya k'ara musu bayani da cewa jininta ya hau a kiyaye b'acin ranta shi kanshi Dr mamaki yake garinya karama kamar wannan ta kamu da hawan jini duk yanda akai da Aira ta ci wani Abu kasawa tayi ko ruwa bata sha ba tun tana kukan harta dawo tana hawaye tana tausayin halin da ta tarar da Arman idan ta tuna kuma da maganganun da ya fad'a mata sai tayi murmushi ta ce "Ina nan jiran ranar dawowar taka my yaya nasan bazaka bar da'd'addiyar alak'armu ta tafi a banza ba Ganin Aira na hawaye kuma tana murmushi ya sanya Wanda ke wurinta tsorata sukace kodai ta zauce cike da tashin hankali Aysha ta kira Mama dayake sunkoma gida sai suka bar y'an matan Wajenta tana kuka ta ce " Mama Aira fa kamar ta zauce wlh kinganta nan tana kuka kuma tana Dariya "cike da tashin hankali Mama ta ce subhanalla Aysha kin tabbatar kuwa" wlh Mama da gaske kinganta nan yanzu haka hawaye take kuma tana murmushi"Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Mama ta fad'a sannan ta ce"Bari na tafi gidan Malam Hassan(k'anin mahaifinta ne malami ne) ayi mata rubutun dakewa insha Allahu idan akayiwa mutum ana dacewa tunda ayar Allah ce"to Mama "Mama bata fad'awa kowaba saboda tasan hankalin Mamy k'ara tashi zaiyi Mama Halima kadai ta fad'awa itama tayi na am da hakan tare sukaje wajen Malam din suka yimashi bayanin komai cikin k'ank'anin lokaci yayi musu rubutu a Allo ya wanke ya zuba musu a leda ya ce Aje a bata ta sha gobe insha Allahu zai rubuta da yawa azo a amsar mata tana sha insha Allahu ko meye zata dake " Godiya Sosai su Mama sukayiwa Malam a Daren wajen shad'aya Mama da Mama Halima suka wuce asibitin A lokacin ma Aira na zaune ta kalli wannan ta kalli wancen sai kuma ta fashe da kuka ta ce "Yaya ku kaini wajenshi akwai maganar da zamuyi" Mama.Halima saida tayi hawaye ganin k'iri_k'iri yarinya na neman haukacewa "Zama Mama Halima tayi tare da daure fuska ta ce " Kiyiwa mutane shiru bansan shirme ke baki da tawakkali ne "kuka Aira ta fashe dashi ta ce " Mama yaya Arman ne fa munyi alk'awarin bazamu rabu da juna ba to me yasa suka tafarmun dashi"dafota Mama Halima tayi ta ce "Kiyi hakuri zai dawo nan kusa anje nema mashi magani ne dazuma munyi waya dashi ance ya farka yana ta tambayarki ya ce ki kwantar da hankalinki zai dawo saikuyi aurenku ko" lokaci guda Aira ta washe hakora ta ce "da gaske Mama sannan ta Rungumeta cike da farinciki ta ce Amma Naji dadi Mama yanzu yana dawowa Aure kawai zamuyi meya sameshi wai plx ku kiramunshi " bata rai Mama Halima tayi ta ce "zazzabi ne kawai sannan kuma Yanzu yayi bacci " bata fuska Aira tayi ta ce "wayyo Allah bashi lafiya To gobe kin kiramunshi " gyad'a mata kai Mama Halima tayi daman tayi mata wannan karyar ne Dan son kwantar mata da hankali"mik'a mata rubutun tayi ta ce "Amshi kisha yanzu " na meye Mama"banason tambaya cewa nayi kisha"Amsa Aira tayi ba musu ta Shanye rubutun tas"Ajiyar zuciya Mama Halima ta sauke sannan ta kalli su Aysha Da su mama ta ce "Zan kwana Wajenta kawai ku tafi gida" tafiya sukayi tare da Addu'ar Allah bata lafiya a hanya Haidar ya ce "Mama ya Aira fa ta zare wlh maganganunta duk na zararru take" Harararshi Mama tayi ta ce "karna karajin maganar nan a bakinka kayiwa y'ar uwarka fatan samun lafiya kaji" gyada mata yayi ya ce "To Allah ya bata lafiya "Mama Halima ita ta kwan wajen Aira sosai ta dinga kwantar mata da hankali harta samu taci abinci sannan ta samu har bacci ya d'auketa sai sannan tayi nata kukan tajima ta na Addur Allah ya kawowa yaran nan sassauci cikin rayuwarsu tukwana itama tayi bacci.washegari aka Sallami Aira Dan jikin nata yayi sauk'i wajen 12:PM suka dawo gida a d'akin Mamy ta sauka Dan bata kulawa jikin nata ya k'ara murmurewa Sosai Mamy ta d'an kwantar da hankalinta ganin y'artata taji sauk'i nan nan kawai take da Aira ga kuma tunaninta na Tasan kila Abbansu ya hakura a farke Auren nan yinin ranar Abba baiko lek'o Inda Aira take ba bare yayi mata ya jiki hakan ko ba k'aramun. K'ara konawa Mamy rai yayi ba ranar sau Ukku ana kawo rubutu daga gidan Malam ana bawa Aira kuma akayi sa a ba musu take sha Sai takejin zafin rad'ad'in dake cikin zuciyarta ya fara raguwa Kwana Ukku akai Aira na shan rubutun nan sosai ta d'an fara rage damuwa Saidai har yanzu tunanin Arman daidai da second d'aya yaki barin kwalwarta Saidai kuma abunda ke bata mamaki yanzu ya fara nutsuwa kuma ta rage kukan da take akai akai gashi Abba baiyi maganar kaita sokoto ba fata kawai take Allah ya wargaza Auren nan ta huta b'angaren Arman an d'an samu cigaba Kad'an amma har yanzu bai farfadoba hatta abinci Saidai a bashi ta hanci ko motsi bayayi Mummy kullum cikin kuka take Daddy ma sosai hankalinshi ya k'ara tashi sosai suka shiga damuwa lokaci guda harsun rame Kullum addua kawai suke Allah ya bawa Tilon d'ansu lafiya Daddy ko k'iyayyar Abba ce ta k'ara ninkuwa a cikin zuciyar shi Dan yasan shine silar shigar d'anshi cikin wannan halin.Bayan kwana hud'u ranar Alhamis Aira sosai ta fara wartsakewa Saidai kewar Arman da tayi mata yawa har lokacin Mama Halima bata tafiba Dan Mamy ta hanata tafiya ta ce itace kawai ke k'ara kwantarwa da Aira hankali Dan Allah ta jira ta Bari aga yanda Allah zaiyi hakan yasa Mama Halima ta zauna Aunty Maryam ko tuni ta koma gidan mijinta yayyun Mamy ma duk sun koma sai yayarta Aunty Ramlat kawai da ta tsaya suna zazzaune a palour Abba ya shigo nan ya shaida musu su shirya gobe Friday dangin Alh Yusuf zasuzo su tafi da amarya daman ya hakura ne shi mijin nata har taji sauk'i yanzu kuma tunda taji sauk'i Alhmdllh haka akeso Ku fara shiri"Sosai hankalin Aira ya tashi amma kawai batasan ya akayiba saitaji wani tawakkali ya zo mata idanunta dake zubar da hawaye duk kallonta mutanen dake wajen sukayi suga wani hali zata shiga sai sukaga kawai ta mik'e cike da hawaye ta ce "Allah ya kaimu" tana gama fad'ar haka ta wuce d'akin su tare da Fad'awa Gado ta jima tana kuka tana tunanin rayuwar da suka tsara Bayan auransu itada Arman k'watsam K'addara ta gifta musu Wannan shi ake kira ka na naka Allah na nashi Goge hawayenta tayi ta yi ta ce "ban isa na ja da ikonka ba Allah Kaine ka tsara duk wannan Allah ka bamu ikon cinye wannan jarabawar da ka jarrabemu da ita ya Allah idan har kasan mutuwa hutuce a gareni ya Allah ka kasheni kafin gob.....saurin rufe mata baki Aunty Ramlat tayi da ta shigo ta ce " ki daina fad'ar haka y'ata a farko kinyi magana me kyau daga karshe kina neman ki b'ata kiyi hakuri ganin kin cinye wannan jarabawar ki daina sanya damuwa a ranki ki nutsu kiyiwa mahaifinki biyayya zakiga fa'idar abun nan gaba"Cikin kuka Aira ta gyad'a mata kai ta ce "To mama" Mama Halima da Aunty Ramlat su suka gamu suka dinga yiwa Aira nasiha mai shiga gami da wa'azi sannan sukayi mata nasiha akan Wanda ya kashe kanshi direct d'an wuta ne karta k'ara yunkurin kashe kanta "Sosai nasihar ta shige ta sannan tayi musu alk'awarin insha Allahu bazata k'ara attempting kashe kanta ba " Sunkai wajen 1 suna mata wa’azi da nasiha tukwana suka rabu da ita sukace ta kwanta Daren ranar bacci kauracewa idanunta yayi tashi tayi tayi alwala tayi salla Addua kawai take akan Allah ya bawa Arman lafiya sannan Allah ya bata hak'urin Auren nan da za ayi dukda ta d'auki alwashin k'untatawa Alh Yusuf har saiya gaji ya saketa Mummy ko haukane kawai batayi ba Bayan barin Aira palour masifa da ruwan bala'i ta shiga surfawa Abba ta ce "Wlh Alh baka da imani baka da tausayi Ka sanya yaran nan cikin wani hali kai wani irin mugu ne ka fiya son kanka da yawa kai mutum ne mai sonkai wlh na gaji da zaman gidan ka yau d'innan saika sawwakemun Ka sakeni kawai " Shima Abba cike da masifa ya ce "Ni zaki dinga zagi Rahama Dan Kinga ina Miki lakwa lakwa harkina samu daman fad'amun magana mahaukaciya kawai wacce batasan abunda take ba" Sosai fad'a ya kaure tsakanin Mamy da Abba Wanda dak'yal Mama Halima da Yayar Mamy suka samu suka basu hakuri Dan Aunty Ramlat saida tayi kamar zata bugi Mamy tukwana ta samu Ta koma daki Nan suka bawa Abba hakuri saida suka kashe case d'innan ne ma suka samu damar zuwa wajen Aira Daren ranar Aira bacci k'auracewa idonta yayi ga wani masifaffan ciwon kai da ya addabeta sai wajen karfe ukku wahalallen bacci ya kwasheta ko Sallar asuba bata samu tayi ba sai wajen Tara ta tashi Shima Dan Ummy ce ta tayar da ita da tazo ba jimawa tana tashi salla Aira tayi tana gama salla ta koma ta kwanta ta Lula duniyar tunanin Arman shin yana wani hali ya yake ta jima tana tunani batasan lokacin da wasu zazzafan hawaye ke zubo mata ba Mama da Mama Halima da Aunty Ramlat su suka shiga shiryen shiryen tafiya da Aira Mamy ko lek'owa batai ba Dan bak'inciki Daman tun last week akaje akayi jere maza sukayi jeren sosai Abba ya kashewa Aira kud'i a kayan daki kayan kitchen da sauransu gara ko ba a magana duk wani Abu da uwa zatayi shi yayi bai bari Mamy tasai ko chokali ba Dan daman yasan bazata sayaba tunda ba son Auren take ba wajen k'arfe biyu na rana y'an uwan Alh Yusuf sukazo su shidda manyan mutane domin tafiya da Amarya Sosai aka musu tarba ta musamman Mama Halima ita taje ta sanya Aira tayi wanka ta had'a mata ruwan Turare Aira na kuka ta na wanka Bayan ta fito kallonta Mama Halima tayi tare da fito da wata tantsetsiyar farar laffaya ita da kanta Mama Halima ta shiryata ba make up ba komai amma tayi bala in kyau dukda damuwar da Aira ke ciki ana shiryata tana hawaye farfesun y'ay'an ciki Aunty Ramlat ta kawowa Aira ita da kanta ta dinga bata tana ci dak'yal Tana ci tana hawaye Wajen k'arfe Hud'u da wani Abu Su Mama Halima suka kama hannun Aira suka fito da ita idonta Rufe cikin laffaya Amma ganin an fita da Aira kuka ta fashe dashi a d'akin bata tab'a jin damuwar Auren nan ba sai yanzu da za a tafi da Aira sosai ta dinga risga kuka Itama Airar kuka take Kama hannunta sukayi sukayi da ita d'akin Mamy suna shiga Kafin su k'arasa Mamy ta ce "ku tafi da ita kawai na yafe mata karku k'ara tayarmun da hankali" Jin haka ya sanya Aira saurin fusgewa tare da rugawa taje ta Rungume Mamy ta fashe da wani irin kuka itama mamyn Rungumeta tayi tana kuka sosai suka shiga rera kuka hatta su Mama Halima saida suka sanyasu kuka Sun d’au minti goma suna kuka ganin abun nasu ba mai kyalewa bane ya sanya Mama Halima zuwa ta kama Aira Fusgewa Aira tayi cikin kuka ta ce "Mamy Mamy karki bari su tafi dani Mamy nasan ke kina sona " Itama sosai Mamy ke kuka Mama Halima ce ta ce "ki mata addu'a ki yafe mata ba kuka zaku zauna kunayiba" Cikin kuka Mamy ta ce "Na yafe mata duniya da Lahira Allah yayi miki Albarka Allah yayi miki Albarka Aira na yafe ma..kasa karasawa tayi sakamakon kukan da yazo mata kama Aira sukayi Dan tafiya da ita sosai Aira ke kuka tana ruk'o Mamy tana cewa" Mamy karsu tafi dani Mamy Mamy......Dak'yal suka samu suka Bambareta suka fito da ita Kai tsaya dakin Mama suka Nufa da ita itama Sosai sukasha kuka tukwana suka wuce da ita wajen Abba "Ganin irin kukan da Aira take karo na farko kenan da Abba yaji tausayin y'ar tashi tunda aka fara abun nan Danne zuciyarshi yayi ya ce " Allah yayi miki albarka Mama na na yafe miki duniya da lahira Allah ya bada zaman lafiya kutafi da ita kawai"Rik'e k'afar Abba Aira tayi dake kuka kamar zata mutu ta ce "Abba karka bari su tafi dani Dan Allah Abba" Rungumota Abba yayi tare da mik'ar da ita ya kalli su Mama halima ya ce Muje Abba da kanshi ya saka Aira mota dake kuka Kallonsu mama Halima yayi da yan uwan Alh Yusuf ya ce "muje na Muku rakiya Airport d'in Abba da kanshi ya tuk'a Aira har Airport......✍🏿 😭😭😭😭😭😭😭 *NI DA YAYA ARMAN it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿🤙🏿 [6/26, 09:43] Hajo hajo: 🅿️..........*63&64* ....Suna isa Airport Abba da kanshi ya kama Aira ya fito da ita Yana gaba itadashi da take Rungume jikinshi tana shashekar kuka sauran y'an rakiyar na baya daman an Riga Angama musu komai ba ayi minti goma ba akace jirginsu zai tashi y'an uwan Alh Yusuf su suka amshi Aira da ke hannun Abba dak'yal suka Bambareta sai risgar kuka take cikin sanyi Abba ya ce musu "Ga amana nan na baku dan Allah ku rik'emun ita amana bata da kowa a chan na damk'ata a hannunku ku rikemun ita amana"a tare suka ce insha Allahu mun karb'a hannu biyu Alhaji mungode Allah ya saka da alkhairi Aira na kuka tana kiran sunan Abba har suka kamata suka shiga jirgin Mama Halima da Aunty Ramlat sukayi mata rakiya a tare suka tafi ba b'ata lokaci jirginsu ya d'aga sokoto Abba ko cike da kewar y'artashi ya koma gida har yanzu duk cikin y'ay'ashi ba Wanda yakeyiwa son da yake yiwa Aira a cikin zuciyarshi ba yanda zaiyine dole sai hakan yana komawa gida ya ci karo da Mamy tana fitowa da akwatinta tare da Amer a hannunta kallonta yayi ya ce " ke kuma ina zaki"Cike da masifa ta ce "Gidanmu zan koma kuma.wlh saika sakeni tunda ka rabani da y'ata ka turata uwa duniya cikin kishiyoyi mararsa imani inma kashemun ita za ai ayi kai ba ruwanka ka cuceni wlh Alhaji sakayyata dakai sai lahira Sannan ka bani takardata na koma gidanmu yau ba Inda zani saida takardata tunda kayi abunda kakeso hankalinka ya kwanta nima kuma zanyi abunda nake so ka bani takardata Alh tun muna mu biyu " sosai maganganun Mamy suka b'atawa Abba rai Danne zuciyarshi yayi ya ce "Kije na aika Miki takardar taki gida sannan ya mik'a hannu ya ce " bani d'ana ai ba da shi kikazo ba ba yaro d'aya ba zaki tafarmun dashi ba Tunda ke mahaukaciya baki da hankali sakarai kawai "Mik'a mishi Amer d'in tayi tare da Kayanshi na d'ayar akwatin ta ce " ga shinan Ai daman bance zan tafar maka da yara ba Shima Dan naga mama yakesha Gashinan Inma kashesu zakayi saika gamu ka kashesu daman ai ka kashe rayuwar d'ayar suma saura su "Mama da Aysha Da suka fito Aysha tayi saurin rik'e hannun Mamy tana hawaye Dan sai yanzu take kukan tafiya da Aira bata iskesuba tana zuwa akace suntafi sosai ta sha kuka kallon Mamy tayi ta ce " Dan Allah Mamy karki tafi kiyi hakuri Dan Allah nasan kina cikin fushi ne kiyi hakuri ki dawo "Mama ko Abba ta Kalla ta ce " Bazaka hanata tafiya ba Alhaji"Tsaki Abba yaja ya ce "ta tafi d'in mana aiba wani abu akayi mata ba bare na bata hakuri sannan ya mik'awa Mama Amer ya ce " Amsarshi ku koma ciki "Haba Alhaji wannan fa ba daidai bane Ku dinga kai zuciyarku nesa sannan ta kalli Mamy ta ce " Ke yanzu Rahama yaron shekara guda zaki tafi ki bari "Ai bani nace bazan tafi dashi ba shiyace na Aje mishi d'a Dan haka bazan tsaya jayayya ba Allah ya raya" Tana gama fad'ar haka Mamy taja akwatinta ta saka a motarta ta zagaya tashiga tayiwa maigadi horn ya fito ya bud'e mata taja ta fice Amer dake Kuka Hannun Mama Aysha ta Goge hawayenta ta amsa Mama ce ta ce "Haba Alh wai meyasa baku sassauta Abu ka maida mata d'anta akwai zalinci fa me yaro karami yayi" cike da b'acin rai Abba ya ce "Ina ruwanki ko bazaki rik'emunshi ba na nemi Inda zan kaishi" Jan bakinta Mama tayi ta ce "Allah ya baka hakuri" Sannan ta juya Kallon Aysha yayi ya ce "zanba Driver yanzu ya kawo muku irin abincin da yakeci ki lallabashi yayi bacci Sannan Anjima ki tafi gidanki bansan wannan zaryar da kike tunda an k'are biki ya isa kuma" To Abba "Aysha ta fad'a tukwana itama ta koma ciki tana jijjiga Amer dake Kuka harta samu yayi bacci sosai Abba yayo sayayyar irin abubuwan da Amer ke sha na yara damanshi bai fiya rigima ba Sosai inba yunwa ba Dan Ya saba da y'an gidan sosai Musamman Haidar dake yawan daukarshi Haidar Bayan dawowarshi daga school ya samu labarin Tafiyar Aira da kuma tafiyar Mamy Sosai ya sha kuka Shima harya hakura ya daina tukwana ya d'auki Amer ya dinga mashi wasa Mamy ko koda ta isa gidan Yayanta kallonta yayi ya ce " ya na ganki da akwati Rahama "Cikin kuka ta ce " Yaya gida na dawo na gaji ya ce ma zai aikomun takardata gida"Dak'uwa yayi mata ya ce " Bansan shiririta Rahama wuce ki koma gidanki"Kuka Mamy ta fashe dashi ta durkushe ta ce "Dan Allah yaya kayi hakuri amma Bazan komaba Saidai na tafi Agadez indai kace saina koma " Matar Yayanta Hindatu ta ruk'ota ta ce "To bar kukan wuce muje ciki " Hindatu bansan irin wannan ki barta ta koma gidanta dukda ban bincika ba nasan ita ce bata da Gaskiya "Haba Alh aikama ka bari ka bincika ko sannan ai bata tab'a zuwa ko yaji ba Tunda kaga haka kila da abunda aka mata " hindatu kenan saikace baki zauna da Rahama ba bakisan halinta ba kinsan halinta fa sarai inta rikice to muje Naji abunda ke faruwa?Bayan sun zauna ya Kalleta ya ce “fad'amun abunda ke faruwa"Cikin kuka ta ce "Yaya maganar Aira ce sanin kanka ne har kashe kanta tayi kokarin yi amma Abbansu bai saduda ba yanzu haka sun tafi da ita sokoto yaya gidan kishiyane fa za a kaita da y'ay'an miji ina Aira ina zama da kishiya yarinyar da bata da wayau ko fad'a bata iya ba" tsaki yaja tare da tashi ya ce "nama zaci ko keda shi ne daman baki hakura da maganar nan ba duk abunda nafada maki baki yarda dashi ba to wuce ki koma gidanki badani ba daurewa karya gindi dama ace wani laifin yayi miki shine da saina d'aukar maki mataki" Kuka Mamy ta fashe dashi ta ce "Yaya ai ban k'arasa fad'a maka ba " a tsaye ya ce inajinki yi Sauri bansan jin shiririta cikin kuka ta ce "Yaya Kuma kullum daya tashi bai kunyar zagi na Gaban kowa har gaban yara na ya dinga Cemun mahaukaciya mai k'aramar kwalwa "To Ai ita d'ince Rahama na rasa me yasa har yanzu bakya girma Abunda zakiyi wani d'an shekara goma ma bazaiyi ba yanzu kin tashi kin taho Ina Amer d'in yake dallah ki wuce ki koma gidanki zanyi magana dashi bazai sake zaginkiba shikenan ko" kuka ta fashe dashi ta ce "Yaya Dan Allah ka bari ko zan koma ba yanzu ba Amer shi ya amsheshi ya ce Bazan tafar mashi da yaro ba " Hindatu ce da ke Dariya ta mik'e tare da kama hannun Mamy tayi ciki da ita dawowa tayi wajen mijin nata ta ce "Kaida kasan Rahama y'ar rigima ce idan tak'i duk bakai ba ka ja da ka shagwaba ta ba Alhaji itafa har yanzu jinta take kamar wata y'ar shekara sha takwas Bata girma Rahama Harta Aurar da Y'a Amma batabar shiririta ba yanzu kawai tunda ta kafe ka barta ta d'an huce zata Huce ai fushi ne "Girgiza kai Yayi tare da murmushin manya ya ce " Allah ya shiryeta Ki dinga mata nasiha da nuna mata rayuwa Dan Allah"Insha Allahu Alhaji zan nuna mata ai dole duk kai ka ja mana wannan aikin da ka dinga shagwabata da yawa ai yanzu Rahama da me fad'awa wanice"murmushi yaya yayi ya ce "Hindatu kenan gata da soyayya ne na nunawa Rahama bawai shagwabata nayi ba kin manta amana ce ita da iyayenmu suka barmana Kingakwa dole na nuna mata soyayya da gata " asalinsu! Mamy su shidda kenan wajen iyayensu Babban yayansu Safiyanu,Ramlat,Asma'u,Aisha,Fadila ,sai autar su Rahama mahaifinsu Alhaji Ibrahim sanannen mai kud'ine a garin Agadez mahaifiyarsu Hajiya Saratu haifaffiyar garin katsina ce Aure ne takaita Niger amma y'an uwanta duk suna Chan suntasone cikin Had'in kai da k'aunar juna Babban yayansu tunda yazo karatu kano yaga wuri Inda ya fara kasuwancinshi a nan kano har yayi Aure ya auri matarshi Hindatu y'ar nan kano ce itama yayyun mamy ma mata duk sunyi aure a nan niger kasancewar sun bata shekaru sosai iyayenta da yayunta suna ji da rahama sosai kasancewar ita ce autarsu musamman iyayensu da suka shagwabata komai ance Auta kwatsam wata rana iyayensu zasuyi tafiya zuwa k'asa mai tsarki Dan yin Umrah A lokacin Rahama na da shekara Bakwai a duniya da tare dazu tafi da ita amma tasa kuka ta ce ita bazata k'ara zuwa ba saboda tsoron jirgi take sun taba tafiya da ita ta tsorata sosai hakan yasa ko jirgi taji an ambata a lokacin sai tasa kuka ana gobe zasu tafi yaya Safiyanu yazo daga kano Dan suyi bankwana Hannunshi iyayenshi suka damk'a da na Rahama suka ce "ga Amanar Rahama nan a hannunka amana amana amana ka rik'e mana Ita amana karka yarda tayi kukan rashinmu ko Bayan ranmu ka zame mata uba kaji ka dauki nauyinta sannan kuma ka jajirce a kanta ka bata ilimin zamani da na arabi " Sosai Safiyanu yayi sanyi ya ce "kidaina fad'ar haka Mama sainaga kamar wani abun ne ko bazaku dawoba insha Allahu na amshi Amanar Rahama har abada" sosai suka dinga yi musu nasiha a lokacin Rahama bata da wayau bata ma sanin abunda Suke cewa ba Sosai a ranar da zasu tafi har aiport suka yi musu rakiya duk sunyi sanyi har suka tafi suna juyowa sunayiwa yaransu bye bye harzasu shiga jirgi Rahama ta Ruga tare da rungumesu sai kuma tasa kuka hakan yasa hankalin y'an uwanta tashi duk tafiyar da iyayensu suke basu tab'a jin ba dadi ba irin wannan tafiyar shafa kanta iyayenta sukayi sukace "Allah yayi miki albarka Rahama kibar kuka kinji ko bakison idan muka dawo mu taho maki da d'iyar roba mai tafiya tana wak'a " Cike da murna Rahama ta ce "Ina so Mama Allah maidoku lafiya" a wannan tafiyar ne aka samu hatsarin jirgi da akayi asaran rayuka Wanda ciki hada iyayensu Rahama cikinsu babu Wanda ya fita Sosai y'ay'ansu suka sha kuka daga karshe suka yi hakuri sukacigaba da yiwa iyayensu addua tundaga lokacin Rahama ta koma kano wajen yayanta da zama Inda shida matarshi suka rik’eta amana sosai Yayanta ke bata kulawa tare da bata dukkan abunda take so bai tab'a yarda daidai da rana d'ayaba Rahama tayi Rashin iyaye Komai takeso mata yake musamman idan ya tuna da wasiyar da iyayenshi suka bar mishi a kanta Ya sanyata makaranta mai tsada tun daga Primary har secondary Wanda da kyal ta k'arasa secondary saboda samari da suke yi mata chaaa saboda masha Allah Rahama akwai fari ga kyau Alh Safiyanu yana da yara hud'u Duka maza ne ana hakane har Daddy Ya shigo rayuwarsu soyayyarsu da Daddy da kuma yanda akai ta koma wajen Abba Wanda son farincikin Rahama ne ya sanya Yayanta yarda akan Amincewa da Abba a lokacin tana da shekara sha takwas akayi mata a yanzu Kuma tana da shekara talatin da bakwai *Wannan kenan* K'arfe Shida da wani Abu tayi musu a sokoto a jirgima Aira har suka iso Kuka take motocine na alfarma su kusan goma suka zo taryar su Aira a ta tsakiya aka sanyata Mama Halima na rik'e da ita tare da Yayar Alh Yusuf a haka har suka isa katafaran gidan Alh yusuf dake Arkilla quarters har lokacin fuskar Aira na lullub'e cikin laffaya gabanta banda fad'uwa babu abunda yake jin abun take tamkar mafarki A haka aka kamo hannunta suka fito ita dai Aira bata ga gidanba saboda fuskarta lullub'e ta ke ta na dai jin dai bud’ar mutane da zasu shiga cikin gidan Mama Halima ta ce "Kiyi bismillah ki shiga da k'afar dama Au'zubillahi minashshaid'ar Rajim Aira ta fad'a tare da shiga da k'afar hagu.......✍🏿 before the writer starts typing she knows what will happen at the beginning of the story in the middle and at the end I can't change my writing style as I originally planned so I'll go with it it was their love style that came with it😢😻 *Ni da yaya Arman it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* _*Miss Hajo ce_* [6/27, 09:57] Hajo hajo: 🅿️.........*65&66* ......Tare da shiga da k'afar hagu girgiza kai Mama Halima tayi batare da tace mata uffan ba harsuka shiga cikin gidan itadai Aira idonta lullub'e yake sai yanda akayi da ita tana ta jin bud'ar mata har aka shiga da ita tana jin an zaunar ita ta tabbatar da an kawota d'akinta kenan sosai ta fashe da wani irin kuka mai cin rai wai yau itace aka kawo d'akin miji amma mijin ba yaya Arman ba wannan wace irin yankan k'auna ce sosai ta fashe da kuka yayyun Alh Yusuf da suka d'aukota saisuka d'auka kukan rabuwa da gida ne Lallashinta suka shigayi sukace "ki kwantar da hankalinki insha Allahu mudin zamu zame maki tamkar iyaye" Mama Halima ce ta rada mata a kunne ta ce "Karna sake Naji ko kin nuna bakisan Auren nan ko kiyiwa mutane rashin kunya ki saki jikinki kinji kibar kukan nan" gyad'a mata kai Aira tayi Alamun to ta daina kenan sosai dangin alh yusuf suka tarbesu da tarba ta musamman abinciccika kala kala wata yayar Alh Yusuf tazo ta ce ya kamata Aje a kaita wajen uwar gidan A had'a su "Sosai gaban Aira ya fad'i " to Mama Halima ta ce "Sannan suka kama hannun Aira suka tafi da ita bangaren uwar gida Suna isa suka isketa ita da Y'ay'anta da y'an uwanta sai cika suke suna batsewa Hakanan suka zauna gaishe da Matar sukayi wacce zatakai sa annin Mama Ta amsa ciki ciki Mama Ramlat ce ta ce " Amarya muka kawo miki y'ar uwa Amana dan Allah ku hada kanku sannan ita munyi mata nasiha insha Allahu Zata girmamaki "Tab'e baki Hajiya saudatu tayi ta ce " Wanda ya kawota zaku ba Amanarta ba niba sannan zaman lafiya za ayishi indai ta zo dashi"Sosai gaban Aira ya tsananta fad'uwa jin kalaman Matar a zuciyarta ta ce "Na shiga ukku an kawoni wajen wata matsalar nidai ina ganin rayuwa" Su Mama Halima sosai ransu ya b'aci tashi sukayi tare da Aira batare da sunce uffan ba yayar Alh Yusuf Hadiza ta ce "kedai saude baki da mutunci wlh iyayen yarinyar nan fa y'an mutunci ne ba da tashin hankali sukazo ba Amma abunda kika fadamusu kin kyauta kenan" Tsaki saude taja tare da tashi tabar palourn Ana komawa da Aira a lokacin ana kiran Sallar magriba sai sannan ta daga idonta ta kalli d'akin dakine babba na gani na fad'a ga kuma tantsara tantsaran kayan da aka zuba mata karewa d'akin kallo tayi Sosai Tasan Abba ya kashe mata kudi a kayan dakinma kansu dukda bataga sauranba Sallah ta tashi tayi suma su Mama Halima sukayi salla Bayan sun. Gama sosai suka shiga yiwa Aira nasiha gami da wa azi akan ta zauna da kowa lafiya kuma tayiwa mijinta Biyayya Allah ba ruwanshi da bakisan auren nan zai kamaki da laifi Aira na jinsu yanda suke fad'a mata maganar na shiga kunnenta haka take fita ta d'ayan kunnen Sannan suka Mike sukace Zasu koma Dan dama ba kwana zasuyiba fly din dare zasubi sosai Aira ta fashe da kuka ta rirrikesu ta ce "Dan Allah Mama Karku tafi ku barni na shiga ukku kuma yanzu Tafiya zakuyi...sosai take kuka su kansu su Mama Halima saida ta sanyasu kuka Dak'yal kannen Alh Yusuf suka bambare Aira dake jikin Mama Halima tana kuka harsuka tafi Aira ihu take tana kukan karsu tafi su barta dak'yal y'an uwan mijinta suka dinga Lallashinta harsuka samu tayi shiru nan mutane da y'an uwa suka shiga shigowa ganin Amarya Aira in banda hawaye ba abunda take wajen karfe goma Wata kanwar Alh ta sanya Aira tayi wanka ta shirya cikin tantsanemen lace d'inta da tasha d'inki ta sanya mata Turare sosai dukda hawayen da Aira take sosai tayi kyau Saida ta gama shiryata tukwana ta mik'e ta ce " to nima na tafi yanzu ba jimawa angonki zai shigo Allah ya bada zaman lafiya "Aira bata iya ce mata komai ba saboda k'ududun bakin cikin da take ciki tana ganin fitarta ta maza taje ta sanyawa k'ofar key tare da barin key din a jiki Da gudu ta fad'a Gado tare da fashewa da kuka mai cin rai tunanin Arman yaki barin kwalwarta Alh Yusuf da murnarshi ya taho bangaren Amaryarsa sai fara a yake tare da ledarshi katuwa yana zuwa ya yi knoking yaji rufe sosai ya shiga Bugawa Aira na jinshi tayi banza ta kyale sai kuka take key ya d'auko ya gwada bud'ewa amma ya kasa hakan ya nuna mai tabar key din jiki kenan sosai ya damu cikin k'asa da murya ya ce " Haba Amaryata ki bud'e mana nasan kina jina please ki budemun kofa kinji"Aira na jinshi tsaki taja tare Kara fashewa da kukan takaici cike da damuwa.Alh Yusuf ya ce "Da Allah na had'aki baby ki bud'emun k'ofar please" cike da jaraba da masifa Aira ta ce "Bazan bud'e d'inba karka dameni Malam Karka takurawa rayuwata tun da sauran mutuncinka a idona bazan bud'e ba Saidai ka kwana a tsaye " tana gama fad'ar haka ta fad'a Gado tare da cigaba da hawaye"Alh Yusuf bai hakuraba haka yayi ta tsayuwa a wajen yana bubbuga mata ko Allah zaisa ta bud'e Hajiya saude ce ta fito cike da masifa ta ce "Da Allah Alhaji ka damemu meye hakan da kake ko kunya babu tunda tak'i bud'e maka ai sai ka hakura Amma wannan Abun da kake zubda girma ne y'ay'anka na jinka wannan wace irin jaraba ce " ta fad'a ta na Jan tsaki "Kallonta yayi ya ce " kinsan dai bansan katsalandan ko saude"to Naji yanzu dai kayi hakuri kaje ka kwanta "Ba tare da ya ce komai ba ya juya ya nufi part d'inshi tsaki saude taja tare da komawa Bedroom d'inta !*Asalinsu*??Alh Yusuf Sanannen d'an kasuwa ne a nan Jahar sokoto da ma ketaran ta Matarshi d'aya Saudatu yar asalin Garin sokoto ce yaransu hud'u Babbar d'iyarsu Zuhura tana nan tana aure anan sokoto yaranta hud'u sai mai biya mata Abubakar Sadiq shi har yanzu baiyi Aure ba,sai Mubarak shi kuma yana matakin Deegree ne anan Sokoto yake karatu sai Autarsu Laila me shekaru Ashirin da d'aya a duniya tana matakin Deegree level 2 Hajiya saude sosai take juya Alhaji sai yanda tayi dashi tunda suke da ita bai tab'a yunkurin ma Kara Aure ba Dan sosai yake shakkarta irin matan nan ne jibga jibga masu jiki da k'iba itama bak'a ce koda Alh zaiyi Auren nan sosai aka sha dagu da ita Dan y'ar bala'i ce suko danginshi daman so suke ya k'ara Aure hakan yasa suka k'arfafa abun tayi shige da ficen ta wajen malamai da Bokaye amma ba nasara Y'ay'antama sosai suke takaici da bakincikin auren da Daddynsu zaiyi musamman Zuhura da laila dan Sadeq baya k'asar shiko Mubarak ba ruwanshi Dan irin y'an duniyar nan ne shiko Alh Yusuf da yake Allah ya d'ora mishi k'auna da soyayyar Aira hakan yasa ko girgiza baiba sai ya jima tsoron Matar tashi da yake ya ragu wannan kenan.....Daren ranar Aira kwana tayi batayi bacci ba kwanan bak'inciki tayi Bayan tayi Sallar asuba wani masifaffan zazzabi ya rufeta da ciwonkai cikin bargo ta shige sai rawar sanyi take hawaye na bin k'umcinta a haka har wani wahalallen bacci ya kwasheta....k'arfe Tara tayiwa Su Mama Halima a Kano Kai tsaye gidan Abba suka sauka suna isa nan ne suka samu labarin Tafiyar Mamy Dafe kai Mama Halima tayi ta ce "ohh muna ganin rayuwa wlh harna gaji da kashe kashen case nidai gobe zan tafiyata Nida garin nan kuma sai an ganni " Aunty Ramlat ko sosai taji haushin Mamy Abba ta samu ta ce "Dan Allah Alh kayi hakuri insha Allahu zamuyi mata fad'a zata daina sannan ina neman Alfarmar da ka bani na tafar mata da yaron insha Allahu kome mukayi gobe zaka jimu" Jinjina kai Abba yayi ya ce "Bakomai Ramlat amma yaron ki barshi a nan tunda ta iya tafiya ta barshi a tunaninta ko bazan iya Rikesu bane ko me gwara ki barmunshi " dak'yal Dai ta samu har Abba ya sauko ya ce "ta tafi da Amer d'in a tare da Amer Aunty Ramlat suka tafi gidan Yayansu suna zuwa sosai Aunty Ramlat ta shiga yiwa Mamy fad'a Inda ta shiga batanan take fita ba itadai Mamy batace uffan ba Hamdalarta d'aya kawai da Ta amso mata Ameer Dan tunda ta taho shi kawai take tunani " Kiyi Hakuri Aunty Insha Allahu hakan bazata k'ara faruwa ba ya hanya kunsha hanya "Allah sa hmm hanya Alhmdllh Aira dai ana Chan gidan miji" Badai taci gaba da kukanba Aunty "Kuka kuma da sauki to amma har muka taho tanayi" Goge hawayenta Mamy tayi ta ce "Amma Aunty kina ganin ba matsala gida d'aya aka had'asu da kishiyar?tab'e baki Aunty Ramlat tayi ta ce " to da sauk'i dai za ace Amma banga Alamun mutunci a tattare da wannan kishiyar tata ba ga Aira ba Wayau ba dad'in abun kawai da dangin mijin da mijin na sonta sun hana Wani abun Amma a yanda naga Alamun kishiyar nan da yaranta banga Alamun arziki a tattare da su ba "Innalillahi Mamy ta fad'a tare da Fara kuka ta ce " wlh Alhaji ya cuceni kawai sayarmun da y'a ne yayi yanzu Dan Allah akwai adalci a abunnan kuwa Aunty Aira za akai uwa duniyar nan kawai kashemun d'iya ne za ayi"tsaki Aunt Ramlat taja tace "daman ban fad'a maki ba rikitacciya kawai ke Ko karar nan ma na y'an fari bakyayi wai d'iyarki da agaban wasu manyan ne zasu miki d'aukar marar Kunya ko Dan ai baki da itama ai wasu ko sunan d'iyan farinsu basa fad'a wlh " ni bawani karar y'ar fari da zanyi akanme masu yinma sun daina wahalshe da kansu ne suma suke ai maganar Gaskiya Ce nidai kawai an cucemu Allah saka mana Mamy ta fad'a tare da d'aukar Amer dake mata kuka tayi ciki Daren ranar da tunanin halin da Aira ke ciki Mamy ta kwana ko baccin kirki batayi ba....Aira ita ce bata tashi ba sai wajen 12 jiri na dibarta haka ta tashi tana tashi Wanka ta shiga tayi tana fitowa ta shirya cikin Atamfarta Riga da sicket cikin k'arfin hali ta shirya ganin ana kiran salla ne ya sanyata tashi ta koma tayo alwala ta tada salla harta gama tana addu'ar Allah yabawa Arman lafiya ta jima tana mashi Addu'ar neman samun lafiya tukwana ta koma Gado ta kwanta yinin ranar a rufe ta yini a d'aki ba tare da taci komai ba yunwar ma batajinta saboda tashin hankalin da take ciki Saidai idan taji kishirwa ta tara ta sha a tap d'in toilet Alh Yusuf ko sosai Rashin fitowar tata ya dameshi sau Ukku yana turawa laila takai mata abinci Saidai ta koma tace mai a rufe shi da kanshi yaje Dan yakai mata amma bata bud'e ba cike da damuwa ya yini Hajiya saude ko mamakin al'amarin nan take Gashi tana son tambayar Alh Saidai kuma tace ba ruwanta idan tayi tsami saji....washegari Aira da azababbiyar yunwa ta tashi ga ciwon kai dak'yal ta iya mik'ewa taje tayi wanka saboda yanda jiri ke d'ibarta shiryawa tayi cikin doguwar rigar lace d'inta black da yasha kyau d'inkin Street gown sosai kayan suka amsheta simple d'aurin dankwali tayi zaunawa tayi bakin Gado tare da tagumi sosai ta Lula duniyar tunani ga yunwa da take ji cikinta banda k'ululu ba abunda yake knoking Tajiyo Hakanan dai ta tashi saboda yunwa a hankali ta bud'e k'ofar Tare da Yin tsaye k'arewa Aira kallo laila ta tsayayi sosai ita kanta ta tsorata da ganin kyau irin na aira kafin ta tab'e baki ta ce "Kije Palour Daddy na nemanki " Sosai gaban Aira ya fad'i idanunta duk sun firfito kamar mai shirin yin kuka ta ce "To gani nan zuwa " Juyawa laila tayi tana Jan tsaki tana komawa Ta zauna kusa da Mamanta sai tsaki take ja "Kallonta mamanta tayi ta ce " Yadai Auta naga kin dawo kina tsaki"Haba Mama wlh Dan bakiga ba yarinyar da Daddy Ya auro ba Duka cikin gidannan ba sa anta hatta ni na girmeta nesa ba kusa ba Duka bata wuce 16to17 ba wannan ai abun Kunya ne Wlh a k'awayena ma sai sumin gori dukga mata nan manya birjik a gari amma ya rasa wacce zai auro sai wannan kamar fara da k'ilama ko fitsarin kwance bata gama ba "Girgiza kai Mama tayi ta ce " Uhm bari dai ta fito nima na ganewa idona takaici"Suna ganin shigowar Daddy sukayi shiru kallon laila yayi ya ce "ta bud'e " Cike da jin Haushi laila ta ce "Eh ta ce gata nan" Cike da farinciki Alh Yusuf ya ce "Bari naje na gani" Cike da takaici Saude ta mik'e ta ce "Ai saika dawo ka zauna ba ankira maka ita ba sai wani rawar k'afa kake gaban yaranka ko kunya" Shidai Alh baice komai ba yadawo ya zauna itama Saude ta zauna tana cika ta na batsewa Laila na wucewa Aira ta saki Ajiyar zuciya tare da Goge hawayen da ya zubo mata ko saboda yunwa yau dole ta fita gyalenta ta janyo tare da d'oroshi a Samar ka flat shues ta sanya sosai tayi kyau a haka ta fito tana tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a ciki harta Iso katoton palourn gabanta na fad'uwa tana isowa tsaye tayi tare da Kallon Matar da ta tabbatar kishiyartace sosai ta k'ara tsorata Dan girman Matar ya tsorata cike da tsoro tayi k'asa da kanta Daddy ko tunda ta shigo yake kallonta yana Kara godewa Allah da ya bashi wannan zuk'ek'iyar Matar yasan ba k'aramun sa a yayi ba cike da farinciki da annashuwa ya ce "Ki k'arasa ki zauna Baby" sai sannan Aira ta Kalleshi tsaki taja a cikin ranta ta ce "tsohon najadu kawai ba ko kunya wai baby" a hankali ta k'arasa shigowa palourn tare da zaunawa kujerar nesa dashi"baby ki matso mana nan"ya fad'a yana nuna mata Inda yake "bata Kalleshi ba Aira Haka bata matsa daga Inda take ba a hankali ta d'ago ta kalli kishiyartata cikin murya mai shirin yin kuka ta ce " ina kwana"Hajiya saude da tunda ta shigo take kallonta Sosai kyan Aira ya tsoratata amma kuma tayi mamakin yarinya k'arama da kyau da komai ta auri wannan tsohon gashi tasan mahaifinta Shima me kud'i ne bare tace Auren kud'i tayi sosai tashiga kogin tunani jin Aira na gaisheta ya sanyata saurin fusgewa ta ce "Lafiya ya bakunta" k'asa da kanta Aira tayi ta ce "Alhamdulilla" Alh Yusuf ne yayi gyaran murya ya ce "to Alhmdllh ba komai yasa na had'aku anan ba sai Dan kusan juna sannan ku had'e kanku Nunawa Aira Hajiya saude yayi ya ce " wannan ita ce Saudatu matata ce uwar gidanki kenan Ki girmamata sannan kiyi mata biyayya "Sannan ya kalli saude ya ce " ita kuma basai na miki bayanin komai ba kinsan komai abunda nakeso Dan Allah ku had'e kanku sannan ku zauna lafiya sai magana ta k'arshe maganar raba kwana kowa saita fad'a yanda takeso Ayi"cike da gadara Hajiya saude ta ce "Masha Allah yayi kyau Ango Nidai bani da matsala da kwana na bar mata nau da nata Har wata Ukku Asha amarci lafiya tana gama fad'ar haka ta mik'e cike da b'acin rai Ta bar wajen " Aira ko gabanta banda fad'uwa ba abunda take tuni harta Fara hawaye Alh Yusuf ko d'age kafada yayi yayi tare da tashi yaje ya zauna kujerar da Aira take suna gogar juna a hankali ya ce "Beauty na kinajin yunwa ko" Laila ko ganin wannan kayan takaicin ya sanyata tashi cike da b'acin rai tabi mamanta cike da masifa ta ce "Wlh akwai d'anyen aiki a gidan nan Mama Dan waccen Amaryar Area take ko uwar wa wlh wataran saina mata d'an banzan dukan da zata kasa tashi yanzu haka fa Daddy ba ko kunya Yaje kamar zai runguemeta ita kuma y'ar duniyar har wani sissine kai take " Tagumi Hajiya saude tayi ta ce "Duka zanyi maganinsu barni dasu ni nama zaci wace macen kirki ce aka auromun har ina tayar da hankalina Ashe wannan figaggiyar ce yo in tsaya kishi da wannan abar ma ai Naji kunya " Wlhko Mama ai zataci ubanta da mu take zancen Ammafa Mama naga kamar tsoro gareta bakijin yanda take magana kamar zatayi kuka "nima na kula da hakan barni dasu...Saurin tashi Aira tayi cike da tsoro Dan ta lura mutumin nan kwata kwata baida kunya tana zumburo baki " murmushi yayi ya ce "Sorry me zaki ci " Komai ma ta bashi amsa tana kauda kai Alh Yusuf da kanshi ya tashi yaje dining ya hadawa Aira break fast tukwana ya dawo cike da kulawa ya ce "na had'a maki Prince's muje " tana cika tana batsewa Aira ta tashi Bayan ta zauna a dining shi ya zuba mata yana kokarin fara bata ta mik'e tare da zare dara daran idanunta ta ce "Wai meye haka Daddy Nifa har yanzu Kallon uba nake maka meye haka d'in ka bari zanci da kaina idan ba so kake Duka na fasa cin abincin ba wlh kaiko kunyama baka da ita " ta k'arasa fad'a tana hawaye "Sorry sorry beauty kici da yawa bari ma na bar wajen tunda bakyaso yafada yana komawa palour tsaki Aira taja Dan ta tsani mutumin Chan Tare da Fara yin break fast d'inta.........✍🏿 *NI DA YAYA ARMAN it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [6/27, 22:01] Hajo hajo: 🅿️.........*67&68* ...Saida ta tabbatar da cikinta ya cika tukwana ta sha ruwa tare da Goge hannunta da tissue satar kallon Daddy tayi ta ga hankakinshi Duka yana kanta tsaki taja tare da mik'ewa tayi hanyar bedroom d'inta ya ce"Beauty bazaki zauna muyi hira ba"Tsaki Aira taja tare da galla mai harara ta ce "Kayi hira da Television badai niba kai ko kunya ma bakaji Auren y'ar cikinka mugu kawai azzalumi ka rabani da Masoyi na Allah ya isa tsakani na dakai ta fad'a fashewa da kuka tare da rugawa tayi bedroom d'inta ta fad'a Gado taci gaba da kuka Soyayyarsu da ARMAN ta shiga dawo mata cikin kwalwa tajima tana kuka yinin ranar ma a d'aki ta yini tare da kulle d'akinta bata fito taci komai ba Daren ranar ma ba irin bugawar da bai mata ba Amma taki bud'e mashi rayuwar Aira gidan Alh Yusuf cikin k'unci taci gaba dayinta Kullum tana rufe a d'aki Saidai idan taji yunwa ta fito taci abinci ta koma bata yarda tana had'uwa da mutanen gidan Alh Yusuf ko hakan sosai yake damunshi a haka har akayi sati guda Aira duk ta rame saboda zullumi da tunanin Arman da misalin k'arfe hud'u na yamma zaune take bakin gadonta tayi tagumi tunanin halin da take ciki kawai take siraran hawaye na zubo mata ita so take ko sau d'aya ne tama ji halin da Arman yake ciki amma ba hali Jiyo knoking tayi a d'akinta Kamar bazata bud'e ba saikuma ta mik'e zuwa tayi bakin Kofar ta ce " wanene"Idan kika bud'e ai zakiga wacece "Laila ta fad'a tana Jan tsoka jin Haka ya sanya Aira bud'ewa " Cike da Kallon rainin wayau Laila ta ce "Kije Palour Mama na nemanki yanzu yanzu sannan kuma batasan jira"To Aira ta fad'a tare da komawa ciki ta sanyo hijab ta d'ora doguwar rigar jikinta kasancewar me d'an d'amewar nan ce a palour ta tarar da Su mama tare da wata mata da yara su hud'u "durk’usawa ar k'asa Aira tayi ta ce " Ina yini Mama"Tsaki Mama taja ta ce "Kinga bansan kinibibi da salon barikanci a ina na zama mamanki idan na haifeki ai bakin auremun miji ba Dan haka ki rik'e sanabe da kinibibinki kina jina " Kasa Aira tayi da kanta hawaye nabin kumcinta "Zuhura ce ta ce " Kan uban Chan Amma wlh Daddy Ya gama damu daman wannan abar ce ya auro har yake wani rawar k'afa wannan ai zubda girma ne Wlh ki dubeta fa Mama da Kad'an ta girmi Intesar babbar y'ata a jikima intesar ta fita idan za a had'asu dambe saita kada ita ma.wlh me yasa Daddy zaiyi mana haka bama sa'ar autarsa ba Laila kanta fa ta girmi yarinyar nan Inma Auren zaiyi yaje ya nemu manyan mata mana wlh Mama har amfara fad'amun magana cikin kishin Sauri na wai ubana ya auro sa ar jikarshi wannan ai raini ne Daddy Ya saya mana wlh "ta karasa fad'a cikin Masifa " Dariya mama tayi ta ce "Kema kya fad'a Zuhura ai tunda har ta iya Aure mun miji Saidai ta zama y'ar boyi boyi na amma nafi k'arfin nayi zaman kishi da wannan abar "Aira dai na jinsu Goge hawayenta tayi cikin ranta ta ce " Da kunsan yanda na tsaneshi da bakun fad'a haka ba ni kaina a ra ayin kaina ina zan auri ubanku sosai takejin da tana da dama da saita fad'a musu magana amma ita harga Allah tsoronsu take Dan karsu jibgeta a banza "Tsawa Mama ta daka mata ta ce " d'ago ki kalleni Munafuka cikin rud'ewa Aira ta d'ago hawaye na bin k'umcinta "ki bud'e kunnanku ki saurare ni da kyau Daga yau babu Wanda zai Kara maki girki kici a gidan nan kamar yanda kikasan Aure Har kika auremun miji to haka zaki saki jiki kiyi aiki daman na Daga maki kafane na sati guda Dan haka daga yau zaki Fara girkinki kina jina" Cikin rudewa Aira ta ce "Eh naji" yawwa to yanzu tashi ki Mike ki shiga kitchen ki girka mana abincin Dinner"Mikewa Aira tayi ta ce "Me za a girka tsaki Mama taja ta ce " tuwo zakiyi mana da miyar agushi"Kamar zatayi kuka ta ce "Wlh Mama ban iya ba kidai fad'a wani abun" Ohhh baki iya ba Aiko yau zaki koya ai Aure kikazo ba Hutu ba saiki koya daga yau"Kuka Aira ta fashe dashi Sakato duk sukayi suna kallonta cike da mamaki Zuhura ta ce "Ikon Allah wai kodai Reno ne Daddy Ya kawo maki Mama bamu saniba" Tsaki Laila taja ta ce "wani salon barikanci ne" Mama Tsawa ta daka mata ta ce "Dukanki nayi da zaki yimun kuka Munafuka" girgiza kai Aira tayi da goge hawayenta cikin muryar shagwabar da ta zaune mata ta ce "To yi hakuri Mama Allah ban iya tuwo ba karnayi kuma ba daidai ba kimun fad'a" Tsaki Mama taja ta ce "Jeki dafa shinkafa da miya" To Aira ta fad'a tare da Goge hawayenta tayi hanyar kitchen Dariya Zuhura ta fashe da ita ta ce "Ai inaga nan gidan zandinga zuwa kallon drama Mama wannan ai fitar da ita gidan nan Abu me sauki ne bakiga yarinya ce kuma matsoraciya wannan ai ba kishiya ba Daddy Ya kawo maki y'a ce sai yanda kikayi da ita" murmushi Hajiya saude tayi ta ce "Zuhura kenan Ai kishiya kishiyace Zandai gyara musu Zama danma karkiga yanda Daddynku ke rawar k'afa a kanta ke daga zuwanta fa harya fara sauyamun saina fad'a magana ya take kingako ai matsala ce ta shigomun gida" haka dai suka cigaba da tattaunawarsu akan Aira Aira ko Tana shiga kitchen din aiki ta fara ba kama hannun yaro tanayi tana kuka Dan ita bata saba da aikin wahala a gida ba tunda Maid house ke masu Saidai wani karin Mamy ta ce tazo ta tayata Dan ta koya mata kafin magriba ta gama komai sai huci take tana hada zufa tana gamawa tahau Jerawa a dining Hajiya saude na kallon shige da ficen ta murmushin mugunta kawai take Dan da gangan ta kori me aikinta saida Aira ta gama Jerawa sai sauke numfashi take tukwana taje ta zauna Kan sopa tana sauke numfashi ta ce "Na kammala Mama" Kallonta Mama Tayi ta ce "Sannu " yawwa Aira ta fad'a tana niyyar tashi Mubarak ya shigo da earpiece a kunnenshi yana tafiya ta y'an duniyar nan "tunda ya shigo ya kafe Aira da idanu harya zauna yana kallonta Wow she's Beautiful babe Mama ina kika samo mana me kyau haka" Aira jin Haka sosai gabanta ya fad'i Mikewa tayi cikin Sauri tare da Kallon Mama ta ce "zan shiga ciki" okay kije "Haba beauty ya zaki tafi kuma bamu gaisa ba " ya fad'a yana karkace baki Kallonshi Aira tayi ta kalli Mama dake aika mishi da harara batare da tace uffan ba ta wuce ciki har tuntube take Dan Sauri tana zuwa ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Ohh nima Allah ya kawoni Allah ka fitar dani daga halin nan da Nike ciki sannan ta fashe da kuka ta ce " Yaya Arman ina kaje kadawo please ga airanka nan cikin wani hali karka manta alk'awarinmu"ta k'arasa fad'a tana rushewa da kuka tana kuka taje tayi wanka tayi salla tana ta addu'ar Allah ya kawo mata sassauci Aira na barin palourn Mubarak ya bita da Kallo har wani Had'iye yau yake Kallonshi Mama tayi cikin b'acin rai Ta ce "Bansan iskanci Mubarak Meye haka" Mama please wacece wlh tana da kyau nidai tayi mun ina sonta plx Mama ina kika samota ko y'ar uwarmuce ban saniba Kai cikin danginku babu farare Mama Plx ina kika samota "Wani irin kallo ta watsa masa ta ce " To ka nutsu tun wuri ma ka kama kanka Amaryar Daddynku ce"what Mubarak ya fad'a yana mikewa ya ce "Wai Mama kina nufin wannan itace amaryar da Daddy Ya auro kai amma wlh Daddy nidai ya cuceni wannan ai dani ta dace ba shiba yayimun shigar Sauri Gaskiya nidai sonta nake" Wlh babu ruwana Mubarak tun wuri ka kama kanka kasan Daddynku ya ji maganar nan ba k'aramun hukunci zai yanke maka ba Sannan karna karajin ka fad'i Kalmar kana sonta kasandai ko sakinta Daddynku yayi babu Aure tsakaninku Dan Haka karna karajin haka ta fito daga bakinka"Cike da jin Haushi Mubarak ya Mike yana gunguni tare da barin palourn yana sharce kanshi da masharcin dake mak'ale cikin sumarshi Haka rayuwa taci gaba Aira kullum cikin k'unci take ga aikin abinci da take azabtuwa Dan Hajiya saude har girkinta Aira take sanyawa tayi mata ita kuma Aira na tsoro dole haka zata dirtsawa katti abinci wani lokacin ma ba ci take ba kullum Saidai ta yini d'aki tana kuka gashi Hajiya saude ta ce ta sake ta fad'awa Daddy tana aiki ita kadai tasan abunda zata mata abun duniya duk ya isheta ga Mubarak da yake takurawa rayuwarta shiyasa yanzu ko Kad'an bata fitowa Daddy ko saita kwana biyu bata ganshi ba Dan har yanzu kulle d'akinta take tabar key din jiki Daddy kullum cikin damuwa yake Dan ko Kad'an Aira taki sakin jiki dashi ko tana palour da taga shigowarshi zata maza ta koma daki ta kulle kamar dodo hakan ba k'aramun damunshi yake ba a haka dai da dad'i ba dad'i har Aira tayi wata guda a gidan Wanda cikin k’unci tayishi Dan Hajiya Asabe da y'ay'anta sosai suke musguna Mata Saidai tayi kuka ta gode Allah duk ta rame lokaci guda Yau Aira ganin Daddy Ya fita wajen la asr ya sanyata fitowa Farfajiyar gidan Sai sannan take karewa gidan kallo tana nan zaune sanye take cikin atamfarta mai golden doguwar Riga rigar ta d'an dameta kallabi kawai ta yafa Mubarak ne ya shigo gidan tunda ya hangota ya sauke ajiyar zuciya Dan Yajima bai gantaba sosai yake kallonta yana k'ara yaba kyau da zubin halitta irin tata harya karaso kusa da ita ya zauna Aira da batasan da wanzuwarshi ba saida taga zaman mutum kusa da ita ya sanyata Juyawa ido hud'u sukayi Da Mubarak gabanta na fad'uwa saurin matsawa tayi murmushi yayi ya ce "Ina yini Auntynmu" Harararshi Aira tayi tare da turo baki "Y'ar Dariya yayi ya ce " tofa Aunty daga gaisuwa sai harara"Kallonshi Aira tayi saikuma ta ce "Lafiya" Yawwa ko ke kefa beauty hutawa kike kenan"ba tare da Aira ta Kalleshi ba ta ce "ummmmm" nan Mubarak yayi ta janta da hira tana kaucewa tun tana harararshi tana fad'a mashi magana harta dawo tana Dan maida mas dan takula Dan naci ne kuma ga alamu duk cikin gidan ya fisu mutunci cikin hirar ne ya ce "Amma na tambayeki mana Aunty" inaji"Aira ta fad'a cike da kosawa Dan ta fara gajiya da surutunshi "Dan Allah wai garin ya kika auri old man d'innan yanda kike da kyau da diri d'innan me ya kaiki Auran tsohon mutumin nan Allah yayi miki kyau da fari kamar baturiya aike matar Manyan Yara ce masu jini a jika y'an tashe ba tsaffi ba " Cike da mamaki Aira ta juyo tana Kallonshi ta na mamakin wai ubanshi yake fad'awa haka Sai sannan ta lura da tsaf d’an duniya ne ma "tsaki taja tare da cewa " Saikaje ka tambayi shi uban naka ya baka amsa"Daddy ne tunda ya shigo yake kallonsu Yasan sarai halin d'an nashi cikin zafin nama ya nufi wajensu kallon Mubarak yayi ya ce "Ubanme kake A nan " Tashi yayi yana wani babbasarwa ya ce "Hutawa nake Nida Beauty " Daukeshi da Mari Daddy yayi cike da b'acin rai ya ce "Matar tawa Dan ubanka d'an iska to wlh na k'ara ganinka kai da ita ni kad'ai nasan Abunda zan maka xakaja in koreka daga gidana " Sannan ya kalli Aira tare da daka mata Tsawa ya ce "Wuce ki koma ciki" Aira sarkin tsoro tuni ta rud'e tare da rugawa tayi ciki Dan yanda taga ranshi ya b'aci kamar zai daketa tana shiga da gudu ta fad'a d'akinta sai huci take kulle d'akin tayi tare da kwancewa ta fad'a Gado tare da fashewa da wani irin kuka mai cin rai ta ce "Yaya Arman ina kashiga ka barni har tsawon wannan lokacin yaya idan baka dawoba zan iya mutuwa ka dawo Ina cikin wani hali yaya ina cikin begenka yaya kazo ka fitar dani daga rayuwar k'uncin nan ina cikin wani hali yaya ba uwa ba uba ba d'an uwa a kusa dani sannan babu kai........✍🏿 _*Miss Hajo Ce*_🤙🏿 [6/29, 14:10] Hajo hajo: 🅿️.........*69&70* ......Sannan kuma Babu kai yaya Ya kukeso nayi da rayuwata ne Wai sosai take kuka tana cikin kukan ta jiyo bubbuga k'ofa Banza tayi ganin yanda ake buga mata da k'arfi ne ya sanyata Jan tsaki ta ce "waye wai" Nine kizo ki budemun kuma wlh kika bari na balle k'ofar na shigo da kaina zakisan sauran"Wara idanu Aira tayi jin muryar Daddy saikuma ta mik'e tare da dauro jarumunta kama k'ugu tayi ya ce "idan kuma nak'i bud'ewar saikayi me" Ki bud'e nace na fad'a maki"Bud'ewa Aira tayi tare da ja da baya Cike da b'acin rai Alh Yusuf ya shigo Aira ko ja baya tayi sosai gabanta ke fad'uwa amma ta fusge"na k'ara ganinki ke da Mubarak ko Wani Abu ya had'aku ranki zaiyi mugun b'aci kina jina"Kallonshi Aira tayi daga sama har k'asa taja tsaki ta ce "da Allah Malam in ka gama zaka iya fita ni ina da aikinyi"kwantar da murya yayi ya ce " Wai meke damunki ne Beauty kin manta ni mijin kine aljannarki tana k'ark'ashin k'afata idan na take bazaki shiga ba meyasa kikemun Rashin kunya ko ba wannan ba aikin darattani Dan girmana da kuma matsayina na abokin mahaifinki"iyeeee Aira tafada tana kama hab'a tare da mashi wani irin kallo ta ce "anzo wajen to kai bakaji kunyar Aure na ba matsayina na y'ar cikinka sai nice zanji kunyar gaya maka magana ai wlh tunda harka nace ka Aure ni ka rabani da Masoyi na to ba wani sauran mutuncinka a idona ya Riga ya zube sannan kuma ni Aljannata bata k'ark'ashin k'afarka in kaga dama ma ka take tana k'ark'ashin k'afar yaya Arma.....Kasa k’arasa maganar tayi sakamakon Rufe mata baki Alh Yusuf da yayi tare matseta jikin Bango cikin zafin rai ya ce " Karna sake na k'arajin kin Ambatarmun sunan wani kato a cikin gida na sannan Aurenki da nayi aiba haramun bane raya sunnanar ma'aikice zaki dinga daukarwa kanki zunubi a banza sannan shi kanshi rufemun k'ofa da kike ba k'aramar azaba kikesha ba sanine bakiyi ba Ga kuma hak'k'ina dake kanki tsawon lokacin nan nayi Aure amma Nida Wanda banyiba duk d'aya muke d'aga miki k'afa ne kawai nake bawai Rashin kunyar da kikemun bace tasa na kyaleki a yau naga damar amsar hakkina dole na amsa kota tsiya ko ta arziki"gwalalo ido Aira tayi a lokacin da za a auna jininta to yahau d'ari Ukku kirjinta in banda dabdab ba abunda yake a zuciyarta ta k'ara jinjina lamari na Alh Yusuf lallaima baida kunya wlh wai haryake mata maganar wani hakki sosai tsoro ya kamata Dan a duniya bata da burin da ya wuce ta kaiwa Arman budurcinta ba wani banza ba Hakan ya sata tsorata Dan tayi alk'awarin ko zata mutu Bazata tab'a bawa wani budurcinta ba Bayan yaya Arman kwantar da murya tayi cikin muryar tausayi ta ce "Dan Allah kayi hakuri Daddy bazan sakeba na daina Dan Allah tadani numfashina na daukewa" Matsawa Alh Yusuf yayi daga jikinta ganin haka ya sanya Aira saurin tashi tare da matsawa "Kallonta yayi ya ce " Daga Yau karki sake kulle d'akinki kinji na fad'a maki ba kulle d'akin zaisa nak'i miki abunda nayi niyya ba "Cikin tsoro Aira da har tafara hawaye ta gyad'a mashi kai ta ce " bazan sakeba Daddy amma Dan Allah bazakamun komai ba idan na bari a bud’en "Murmushi yayi Dan sosai yarintar Aira ke burgeshi komai yarinyar tayi burgeshi yake cike da kulawa ya ce "Ba abunda zan maki Amma kidainamun rashin kunya Kinsan dai ba kyau yiwa na gaba dakai rashin kunya ina son ki saki jikinki da ni da mutanen gidan nan d'in gidankine banason d'ari d'arin da kike banajin dadi ko ana k'untatawa maki idan bana nan idan ana maki wani abun fadamun" Ajiyar zuciya Aira ta sauke ta ce Bazan sake maka Rashin kunya ba daga yau Daddy ba abunda akemun "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " ba abunda kike buk'ata"Hawaye na bin k'umcinta Aira ta ce "Bakomai Daddy amma Dan Allah Dan girman Allah Dan darajar fiyayyan Halitta ka sakeni na koma gidanmu Dan soyayyarka da manzon Allah " kallon baki da wayau Yayi mata ya ce "idan kina wannan mafarkinma ki daina ban aureki Dan na sakeki ba Karki k'ara rokata akan wannan idan kina buk'atar wani Abu ki dinga sanar dani yana gama fad'ar haka yabar d’akin durk'ushewa Aira tayi a wajen tare da fashewa da kuka mai cin rai....Inna koda ta dawo daga Umrah ta samu wannan Bak'in Labarin sosai ta shiga surfa ruwan masifa da bala'i Kuka ko ta shashi ba iyaka tsare Abba tayi da masifa akan saiya kaita ta taho da Aira shidai Abba banda lallashi ba abunda yake sosai Inna ta tubure ta rude jin y'an lelen nata Duka biyun na cikin wani hali Kuka ta dinga rafsawa tare da had'a kayanta ta ce " Garin zata bari Bazata cigaba da chusar bak'inciki ba Duk yanda Abba yaso ya shawo kan Inna kasawa yayi da kyal dai saida ya had'a da dangin Abbansu ana ta bata hakuri tukwana ta hakura ta zauna Amma kullum saitayi mita da kukan kewar Arman da Aira shidai Abba Saidai yayi ta Lallashinta Dan ba yanda ya iya....Mummy saida tayi sati Ukku a gida batare da Abba yaje ba Sosai hakan ya b'atawa Yayanta rai Itako kullum da tunanin zullumin halin da y'arta take ciki take Dan ko ta Abba batayi...Abba dai ganin Abun na Mamy ba mai ci ba mai cinyewa bane A daddafe yayi kwanakinnan ba tare da ita ba Ganin zaiyi sakakka ya sanyashi shiryawa cikin sati na hud'u yaje bikon Mamy Sosai Yayanta ya nuna mashi rashinjin dad'inshi da kyal dai Abba ya bashi hakuri ya sauko kiran Mamy akayi Dan ayi musu sasinci tana zuwa ta ce "Yaya nidai ba wani sasinci kawai yabani takardata daman ai yace zai biyoni da ita " Kallon baki da hankali Abba ya mata yo ko giyar wake yasha ya saketa ina zai samu kamarta ga kyau ga tsafta ga gayu ga yanda take da d'an jikinnan ba a tab'a cewa ma ta haifi kamar Aira sai ace Amer ma shine d'anta na fari Dan saika rantse bata jima da Auren fari ba Ai ya saketa tuni wani zai aureta Kwantar da kai yayi ya ce "Babu saki A Aurenmu Rahama mutu ka raba insha Allahu idanma nayi miki laifin kiyi hakuri ki shirya ki koma d'akinki" Jin haka ya sanya Mamy yin sanyi Da Abba da Yayanta suka sasinta abun Yayanta yacewa Abba "ta fad'amun ta ce batajin dad'in zaginta da kake gaban kowa Dan Allah ku daina ba girmanku bane Alh kusan kun girma wannan ai Saidai yara ku masu yiwa wasu fadane" nan Abba ya shaida mashi Bazai sakeba umarta Mamy Yayanta yayi da taje ta shiya tabi mijinta su tafi Bayan yayi mata fad'a akan karta k'ara magana akan duk hukuncin da zai yankewa y'ay'anshi ba ruwanta yaranshine shike da hakki a kansu "insha Allahu bazan sake ba yaya "Mamy ta fad'a cikin ladabi a ranar Abba ya mayar da Mamy a mota ma sai cika take tana batsewa shidai ABba in Banda Lallashinta ba abunda yake.. Yau Aira na kwance a d'aki tana karatun alk'urani Dan yawaicin kwanakin nan kullum shi take karantawa kuma sosai takejin damuwa da kadaicinta sun ragu Laila ce ta shigo ta shaida mata Mama ta ce taje Mikewa tayi tare da ninke Quran din ta bi Bayan Laila tana zuwa Bayan ta gaishe da Mama ta amsa mata ba yabo ba fallasasa sannan ta ce " Daman aikine zaku shiga kitchen Kuyi tare ke da laila na musamman Sadiq ne zaidawo yana hanya yanzu haka daga Paris kuyi mashi komai na musamman plx"To Mama Aira tafada tare da tashi a tare da Laila suka shiga kitchen suka fara girke_Girke kala_Kala sai wajen la'asr suka samu suka gama Wanda Aira duk ta gaji tana gamawa ta fad'a d'akinta Tare dayin wanka Ta shirya cikin lace d'inta riga da sicket da yasha d'inkin zamani.... Arman jikin nashi ba acewa komai sai Alhmdllh Dan kullum cikin samun sauk'i yake dukda har yanzu bai farfadoba tsawon wata guda kenan Saidai komai a mashi danma ya gamu da kwararrun likitoci Mummy ta kasance a wajenshi yayinda Daddy yake komawa 9ja Duk weekend yake zuwa yaga jikin nashi Bayan a nan ma ya rabawa malamai mak'udan kudi akan su tayasu addua Allah yabawa d'an nashi Lafiya Yau Akesa ran farkawar Arman Wanda Mummy tun safe take zumudi ta kasa matsawa daga Inda yake Wajejen 6Pm Arman ya farka Wanda jinshi yake tamkar wani sabon mutum Mummy ganin yayi motsi ya sanyata matsawa kusa dashi cikin farinciki marar musaltuwa ta kama hannunshi ta ce "My son ka farka ka tashi ka kalleni mummynka ce " A hankali Arman ya fara bud'e idanuwanshi da sukayi mashi nauyi yana bud'ewa ya maza ya maidasu ya rufe "Alhamdulilla Allah na gode Maka Mummy ta fad'a tana daga hannu sama nan likitoci suka shigo suma sosai sukayi hamdalar farkawar ta Arman Dan Gaskiya su kansu sunsha tsananin fama akan wannan ciwon nashi Dan su kansu basuyi tunanin zai tashi ba Dan wad'anda zuciyarsu har takai stage d'innan ba lafiya tashi ba congratulations sukayiwa Mummy Akan farkawan yaron nata Dan su kansu sun yaba da irin k'auna da soyayyar da Mummy ke yiwa Arman Cikin farinciki Mummy ta kira Daddy tayi mishi wannan Babban Albishir Ai Daddy farincikin da ya shiga bai musaltuwa a lokaci ya mike tare da cewa a shiryamai tafiya Egypt Arman ko jinshi yake kamar bashiba Abubuwan da suka farune suka dinga dawomai ji yake tamkar a mafarki Mummy ce ta ce " son ka bud'e idonka ka kalleni mummynka ce"jin haka ya sanya Arman bud'e idanuwanshi ya kalli Mummy Rungumeshi Mummy tayi cikin farinciki ta ce "Alhmdllh Allah abun Godiya Allah ya k'ara maka lafiya my son " Gyad'a mata kai kawai Arman yayi Dan bayajin zai iya wata doguwar magana Tea me kauri Mummy ta had'a mashi da taimakon Dr da sukazo tare da shi suka tayar da Arman a hankali Mummy ta shiga bashi tea din Arman na kurba kamar wani k'aramun yaro yasha sosai Inda hakan yayiwa Mummy Dad'i Kallonshi tayi ta ce "ba abunda kake buk'ata son" Gyada mata kai kawai yayi tare da komawa a hankali ya kwanta "Ba wacce ta fad'o masa a rai idan ba Aira ba ?Ta na Ina?wani hali take ciki?Shin tsawon wani lokaci ya d'auka kwance?Kallon Mummy yayi da murmushi yaki barin fuskarta Nuni ya mata da ta matso yanason magana da ita cikin Sauri Mummy ta matsa tare da Kara kunnanta a bakinshi ta ce " me kake so kace son"Kamar mai koyon magana Arman A hankali ya ce "Mu m my I na A ira?Sosai gaban Mummy ya fad'i idonta tane suka cicciko da hawaye Mikewa tayi tare da girgiza masa kai tana hawaye ta ce " Karkamun haka ARMAN ni mahaifiyarkace nafi kowa so da Kaunarka karka k'ara komawa cikin wani hali a saboda ita Arman ina sonka sosai ina buk'atar rayuwarka fiye da komai dake cikin duniyar nan nasha wahala a Rashin lafiyar nan taka tsawon wata guda kenan Arman Karkamun haka karka k'ara komawa cikin wani halin a saboda ita plz son "Arman sai yaji tausayin mahaifiyartashi ya Kamashi kama hannunta yayi tare da girgiza mata kai alamar tabar kuka sannan ya lumshe ido ya bud'e tare da sakar mata murmushi Alamun bazai Kara shiga wani halinba " Ajiyar zuciya Mummy ta sauke tare da zaunawa ta ce "Nagode my son Allah yayi maka albarka ya jikin naka yanzu bakajin komai" ameen ya fad'a a hankali Dan magana yanzu wahalar masa take Sannan ya jinjina mata kai Alamun ba abunda ke idanunshi...... da misalin takwas na dare zazzaune suke a Babban pourm gidan Har Aira Dan itama tanaso taga wannan sadiq din da ake ta rid'in zuwanshi taga har daddyma sai Farinciki yake tana cikin wannan tunanin tajiyowa sallamarshi "badai ta d'ago idontaba har Taji shigowarshi sai Sannu da zuwa ake mai ana oyoyoy yana amsawa cikin barkwanci sosai Aira gabanta ya fad'i jin muryar kamar ta tab'a sanin me ita D'aga idanunta tayi Dan tabbatarwa da abunda kunnanta ya jiye mata tana d'agawa idonta karaf ya had'e Dana sadiq dake kallonta Shima a tare suka wara idanu musamman Sadiq cike da mamaki ya ce " Aira.......✍🏿 *Ni da yaya Arman it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/29, 15:40] Hajo hajo: 🅿️.........*71&72* .......Ya ce “Aira ”kallon mamaki Aira ta dinga binshi dashi ba tare da ta ce uffan ba sai k'asa da kanta da tayi"Sadiq ne ya kalli Mama ya ce "Mama a ina kika San Hajara" Kunsan juna ne daman? Mama ta bashi amsa"Sani ma kai Mama ita ce wacce na dinga baki labari lokacin zuwana kano budurwar da nayi ina sonta sosai Mama dalilin wannan tafiyar nema da nayi Yasanya ban kuma waiwayartaba amma daman niyata ina dawowa zan tashi daga Inda na tsaya Kinga Allah ya kawomun ita har gida garin yaya mama a ina kuka Santa"Tirk'ashi Mama ta fad'a tare da Kallon Daddy da ya had'e gidan sama data k'asa Sadiq ta Kalla ta ce "To ka kiyaye kanka ita ce Amaryar babanka "what Sadiq ya fad'a yana Mikewa ya ce " me kikeson kicemun Mama kina nufin daman Aira ce Daddy Ya auro"Ga Kat kuwa ka gani Dan haka saika nemi wata ubanka dai ya kasaka"Kallon Aira sadiq yayi duk mamaki ya gama kulle mashi kai ya ce "Garinya Aira kika auri tsoho me yasa tun lokacin da nace inasonki kika k'i amincemun meya kaiki Auren sa an babanki Aira dan bakisan kalar son da nake maki ba....cike da masifa daddy ya ce "Banson iskanci Sadiq na k'arajin makamanciyar Kalmar nan a bakin ka a gidan nan wlh ranku zaiyi mugun b'aci Nakarajin ka k'ara danganta Kalmar so mata ta zakusha mamakin abunda zan muku " Aira kamar wacce kwai ya fashewa haka ta tashi al'ajabi duk ya gama cika mata kai kenan mahaifin Sadiq ne Aka auramata chabdi A zuciyarta ta ce "Allah yasa daman banyi wata soyayya dashi ba Chan ta matse musu wahalallu wucewa bedroom d'inta tayi batare da ta kuma waiwayar suba harta b'acewa Sadiq gani yana kallonta cike da bala I Daddy Ya ce " Na rantse da Allah Na kusa korarku kaida Mubarak daga gida na ku duk iskancinku akan matata ma ya k'are kaida nake maka kallon mutumin kirki shine kaima zaka b'ullo da wani sabon iskancine to wlh ko kallo karna sake ganin Wanda ya kuma kallonta tunda ku mutanen banza ne"Sakato saude tayi tana Kallonshi ta ce "Ikon Allah to saika kori Y'ay'anka saboda mace Sannu salamamme to wlh karka k'ara aibantamun y'ay'a d'iyan kirki y'an albarka Chan kuje ku karata da amaryarka amma kar a sakamun y'ay'a"a bakin duniya" Tsaki Daddy yaja tare da mik'ewa "ya ce aina fad'a muku dai kuci gaba kuga hukuncin da zan yanke" Yabar palourn cikin fushi Sadeq ko ya jima yana mamakin wannan al'amarin har saida ya goge hawaye dan ba karamun so yakeyiwa aira ba abunda aka shirya mashi dinma dak'yal mama ta lallabashi yaci danshi wannan zuwan nashi bai mashi dad'i ba Aira ko Tana komawa salla tayi ana kiran isha I ma tayi tabi ta haye Gado Dan daman baccin gajiya ya kwasheta washegari itace bata tashi ba sai Takwas Sosai tayi mamakin makara Sallar asuba da tayi abunda bata saba ba Cikin gaggawa Tai salla tayi wanka ta fito kenan Daga wanka jikinta daure da towel ta tsaya jikin mirror tana busar da gashin kanta Daddy Ya shigo tunda ya shigo ya kafeta da idanu bako k'iftawa har wani Had'iye yau yake Aira na juyowa sukayi ido hud'u dashi Ai batasan sanda ta fasa uban k'ara ba tare da durk'ushewa a wajen Matsowa Alh Yusuf yayi ya ce "Subhanallahi meke faruwane beauty ko wani abun ne ya sameki" Kuka Aira ta fashe ta ce "Dan Allah Daddy ka fita" Sakato yayi yana kallonta ganin yana Matsowa Kamar zai Rungumeta ya sanya Aira kwasar k'afarta a guje ta koma toilet tare da rufewa ta sanya key Huci kawai take tare da dafe k'irji ta ce " nashiga ukkuna ni Aira " Alhaji Yusuf ko girgiza kai yayi tare da barin d'akin dukda ba haka yasoba Dan a yanda yaga Aira sosai ta rud'ar dashi yaso ace ko rage zafi ne yayi Aira tafi minti Talatin a toilet saida taga dai da gaske yabar d'akin tukwana ta lek'o tana ganin bainan ta sauke ajiyar zuciya Tare da fitowa ta maza ta je ta rufe d'akin sai huci take kamar wacce tayi wani aiki Cikin Sauri ta shirya daman tunda tazo gidan ba make up take ba ko hoda bata shafawa Turare kawai ta fesa sannan ta yafa beil din doguwar rigar a sanda ta fito daga d'akinta Takoyi sa a laila kad'ai ta tarar a palour zaune a kan sopa earpiece mak'ale a kunnenta tana bin wak'a Hartaje tayi break fast ta dawo palourn tana zaune Inda ta barta zaunawa Aira tayi tana son ta tambayi Laila ta ara mata wayarta ta kira Mamy tana tsoro tad’au minti ashirin zaune tana sak'e sak'en dak'yal dai ta tattaro jarumta ta ce "Laila Dan Allah wani taimako zakimun" Kamar bazatayi magana ba Saikuma ta cire earpiece d'in ta ce "Ina jinki" Kamar mai shirinyi kuka Aira ta ce "Dan Allah wayarki nake so ki aramun zan d'anyi kira minti biyu inba damuwa" Kallonta Laila tayi sama da k'asa kamar bazata bataba saikuma ta Mik'a mata ta ce gashi"Cike da farinciki Aira ta ce "Nagode sis " Tab'e baki Laila tayi tana wani girgiza k'afa "Aira na amsar wayar Number Arman ta fara dialing Tajita kashe sosai taji wasu hawaye sun zubo mata Goge number tayi tayi dialing number Mamy Tare da karawa a kunnenta " Ringing Biyu Taji an d'aga Daga bangaren Mamy ta ce "Assalamu alaikum" Wani sanyi Aira taji a ranta jin muryar mahaifiyar tata tsawon wata guda kenan bataji muryarta ba tuni hawaye sun wanke mata fuska tama kasa magana "Mamy ce ta k'ara cewa Hello Yadai an kira anyi shiru" Cikin shashekar kuka Aira ta ce "Mamy...Ai Mamy Mikewa tsaye tayi jin muryar y'artata cike da farinciki ta ce " Aira ta kece kuwa "Cikin Kuka Aira ta ce " Nice Mamy "kina lafiya kuwa Naji muryarki haka Aira ko bakyajin dad'in zaman" Kuka Aira fa fashe dashi kamar wacce akayiwa mutuwa "Sosai hankalin Mamy ya tashi cikin damuwa ta ce " Karki k'ara tayarmun da hankali please daughter me yake damunki kukan me kike maimakon ki kwantarmun da hankali Aira ko so kike jini na ya hau"cikin shashekar kuka Aira ta ce "Mamy Please kizo ki tafi dani Dan Allah Mamy nasan ke kina sona" Dafe goshinta Mamy tayi ta ce "To Naji amma fad'amun ba abunda ya faru dake are you okay dear ko wani abun ake maki a gidan" Girgiza kai Aira tayi kamar tana gabanta ta ce "a a a Mamy nidai gida nakeso bazan iya zama a nan ba Dan Allah Mamy kizo ki tafi dani"ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka " Itama mamyn hawaye take amma Dan son kwantarwa da y'artata hankali ta ce "Ki kwantar da hankalinki daughter Allah na tare damu ki dage da addu'a kinji sannan idan kinsamu waya ki dinga kirana Inajin muryarki ko Naji sauk'i damuwar dake tare dani Kidaina tayarmun da hankali ko so kike hawan jini ya kama mamyn naki ta mutu" Cikin Sauri Aira ta fara Goge hawayenta tare da girgiza kai ta ce "A a a Mamy Nadaina banason komai ya sameki " To kidaina kuka kinji ki dinga addua itace takobin mumini"To Mamy bazan sakeba Mamy ina Haidar da Aunty Aysha Da Amer nasan yanzu Amer ya manta dani"Haidar yana school Amer gashinan yana wasa Waneshi wane mancewa da Babbar yaya yana nan yana kewarki Aysha Da kowa Duk suna lafiya""Murmushi Aira tayi tanajin wani sanyi Cikin zuciyarta jin muryar mahaifiyartata a hankali ta ce "Ki gaishemun da su Mamy sai anjima karna cinye mata credit"" zasuji wayar wacece kika samu"cikin k'asa da murya Aira ta ce "ta y'arshice" Okay to sai Anjima ki dinga kirana kinji Allah maki albarka "Ameen Mamy nagode I miss you" Miss you too daughter ki dinga kulamun da kanki kinji"murmushin da Aira tajima batayiba tayi ta ce "Nima ki kulamun da kanki kinji Mamy na" Tukwana sukayi Bankwana Laila duk tana jinsu gwanin burgewa take kallon Aira Aira na gama wayar murmushi tayi mata ta ce "Gashi sis nagode" Itama murmushin Laila ta sakar mata ta ce "DM Dear Amma na tambayeki mana Dan Allah" Sosai Aira tayi mamakin yanda Laila yau tayi mata murmushi cike da kulawa ta ce "Inajinki" Dan Allah Ko zaki d'anban labari sai a kwanannan na lura da kamar bakya son Daddy Kuma Naji kina waya nasan mamankice akan tazo ta tafi dake""Murmushin takaici Aira tayi tare da Goge hawayenta Ta ce "Banason Tuno da labarin da ya wuce kamar zan k'ara fama raunin da yakasa warkewane a cikin zuciyata " Dan batajin zata fad'awa wani cikin gidan sirrinta Dan bata gama sakewa dasu ba"kad'a kai kawai Laila tayi ta ce "Shikenan badamuwa" Nagode Aira ta fad'a tare da tashi"ta koma bedroom d'inta Aira na barin wajen Laila d'akin mamanta taje ta ce "Mama wai kin lura da abunda na lura kuwa Amaryar Daddy fa kamar batason Daddy sainakega kamar ma ba da son Ranta ba akai auren nan ta bata labarin maganar da taji Aira tayi da Mamanta" Hajiya saude ce ta ce "Nima na lura da hakan koma dai meye idan tayi tsami Maji.....Arman tundaga lokacin nan yaci gaba da samun sauki amma har yanzu tunanin Aira na nan mak'ale a cikin zuciyarshi tausayin mahaifiyarshi ya sanyashi fara Rage damuwa a ranshi ana samun cigaba sosai Dan yanzu har yana Mikewa yayi sallah dukda a zaune yakeyinta Magana ce dai ba Sosai yakeyiba a zaman arman asibiti Daddy sun kashe kud'i sun haura 30 million's sati biyu da Farkawar Arman aka Sallamesu dan jikin nashi Alhmdllh Bayan ambasu magunguna ankuma fad'a musu dokokin da zasubi Dan kula dashi Arman jinshi yake cikin farinciki Dan tunda ya farka ya gaji da zaman Asibitin ga kuma farincikinshi na komawa k'asar da sahibarshi take Dan yayiwa kanshi alk'awarin ko birnin sin Aira take saiya nemo ta.........Alh Yusuf sosai ya fara gajiya da Abubuwan da Aira take mashi duk yanda yaso ko d'an rage zafi ne yayi da ita amma ta kafe tak'i yarda ko yatsanta ya rik'e yaudai ya gaji wata kusan biyu da Aure amma Ba abunda ya shiga tsakaninsu da Ita hakan yasa yad’au D'aurarriyar aniyar kota arziki kota tsiya saiya Nemi hakkinshi.....da misalin Sha d'aya na dare Aira harta kwanta bacci Dan yau a gajiye take ta mantama ko rufe d'akin batayi ba Alh Yusuf sosai yayi hamdala lokacin da ya zo d'akin Aira ya ganshi a bud'e hamdala yayi tare da shigowa ganin tana bacci ya sanyashi murmushi Ya ce "Yau Ranar tawace komai yazomin a sauk'ak'e daga yaudai beauty Zamu zama d'aya Cikin Sauri ya cire babbar rigar jikinshi cikin sand'a ya haye gadon Tare da janyota a hankali ya fara sarrafata cikin wani irin salo Aira cikin bacci takejin Abu kamar a mafarki ga wani nauyi da takejin an hayeta Jin Abu nayin gaba Ya sanyata farkawa koda ta farka taga mutum a kanta ihu ta fasa iya k'arfinta ta ce " wayyo kwart.....saurin rufe mata baki Alh Yusuf yayi ya ce "Ba kwarto bane nine mijinki"wara idanu Aira tayi tuni harta Fara kuka ta ce "Daddy me keke shirinyimun na shiga ukku Dan Allah ka rabu dani ka tadani wayyyo ni Aira shikenan na mutu'" K'ara mirginawa Alh Yusuf yayi kanta tare da Fara k'ok'arin Rabata da rigar jikinta ya ce "Hak'k'ina zan Amsa wajenki beauty kinsan dai na d'aga maki k'afa to yau hakuri na ne yazo k'arshe Gwarama ki bada kai kawai bori ya hau Dan yau babu mai kwatarki a wajena Karkiyimun gardama Naji maki ciwo my beautiful bride a hankali zan biki........✍🏿 *Tirk'ashi*🏃🏿‍♀️🙆🏽‍♀️ *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [6/29, 22:56] Hajo hajo: 🅿️..........*73&74* ....A hankali zan biki"Aira jin maganganun take tamkar a mafarki kuka ta fashe da shi ta ce "Ka tadani Daddy Dan soyayyarka da annabi muhammad (s a w) Karkamun komai " Ai Alh Yusuf baimasan tanayiba tuni harya zuge mata zif din rigarta yana kokarin raba ta da rigar jikinta ganin da gaske dai yake "ki rik'emun Amanar Komai dake tattare da ke na baki Amanar kanki Da kanki" Tunowa da maganar Ta da Arman Ta k'arshe Ai batasan sanda wani k'arfi yazo mata ba hannun Alh Yusuf ta samu ta gantsarwa cizo iya k'arfinta har saida Fatar wajen ta fara fita Ai Alh Yusuf najin azabar cizon da Aira ta gallamai ba baisan lokacin da ya yi k'ara ba Ya mirgina gefe Aira na ganin ya d'agata cikin sauri ta mik'e cike da tashin hankali hawaye duk sun cika mata fuska Kallonta Alh Yusuf yayi ya kalli hannunshi ya ce "Tunaninki wannan cizon da kikamun shi zai kwaceki daga wajena sainaga ta Inda zaki fice daga d'akin" Cikin kuka Aira ta ce "Wlh baka isa kayimun komai ba mugu azzalumi macuci tsohon banza kawai" Alh Yusuf cike da zafin rai ya tunkarowa zai Kara chafketa Cikin rud'u Aira ta fara waiwayen neman mabugi Kwalbar turarruka da aka jera mata akan Mirror d'inta ta kwaso Tare da Jefa mashi katuwa a goshi"Alh Yusuf ba k'aramar azaba yaji ba tuni goshinshi harya fashe ya fara fitar da jini Durk'ushewa a wajen yayi yana sauke numfashin wahala Aira ganin hakan ya sanyata saurin Rugawa tayi hanyar kofa tare da Fara k'ok'arin bud'ewa "ni kika fasawa goshi Illatani kike son kiyi Aira to Karki fice daga d'akin nan kome na miki ke kikaja" cikin kuka Aira tana bud'e k'ofar ta ce "idan ka tashi ka kasheni sannan wlh saika sakeni" Ganin Alh Yusuf ya Mike jini nabin goshin shi sosai ya fashe ya sanya Aira saurin bud'ewa cike da tashin hanki ta Ruga a guje Alh Yusuf ya Mara mata baya yana ina zakije Ai Aira bata zarce ko ina ba sai d'akin Hajiya saude taci sa a ko a bud'e A guje ta Ruga tayi d'akin sai hak'i take tana kuka Hajiya saude da har ta kwanta Jin Banko k'ofar ya sanyata tashi cike da mamaki take kallon Aira ta ce "Me ya kawoki nan ke kuma" Kafin ta k'arasa maganar Alh Yusuf ya shigo rik'e da goshin shi dake fitar da jini cikin kid'imewa Saude ta mik'e Aira ganin ya biyota ai da gudu ta Ruga ta boye Bayan Saude tare da kankameta ta fashe da kuka ta ce "Dan Allah Mama ki taimakeni " Cike da masifa daddy ya ce "ki fito na fad'a maki " Mama saude tsaye tayi ta kalli wannan ta kalli wancen "ta ce " wai meke faruwane Alh yanaga jini a goshinka ka"Matsowa yayi yana cije baki ya ce "Ba ruwanki ke kuma ki fito Daga bayanta idan kuma kika bari na kwaceki da kaina zaki yabawa aya zak'inta " Kuka Aira ta fashe dashi tare da kankame Mama saude ta ce "Mama Dan Allah karki bari ya tab'ani kasheni zaiyi kimun rai Mama Dan Allah kisa ya sakeni Daman bana sonshi aka auramunshi Dan Allah ki taimakeni Mama "Rik'e Aira saude tayi tare da gallawa Daddy harara ta ce " Ficemun daga d'akin Alhaji"bazan fita ba ina ruwanki wai ba mata ta bace wlh ranku Duka zai b'aci"Aira najin haka ta k'ara fashewa da kuka ta ce "Mama Dan Allah karki bari ya tafi dani " Mama saude mamaki duk ya cika mata kai kwantar da murya tayi ta ce "Kayi hakuri Alhaji ka fita na turo maka ita Sannan kaje a duba maka goshin naka kafin nan zan lallaba maka ita" Badan Alh yaso ba Kamar Wani sakarai ya ce "to" yana ficewa daga d'akin Aira ta sauke wata nauyayyar Ajiyar zuciya Rufo d'akin Mama saude tayi tare da sa key ta juya Kallon Aira tayi dake tsaye har lokacin tana kuka Dafota tayi ta ce zauna muyi magana"ba musu Aira ta zauna gefen gadon tana kuka dukta rikice numfasawa saude Tayi ta Ce "Inason kiban labari komai bana son ki b'oyemun Naji kina cewa bakisan Alhaji to garinyaya Akayi Auren nan " Cikin shashekar kuka Aira ta ce "Eh Mama wlh bana sonshi Auren dole ne akamun dashi" Cike da mamaki saude ta ce "Auren dole Kuma tun yaushe aka wuce yayin Auren dole garinya Haka ta faru" Goge hawayenta Aira tayi ta ce "Ina da Wanda nake so tun yarinta.......tas ta bata labarin komai da soyayyar su da Arman har zuwa Aurenta da Alh Madugu " amma ta boye mata zarginsu da Abbanta yake da kuma birthday din da ya hada mata da kamasu a hotel da akayi ta k'arasa fad'a cikin kuka mai cin rai Dan sosai ta k'ara tunowa da soyayyar su da Yaya Arman"Hajiya saude sosai tayi sanyi ta kuma tausaya wa Aira a zuciyarta ta ce "Ashema haukan banzana nake Yarinyar ba sonshi take ba" Kiyi shiru ki bar kukan nan kinji a Gaskiya ni kaina na tausaya miki "Cikin kuka Aira ta ce " Dan Allah Mama ki daina kallona matsayin kishiyarki wlh ni kallon uwa nake maki Dan Allah ki sanya Daddy Ya sakeni wlh bazan iya zama dashi a matsayin miji ba ki taimakeni Mama kisanya ya sakeni"Karki damu y'ata daga yanzu nadaina kallonki matsayin kishiya duk bansan da wannan al'amarin ba sai yanzu da kika fad'amun yanzu ki koma d'akinki kije ki kwanta gobe ma k'arasa magana"Mama Dan Allah ki bari na kwana a nan wlh ni ko a k'asa Ne saina kwana Amma bazan iya komawa ba Chan tsoro nakeji zai iya bina Dan Allah Mama ki taimakeni"sosai Aira ta bawa Mama tausayi Hakan ya sata cewa "to shikenan tunda kin tsorata hau gadon ki kwanta saimu kwanta tare" Murmushin farinciki Aira tayi ta ce "Nagode Mama Allah saka da alkhairi" A tare suka kwanta Gado d'aya Aira har lokacin fargaba take Saidai kuma.ta d'anji sanyi a ranta da suka fahimci Juna da Mama saude koba komai yanzu damuwarta a gidan zata ragu Itama saude cike da mamakin al'amarin nan ta kwana (Sabon salo kwana Gado d'aya da kishiya 😂😅)Alhaji Yusuf ko kai tsaye wani k'aramun clinic ya nufa Inda aka duba mashi raunin Saida akai mashi d'inki shi kanshi yayi mamakin irin yankan da Aira ta mishi saida aka gama mishi d'inkin tukwana ya koma gida takaici biyu ga bai cimma abunda yaje samuba ga azabar ciwo Washegari koda suka tashi cikin ladabi Aira ta gaishe da Mama saude ta amsa mata cikin mutuntawa Nan Aira ta shiga gyara mata d'akin dukda tayi da ita ta Bari ammata k’i tana cikin shara Laila ta shigo kallon Aira tayi cike da mamaki tukwana ta kalli mamanta ta ce "Mama wannan kuma me take maki a d'aki da sassafen nan" Janyo hannunta Mama saude tayi ta ce "Aikine take tayani Sannan ta ce " Daga yau Laila karna k'ara ganin magana marar dadi ko harara ko hantara ta shiga tsakaninki da Aira ki d'auketa tamkar y'ar uwa kinji"zumburo baki Laila tayi ta ce "To akanme Mama kishiyarkice fa" Aira ce ta ce Mama zan wuce "murmushi saude tayi mata ta ce " To Aira nagode kije kiyi bacci Naga baki rintsaba sosai sannan karkishiga kitchen nayi magana da mai aikinmu zata dawo yanzu idan ta gama break fast zanturo Laila ta kiraki kinji "To Mama nagode" Aira na barin d'akin Laila cike da mamaki Tace "wai Mama Lafiya naga kin sauya lokaci guda" Hmmm kede bari Laila ai dole kiga haka Ashe duk haukan banzan mu muke.....tas ta kwashe komai da Aira ta bata labari ta fad'awa Laila itama Laila sosai ta tausaya wa Aira tasan Tabbas ko itace akayiwa haka saita girgiza...Aira na fitowa a palour taci karo da Sadiq Kallo d'aya yayi mata ya kauda kanshi ganin haka ya sanyata saurin wucewa bedroom d'inta tana shiga ta rufe tabar key din jiki tare da hamdala wanka tayi ta sauya kaya ta haye Gado cike da tunanin Arman bacci ya kwasheta itace bata tashi ba Sai wajen 10 Shima Knoking d'in Laila ne ya tayar da ita tana bud'ewa murmushi Laila tayi mata ta ce "Baccin kikasha kenan sis muje muyi break fast " Murmushin Aira ta mayar mata ta ce "banma San nakai lokacin nan ba muje to" a tare da Aira da Laila suka fito Aira ganin Daddy a dining d'in sosai gabanta ya fad'i zata juya Laila tayi saurin rik'e mata hannu ta ce "matsoraciya kawai daddyn namu ne ya zame miki dodo" A sanyaye aira tabi Laila gabanta na fad'uwa kujerar kusa da Mama Laila ta ja ta zauna gabanta sai fad'uwa yake cike da kulawa Mama ta ce "Harkin tashi kenan " Kanta a k'asa tana wasa da zoben da yaya Arman ya sanya mata ta ce "Eh Mama" Laila kiyi serving d'inta "to Laila tafada tare da Fara serving d'in Aira Daddy ko idonshi nakan Aira ko k'iftawa baiyi Ga kuma mamakinshi na yanda yaga Saude na nan nan da Aira Cike da fargaba Aira tafara tsakular abincin d'ago idonta tayi a hankali Suka hada ido da Daddy saurin k'asa da kanta tayi sosai gabanta ya fad'i ganin irin ciwon da taji mashi Batare da ta k'oshi ba ta mik'e Mama ta ce " Badai harkin koshiba"murmushi Aira tayi ta ce "Wlh na k'oshi Mama " To shikenan"Daddy ne shima ya Mike cike da gadara ya kalli Aira ya ce "Muje zamuyi magana" Aira tuni harta fara hawaye Kallon Mama tayi ta ce "Dan Allah Mama kice karya dakeni " dan ita a tunaninta rama ciwon da tajimai ne zaiyi "Kallon Daddy Mama tayi ba wasa ta ce " Alhaji koma ka zauna"Cike da jin Haushi Daddy Ya ce "waike ina ruwanki saude Nifa na kawota gidan nan aurota nayi kamar yanda na auroki Dan haka ki daina shiga tsakanin Nida matata idan ba so kike ranki ya b'aci ba" kallon Aira Mama tayi ta ce "Wuce ciki Aira" Aira hada gudunta ta Ruga "Laila ma tashi tayi tabar wajen Kallon Daddy Mama saude tayi ta ce " Kaidai kaji kunya wlh Alh ashe tirsasawa yarinyar nan kukayi Auren ka to Naji komai da bakaso Naji kuma daga yau karka k'ara takurawa yarinyar mutane kaiko kunya ma bakaji Yanzu wa gari ya waya bagashi nan taji maka ciwo ba to wlh nan gaba saita illataka indai kaci gaba da Haye mata Dan Idan mace batason namiji komai tana iyayi wlh ni mamakima kakeban godai godai dakai da tsufanka da komai amma baka hakura da duniyaba har kake k’ok’arin fad’awa yarinya k’arama kusan sa ‘ar jikanka kadaiji kunya wlh "Cike da masifa ya ce " Ohhh wai hademun Kaine nan zakuyi to ina ruwanki Inma batasona aidai Nina aurota"Tsaki taja tare da barin Wajen tace "Chan ta matse maka " Daddy cike da jin haushin matan nashi ya bar gidan duk sungamu sun chaza mashi kai ....tun daga lokacin nan Aira da Mama saude suka had'e kansu sosai Aira take yiwa Mama saude biyayya yanzu bata aikin komai ga kuma Ita da laila sun zama kawaye Saisu zauna susha hirarsu kamar basune ba ga kusan kullum Laila saita kirawa Aira Mamy Dan Wani lokacin ma da kanta take cewa baza a kira miki kowaba Sosai hakan ya farawa Aira dadi Dan yanzu Bata da matsala da mutanen gidan idan ta amshi wayar Laila takan kira layin Arman Amma koda yaushe switch up Saidai tayi kukanta a d'aki ta gode Allah Alhaji Yusuf kuwa ido ya sanya musu yaga gudun ruwansu hakan ko sosai yayiwa Aira dad'i Dan ko gaisuwa Bata had'ata dashi Ammafa duk Inda ta gitta idonshi a kanta.......Sanye yake cikin K'ananan kayan da sukayi mugun karb'ar shi dukda Ramar da ya d'anyi Fuskarnan tashi tayi fayau ta k'ara kyau da haiba Sumar nan tashi lufluf kamar wacce ake shafama mai A hankali yake Saukowa daga matattakalar benen jirgi Mummy na gefenshi kallo d'aya zakayi mata kasan tana cikin farinciki rik'e take da hannunshi tana binshi a hankali kamar wani yaro har suka k'arasa Saukowa Kallon filin jirgin ayayi garin yayi lufluf Kamar za ayi ruwa Alhamdulilla finally yaudai gani a 9ja K'asar da Masoyiyata take cikinta Murmushin da harya mance yaushe rabon da yayishi yayi a hankali yanda ba wanda zai ji ya ce "a duk Inda kike a fad'in duniyar nan ko da kuwa nisan wajen ya kai birnin sin saina nemo ki masoyiya............✍🏿 *Ni da yaya Arman it's not free it's for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* _*Miss Hajo ce_*🤙🏿 [7/1, 23:00] Hajo hajo: 🅿️..........*75&76* ....Saina nemo ki masoyiya ya k'arasa fad'a yana murmusawa ta gefen baki"Daddy ne ya taryoshi Rungumeshi yayi ya ce "highly wellcome my son I m very happy to see you Allah ya k'ara maka lafiya"Ameen Arman ya fad'a Shima yana Rungume Daddy Mummy ta matso cike da farinciki Dan yau jinta take cikin farincikin marar musaltuwa Dan samun lafiyar yaron nata a yanzu ta fiye mata komai cike da farinciki suka bar airport d'in koda suka isa gida sosai goverment house din ta cika da mutane Dan ko a Chan Egypt d'in mutane sundinga tururuwar zuwa y'an uwan Mummy ma dake yola duk sunzo domin duba jikin na Arman gidan saiya kasance kamar ana wani shagali Arman ko dayake baisan damuwa da hayaniya tunda ya shiga katafaran bedroom d'inshi bai lek'oba Dan wasu idan suna son ganinshi Godiya Mummy takeyi musu tace ya samu bacci Dan tana kiyaye dokokin da likita ya dorasu a kansu Arman ko kwance yayi a makeken Royal bed dinsa ya d'ora kanshi bisa hannunshi yana kallon sama tunanin Inda Aira take kawai yake tare da tunanin yanda zai nemo ta dan baitab'ajin ya karaya ba ko sau d'aya indai akan Aira ne lokacin shan maganinshi nayi Mummy tazo da kanta ta b'alla masa ta bashi yasha. Tunda aka Sallamo Arman kullum gidan cike yake da mutanen Arziki masu zuwa dubiya Mama Halima ma tazo daga kaduna ita da Hafsa Dan duba jikin nashi Tunda Mama Halima tazo batayiwa Arman zancen Aira ba haka Shima baiyi mata ba dukda yana son tambayar Inda take Zaune suke a palour ya kwanta saman sopa Mama Halima da Mummy na hira jefi jefi yayinda Hafsat ke waya k'asa k'asa Shidai Arman idonshi rufe ba wacce takeyimai gizau idan ba Aira ba Shi ina ma take?ya tambayi kanshi Bud'e idonshi yayi a hankali ya sauke akan Hafsa dake lumshe ido tana waya bamaijin abunda take cewa "Tsaki yaja Tare da yunkurawa zai tashi cikin Sauri Mummy taje ta taimaka mashi ya mik'e tare da yi mashi Sannu" Gyad'a mata kai yayi a hankali ya ce "Mummy zan iya fa tafiya da kaina kije ki zauna Naji sauk'i fa" Murmushi tayi ta ce "Ka tabbatar dai ba wata matsala" gyad'a mata kai yayi tare da d'an murmusawa kad'an da mahaifiyar tashi taji sanyi"Sosai kwa hakan yayiwa Mummy dad’i ta ce "To shikenan ka kula Allah ya k'ara lafiya" Ameen ya fad'a tare da Fara tafiya ya nufi bedroom d'inshi Yana isa kan bed ya zauna tare da dafe saitin zuciyarshi dake mashi ciwo Dan tunanin Aira da ya zurfafa Kwance yayi wasu siraran hawaye na zubo mashi wace hanyace zai samu ya had'u da Aira tunani yayi Tabbas Hafsa tasan Inda take kuma zata iya fad'a mashi hakan yasanya shi janyo telephone d'in dake gefen gadon ya Danna number Mummy tana d'auka ya ce "Mummy a bawa Hafsa ta kawomun Tea " Daga bangaren Mummy Ajiyar zuciya ta sauke tare da Kallon Hafsa ta ce "Jeki had’awa yayanku tea ki kai mashi d'aki amma karki cika sugar kinji daughter" Katse wayar da suke da yaya Umar tayi tare da mik'ewa ta ce "To Mummy " Bayan tafiyar Hafsa kallon Mama Halima Mummy tayi ta ce "Ni wlh daman Hafsat Arman ya komawa Tunda dai Airar tayi Aure kuma naga Kamar ya d'an fara hakura da ita tunda ko maganarta bayayi" Cike da Rashin nuna jin dad'i Mama Halima ta ce "Aunty kibar wannan Maganar Dan Allah karma ta zame matsala " murmushi Mummy tayi ta ce "Ai daman ceewa nayi daman naga Hafsa d'inma kamar da Wanda takeso tunda na kula tunda tazo kullum tana waya" Wlh ko wai Umar nefa suke soyayya dashi ni farkon d'aukarma wasa nayiwa Abun saidaga baya na lura itama sonshi take "ikon Allah To Allah tabbatar da alkhairi kice tuwo na maina za ayi amma ai yana da mata ko" Eh yana da mata Allahdai tabbatar da alkhairi kawai Amma banson kai y'a gidan mai mata dukda dai d'an uwanta ne "Ameeeen ya Allah ai fatan Alkhairi kawai ake Wani gamin saikiga Auren mai Matar ma yafi na saurayin kwanciyar hankali Yanzu barin Kasu d'in da ta shiga zatayi kenan idan Auren ya taso" a a. Gaskiya banjin Abbanta zai cireta tunda Shima ak'ida garai cewa yayi saitagama karatu ko yana mata Aure "Nan dai sukaci gaba da tattaunawarsu Hafsat ko Bayan ta had'a tea d'in d'akin Arman ta nufa knoking tayi ya bata izinin shigowa tana shiga Ta duk'ursa ta ce " Sannu yaya ga tea d'in"yunkurawa Arman yayi ya tashi zaune tare da cewa "Ajeshi kan center Table " Nan ta Aje harzata juya ya ce "zo muyi magana Hafsa " Juyowa tayi tare da zaunawa Kujerar dake gefen gadon ta ce "Gani yaya" Numfasawa yayi kamar bazaiyi magana ba kallonta yayi ya ce "Kinsan Inda Aira take tana gidansu har yanzu kuwa ?"Sosai Hafsa tayi mamakin tambayar da Arman yayi mata cewa tayi "a a a ta na sokoto " what sokoto kuma?Arman yafada cike da mamaki"Gabanta na fad'uwa Dan tsoro take kar wani abun ya kuma samunshi ta ce "Kayi hakuri Yaya Yanzu Aira ai tafi wata guda a gidan mijinta Ammafa har yanzu tana sonka yaya dukda yanzu bama tare A dalilin Auren har kokarin kashe kanta tayi Tasha fiya fiya" Kashe kanta fa kikace Hafsa yanzu dai fatan tana lafiya ba abunda ya sameta "gyada mashi kai tayi ta ce " Eh taji sauki tun lokacin ta warke"nauyayyar Ajiyar zuciya Arman ya sauke Sosai yaji zafi da kishi da rad'ad'in jin wai Aira na gidan mijinta mijin ma bashiba "Ya sunan mijin nata?ya fad'a cikin k'arfin hali" Kamar mai nazari Hafsa tayi Dan sunan ya shige mata saikuma ta ce "Inajin dai akwai Madugu a sunan nashi Amma na manta ainahin sunan"Kallon Hafsa yayi ya ce " okay thnks u can go but don't tell anyone munyi wannan Maganar dake "gyada mashi kai tayi ta ce " Insha Allahu "tare da barin d'akin tana tunanin me Arman zaiyi da sunan mijin Aira Arman ko tana fita Sosai ya k'ara shiga damuwa wai Aira ce Ke gidan wani har tsawon wata guda Sosai wani irin kishi ke taso mashi shikenan kenan Wani banza sakarai ya rigashi sanin Airarshi sosai zuciyarshi ta dinga tafarfasa. Da misalin tara na dare Zaune suke a palour ita da Laila suna Hira Laila na bata labari har Dariya take Sadiq ne ya shigo da sallama a bakinshi Kallo d'aya Aira tayi mai tayi kasa da kanta Dan nauyin had'a ido dashi ta ke " Zaunawa yayi yana sauke ajiyar zuciya Laila ce ta ce "Sannu da zuwa yaya Ga alamu kashayo gajiya" Yawwa Sadiq ya fad'a ya ce"wlhko na kwaso gajiya jeki d'auko mun ruwa"To yaya Laila ta fad'a tare da tashi tabar palourn Kallon Aira yayi da tayi kasa da kanta tana wasa zobe yayi ya ce "Auntynmu ba magana to ina yini " D'agowa Aira tayi ta Kalleshi tare da turo baki ta kauda kai"Murmushi yayi ya ce "Baza a amsa gaisuwarta tawa ba kenan Mamanmu" Dagowa Aira tayi ta Kalleshi tare da Fara hawaye Cikin shagwaba ta ce "Ni ba mamanka bace ina nazama mamanka please mai sunan Abba ka daina "Dariya Sadiq yayi ya ce " sorry to na daina Auntynmu zance kenan"Turo baki Tayi ta kauda kai"Wai ina Aunty Aysha kuwa kun bani ita tunda dai Ke yanzu kin zama mamanmu "ya fad'a cikin sigar zolaya " Murmushi tayi ta ce "Tana Chan kano Ai tayima Aure tafi 5 moths ina tunani" Cike da nuna Rashin jin dad'i Sadiq ya ce "Ayya to Allah ya basu zaman lafiya"Ameen Aira tafada" Laila ce ta dawo tare da mik'awa Sadiq ruwan kallon Aira tayi tare da mik'a mata wayarta ta ce "Natafi kuma sai Mamy ta kira zan kawo maki kuma saita katse amshi ki kirata...kafin Aira ta amsa ta sake kira" yawwa ma gashi ta sake kira Laila ta fad'a tana mik'awa Aira amsa Aira tayi tare da d'aga wayar daga d'ayan b'angaren Mummy tayi sallama "Aira ta amsa tare da cewa " Ina yini Mamy"Lafiya qlau Aira ya sokoto kindai zama basakwakwaciya"tashi Aira tayi tare da barin palourn tayi d'akinta ta ce "Haba Mamy ni har yanzu bakaniya ce Sokoton da ko ganinta bantaba ba Tunda nazo banje ko ina ba"Haba dai to ai gwara haka daman Banason yawo amma naga kamar kuna zaman lafiya da mutanen gidan ko Aira " Eh Mamy yanzu lafiya qlau muke zaune da dai suka bani wahala Amma yanzu Alhamdulilla "To masha Allah haka nakesonji daman ki hakura kiyi zaman aurenki kinji Aira tunda Allah ya kaddara miki" hawaye ne suka zubowa Aira ta maidasu "Uhm kawai tacewa Mamy" Sannan ta ce "Mamy ban Amer mu gaisa" Murmushi Mamy tayi ya ce "shidai bai magana Saidai yayi miki gwalamgwamtu ta fad'a tana Kara mishi Wayar a kunne" My boy Aira ta fad'a jin gwalamgwalamtun Amer nan ta biyeshi suka yi ta shiririta tukwana ta ce "a bata Haidar kiran Haidar Mamy tayi Shima ta bashi Sosai yaji dadi cikin farinciki suka shiga gaisawa da y'ar uwartashi ya ce " ya Aira munyi missing d'inki wlh gidan duk ba dad'i inna ma kullum saitayi kukan rashinki"Goge hawayenta Aira Tayi ta ce "Nima nayi missing naku sosai bro Kaico my Inna kenan ta dawo nima nayi kewarta"Amsar wayar Mamy tayi ta ce " "ba abunda kike buk'ata inbada ko mota ne a kawo maki...Dariya Kad'an Aira tayi ta ce " Kai Mamy yanzu ko nace inason wani Abu saiki bada a kawomun tundaga kano a a bana buk'atar komai ganinku kawai nake buk'at....kasa k'arasa maganar tayi sakamakon ganin shigowar Alh Yusuf da tayi a murtuke Ihu ta fasa tare da wulli da wayar ta ce "Na shiga ukku Daddy Dan Allah fita" k'arasa shigowa Daddy yayi ya ce "Bazan fita ba ke nifa ba haka nan na auroki Dan na dinga kallonkiba ba biyan buk'ata shine kuka hademun kai keda saude ko to yau zanga ta Had'in kai saitazo ta kwaceki" ya fad'a yana rufo d'akin tashin hankali ba a gwada maka rana da gudu Aira Ta Ruga ta shige toilet tare da sanya key ta ciki ta rufe durk'ushewa tayi jikin kofar tare da fashewa da kuka Alh Yusuf ko sosai ya shiga buga kofar toilet din kamar zai ballata ya ce "ki bud'e nace Wlh karki bari raina ya b'aci" Aira ba abunda take inbanda kuka ta ce "Bazan bud'e d'inba mugu azzalumi" Alh Yusuf ya dau minti ashirin tsaye yana mata magiyar ta bud'e amma takiya sai kuka take jin bazata bud'e d'inba ya sanyashi Juyawa cike da jin Haushi Mamy cikin waya ta dinga cewa Hello hello amma taji shiru ta cikin waya ta dinga jin Abunda ke faruwa cikin Sauri ta maza ta kashe wayar gabanta na fad'uwa Laila ko ta biyo Aira Dan amsar wayata tajisu saurin Juyawa tayi cikin Sauri cike da kunyar abunda mahaifin nasu yake Aira ko sosai take kuka a toilet d'in ta durkushe ita wannan wace irin jarabawace Allah ya jarabceta ita kwata_kwata tsohon najadun nan ya takurawa rayuwarta Arman kawai take kiran sunanshi tana kuka tana cewa "Yaya ka kawomun d'auki plx " tana kuka har bacci ya d'auketa a toilet d'in saida asuba ta farka ta ganta a toilet cike da tsoro ta mik'e ta ce "Na shiga ukku yau nice da kwanan toilet abubuwan da suka faru Daren jiya suka shiga dawo mata A hankali ta bud'e k'ofar toilet din ta tura taga ba kowa cikin Sauri ta fito tare da rugawa taje ta rufo d'akinta tasa key tabarshibu jiki Juyawa kan Gado tayi taga wayar Laila Na vibration Cikin Sauri taje ta d'auka tana ganin number Mamy ce " Cikin Sauri ta d'auka tare da fashewa da kuka cike da tsoro Mamy ta ce "Kina lafiya Aira kukanme kike what happend to u " Cikin kuka ta ce "Mamy Dan Allah kizo ki tafi da ni wallahi nagaji Mamy nasan ke kina sona kizo ki tafi dani Dan Allah kafin mutumin nan ya kasheni wlh Mamy kusan kullum sai yayi k'ok'arin yimun fyad'e Allah yake tsareni yanzu haka yau a toilet na kwana Mamy Allah Abba d'an iskane kawai ya auramun Mamy kizo ku tafi dani kafin na mutu" ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka. Mamy ita bada magana ba Amma sai kunya ta kamata ruwa yabi ya cinyeta Daman tun jiyan ta kasa bacci tana tsoron ko wani abun ne ya samu Airan hakan yasa tunda safe ta kira Sosai a ranta tayi mamakin kenan tunda akayi Auren wani Abu bai shiga tsakaninsu ba"murtukewa tayi kamar tana gabanta ta ce "Bansan shirme da shiririta Aira karna k'arajin maganar nan kin fad'awa kowa waike har yanzu bazakiyi hankaliba waya gaya miki kowace magana ake fad'a daga yau karna k'arajin maganar nan a bakinki" Cikin kuka Aira ta ce "To Mamy Nadaina Amma yaushe zakizo ki tafi dani Dan Allah Mamy na Allah ina cikin wani hali" Dan son kwantar mata da hankali ya sanya Mamy cewa "karki damu na kusa zuwa Natafi dake inason ne na shayo kan Abbanku sai muzo tare mu tafi daken sannan karki k'ara kwana a toilet komai zai faru karki sake ki k'ara kwana a toilet akwai kwankwamai kinji" cike da farinciki Aira tace "Da gaske Mamy sannan ta b'ata rai Ta ce " To Mamy bazan sake kwana a toilet ba amma ai gwara da na kwana Allah da ban kwana ba da yanzu saidai ace miki na mutu wannan shirgegen k'aton banzan daman haka kwanaki Allah ne kad'ai ya kwaceni Harsaida na fasa masa kai Mamy na farajin Aira ta fara sakin layi ta kashe wayarta saida Aira takai karshe jin shiru ya sanyata Duba wayar taga Mamy ta kashe turo baki gaba tayi tare da Aje wayar ta cire kayanta ta fad'a toilet tayo wanka tare da alwala Tana fitowa tasa doguwar Riga marar nauyi ta tada salla tana gamawa ta haye Gado tare da Fara Game da wayar Laila Jiyo knoking ya sanyata mik'ewa daidai bakin Kofar taje ta ce "waye?Nice " jin muryar Laila ce ya sanyata saurin bud'ewa Kallonta Laila tayi ta ce "Ina kwana Auntynmu " Turo baki Aira tayi ta ce "Yau kuma hada zolaya ta fad'a tana kamo hannunta sukayi ciki wayarta ta mik'a mata ta ce " gashi sis Laila nagode jiyan naso Na Kawo miki bacci ya daukeni kiyi hakuri"Murmushi Laila tayi tana jin yanda Aira ta shirga mata karya nanko batasan ba Taji komai dukda dai taga da Alamun ba abunda ya shiga tsakaninsu ta ce "Ayya karki damu sis daman Kiranki nayi muje muyi break fast " Uhm Dan Allah Laila ko zaki kawomun nan Banason fitar Dan Allah "Batare da gardama Ba Laila ta ce " Okay bari na d'auko mana sai muci a nan "Ajiyar zuciya Aira ta sauke ta ce " yawwa Thnks my sis"a tare sukayi breakfast a d'akin Aira suna ci suna Hira harsuka gama Laila taje ta kawo musu Ruwa Laila ce ta ce "Nidai bacci zanyi wlh " Mikewa Aira tayi ta ce "Nima baccin zanyi saimu kwanta ta fad'a tare da zuwa ta rufo d'akin tasa key" Kallonta Laila tayi ta ce "Meye na sanya key kuma" Sosa kai Aira tayi ta ce "Uhm kedai kawai ki barshi hakan" Girgiza kai Laila tayi Dan tasan saboda Daddy take rufe d'akin a zuciyarta ta ce "in banda abun Aira Kome zaiyi ai bayayi ina d'akinba " Cikinsu ba Wanda ya k'ara cewa uffan Aira ta kwanta itama Ba b'ata lokaci bacci yayi awon gaba dasu musamman Aira da daman jiya a takure ta kwana a toilet. Alhmdllh Arman yana ta samun sauk'i Sosai Mummy da Daddy ke kula dashi cikin sati biyu Arman ya warke ya murmure komai shi yakeyiwa kanshi Saidai Rashin yin magana da bayayi sosai koda yaushe tunanin Aira yaki barin kwalwarshi wani lokacin yana tunanin baisan lokacin da hawaye ke zubar masa ba suna zaune a kan sopa shida Mummy Daddy Ya shigo Sannu da zuwa sukayi mishi Bayan ya zauna "Kallon Arman yayi ya ce " Alhamdulilla son daman jira nake jikinka yayi sauk'i mu fara da maganar Aurenka Kamar yanda na fad'a Aure zanyi maka to ba chanji Dan haka ni da kaina mahaifinka na zab'a maka matar da ta dace dakai munyi magana da mahaifinta daman kuma ya shaidamun yarinyar ta amince Dan haka ni bana buk'atar amincewarka tunda nine mahaifinka gobe za a sanya Ranar auren ka da........✍🏿 *kada ku fitarmun da littafi y’ar uwa kudin karantawa kuka biya bana mallakaba duk mai bukatar saya ya tuntubeni akan number wayata 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/3, 10:37] Hajo hajo: 🅿️.......*77&78* ....Ranar Aurenka kai da "Asma'u husna y'ar gidan Alhaji Zakari Commissioner of Sport kuma bikin bazai d'auki lokaci ba Dan sati biyu zamu sanya saikaje ka fara shirye shirye" Tunda Daddy Ya fara maganar Arman yake mamaki Harsaida yakai k'arshe d'agowa yayi tare da had'e rai fuskar nan tashi murtuke ba alamar Dariya ya ce "Wai Daddy ni kake nufi zakayiwa Aure ?Eh kai nake nufi ko ban isa da kaiba " A a Daddy ka isa dani amma dai kasan ni ba mace bace bare kace Auren dole zakamun Gaskiya ka janye maganar nan bamai yiwa bace "cike da b'acin rai Daddy Ya ce " Zaka San bamai yuwa bane Indai nine mahaifinka Auren nan ba fashi kamar yanda ita wacce ka so din tayiwa mahaifinta biyayya ya Aurar da ita ta zauna d'akin mijinta to haka nima Idan har na isa dakai zan Aurar dakai "shi Arman mamakima ya gama cikamai kai ya ce " Amma Daddy ai ita macece Nifa namijine ina aka tab'ayi"Za a fara a kanka ko Rashin kunya zakayimun"Tunda suka fara maganar Mummy batace uffan ba sai yanzu Kallon Arman tayi ta ce "Karka sake magana Son" Kallon Mummy Arman yayi sai kuma ya koma ya kwanta kan sopa tare da lumshe idonshi Kamar mai bacci a ranshi ya ce "Lallaima Daddy wai ni zai duba yace zaiyiwa Aure murmushi yayi danshi abun ma Dariya ya bashi shiyasa ko a kanshi bai damuba" Kallon Daddy Mummy tayi cike da damuwa ta ce "Dear maimakon ka bari jikin Nashi ya k'ara sauk'i yanzu kuma kazo da maganar Aure ko shiri babu two weeks fa" d'aga mata hannu Daddy yayi tare da mik'ewa ya ce "Na Riga na yanke hukunci ba neman shawarar wani cikinku nazo ba umarni ne na bada ba shawara ba" Jan bakinta Mummy tayi shiru ita tsoranta d'aya kar Arman ya kuma shiga wani hali Kallonshi tayi taga hankalinshi kwance kamar ma ba a kanshi ake magana ba Bayan Daddy Ya bar palourn Mummy ta matsa kusa da Arman cike da nuna Rashin jin dad'i ta ce "Kayi hakuri karka sanyawa kanka damuwa kasan ba abunda na tsana sama da b'acin ranka kar wannan ya dameka kaji son please Karka k'ara jefa kanka cikin halin da ka shiga a baya ba bazan jureba kai d'aya garan Arman ina sonka sosai" ta k'arasa fad'a hawaye na zubowa daga idanunta " Lumshe idonshi Arman yayi ya budesu a hankali tare da yunkurawa zai mik'e Mummy ta rikeshi ta ida mik'ar dashi kamo hannayenta biyu yayi tare da Goge mata hawayen da suka zubo mata sosai Mummy take bashi tausayi iirin son da ta ke mashi Shima sosai yake so da k'aunar mummyntashi ya ce "Karki damu Mummy bazan k'ara shiga Cikin wani hali ba kidaina damun kanki kinji my first love " Rungumeshi tayi ta ce "Nagode my son Allah maka albarka" Murmushin k'arfin hali Arman yayi ya ce "Ameen mom" koda Arman yaje kwanciyar bacci da Tunanin Yanda zai yi ya samu Aira kawai ya ke dukda tayi Aure amma bayajin karaya a kanta tunaninshi Duka yana kan mafitar da zai samu harya isa gareta kwata kwata shi maganar Daddy ma bata dameshi ba saboda yasan ba abune mai yuwa ba washegari aka sanya Ranar Auren Arman tare da husna wacce sai d'auki da farinciki take Dan bata tab'a tunanin zata auri Arman ba mutum maiji da kyau,kud'i,mulki,Dan kwalisa tuni harta fara rawar kai tana jin tazama big girl Arman ko yinin Ranar a guest house d'inshi yayishi Saida dare ya koma gida Nan ya samu labarin sanya ranar Auren wajen Mummy d'age kafad'a yayi ba tare da nuna damuwa ba ya ce "yayi kyau" Sosai Mummy tayi mamaki ta ce "Wai Arman Yanaga baka damu da Auren nan Daddynka zaiyi maka ba Kodai da abunda kake shiryawane " murmushin yak'e yayi ya ce "bakomai Mom Good night ina buk'atar hutawa" daren ranar Arman ya samu bacci sosai Dan shawarar da ya yanke akan mafitar da yake tunanin zai gamu da muradin ran nashi Haka aka fara shirye shiryen biki Wanda Arman kosa hannu baiyiba sannan ya ce karma Mummy ta shirya shagaalin komai sannan karta gayyaci kowa nata"Sosai Mummy ta damu ta ce "Son me kake nufi kenan da karnayi gayya " Mummy nadai fad'a maki karki gayyaci kowa hakan ne zaisa na kwantar da hankalin da kikeso nayi amma idan kikamun gayya zan shiga damuwa"Ya fad'a mata hakane Dan yasan ta hakan ne kawai zata yarda Dan abunda yake shiryawa bayason ya kunyata Mummy cikin mutane"Girgiza kai Mummy tayi ta ce "To zanyi yanda kace son indai hakan zai sama maka farinciki" murmushi yayi tare da Rungumeta ya ce "I love you so much My dear mom d'aya tamkar da trilillion" Love you too my one nd only Dan lelen mummynshi"Murmushi Arman yayi yana shafa sajenshi.Bangaren Daddy sosai suka shiga shirye_Shiryen biki Mama Halima ya sanya takanas taje ta had'o Lefe a Dubai dukda itama batajin farincikin Auren amma ba yanda za ayi tunda Airar tayi Aure Shima Arman d'in gwara yayi tunda shekarunshi ja suke shidai Arman ya sanya musu ido ba um ba umm umm.duk yanda Daddy yayi dashi akan Yaje su gana da Asma'u kin zuwa yayi rabuwa dashi Daddy Ya ce "Ai idan Akai Auren dole kaje ka ganta Arman dai ganin gadan gadan Daddy da gaske yake Aure zai mashi gashi a yanda yaji suna lissafi Saura sati bikin Ranar da Aunty Halima ta dawo laifen ya k'ara tabbatar mai da Daddy da gaske yake fezar da iska mai zafi yayi ya ce " Impossible wlh bama zan yarda a d'aura Auren nan ba kamar naci amanarki cutie da kuma Amanar soyayyar mu ke kanki Auren da Akayi miki fin k'arfinki akayi kuma ke macece mai rauni ni kuma namiji ne Wanda zan iya gwagwaarmaya akan komai Zaunawa yayi bakin Gado tare da dafe kanshi Duka biyun dake Sara mashi soyayyarshi da Aira ta shiga dawo mashi cikin kwalwa mik'ewawa yayi tare da zuwa daidai saitin Inda hoton ta yake manne jikin Bango d'akinshi Tsaye yayi tare da Fara shafa hoton sosai tayi kyau cikin Rigar sanyi Red mai shegen kyau da black d'in wando ta kyalkyale da dariya a daidai bitch akayi hoton "Sosai Arman ya kafe hoton da idanu bako k'iftawa soyayyya da k'aunar Aira na k'ara fisgarsa yanajin wata sabuwar k'aunarta na ratsa ko wani sassa na ilahirin jikinsa baisan lokacin da wasu zazzafan hawaye suka zubo daga idanuwanshi ba k'ara shafa hoton yayi tare da lumshe ido ya ce " I love you you my cutie bazan iya rayuwa ba tare dake ba kiyi hakuri tsawon lokacin da Na d'auka batare da na cika alk'awarin da muka d'aukarma junanmuba ki sani a duk Inda kike gangar jikinmuce kawai tayi nesa da y'ar uwarta amma zuciyoyinmu suna Tare a waje guda for ever and ever har gaba da abada bazan tab'a daina sonki ba sannan bazan tab'a karaya a soyayyarki ba Sannan yayi kayataccen murmushin da ke karawa kyakyawar fuskarshi kyau da haiba ya ce "Ki shirya ina nan zuwa gareki yake sahibata" Wani Frame d'in hotonta dake gefe ya ciro shi kuma sanye take cikin Abaya Tasha nad'in larabawa sak ta yi kamar balarabiya komawa yayi kan bed d'inshi tare da Rungume hoton ya kwanta yanajin kamar ita ya Rungume shauk'in kaunarta na k'ara ratsashi sosai ya matse hoton a jikinshi yana sakin smiling a haka bacci mai dad'i yayi awon gaba da shi. Aira na zaune a kan sopa suna kallon wani serries a Bollywood sosai ta maida hankalinta ga kallon da take Laila kuma na chat Alhaji Yusuf ne ya shigo saida gaban Aira ya fad'i Dan rabon da ta yarda sun had'u tun ranar nan ya yaso Fad'a mata amma bata nunaba a fuska saici gaba da kallonta da tayi Kallo d'aya Daddy yayi mata ya kauda kai Dan fushi yake da ita dukta jagula mai lissafi kullum da tunaninta da sha'awarta yake bacci cike da girmamawa Laila ta ce "Sannu da zuwa Abba " Yawwa Auta ina mamantaki"Tana ciki ta bashi Amsa Barin palourn daddy yayi tare da nufar d'akin uwar gidanshi cike da jin haushin Rashin ladabin da Aira ke mashi dukda dai Shi ya ja ya aurota batasonshi amma wata biyu ai yaci ta hakura kallon Aira Laila tayi tare da b'ata rai Ta ce "mijinki ya dawo ba ko Sannu da zuwa bare gaisuwa " ta fad'a da sigar zolaya "Harara Aira ta maka mata tare da cewa " Allah yarinyar nan ki kiyayeni ke duk yanda zaki zolayeni kin iya ko Uhm su miji manya" "Kardai ki fad'a wata maganar daga wannan " Kallonta Aira tayi saikuma ta kauda kai tare da Yin tagumi Ba wanda ya fad'o mata a rai sai Arman batasan lokacin da wasu hawaye masu d'umi suka shiga zubo mata "Shin wani hali Arman yake ciki,ya warke koko har yanzu yana cikin halin da na tardashi,Yaushe zai dawo gareni,yaushe alk'awarin Soyayyarmu zai cika ,yaushene zai dawo gareni kamar yanda ya fad'amun sosai hawaye suka shiga zarya daga idanunta zuwa kumcinta " Da mamaki Laila take kallonta kamar mai iska lokaci guda lafiya yanzu kuma ta fara hawaye "Dafota tayi ta ce " Sis lafiya kuwa?tunanin me kike haka harda su kuka"Hakan ya dawo da Aira daga Duniyar tunanin da ta Lula kallon laila tayi tare da Fara goge hawayenta ta ce "ba komai sis" B'ata rai Laila tayi ta ce "kinn manta mun zama kawaye plz karki b'oyemun fad'amun tunanin da kike kika sani ko zan iya taimaka maki da wani abun" jin hakan cewar ko zata iya taimaka mata da wani abun ya sanya Aira Numfasawa tare da kama hannun Laila ta fuskanceta ta ce "Na rasa ya zanyi da soyayyar Yaya Arman Laila ina sonshi so mafi muni da bazan iya kwatanta maki kalarshi da komaiba a koda yaushe idan na kwanta kyakyawar fuskarshi nake gani murmushin mai narkarmun da zuciya tare da Kalamanshi masu ratsa ko wani sassa na ilahirin jikina a koda yaushe Fuskarshi da Kalamanshi gizo sukemun laila bazan iya rayuwa babushi ba...ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka Rungumeta Laila tayi sosai ta tausayawa Aira halin da ta tsinci kanta Dan kullum idan tana bata labarin soyayyarsu da Arman har hawaye take batare da ta sani ba daddab'ata tayi ta ce " Kiyi Hakuri sister Allah yana tare daku nasan zafi da rad'ad'in so ba abune mai sauk'i ba a Gaskiya ko a labarai bantab'a ganin masoyan Asali masu k'aunar junansu da zuciya daya ba sama da yanda kikebani labarin soyayyar da kike yiwa wannan bawan Allahn Amma ina mai baki shawara da Kibi komai a Sannu ki daina yawan tunanin wani a cikin ranki saboda yanzu kina matsayin Matar wani ce Karki bari shaid'an yayi galaba a kanki Allah babu ruwanshi da Rashin son Auren da bakiyi zai iya kamaki da laifin hakkin Daddy please sis ki rage wannnan soyayyar da kikeyiwa bawan Allahn nan tunda kinyi Aure"Numfasawa Aira tayi da kukan da take tare da gyadawa Laila kai Alamun to amma batajin daidai da second d'aya zata iya daina tunani da soyayyar Arman murmushi Laila ta sakar mata ta ce "ko kefa sis niko zanso naga Arman d'innan da ya zuzutar mana da Amarayr daddynmu guda " Hararar wasa Aira ta galla mata tare da turo baki ta ce "bako zaki ganshiba " Dariya Laila tayi sosai ta ce "Maida wuk'ar naga har kin fara kishi Daga ambatar sunanshi" Dariyar da bata shiryaba Aira tayi ta ce "Hada sharri ko sis" ba wani sharrri Amaryan daddynmu "Tilla mata Pillow Aira tayi tana turo baki.. Zuhura ce ta shigo Tare da yaranta Sakato tayi tana kallon yanda Laila da Aira suke wasa kamar wasu y'an uwa ko aminai kasa shiru tayi cike da fad'a ta ce " me Zan gani haka Laila keko wani Rashin sanin ciwon kan ne ya kaiki mu'amula da yarinyar nan harda Dariya"Sai sannan suka Kalleta Mikewa Laila tayi tare da zuwa ta amshi boy din dake hannunta ta ce "oyoyoy my Aunty kece da Yammar nan " Harararta Zuhura tayi ta ce "Amsa nace kiban ka wani iyayi ba " Murmushi Laila tayi tare da kama hannunta ta ce "Aunty jarabatu kenan muje ciki saina baki Amsar sannan ta kalli Aira ta ce " ina dawowa sis yanzu karki tafi akwai labari"murmushi kawai Aira tayi ta ce "To saikin fito" Bata gaishe da Zuhura ba saboda taga yanda take aiko mata da harara"Suna zuwa daki Zuhura Cike da fad'a tacewa su mama me yasa suke sakewa waccen Banzar yarinyar fuska Mama da kanta ta bawa Zuhura labarin da Aira ta basu sannan ta d'ora da cewa "ki kwantar da hankalinki ai yarinyar Chan da kike gani ba ma saimun bata lokacinmu wajen fitar da ita ba mu daukarwa Kanmu zunubi a banza da kanta zata fitar da kanta idan muka zuba musu ido " Tabe baki Zuhura tayi ta ce "ku dai daina sake mata da yawa haka " Itako Laila har ranta yanzu son Aira take Dan sun shaku sosai cikin y'ar abutar da suka k'ulla ta kwanannan gashi ta lura Aira bata da matsalar rayuwa D'aukar Junior K'aramun Dan Zuhura tayi tare da ficewa Zuhura ta bita da harara Laila na komawa Inda ta bar Aira ta sameta Zama tayi nan suka cigaba da Hira Bayan Aira ta amshi junior tanayi mashi wasa a yanzu Saukin Aira daya yanda Daddy Ya shareta hakan ko yayi mata bala'in dad'i yanzu ko kokarin rik'e mata hannu bayayi hakan ya sanyata yanzu fara sakewa ta daina Yawan zaman d'aki Saidai idan kwanciya zatayi rufe d'akinta ne ko yanzu koda mistake bata mantawaba saita rufe tabar key d'in jiki yanzu ta fara sakin jikinta da y'an gidan Sadiq ne dai saitayi ma sati bata ganshi ba mubarak ko harta mance rabon da ta ganshi hakan ko yayi mata dadi Dan daman Duka gidan tafijin nauyinshi har yanzu bata bar kukan Rashin Arman ba Dan daidai da rana d'aya bata tab'a fashin kukan Rashin shiba musamman idan tazo kwanciyar bacci.. Arman koda ya kwanta mafarke mafarken Aira kawai ya dingayi Inda mafarkin yake yimai nuni da tana buk'atar shi a kusa da ita hakan yasa tunda ya tashi ya shiga damuwa yinin ranar bai samu ya leko ko palour ba saboda azabar ciwon da kanshi ke mashi Sosai ya zurfafa tunanin Aira Inda daga karshe ya yanke shawarar da yake tunanin indai yabita idan yaci sa a zata b'ulleshi a lokacin karfe Tara na dare Mikewa yayi kamar Wanda aka zabura cikin Sauri ya d'aga locker Kayanshi Tare da bude k'aramar had'ad'd'iyar box dinshi Kala hud'u ya sanya cikin Kayanshi Tare da saka abunda yake ganin zai buk'ata na yau da kullum Yana gamawa ya ja akwatin ya rufe takarta da biro ya ciro tare da zaunawa ya fara rubutun doguwar wasik'a yana gamawa ya linke sannan ya k'ara bud'e wata ya sake wani rubutun Wanda baikai na wancen ba Shima ya linke saida ya lek'o palour yaga ba kowa Ajiyar zuciya ya sauke tare da saurin komawa yaje ya janyo akwatinshi harya fita daga Part d'insu bai hadu da koawaba saida ya fito ne yaci karo da securities D'aya daga cikinsu ta nufa wajenshi Wanda yasan Daddy Ya aminta dashi fuskarshi a daure danma kar wani cikinsu yayi mashi wata tambayar rainin hankali cike da gadara ya je ya mik'awa security d'in tare da mik'a mashi takaddun nan guda biyu ya ce "Gashi gobe da safe ka bawa Daddy d'ayar kuma Mummy zaka bawa"to ranka ya dad'e zan kai musu amma ina kake shirin zuwa da Daren nan na ganka kamar kana shirin tafiya" wani banzan kallo Arman ya watsa mashi tare da cewa "is not your business " yana gama fad'ar haka ya kira d'aya daga cikin driver d'in gidan umartarshi yayi da ya sanya mishi akwatinshi cikin boot din motar sannan ya bud'ewa Arman back sit ya shiga Shima ya shiga ya tada mota cike da girmamawa ya ce "ranka ya dad'e ina muka nufa" Airport zaka kaini"Koda suka isa airport Bayan driver ya fitowa da Arman da akwatinshi Kallon Arman yayi ya ce "Allah ya tsare hanya ranka ya dad'e " Ameen Arman ya fad'a tare da cewa"duk Wanda ya tambayeka Inda ka kaini kada ka bashi amsa a Daren nan ka fad'awa wani ka kawoni Airport kaima kasan sauran"insha Allahu hakan bazata faru ba ranka ya dad'e a dawo lafiya"Arman bai Kara cewa komai ba ya bar wajen cikin k'ank'anin lokaci aka shirya mishi tafiya sokoto kamar yanda ya umarta Dan a lokacin ma babu jirgin da zaije sokoto mak'udan Kud'i Arman ya kashe Dan bayason ya k'ara kwana d'aya a garin nan ba tare da ya isa garin da masoyiyarshi take ba ba ayi 1 hour ba jirginsu ya d'aga sokoto Wanda cikin k'ank'anin lokaci suka isa a lokacin kusan 11pm saura Koda suka isa a hankali Arman ya dinga Saukowa Daga benen jirgin Wani farinciki da annashuwa ya mamayeshi harya gama Saukowa k'ayaitaccen murmushi ya saki ya ce "Yau Gani a garin da ban tab'a mafarkin zuwa ba Amma soyayya ta kawo ni Alhmdllh yau gani garin da masoyiyata Take cikinshi a halin yanzu nima ina cikinshi Tabbas Gaskiya ne da y'an magana sukace Garin masoyi baya nisa..........✍🏿 *Garin masoyi baya nisa💃💃💃💃💃juyo ki ganni gani a kusa💃💃💃💃a kanki ba abunda zana fasa🙅🙅ba Wanda Zai magana in jisa...😅ku k'arasa da kanku Fans aikin nan naku ne*💃💃💃 *Shafin nan na sadaukar dashine ga kungiyata daya tamkar da dubu jarumai Writer’s Association bisa ga cikarta shekara biyu da kafuwa Allah ubangiji ya kara daukaka wannan kungiya mai albarka tare da jaruman dake cikinta yan uwa da suka tayamu murnar anniversary muna godiya sosai da sosai Allah ya bar zumunci* *_Miss Hajo Ce_*🤙🏿 [7/4, 15:35] Hajo hajo: 🅿️.........*79&80* Garin masoyi baya nisa wani farincikine yaji ya mamaye zuciyarshi ji yake ai matsalarshima ta kusa zuwa karshe tunda dai gashi a garin da masoyiyarshi take cikinshi Tunani yayi yanzu ina zai dosa shida bai tab'a zuwa garinba baisan ko ina ba na garin wani abokinshine musa ya fad'o masa a rai Wanda sukayi karatu a Misra d'an sokoto ne Wayarshi ya lalabo tare da kunnawa Dan tajima kashe Contact d'inshi ya shiga ya shiga laluben sunan Cikin sa a kusa yaga yana da number Dannawa number kira yayi kiran farko saida ya katse a na biyu aka d'auka Daga d'ayan b'angaren musa ya ce "Yau wace rana ce wannan Arman ka kirani da kanka kaida ka yada mutane" Murmushin da baikai ciki ba Arman yayi ya ce "Yau Juma a kaga ko babbar rana ce Shiyasa" hhhh Gaskiya ne manyan k'asa to ya garin"Alhamdulilla Yanzu haka ina garinku shine nace bari na kiraka kazo ka d'aukeni ina Aiport"Cike da mamaki musa ya ce "da gaske Abokina ko wasa" da gaske mana muntaba wasan nan haka dakai da Allah Malam kazo ina Aiport bansan doguwar magana"Murmushi musa yayi ya ce "Har yanzu halin nan naka na nan kenan Abokina Gaskiya nid'in yau d'an baiwa ne mr Arman guda a garinmu gani nan zuwa yanzu yanzu" murmushi kawai ARMAN yayi ya ce "Saikazo ina jiranka" tukwana ya katse wayar minti Ashirin me kyau tayiwa musa a aiport Sosai yayi mamakin ganin Arman Rungume juna sukayi cike da farincikin sake ganin juna Dan rabon da su had'u tun a makaranta musa da kanshi ya sanyawa Arman jakarshi a boot Bayan Arman ya shiga Shima ya shiga ya jasu suka nufi hanya Kallonshi Arman yayi ya ce "Hotel zaka kaini" Hotel kuma Abokina Nazata ai gidana zaka sauka?A a ka kaini hotel me kyau kawai "ka bari yanzu ka fara sauka gidana muje ka huta kaga harna sanya iyalina Ta yi maka girki" da mamaki Arman ya ce "Wai kana nufin har kayi auri" Dariya musa yayi ya ce "Hada yara ma biyu kuwa zauna anan har tsufa ya fara kama Ka" Murmushi Kad'an ARMAN yayi ya ce "Soon nima zanyi Saidai kuji a bazata" To Allah ya yarda Kace ka fara soyayya kenan Dan a sanin da maka ko kallon mata bakayi "ai soyayyar ce ma ka kawoni garin nan harka samu ganina?da mamaki Musa ya ce " kana nufin wai saboda budurwa kazo garinnan"of course "ya fad'a yana basarwa "da mamaki Musa ya ce 'Chabd'i amma wannan wace y'ar baiwarce nan garin take kenan" cikin kosawa da magana Arman ya ce "Nifa bazan iya da surutunka ba kamar mace gobe mayi Maganar" Dariya musa yayi ya ce "bazaka chanza ba Abokina?Kaima bazaka tab'a chanzawa ba " Arman ya fad'a yana kallon hanyar da ssukebi har suka isa gidan musa cikin girmamawa matarshi ta tarbi Arman tare da ajemai drinks kala kala Kad'an yasha baijima ba musa ya wuce dashi wani hotel dake ba nisa dasu Bayan Arman ya biya daki Musa ya koma gida da niyyar gobe zai dawo suyi magana Arman kasancewar akwai gajiya tattare dashi sosai yayi baccin da ya jima baiyi irinshi ba Dan jinshi yake cikin Wace irin nutsuwa marar musaltuwa. Da sassafe Mummy da Daddy na break fast Daddy yayi shirin Tafiya office Security ya shigo Bayan ambashi izinin shigowa saida ya bari suka gama sun fito palour ya Gaishesu cikin mutuntawa suka Amsa Mik'a wa Daddy takardar yayi ya ce "ga shi Ranka ya dad'e ya bani jiya da dare akan yau da safe na kawo muku" Amsa Daddy yayi da mamaki Dan yasan Arman ne suke ceman ranka ya dad'e sannan ya kalli Mummy ya ce "gashi kema Hajiya ya ce Wannan a baki" Da mamaki Mummy ta amsa Sallamarshi sukayi ya zuya ya tafi Daddy ne ya fara bud'e takardar cin karo da dogon rubutu da yayi kuma note d'in Arman Cikin k'asa da murya ya fara karantawa kamar haka " ```Assalamu alaikum Mahaifina na rubuta maka wannan letter badan komai ba saidan fitar daku daga wasi wasin ina na tafi na bar garin nan tafiya mai nisa ka gafarceni mahaifina bazan iya Aurar wacce ka zab'a munba ni namiji ne ina da right d'in kaina Dan haka idan ma kun d'aura na saketa saki Ukku I m so Sorrry my dear father karkayi fushi dani duk sanda ka huce zandawo gareku daga tilon d'anka Mujahed Kabir``` sosai Daddy Ya shiga rud'u da tashin hankali da tsananin b'acin rai Bayan ya gama karanta takkadar cikin bakin ciki ya ce "Ni Arman zai kunyatani,ni zai nunawa ban isa dashi ba Aiko kamar yanda yabar gidan nan yakiyimun biyayya ya barshi har abada bani bashi" cike da damuwa Mummy ta ce "Alh lafiya me Arman din yayi tana rik'e da takardar dake hannunta tama kasa karantawa" Cike da b'acin rai ya ce "Guduwa yayi Amshi ki karanta abunda Ya rubuto mun " Amsa Mummy tayi hannunta na karkarea tsabar rud'u tana gama karantawa ta fashe da kuka ta ce "Shikenan Alh ka sanya ya gudu Arman me yasa zaka mana haka me yasa " ta k'arasa fad'a tare da bude takardar da ya rubuto mata hannunta har karkarwa yake ta fara karantawa kamar haka "```Assalamu alaikum Mahaifiyata d'aya tilo da babu kamarta a duniya ina mai baki hakurin Tafiya da nayi please Mummy ki gafarceni ki yafemun nayi hakan ne badan komai ba saidan nemawa kaina y'anci nasan ke uwace kuma bazakiso wani Abu ya samu d'ankiba ki tayani da addua tare da sanyamun albarka Tabbas albarki ita ce kawai abunda nake buk'ata a koda yaushe sannan ina rokanki akan karki tayar da hankalinki please mummy nah kada ki shiga damuwa a saboda ni ni ba yaro bane bazan shiga wani hali ba I love so much I really love you so much My first love```sosai Mummy take kuka Bayan ta gama karantawa ta ce " me yasa zakayimun haka ARMAN ka gudu ka barni Bayan kasan irin tarin k'aunar da nake maka me yasa zaka zabi guduwa ka barni amma bakomai a duk Inda kake Allah ubangiji ya tsare munkai yayi maka Albarka "Cikin b'acin rai Daddy yabar gidan tare da fushin Arman Mummy ko number Arman ta dinga dialing amma a kashe Tasha kukanta Har ta gode Allah sannan ta bishi da Addu'ar Allah ha tsare matarshi aduk Inda yake daddyko hakuri yabawa Abban husna sannan yace subar duk abinda ya kashe har lefen yabar musu bainuna mishi komai ba Abban husna yace Allah sa haka shi yafi alkhairi .. Yau Aira ita kad'ai a gidan Laila ta tafi school Suna da evening lectures yayinda Daddy baya nan Mama ta fita biki a palour ta yini tana kallo cike da kad'aici kad'aicin ne ya isheta ya sanyata fitowa Farfajiyar gidan Hakanan yau take jinta cikin y'ar annashuwa da ta rasa dalili Sosai ta fad'a duniyar tunani gata nan ita da ARMAN sun zama miji da mata ya kaita bitch sai wasan ruwa suke haka dai tayi ta wasik'ar jakkanta ita kadai daga karshe kuma ta hade kanta da gwuiwa ta fashe da kuka inama ace tunaninta ya zama Gaskiya,ina ma ace Yau Arman ne mijinta,Sosai take kuka daga karshe ta Goge hawayenta tare da mik'ewa D'anta koma ciki taga ana kiraye kirayen magriba tana Mikewa taga Mubarak a gabanta kamar Wanda Yasha ya Bugu" Tsoro ya bata hakan ya sanyata saurin kaucewa zata tafi saurin shan gabanta yayi ya ce "Haba my Beauty ina kuma zaki Bayan saboda ke nazo nan d'in" ya fad'a cikin muryar bugaggu"Cike da b'acin rai Aira ta ce "Ka matsa ka bani hanya nace" k'ara wara hannunshi yayi tare da tare mata hanya ya ce "Bazan matsaba ya fad'a ya na kamo hannunta" Kallonshi Aira tayi ta kalli hannunshi wani mugun b'acin Raine ya zo mata Ta fusge hannunta Tare da wankeshi da Mari "rik'e kumcinshi Mubarak yayi ya ce " ni ni ni kika Mara"An marekad'in d'an iskan banza marar mutunci "" d'aga hannu Mubarak yayi zai shararawa Aira Mari yaji an rik'e hannunshi ta baya Tare daukeshi da Mari"Da mamaki Aira take kallon Sadiq da idanunshi suka fara sauya launi tsabar bacin rai"Kallonshi Mubarak yayi ya ce "Ni ka Mara" An mareka Dan ubanka marar mutunci Matar uban naka zaka tara harkayi kokarin marinta Dan kana Dan iska marar mutunci"Cije baki Mubarak yayi yana jin zafin Marin da yasha biyu tare da Kallon Aira yayi mata nuni da yatsa ya ce "zamu had'e Dan ubanki" Sadiq ne zai k'ara kai mishi wani Marin yayi saurin barin wajen Dan Duk iskancinshi yana shakkar Sadiq "Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da K'asa da kanta ta ce " na gode mai sunan Abba"Badamuwa Aira kiyi hakuri haka yake baida d'a a ki dinga kiyayewa idan kin ganshi kinji"gyada mishi kai Aira tayi tana Hawaye"Sosai yayi mamakin hawayen dake zubowa daga idanunta ya ce "Kukan me kike Aira ko wani abun ya faru ne" Girgiza mashi kai tayi tana Hawaye ta ce "Dan Allah Mai sunan Abba ka sanya Daddynku ya maidani gidanmu"da mamaki Sadiq yake kallonta ya ce " gidanku kuma Keda kikazo Aure Aira "Kuka Aira ta fashe dashi " Wlh Auren dole ne akayimun da Daddynku bana sonshi ina da Wanda nakeso Kawai Dan yana abokin Abba shine ya aura munshi "ta fad'a tana rushewa da kuka"Sosai Sadiq yayi mamaki Dan saiyau ya tab’ajin maganar nan ya ce "da gaske kike Aira Haba ai konima kaina nayi mamakin da kika auri Daddy " Cikin kuka ta ce "Dan Allah kasa ya sakeni ko kai ka maidani gidanmu nasan kai kana da tausayi mai sunan Abba" Numfasawa Sadiq yayi tare da cewa"Bani da ikon da zansa Daddy Ya sakeki Aira mahaifinmu mutum ne mai kafiyar bala I zaiyi wahala ya sakeki amma zan tayaki da addua akan Allah zaba miki abunda yafi zama Alkhairi sannan daga yau ki daina jin kunya ta tun lokacin da Na samu labarin Kece wacce Daddy Ya auro na hakura dake Aira saboda babu Aure tsakaninmu akwai zumunci insha Allahu zan taimaka maki wajen rage maki kadaici "Goge hawayenta Aira tayi ta ce " Nagode mai sunan Abba "masallaci Sadiq ya wuce yayinda ita kuma Aira ta koma gida kasancewar tana fashin salla D'akinta ta shige ta kunna kallo a plasma d'in dake manne a d'akin. Zaune yake akan Kujera k'aramun littafin Alquran a hannunshi yana karantawa sosai yakejin dad'in iskan farfajiyar hotel d'in Musa ne yazo mik'a mashi Hannu yayi suka gaisa tare da cewa Ya bak'unta" Bayan sun gama gaisawa nan musa Shima yaja tashi kujerar ya zauna "yawwa Abokina inajinka ina son sanin labarin nan da kace zaka bani yau Dan a k'age na kwana da sonjin labarin" kamar bazaiyi magana ba saikuma ya fara bashi labarin soyayyarsu da Aira da abunda ya had'a mahaifansu rigima har suka rabasu haryakai karshen labarin Inda ya d'ora da cewa "Ina buk'atar taimakon Abokina wajen gano gidan da Airata take Dan Allah patan zaka bani Had'in kai" Sosai musa ya tausayawa abokin nashi Tabbas akwai abun tausayi a labarin "Numfasawa musa yayi ya ce " a Gaskiya Kunga jarabawa Abokina Allah baku ikon cinyeta Saidai abunda ban fahimta ba a nan me ya kawoka garin nan me zakayi idan ka gano gidan da take"a saboda Aira nazo garin nan ina son sanin Inda take ne bazan iya cigaba da rayuwa batare da ita a kusa dani ba tayi nesa da idanuwa na Amma har yanzu kusa take da zuciyata bazaka gane irin son da nake mata abokina ba hakan yasa na yanke shawarar zuwa Inda take Dan na nemu gidan da take Na nemu Aiki a gidan hakan ne kawai zaisa naci gaba da arba da ita "da mamaki Musa ya Mike ya ce " kana da hankali kuwa Abokina Aikifa kace Haba impossible wlh kamarkai da darajarka da komai ka kaskantar da kanka a saboda mace kana d'an governor guda kace zakayi aiki a k'ark'ashin wani Gaskiya shawarar nan da ka yanke batayi ba so hauka ne aka gaya maka"so yafi hauka Abokina Son da nakeyiwa Aira ya wuce duk yanda kake tunani kada ka kashemun kwarin guiwa inason ka karfafamun hakan yasan ban nemu taimakon kowaba ba na nemu naka Saidai idan bazata taimakamunba kawai ka fad'amun"ya fad'a cikin daga murya "kwantar da murya musa yayi yana mamakin wani irin sone wannan ya ce " ba haka bane Abokina amma Ina mamakinkane Shawarar da ka yanke ce nake ganin bata dace ba Kadubafa matsayinfa maid house zakayi Haba Abokina da iliminka da kyanka da kudi ga mulki ga matsayi ka duba fa "Numfasawa Arman yayi ya ce " Tabbas hakan ya shaidamun baka San meye so ba musa so babu ruwanshi da mulki,kud'i,sarauta,matsayi da sauransu Zan iya komai a saboda Soyayyata so ba Karya bane karka k'ara katseni akan Abunda nayi niyya idan zaka Taimakeni ka tayani neman gidan if bazaka iya ba kawai ka fad'amun bazaka iya ba na nemu taimakon wani "Sorry Abokina kayi hakuri idan ranka ya b'aci yanxu shikenan yaushe zamu fara neman Gidan" Mikewa Arman yayi ya ce "For now" Girgiza kai musa yayi Dan yalura abokin nashi yayi mugun nisa a soyayya A mota musa ya Kalleshi ya ce "kasan sunan mijin nata" Harara Arman ya maka mai tare da Jan tsaki ya ce "Wlh ka k'ara ambatarmun sunan wai mijinta a nan zakayi mamakina" Dariya musa yayi k'asa k'asa ya ce "Allah huci zuciyar manya to ya sunan shi mutumin" Tsaki Arman yaja yanajin tsanar sunan ya ce "Wai Madugu? ai Madugu suna da yawa a garin nan wanne kenan Real name d'inshi zaka fad'a" Tab'e baki Arman yayi ya ce "Bansan asalin sunanshiba nasan dai ana ce mashi Madugu " Aiki ja Kace aikin namu babba ne Aiko nemoshi a garin nan akwai aiki "bincikawa zamu tayi har Allah yasa a dace " Ganin yanda Arman ya had'e rai ya sanya musa Jan bakinshi a haka sukayi da Yawata gari suna neman mai suna Madugu amma duk kwatancen da akayi musu sai suga bashi bane Sai magriba suka Koma gida cike da gajiya musamman musa da aka tada mashi aiki tun daga ranar nan kullum Arman da musa sai sun fita neman Gidan amma sun kasa samowa saida sukayi kwana biyar suna Abu d'aya sosai sukeshan wahala ba karama ba Dan Duk Inda suka tambaya Sai ace su dai fad'i lak'anin yaudai musa ya fara gajiya Dan sun gama yawatawa amma Ba nasara kallon Arman yayi yace Gaskiya Abokina na fara gajiya haka fa zamuyi ta gararanba a gari batare da mungano gidan ba"Kayi hakuri nasan ina sanyaka wahala insha Allahu jikina na bani yau za a dace "to waikai bazaka iya tuno sunan ba?wlh bansan sunansa ba amma me zai hana mu zagaya unguwowin masu kud'in garin nan tunda Shima yana da kud'i" na am da wannan shawarar musa yayi nan suka zagayawa unguwowin masu duk Inda sukaje su tambaya Dan Allah Ko sunsan gidan Alhaji Madugu sai ace musu basu saniba a haka har Allah ya kaisu Arkilla quarters Inda suka hangi wani wajen chaji Musa duk ya gaji a tare suka fito Dan tambayar mai chajin ko Allah yasa a dace Dan haka suke duk Inda suka samu tambaya suke Suna isa mik'a mishi hannu sukayi musabaha musa ya ce "Dan Allah Abokina tambaya muke ko Allah zaisa a dace" To inajinku Allah yasa na sani"mai chajin ya fad'a yana fuskantarsu"Dan Allah gidan wani Alhaji Madugu muke nema ko ka sanshi" Ciza yatsa Mai chajin yayi ya ce Madugu,Madugu,Madugu To mudai Madugu anan Unguwar Biyu ne akwai Alhaji Yusuf da kuma Alhaji bukar" Cikin Sauri Arman ya ce "Eh shine Alhaji Yusuf sai sannan ya tuno da sunanshi da aka fad'a a lokacin da Aka fad'a a gidan television " Kallonshi mai chajin yayi ya ce "Wanda ya auri wace Yarinya k'arama kwanaki Y'ar kano shi kake nufi kuwa"Eh shine Dan Allah gidan mukeso ka nuna mana" ya fad'a cike da zak'uwa "Kallonshi musa yayi ya ce " Daman kasan sunan ka bari muke ta shan wahala"mancewa nayi sai yanzu da aka fad'a na tuna da sunan"Kallon mai chajin musa yayi ya ce "Dan Allah Abokina zo zaka gwada mana gidan" Badamuwa me chajin ya fad'a tare da rufe wajen chajin ya ce "da y'ar tazara Saidai muje Tare na muku rakiya" Cike da farinciki suka yi mashi Godiya suka shiga mota Shima ya shiga A baya ya dinga nuna musu hanyar gidan Har yakaisu daidai kofar gidan tukwana ya ce "nan yayi ga gidan nan ya fad'a yana nuna musu kofar gate d'in " a tare suka kalli kofar Wani farinciki na shiga zuciyar Arman wai yau shine a kofar gidan da Cutie d'inshi take hamdala yayi a zuciyarshi ya godewa Allah Kallon musa yayi ya ce "Ka gane gidan daiko" Eh ai nama San unguwar muke ta shan wahala ya fad'a su suka maida mai chajin Inda suka daukoshi sosai sukayi mashi Godiya Inda Arman ya rubuta mishi check d'in Dubu d'ari biyar ai mai chajin nan godiyar da ya shiga kwararawa Arman bata lissafuwa harda kukan farinciki yayi wai yau shine akayiwa kyautar har Rabin million.kudin da ko kwatarsu bai tab'a kamawaba sosai ya shiga kwararawa Arman addua shi arman har gajiyawa ma yayi da amsawa a hanya musa ya Kalleshi ya ce "to mungama me wahalar yanzu meye shirin ka na gaba"shirina na gaba daga gobe zai fara kaidai abunda nakeso dakai inason ka nema mun irin abun nan na nad'in buzaye tare da kayan buzaye wad'anda suka d'an sha wahala " Dariya musa yayi ya ce "kace buzu kuma zaka koma" tsaki Arman yaja ya ce "matsalata dakai Maida serious magana wasa" washegari wajen 4 PM musa ya kawowa Arman abunda ya buk'ata Suka d'auki Hanya Suka nufi Arkilla quarters nesa da gidan sosai Arman ya ce "ya tsaya nan ya isa" Sannan ya amshi kayan ya ce Ka fita zan sanya a cikin mota"musa na mak'e dariyarshi ya fita kasancewar motar mai tinted ce hakan yasa cikin Sauri Arman ya cire kayan jikinshi ya mayar da kayan buzaye nan Duk da a k'yamace ya sanyasu amma idan ya tuna da A saboda masoyiyarshine saiyaji ma ya daina kamar kayan yana gama sanyawa tare da nad'in Buzaye bud'e motar yayi ya fito ai musa tunda ya Kalleshi yake kakkabewa da dariya hada rik'e ciki ,tsaki Arman ya ce "da yake mahaukacine ni da zaka dinga mun Dariya" Cikin Dariya musa ya ce "Sorry Abokina wlh shigarkace taban Dariya Sak ka fito wani buzu" tsaki ARMAN yaja ya ce "Bansan wulakanci lokaci na kurewa muje kawai ka rakani saida ya rakashi Har kofar get d'in sannan kuma ya juya da niyyar zasuyi waya duk yanda sukayi" Arman ya jima tsaye yana karewa unguwar kallo kafin ya fara knocking d'in get d'in gidan mai gadi ne ya fito tare da bud'ewa Karewa ARMAN kallo yayi ya ce "Malam lafiya" lafiya qalau Mai gidan yana ciki"Arman ya bashi amsa cikin muryar buzaye daya kirkira "eh yana ciki wa yake nemanshi"? ni nake nemanshi Dan Allah Ko zakamun iso da shi" Tsaf me gadin ya k'ara karewa Arman kallo ya ce "Ikon Allah yau kuma buzu ne a gidan Ya fad'a tare da shiga cikin gidan a lokacin Alhaji na palour yana Danna lapton mai gadi ya shigo ya shaida mashi yana da bako Okay ina zuwa ka shigo dashi Alh yafada tare da mik'ewa mai gadin na komawa yabawa Arman hanya ya ce " ka shigo"a hankali Arman ya shigo gidan daidai lokacin da Alhaji magudu ya fito da Kallon tsana Arman ya bishi dashi yana jin dama da dama da saiya kashe mutumin Chan da ya rabashi da masoyiyarshi Karasowa Alh yayi da mamaki yake kallon Buzun mutumin Tare da cewa "Malam lafiya" Dagowa da idanunshi Arman yayi ya sauke a na Madugu dak'yal ya iya yak'i da zuciyarshi yanda yakejin kamar ya Fard'o mutumin cikin muryar buzanci ya ce "Ina wuni Alhaji ni bak'one a garin nan ina neman Aiki ne ko da gadi ne indai zansamu inci insha shine kawai burina koda bansamu albashi ba" Kallonshi kasa da sama Alh yayi kafin ya ce "to nidai Gaskiya nan ina da ma aikata ina da mai gadi da masu bawa flowers ruwa driver ne kawai nake nema Wanda zai dinga kai iyalaina unguwa kai kuma banjin ka iya tuk'i " Cikin Sauri Arman ya d'ago ya ce "Alhaji ai na iya tuk'i" Kallon rainin wayau Alhaji yayimai ya ce "Kai dinne ka iya tuk'i ina ganinka a haka" wallahi Alhaji na iya tuk'i a aikace aikacen da nayi nayi driver kuma idan kana kokonto zaka iya gwadawa"Shidai Alhaji mamaki yake yaza ayi Ace buzu dayazo daga rugage ya iya tuk'i Dan son tabbatarwa mik'awa Arman key d'in motarshi yayi ya ce "Amshi ga mota ta Chan a parking space fiddomun ita ka kawo ta nan" Amsa ARMAN yayi yana hamdalar ya taka nasarar matakin farko cikin Sauk'i haka ko akayi yanda Alhaji ya fad'a haka ya fito da motar"Cike da farinciki Madugu ya ce "Eh Gaskiya ka iya tuk'i gashi cikin nutsuwa daga yau na d'aukeka Aiki duk wata zan dinga biyanka dubu talatin " Kasa da kanshi ARMAN yayi ya ce "Saidai wani hanzari ba gudu ba Alhaji bani da wajen kwana " karka damu akwai BQ zansa a share maka d'aki nan zaka dinga kwana"to nagode Alhaji Allah Kara budi"Arman ya fad'a zuciyarshi na mashi zafi "Karka damu yaro ai na yaba da hankalinka yanzu bari naje na fito da mutanen gidan na gabatar musu dakai sosai gaban Arman ya fad'i amma ya fisge Alh Yusuf na shiga gida ya shaidama su Hajiya saude ya d'aukar musu driver suje su ganshi Laila hada tsallen murna a lokacin Aira na mata kalaba Mikewa tayi ta ce " Sis taho muje Tare"B'ata fuska Aira tayi ta ce "kuje kawai ni basainajiba" Mama saude ce ta ce "a a a kema fa saikinje ai hakkin kine " Saude Da Alhaji saida suka fita tukwana Laila ta mik'ar da Aira suka fito Hakanan Aira tajita yanayinta ya sauya kallon Arman Hajiya saude ta yi ta ce "Alhaji ai wannan yayi nutsuwa Saidai naga kamar ba buzu ba kamar yafi kama da bafullatani" Gaban Arman ne ya bada daram Alhaji ne ya ce "inbanda abunki saude meye maraban buzu da Fulani sannan ya kalli Arman ya ce " wannan itace uwargina "Juyawa yayi ya kalli su Aira dake Tunkarosu tare da cewa " wad'anchan kuma Y'ata ce tare da Amarya"gabanshine ya bada daram daidai lokacin da ya d'ago idonshi ya sauka akan na Aira da itama shid'in take kallo karaf idanunsa suka sartse Dana juna" Rumtse idonshi Arman tare da budesu ya k'ara saukesu a nata jin abun yake tamkar mafarki sosai yaga ta k'ara mishi kyau Saidai kuma ta rame Aira ja tayi turus ta tsaya Inda take bugawar zuciyarta ya tsananta Ji take kodai mafarkine idan ba idon tane ya gane mata ba daidai ba Arman take gani da shigar buzaye gabanta Nunashi tayi da yatsa tana son magana mamaki ya gama cikata Duk kallonta suka tsayayi da mamaki sukace kin sanshi daman "Rumtse idonshi Arman yayi ya ce " Innalillahi wa inna ilaihiraji'un shikenan Aira zaki ruguzamun plane da na jima ina shiryawa............✍🏿 *Tofa ya kenan Fans Ga Aira ga Arman Me kuke tunanin zai faru nan gaba karfa Aira ta kwafsamai ta ruguzamai shiri*💃🏾💃🏾💃🏾💃🏾💃🏾Warrrrrrrrrr💃🏾 _*Miss Hajo ce*_ [7/5, 17:12] Hajo hajo: 🅿️...........*81&82* ...Ruguzamun plane d'in dana jima ina shiryawa "sauke hannunta Aira tayi tare da rumtse idonta ta ce " wai meyake neman damuna karfa na haukace Yaya Arman gizau yake mun mema zai kawo Arman gidan nan meya had'ashi da buzanci kuma "duk cikin zuciyarta take maganar nan" Laila ce ta dafata ta ce "Yadai ko kinsanshi ne" Bud'e idonta Aira ta sakar mata murmushi ta ce "a a a bansanshiba Yadai yimun kama da wani Wanda na tab'a ganine sai yanzu na lura bashi bane" tana gama fad'a ta Juya Dan batason k'ara had'a ido da Buzun mutumin nan zuciyarta neman tarwastewa take "Da kallo suka bita har ta wuce" Arman ko wata nauyayyar Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Alhamdulilla Allah na gode Maka Amma yayi mamakin yanda Aira ta kasa ganeshi gashi da farko dai Ta nuna ta ganeshi ko meyasa kuma ta nuna bata sanshiba " Aira tana komawa d'akinta ta nufa saboda tsananin sara mata da kanta yayi Gado ta haye tare da rumtse idonta ta ce "Ya Allah Arman harya faramun gizau to meyasa da Chan bana kallon mutane a matsayinshi sai wannan buzun da sak yaya Arman d'ina nake gani,tsaki taja ta ce " Lallai na fara haukacewa Ma me zai kawo Arman gidan nan " a haka tayi ta sake sake akan buzun nan a cewarta. BQ aka sharewa Arman tare da samashi Katifa a ciki da niyyar gobe zai fara aikinshi Koda Ya kwanta bacci k'auracewa idanunshi yayi Kallon d'akin yayi tare da Inda yake kwana Wanda gaba d'aya gidanma yana da dukiyar da zai rabawa sama da mutum d'ari irinshi ba tare da dukiyarshi ga girgiza ba "Murmushi Yayi tare da sanya hannunshi a baya ya had'esu ya d'ora kanshi ya ce " So kenan" washegari tunda Safe ya tashi Ya kai Laila school ya dawo a lokacin Aira ta lek'o kenan ta window shi kuma yana fitowa murza idanunta Aira tayi ta k'ara budesu tsorata tayi da ganin shi d'inne da gudu ta Ruga ta koma d'akinta tana ta karanto duk addu'ar da tazo bakinta Kardai Gamo ne take tayi. Arman ko sosai yaso had'uwa da Aira A lokacin amma ya gagara da Yamma yaje ya d'auko Laila daga school Wanda tun a hanya sai iyayi take yimashi shidai shiru yayi yanajin haushin ta da tsananta Dan Duk abinda ya shafi mutumin nan ya tsaneshi musamman yarinyar da yaga sai shishige mai take Laila ko tana dawowa bata iske Aira ba A palour bedroom d'in Aira ta nufa tana zuwa ta isketa tana salla saida ta jira ta gama da zumud'i ta ce "Wai kinsan Me sis?A a saikin fad'a " Lumshe idanunta tayi tare da murmushi ta ce "Wlh sabon driver d'in nan ya had'u ke saima kinji muryarshi zazzak'a da ita har so nake yayi magana saboda karkiga yanda muryarshi ke rikitani" Gaban Aira ne ya fad'i saurin fisgewa tayi ta ce "Uhm Laila kenan to ya school d'in kunyi text d'in kuma" Dan son barin wancen zancen "tab'e baki tayi ta ce 'wlhko munyi Ai lecturer nan baida mutunci Da banjeba fa da na fad'i " Daga nan suka cigaba da hirar makaranta Wanda Aira Duka hankalinta na kan buzun nan Da daddare Bayan isha'i Aira kasa daurewa tayi Dan so take ta tunkari buzun nan Dukda fargabar da take Dan a zatonta Aljanine yake mata suffar Arman d'inta Hakanan tayi shahada ta fito saida ta lek'a ko ina taga bamai ganinta kuma taci sa a palourn ba kowa cikin Sauri ta nufi BQ d'in gidan Dan Laila ta fad'a mata Chan aka saukeshi tana sanda haka harta isa d'akin da tagani bud'e da labule ya tabbatar mata da nan yake a hankali ta tura kofar tare da Yin bismilla tana shiga ta ganshi kwance yana d'an latsa waya Arman jin shigowartata kawai yayi cikin Sauri ya Mike daga kwancen da take Da mamaki yake kallonta Cike da farinciki ya ce "My Cutie" Wara idanu Aira tayi jin ya ambaceta da sunan da Arman d'inta kad'ai yake kiranta dashi cike da tsoro ta ce "Dan Allah kai D'in mutum ne ba aljaniba meyasa kakemun suffar mutumin danafi k'auna a rayuwata " murmushi Arman yayi tare da wara mata hannu Alamun tazo gareshi ya ce "Ba aljabi bane my cutie nid'in ne dai Arman d'inki" Cike da mamaki Aira ta ce "Yaya Arman Me ya kawoka nan kuma" Murmushi yayi mata tare k'ara wara mata hannuwanshi ya ce "So my cutie soyayyarki ta kawoni" Da gudu Aira ta Ruga tare da Fad'awa jikinshi ta fashe da kuka mai cin Rai"wace nutsuwace ta dirarwa Arman Ajiyar zuciya ya sauke "Jin abar K'aunar tashi a jikinshi Dadddabata ya fara kamar yanda yake mata a baya ya ce " is okay my Cutie ba kuka ya kamata kiyi ba farinciki ya kamata kiyi"Lafewa Aira tayi tana shakar daddad'an k'amshin turarenshi da bazata tab'a mantawaba dashi a rayuwarta ba Irin salon yanda yake daddab'a Bayan nata ya k'ara tabbatar mata da shi d'inne lumshe idanunta tayi ta ce "Yaya da gaske Kaine please Idan mafarkine nake ya Allah kada ka tasheni daga wannan mafarkin Ka dawwanar dani a cikinsa har k'arshen rayuwata" Shafa bayanta yake a hankali ya ce "Ba mafarki bane cutie a zahirance d'in nine dai yaya Arman d'inki da Abba ya rabamu Allah ya sake had'amu" Tashi Aira tayi tare da Kallonshi Kamo hannunshi tayi cike da farinciki ta ce "my yaya da gaske Kaine dai na kasa gaskata mafarkinnan"murmushin da ya mance yaushe rabon da yayishi yayi tare da shafa mata fuska ya ce "nid'inne dai Arman yayanki kuma mijinki insha Allahu mai k'aunarki na har abada"Wara idanu Aira tayi cikin fara a ta ce " yaya Ya akai kazo wajen nan me yakawota nan gidan matsayin driver kuma ?murmushin gefen baki yayi ya ce "a saboda soyayya ba abunda bazan tab'ayiba a rayuwa Aira a saboda son da nake maki banajin bazan iya afkama ko wani hatsari ba a saboda ke soyayyarki daga Allah ne ked'in a jinin jikina kike Bazan tab'a iya jurewa rashinkiba a tare dani hakan yasa Bayan Naji sauk'i na yanke shawarar nemoki a duk Inda kike Wannan ce kawai nayi tunanin mafitar da zan samawa kaina ta hanyar aiki a k'ark'ashin mijinki...rumtse idonshi yayi yanajin kamar wani dutse ya tokare mashi zuciyarshi " Tuni hawaye sun gama wankewa Aira fuska Shafa fuskarshi tayi ta ce "Hak’ik’a aya kaid'in ka cika masoyi na Gaskiya Wanda babu kamarsa a duk fad'in duniya Allah nagode maka daka had'ani da masoyin da babu kamarsa mai yimun soyayyar da babu irinta mai sona saboda kai ya Allah Sannan ta fad'a Jikinshi ta fashe da kuka ta ce " I love you yaya bansan irin kalar adadin Kaunarka a cikin zuciyata please yaya wannan dama ce muka sake samu please ka tashi kawai mu gudu muje muyi Auren mu?Shafa bayanta yayi yana goge hawayen da suka so zubo mata ya ce "Bazamu gudu ba cutie " Da mamaki ta d'ago hawaye jab'e jab'e a fuskarta ta ce "saboda me.yaya Bayan mun sake samun dama" Saboda da igiyar Auren banzan Chan a kanki ya sanya bazamu gudu ba harsai Ya sakeki"Cikin kuka Aira ta ce "Ni yaya Banajin a jikina ina da wani Aure ni ban daukeshi matsayin mijina ba kawai mugudu yaya" shafa kanta yayi cikin sigar lallashi ya ce "Komai ba ayinshi cikin gaggawa my cutie ba yanzu ba" Lafewa jikinshi tayi tare da turo baki ta ce "To sai yaushe" Lakutar kumatunta yayi cikin sigar zolaya ya ce "Sai sanda kika zama jawar da kud'in yaro" Bugunshi a k'irji Aira tayi tare da turo baki cikin shagwaba ta ce "Allah yaya zan sanya maka kuka " Murmushi yayi ya ce "I m sorrry my prince's d'ina ayi hakuri kar ayi kukan nan wasa nake" Murmushi tayi tare da kafesshi da idanu ta ce "I love you so much My buzuna" Murmushi yayi ya ce "I love too Matar buzu" Duka Dariya sukasa a lokacin jinsu suke cikin farinciki da annashuwa marar musaltuwa harsun manta da damuwar da suka shiga a baya Arman ne ya ce "Had'in kanki nake buk'ata cutie wajan ganin mun cimma burinmu karki sake ki nunawa kowa kin Sanni zamu dinga mu'amula da juna a sirri kingane "Gyad'a kanta tayi ta ce " to my yaya"Jinjina mata hannu yayi ya ce "Good girl " Amma wai ya akayi jiya kad'an ya hana ki kwafsamun"Murmushi tayi ta ce "Na d'auka gizau ne kakemun Ko kuma Aljanine ya kemun siffarka Dan Yaga ina mugun sonka zai tsoratani da kai" Dariya yayi ya ce "Lallai My cutie Aljanin nan da bai kyauta ba kice har yanzu ina ranki alk'awarinmu bai tafi a banza ba" Murmushi tayi tare da kama hannunshi ta murza hannunshi ta ce "Kar Allah ya kawo ranar da zan manta dakai my yaya da ranar tazo gwara mutuwa ta Alk'awarin mu bazaije ko ina ba ya na nan har abada" Sun tab'a Hira sosai Cike da farincikin da sun manta yaushe rabon da su shiga irinshi Wanda basu sani ba har sha d'aya tayi saida Arman ya duba agogo wara idanu yayi ya ce "Maza cutie tashi ki koma kalli agogo " Turo baki tayi ta ce "Ni nan zan kwana" wara idanu yayi sai kuma yayi murmushi ya ce "Kiyi hakuri ki koma ciki ai koda yaushe muna tare banason a fara samun matsala tun ba Aje ko ina ba" tana gunguni Aira ta mik'e Shidai lallab'ata yake Shi ya rakota har wajen Haske tukwana ya juya tana waiwayen shi Harta k'arasa part d'insu Arman tun a hanya ya fara istighfari Dan yasan a yanzu Aira da Auren wani a kanta amma babu yanda zai iya da zuciyarshi D'aga hannu yayi ya ce "ya Allah ina neman gafara da yafiyarka ya Allah na kasa jurewa ne a kanta koda ya koma ya kwanta bacci mai dadine yayi awon gaba dashi saboda tsananin farincikin da yake ciki Airako koda ta koma cikin sand'a ta shiga gidan Allah ya taimaketa ba kowa kowa yana Dakinsu cikin sand'a ta nufi part d'inta tana shiga ta sauke ajiyar zuciya Cike da farinciki ranar tayi baccin da har ta manta rabon da tayi bacci cikin kwanciyar hankali haka y'an gidan ko kasancewar sunsan Aira gwanar zaman dakice ta kulle kanta ya sanya basu damu da Rashin ganin nata ba Alhaji Yusuf ko lokacin daman dakin Hajiya saude yake kuma fushi yake da Airar ya sanya baibi ko ta kanta ba washegari Aira cikin farinciki ta tashi Wanda har Laila saida ta gane hakan tambayar ta tayi ta ce " wai Sis ya akayi yau naganki cikin farinciki Dariya Aira tayi ta ce "kawai Hakanan nima najini cikin farinciki" Dariya Laila tayi ta ce "kodai Anfara son dadynmune" Harara Aira ta galla mata tare da tilla mata Pillow ta ce y'ar air kawai"Murmushi tayi tukwana sukaci gaba hira Arman ko Alhaji Yusuf ne ya kawo mashi wasu kaya Zasukai kala shida ya ce "ga shi ya dinga sawa Ya daina shigar buzayen" Godiya yayi mishi a yana fita ya ja tsaki tare da Wulli da kayan wai yau shine ARMAN har wani banza zai bashi jace"Saikuma yayi murmushi ya ce "a saboda so ne Ai " Hakan ya karamai kwarin gwuiwar Dan bayajin ciwon kome zaiyi kome zai sameshi indai a soyayyar Aira ne daga kayan yayi yaga suna da tsafta kuma basu sha jikiba kamar sabbi Tsaki yaja Dan daman ya gaji da kayan buzayen koda yayi wanka shiryawa yayi cikin wani black yadi da yasha d'inkin Kufta sosai ya fito yayi kyau ya dawo asalin Arman d'inshi koda ya fito domin kai Laila school kasa Daina Kallonshi yayi Wanda har saida yaja tsaki shiyadawo da ita daga duniyar tunanin data Lula sosai ya tafi da imaninta Dan ita a yanda ta ganshi baiyi mata kama da driver ba kwata kwata ya koma kamar wani basarake ko kuma hamshak'i Dan yanayin fatarshima daka gani kasan Hutu ya zauna a ciki da wannan tunanin har ya kaita school koda ya maido da ita d'akin Aira ta nufa a lokacin tana linke kayanta kamo hannunta tayi ta ce "Sis wai kinsan wani abun mamaki kuwa wlh sabon driver d'innan kwata kwata baiyi kama da kaskantacce ba Karkiga yau da yasa kayan hausawa yanda yayi masifar kyau har tuntube nasoyi Dan Kallonshi Gaskiya guy din ya had'u wlh tunda nake bantab'a ganin guy me kyanshi ba sis Kinga kuwa fatarshima kuwa Yanda take shining Gaskiya guy d'innan ya had'u iya had'uwa Dan a ko novel da nake karantawa yanda ake zuzuta mazan novels to zan iya ce maki wannan yafi Namijin novels kyau tak'amaimai dai in fad'a maki sis Ki kirashi da mijin novel kawai (lol😝)Dan yakai duk Inda baki tunani.Sosai Aira taji wani wutar kishi na taso mata wai Arman dintane wata mace ke yabawa haka lokaci guda taji tsanar Laila tatsargu cikin zuciyarta Danne b'acin ranta tayi da zafin da takejin cikin zuciyarta ta ce " Uhm su Laila manya"Harararta Laila tayi ta ce "haka ma zakice wai meyasa jiyama na kawo maki maganarsa kin shareni" Tab'e baki Aira tayi ta ce "To me kikeson nace maki Laila" Bata fuska tayi ta ce "Tayani zakiyi ko zanji dadi sannan ki bani shawara Dan wlh sonshi nake" A matuk'ar zabure Aira ta mik'e ta ce "so so fa kika ce Laila" Da mamaki Laila take kallonta ta ce "Meye naga kin tada jijiyoyin wuya saikace wacce ta ce tana son mijinki"ko saurayinki ?Rumtse ido Aira tayi ganin zatayi baram baramma ya sanyata saurin gyarawa ta ce "Amma dai Laila baki da hankali ki rasa Wanda zakiso sai Wanda yake K'ark'ashin mahaifinki driver d'inki ne fa Haba Is not your class ke ai Matar manyace" Ajiyar zuciya Laila ta sauke ta ce "Daman a saboda wannan ne ni har kin tsoratani Ai ba wani Abu bane Dan kaso Wanda yake k'asa dakai Sai Abba ya mayar dashi mai kud'in wannan ba wani Abu bane tunda dai ina sonshi nasan shima zai soni ta fad'a tare da tashi tace “Kinga bari naje na watsa ruwa na Shawo rana" Tana fita Aira taja dogon tsaki tare da Wulli da Kayan linkin ta ce "Chabd'i wlh bazai yuba Kujimun wani sabon iskancin Tama rasa Wanda zataso sai Arman d'ina Wanda mallakin nawa ni kad'ai sosai ta karajin tsanar Laila a ranta kasa daurewa tayi cike da jin Haushi tana cika tana batsewa ta fito farfajiyar gidan Hangoshi tayi a wajen parking space Shima ita yake kallo yana mamakin yanda ta wani had'e rai wajenshi ta k'arasa yana ganin haka yayi saurin janta wajen lambu Dan kar a gansu kallonta yayi cike da kulawa ya ce " Yadai naganki haka my prince's me ya faru"Kama k'ugu tayi tare da turo baki ta ce "Nidai Gaskiya Yaya daga yau karka k'ara kai Laila school banason ganinka da ita cewafa tayi tana sonka dan iskanci" Shi maganar ma dariya taso ba Arman saida ya d'an dara tukwana ya ce "Ummm cutie manya Wannan kishi haka kamar zaki tashi sama" Harara ta galla mai ta ce "wasa ka d'auka ko?Kama hannunta yayi ya ce " inbanda abunki cutie ina ruwana da ita keda kikasan halina ai Saidai kiba wani labarina Me zanyi da wata Gaki kalloma ni bata isheni ba haryau bazan iya ce miki ga kalartaba saboda ko kallonta ban tab'a yiba calm down ki nutsu karki damu da wannan kisa a ranki danke kad'ai akayini " Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da turo baki ta ce "To nidai na k'agara mu tafi mu bar garin nan yaya" gyara mata gashin kanta yayi da ya bazo ya ce "Karki damu akwai lokaci ai" Sun tab'a Hira sosai a nan Saida Aira ta Hango Motar Daddy Ya sanyata tashi cikin Sauri ta bar wajen shikuma Arman ya koma BQ. Kullum Arman da Aira saisun kebe sun zuba love d'insu kamar saurayi da budurwa Dan Arman mancewa ma yake da Akwai Aure a kanta itako Aira daman bata daukin Auren da komai ba Dan bata tabajin kanta a Matar Aure ba Satin Arman guda kenan Kullum saisun had'u batare da wani ya tab'a ganinsuba Dan Daddy yayi tafiya kwana huduma bare ya takurawa Aira ranar da ya dawo Aira Sun shirya fita da Arman Ta rasa yanda zata tambayi Daddy haka nan tayi shahada ta je palourn da yake yana zaune yana shan fruit nesa dashi ta tsaya tana wasa da zoben hannunta shiko tunda ta shigo ya zuba mata Idanu ba ko k'iftawa sun kai minti biyar ba Wanda ya ce uffan da kyal Aira ta iya d'ago baki ta ce "Ina yini Daddy andawo lafiya" Ajiyar zuciya tajo ya sauke Tare da cewa "Alhamdulilla my Beauty kin fara hankali ko" Tsaki Aira taja a ranta a fili kuwa murmushi tayi Wanda baikai cikiba sosai Alh Yusuf yayi farinciki ya ce "Inaga beauty ta hakura " Cikin y'ar in ina ta ce "Uhm Uhm Daddy Daman fita nake so nayi tunda nazo banje ko ina ba gashi ina son naga gari" Cikin fara a ya ce "Ai ba matsala Beauty gashi na gaji ai dani da kaina ma zan kaiki Na kaiki ko ina amma ba matsala Bari nayiwa driver magana saiya kaiki duk Inda kikeso Ko" Hamdala Aira tayi a cikin ranta Murmushi tayi tare da mik'ewa ta ce "Thnks Daddy Bari naje na shirya" murmushi yayi ya ce "Bazaki daina Cemun wannan daddyn ba ko" k'asa da kanta tayi tare da barin D'akin cikin Sauri ta shirya cikin Abaya doguwar Riga black da tayi mugun amsarta ta yafa belt din rigar sosai yayi mata kyau Ga gaban lallausan gashin kanta da ya kwanta ya fito Tunda ta fito Alhaji ya kafeta da idanu bako k'iftawa sosai yake godewa Allah daya bashi zuk'ek'iyar mata kama hannunta yayi ya ce "kinyi kyau my baby" Sosai Aira taji haushin rik'e mata hannu da tayi Dan ba yanda zatayi a tare suka fito shida ita hannunsu rik'e Dana juna Arman dake cikin mota tunda ya hangosu yaji wani irin bak'inciki Ya mamayeshi Ji yake kamar yaje ya fisge Aira daga hannun Alhaji Yusuf Rumtse idanunshi yayi da karfi Dan bai buk'atar Kara ganinsu har mota Alhaji ya kai Aira tare da bude mata back sit ya sanyata Tare da rufewa zagayawa yayi ya kalli Arman ya ce "Ka bimun ita a hankali kaji Dan daman ya fad'a mashi Inda zai kaita sannan ya bashi kudade dan ya mata sayayyar abunda take buk'ata Dak'yal Arman ya iya d'aga baki ya ce " To tare da Jan motar Horn yayi mai gadi yazo ya bud'e masu a guje sukabar gidan........✍🏿 _*miss hajo_*🤙🏿 [7/5, 22:01] Hajo hajo: 🅿️.........*83&84* .....A guje suka bar gidan Aira har tsoron gudun da ya sharara tayi Sun d'an bar layin taji ya tsaya ba tare da ya kalletaba ya ce "Dawo gaba" A sanyaye ta fito ta koma gaba tare da rufe k'ofar Kallonshi tayi taga yanda ta had'e girar sama da ta kasa a hankali ta ce "Ina yini Yaya" Ba tare da ya kalletaba ya ce "Lafiya" Cike da nuna Rashin jin dad'i ta ce "Yaya ko nayi maka wanin abun naga kana b'ata rai" Kallonta yayi yaga yanda tayi bala in kyau lokaci guda yaji tsananin kishinta na k'ara ninkuwa cikin zuciyarshi tab'e baki yayi ya ce "Shine Dan ki nunamun kinyi Aure hada Fitowa hannunki mak'ale da nashi ?Cikin marairaicewa ta ce " Yaya nima bani nace ya rik'emun ba Bafa kuma nima banso ya rik'emun hannuba abunda yasama na Kyaleshi Dan Karya hanamu fita"Uhm kawai ya ce Tare da lalubo Wayarshi itadai Aira ta zuba mashi idanu bako k'iftawa Dan idan tana Kallonshi ji take kamar za a kwace mata shi Arman musa ya kira yayi mashi kwatancen Inda suke Ya shaida mashi gashinan yana kashe wayar kallon Aira yayi da ta zuba masa idanu hura mata iska yayi a idanu tare da cewa "wannan kallo haka ai saiki cinyeni" Firgit ta dawo cikin hankalinta tare da turo baki ta ce "Kai yaya saikace mayya" Zan Bugi bakin fa"Dariya tayi ta ce "Sorry my yaya" kinyi kyau cutie"Murmushi tayi tare da K'asa da kanta ta ce "thnks kaima kayi kyau my yaya " sosai suka shiga hira da labarai Wanda har saida ta mantar da Arman haushin da yakeji a haka musa ya samesu Kallon Aira yayi ya ce "Amma fa Gaskiya Kin rikitamun aboki da yawa kin zautashi Kotu ta kamaki ba k'aramun hukunci zata yanke maki ba " murmushi Aira tayi tare da K'asa da kanta "Kallon Arman yayi ya ce " Ammafa Abokina ba k'arya dole ka zauce ko nine na samu wannan zanyi abunda yafi naka"Wata irin harara Arman ya banka masa tare da cewa "ka iya bakinka wlh Wama yasa ka kallemun ita Dan sa ido kawai " Dariya musa yayi ya ce "Maida wukar yanzu dai ina ne za a Naji kiran gaggawa" wajen shakatawa za a kai cutie to kasan bansan ko ina a garin nan ba shine na kiraka ka mana jagora"Musa yayi musu rakiya duk wani wajen shakatawa yayinda Arman yayi wulli da kud'in da Alh Madugu ya bashi akan yayiwa Aira sayayya itadai Aira batace uffan ba Dan Tasan halin kayanta saida lallamo sosai suka shakata suka sha love d'insu kamar saurayi da budurwa Sune basu koma gida ba sai wajen isha'i sosai Aira take nishad'i Suna komawa Aira ta fito tana Dariya Shima Arman ya fito yana fara'a Daidai lokacin da laila ta lek'o da mamaki take kallonsu Sosai gaban Aira ya fad'i Arman ko fusgewa yayi cike da fargaba Aira ta nufi Inda Laila take ta ce "Ina zuwa sis" Bako ina Laila ta bata amsa tare da komawa ciki tana tunanin Me ya maida Aira gidan Gaba ?sannan tunda tazo bataga fara'arta buzu ba (Dan haka suka samai suna saboda basusan sunanshi ba Kuma babu Wanda ya tambayeshi game da sunanshi ko Tarihin shi) amma yanzu shine ta gani yana Dariya sannan tunda aira tazo garin nan bata taba sha'awar fita wani wajeba sai zuwan buzun nan zuciyarta chunkushe da tunani Aira ko tabe baki tayi tashigewarta Takoyi sa a Daddy bayanan tun daga lokacin nan Laila ta sanya musu ido Yayinda su kuma harkar gabansu suke ga kirkirar zuwa shopping ko saloon da Aira take tarka Wanda Daddy yake sanya Arman ya kaita sosai sukeshan love d'insu batare da sanin kowaba amma kuma ko hannunta yanzu arman baya yarda ya taba saboda yasan haramun ne tunda da igiyar wani a kanta ko rungumarsa tazoyi kaucewa yake hakan yasa itama tadaina yunkurin fadawa jikinshi Wanda Laila duk tana ankare da hakan hakan yasa yanzu sama sama takeyiwa Aira itako hakan bai dameta ba saboda yanzu Arman ya maye mata gurbin kowa data rasa hakan yasa hankalinta kwanciya a haka har Arman yayi wata guda a gidan yau Aira tana d'akin Arman suna ta shan Hira har Sha biyun dare tayi batare da sun sani ba saida suka Ankara tukwana Aira ta baro BQ din cikin sand'a ta shiga cikin gidan Kichibus sukayi da Laila dake kokarin shiga kitchen Dan harta kwanta bacci taji yunwa hakan ya sanyata zuwa ta had'a tea Sosai cikin Aira ya d'uri ruwa cike da Kallon tuhuma Laila ta bita ta ce "Daga ina kike da Daren nan ke kuma" Cikin muryar Rashin Gaskiya Aira ta fara in ina saikuma ta ce "Uhm mura ce ta kamani wlh shine na D'an lek'a na ga ko naga Wanda zai sayo man magani" tunda ta fara maganar Laila tasan karya take tab'e baki tayi ta ce "hmmmmmm " Tare da shigewa kitchen Aira ko tsaki taja tare da Wucewa d'akinta Tana zuwa ta iske Alh Yusuf sai safa da marwa yake Sosai ta tsorata Juyowa yayi cikin b'acin rai tare da daka mata Tsawa ya ce "Daga ina kike" Sosai Aira ta rude cikin in ina tace ba ko ina yanzu na fita fa"na kusa awa d'aya a d'akin nan shine zakicemun yanzu kike fita daga gidan ubanwa Kike"Ganin ya na hayayyak'o mata ya sanya ta murgudamai baki tare da Jan tsaki Saurin Juyawa da gudu tayi bedroom d'in Laila kallonta Laila tayi ta ce "Lafiya kuwa" rufo d'akin tayi ta ce "Nan zan kwana tare da nufar gadon ta kwanta" Mamaki duk ya gama cika Laila Tab'e baki tayi tare da Gama shan tea d'inta itama taja ta kwanta a lokacin Bacci har ya d'auki Aira washegari koda ta tashi bataga Laila ba fitowa tayi a palour ta tarar da Mama tare da Daddy da ya kura mata Idanu kasa tayi da kanta ta ce "Ina kwana Mama" ba yabo ba fallasa ta amsa Da lafiya Qalau"Kallonshi tayi ta ce "Ina kwana" Lafiya qalau my Beauty Kintashi lafiya"Harara Mama ta gallamai tare da Jan tsaki Aira ko alhmdll kawai ta ce ta wuce cikin Sauri sosai tayi mamakin yanda bai mata magana akan jiya ina taje, Da Yamma Aira na zaune a lambu sai Hirarsu sukesha Dan wajen babu kowa Aira hira tayi dad'i ta d'ora kanta saman kafad'arshi duk yanda Arman yayi ta tadashi kiyawa tayi "Aira ce ta ce " wai yaya zaman me muke haka har yanzu kak'i sama mana mafitar da zai sakeni ni wlh nagaji yanzu fa watana ya kusa hud'u gidannan ni wlh na gaji "Nima tunanin hakan kawai nake my cutie Saidai kuma har yanzu na kasa Nemo mana mafitar da zai sakeki din muje muyi Auren mu nafiki damuwa da hakan cutie Dan bakisan yanda nake kishin zamanki a gidan nan ba"Lumshe ido Aira tayi ta ce " Uhm My yaya wai ina Mummy Dan Allah kiramun ita nayi kewarta " cutie kenan so kikema su gane muna tare asirinmu ya tonu Bayan na baki labarin ta yanda na taho ai ko sim d'ina sabo na sauya saboda karma a nemeni a wancen Dan nasan Mummy zata neme ni"dafe goshi Aira tayi ta ce "Kuma fa hakane Amma fa yaya nayi mamakin dabarar nan taka Gaskiya kaid'in na musamman ne basirarka tayi yawa" Murmushi yayi tare da shafa kanta ya ce "Ko my Quen " Murmushi tayi tare da Lafewa jikinshi ta ce "Eh mana my Zuma na" Wara idanu yayi tare da cewa "Wow Yau na samu sabon suna kenan" Dariya tayi tare da rufe fuska Hango Laila Da Aira tayi tana nufo wajen ya sanyata saurin tashi gabanta na fad'uwa duk ta rikice sai sannan Arman ya lura Inda take kallo tsaki yaja tare da saurin barin wajen Laila ko tana isowa da wani irin banzan kallo ta dinga bin Aira dashi Tare da Jan tsaki ta ce "a juri zuwa rafi dai kuma ki sani a tafin hannuna kike yawo zanga gudun ruwanki idiot kawai da Aurenki da komai" Da mamaki Aira take kallonta ta ce "Me kike nufi wai " duk yanda kika d'auka "Tsaki Aira taja ta ce " Kanki akeji "Tare da barin Wajen Laila ko cike da b'acin rai Ta koma ciki tare da zuwa d'akin mamanta ta na hak'i ta ce Wlh Mama akwai matsala gidan nan" wace matsala kenan Laila?"Mama wlh zargin Aira tare da Buzun nan nake nan ta bata labarin duk abubuwan da take gani a tare da su"Dafota Sa a tayi ta ce "Meye abun had'a jijiyoyin wuya Ai wannan babbar dama ce ta samemu da zamu fitar da shegiyar yarinyar nan daurewa kawai kikaga inayi amma babanki yanzu zaman hakuri kawai nake dashi hankalinshi duka yana kan figigiyar yarinyar chan Dan haka ki k'ara sanya musa ido sosai har lokacin da zaki kamasu Turmi da tabarya Kinga daga nan ai ko ta gwal ce ya saketa " Goge hawayenta Laila tayi ta ce "Mama son buzun fa nake " Harara ta galla mata ta ce "Ke bansan shirme ki rasa Wanda zakiso sai na kasa dake wuce kiban waje sannan kiyi abunda nace kinji" gyada mata kai tayi ta ce "Insha Allahu Mama" Tundaga ranar Laila ta k'ara sanya musu ido sosai. Yau Aira tunda ta tashi ta tashi da zazzabi mai tsananin gaske ga ciwon ciki da ya addabeta ko fitowa ta kasa Haka ta yini a d'aki rufe cikin bargo Koda Alhaji Yusuf ya leko ya sameta a wannan halin sosai ya damu tare da cewa ta shirya ya kaita Asibiti ta ce "a a a taji sauk'i parasitimol ya b'alla mata Tasha wanda saida ta amayoshi A toilet bayan barinshi dakin . washegari ma haka Aira ta tashi da wannan zazzab'in Dak'yal dai ta samu harta fito palour abincima dak'yal taci saida Alh ya takura mata Mama ko Sannu ita da Laila basu mata ba a palour ta zauna gefen kujerar da Laila take Amai ne taji yazo mata da gudu ta fad'a toilet d'in palour tare da Fara kwarara amai duk abunda taci saida ta amayar Alh Yusuf shi ya taimaka mata ta gyara jikinta sai Sannu yake yi mata harta fito Mama Ce ta Kalleshi ta ce " Gaskiya ya kamata a kaita Asibiti tunda naga Ta fara galabaita "Eh daman asibitin kawai zamu ya fad'a yana Mikewa tare da Kallon Aira ya ce " Jeki sanyo Hijab d'inki "Ba Dan Aira tasoba taje ta sanyo hijab Hajiya saudema Mikewa tayi tace muje Tare Laila ko sai aikawa da Aira harara take har suka fito a lokacin Arman Na wajen mai gadi suna d'an hira Kad'an yana ganinsu Ya taso tare da cewa Alhaji lafiya " nuna mashi Aira yayi data tsugunna Dan ta kasa jurar tsawuyar ya ce "Amarya ce zamu kai Asibiti ba lafiya " Subhanalla Arman ya fad'a tare da cewa Allah ya bata lafiya Aira na jinshi bata d'agoba Arman ya ce "To bari na d'auko motar na kaiku" A a a ka barshi zan tuk'a da kaina Alhaji Yusuf ya fad'a tare da nufar parking space ya d'auko mota Arman ko sai kallon Aira yake tama d'ago taki Dagowa Saida Mama saude ta mik'ar da ita tare da kama hannunta suka shiga mota a lokacin ne Arman ya kalli fuskarta sosai yaga ta fad'a da ka ganta kaga marar lafiya saiyaji daman ciwon ya dawo jikinshi dukda baisan abunda ke damunshi ba a haka har motarsu ta fice daga gidan koda suka isa Asibiti basu bi wani layi ba saboda Dr d'in d'an Yayar Alhaji ne hakan yasa aka amshesu cikin mutuntawa gashi daman private hospital ne "Kallonta Dr Luqman yayi ya ce " Me yake damunki"Cikin k'arfin hali ta ce "Tun shekaranjiya ne nakejin zazzabi to jiya da yau yafi matsamun " Kina amai ko jin tashin zuciya? A a banajin tashin zuciya Amma dai jiya da dazu nayi amai"Kallon nurse Yayi ya ce "Kuje da ita lab ki fara mata gwajin fitsari?A tare da Nurse din Suka nufi lab ta dauki jininta tare da fitsarinta Tukwana Aira ta dawo office d'in Inda ta tarar Alh suna Hira da Dr Jan kujera tayi ta zauna tare da buga tagumi Ba ayi 20 minutes ba Nurse d'in ta dawo tare da Result a hannunta ta mik'awa Dr Amsa yayi tare da fara karantawa Yana gama karantawa cike da Fara'a ya d'ago ya kalli Daddy tare da cewa " Congratulations Alhaji ur Wife she's pregnant for 4 months Allah ya raba lafiya"A tare Alhaji da saude suka Mike sukace " Ciki wata hud'u Luqman"!!!!! Aira ma cikin tsananin tashin hankali ta mik'e ta ce ciki Kuma Dr.........✍🏿 *Tofa wata sabuwa ana wata ga wata me ya had'a Aira da ciki Kuma*🙆😯 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/7, 16:40] Hajo hajo: 🅿️...........*85&86* Ciki Kuma Dr Gaskiya ka duba badai niba"Shima Alhaji cewa yayi kadai duba Luqman "Mik'a musu Result d'in yayi gashi ku gani da idonku Alhaji shekara nawa ina Aikin nan Ciki ne da ita wata hud'u ma kuwa " Amsar takardar Daddy yayi tare da karantawa yagani Tabbas cikine wata hud'u "Cikin tsananin tashin hankali Ya kalli Aira ta ta ma rasa Inda hankalinta yake tsabar rud'u ya ce " Cikin uban waye"Kuka Aira ta fara tana hawaye sosai Tare da Jan baya ta ce "Nima bansaniba Wlh Daddy" Da mamaki Luqman yake kallonsu Ya ce "Me kake nufi Daddy kaida Matarka " dafe kai Daddy yayi sai sannan ya tuna gaban Dr suke "Mungode Dr ya fad'a tare da fardar hannun Aira yayi waje da ita ba abunda take In banda kuka Cikin Sauri Hajiya saude ta bisu Tana " Allah ya k'ara a cikin ranta "Yana zuwa back sit ya wullata tare da rufewa Hajiya saude ganin haka cikin Sauri ta maza ta shiga gaba kafinma ta k'arasa rife kofa yaja motar a guje Airako Had'e kanta tayi da gwaiwa tana kuka mai cin rai to ita mema zai had'ata da ciki Alhaji Yusuf ko baka tab'a Tantance irin b'acin ran da yake ciki Suna isa cikin b'acin rai ya fito tare da fito da Aira ya jata bai dire ta ko ina ba sai palour ya wullata kan kujera tare da wanketa da wani wawan Mari rik'e kumcinta tayi Dan sosai Marin ya shigeta tare da fashewa da kuka shak'eta yayi ya ce " Cikin uban waye kikazomun gida dashi Dan ubanki"nima bansaniba Daddy "ta fad'a cikin kuka Kara shak'eta yayi ya ce " bazaki fadamunba har saina sauya maki kamanni "sosai Aira take kuka duk ta rikice tama kasa maidamai Laila ko Mamaki tayi ta ce " Ciki Kuma "Daddy ko Kara wanke Aira yayi da wani Marin da yafi na d'azu ya ce " bazaki fadamunba har saina sauya miki halitta "Hajiya saude ce da takejin ranta kall taje ta rikeshi ta ce " Karka illata ta Alhaji kabari abi komai a Sannu har a samu ta fad'a Wanda yayi mata d'in"Cikin huci ya nuna Aira da yatsa ya ce "Kin ban mamaki wlh bantab'a zaton haka halinki yake ba y,ar iska kawai " Aira ko sosai take kuka gwanin tausayi Tana ganin ya sake shakewar da yayi mata da gudu ta ruga ta fad'a d'akinta Tare da kullewa a jikin kofar ta durkushe ta fashe da kuka maicin rai Ta ce "wannan wace irin jarabawa ce bata rabu da bibiyata ba ni Aira na shiga Ukku to cikin waye jikina Bayan Bantab'a zina ba Sosai take kuka tunowa da Ranar da Arman yayi kokarin Tab'ata a hotel tayi saurin Mikewa tare da dafe saitin zuciyarta ta ce " na shiga ukku yaya Arman Kardai kai kayimun sosai ta k'ara fashewa da kuka ga wani azababben zazzabi da ya k'ara rufeta sosai take kuka a d'akin Daddy ko cike da tashin hankali ya zauna tare da dafe kanshi Hajiya saude ce tace kayi hakuri Alhaji To amma kai kana ganin ba cikin ka bane kuwa"Wani banzan kallo ya watsa mata ya ce "a gidan ubanwa ya zama nawa yarinyar da ba abunda ya tab'a shiga tsakaninmu" Dariya Hajiya saude tasoyi Ta fusge a ranta ta ce "Ai yau dole nayi rawa da wak'a duk dai d'okin da ake akan amarya saiga amarya tayi abun Kunya " Laila ko sosai taji tsanar Aira a ranta Arman ko yana ganin dawowarsu Aira da lokacin da Daddy Ya jata sosai ya shiga rud'u yanason ya ji abunda yake faruwa Amma ba dama Sukuku ya yini ranar Har karfe sha biyun Dare Aira na d'aki tana kuka saurin Mikewa tayi tanajin kanta kamar zai rabe gida biyu ta bud'e d'akin ta lek'a taga ba kowa cikin Sauri tabar part d'in tare da nufar BQ d'akin Arman Wanda dak'yal take tafiya tana tangadi harta isa zaune ta sameshi yayi tagumi Dagowa yayi ya Kalleta Itama din shi take kallo da gudu ta fad'a Jikinshi tare da fashewa da matsanancin kuka Sosai Arman ya shiga tashin hankali cike da damuwa ya shiga tambayarta me yake faruwa Amma ta kasa amsa mashi sai kukan da take tadau minti ashirin tana kuka batare da tace komai ba 'cike da damuwa ya ce Kin tayarmun da hankali cutie ki fad'amun me yake faruwa kin sanyani cikin duhu"Cikin shashekar kuka ta ce Yaya na shiga Ukku wai ciki ne dani"a zabure Arman ya Mike tare da rik'eta ya ce "What ciki fa kikace Aira ni na shiga ukku ba ke ba Daman Baki rik'emun Amanar da na bakiba Aira saida kikaba tsohon banzan nan kanki" cikin kuka ta ce "Yaya Wlh banbashi kaina ba bai tab'amun komai ba yaya kawai dazu muna zuwa Asibiti Dr ya ce Wai Ciki garan wata hud'u kuma Auren wata Ukku dayi Shima Kanshi Tuhumata yake dazu dak'yal nasha akan saina fito da Wanda yayi mun Bayan nima bansaniba" ta k'arasa fad'a cikin kuka mai cin rai "Sosai Arman ya shiga rud'u da damuwa Kallonta yayi ya ce " Kin tabbatar bai tab'a miki komai ba ko da bakya cikin hayyacinki"na rantse maka da Allah yaya bai tab'amun komai ba"Ajiyar zuciya Arman ya sauke tare da zaunawa itama ya zaunar da ita cikin k'arfin hali ya ce "To cikin waye Aira karki b'oyemun kinsan duk tsanani bazan tab'a gujarkiba ki fad'amun cikin waye ko wani ya tab'a miki fyade" Cikin kuka ta ce "Yaya wlh nima bansaniba Saidai idan cikinka ne" What cikina kuma Aira "ya fad'a da mamaki" Eh Yaya saidai in kai kayimun ka fad'amun Ranar nan Idan akwai abunda ya shiga tsakaninmu yaya Dan Allah karka b'oyemun ka fad'amun karka sanyani cikin wani hali"tashin hankali ba a gwada maka rana Arman cike da damuwa ya ce "Harfa da Qur'an na rantse maki Sannan idan nayi maki wani Abu aike kanki kinsani me yasa wai baki ganewane Aira babu abunda nayi maki wallahi tallahi ban tab'a zina ba Kuma banyi dake ba" Karawa kukanta volume Aira tayi ta ce "To yaya idan ba kai ba wa yayimun?Dafe kanshi Arman yayi ya ce " Ke zan tambaya Aira"Kuka ta fashe dashi sosai tace "Yaya wlh nima bansaniba nima na rantse maka da Allah bantaba zina ba idan na tab'a kar Allah yayi mini Rahama duniya da lahira Allah dawwamar dani cikin wutar jaha....saurin rufe mata baki Arman yayi tare da girgiza mata kai ya ce " karkiyi irin wannan rantsuwar cutie na yarda dake d'ari bisa d'ari dukta kare dai akwai lauje cikin nad'i"Fad'awa jikinshi Aira tayi tana ci gaba da kuka har karfe biyun dare Arman na Lallashinta dak'yal ya dinga daddabata ga jikinta da yayi rauu yad'au zafi Alamun zazzabi sosai ya tausaya mata. A haka har wani wahalallen bacci ya kwasheta a jikinshi sosai Arman ya shiga rud'u da damuwa akan cikin da akace Aira na da shi sai wajen hud'u na dare Shima wani wahalallen bacci ya daukeshi kanta na saman k'irjinshi yayinda shi kuma kanshi yake saman pillow.Daren ranar ba neman da Daddy bai yiwa Aira ba Amma bata part din d'akinta a bud'e palour ya zauna yaga ta Inda zata bullo amma ba ita ba labarinta a haka har bacci ya daukeshi washegari tunda Safe su Laila da Mama sun fito kallonsu yayi ya ce "Ina Aira ?da mamaki suke Kallonshi sukace Aira kuma ai Alhaji rabonmu da ita tun Bayan dawowarmu daga Asibiti" cikin tsananin tashin hankali ya ce "To ina ta kwana badai guduwa tayi ba " ya fad'a yana Mikewa "Laila ce ta ce " Dukta k'are a d'akin buzu ta kwana?What buzu fa kikace Laila "Eh Daddy Daman Tasha zuwa wajenshi nasha ganinsu tare har inama zarginsu banason dai na fadane ace na musu sharri amma Aira da Buzun nan take tare" kin tabbata Laila ba sharri kike musu ba "Wlh dady ba sharri nake musu ba muje Chan din mu gano Daddy kamar zai tashi sama haka suka fito Laila da Mama na biye dashi A haka har suka isa BQ d'in Suna yaye labulan d'akin suka same Aira da Arman suna bacci mak'ale da juna" Cikin tsananin tashin hankali dukansu suke kallonsu da mamaki kallon Daddy Laila tayi ta ce"Kagani Daddy Daman na fad'a maka"Daddy ko ya kasa magana tsabar tashin hankalin da yake ciki"ita kanta Mama saida tayi mamakin al'amarin nan cikin zafin Rai Daddy Ya buga kyauren d'akin da karfi ya ce "ku tashi y'an iska Yau asirinku ya tonu" Firgit suka Mike A tare Murza idonta Aira ta fara harta budesu ya sauka akan su Mama wara idanunta tayi ta kalli Arman da Shima su d'in yake kallo Bayan Arman ta koma Tare da boyewa ta ce "Yaya karka bari su dakeni" yaya Laila ta maimaita "Alhaji ko cikin zafin nama ya shake Arman ya ce " Daman kwarto na Aje gidana bansaniba D’an iska na janyoka daga rana na sanyaka inuwa ka rasa dame zaka sakamun sai da haka tare da matata ta Dan cin amana yau zanga Wanda zai kwaceku a wajena duk saina kasheku '"Cikin tsananin Zafin rai Arman ya fusge chukumar da Alh yayi mashi tare da Wulli dashi har saida yayi taga taga zai fad'i Cikin masifa Arman ya ce "Kai harka isa ka dangantani da kazamiyar kalma waye kai a k'asar nan ta ubanwa kake ci to idan baka saniba yau ka Sani Ni ba kaskastacce bane ba Rashin Kudi ya kawoni gidanka ba soyayya ta kawoni gidanka soyayyar Wacce ka yi sanadiyar rabewar alak'armu Ba kaskantaccen buzun da kake tunani bane a gabanka Mujahed Kabir Umar kake magana dashi " cike da mamaki Alhaji ya ce "Mujahid Kabir Umar d'an gidan gwamnan kano kake nufi?su kansu su Mama saida sukayi mamaki musamman Laila kenan Arman din Aira ne shiyasa Duk sanda ta nuna tana sonshi take kishi Haba no wonder daman tasan mutumin nan baiyi kama da k'aramun mutumba Alhaji Yusuf ko cike da masifa ya ce " daman yaudara ta kayi Arman ne daman ?tsaki Arman yaja ya ce "Abunda yafi yaudara soko kawai tsohon najadu “Chabd'i Alhaji ya fad'a tare da Kallon Aira da duk ta tsure cikin Tsawa ya ce "Waye uban cikinki kinsan dai karya kike ki lak'amun shege Bayan Kinsan ba nawa bane " Nine nan uban cikin nine nan na mata "Arman ya fad'a yana nuna kanshi duk a mamaki suke Kallonshi musamman Daddy da Yama kasa magana cikin k'arfin hali ya ce " Lallai Alh Abubakar ya cuceni daman yasan da ciki ya auramun ita shiyasa yasa gaggawa a bikin Dan kar asirinshi ya tonu ni ya tonamun nau "Mama ko cewa tayi Haba shiyasa Nayi mamakin Ace idan ba kangara yarinyar nan tayiba iyayenta su baka ita amma an cucemu wlh wannan ai b'acin suna ne " Kallon ta Alh yusuf yayi ya ce "Kansu zasu b'atawa suna ba dai niba Sannan ya kalli Aira ya ce " Kije na sakeki sake ki saki d'aya!!Duk tashin hankalin da Aira take ciki baihanata sauke ajiyar zuciya ba Hajiya saude ce ta ce "Alhaji meye abun saki d'aya kuma saki Ukku zakayi mata me zakayi da y'ar iska kuma " kallonta yayi ya ce "Kuma fa hakane sannan ya k'ara kallon Aira yace na sakeki saki biyu na sakeki saki Ukku " Ajiyar zuciya saude ta sauke Arman ko baka iya Tantance yanayin da yake ciki Fard'o hannun Aira yayi tare da nufar hanya kofa da ita cikin taananin bacin rai ya ce "Ku bamu hanya mu wuce" Cikin masifa Daddy Ya ce "Gidan ubanwa zaka da ita ai baka isa kaje ko ina da ita ba kamar yanda daga gidan ubanta na daukota hakan zan mayar masa da tsiyarsa............✍🏿 *Ki biya ki karanta cikin nutsuwa 200 ta wannan number 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/8, 20:01] Hajo hajo: 🅿️...........*87&88* ..Haka zan mayar masa da tsiyarsa "Cikin tsananin b'acin rai Arman yace wannan ne kuma baka isa ba ko kai wanene yana gama fad'ar ya fisgi Aira tare da bangajeshi yayi waje da ita janta kawai yake kamar zai tashi sama da ita A haka har suka bar cikin gidan Sosai Aira take kuka Wanda Arman jin kukan nata yake har cikin ranshi Alhaji ne da duk ya tashi hankalinshi Kallon Saude yayi ya ce " ji nake zuciyata kamar zata fashe saude "Haba Alhaji akanme zaka damu hankalinka Tunda Allah ya Rabaka da k'aya ai gwarama da ya tafi d'in da ita kuma zaman me zatayi mana a gida kamata fa akayi banda Cikin da tazo maka dashi gida kaidai kawai an cuceka wlh wannan Auren masifa ya zame maka" Numfasawa yayi ya ce "Alhaji Abubakar zaisan ni yayiwa haka wlh duk abunda na kashe sai ambiya ni Aure ko masifa ba abunda na Mora da Auren sai masifa wlh bazanyi asarar kudinaba hatta cida ta din da nayi saiya biyani yana gama fad'ar haka Fuuu yabar wajen Laila da Mama suka bishi Aira ko suna fita hanya Suka mik'a Arman xaka Kalleshi kasan ba k'aramun b'acin rai yake cikinshiba janta kawai yake Ita kuma sai kuka take sunyi nisa sosai Ja yayi ya tsaya tare da kallonta cikin b'acin rai ya ce " Kukan me kikemun ko so kike ki koma gidan matsiyacin chan ?Girgiza mashi kai tayi ta ce "A a a yaya ina tsoron Abba ne Idan yaji abun nan nasan tsinemun zaiyi ta k'arasa fad'a tana rushewa da kuka" Sosai ta bashi tausayi Hakan ya sanyashi saurin Saukowa cikin lallashi ya ce "Kiyi shiru ki daina kukan nan Hamdala zakiyi da Allah ya rabaki da k'addararran Auren nan sannan bazai tsine miki ba insha Allah " Goge hawayenta tayi ta ce "To yaya Amma Dan Allah karka maidani gida yaya Dan Allah Abba kasheni zaiyi kokuma ya sake rabamu bana son komawa kano kwata_kwata yaya " kan wani dakali ya zaunar da ita Shima ya zauna tare da cewa "Bazamu komaba cutie guduwa zamuyi" Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da hade kanta da gwuiwa "lalubo Wayarshi Arman yayi ya dannawa musa kira Bayan ya d'auka yayi mashi kwatancen Inda suke tare da cewa Dan Allah duk Inda yake yazo yayi gaggawar zuwa " Minti Sha biyar me kyau musa yazo ya samesu a wajen da mamaki yake kallonsu Ya ce"Yadai Abokina yana ganku haka ku biyu kuma yanayinku kamar ba dad'i"Kama hannun Aira Arman yayi tare da mik'ar da ita ya ce "Muje kawai munyi maganar later" A back sit ya sanya Aira shi kuma ya shiga gaba har suka isa gidan musa bamai cewa Uffan saida suka isa Arman ya fito tare dabudewa Aira ita ta fito a palour gidan suka d'auka Inda matarshi ta tarbesu hannu bibbiyu dukda k'in sakewar da Aira take kallon Sarat Arman yayi ya ce "Maman boy Dan Allah toilet zaki nuna mata ta tayi wanka kafin mu dawo" da to ta amsa tare da kama hannun Aira ta ce "Sis muje " ba musu Aira ta bita toilet d'in ta nuna mata tare da bata towel tabar d'akin Saida ta cire kayan jikinta tukwana ta d'aura towel din daman daga ita sai kayanta ko Hijab babu jikinta haka sukazo Arman ko fita sukayi tare da musa Kallonshi musa yayi ya ce "baka ban labari ba Abokina meya faru" Numfasawa Arman yayi ya ce "ya saketa" wara idanu musa yayi ya ce "Serious Abokina" Da gaske mana muna irin wannan wasan dakai"Wow amma natayaku murna wlh congratulation Amma garinya harya yarda ya saketa"ya gaji da Zama da itane bata da amfani a gareshi shiyasa kawai ya saketa "ya bashi amsa a takaice don baijin zai iya Fad'ar gaskiyar Lamarin abunda ya faru kamar ya tozarta cutie d'inshi ne dukda har yanzu zuciyarshi bata lamunta da zargin cikin da ake mata ba a wani boutique dake kusa dasu sukaje Arman ya sayowa Aira doguwar Riga wacce zatasa sannan suka biya suka sai mata yadin hijab suna tsaye aka d'inka mata hijab d'in yadi hud'u tukwana suka koma gidan a lokacin Aira harta fito daga wanka Sarat sukaba kayan akan ta kai mata Zaune ta sameta tayi tagumi " Mik'a mata kayan tayi ta ce "Gashi y'ar uwa kisanya" Nagode Aira tafada tare da amsa saida ta fita tukwana ta bud'e rigar ta sanya ko madubi bata tsaya kallaba bare taga ma yanda tayi mata hijab din ta warware Blue har kasa tare da sanyawa ta fito palour anan ta tarar da Su Arman Mikewa Arman yayi tare da mik'awa musa hannu ya ce "Abokina zamu wuce nagode nagode Allah yabar zumunci Kayimun abunda bazan tab'a mantawaba dashi a rayuwaba Allah ya saka da alkhairi" Bakomai Abokina ai yiwa Kaine bazaku bari Kuyi break fast ba tukwana ku wuce "a a a Gaskiya Sauri muke Abokina kallon Aira yayi ya ce Taho muje Godiya Aira tayiwa Matar musa tukwana ta bisu musa ya kaisu Har airport saida yaga sun yanki ticket sunyi clearing d'in komai jirginsu 12 zai tashi zuwa Abuja ganin lokacin ya kusa ya sanyashi yi musu bankwana akan zai koma Account number shi Arman ya amsa tare da yi mashi Transfer 10 million" Sosai musa yayi mamaki yaji dadi sosai sannan yayi mishi Godiya cike da kewar abokin nashi ya koma gida"K'arfe 12 daidai jirginsu Ya tashi Bayan y'ar takaitacciyar tafiyar da sukayi jirginsu ya sauka Abuja Taxi suka hau A lokacin Jikin Aira yayi rauu zafi sosai Sannu kawai Arman ke mata har suka isa katoton gidanshi dake G R A Sosai gidan ya burge Aira Dan ya had'u karshen had'uwa Aljannar duniya kenan Knoking Arman yayi mai gadi ya leko yana ganin Arman yafara fara a tare da washe baki ya ce "Ranka ya dad'e kaine tafe Sannu da zuwa ya fad'a yana bud'e musu tare da basu Hanya " Alhmdllh kawai Arman ya fad'a ya shige ciki Aira na biye dashi a makeken Palourn gidan da fad'ar tsaruwarshi bata baki ne suka yada zango Kallon Aira yayi da duk tayi sanyi tare da kamo hannunta ya ce "kodai jikin ne cutie mu wuce Asibiti " girgiza mashi kai tayi ta ce "a a a yaya ni bansan zuwa Asibiti bazan k'ara zuwaba tunda basa fad'ar alkhairi" D'an murmushi yayi tare da cewa to shikenan yanzu ki kwanta anan naje na had'o maki break fast"Na koshi yaya Banajin yunwa"Hararar wasa yayi mata ya ce "Baki isa ba inke bakyaso ai baby na yaso ya fad'a yana kallon cikinta da yake a shafe" Hawaye Aira ta fara ta ce "Cikin da ba asan ubanshi ba Kake dangantawa da babynka yaya Dan Allah ka kaini a ciremun please" murza hannunta yayi ya ce "Baza a cire ba cutie Har yanzu bangama yarda akwai ciki a tattare dake ba sannan koda ace da gaskene to kisani a soyayyar da nake maki ko Kad'an bazata ragu ba saima karuwa da zatayi sannan ni zan amshi cikin a matsayin nawa koda kuwa duniya zata tsinemun Amma ki bari please muje Asibiti a gwada " cikin hawaye take Kallonshi tana Kara godewa Allah da yabata masoyi na Gaskiya hakika Arman da wanine a wannan lokacin ne zai gujeta amma gashi ko a kanshi sannan bai nuna mata kyama ko hantara ba "Girgiza kai tayi ta ce " Yaya bazanje Asibiti ba nan gaba kila su fad'amun abunda zai tarwatsarmun da zuciya"ta k'arasa fad'a tana hawaye "To shikenan bar kukan my cutie kinsan ba abunda na tsana sama da kukanki abunda nake so dake ki kwanta ki huta kinji kafin na fito" gyada mishi kai tayi tanajin soyayyarshi na k'ara ratsata Har ya bar wajen tana Kallonshi saida taga shigarshi kitchen tukwana ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Allah ka kawo mana mafita cikin wannan rud'addiyar rayuwar da muke ciki Arman yana shiga kitchen yaga basu da kwai ta k'ofar baya yaje ya bawa Mai gadi kudi akan yayi Sauri ya samo mashi kwai ba b'ata lokaci kuwa yana tsaye har yaje ya dawo"itadai aira tana kwance yayinda idanunta suke a bude ba ayi 30 minutes ba taga ya fito hannunshi rik'e da plate zuwa yayi ya Aje gabanta sannan ya koma ya d'auko Cup d'in tea da yasha Had'in kauri Shima ya Aje gabanta cike da kulawa yaje ya ruk'ota tare da cewa " Mike to kici kinji my prince's zakiji k'arfin jikin naki"A hankali Aira ta mik'e Plate d'in soyayyar wainar k'wai sai k'amshi yake tashi ya bud'e mata tare da gutsuwa yayi saurin kai bakinta ya ce "ha a bud'e bakin" Murmushi Aira tayi mishi tare da bud'e bakin shi ya dinga bata tare da tea din sosai taji dad'inshi har batasan taci da yawaba Kallonshi tayi tare da marairaicewa ta ce "Yaya na koshi kaima kaci please" Murmushi yayi ya ce "a a ni na k'oshi ki daure ki k'arasa cinye wannan zakiji k'arfin jikinki" girgiza mai kai tayi tare da Amsar plate d"in itama ta gutsuro takai saitin bakinshi "murmushi ya sakar mata Itama ta mayar mai a haka itama ta dinga bashi har wainar kwan ta k'are Mikewa Aira tayi ta ce " Yaya salla zanyi"Shima mikewar yayi ya ce "Muje na nuna maki bedroom d'inki binshi tayi ya gwada mata d'akin tare da fita Dan Shima yaje yayi salla Dan lokacin ta ya wuce sai a gida yayi Aira ma cire hijab din tayi tare da Shiga Toilet taje tayi alwala Ta fito ta sanya hijab d'inta tare da shimfida abun salla raka'a biyu tayi tare da nafila biyu saboda k'asaru ce Tana gamawa ta jima tana adduo'i a haka Arman ya sameta Saida ta gama tukwana ta juya ta Kalleshi murmushi ya sakar mata ya ce " Fatan an sakamu a Addua'ar "Uhm yaya Ai Addu'arma gaba d'aya taka ce " ta fad'a tana rufe fuska murmushi yayi ya ce "Ah kice Duka tawace to Allah ya amsa mana" Ameen Aira ta fad'a kasa kasa tare da Yin kasa da kanta Kallonta yayi ya ce "ki kwanta yanxu ki huta Dan Allah zanje na samo maki magani kinji cutie sannan kiyimun alk'awarin bazakiyi ta kukan da kika saba ba ke bakyama gajiya da kuka kanki yayi ta ciwo a Banza"Mikewa tayi tare da Kallonshi ta ce " to yaya insha Allahu bazanyi kuka ba karka jima please "to y prince's kafin in dawo ki tabbatar kinyi bacci" murmushi tayi ta ce "To my yaya" yana barin d'akin ta cire Hijab d'inta jikinta tare da hayewa Gado Ba jimawa bacci ya d'auketa Dan daman a gajiye take. Abba na zaune a palour da misalin karfe Tara na dare yana kallon labaran N T A News Kira ya shigo Wayarshi duba mai kiran yayi yaga Alhaji Madugu ne Amsawa yayi tare da Kara wayar a kunnenshi ya ce "Assalamu alaikum" Wa alaikumussalam Alhaji Madugu ya amsa daga ganin kasan yana cikin fushi cikin Fushi ya fara magana "A Gaskiya Alh bukar ka cuceni ka zalince ni daman Kasan y'arka y’ar iskace baka bata tarbiya ba dan tayi cikin shege shine ka lik'amun ita to kasani asirinku ya tonu dan asibiti mukaje dr ya tabbatar mana da tana dauke da juna biyu na wata hudu Bayan aurenmu da ita wata ukku da kwanaki ne hasalima ni wani abu baitab’a shiga tsakanin ni da ita ba sannan nakirakane Dan na fad'a maka a halin yanzu y'arka bata hannuna na saketa tabi Tsohon Saurayinta da ya yaudare ni kusan wata guda yake Aiki a karkashina ashe shirine sukayi da ita Bayan mun kamasu dumu dumu dazu da safe na saketa saki Ukku Ta bishi sun tafi Dan karma ka bincika y'arka wajena bata hannuna tabi tsinannan saurayin da yayi mata Cikin da bakinshi ya fadamun cikinshine daman sone kukayi ku likamun cikin shege shiyasa ka lakabamun ita sannan kuma ka sani duk abunda na kashe tundaga neman Aurenta har zuwa yanzu saika biyani Dan bazanyi asara a banza ba "Tunda Alhaji Yusuf ya fara maganar Daddy Ya shiga tsananin tashin hankali har yakai karshe " Innalillahi wa inna ilaihiraji'un ya fad'a wayar tuni ta sulale a hannunshi A tsayen da yake ya dire kan kujera tare da dafe saitin Zuciyarshi a rarrabe ya ce "Ci ki Aira " Ai tuni Yaji hankalinshi ya fara gushewa Ya fara ganin jiri Mama ce da tafito taga yanayin da yake cikin cikin tsananin tashin hankali Ta nufe wajenshi tare da cewa "Alhaji lafiya? Me ya faru " Wayarshi ya nuna mata a rarrabe ya ce "Ki ki ra mun Dr cikin Sauri Mama ta dauki wayar tare da Nemo number Dr bashir ta kira ring Ukku ya d'aga cikin tsananin damuwa ta ce " Dr kazo gidanmu yanzu ka taho tare da kayan aiki ina tunanin jinin Alhaji ne ya hau sosai "Tana kashewa ta kwalawa Mamy kira " Rahama ki fito Alhaji ba lafiya!Cikin tsananin tashin hankali Mamy ta fito tare da nufar wajen ta ce "Subhanallahi me ya sameshi yanzu fa muka rabu dashi lafiya" wlh ko nima haka yanzu na sameshi"Su amma da su Haidar ma duk sun fito Cikin tashin hankali sunyi jugum jugum a haka Dr ya shigo cikin Sauri ya nufi Inda Abba yake tare da Fara Dubashi Abun awon DP ya fara mashi yana dubawa yaga jininshi yahau sosai irin yanda yake bada matsala cikin Sauri ya sanya mishi semomitre a harshe tare da saurin had'a allura Yayi mashi su mama dr ya Kalla yace su taimaka a kaishi daki Mama da Mamy suka taimakamai aka kwantar dashi a kan gadon Mama Wanda tuni bacci ya daukeshi Dan allurar ta bacci ce Daman kallonsu Dr yayi ya ce "wani Abu aka fad'amai kafin ya fara haka Dan kadan ya hana ya samu heart attack" Subhanalla heart attack kuma Dr Gaskiya nidai bansan anyi mashi wani ba Saidai ko Yaya idan ta sani "Mamy ta fad'a tana kallon Mama " itama cewa tayi bata saniba magunguna Dr ya rubuta musu akan a sayo daya tashi ya cigaba da shansu sannan su barshi shi daya ya huta a dakin har zuwa sanda zai tashi kar a tasheshi jinin zai sauka Daman yasan Abba yana da hawan jini amma irin na manyanta ka ne bamai matsala ba magani kawai yakesha "Godiya su Mamy sukayiwa Dr Bayan ya tafi suma Duka barin d'akin sukayi Dan kar ayi hayaniya kowannensu ya shiga kogin tunanin meye ya sanya jinin Abba hawa a take. Washegari sai wajen goma na safe Abba ya farka jinin nashi ya sauka Saida Dan Rashin jin dad'i da bayayi a lokacin Duka iyalannashi na dakin Sannu kawai suke jera mishi da kanshi ya Mike " Kallon Mama yayi ya ce "Banyi asuba ba ko?Eh Alhaji bakaiba Dr yace a barka ka tashi da kanka shiyasa" Cewar Mama "Aida kun tasheni ya fad'a tare da shiga toilet ya dauro alwala yaxo ya gabatar da salla Mamy ce tayi k'arfin halin cewa Ya jikin" Da sauki ya bata Amsa Kallon Mama yayi ya ce "Ki kira su Aisha da Ummy Dukanku karfe sha biyu ku sameni a palour na yana gama fad'ar haka Ya fice daga d'akin ya koma part d'inshi sosai duk sukayi sanyi Basusan me yake faruwa ba kamar yanda Abba ya fad'a haka Mama ta kirkira su Aysha karfe sha biyu tayiwa kowa na gidan a Babban palourn Abba har Inna saida yasa aka kira idan aka cire yaya Umar da Maryam sai Aira Bayan kowa ya zauna Aysha Abba ya Kalla ya ce " Kiramun Maryam a waya kisa hads free "Sannan ya kalli Ummy ya ce " Ke kuma kiramun Umar Duka inason kowa ya saurari abunda zan fad'a "hakanko akayi Duka aka kirasu Gyaran murya Abba yayi ya ce " To ba bakomai yasa na taraku anan ba Saidai In kafa hujja sannan ku shaida ku sani a gaban kowa daga yau Ni Abubakar Umar na cire Hajara a cikin jerin y'ay'an da na Haifa daga yau babu ni babu ita Sannan duk d'an Dana Haifa Shima na rabashi da ita babu ku babu ita Na yanke zumuncin dake tsakaninku ko a boye wani yayi mu’amula da ita ban yafe mashi ba daga yau kar a k'ara alak'antata da y'ar da na Haifa na yafeta a cikin jerin y'ay'an da na haifa ...........✍🏿 *Jumaat khareem* *ina yiwa yan uwa musulmai murnar nuna mana wannan rana ta Arafa mai Cike da albarkoki Allah yasa muna daga cikin masu dacewar wannan rana ya yafe mana kura kuranmu ya amsa mana adduoin mu da ibadinmu Allah bamu ikon zuwa wannan k’asa mai tsarki don muma mu sauke farali Ameen ya Allah* *zamu shiga hutun sallah koda na kwana biyu ne kuyi hakuri kunsan hidimar sallah bazata bari nasamu damar typing ba Ayi salla lfy sannan kowa ta ajemun nama na yawan nama yawan typing*😂 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿🤙🏿 [7/11, 12:53] Hajo hajo: 🅿️............*89&90* .....Na yafeta a cikin y'ay'ana sannan koda wasa na sameta a cikin gidan nan ta shigo naga akwai sa hannun wani cikinku wlh zakuyi mamakin matakin da zan d'auka kowaye Shima Saidai ya bita hatta mahaifiyarta"kowannensu idan ka kalleshi zakasan yana cikin tsananin tashin hankali musamman Mamy cikin tashin hankali ta ce "Me kuma tayi Alhaji na shiga ukku ni Rahama " Ai zakiji kome tayi "Inna ce ta mik'e ta ce " Amma wlh habu baka kyautaba Kazo ka zauna ka dinga tsinewa y'arka To tukunma me tayi "Ban tsine mata ba Inna na bartane da duniya Sannan Abunda tayi ba abunda Zan d'aukeshi bane ciki taje dashi gidan Aurenta" Cikin tsananin tashin hankali kowa ya mik'e kamar sun had'a baki wajen fad'ar ciki?Tabbas ciki Jiya da Daren mijinta ya kirani yake shaidamun Sunje Asibiti bata da lafiya likita ya shaida musu Cikine da ita harna wata hud'u kuma ba nashi ba saboda ba abunda ya shiga tsakaninsu sannan Bikinsu kowa ya duba invitation yasan wata ukku ne Sannan Yaron nan Arman ashe Had'in baki sukayi ya bita Gidan a matsayin Driver suke cigaba da mu amula dashi karshe dai ya ce sun kamasu a d'aki Wanda Dalilin hakan ya sanya ya saketa saki Ukku Bayan Arman d'in ya tabbatar mashi shi yayi mata Cikin shine ita kuma ta bishi to shiyasa na yanke wannan hukuncin daga yau ko ambatar sunanta kar a k'ara mun a gida "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un kawai suke Ambata sosai kowa dake wajen yayi mamakin irin abunda Aira tayi musamman Mamy da takejin zuciyarta kamar zata rabe gida biyu Aisha ko ba abunda take inbanda kuka haka Amma mamy ko cikin k'arfin hali Ta ce " Sakayyar da Aira zakayimun dashi kenan ta kyauta ta cika y'a tana gama fad'ar haka ta shige cikin d'akinta tayi tagumi sosai take hawaye tanajin zafi da rad'ad'in abun Tabbas Aira ta kunyata k'untatawa.mafi muni kuwa ai yanzu kuma bata da bakin magana a cikin gidannan innako Salati ta rafka ta ce "Na shiga ukku ni Halima cikin Shege a gidannan Amma mujahid Anyi lalatacce daman saida ya lallaba ya kumsawa yarinyar nan Ciki Goge hawayenta tayi tare ciro wayarta cikin Dan tofi Haidar ta mik'awa tace amshi maza maza kiramun Kabir " Amsa Haidar yayi a sanyaye ya kamo mata number Daddy saida yaga ta fara ringing tukwana ya mik'a mata ta k'ara a kunne Daddy na d'auka cikin Masifa ta fara cewa "Kabir ina Mujahid" a lokacin Daddy na tare da Mummy a palour Dan hutawa yau ya ke ya ce "Inna Mujahid kuma ai rabona dashi anfi wata " Eh Mujahid duk Inda yake ka nemo munshi wlh bai isa ba munafuki ina ganinshi kamar mutumin arziki ashe da abunda ya taka Saida ya yi yanda yayi ya kumsawa yarinyar nan Ciki ai wlh bai isa ba ya maidomun jikata duk Inda ya kaita ko inyi rashin mutuncin da na jima banyiba "Cikin tsananin tashin hankali Daddy Ya ce " Inna wace yarinyar kike maganar yayiwa cikin ?yo wa ka sani mana idan ba Hajara ba tunkan ayi Auren ashe da ciki taje bai kyaleta ba a haka ba saida ya bita har gidan Aurenta shiga d'an iska yaje a matsayin matuki yaje ya dinga nanikarta har saida mijin suka kamasu karshe dai ya kashe mata Aure kuma ya gudu da ita to wlh Kaine ubanshi saika nemo munshi Tare da jikata zan nuna masa na fisa iya shak'iyanci "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un kawai Mummy da Daddy ke furtawa Dan hands free Wayar take taji komai kashe wayar Daddy yayi ya ce " Kinji abunda d'anki ya aikata ko?Keda kike d'aure mashi Ga abun kunyar da ya aikata mana to wlh kisani daga yau babuni babushi dukda shi kadaii na Haifa na gwammace nayi rayuwa batare da kowaba sannan duk Inda Yake zansa a kamasu sainasa an rufeshi Su kuma ya maido musu y'arsu sosai Daddy Ya shiga Surfa masifa Mummy ko hawaye kawai take tana Nazarin Arman bazasu aikata haka ba Saidai ance ba a yabon d'an kuturu duk irin masifar da Daddy yayi mata tanka shiba saboda ance d'an goruba mai jawa uwarshi jifa Dan har ita Daddy Ya hada yake surfawa masifa Saida ya gama tukwana ya fara kiraye kirayen Airport tare da tura hoton Arman ya ce da sun ganshi su kamashi sannan ya Ce har gidan nashi na Abuja zansa Aje Duk iskancinshi zan nuna masa k'arshenshi Mummy ko sosai tashiga tashin hankali ta ce "Alhaji karkayi haka karkasa a kama d'anka idan rai ya baci hankali baya gushewa " Daddy baima kulataba sai barin d'akin da yayi cikin tsananin tashin hankali Mummy ta shiga cikin d'akinta Tare da janyota wayarta number Arman kawai take Kira amma a kashe Tana hawaye tayi ta tura mashi text kala kala dukta rude Hankalinta duk ya k'ara tashi Dan bazata juri A rufe mata d'a a banza ba Dan ta lura Daddy da gaske Yake kuma idan yayi irin wannan kafiyar Babu mai tankwarashi hakan yasa hankalinta tashi gashi duk ta kira layukan Arman Amma a kashe zama tayi bakin Gado tare da tafka uban tagumi Tana hawaye. Arman koda ya dawo bacci ya tarar da ita tanayi Wanda hakan sosai yayi mishi dadi Take away d'in da yayo mata ya Aje tare da maganin ya nufi bedroom d'inshi yaje yayi wanka Bayan ya fito ya shirya sosai yayi kyau cikin Dakakkiyar light blue din shaddarshi sai maiko take d'akin Aira ya koma yaga har lokacin Bacci take zaunawa yayi kan sopar Dake gefen gadon tare da kafeta da idanu bako k'iftawa wutar sonta na k'ara fisgarsa Yakai one hour yana kallonta sai wajen la'asr ta tashi A hankali take bud'e idonta ta saukesu a nashi murmushi tayi mishi Shima ya mayar mata Brush taje tayi shiya taimaka mata taci abinci tukwana tayi Salla maganin da ya sayo ya b'alla mata tana Yatsine fuska ta sha kallonta yayi ya ce "To ya jikin naki? Dasauki yanxu banajin zazzabin Saidai ciwon ciki Kad'an " Insha Allahu Shima zai daina dia Allah ya k'ara miki lafiya"Ameen Aira ta fad'a tana jingina kanta ga jikin gadon Wayarshi Arman ya lalubo ya ce "Kinga Tunda mukazo ban kira musa ba na shaida masa mun Iso lafiya Nasan yana ta nema na bari na kira shi ya fad'a yana bud'e wayar Yana bud'ewa yaji text message na shigowa Rututu daga sama kuma yaga number Mummy ce message d'in farko ya shiga Inda ta rubuto'" Son ka bud'e wayarka zamuyi magana dakai Dan girman Allah"Na biyun kuma ta ce "Arman ka taimakeni indai naci darajar haihuwarka da nayi ka kirani akwai matsala Arman " Na ukkun kuma ta rubuta"Na hadaka da girman Allah Arman idan na kiraka ka amsa kirana nasan duk kiran da nake maka kwanaki kana gani kake kin d'auka wannan Karin muddin baka daukaba zanyi fushin da..bai k'arasa karantawa ba yaji kiranta cikin Sauri Arman ya d'aga cikin damuwa ya ce "Mummy kina Lafiya" nauyayyar Ajiyar zuciya yaji Mummy ta sauke wanda har a waya saida yaji ta ce "Ba lafiya ba Arman kuna ina kaida Aira ?Kallon Aira yayi da hankalinta na kanshi ya ce " Muna Abuja Mummy please karki fad'awa kowa"Cikin Sauri Mummy ta ce "akwai matsala ka maza ka d'auketa Kushiga Mota ku tafi Adamawa Karku sake Kuhau jirgi Daddynka ya sanya a kamaka sannan har nan Abujar ya sanya azo gidanka sannan ka sanya face marks yanzunnan ba sai gobe ba ka maza ku tafi Adamawa gidan Mahaifina Zan sameku a Chan ko zuwa gobe ne" Cikin marairaicewa ya ce "Mummy Dan Allah ba wani shirin kukayi mana ba baso kuke ku Kara rabamu ba"ba Numfasawa Mummy tayi ta ce " Arman ba ka yarda dani ba kenan Babu wani shiri da na shirya wlh ina son kawo karshen matsalar nan ne Kayi abunda nace maka yanzunnan cikin gaggawa"To to Mummy yanzu zamu tafi nagode ya fad'a tare da Kallon Aira ya ce Cutie maza ki shirya Adamawa zamu tafi"Adamawa kuma Yaya wajen me"yanzu Mummy ta kirani ta ce "Muje Chan itama zataje karmu tsaya bata lokaci tashi mu tafi " a sanyaye Aira ta mik'e tare da sanya Hijab d'inta ta ce "Muje Yaya" Makullin motarshi mai tinted ya d'auko Suna zuwa parking space ya bud'e mata gaba tana shiga ya zagaya yaja motar Horn yayi mai gadi ya fito Cikin Sauri ya bud'e Zage glass din motar Arman yayi ya ce "Duk Wanda yazo nemana karka shaida musu nazo garin kace rabona da gidan amfi wata hud'u kuma wlh ka sake ka fad'awa wani nazo gidan nan nadawo a bakin aikinka" Yana gama fad'ar haka ya zuge Glass din baijirama amsar mai gadin ba ya figi motar a guje Sosai Arman ya dinga sharara gudu Suka d'auki hanyar Adamawa a lokacin hud'u Harta gota sosai suke sharara gudu Wanda Aira a lokacin zazzabinta ya dawo sunyi nisa sosai taji Tanajin Amai Kallonshi tayi cikin k'arfin hali tace Yaya "Amai nakeji" tsaida motar yayi tare da bude mata Ta sauke kafafunta waje nan ta shiga Yin aman saida ta gama tukwana ya mik'a mata ruwa ta kuskure bakinta Tare da wanke fuska Kallonta yayi ya ce Sannu Allah baki lafiya"gyad'a mishi kai tayi ta ce "Amen yaya " Fitowa yayi tare da rik'eta ya mayar da ita back sit tare da kwantar da ita saman kurerar ya ce "Ki kwanta ki huta" gyada mishi kai tayi Dan daman hutawar take buk'ata shi kuma ya zagaya ya koma Tare da tada mota ba ayi minti goma ba bacci ya d'auketa tafiyar awa Hud'u sukayi Karfe 8pm tayi musu a garin Adamawa Wanda sai lokacin Aira ta tashi Sannu yayi mata ta amsa da yawwa tare da cewa "Amma yaya munyi Sauri harmun Iso kenan " Murmushi ya sakar mata ya ce "Kina baccinki ai dole kice Munyi Sauri tunfa biyar kike bacci " Wara idanu tayi ta ce "Kaiii Ammafa nasha bacci shiyasa da na tashi Naji ba ciwon kan" Koda suka isa gidan Wazirin Adamawa mahaifin Mummy kenan a bakin get d'in gidan yayi parking Ya fita itama Aira bud'ewa tayi ta fito tare da Kallon get d'in da bangon gidan an kawatashi da zanen sarauta tundaga get d'in gidan Har bangon gidan irin na al'adarsu kama hannun Aira yayi ya ce "Muje ciki" A tare suka shiga cikin gidan Wanda Aira sai kallon gidan take tana kallon yanayin tsarin gidan sosai ya burgeta Kai tsaye bangaren Mahaifiyar Mummy Hajiya Zaituna Arman ya nufa da ita ita dai Aira na biye dashi da Sallama suka Shiga palourn Kallon y'an d'akin Aira tayi tsohuwace d'aya sai y'an mata guda Ukku"Cike da farincikin Ganinshi Hajiya Ta Mike tace "lale marhaban mai Gidan " murmushi Arman yayi ya ce "Tsohuwar daman baki gangara ba har yanzu?Uwaka ce zata mutu bani ba ja iri ta fad'a tana tashi tare da kamo hannun Aira ta ce " Sannu da zuwa kishiyata kunshawo hanya"ta fad'a tana zaunar da Aira gefen ta"K'asa da kanta Aira tayi ta ce "Ina yini Mama" Lafiya qlau y'ar nan ki saki jikinki nan d'in gidankune kinji"gyada mata kai Aira tayi y'an matan dake wajen ne suka gaishe da Arman ya amsa a takaice d'aya daga cikinsu ce ta kalli Aira tare da cewa "Wow waida tare kuke da Auntyn tamu yaya Ita ce ko?Harara Arman ya maka mata bata damuba Dan tasan Halin sauran ne suma suka kalli Aira sukace wow she's beautiful Yaya Gaskiya ta had'u Auntyn tamu ta fad'a Tare da zuwa ta zauna gefen Aira Ta kama hannunta ta ce " Sannu da zuwa Auntynmu ansha Hanya ya gajiya"Murmushi Aira tayi mata cike da kunya ta ce "Alhamdulilla" Sauran biyun ne suka mik'e D'aya ta je ta janyo hannun Aira ta ce "Muje ciki ki huta Karki biyewa tsohuwar nan ta k'ara miki Gajiya " ta fada tana kama hannun Aira dukansu sukayi cikin wani daki da ita Ja irai Hajiya tafada tare da kallon Arman ta ce "oh ni Mujahid yaushe rabonka da garin nan........✍🏿 *Barka da Salla fatan kowa yayi sallah lfy Allah amshi ibadunmu ya nuna mana bad’i da rai da lafiya* *Masu fitarmun da littafi ina sane daku kuma ku sani na barku da Allah saboda hakkinane Ni da Yaya Arman na kudine akan Naira 200 kachal ku tuntubeni akan number wayata 07026166536 ki saya naki ki karanta cikin kwanciyar hankali ba sai an sata an kawo maki kikaranta ba ba girmanki bane hajiya*🙅🏻‍♀️ _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/12, 14:52] Hajo hajo: 🅿️.......*91&92* Mujahed yaushe rabonka da garinnan "Dan sosa kai yayi ya ce " gwaggo kinsan yanayin aikin namu ne sai a hankali"Kaidai baka zumunci ne kawai zaka likawa aiki bikin y'an uwanka nawa akayi amma bakazoba To yanzu ba wannan ba ya jikin naka kasan munso zuwa Chan mu duba ka Allah baiyiba"Alhamdulilla Inna jiki yayi sauk'i "Masha Allah Ubangiji ya k'ara sauki Ai dazu mahaifiyar taka take kirana take Cemun Zakuzo kaida Bakuwa tafarayimun bayani kuma sai tace Saidai tazo" Sosa kai yayi tare da mik'ewa ya ce "Wlhko gwaggo bari naje na gaishe da Bappa " yana fad'ar haka yabar palourn Dan karma tayi mashi wata maganar..bangaren su Aira Suna janta a Gado suka zaunar da ita d'aya daga cikinsu ta ce "Ni suna Hasina wannan Maryam Waccen kuma y'ar bak'ar murjanatu" Ta k'arasa fad'a tanayiwa murjanatu Dariya "Hararta tayi ta ce " banza kin saba ko ina saikin nuna halinki na hauka"Tsaki Hasina taja ta ce "Kece ai za Ama kallon mahaukaciya bani ba" Tsaki Maryam taja ta ce "kudai kunji kunya gaban kowa saikun gwada halin " Itadai Aira na jjnsu batace uffan ba Maryam ce tashi sis kije ki watsa ruwa na hada maki komai na wanka "murmushi Aira ta sakar mata ta ce "To tare da mik'ewa ta shiga toilet ba ayi minti goma ba ta fito d'aure da towel jikinta lokacin da ta fito tuni hasina ta fito mata da wata rigar bacci Doguwar Riga Sanyawa Tayi Aira Bayan ta gabatar da Sallar magrib da isha i Abinci kala Ukku suka kawo mata ba yanda basuyi da itaba taci amma ta ce ta k'oshi " Mujanatu Ce ta ce Bari naje na fad'awa yaya takicin komai Tana fita ta sameshi a palourn Inna sunashan hira Bayan dawowarshi daga gaishe da baffa Kallonshi tayi ta ce "Yaya Aunty tak'icin komai fa ba yanda bamuyi da ita ba " Mikewa Arman yayi ya ce "tana ina" tana ciki "Bai jira ta sake cewa wani Abu ba ya nufi d'akin zaune ya sameta da hijab akan prayer mat Kusa da ita yaje ya duk'ursa ya ce " me yasa bakison cin abinci my cutie so kike ulser ta kama munke"Dagowa tayi ta Kalleshi tare da marairaicewa ta ce "Yaya banajin yunwa ne shiyasa zazzabin ne kamar yakeson dawomun" Tab'a jikinta yayi yaji ya fara zafi cike da damuwa ya ce "Sannu my dia Allah baki lafiya yanzu dai dan Allah idan baso kike hankalin yayanki ya tashi ba please Ki daure kici abincin ko Kad'an ne kinji y'ar lelena" Gyada mishi kai tayi ta ce "To yaya" Kallon Maryam yayi ya ce "mik'omin plate d'in" cikin Sauri ta mik'a mashi zaunawa yayi tare da Fara bata tana amsa batasaniba sosai ta ci Dan Arman na bata yana binta da zafafan kalamai bata saniba harta cinye plate din"wara idanu tayi ganin plate din ba komai ta ce "Yaya Amma tare mukaci" Dariya yayi ya ce "a a a da aljani kikaci" Hararar wasa tayi mishi ta ce "Sarkin fadan magana" Shafa sajenshi yayi ya ce "nid'in " Ehmana ta fad'a tana aika mashi da harara"Dariya Kad'an yayi ya ce "Ina son harararnan fa sosai cutie please kici gaba dayimun" Wara idanu tayi ta Kalleshi sai kuma tayi dariya magani ya b'alla mata Tasha tukwana ya Mike ya ce "ki huta sosai nima zanje na kwanta na Shawo gajiya" To my yaya have a nice dream "yana fita su Hasina suka kwashe da dariya " Hararar wasa Aira tayi musu ta ce "me kukema Dariya" Salon love mana Muma dai koba komai mun k'aru "Murja ta fad'a tana Dariya Nan suka shiga mata tsiya Inda ta Kyalesu Tayi Tare da kwanciya kan Babban gadon da saiya d'auki mutane da yawa Ba jimawa baccin gajiya ya kwasheta. Washegari da misalin Goma na safe tayiwa Mummy a garin yola Wanda Bata fad'awa Daddy dalilin zuwantaba tadai cemai ne zataje zumunci wajen y'an uwa shi kuma daman baya hanata kasancewar Jirgi tahau yasa tazo da wuri Bayan tazo ta huta Inda y'an uwanta maza da mata suka dinga zuwa gaisheta tare y'ay'an y’an uwanta Dan masha Allah gidansu badai yawaba kasancewar mata hud'u Bappa ya jera Allah yayiwa biyu rasuwa yanzu saura biyu sannan mutane ne masu zumunci da girmama na gaba dasu kasancewar Mummy itace ta ukku a Duka gidan cikinsu Talatin a lokacin da tazo Aira bata saniba tana Chan sun baje dasu hasina sai hira ake Dan tuni ta saki jiki dasu kamar daman sunsan juna Dan sudin suna da wayau sosai irin wannan mutanen ne masu saurin sabo Arman ma baisaniba saida wani cousin d'inshi Suleman yazo ya fad'a masa Dayake part d'aya suka kwana Bayan ya shirya around 12 ya shigo Palourn a lokacin daga mummy sai gwaggo da Baffa saikuma Babban Yayan su Mamy Nasiru har kasa ya duk'ursa ya gaishe da mutanen palourn yayinda Mummy idonta nakan d'an nata Yana Dagowa suka hada ido biyu Harara ta maka mai da ta sanyashi yin kasa da kanshi '"Sanyawa bappa yayi aka kira Aira fitowa tayi cikin doguwar hijab d'in Hasina saboda kayantane ma ta sanya kasancewar irin jikinsu daya A sanyaye ta fito Kallonta mummy tayi tare dayi mata fara a ta ce "taho nan y'ata " a sanyaye Aira taje wajen Mummy tare da zama k'asar kujerar da take a kunyace ta gaishe da mutanen dake d'akin gaba d'aya suka Amsa mata cikin sakin Fuska"gyaran murya Baffa yayi tare da Kallon Arman ya ce "Yanzu mahaifiyarka tayi mana bayanin komai dake faruwa Wanda mu bamu da labari sai yanzu kamar yanda kukasani bana magana me yawa Saidai nayi Kad'an walau tayi dad'i walau kada tayi yanzu kai Mujahed maganar da Aka fad'a Gaskiya Ce Kai kayiwa y'ar uwarka ciki Dan Rashin Imani" D'agowa Arman yayi ya kalli vappa tare da Kallon Aira da tayi kasa da kanta tana hawaye ya ce "Wallahi tallahi Bappa ni wani Abu bai tab'a shiga tsakani na da itaba kuma gata nan a gabanku ku tambayeta" Kallon Aira Bappa yayi ya ce "Kinji abunda Yafada jikata da gaske yake ko Karya karkiji nauyi ko kunyar kowa ki fadamana Gaskiya" Ba abunda Aira take inbanda hawaye Cikin k'arfin hali ta gyad'a kai ta ce "Da gaske yake " Kallon Arman Bappa yayi ya ce "To meyasa akace ka amsa cewar kai kayi mata Bayan ba haka bane" Kanshi na kasa ya ce "Na amsane kawai baffa banason Ana cira magana d'ayane shiyasa " Kallon Aira Baffa yayi ya ce "To ke jikata Wa yayi miki Tunda dai tsohon mijinki ya ce " ba shi bane,sannan Mujahid ya ce bashi bane "Kukan da take rikewa Aira ta fashe dashi tare da cewa " Wlh Baffa zan iya rantsewa da alquran mai girma akan ban tab'a zina ba Nima bansan ya akayi hakan ta faruba amma wlh bantaba ba Banmasan ya ake ba ta k'arasa fad'a tana rushewa da kuka"Rungumeta Mummy tayi tare da Lallashinta ta ce "ki kwantar da hankalinki y'ata ni kaina ina tantama akan Abunnan kallon Bappa tayi ta ce " Bappa inason ka bamu izinin mu kaita Asibiti yanzu a k'ara gwadata Dan Gaskiya ni banga alamar wani ciki a tattare da itaba sannan ban yarda zata aikata hakanba"To Fatima kuje asibitin dan a tabbatar din ba matsala kallon nasir yayi ya ce "Nasir gashi ka rakasu asibiti Gwaggo ta ce " Gaskiya kam gwara Aje asibitin amma ni banga Alamun ciki a tattare da yarinyar nan Mai ciki kama da wa yake kowa yayi na am da wannan shawarar har Arman A tare da Mummy da Arman da Aira tare da Baba Nasir dake tukasu suka nufi general hospital Adamawa Suna zuwa basu bi wani layina Nan aka Auni jinin Aira tare da fitsarinta Dan Mummy ta ce awon komai za ayi mata itadai Aira tayi tagumi Sundau minti ashirin Tukwana Result ya fito Bayan Dr ya duba ya karanta kallonsu yayi ya ce "Ba wani Abu ke damunta ba face Typord ya kama ta sosai tun baikai haka ba Rashin shan magani yasa ya fara tsanani Sannan aman ma da take typord dinne shike sanya wannan Amma yanzu zan rubuta muku magani insha Allahu tayi sati Tana sha zata samu sauk'i Allah ya k'ara lafiya ya fad'a tare da Fara rubuta musu maganin" Sosai sukayi mamakin jin Abunda dr ya fad'a Arman ko wata nauyayyar Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Alhamdulilla daman nasan cutie bazatayi irin wannan Abun ba" Aira ko Itama Ajiyar zuciyar ta sauke Dan daman tayi mamakin Ace tana da ciki idan dai ba a ruwa ake shan cikinba Mummy ko sosai tayi hamdala Dan dama bata gama yarda ba Bayan Dr ya rubuta musu magunguna a asibitin suka saya Dan son tabbatarwa Bayan sun bar asibitin nan Saida sukaje Private hospital Ukku amma Duka result d'in d'aya ne typord ne ke damunta sosai sukaji dadi sukayi murna musamman Arman Saidai kuma sosai sukayi mamakin wancen result d'in na sokoto cikin farin ciki suka koma gida Inda suka tari su Gwaggo da wannan daddad'an labarin sosai suma sukayi hamdala da murnar AL amarin nan Bappa ya ce "Ba abunda zamuyi sai hamdala ga ubangiji to amma ko meyasa Chan Sokoton suka bada result haka" Wlh Bappa inaga kawai shirine akai ko da kishiyar kasan mu mata ba abunda bamu aikatawa"hakane kuwa to Allah ya tsare mana imaninmu"ARMAN ko cikin zuciyarshi cewa yayi "wannan ai likitan ma na ganshi Dana bashi tukuici tunda yayi sanadiyar Raba cutie da wannan k'ayar" Gyaran murya Bappa yayi ya ce "To Alhamdulilla yanzu sai magana ta gaba a Gaskiya duk abunda yake faruwa bamu da masaniya mu godewa Allah da ya sanya yaran nan basu fad'a muguwar hanya ba dukda dai suma da nasu laifin amma ni nafi ganin laifin iyayensu sannan irin wannan Abun da iyayensu suke ba Abu bane me kyau Suna son su jefa yaransu ne cikin Wace hanya ta daban tun yaushe aka wuce da Yayin Auren dole illolinshi yafi amfani shi yawa sannan idan saurayi da budurwa suka nuna sunason junansu to abunda yafi shine ku barsu su Auri junansu saboda idan ba a haka ba zasu iya aikata abunda iyayen suzo sunayin nadama a Gaskiya Kabir da Abubakar basu kyauta ba Suna matsayin y'an uwa su dinga Abu kamar Annabi da kafiri Musamman Abubakar da yake da y'a mace shi ya kamata ace ya fara saukowa amma dukansu Suna zurfafa abu to yanzu Nidai a shawarata da tunanina namu na manya na yanke shawarar d'aurawa yaran nan Aure Saboda gujewa abunda zaizo ya faru nan gaba tunda yanzu an samu an tsallakewa wannan Abun kamar wasa nan gaba zai iya zama gaske ya kika gani Fatima kina ganin ba matsala" Ajiyar zuciya Mummy ta sauke ta ce "Alhamdulilla Bappa ai maganar da tazo dani kenan kawai a daura musu Aure a huta amma banason ayi da masaniyar iyayensu har zuwa muga lokacin da Allah zai daidaita abun dan yanzu Duka iyayen sun dau zafi"daman baza a sanar dasu ba insha Allahu mu nan mun isa mu wakilcesu gaba d'ayansu su biyun d'aya suke a wajena " Wani sanyi da farincikin da basu tab'a shiga ba ya ziyarci zuciyar sannan masoyar Alhamdulilla kawai suke furtawa "Kallon Arman Baffa yayi Ya ce " Kai Mujahed kaji hukuncin da muka yanke ka amince sannan kana sonta?Sosa keya Arman yayi Tare da cewa "Ai bappa so bama saina fad'a ba kowa yasan ina kaunarta Amincewa kuwa da gudu ma ai saida kawai muce mungode Allah ya k'ara girma da dattako "Dariya Bappa yayi tasu da manya yace kaji mun yaran zamani ba kunya" Mummy ko girgiza kai tayi tana murmushi Gwaggo ce ta ce "Kaji fitsararren yaro" Baba Nasir ne ya ce "Ai abunda ke ranshi ya fad'a ba laifi bane" Duk Dariya sukayi yayinda Aira kanta na kasa tana mamakin yanda Arman bayajin kunyar nuna soyayyar da yake mata gaban kowa"Bayan anyi shiru Sannan Bappa ya kalli Aira ya ce "To saura ke jikata Kinji duk abunda muka fad'a Kin yarda kin amince mu d'aura muku Aure ba tare da sanin Iyayenku ba ?Aira kunya dukta rufeta Gyad'a kai tayi tare da tashi cikin Sauri ta Riga da gudu Tayi Dakinsu Maryam" Duk Dariya y'an palourn sukayi "Bappa ya ce Kinji yaran zamani ko" Airako na zuwa su Maryam suka dareta Dan suna lab'e sunji abunda akecewa sukace "Wow congratulations sis Finally dai Kin kusa zama real Mrs Arman.......✍🏿 *A hayye sama rijiyar nisa*💃💃💃💃 *ai wannan kid'an da Nida yaya Arman fans Nake*💃💃💃💃💃💃 *a hayye warrrrrrrrrr*💃💃chashewa zamuyi fans tunkan abun yazo mu fara training d'in rawa💃💃💃💃😅 Manage ba yawa😌 _*Miss Hajo ce*_ [7/13, 12:09] Hajo hajo: 🅿️.........*93&94* .....Finally dai Kin kusa zama real Mrs Arman "Dariya Aira tayi tare da rufe fuska nan suka shiga yi mata tsiya itadai bata tankasu Dan yau jinta take kamar salla Abu kamar wasa. Bayan barin Aira wajen Bappa ya kalli Mummy ya ce" to yanzu sai mu jira lokacin da zata gama idda sai a daura Auren "Dagowa Mummy tayi ta ce " Bappa ai a tunani na babu iddar wancen mijin a kanta bai d'ora mata idda ba"Kallonta yayi ya ce "kun tabbatar kuwa Fatima" Eh Baffa haka maganar take"Ajiyar zuciya Baffa ya sauke ya ce "masha Allahu abu yazo cikin sauki To ke yanzu Fatima ya kike ganin Abun zai kasance zuwa yaushe kikaga za a D'aura Auren Dan banson abun yad'au nisa " Bappa duk yanda ka yanke Amma ni yanda naso a had'e da bikin Maryam tunda kaga saura wata guda sai a game ayi sannan an kikkimtsa komai "Hakan yayi to Allah ya kaimu lokacin yanzu sai a fara shirye shirye har zuwa lokacin" Cewar Bappa "Arman ne ya kalli Mummy tare da marairaicewa ya ce " Mummy Wata guda baiyi nisa ba"Jefa mishi Mafirfici Mummy tayi tare da cewa "tashi ka bamu waje marar Kunya" Gwaggo ko kama hab'a tayi ta ce "nikam inaga ikon Allah" Murmushi Bappa yayi ya ce "Yaran zamani ne sai hakuri" Barin d'akin Arman yayi yana murmushi ga kuma haushinshi na Wata guda da akasa shi yaxaci ma cewa za ai gobe kawai a daura musu Aure ya tafi da Cutie d'inshi Nan dai su Baffa sukaci gaba da tattaunawarsu Inda daga karshe magana ta tsaya akan wata guda mai zuwa Za a daura D'akin su Maryam Mummy ta nufa Inda ta tarar sun sanya Aira tsakiya sai tsokanarta suke"Murmushi tayi ta ce "Dan Allah ku barmun y'a haka Karku takura mata Bata da lafiya " ta fad'a tare da zama Gefen Aira ta tab'a jikinta taji da d'an zafi"Aira ko duk kunyar Mummy ta kamata kasa tayi da kanta "ya jikin daughter me kikeji yanzu" Cikin k'asa da murya ta ce "Bakomai mummy" Kama hannunta Mummy tayi ta ce "ki saki jikinki dani Banson d'ari_d'ari matsayin uwa zaki d'aukeni ba suruka ba keda Arman Duka d'aya na daukeku ban daukeki a suruka ba ki saki jikinki dani kinji " Gyada mata Kai Aira tayi ta ce "To mummy" Murja Mummy ta sanya taje ta zubo abinci da kanta ta dinga bawa Aira a baki gwanin sha awa har saida ta tabbatar ta koshi tukwana ta d'auko Ledar maganin da Dr ya rubuto musu ita ta dinga b'alla mata tana bata tana sha tana Yatsine fuska tare da rumtse ido a haka harta Shanye magungunan Mummy ta mik'awa Maryam ta ce "Amshi kinfi wad'anchan nutsuwa da lokacin shansu yayi ki tabbatar kin bata Tasha Sannan ki kula da cin abincin ta kinji" Dariya Maryam tayi tace "To mummynmu" Hasina ce ta ce "Kai Mummy kenan mu bamu da nutsuwa" Zadai Kuyi nan gaba Idan na Aurar daku "Dariya sukayi nan suka cigaba da barkwanci da Mummy Wanda har Aira Dan Mummy mace ce mai sakin fuska Duka d'iyan k'annenta da yayyunta d'aukarsu take tamkar nata ga bata girman kan Wasa da dariya dasu wani lokacin. Cikin kwana Ukku Aira ta warke garas kamar bata tab'a ciwo ba saboda kula da shan maganinta da Mummy suke gashi biyu aka had'asu hada na hausa ake bata tana sha ganin taji sauk'i ya sanya hankalin Mummy kwanciya Fitacciyar mai gyaran jikin Amare tundaga dilka k'amshin jiki Da sauransu Mummy ta daukota daga Sudan akan ta gyara mata y'arta na wata guda Bayan ta biyata mak'udan kudade gidan yaya Nasir Mummy ta sanya Aira ta koma Dan a gyarata a nutse Matar yaya Nasir d'in Daman itama gwanar gyaran jikice Gata tana da kirki mahaifiyar Hasina da Maryam " Ita kuma Murjanatu d'iyar kanwar Mummy ce mai biya mata Amina ita tana aure ne a gombe Su kuma suna zaune ne a gidan kakanninsu Su ukkun Sosai Aka shiga yiwa Aira gyara na musamman Wanda cikin kwana biyu tuni harta sauya ganin komai ya fara daidaita ya sanya Mummy bankwana da Yola Ta koma katsina Daddy tayima dabara ta ce "zataje Dubai domin sayowa Maryam kayan daki bikin yanzu saura sati ukku" Cikin sauki Daddy Ya amince mata saboda daman duk bikin da za ayi yawaici na family d'insu itake d'aukar nauyin Kayan daki Hakan yasa Shima ya k'ara mata da 15 million akan ga gudummawarshi Godiya Mummy tayi mashi Bayan ta ce mashi daga Chan Yola zata wuce Har sai Angama bikin nan ne ma dak'yal ta samu daga karshe ya yarda washegari Mummy ta wuce Dubai domin hadoma Tilon d'an nata Lefe tare kuma da kayan d'akin Aira da Maryam. Arman duk ya shiga busy saboda Rashin samun ganin Aira da bayayi Dan tunda aka fara mata gyaran jiki ya daina ganinta Wanda Mummy Ce ta sanya a hanashi ganinta hakan sosai yake damunshi itama Airar sosai take son taga sahibin nata yanzu sati guda kenan ana mata gyara Wanda idan ka ganta saika rantse ba ita bace Saboda wani fitinannen kyau da Haske data Kara ga duk Inda ta gitta tabar wajen Sai Ya bide da k'amshin ni ima da dad'i ga k'iba data fara ta murmure tayi kyau saboda kullum Safina Matar yaya Nasir saita dafa mata farfesun kaji Wanda take hadashi da magunguna kuma ta tsare Aira dolenta saitaci kuma ta Shanye romon dukda ba jin dad'inshi take ba ga kuma lafiyayyen tuk'ud'i da ake dama mata mai dad'in gaske kullum hakan yasa tuni ta cicciko ramar nan Duka babu"Yau Arman ya gaji hakan ya sanyashi zuwa gidan Goggo saboda gidanshi dake Yola ya koma Dan bayason zaman hayaniya gidan Baffa ko baya rabuwa da mutane yana zuwa ya sanya yaro.ya kira mashi murja Dan yanzu daga husina sai Murja saboda Maryam tare ake musu gyara da Aira Bayan ta fito kallonta yayi yace "jeki sanyo hijab ki rakani Wani waje" Cikin Sauri taje ta sanyo hijab d'inta Ya shiga mota itama ta shiga yaja sukabar gidan batare da ya kalletaba ya ce "Gidan Baba Nasir zamu dabara zakiyi ki fitomun da Aira" To yaya "ta fad'a suna isa Arman yayi parking a waje ita kuma Murja ta shiga koda taga Aira dak'yal ta ganeta " Ya subhanalla Ta fad'a tana wara idanu"Dariya Mai gyaran jikin tayi "Zaunawa Murja tayi tare da kama hannun Aira ta ce " Sis Kinga kuwa yanda kika koma wlh kin zama sak baturiya wlh bame kallonki ya ce "a k'asar hausa aka haifeki ke Kinga yanda kika koma kamar baki tab'a ganin rana ba jifa jikinki laushi kamar Auduga yo ko Auduga wannan kin fita laushi yacin"Dariya Aira tayi ta ce " kai sis kin iya zuga fa"Ai ba zuga bace Gaskiya Ce wannan yaya Arman ya ganki ai susucewa zaiyi ya ce "Sai an d'aura yau” Dariya Aira tayi tare da K'asa da kanta Sosai tayi missing habibyn nata "kama hannunta tayi tare da janyo mata gyale ta yafa mata ta ce " zo kiji wani abu"Kallonta mama Safina tayi ta ce "Ina kuma zaku da ita Bata fita Ai in ana gyaran jiki ba ashiga rana" Marairaicewa Murja tayi ta ce "Aunty wata magana ce fa kawai zan fad'a mata ba waje ba zamu fita muna bakin Barrander " bata Kara cewa komai ba Yayinda cikin saurin Murja taja hannun Aira bata direta ko ina ba sai Gaban motar Arman ta bud'e mata tashiga ita dai Aira ta zama hoto "murmushi tayi ta ce " yaya na gama aikina saura kuma tukuici"Bandir d'in y'an Dubu_Dubu ya mik'a mata tare da cewa "ga tukuicinki Ya fad'a yana jinjina mata hannu Rufo musu kofar Murja tayi tana Dariya ta maza ta tari taxi saboda tasan ta koma ciki Aunty Safina Masifa zatayi mata "" Wow"Arman ya furta lokacin da ya juyo ya kalli Aira da yaga ta sauya mashi ta k'ara wani fitinannen kyau Ga k'amshin dake tashi daga jikinta tunda ta shigo motar ta turnuke da k'amshi "murmushi Aira tayi tare da d'aga idanunta a hankali ta saukesu akan na Arman daya kafeta da idanu bako k'iftawa " Murmushinshi mai tsada ya sakar mata ya ce "Kinga kuwa Yanda kika koma cutie ai da har zance kodai sauyamun Matar akai bakigaba yanda kikayi kyau" Dariya Aira tayi tare da rufe fuska"yau kuma kunyata akeji "Murmushi tayi tare da sauke hannun langabar da kai tayi A hankali cikin zazzak'ar muryarta mai sanyaya zuciyar mai sauraro ta ce i really miss you my Yaya "Kama.lallausan hannunta yayi Wanda yakejinshi tamkar auduga take taji wani abu ya tsargarmasa tundaga samar kansa Saurin rumtse ido yayi tareda bud'ewa ya Kalleta a hankali ya ce " miss you too my cutie nakasa daurewa jure rashin ganinki ke naga kamarma bakiyi missing d'ina ba"Wara idanu tayi ta ce "injiwa yaya ai nafiyinma missing d'inka yana rik'e da hannunta yana murzawa ya ce " Uhm Gaskiya Mummy na gyaramunke tanason d'anta ya shana da yawa"rufe fuska Aira tayi ta ce "Uhm kai yaya" Murmushi yayi tare da cire hannun data rufe fuskar dashi ya ce "Kinsan bansan kunyar nan Please kidaina Zata Takuramun da yawa karkijemun da ita gida ki barta ma tun anan " kasa da kanta Aira tayi batare da tace uffan ba"Zaki daina jin kunyartawa ko cutie"?Dagowa tayi tare da marairaicewa ta ce "My yaya ai kunya wazibi ce ga kowace y'a mace ka manta manzon Allah S A w ya ce duk... Rufe mata baki yayi tare dayin Dariya ya ce " ya isa malamata shine za a janyo mun hadisi Naji "Dariya tayi Kad'an ta ce " yaya kenan"b'ata fuska yayi ya ce "Daga Ranar Da aka daura ki tanadi sunan da zaki dinga kirana dashi Dan bazan k'ara Amsa yaya ba" murmushi kawai tayi tare da girgiza kai ta ce "Uhm " Uhm "Shima ya maimaita a tare sukayi Dariya sun.kwashi awa biyu a motar suna shan hira Airace ta Kalleshi ta ce " Yaya bari na koma ciki karsu zaci wani wajen naje"Harkin gaji da ganin Yayan naki "ya fada yana langabar da kai" marairaicewa tayi ta ce "Nina isa na gaji da ganin yayana abun alfahari na bank'i mu Dawwama a haka ba kasan da hakan banason ne Mama Safina tayi fad'a " Sakin hannunta yayi ya ce "to shikenan hakan ma nagode my prince's Ki kulamun da kanki kinji" Murmushi ta sakar mai ta ce "kaima haka " I love you "I love you 2 ta fad'a tare da barin motar Dan karya Kara tsareta Dan ta lura baida niyyar barinta Murmushi Arman yayi tare da barin Wajen koba komai yaji sassauci a ranshi Aira ko cikin sand'a ta shiga gidan Mama Safina da ta fito Harararta tayi ta ce " Ja irai Watau Murja Ni tayiwa wayau zata dawo ta sameni ke kuma hada biyeta"k'asa da kanta Aira tayi tana wasa da zoben hannunta ta ce 'Mama nima bansan shi bane "Kudai kuka sani yanzu ki maza.kije Ummu Rumah ta gama had'a ruwan wanka ki maza kije Tund'azu itama ke take jira 'to Aira tace " tare da sauke ajiyar zuciya bata mata fad'a ba "D'akin da ake mata gyaran Jikin ta nufa. Biki ya rage sati guda Mummy ta dawo daga Dubai tare da lefen Aira saida ta had'o akwatina set goma Wanda ko wani set mai guda biyar ne akwatina hamsin kuma dukansu shak'e suke da abun duniya na ban mamaki Dan akwatin gold ma daban A gidansu aka baje akwatinan saikuma Sayayyar kayan D'akin Maryam hadaddu y'an daure Mummy ko hutawa bata gama ba ta ce " A kaita taga y'arta"Hafiz d'an kaninta Umar shi ya d'auketa ya kaita gidan Baba Nasir Tana shiga a palour ta tarar da Aira tana shan fruit "Aira na Dagowa ta kalli Mummy wara mata hannu Mummy tayi da gudu ta ruga tare da Fad'awa jikinta cike da farinciki ta ce " Oyoyoy Mummynah Sannu da zuwa"Murmushi Mummy tayi tanajin k'aunar Aira har ranta ta ce "Lafiya qalau Daugher ta Ai dak'yal na ganeki" Murmushi Aira tayi tare da kama hannun mummy suka zauna "Kallon ummu Rumah Mummy tayi ta ce " Ammafa Gaskiya Ummu Rumah kinfitomun da y'a nesa ba kusa ba Jifa irin kyan da tayi Godiya nake dole na k'ara had'a maki da tukuici "Dariya Ummu Rumah tayi cikin hausarta da bata gama.nuna ba ta ce "Ai aikienane Hajiya Nema nagode" Matar yaya Nasir taje ta cikawa Mummy gaba da kayan makuleshi itama Sosai Mummy tayi mata Godiya akan kula da y'arta da take ta ce "ba komai ai d'a na kowa ne" Maryam ce ta fito itama ta gaishe da Mummy"Amsawa Mummy tayi cikin fara a ta ce "Ahh masha Allah Amaren namu dai ba karya" Murmushi Maryam tayi tare da kama hannun Aira zasu bar wajen"rik'e Aira mummy tayi ta ce "a a barmun d'iyata bata gama Jin gumin mamantaba" Bata fuska Maryam tayi ta ce "Kai Mummy yanzu komai Aira kindaina yina ma" Murmushi tayi tare da janyo ta itama ta zaunar da ita gefenta ta ce "Ai ku yanzu na yayeku" Itakuma Kinga jaririyace"Duk Dariya sukayi yayinda Aira tayiwa Maryam gwalo ta lafe jikin Mummy tana tunanin ko Mamy yanzu tana wani hali Hakanan kawai taji tausayin mahaifiyartata tana jin kamar batayi mata adalci ba saurin Goge hawayenta tayi Dan kar kowa ya Gani ta ce "Ku yafemun please mamy Abba nasan banyi muku adalci ba. Juma'a a aka sanya Ranar D'aurin Auren Bayan anyi gayyar mutanen Arziki ranar laraba su Aira sukaje Saloon sosai gyaran kan nata yafi na kowa yin kyau wanda su kansu masu gyaran kan sai santin yanda kan yayi suke ga wani k'amshin ni'ima da gashin yake Dan a lullubeshi da manyan mayuyyuka masu kyau da tsada Wanda Mummy ta sayosu daga Dubai Sosai Aira ta k'ara fitinannen kyau Daga wajen saloon kai tsaye gidan kunshi suka wuce Inda fitacciyar mai K'unshin ta Zane Aira tasss sosai tayi mata kunshi mai bala in kyau abunka ga farar fata sosai K'unshin ya k'ara fito da ita a lokacin daka kalli Aira dole kayi sha awar Kara kallonta saboda kyan da tayi Saidai kawai a tofeta da wala haula su Murja ma da su Maryam sai santin lallan Aira suke a gajiya suka koma gida Suna komawa kuma aka dasa da gyaran jiki akan Inda aka tsaye ciki da bai tsaf ake gyara Aira. Washegari aka shirya walima Wanda aka kira manyan manyan malaman sunna Dan suyi wa azin mata A wani Babban Hall Wanda wannan shirin Mummy ne Dan ta ce Batason ayi bidi'a a bikin yaron nata Dan yayi albarka Aira sosai tayi kyau cikin tsadaddar doguwar Riga pink wacce ta Cikin lefentane da Mummy ta sayo a k'alla Rigar zatayi Sama sa dubu d'ari biyar banmayi k'arya ba Ba make up fuskarta sai ainahin kyaun da Allah ya bata Sosai rigar tayi mata bala in kyau a haka malamai mata suka shiga wa azi ba kama hannun yaro Wanda yawaici duk akan aurene da hakkin mace akan mijinta da hakkin miji akan matarsa da azabar da Allah ya tanadarwa Wanda basa yiwa mazajensu biyayya sosai aka shiga wa azi mai ratsa jiki Wanda jikin kowa saida yayi sanyi hatta iyaye Aira ko saida tayi hawaye haka aka k'are walima lafiya aka k'are Inda aka raba kyaututtuka na ban mamaki sosai wajen yayi mutane ni da Yaya Arman fans ma ba abarsu a baya ba dan sosai suka cika wajen wanda bama zan iya Gane wasu ba Dukda naga cikinsu wasu na gunguni akan mummy ta kwafsa musu da bata Bari suka chasheba sunajin haushin duk training din rawar da sukayi ya tafi a banza suna shirin yin warrrrr kawai an warware su (🤣)tukwana kowa ya koma gidanshi Wanda mota d'aya Mummy da Aira suka shiga Gidan Baba Nasir aka wuce da Aira Dan Chan y'an matan suke Hidimominsu. Washegari da misalin k'arfe 1:PM Aka d'aura Auren *Hajara Abubakar Umar* tare da Angonta *Muhajed Kabir Umar* Akan sadaki Naira Dubu d'ari Dan ance sadaki Kad'an yafi Albarka bayan nan aka daura na Maryam da angonta Salis Baffa shi ya zama wakilin Auren Aira shikuma Arman maimartaba Sarkin Adamawa shi ya zama wakilin shi d'aurin Auren da ya samu halartar manyan mutane Sosai wajen d'aurin Auren ya cika da mutane Saidai kuma an hana koda a waya ne a d'auki hoto ko vedion d'aurin Auren Arman sosai yayi kyau cikin Farar shaddarshi da Tasha surfani na ban mamaki sai kyalli yake duk Inda ya gitta zaka gane shine Angon saboda ya fita da kowa a wajen koda yaji an d'aura Auren rasa Inda zai sanya kanshi yayi saboda Farinciki A wajen yayi sujjada Ya jima yana kwararo yabo da Godiya ga ubangiji cousin d'inshi duk Dariya suke mai yayi minti goma yana sujjada tukwana ya d'ago cikin fara a ya ce "Alhamdulilla Allah na gode Maka daka nuna mana wannan rana daga hannunshi yayi sama sosai ya ce " Alhamdulilla Allah nagode nagode nagode Ka gamamun komai ya Allah Alhamdulilla "murna saida ta kusan zautar da Arman Y'an uwanshi sai Dariya suke mai cikin Sauri ya ja hannun Suleman ya ce " ta Ho mu wuce gida ". Aira sosai tayi kyau cikin tsatsadan white material Fitet gown da yayi mugun amsarta yayi Mata das a jiki Anyi mata nad'in headgolden wuyanta ko da hannayenta duk gold ne masu matukar tsada sosai tafito tayi wani irin masifar kyau ga make up da akayi mata tayi mugun mata kyau kasancewar bata make up A palourn Aunty Safina Y'an matan cousins din Arman duk suka baje sai tsiya suke yiwa Aira Itadai tayi shiru tayi sanyi Maryam ma sosai tayi kyau su biyun aka hadu aka dinga kashewa Hotuna Bayan anyi mata ita kadai a waya da kuma photograper wanda daya gama zai tura musu ya goge a haka sukayi dashi kuma Mummy ta ce Kar ayi posting koda a what's app ne kawai ayi saboda tarihi Itama Mummy sosai tayi kyau cikin lace d'inta mai mugun tsada hannuwanta da wuyanta shake yake da gwagwalai daka ganta zakaga asalin bafullatanar Yola Dan Mummy itama badai kyau da gayu ba shiyasa Arman yayi masifar kyau saboda biyu ya had'a ga kyan Mummy ga na Daddy Mummy na gefen Aira Ta kama hannunta nan aka shiga musu hotuna masu masifar kyau kamar y'a da uwa(kodan ai sune) ana cikin hotuna sai ganin Arman sukayi kamar daga sama ya fad'o kai tsaye wajensu Mummy ya nufa Tare da Rungumesu ita. Da Aira kamar k'aramun yaro saiji sukayi ya sanya kuka y'an palourn duk Dariya sukasa yayinda wasu suka fara musu video Aunty Safina ta ce "Haba ya haka ango da kuka kuma" wata kanwar mamy ta ce "kukan farincikine" Sosai Arman yake kuka jikin Mummy Danne zuciyarta tayi ta fara Lallashinshi Itama Airar kuka ta fara a jikin Mummy"Ikon Allah Mummy ta fad'a ta ce "To nima kukan kukeso nayi" Zaunawa tayi suna jikinta suna kuka Dak'yal Arman ya sassauta ya ce "Thnks you Mummy mungode mungode Allah saka maki da gidan Aljanna hak'ika kin cika uwa ta gari da kowani d'a zaiso ki kasance uwa a gareshi Mummy kingama mana komai Allah ya biyaki da gidan Aljanna Allah ya baki farinciki Fiye da yanda kika bamu" murmushi Mummy tayi ta shafa kanshi ta ce "Ameeen Ameen Allah yayi muku Albarka ya sanya Albarka a cikin aurenku ya baku zuri'a Dayyiba " Ameen Mummy"Arman ya fad'a yana Goge hawayen shi "murmushi Mummy tayi ta ce " Kazo ka rikitamun y'a kaga ka sanyata kuka"Dagowa Arman yayi ya kalli Aira dake jikin Mummy tana shashekar Kuka "Tashi yayi tare da zagawa gefenta Ya Rungumeta sosai tare da shafa bayanta ya rankwafar da kanshi yana sinsinar wuyanta a hankali ya ce " Alhamdulilla My beautiful wife finally dai An daura mana Aure kin zama mata ta Cutie ji nake kamar mafarkine nake Tabbas yau rana ce da bazan tab'a mancewa da ita a rayuwa ta ba"Lafewa Aira tayi jikinshi Tare da Yin shiru tana sauraran Kalamanshi itama d'in ji take tamkar a mafarki wai yau itace Matar Arman Bayan gwagwarmayar da aka sha a baya shiru tayi tana sauke ajiyar zuciya Tare da Yin luff a jikinshi "Y'an palourn sim sim kowa ya dinga Zamewa yana fita Dan bazasu iyaga wannan Rashin kunyar ba Mummy girgiza kai tayi tare da barin Wajen Dan tasan Arman gaban kowa zai iyayin komai indai akan Aira ne ta Riga da tayi mishi uzuri Suko tuni sunma manta da wanzuwarshi wasu mutane a palourn musamman Arman Ganin tsayuwar bazata fishshesu ba ya sanya su zaunawa kan kujera Suna Rungume da juna Arman tuni notin kanshi ya fara sincewa Dan Aira ta gama rikitar dashi a hankali ya rad'a mata ya ce " Kinyi kyau my wife"Uhm kawai tace tana shak'ar daddad'an k'amshin turaren mijin nata shinshina wuyanta ya fara tundaga kan wuyanta Yanajin wani sabon yanayi baisan lokacin da ya fara kissing d'inta ba Ta ko ina Aira ko kasa hanashi tayi Dan sak'on yana shigarta sosai jikinta tuni ya mutu batayi aune ba saiji tayi y Had'e bakinsu waje d’aya ........✍🏿 *chakwaiiiii yaufa chashewa zamuyi yacin kowa yau ta fito ta gwada mana kalar farincikin da ta shiga Finally dai yau Aira ta zama Mrs Arman chakwaiiiiiiii*💃💃💃💃💃kowa ya fito yayi musu wak'a nidai ga tawa😹 _Naga amarya Aira tana ta yanga naga ango Arman yana ta burga naga Nida yaya Arman fans suna ta takuuuu_💃💃 _Ranar kuke jira yau gashi tazo muma da tamburanmu gamu munzo Ango Arman shida Aira Amarya kuyo rawa ta murna anyi Aure_ 💃 _Allah ne ya had'a ba wani mutum ba_💃💃💃💃 *Lokaci ne gashi naku yazo aurenku anka d’aura yau kuncimma burinku a kauna Happy marriage life Aira&Arman *🍭🍬🍡🤸🏼‍♂️🎈🎈🎁🎊✉️📩📨 *Warrrrrrrrrrrrrrrrrr*💃💃💃💃😂 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/14, 12:42] Hajo hajo: 🅿️.........*95&96* .....Had'e bakinsu yayi waje d'aya Tare da Fara mata wani irin tsotsa Sosai suka shagala suka ma manta a wajen da suke Ringing d'in wayar Arman ya dawo dashi cikin hankalinshi cikin Sauri Arman ya matsa Itama Airar matsawa tayi tanajin kunya Daga kiran Arman yayi daga bangaren Mummy ta ce "Sarkin marassa kunya saika kyaleta tazo mutane su ganta Idan kayi hakuri ba kai maka ita bama za ayi ba Ka kawomun ita yanzu yanzu gidan Baffa" Sosai k'eya Arman yayi ya ce "Sorry Mummy gamu nan" kama hannunta yayi ya ce "Taso muje gidan Baffa my cutie" Kanta na kasa ta bishi suka bar palourn Duk kunya ta gama cika Aira ganin yanda Ake kallonsu yayinda shi kuma Arman ko a kanshi A motar Suleman suka shiga shi ya kaisu gidan Baffa koda suka fitoma Hannunsu mak'ale Dana juna kannen Mummy sai tsiya sukeyiwa Arman yana murmushi Itako Aira duk kunya takeji A haka suka ratsa mutane suka shiga cikin palourn Wanda cike yake da y'an uwa kai tsaye Aira wajen Mummy taje ta zauna Kasa tare da d'ora kanta saman cinyarta nan Mummy ga shiga nunawa sauran y'an uwan nata surukar tata kowa Sosai suka yaba da kyan Aira ga kuma nutsuwarta da kunya Nan aka shiga hotuna da y'an uwa Wanda Mummy na tsaka Aira da Arman na gefenta sauran kuma Su Bappa da Gwaggo da sauran y'an uwanta nan aka shiga hotuna masu kyau Alhmdll biki yayi biki Saidai ace Alhamdulilla Dan komai ya tafi yanda akeso Bayan magriba aka wuce da Maryam gidan mijinta dake nan garin Yola wajen Takwas da wani Abu Mummy ta sanya Aira taje tayi wanka da ruwan turaren da ta had'a mata Bayan ta fito ta bata atamfa me kyau ta sanya tare da yafa mata gyale kama hannunta tayi suka fito palourn Inda ta tarar da Arman anan yana gefen Gwaggo yana janta Sai Bappa da yayyun Mummy A kunyace Aira ta gaishe dasu suka Amsa cikin mutuntawa Mummy ce ta ce "To abunda yasa Mukayi zaman nan akan hukuncin da na yanke na Inda zaku zaunane bazaku zauna anan k'asar ba London zaku tafi na Riga da nasa an buga muku biza da passport d'inku nasa an yankan muku ticket gobe insha Allahu jirginku zai tashi da misalin k'arfe Sha biyu na rana bazaku dawoba har sai munga yanda hali ya bada sai mungama da matsalar Iyayenku tukwana"da mamaki Arman ya ce " Mummy London kuma Haba Mummy mu fara zama Abuja mana"Bazaku zauna ba nan Arman Na riga da na gama yanke hukunci hankalinku zaifi kwanciya a Chan"Amma Mummy Wajen aikinafa kinsan ya kamata na koma kan aiki tunda sun mana uzurin Rashin lafiyata yanzu Dana warke ya kamata na koma"Na gama da wajen aikinka kasan daman sunsan baka da lafiya tunda har daga Chan wajen Aikin naka wasu sunje duba ka kana kwancen wannan to zatonsu har yanzu baka da lafiya sannan jiya na samu munyi waya da Matar president Akan baka da lafiya har yanzu tace babu matsala duk sanda ka warke zaka koma kan aikinka harma Bayan nan ta bani shi mai girman president d'in Shima kuma ya maimaitamun hakan akan duk sanda ka warke zaka koma kan aikinka to ai kaga bamu da matsala da wannan sannan kaga har yanzu albashinka na shigo maka duk wata "Ajiyar zuciya ya sauke Dan daman matsalarshi wajen aikice kawai ya ce " To Mummy "mummy ce ta kalli Aira ta ce " Daugher Lefenki yaza ayi dashi ina za a kai maki shi"kasa da kanta tayi a hankali ta ce "mummy duk yanda kukayi" A a a a ke zakiyi magana kinga ai hakkinkine naga sunyi yawan da bazaku iya tafiya dasu bane shawarar da na yanke zaku tafi da akwati hudu ne kawai a saka abubuwan da suka fi important sauran kuma saiki fada inda za a aje maki"cikin jin kunya ta ce "Mummy Allah duk inda kika ajesu yayi" Arman ne ya ce "bari na ari bakinta ki aje mata a wajenki kawai mummy" Kallonta mummy tayi ta ce "kinji wai abunda yace hakan yayi miki" Gyad'a mata kai tayi"To masha Allah kowa ya ce sannan Baffa ne ya d'ora musu da nasiha akan su zauna da juna lafiya da amana Inda Mummy ta dora da cewa " Ga kuma Amanar y'ata nan na baka karka sake ka b'ata mata "Murmushi Arman yayi a ranshi ya ce " Ai Mummy bani Amanar cutie ma b'ata bakice "Nan dai y'an uwa sukayi musu nasiha tukwana kowa ya nufi wajen kwananshi kama hannun Aira mummy tayi ta nufi d'akin da ta sauka Inda lefen suke Ganin Mummy ta wuce da Aira ya sanya Arman Shima komawa masaukinshi yaso ace d'akin su Maryam Aira ta koma ya samu damar kebewa da ita amma yanda yaga Mummy ta rirrike ya sanyashi bai tanka ba Suna shiga Mummy da kanta Tare da Murja da Hasina suka kama mata ta dinga fiddo akwatinan tana bud'ewa tana tambayar Aira ta fad'a abunda take buk'atar a saka mata a Wanda zasu tafi dashi Ganin kunya takeji ya sanya su Hasina tayata zaba Kaya dinkakku kala sha biyar kawai aka saka sai English wears akwati guda sunema sukafi yawa Saisu under wears da su ineer da sauran abubuwan amfanin yau da kullum Akwati Ukku Aka cika D'an Mummy tacema hud'u tayi yawa sauran abubuwan yasai mata a Chan Saida suka gama mata Parking d'in komai tukwana Mummy ta Sallami su Murja kama hannun Aira mummy tayi ta ce " d'ago ki kalleni sannan ki saurareni da kunnen basira Nasihace zan maki ta y'a da uwa ba wai surukarki ba "Aure da kikasani d'an hakuri ne Idan kin had'a da biyayya nasanki baki da matsala Aira ki k'ara akan kyawawan halayyarki Dana sanki dasu sannan ki dage da tsafta karki sake ki yarda mijinki yaga kazamtarki duk kankantarta kuwa sannan ki dage da gyaran jiki mace y'ar gyara ce Mu Kanmu manya da kika gani gyarawa muke bareku yara ki dage da tsafta iya girki,iya kwalliya,kissa da kisisina ,Jan aji namu na mata ,ki kama mijinki a hannu kam yanda bazai tabajin sha awar kallon wata a wajeba Idan bake ba sannan zaman Aure Dan hakuri ne ki gani kiji ki kauda idanu Sannan karki yarda wata ta samu kofar Rabaki da mijinki Arman yana sonki so bana wasa ba Aira ki kama mijinki kar kisa yarinta ko shirme Kinji sannan ta janyo wata leda ta bud'e ta fiddo katoton kwalbar miski ta mik'a mata ta ce " Kinga wannan farin miskine mai matuk'ar amfani karki sake kiyi wasa dashi koda ya k'are karki yarda kwalbar duk shagon da kika nuna musu zaki sameshi Ya kasance kullum kina matsi dashi kindai gane "K'asa Aira tayi da kanta cike da kunya ta gyad'a mata kai Aje kwalbar Mummy tayi sannan ta fiddo wasu magunguna cikin hikima duk ta shiga yiwa Aira bayanin yanda zatayi amfani dasu Inda ta hade mata su waje guda Dan karta manta ma rubuta mata yanda ake amfani dasu Cikin wata akwati ta sanya mata su ta ce " Kingansu nan sannan karki yarda ya gani ko yasan kina amfani dasu kinji da kunje ki samu waje ki boyesu "gyada mata kai Aira tayi tana goge hawayen da suka zubo mata Tabbas tasan tayi sa ar suruka mai kaunarta Kallonta Mummy tayi ta ce " Kiyimun alk'awarin Duka zakiyi amfani da abunda na baki "Cikin muryarta mai shirin yin kuka ta ce " Insha Allahu Mummy "wanka ta k'ara sanyata tayo da ruwan turarruka Bayan ta fito ta sanya slepping dress Gado Mummy ta ce ta kwanta sannan tace ki huta sosai saboda Kinga gobe zakuyi tafiya bacci ne me dadi ya d'auke Aira Bangaren ARMAN ko kusan kwana yayi yana Sallar Godiya da ubangiji . Washegari k'arfe Goma sha d'aya tayi musu a Airport Mummy ta rik'e hannun Aira sosai Aira tayi kyau cikin tsatsadar laffaya black kunsan yanda bakin abu yakeyiwa fari sosai tayi kyau haskenta ya k'ara fitowa sanye take da dogon takalmi Fuskarta a rufe itama mummyn sanye take cikin laffaya itakuma fara itama Sosai tayi kyau shikuma Arman sosai ya hakimce cikin babbar riga milk koban fad'a kyau da tsadar shaddarba kunsandai Arman baya sa karamun kaya sannan baya rainanniyar shiga fadar kyaun da sukayi ma bata nakine a lokacin sosai aka shiga daukarsu hotuna Wanda saboda tarihi ake d'auka badan ayi post ba Su Baffa ma da su Gwaggo sunyi musu rakiya tare da kannen Mamy jirginsu zai tashi har amfara kiraye kirayen suna Hakan ya sanya Arman ya fara bankwana da iyayen nashi har k'asa ya durkusa ya tab'a k'afar Mummy murmushi tayi tare da tasoshi ta shafa kanshi ta ce "Allah yayi mukua albarka ya sanya Albarka a cikin rayuwar aurenku ya sanya badi ya haka suna mukazo ina Kara fad'a maka dai ka rik'emun y'a amana" murmushi Yayi ya ce "Amen nagode Mummy bazan tab'a gajiya da gode maki ba mungode insha Allahu kuma zanrike maki y'a da amana"had'a hannunshi da na Aira Mummy tayi ya ce " Allah yayi muku Albarka ku rik'e juna da amana "Rungume Mummy Aira tayi ganin za a tafi ta fashe da kuka " Daddab'a bayanta Mummy ta fara cikin sigar lallashi ta ce "Kiyi shiru kinji Daugher Allah muku Albarka kuje jirginku zai tashi Insha Allah idan na samu dama zandinga zuwa ganinku Allah muku Albarka" Cikin shashekar kuka Aira tace "Mungode Mummy Allah saka maki da gidan Aljanna bamu da bakin da zamu iya gode maki Ked'in uwace ta gari Mummy " ta k'arasa fad'a cikin kuka "Duk yanda Mummy taso daurewa saida suka sanyata kuka Dak'yal Arman ya samu ya raba Aira da Mummy Wanda Shima ji yake kamar yayi kukan har suka shiga jirgi Mummy na Daga musu hannu Shima yanayi mata bye bye Airako tana jikinshi tana mashi kuka ko a jirginma dak'yal ya samu ya lallasheta tayi shiru kasancewar kujerarsu na kusa na juna ya sanyata Lafewa a jikinshi ba b'ata lokaci jirginsu ya d'aga sararin samaniya...✍🏿 *Kibiya ki karanta cikin kwanciyar hankali akan Naira 200 kachal 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/14, 12:43] Hajo hajo: 🅿️.........*97&98* .....Lagos jirginsu ya sauka wanda daga chan suka hau jirgin london Tafiyar awa Shida da Rabi ta kaisu kasar London Wanda Aira baccinta Tasha jikin Arman koda Suka isa saida ya tasheta hannunsu mak'ale Dana juna suka fito a lokacin baka ganin komai sai Haske Alamun su k'asar ma dare ne amma kuma Kamar rana Dan kowa Harkarshi yake Karewa wajen kallo tayi ta ce "Wow yaya K'asar ta had'u Gaskiya" Dan Mitsininita yayi a hannu ta ce "Auchhh sorry to my Zumah" murmushi yayi ya ce "kinmasan laifinki kenan" Langabar da kai tayi ta ce "kasan na sabane sai a hankali zan daina "har suka fito daga Airport Aira sai kalle kalle take Taxxi Arman ya tarar musu Bayan sun shiga ya fad'a musu unguwar da zai kaisu koda suka isa bakin get d'in gidan Sosai Aira ta zama bakauya Dan gidane na alfarma tun daga wajenshi Knoking Arman yayi ba ayi minti biyu ba baturen Mai gadin ya fito yana ganin Arman ne ya fara fara a cikin harshen turanci ya ce " Sannunku da zuwa mai gida marhaban "Hannu Arman ya mik'a masa suka gaisa Bayan shigarsu gidan cikin harshen turanci ya gaishe da Aira ta amsa da yaren Arman ko jinjina mishi yayi da hannu ya ce " Gaskiya kana kula da gidan yanda ya kamata"cikin harshen turanci"mai gadin shi ya shigo musu da akwatinansu cikin gidan ya aje bakin kofar palourn yayinda su kuma kai tsaye cikin harabar gidan suka Nufa madaidaicine da ya tsaru da shuke shuke gwanin burgewa da sha'awa ga tsarin gidan kanshi abun kallone parking space d'in mota hudu ce d'aya daga gidan Arman ne Dake nan k'asar London saboda Daddyma yana da nashi gidajen Ukku a k'asar Kasancewar suna yawan zuwa Hutu kasar "Da remote yayi amfani wajen bud'e k'ofar palourn Ai sumar tsaye nayi numfashina saida ya d'auke na y'an sakanni wannan shi ake kira da Aljannar duniya kenan Kujeru ne shak'e a palourn sabbi katakar na Alfarma Ga wani lallausar carpet dake baje a tsakiyar palour center Table d'in kanshi ya isa abun kallo Banda TV stand d'in dake baje Duka jiginta glass ne yanda kasan anyi tsomen gold saboda yanda take d'aukar ido ga k'atotuwar plasma d'in dake manne a Bango jikin glass din TV stand d'in Duka shake yake da kwalbar turarruka hatta d'akin da labulayen d'akin ya bud'e da k'amshin Rahama gefe kuma wajen dining ne Wanda irin na kujerun ne nan kadai ma ya isa kayi kauyanci selling din gidan ko kanshi Saiya tsorataka kamar hadari hadari nidai tsawon rayuwata bantabaga irinshiba Jinjina kai Arman yayi Dan Duka sabbin kaya ne a d'akin yasan wannan Aikin Mummy ce Aira ko cewa tayi " wow amma fa my Zuma gidan yayi da kayan d'akin ji yanda yake k'amshi kamar dama mutane a ciki"murmushi ya sakar mata danson tabbatarwa mai gadi ya kwalawa kira Bayan yazo tambayeshi yayi ya ce "Wa ya sanya akayi gyaran nan " Hajiya ce Ranka ya dad'e ita tazo da masu Daura kayan aka cire komai na gidan aka saka sabbi sannan ta dauki Wanda yake zuwa kullum yake zuwa yake gyaran gidan naga har ciki yake shiga yanzuma baijima da tafiya ba ya ce Hajiya ce ta aikoshi"Murmushi Arman yayi yana karajin soyayyar mahaifiyar tashi har ranshi ya ce "zaka iya tafiya(Karku manta duk maganganun nan da turanci sukeyinsu) Airama sosai taji k'auna da soyayyar Mummy na k'ara ninkuwa cikin ranta Allahsrk Mummy tayi mata abunda iyayenta zasuyi mata " Cikin palourn suka yada zango Inda Arman ya sauke Nauyayyar Ajiyar zuciyar ban gajiya Tare da janyo Aira jikinshi basuyi hutawar minti biyar ba ya Mike tare da ita d'akunan Suka shiga d'aya Bayan d'aya daman bedroom hudu ne Na farkon sosai yayi kyau kayan cikinma na ban mamaki y'an daurene Wanda koban fadaba kunsan Sunkai Duk yanda ba a tunani sosai kayan suka burge Aira tukwana suka Shiga dayan Shima Dai ba karya kayan sun hadu Duka kayan d'akin tundaga kan kujerun milk ne da ratsin golden kayan na masu tsaftane sannan suka shiga na ukkun shima shake yake da abun duniya Dayan bedroom d'in suka shiga Inda suke iske Gadon yara guda hud'u kowanne da drawer su da Abubuwan wasa birjik a d'akin Na wasan yara "Dariya Sosai Aira tayi ta ce " Allah bar mana mummynmu wannan d'akin kuma ko na waye jifa Duka kayan yara ne ciki "Rungumeta yayi ta baya Tare da Fara shinshinar wuyanta cikin kasalalliyar muryarshi ya ce " ta yaranmune da zamu Haifa Kika sanima ko yau na baki Twins"Rufe fuska tayi ta ce "Uhm my Zuma kenan" A hankali ya ce "My wife kenan" murmushi tayi Shima ya mayar mata cike da so da k'auna ya kama hannunta suka fito palour kallonshi tayi ta ce "to inane bedroom d'ina dia" Harararta yayi ya ce "Ai babu raben bedroom da zamuyi kowanne na kowane Ki saka kayanki Inda kikaso nima na saka nau Inda naso nidake kin manta Abu d'aya ne"murmushi tayi tana karajin k'aunar mijin nata na ratsa kowani sassa na jikinta Tashi Arman yayi ya dinga shigo da akwatinan Mikewa tayi ta ce " My Zumah na tayaka ko"Rufamun asiri ina kikatabaga amarya tayi aiki aike yanzu gimbiyace komai Saidai nayi miki "Cikin shagwaba ta ce " To ai nima banson naga Habiby na yana wahalshe da kanshi"Dariya yayi tare da nuna mata damtsenshi ya ce "kwantar da hankalinki Matar mijinta ai ba rago kika aura ba kalli Mijinnaki naki akwai k'arfi ai" Dariya Aira tayi sosai ta zauna tana Kallonshi har ya gama shiga da kayan ciki tukwana yazo ya zauna tare da d'ora kanshi a kafadarta kamar yaro Cikin shagwaba ya ce "Uhm my cutie ni kuma yanzu yaza ayi dani" Dariya Aira tayi Kad'an ta ce "Sorry my boy ko yunwa kakeji" Dariya Arman yayi ya ce"boy d'inki na koma kenan"d'age mishi gira tayi "mik'ewa yayi kamar Wanda aka tsunkula ya ce " Kije ki shirya tarbar mijinki ina dawowa nan kusa"Gaban Aira ne ya fad'i amma ta fusge ta ce "Ina kuma zaka my Zumah"peck ya bata a kumatu ya ce "Yanzu zandawo karkiyi salla kijira na dawo muyi tare kinji" gyada mishi kai Aira tayi ta ce "A dawo lafiya my hero" murmushi yayi yana karajin k'aunar Matar tashi ya fita Ya d'auki mota Aira najin Tada motarshi ta mik'e dukda tana d'anjin tsoro Inda taga ya sanya mata akwatinanta d'akin ta shiga tana zuwa ta cire kayan jikinta ta d'aura towel koda ta shiga toilet din saida taso tayi kauyanci Saboda yanda toilet din ya had'u wanka tayi Bayan ta fito ta had'a ruwan turaren da Mummy ta bata ta koma ta karayin na karshe dashi hatta toilet din saida ya bud'e da k'amshi daga nan tayi alwala Tana fitowa ta d'aga akwatin English wears din wata shalaulawar rigar bacci ta sanya Wacce da ita da babu duk d'aya iyakarta gwuiwa ita kanta saida taso taji kunya amma tunowa da hud'ubar da Ummu Rumah ta dinga mata ya sanyata barin rigar jikinta cikin Sauri ta d'auko magungunan da Mummy ta bata tayi amfani da miskin kadai sauran ta boyesu Inda Arman bazai iya ganiba Ganin ba abunda take ya sanyata Fara shirya kayanta a drawer Tana cikin shiryawa taji shigowar Arman juyawar da zatayi ta Kalleshi tsaye sosai yayi mata kyau cikin shigar k'ana nan kayan da sukayi mugun Karbarshi Ga wani k'amshi dake tashi daga wajenshi kamshin shi da nata suka had'u suka bada wani irin sanyayyen sanyin kamshi mai ratsa zuciya Arman ko saida numfashinshi ya d'auke na Dan wasu dakiku kafin ya dawo sosai Shigar ta cutie d'inshi ta tafi da imaninshi take yaji wani irin yanayi Wanda tunda yake bai tab'a shiga irinshi ba Dak'yal ya iya karasowa cikin dakin Kallonta yayi tare da bata rai ya ce "Cutie kinason wahalar da kanki ko ki bari aikin nan ba yanzu ba" Ajewa tayi ta ce "Daman naga bana komai ne shiyasa My hero Ammafa kayi kyau sosai yaushe ka shigo ka shirya bansaniba" murmushi ya sakar mata yana kallonta tundaga sama har kasa a take ya had'e wani irin miyau muk'ut ya ce "Shigar nan tayi mun my prince's daga yau irinta za adingayimun" Dukda gabanta dake fad'uwa Hakanan ta daure ta ce "Uhm to my husband komai kace ayi ai shi za ayi" Kama hannunta yayi ya ce "Shiyasa nake Kara kaunarki koda yaushe my prince's wannan na Daga cikin halayyarki da nafi k'auna Rashin gardama plz karki chanza daga haka" Murmushi ta sakar masa batare da tace uffan ba Arman Ganin alwalarshi na neman karewa ya sanyashi cewa "kina da alwala 'gyada mishi kai tayi " yawwa to sanya hijab d'inki muyi salloli To ya...saikuma tayi dariya ta ce "Tohm my Zumah" murmushi yayi mata Yana karajin k'aunar Matar tashi na ratsa ko ina na jikinshi Hijab har kasa Aira ta sanya Bayan ya shimfida musu prayer mat yana gaba tana bayanshi nan ya dinga jansu salla saida suka rama Duka sallolin da basu samuba tukwana suka dora da nafila Bayan sun salamce Ya juyo tare da dafe kanta nan ya shiga kwararo dukkan addu'ar da tazo bakinshi na nemawa aurensu albarka tare da zuri a ta gari da Larabci yake addu'ar sosai kamar yanda manzan Allah S A W ya koyar damu yakai minti ashirin yana kwararo adduo kafin ya gama Ledar da ya shigo da ita ya janyo Tare da fita Dan ya d'auko plate ita Aira bacci ma tafaraji bai dau wani lokacin ya dawo tare da plate da cup gasassiyar gasar gashin oven tunda aka bud'e ta wajen ya mamaye da k'amshin dadi Sannan ya bud'e fresh milk tare da tsiyayawa a cup Matsowa yayi tare da kallonta da tayi kasa da kanta ya ce "ha a cutie" Kallon kazar tayi tare da marairaicewa tana shirin magana taji ya sungumeta bai direta ko ina ba sai saman cinyarshi itako uwar son jiki Lafewa tayi jikinshi a haka ya dinga yago kazar yana bata tana ci yana binta da zafafan kalamai masu sanyata zuciya yana bata tana amsa Sosai ya samu taci Inda daga karshe ta cije baki"cike da kulawa ya ce "plx cutie ki bud'e" Cikin shagwaba ta ce " umm Ummm my yaya ni na k'oshi Allah cikina zai cike"Fresh milk d'in ya bata Tasha Kad'an "Kallonshi tayi ta ce " Baby kai bazakaci ba"Kashe mata ido guda yayi ya ce "bazanci ba Wanda dai kikaci zan cinye yanzu" kamarya yaya"Mikewa yayi a tare da ita in bridal style ya ce "me kikeci na baka na zuba yanzu zakiga yanda zan cinye" yana gama fad'ar haka ya yaye hijab d'in jikinta tare da kwantar da ita kan bed ya kashe fitulun d'akin tare bin kanta Ya haye Sosai gaban Aira ya dinga fad'uwa tana shirin kuka yayi saurin had'e bakinshi da nata sosai yake yimata wata irin zafaffar tsotsa kissing d'inta ya shigayi ta ko sosai yake romance d'inta cikin salo mai kashe jiki tuni jikin Aira ya mutu Dan sak'on sosai yake shigarta A haka ya samu har ya rabata da rigar jikinta Inda ya shiga wasa da tsayayyun na shanunta da su suka k'ara rikirkitashi Sosai Arman ya fita daga hankalinshi ya fara zaucewa Sosai a zafafe yake yin komai gaba d'ayansu saida yazamana ba komai a jikinsu ganin hakan ya sanyani saurin barin d'akin saboda wannan sirrinsu ne Zaune nayi a palour nayi tagumi Chan na jiyo wani gigitaccen k'aran Aira Wanda ya kauraye ilahirin gidan Sosai ta cika gidan da kuka Ni kaina saida nayi hawayen tausayinta Inason na koma na d'auko muku rahoto ina tsoro hakan yasa nayi zaman Inajin kukan Aira yayinda Arman ba abunda kakeji sai gurnaninshi da kukan dad’i dan yariga ya fita daga hayyacinshi ya lula wata duniyar ta daban (lol) *Sokwattawan shehu* "Daman ashe asibitin banza ne bansaniba mata ta tazo a duba ta Dan Rashin sanin aikinyi Ku bata result ba daidai ba ku d'irka mata maganin typord Mukaje tayi ta d'irka kullum ta dinga ciwon ciki wata guda kenan matata tana dirkar maganin typord Alhalin ba wani typord dake damunta Cikine da ita karshe sai b'arin cikin tayi a Gaskiya Dr ka cucemu Ka zaluncemu Kayi mana sanadiyar zubewar gudan jininmu da mukasa buri a kanshi yanzu haka Aikine kuke yanzu idan da mutuwa tayifa sosai mutumin dake tsaye gaban Dr Luqman ya shiga Surfa mashi masifa Inda ya shiga ba ta nan yake shiga ba " Dafe kanshi Dr Luqman yayi tare da mik'ewa nan ya dinga bawa bawan Allan nan hakuri Dak'yal ya samu ya hakura ya koma cikin fad'a ya kirawo nurse din da ta bada result d'in ba daidai ba dan bai manta da lokacinba cikin Masifa ya ce "Daman Bakisan aikinyinkiba Kintuna ranar da Alhaji Madugu ya kawo matarsa bata da lafiya kekikayi awon ina sane me yasa kika bada result ba daidai ba so kike ki tab'amun Carrier Asibiti na yanzu kinje kin bada result d'in me typord matsayin mai ciki kin bawa Mai ciki typord sanadin haka tayi asarar cikinta yanzu haka dak'yal na karkare da mijinta" Sosai nurse din ta shiga bawa Dr hakuri ta ce "Ranka ya dad'e kayi hakuri karka koreni daga aiki wlh Tsautsayine a lokacin na d'auki jinin waccen itama na d'auki nata haka fitsarin nasu a tare na dauka to Natafi na yiwa wata allura saina mance wannene nasu kuma naga kuna da alaka dashi sosai hakan yasa na fara Auna na matarsa Bansaniba kenan na waccen ne na fara aunawa Ta nan ne aka samu matsalar Amma Dan Allah kayi hakuri" Sosai ran Luqman ya b'aci Tsawa ya daka mata ya ce "wuce kiban waje Wayarshi ya lalubo cikin Sauri ya dannawa Alh Madugu kira ringing biyu ya d'auka Bayan sun gaisa daga bangaren Alh Madugu yana palour tare da matarshi da yaranshi " Alh Dan Allah kayi hakuri ranar da ka kawo amarya Asibiti an samu mistake ne wajen awon bamu saniba sai yanzu muka gano ba awon Matarka bane aka baka na Wata baiwar Allah ce take d'auke da ciki wata hud'u Matarka typord ne ke damunta bata da juna biyu Dan Allah kayi hakuri Ayi mana uzuri"Alh jin maganganun Luqman yayi tamkar saukar aradu a ka tuni wata uwar zufa ta karyomai da hannu ya fara firfitu ya ce "what Luqman me kake nufi kana nufin ba ciki ne da Aira ba typord ke damunta" Eh Alh kayi hakuri Ayi mana afuwa matsala ce aka samu"ba wata matsala sakarcine dai bakusan aikinyinkuba daman Ka bada awon da ba daidai ba ka hassadamun tashin hankali Luqman Naji Daddy Ya fara fad'a yayi saurin kashe wayar Wulli da wayar Madugu yayi cikin tashin hankali ya ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un" Zaune yayi dafe da kanshi yana Salati Mama saude ce ta ce "Alhaji lafiya" Cikin tashin hankali ya ce "Wai ashe ba cikine da Aira ba typord ke damunta Amma dai Allah ya tsinewa Luqman yaja na saki matata Firgit yace bazaiyuba wlh na maidoki " Sosai Hajiya saude tayi mamaki itama Kallonshi tayi ta ce "Amma Ai Alhaji saki Ukku ne fa kayi mata kuma a rarrabe bare ace saki d'aya yake" Innalillahi wa inna ilaihiraji'un Daddy Ya fad'a tare da mik'ewa kallon saude yayi ya ce "Amma kun cuceni kun zalunceni" wai Alh meye abun tashin hankali a nan Inma bata da ciki ka manta dumu dumu muka kamata ita da Saurayinta a d'aki meye abun tashi. Hankali a y'ar iska "cikin tsananin Zafin nama ya Mike tare da wanke ta Mari ya ce " Kika Kara danganta matata da y'ar iska zakici ubanki Munafuka duk bake kikaja mun ba ke kika sanya nayi mata saki Ukku saki d'aya nayi niyyar mata ba ukkuba "Ni ka Mara Alhaji " An mareki Munafuka Wlh inbanda darajar y'ay'anki yau kema da saina sakeki Munafuka kinja na saki matata Sosai ya shirga Surfa ruwan masifa da ba I da Wanda yaji da wanba baijiba kan uwar wa da wabi kawai yake .......✍🏿 *wannan shi ake kira ana tunanin wuta a makera sai aka Sameta a Masaka kowa yayi tunanin mama saude ce ta shirya abunnan to haka rayuwa take wani lokacin wanda akafi zargin zai aikata abu bashi yake aikatawaba Allahsa mudace duniya da lahira happy juma at khareem 2@ll muslims Allah sadamu da aikhairan dake cikinta*🕋🕌 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/15, 18:04] Hajo hajo: 🅿️........*99&100* ...Bari mu lek'a bangaren amarya da Ango zaune take saman Gado yayinda ta lafe jikinshi sai shagwaba take zuba mashi Arman ko Lallashinta kawai yake cike da so da k'auna ya ce "Kin gamayimun komai a duniya cutie tunda kika kawomun budurcinki na rasa da wasu irin kalamai zanyi amfani wajen gode maki da nuna maki kalar soyayyar da nake maki Saidai kawai nace Allah yayi miki albarka my beautiful wife " Arman jinshi yake cikin farincikin da bai tab'a shigar shiba Dan sosai Aira ta jiyar dashi dad'in da baitab'a jin irinshiba a duniya Lafewa tayi a jikinshi tare da Fara hawaye ta ce "Yaya Har yanzu fa zafi wajen “cike da kulawa ya ce "Sorry my love zaidaina bari muje ki k'ara shiga ruwan zafi Daukarta yayi kamar wata baby Dan shakwal yake jinta bathroom suka nufa Inda ya k'ara gasata sosai saida ya sanyata ruwa sau Ukku dukda tana raki a haka dai ya samu ya gasata sosai taji sassauci akan dazu daukarta yayi suka fito zai dorata kan bed cikin shagwaba ta ce " yaya Ajeni kamarma zan iya tafiya"k'in tabbata my love"gyada mishi kai tayi sauketa yayi a hankali Cije baki tayi tare da mikewa ta kama hannunshi kamar mai koyan tafiya shiko sai Lallab'ata yake tana d'an dingisawa Kad'an a haka suka fito palour akan three siter ta zauna tana turo baki"sorry my love da sauki ko"Eh "ta fad'a tana kauda mishi kai murmushi ya sakar mata ya ce " kodai fushi ake da yayan "Mayar masa da murmushin tayi ta ce " Nina isa nayi fushi da my nasful hayat "Rungumeta yayi yana karajin sonta na k'ara ratsa dukkan sassan jikinshi ya ce " I love you so much My everlasting"sannan ya Mike ya nufi kitchen cikin.kankanin lokaci ya had'o mata lafiyayyan breakfast din soyayyan dankalin turawa da kwai sai kazar jiya d'aya dumama mata Yanzun ma da kanshi ya dinga feeding d'inta Inda daga karshe itama tayi feeding d'inshi yinin Ranar dai haka suka yishi cike da k'aunar juna Dan tuni Aira harta mance wahalar da tasha soyayya kawai suke zubawa ba kama hannun yaro washegari a tare sukayi wanka Bayan sun fito Aira na gaban mirror daure da towel jikinta Ya fito Shima daure da towel ta baya ya rungumota tare da far'a sinsinar wuyanta Ta madubi yake kallonta murmushi ta sakar masa ta madubin "Uhm baby yaza ayi dani" ya fad'a yana y'ar shagwaba "y'ar Dariya Aira tayi ta ce " Zumah na kenan ko yunwa kakeji"Jujjuya kai yayi ya ce "Ummm amma bata abinci ba" jin hakan ya sanyata Jan bakinta tayi shiru"Bakice komai ba my cutie ya fad'a yana shafa lallausan hannunta dake d'auke da kunshi"turo baki tayi ta ce Uhm yaya Me zance to"sorry my babe ki taimakawa Yayanki mijinki kinji"yaya zafi fa."Daukarta yayi tare da Yin sama da ita ya ce "Wannan Karin bazakijiba Kad'an zan miki" bai direta ko ina ba sai kan bed lokacin nan ma Aira ta dansha azaba gogan naku ko abunki ga sabon shiga Shine bai kyaletaba sai 12 na rana Shima saida yaga ta dinga yimai ihu hakan yasa ya rabu da ita Da kanshi yayi mata wanka sannan sukayi wankan tsarki suka fito Aira sai turomai baki take ala dole yayi mata laifi shiko bawan Allan lallashi kawai yake yana bata hakuri saida suka koma ya k'ara gasata sosai tukwana suka fito shi ya shiryata cikin shalauliyar wata k'aramar Riga Ganin ana kiran salla ne ya sanyashi kallonta cikin marairaicewa ya ce "Cutie naje masallaci nayi salla ko nayi a gida" tana tutturo baki ta ce "Kaje am okay" Kama kunnenshi yayi ya ce "a'm sorry my love nayi laifi ko yi hakuri" kamar mai jira ta fashe da kukan shagwaba ta ce "Aishine kamun wayau kace bada yawa zakayiba yanzu haka zafi nakeji" Rungumota yayi ya ce "Sorry my prince's ayiwa Yaya hakuri bazai sakeba kinji my love " turo baki tayi ta ce "Uhm Uhm " Saukowa yayi tare dayin knell down ya kama kunnanshi ya ce "Sorry my cutie to ki zaneni indai zaki huce" Sosai hakan yabawa Aira Dariya saida tayi dariya sosai kafin ta mik'e ta ce "Kai my Zumah Inani ina dukanka wace ni na hakura ka maza kaje karka makara salla" Murmushi yayi mata tare da mik'ewa yayi hug d'inta tare da bata peck a kumatu ya ce "ki kulamun da kanki kafin na dawo" Nima ka kulamun da kanka my hero Allah ya tsare munkai a cikin tafiyarta da kuma dawowarka sannan banda kallon y'an mata ta fad'a tana aika mishi da Hararar wasa"Dariya yayi yana karajin soyayyar Matar tashi sosai yaji dadin addu'ar da ta masa ya ce "Ameen Matar aljanna sannan yayi dariya ya ce " Ina ni ina kallon y'an mata ina da wannan zuk'ek'iyar a gida ai kowace mace kallon namiji nake mata ke kad'aice nakeyiwa kallon mace my prince's zuciyar Arman takice ke kad'ai ko kin manta ne"Murmushi tayi tana jin dad'i sosai ta ce "Hakane my hero a dawo lfy" yana fita itama ta mik'e Bayan ta dauro alwala ta gabatar da tata Sallar Azahar din Bayan tagama tajima tana addua nemawa aurensu albarka tukwana ta mik'e tana d'an tafiya dak'yal palour ta nufa kai tsaye kitchen ta shiga tana shiga tayi dube dubenta bataga komai ba na girki Juyawa tayi ta fito palour daidai da shigowar Arman kallonta yayi ya ce "Me ya kaiki kitchen matas" k'arasowa Inda Yayi tayi ta ce girkine zan daura kuma nashiga naga ba komai"Kama hannunta yayi tare da zaunar da ita ya Ce "wai gidanwa kikatabaga amarya tayi girki amaryarma Ta musamman kamarke babyn Yayanta aike y'ar hutuce Dan haka karna k'ara ganinki a kitchen akwai kuku da mukayi magana dashi zaidinga zuwa yana girki daga mundawo daga honeymoon Hakan yasa ban Aje komai ba saboda order zamu dingayi " Marairaicewa tayi ta ce "Amma my...rufe mata baki yayi yace " Nasan kinajin yunwa ya fad'a tare da bude take away din da yayo musu Shi ya dinga Bata a baki saida ya kosar da ita tukwana itama tayi feeding dinshi suna gama Aira ta kwanta Saman cinyarshi ta mik'ar da kafarta kan kujera wayarshice da ya saka layinshi na k'asar ba jimawa yaji tayi ringing cikin Sauri ya duba yana ganin number Mummy ce Sai sannan ya tuno laifin da yayi mata tunda sukazo bai kirataba yace mata Sun isa lafiya cikin Sauri ya d'aga tare da cewa "Hello Mummynah" ba wani Mummy ni ba kai nakiraba y'ata na kira Naji lafiyarta nasan da ita take da waya ai bazata kwana biyu bata kiraniba Kodan Naji saukarku lafiya "sorry mummynmu nayi laifi ayiman afuwa wlh tunda nazo ban d'ora layin k'asar nan ba sai yanzu shysa kiyi hakuri kinji mummynmu bazamu sakeba" Murmushi Mummy tayi ta ce "Sarkin dad'in baki to yakukaje lafiya " Alhmdllh Mummy munga gyara da akayi mungode Allah ya saka da alkhairi ya k'ara girma"ameen kawai Mummy tace tare da cewa "Ina y'artawa fatan dai kana kulamun da ita" Dariya yayi tare da shafa sajenshi ya ce "Mummy y'arki gata nan ina kula miki ita kamar kwai " Masha Allah haka nakesonji bani ita mu gaisa"Aira da tana jinsu cikin Sauri ta amsa wayar cikin zazzak'ar muryarta ta ce "Hello mummynmu nayi kewarki" Daga bangaren Mummy tace "oyoyo y'ata nima nayi missing d'inki kin tafi kin barni da kewa To ya k'asar fatan dai kinajin dad'in gidan" Lafiya qalu Mummy Alhmdllh Ya su Murja"Lafiyansu qlau su Murja na barosu Chan nadawo kano suna cewa idan kinyi waya a basu numberki suna son. Ku gaisa"murmushi tayi ta ce "Allah srk ina Gaishesu Mungode Mummy Allah kara arziki da girma “murmushi tayi ta ce "amen d'an tashi kusa dashi muyi magana" Kallonshi Aira tayi da Shima ita yake kallo"Ganin yanda ya bata fuska ya bata Dariya tare da tashi tashiga Bedrom ta ce "Mummy na baro" yawwa y'ata abubuwan nan Dana baki kina amfani dasu kuwa?kasa kasa ta ce "Nadaiyi amfani da miskin Mummy sauran ne banfara amfani dasu ba" Ajiyar zuciya Mummy ta sauke Dan daman batason ta fara amfani dasu kafin ya santa anfiso daga baya cewa tayi"to shikenan daga yanzu ki fara amfani dasu kinji suna da amfani sosai musamman Kinga sanyin nan da yayiwa AL Umma yawa "kasa da kanta tayi ta ce " to Mummy insha Allahu"Allah miki albarka maida mashi wayar fitowa palour Aira tayi tare da Kallon Arman dake shshsan magani Kara mishi wayar a kunne tayi amsa yayi cikin shagwaba kamar wani yaro ya ce "Shine Mummy Dan ba Aso inji abunda zakuce shine zaki ce ta tashi yanzu fa naga duk wariya ake nunamun ''Ai sirrin y'a da uwa ne ba dole saikajiba sarkin y'an sa ido sai anjima Ka dai dinga kulamun da y'ata sannan kar a takurata " tana gama fad'ar haka ta kashe Kallon Aira Arman yayi ya ce "Baby gulmata kukayi ko" Dariya tayi tayi da mashi gwalo tace "sarkin wayau badai zakajiba Mikewa yayi zata Ruga kamu d'aya yayi ya chankofa tare da dorata kan kujera nan ya shiga kissing dinga ba kakkautawa Aira ganin Abu na neman wuce goma da iri ya sanyata fashewa da kuka dolenshi ya kyaleta sati guda sukayi suna zuba love d'insu a gida Arman tuni ya fara mayar da Aira yar hannu Dan yanzu hartafara sabawa dashi Dan ta lura mijin nata Yana da tsananin bukatuwa ita kuma a duniyar nan bataga abunda zata hana Arman ba ga kuma magungunan da take amfani dasu na wajen Ummy Wanda suke Kara rikitashi Satinsu guda suka fara fita outing cikin gari sosai Arman yake zagayawa da ita wajejen shakatawa love sukesha ta ban Mamaki yauma sanye suke sunyi ankon K'ananan kaya amma rigar ta Aira irin polo dinnance Shima irinta a jikin rigar tata an rubuta Quen shi kuma an rubuta Princess ta yafa black din mayafi a kanta tayi rolling d'inshi sosai tayi kyau a bakin ruwa suka zauna sunata shan love d'insu tare da wasanni ta Ruga ya bita sosai suka shagala suke nishad'i sunyi ciye ciye sosai su ice cream komai ya burgesu saya suke yayinda suka biya mai hoto ya dinga kashe musu hotuna Inda daga karshe ya durk'ursa Aira ta Dare bayanshi tana Dariya Kowa na wajen harkokinshi yake kunsan rayuwar turawa ba ruwan kowa da kowa Ganin da gaske Arman a goye zai tafi da ita ya sanyata Fara zillo cikin shagwaba ta ce "Honey please saukeni" Dariya yayi ya ce "Ai tunda kika hau keda sauka sai a mota" Rufe fuskarta Aira tayi tare da tutsata a bayanshi"Dariya yayi sosai ya ce "Ai kunyarki a nan wajen ta banzace ba 9ja bace nan kowa Rayuwarshi yake a haka har saida ya kaita mota tukwana ya direta dukda kowa Harkarshi yake amma saida suka burge wasu mutanen a wajen, Da dare tana jikinshi suna kallon hotunan da sukayi a wayar Arman sosai hotunan sukayi bala in kyau karewa hoton kallo Arman yayi ya ce " Ammadai na fara zama mijin tace wlh cutie da har na biyeki kika sanya wannan kayan kartan banza na ganemun surarki"Dariya Aira tayi ta ce "Yaya Ka manta kowa Rayuwarshi yake ba ruwan wani da wani" Harararta yayi ya ce "Kin manta a musulunce haramun ba maganar right ake ba" Jan bakinta Aira tayi shiru"janyota jikinshi yayi ya ce "Daga yau a gida kadai za a dingamun irin shigarnan cutie ki daina cewa Na barki ki sanya kinsan wani ganin ba komai nake iya hanaki ba saboda bansan b'acin ranki plc karki sake cewa zakisa kinji" tohm my prince's insha Allah bazan sakeba dazun ma naga kayan iri d'ayane kuma sunyi mana kyau shiyasa"Halshenshi ya sanya a Bayan kunnanta tare da Fara mata wani irin Abu marar fassarawa lokaci guda Aira itama ta kawo wuta Sosai sukayi ta abubuwansu a palour Inda daga karshe ya sungumeta sukayi bedroom d'insu". Washegari jirginsu ya d'aga Paris Dan fara yawon honey moon Tunda sukaje k'asar kullum saisun fita Dan a hotel suka sauka haka zasu fita suyi ta hotuna a gurare da snap Sosai suke zuba love ta ban AL ajabi Satinsu Biyu a Paris suka wuce England Chanma sosai k'asar tayiwa Aira dadi Dan kullum Chanma saisun fita sun shakata saida sukayi wata guda a England Dan Aira k'asar sosai tayi mata dadi daga Chan kai tsaye Dubai suka wuce Ai Aira zuwanta Dubai ji tayi kamar karsu koma Dan k'asar tayi mata bala in dadi a nan ma har tayi wata kawa Zainab balarabiya ce sunje shakatawa suka had'u har tab'ata numberta kasancewar Aira najin labarci hakan yasa sukayi saurin sabo Saida suka kwashe wata biyu a Dubai Wanda Allah keda kullum saisun fita Daga nan k'asa mai tsarki suka wuce Dan gudanar da Aikin Umrah Sosai Aira taji wani sanyi da annashuwa a ranta jinta a kasa mai tsarki saitaji ai Duka k'asashen da taje ba Inda yafiyi mata dadi kamar saudiya sosai ta Zage damtse ta dinga gudanar Da ibadodinta Da kuma addua a kan Allah ya daidaita tsakaninsu da mahaifanta Satinsu Biyu suka gama aikin Umrah lfy suka wuce London Gidansu suka sauka Wanda kullum sai anshiga a gyarashi a lokacin watansu biyar da Aure Bayan sun huta sunci abinci Lafewa Aira tayi jikin Arman Ta ce "umm baby wai yaushe zamu koma 9ja nasan Mamy ma yanzu fushi take dani" shafa cikinta yayi ya ce "Ba yanzu ba Honey sai Babynmu yayi kwari sannan saisun Kara hucewa" k'asa tayi da kanta Tare Goge hawayenta ta ce "Yaya banda komai fa har yanzu" K'ara shafa cikinta yayi ya ce "Nidai ban yarda ba Inajin kamar nayi ajiya a cikin nan"Dagowa tayi ta ce " Yaya serious yanzu haka perioud nake"na yarda my prince's insha Allahu soon munkusa zama iyaye"wayarshice tayi ringing dubawa yayi yaga mummy ce kiranshi video call kasancewar ya bar data bud'e d'auka yayi tare da Kallon mahaifiyartashi ta Cikin waya ya ce "mummynmu"Aira ma murmushi tayi ta ce " mummynmu ina yini"Cikin fara a Mummy ta ce ''lafiya qalau ya gajiya sarakan yawo kunje sai wahalarmun da jika kuke daga dai yanzu saiku nemu waje ku zauna"kallon juna Aira da Arman sukayi sai suka kalli Mummy kasa da kanta Aira tayi yayinda Arman ya ce "Mummy wani jikan kenan" cikin jikin daughter mana nasan k'ilama ya fara girma b'oyemun kawai kuke ko?A a a Mummy ai kinsan da tana da ciki kece zaki farajin wannan albishir din wlh bata da komai yanxu haka perioud take"Jikin Mummy ne yayi sanyi Dan duk daukarta tuni Aira ciki gareta har tafara sa ran Dan sosai ta matsu taga y'an jikokin nata murmushi tayi ta ce "To Allah ya kawo mai amfani" Ameen Arman yace yayinda Aira ta tashi tana Goge hawaye tayi bedroom da kallo Arman ya bita Nan suka cigaba da Hira Mummy Wanda hankalinshi Duka yana kan Aira saurin yiwa Mummy bankwana yayi tare da binta yana zuwa ya sameta ta hade kai da gwuiwa tana kuka subhanalla meye haka cutie me akayi miki kike kuka kin.manta ked'in amanace a wajena kukanki kamar yana nufin ban rik'e Amanar da aka bani ba ya k'arasa fad'a yana zuwa tare da rungumota "Cikin shashekar kuka ta ce " Yaya wata biyar Da Aurenmu amma har yanzu bansamu ciki ba nasan kaida Mummy Duka kunaso karfa naki haihuwa ka daina sona"Rufe mata baki yayi ya ce"Banyi tunanin haka daga bakinkiba cutie ko da haihuwa ko babu bazan tab'a daina sonki ba sannan haihuwa da kika sani ta Allah ce Duka yaushe mukayi Auren wata biyar nefa har zaki Fara mita sannan Nida Mummy Duka munasanki wa ya ce maki baki haihuuwa da zaki zauna kina kuka Cutie bantaba fushi dake ba Amma kika k'ara irin haka zanyi fushi ki maza ki Goge hawayen nan"Cikin Sauri ta Goge hawayenta tare da cewa "Sorry my hero bazan sakeba daga yau kayi hakuri please" gyada mata kai yayi ya ce "na hakura cutie na y'ar gatan Yayanta" murmushi tayi tare da Lafewa jikinshi tana jin dad'in daddad'an k'amshin turarenshi A haka bacci ya kwasheta Arman ya jima Rungume da ita yana Kara tunanin yarinta irin ta Aira wai kawai ta zauna ta dinga kuka sai kace wacce ta shekara goma bata samu haihuwa ba murmushi yayi tare da kwantar da ita a hankali ya ce "Allah ya shiryamun ke my cutie Gefenta ya kwanta yana kallon kyakyawar fuskarta mai cike da kwarjini da haiba wutar sonta na k'ara fisgarsa shafa fuskarta ya fara a hankali tare da Rungumeta yayi kissing d'inta a goshi a haka Shima bacci mai dad'i ya kwasheshi cike da gajiya Dan akwai gajiya sosai tattare dasu......✍🏿 *07026166536 domin magana da marubuciyar* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/15, 18:39] Hajo hajo: 🅿️.........*101&102* ......Sune basu tashi ba sai washegari karfe Tara Arman yayi farkon tashi Kallon Aira yayi dake baccinta hankali kwance kallon agogo yayi yaga Tara hada wani Abu cikin Sauri ya Mike yayi saurin fad'awa toilet Dan baisan har yakai hakaba batare da yayi salla ba Bayan ya gabatar da salla kallon Aira yayi yaga baccinta take har yanzu kin tadata yayi Dan yasan tana fashin salla kuma tana buk'atar Hutu palour ya fito Inda ya samu sabon kuku din da ya d'auka A palour ya tarar dashi Yana mopping har ya gama shara jinjina mashi da hannu Arman yayi shikuma baturen ya gaisheshi cikin girmamawa Bayan Arman ya amsa zaunawa yayi tare da komawa ya d'auko paper da biro ya rubuta duk wani kayan abincin da zasu buk'ata Mik'a mashi yayi ya ce "yaje ya sayo " Arman yana zaune harya dawo sosai ya shigo da jibga jibga kayan abinci Inda ya shiga sintiri dasu store din Gida har ya gama Kallonshi Arman yayi ya ce "Idan kazo da safe zaka gyara iya palourn kawai da kitchen iyanan zaka dinga gyarawa 6am ya kasance kazo ka gama sannan daka gama ta kitchen zaka dinga fita idan kana buk'atar wani Abu ka kirani a waya kawai basai ka shigo cikiba " Jinjina kai Yayi Alamun ya fahimta "Check din kudi sosai ARMAN ya rubutamai sannan ya yanke albashin da zai dinga biyanshi mai tsokar gaske daga lokacin nan kukun ya shiga kitchen ya fara aikinshi. Arman ko dayan bedroom d'in yakoma Bayan yayi wanka ya shirya d'akin da Aira take ya nufa Inda ya sameta ta fito daga wanka daure da towel jikinta hand drayer a hannunta tana busar da gashin kanta da ta wanke ta baya ya rungomata " Dan Kara Aira tayi Dan ta tsorata"Dariya Arman yayi ya ce "Sarkin tsoro nine fa" Cikin shagwaba ta ce "Shine ka tsoratani hero" Murmushi ya sakar mata ya ce "Sorry Prince's" amsar hand drayer din yayi tare da Fara yi mata "Dariya Aira tayi ta ce " Kai Zumah me ina ka iya gyaran gashi"yau xanfara akan matas kede kawai kisa ido kiyi kallo yarinya"murmushi Kawai Aira tayi suna kallon juna ta madubi shiya gyara mata kan nata yayi mata stretching ya shafa mata mayiyyuka masu k'amshi Bayan tayi mata Parking "Sosai yayi kyau sai kyalli gashinan yake ya dirar mata har gadon bayawow yaya Amma fa yayi kyau kamar naje saloon" Murmushi yayi ya ce "da kina wasa ne da mijin naki" jinjina mai hannu tayi ta ce "Thnks mijin da yafi na kowa" Peck a kumatu yayi mata ya ce "Nagode Matar da tafi ta kowa a duniya" Saida sukayi shiriritarsu nan ma tukwana ya rabu da ita ya fita palour ita kuma ta shirya Cikin doguwar rigar atamfarta green Street gown sosai ta matseta d'an a jiki D'aurin zarah buhari tayi Ita kanta data duba kanta madubi tasan tayi masifar kyau Turarruka masu k'amshi ta faffesa palour ta fito Inda ta samu Arman yana kallon ball Kallonta yayi tare da sakar mata smiles ya ce "Kinyi kyau My beautiful wife" Far da ido Aira tayi ta ce "Thnks my beautiful husband" ta fad'a tana k'arasa shigowa palour tare da zaunawa gefenshi ta zagaye hannunta a “yau shigar hausawa aka yimun kenan "Uhm hubby " Kinajin yunwa ko Prince's ya fad'a yana shafa kanta"Cikin shagwaba ta ce "Eh mana Baby " Sorry babyn Yaya muje tund'azu kuku ya gama breakfast banson na tashekime shysa"Kallonshi tayi da mamaki ta ce "Wai honey da gaske kuku ka d'auka Haba Darling meye amfanina a gidan kowace mace fa tayi Aure ita take girkama mijinta abinci meyasa bakasan na samu ladan wannan sannan nasan Mummy ma taji Bazataji dadi ba" kama hannunta yayi tare da mik'ewa suka nufi dinning ya ce "Bazakiganeba Cutie bazan juri ganinki kina wahala ba shysa Sannan lada kullum cikin samunta kike yanda kike kula dani kike jiyar dani dadi kadai ladan bata wasa bace ba saita girki bane kawai zaki samu lada akwai hanyoyin samun lada da yawa a Aure kuma girkin ma zaki samu ladar niyya tunda Kinga ninace na yafe Kinga kuwa ai kina da lada my prince's Mummy da kanta ta fara cewa Na d'aukar maki kuku"Uhm Yaya Amma dai Gaskiya ko ran Friday ne zan dingayi please karkace a a " To shikenan tunda kin ce Friday din saiki dingayi shikenan ko hankali ya kwanta"Murmushi tayi tana zama kujerar dining d'in Bud'e kulolin tayi k'amshi sai tashi yake serving d'insu tayi Inda ta zauna ta fara ci lumshe ido tayi Dan babu laifin abinci akwai dadi dukda ba irin namu bane"Kallonta Arman yayi ya ce "da dadi ko my prince's" yatsune fuska tayi ta ce "Uhm ba laifi amma da ni nayi da saitafi dadi" Dariya yayi ya ce "Ai daman inama za a hada abincin matas da wannan ai kinzarce wannan nesa ba kusa ba" washegari da Yamma suna zaune a palour suna kallo yayinda tana gefenshi tana shan tuffa Hakanan yau kawai ta tashi da tunanin Mamy kusan shekara kenan ba ta sanya mahaifiyarta a ido Dan tundaga aurenta da Alh Madugu rabonta da gida "wasu hawaye ne suka gangaro mata batare da ta sani ba "da mamaki Arman ya Kalleta ya Ce " Yadai me ya faru cutie "Cikin murya mai shirin fashewa da kuka ta ce " yaya Mamy"Ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka "Rungumeta yayi yana Lallashinta Ya ce " kiyi hakuri cutie komai zai daidaita insha Allahu kibar kukan nan kinsan bansan zubar hawayenki"yaya Kusan shekara fa rabona da Mamy nasan tana Chan kila cikin damuwa yaya Dan Allah kiramun ita a waya please "To yi shiru saina kira maki ita kinji" gyada mashi kai tayi tare da Goge hawayen mik'a mata wayar yayi Karba tayi tare da sanya number Mummy Cikin zumud'i ta danna mata kira cikin sa a kuwa taga ta shiga tana ringing Mummy ko tunda abunnan ya faru bata da zaman lafiya sosai hankalinta ya tashi akan Abunda akace Aira tayi kullum da bakincikin abun take kwana take tashi dukta rame yanzu haka bata da lafiya tana kwance Dan tunda abunnan ya faru yau lafiya gobe ciwo Danma Abba yana kula da ita bai nuna mata komai ba akan abunda y'arta tayi yauma tana kwance tana bacci taji ringing d'in wayar koda ta mik'e taga code din wata k'asa kuma ba na Niger ba bare tace y'an uwanta ne tayi mamaki sosai Tana shirin dagawa kiran ya katse Aira ko hawaye tayi ganin kiran ya katse Kallonshi tayi ta ce "Yaya bata dagaba"ki sake trying insha Allah zata d'aga " Sake kiran tayi cikin sa a kuwa ring d'aya aka daga wata nauyayyar Ajiyar zuciya ta sauke Wanda har saida Mamy taji daga waya Hello wake magana"Mamy ta fad'a "Sosai Aira taji nutsuwa jin muryar mahaifiyartata shashekar kuka ta fara ta kasa magana " Wai baza ayi magana ba"Mamy ta fad'a"Aira kasa magana tayi sai shashekar kuka "Mummy dukda taso ta gane ita ce ta ce " To idan baza ayi magana ba zan kashe ina da aikinyi"Cikin Sauri Aira ta ce "Mamy Aira ce" Aira Mamy ta maimaita cikin ranta dukda kewar y'ar tata da tayi hakan bai hanata fushi ba ta ce "Wace Airar" Airarki Mamy "ta fad'a tana cigaba da hawaye" tsaki Mamy taja ta ce "me kika kira na maki ai tunda kika zab'i namiji akanmu muma muka hakura dake Dan haka karki sake kirana " tana gama fad'ar haka ta katse kiran"Sosai Aira ta fashe da kuka tare da Fad'awa kan Arman ta ce "Na shiga ukku yaya shikenan Mamy Ma fushi take dani nasan k'ilama ita da Abba sun tsinemun yaya Ya zanyi da rayuwata"Sosai ta bashi tausayi Rungumeta yayi ya ce " Kiyi Hakuri Allah yana tare damu Insha Allahu babu wanda zai tsine maki cutie anringa an b'ata mu a wurinsune Wanda Goge hakan sai Allah insha Allahu nan gaba Gaskiya zata bayyana zasu yafe mana "cikin kuka ta ce " yaya sai yaushe Nifa Duka iyayena suke fushi dani ina tsoron hakkinsu yaya karya bibiyeni nasan ban kyautawa Mamy ba "daddabata ya fara ya ce " Insha Allah ba hakkin da zai bibiyemu cutie Allah da zuciya yake amfani kuma shi ya jarabcemu da son junanmu Wanda Bazamu iya rabuwa da junanmu ba Amma kina gani Iyayenmu saida sukayi yanda sukayi suka rabamu akan dalilinsu marar ma ana da tushe Sannan Abba da Daddy suma Allah zai fara kamawa da laifin yanke zumuncin da sukayi Bayan nasu suka hada da namu kin manta hadisin manzon Allah S a w da yake cewa "dukkan mai yanke zumunta bazai shiga aljanna ba " bana nufin iyayenmu bazasu shiga aljanna ba a a a ina nufin girman laifinsu yafi namu na farko dai Kinga ba zina muka aikata ba hasalima sharri akai mana"Sannan na biyu Aure da Mukayi ba haramun bane inbanda Lada da zamu samu saboda raya sunnar ma aiki da mukayi ko a mutuwar auren wancen ya isa ki gane Allah yana tare damu cutie sannan ki kwantar da hankalinki Mamy uwace bazata tab'a maki mugun bakiba Kinga kamar yanda Mummy tayi tsayin daka wajen ganin farincikinmu to hakan take ta bangaren Mamy itama uwace kuma har yanzu tana sonki kuma tanayimiki addu'ar alkhairi kisa wannan a ranki kinji my cutie ki kwantar da hankalinki "Shiru Aira tayi tana sauke ajiyar zuciya Tadanjin sauki a ranta nan yaci gaba da yi mata nasiha har ya samu ya mantar da ita damuwar da ta shiga. B'angaren Mamy kuwa sosai tayi kuka Bayan katse kiran Sosai Abun yake damunta ga kuma bakincikinta na bin namiji da Y'arta tayi kenanma barin k'asar sukayi tunda gashi da code din wata k'asa Suka kirata sosai Mamy ke kuka ta ce " ina ganin rayuwa ni Rahama Y'ata mace kenan a duniya ta kasa zama lfy ta kasa barinmu mu zauna lafiya Ta gurbata rayuwarta akan d'an namiji sosai take kuka Amer ne ya shigo cikin maganarsu ta y'an koyo ya ce "Mamy miya chameki" Shiru tayi mashi tana cigaba da hawaye "Shima kukan ya fara tare da rumgumeta washegari Mamy ta tashi da Rashin lafiyar koda sukaje Asibiti shaida musu akayi jinintane ya hau tana yawan tunani da sa damuwa a ranta saida aka kwantar da su na kwana biyu kafin a sallamesu. Kwana Ukku Aira tayi wanka Wanda ta fara salla daman Ka idar AL adartane kwana Ukku ko hud'u Daga ranar suka d'ora sabuwar rayuwarsu daga Inda suka tsaya batare da haufi ba soyayyar da Aira da Arman suke zubawa taban mamakice wacce zan iya cewa tsawon Rayuwata bantaba ga masoya masu k'aunar junansu irin haka ba ranar Friday tanayi Aira ita da kanta ta shiga kitchen ta girkama mijinta special food naban mamaki banda drinks da ta harhada da kanta Bayan taci gayunta cikin K'ananan kaya jiens da wando Sosai tayi wutar kyau Fitowa tayi a lokacin da yake shigowa Bayan yadawo daga masallacin Juma a wajenshi tayi tare da Rungumeta ta ce " highly wellcome my husband"Shafa kanta yayi ya ce "Thnks my Prince's" Kama hannunshi tayi ta ce "Muje ciki nasan ka kwaso gajiya a tare suka shiga ciki Ta taimaka mashi ya sake wanka Inda ya shirya cikin K'ananan kayan da sukayi mashi masifar kyau kai tsaye dining suka nufa tayi serving d'inshi tana murmushin ta Shima murmushin yak'e sakar mata na so da k'auna Spoon ta d'auka tare da zubo abincin takai saitin bakinshi tace ha a my honey" murmushi yayi ya d'aga bakin zuba masa tayi Arman koda ya tauna lumshe idanu yayi jin girkin da bai taba nin dad'in irinshiba da yana cewa duk duniya Mummy tafi kowa iya girki ashe Aira ma gwanace wajen girki"Ganin yanda yake lumshe ido yasanya Aira Dariya ta ce "Baby yadai mark nawa na samu" Jinjina mata hannu yayi ya ce "Ai mark d'inki ya wuce 100% saida trillion % Dariya sosai Aira tayi ta ce " a sa masa waigi"Dariya yayi ya ce "Serious fa Bantabajin girki mai dad'in wannan ba matas yayi dadi sosai yanda baki tunani kice yau dad'i biyu za Ajiyar dani gana girki gana bed ya fad'a yana kashe mata ido" Kashe mashi ido itama tayi ta ce "Yau kai din d'an gata ne Ai hero Har Arman ya gama cin abincin yana santi Da sanyawa Aira Albarka koda yasha drink dinma Shima sosai taji dad'inshi Aira ko sai dadi takeji yanda mijinta ke yabawa. A satin ne ya fara koya mata mota kullum fitarsu suke Inda ba kowa Sosai take ganewa Wanda cikin sati ukku Aira ta iya tuk'a mota inbanda in sunfitama a shiririta Rabi ake karewa shiyasanyama bata iya da wuri ba ranar ta karshe ita ta tukosu har gida Sai murna take ta iya driving Dan yana daga cikin abunda tafiso ta ganta tana driving Aira sosai takeson Arman yasaya mata waya amma tanajin nauyi Dan bazata iya rok'arshi Abu ba hakan yasa ta hakura koda yaushe cikin waya da video call suke da Mummy. Mummy duk yanda taso ta Ganar da mijin nata gsky abun ya gagara da ta ma d'auko masa maganar Arman yake dakatar da ita akwai lokacin da Kamar ya buge ta Sosai ya shiga mata bala I akan ta k'ara mashi zancen Arman ranta zaiyi mugun b'aci hakan yasa ta daina mashi Sosai Abun ke damunta d'an tama kasa samun y'ar damar da zatayi mashi bayanin abunda ke faruwa koda ta kira mahaifinta ta fad'a masa halin da ake ciki ce mata yayi karta sake mashi maganarsu ta rabu dasu akwai lokacin da yake so Akai Wanda shida kanshi zaizo ba yanzu ba sannan karta Fad'awa kowa maganar Aurensu Aira har yanzu taci gaba da rufewa. Bayan wata Ukku idan ka kalli Aira ta k'ara murjewa da kyau Ga wani fresh da take karawa ko ina na jikinta ya cicciko tayi gwanin sha awa Shi kanshi Arman ya lura da Yanda tayi kallonta yayi ya ce "Cutie Kinga kuwa Yanda kika koma baki tab'a kiba Irin haka ba" Far da ido tayi ta ce "Allah ko Honey" Shafa Hips d'inta yayi cikin wani irin salo ya ce "Serious har nanma jifa yanda suka ciko Gaskiya na iya kiwo" Dariya tayi ta ce "Allah ko hero" Eh mana Baby "Uhm Gaskiya ne ka iya kiwo nikuma Fa ban iya kiwo fa kenan kaima ai kayi kiba gashi na sanyamaka Haske kaima ka k'ara Haske"Nina isa nace Cutie bata iya kiwo ba Ai kecema kikafi kowa iya kiwo My Prince's Hh Haske nima ai na goga maki namu na Fulani Gashinan yanda kike k'ara haskawa kamar wata Daren goma sha hud'u" turo baki tayi ta ce "Uhm Amma dai nafi goga maka nau da yawa wayau ma kakemun ka had'a Haske biyu na kusa amshe abuna" Dariya yayi tare da sungumarta ya ce "ayi hakuri kar a amshe a barni na cigaba da dangwalar arziki. Sosai Arman yake lura da sauyi Daga gareta Yanzu Abu Kad'an zatayi tace ta gaji ga kwadayi da ta tarka kullum suna hanyar yawo sayayya ga bacci kamar kasa minti kadan sai bacci ya kwasheta shidai ARMAN baikawo komai a kanshi haka dai har wata guda yauma ta fito daga Bedrom d'insu Zuwa palour iskeshi tayi kan sopa yana kallo gefenshi ta zauna tare da d'ora kanta kafarashi ta ce " wash na gaji wlh kamar nayi wani aiki da yawa"Da mamaki ya Kalleta ya ce "Daga daki zuwa nan ne kika gaji ko wani aikin kikayi" girgiza mashi kai ta yi ta ce "ba abunda nayi y'ar tafiyar da nayi ce Na gaji wlh" galala yayi yana kallonta cike da damuwa ya ce "Cutie kodai Asibiti muke tafiya Nifa abunnan naki ya fara bani tsoro Kinga Inma wata chutar ce Saisu gani'turo baki tayi ta ce " um um naki Nida lafiyata qalau ba abunda ke damuna"Ba yanda baiyi da ita ba akan su tafi Asibiti takiya A haka baccima ya kwasheta a jikinshi"Kallonta ya tsayayi yana k'are mata kallo Sosai cike da damuwa Dan yana tsoron ace wani abun ne ya samu cutie d'inshi Dan baccin nan nata da kasala bana lafiya bane. Washegari Suna zaune kan Bed suna Video call da Mummy a laptop d'in Mummy Aira sai shagwaba take zuba mata akan taki zuwa ganinsu"Murmushi Mummy tayi ta ce "yi hakuri y'ar Mummy insha Allahu zanzo nan kusa" ihun murna Aira tayi ta ce "yeyeye Mummynah Allah ya kawomun ke lafiya wlh munyi missing d'inki sosai ko Yaya" ta fad'a tana kallon Arman dake gefenta "gyada mata kai yayi ya ce " eh Mummy munyi missing naki sosai "to Karku damu ina nan zuwa kusa " Bacci ne ya kwashe Aira batare da ta sani ba ta kwantar da kanta jikin Arman "Kallon Arman ta Cikin laptop Mummy tayi ta ce " son ya naga daughter tayi fresh ta k'ara k'iba da fari Jifa ana waya ta bige da bacci Anya baku b'oyemun wani Abu kuwa?cike da damuwa Arman ya ce "Wlh Mummy tayi wata hud'u ina Ganin haka tattare da ita ga bacci kamar kasa yanzu fa Rabin rayuwar a bacci takeyinta ga kasala komai tace ta gaji ni tsoroma nake Kar wata chutar ta shigarmun ita" cike da zak'uwa Mummy ta ce "wata hud'u fa kace Arman Tana zazzabi da ciwon kai ko amai?a a a Mummy batayin ko daya Saidai ciwon kan Shima ba Koda yaushe ba"yaushe rabonta da perioud" Tunani yayi sai yanxu ma ya kawo tunanin a ranshi kwata kwata cikin Sauri ya ce "Mummy ai takai wata Ukku ko fi batayi perioud ba" Salati Mummy tayi ta salamce ta ce "kudai anyi mashiririta Nifa ince Yarinyar nan Ciki ne da ita to ka maza ku shirya ku tafi Asibiti yanzu yanzu" ciki mummy"Arman ya fad'a da mamaki"Tabbas kuwa cikine da ita Ah Alhamdulilla ni Fatima burina ya cika Ka marmaza ku tafi Asibiti kuna dawowa ku kirani ku sanarmun wata nawane "Mummy tafada cike da farinciki tare da katse kiran hamdala kawai take tana godewa Allah Arman ko Sakato yayi yana tunani Tabbas shi gama zama soko wlh Sai yanzu shataf ya kawo a kanshi kodan ba sanin sign din masu ciki yayi ba cike da farinciki ya mike ya ce ''Alhamdulilla Allah na gode Maka kallonta yayi tare da shafa Fuskarta ya ce " Thnks you cutie Thnks you so much kingama yimun Komai a rayuwa sannan ya shafa Cikin tare da kissing d'in cikinta da ya d'an fara tasowa Sam shi baima lura da Hakan ba sai ya zaci ko k'iba ce ta sanyata fara tumbi ya ce "I love you so much My unborn Allah fitomun da ke\kai lafiya Farkawa Aira tayi taga Arman yana shafa cikinta Da mamaki take Kallonshi Shima kallonta yayi sai sakar mata murmushi yake " Juyamai idanu tayi ta ce "Yadai " murmushi ya sakar mata tare da mik'ar da ita ya ce 'Yau rana ce ta musamman a garemu cutie ina d'auke da Babban Albishir Wanda Ke ya kamata ki farayimun shi Amma ni zanyi maki "albishir kuma honey na me kenan" Sungumarta yayi tare da nufar toilet da ita ya ce "Wanda kika jima kina burin samu shi yayi mata wanka ita dai Kallonshi kawai take yanda yake wani sabon tattalinta da tarairayarta har mai shi ya shafa mata hatta kayan da zata sanya shiya fiddoata tare da sanya mata Bayan ya sanya mata hijab ya kama hannunta ya ce Muje my cutie" Muje ina Yaya"bai bata amsaba saboda ya fad'a mata Asibiti zasu yanzu zata kawo mashi kalula suna fita mita suka shiga ya yi motar key sukabar gidan kai tsaye wani had'adden clinic dake ba nesa dasu Suka nufa Bayan yayi parking a Farfajiyar asibitin Kallonshi tayi tare da marairaicewa ta ce "Darling me zamuyi a Asibiti kuma ?Murmushi ya sakar mata tare da kama hannunta ya ce " zaki gani my cutie yana gama fad'ar haka ya fita tare da bude mata itama ta fito kai tsaye cikin clinic din suka nufa babu wani layi hakan yasa suna shiga suka samu ganawa da likitan Bayan sun gaisa da Arman Cikin harshen Turanci yayi mashi bayanin abunda ke damunta "Itadai Aira na jinsu tayi jugum " wata nurse ya kira Tare da had'ata Da Aira yayi mata bayanin irin awon da za a mata ba jimawa Aira tadawo ta zauna Bayan an gama d'aukar abunda za a d'auka ba ayi 20 minute ba Nurse din ta dawo tare da mik'awa Dr result d'in karantawa Dr yayi da murmushi a fuskarshi ya kalli Arman tare da mik'a mashi Hannu sukayi musabaha ya ce "Congratulation your wife she's pregnant for 4months one week...✍🏿 *Ni da Yaya Arman na kudine akan 200 kachal katin mtn ta wannan number 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/16, 21:47] Hajo hajo: 🅿️........*103&104* .....4months One week "cike da farinciki Arman ya Mike Aira bata gama mamakinta ba Taji an d'auketa anyi sama da ita juyata sosai Arman yayi tare da Rungumeta ya ce " Alhamdulilla My cutie kingamayimun komai a rayuwa Allah ya saukeki lafiya ya k'arasa fad'a yana kissing din wuyanta "Da mamaki Aira ta ce "Yaya kana nufin wai ciki ne dani" Eh mana cutie ai shine albishir din da zanyi maki ai yau ranace ta musamman a garemu dole ne na fara baki k'aramun tukuici Babban kuwa Sai my unborn ya fito"ya fad'a yana shafa cikinta"Alhamdulilla Aira ta fad'a Sosai itama ta shiga farinciki marar musaltuwa shidai Dr Dariya yayi musu Dan sosai love d'insu ta burgesu Shi kanshi Dr d'in saida ya shaida Dan Arman barin kudi yayi mashi Ranar saida yabi Duka marassa lafiyan asibitin yayi musu Alheri Na nuna godiyarshi ga ubangiji "(Haka ake so idan abun alkhairi ya samu mutum ya godewa Allah Sannan yayi alkhairi Bawai kida da sauransu ba Allah sa mu dace)Koda sukabar asibitin basu zarce ko ina ba sai wani katafaran shagon sayar da waya IPhone 14 ya saya mata a kwali savuwa dal wacce ko wata batayi da fitowa ba A mota ya sameta Bayan yashiga Kallonta yayi tare da mik'a mata kwalin ya ce " ga tukuicinki my cutie na rasa dame zan saka maki bani da abunda zan saka maki a duniya Saidai nace Allah ya Barmu tare har Abada"Murmushi Aira ta sakar masa ta ce "Nima bani da abunda nake dashi da zan saka maka mijina kaid'in haske ne a cikin rayuwata Bud'e wayar tayi Zaro ido tayi ganin wayar da Batayi tsammaniba Ai batasan sanda ta Rungumeshi saida tayi hawayen farinciki ta ce " Thnks Thnks you so much My hero Allah ya k'ara budi da arziki mai amfani "Shittt Arman ya fad'a yana rufe mata baki ya ce " banason Godiya cutie kin chnachanci fiye da haka wannan bakomai bane "Sosai Aira tayi farinciki sai zumudi take sim din d'aya saya na k'asar ya sanya mata a wayar Koda sukabar wajen joint suka wuce Inda Arman ya sanya Aira ta zaba abunda ranta yakeso saida suka cika cikinsu tukwana suka dawo gida Suna isowa ana magriba Bayan sunyi sallah a palour Cikin zumud'i Aira ta fiddo wayar Ta ce " yaya sanyamun number su mummy"murmushi yayi tare da Amsar wayar ya sanya mata number su mummy da Murja da su Hasina Bayan nan ya shiga ya d'auko mata apps da abubuwa masu amfani what's app kawai ya d'aukar mata danshi kadai yakeson tayi yana cikin saita mata Mummy ta kira cikin zumud'i ya d'auka ya ce "Mummy albishirinki" Goro "Mummy ta fad'a cike da zak'uwa" An dace Arman ya fad'a tana Dariya"Itama dariyar Mummy tayi ta ce "Kai Alhmdllh son kace an dace wata nawa kuma?Dariya sosai Arman yayi yana mamakin yanda Mummy ke biye musu ya ce " Mummy 4months hada sati d'aya"Alhamdulilla Ai yau da ina da hanci da nayi gud'a kai Allah mungode maka Mummy tafada tare da cewa "bani y'artawa " Aira na jinsu duk sai kunya ta kamata a kunyace ta amshi wayar 'Sosai Aira tayi mamakin yanda Mummy ta shiga sanya mata Albarka da jera mata adduo i ita duk kunyama ta kamata Daga karshe Mummy ta ce "Yanzu bake kadai bace daughter ki k'ara kula da kanki Da abunda zaki dinga ci sannan karki Kara shan ruwan sanyi ki yawaita shan fruit,Zuma,Dabino da dai sauran kayan lambu sannan banda wasa da ciki karki zauna da yunwa kinji Daugher na" murmushi Aira tayi cikin jin kunya ta ce "To Mummy insha Allahu" Baki buk'atar komai?Eh Mummy "idan kina buk'ata ki fad'amun " murmushi aira tayi ta ce "Bakomai Mummy" masha Allah to Allah ya raba lafiya ya baki lafiya "Amen Aira ta fad'a kasa kasa tare da mik'awa Arman wayar nan suka shiga tsara abubuwa shida Mummy itadai tana jinsu tana mamakin yanda suke k'aunar cikin tun baizo duniya ba ". Ranar Aira ta kira Su Murja Inda suka shiga yi mata tsiya Abunka ga sun saba itama Aira ta biyesu Sosai taji dad'in yanda suka sha waya Inda daga karshe sukace saisun hade a what's app nan suka turo mata number Maryam Dan tayi mata barka ta haifi baby boy d'inta kiranta tayi ta mata barka nanma sunsha waya sosai Inda Har Maryam ta ce Zata bada numberta a sanyata wani grp na karuwa hakan ko yayiwa Aira dad'i Dan koda akasakata taga grp din Akwai karuwa sosai musamman akan zamantakewar Aure Ganin yanda ta shagala ya sanya Arman amshe wayar tare kasheta Kallonshi tayi ta ce " Honey..."Janyota jikinta yayi ya ce "Wayar nan naga alamar Kade maki hankali take nemanyi Bayan mijinki na bukatarki" Cikin shagwaba ta ce "Uhm honey Ammafa kasan babynmu zai wahalta ko kaida ba saurarawa kakeba" Dariya yayi tare da Fara Aika mata sakwanni ya ce "nak'i wayan ai babyna yanason jin d'umin Daddynshi Zai k'ara kwari bata karacewa komai ba Dan itama tuni ta fara kawo wuta Daga nan labari ya sauya salo suka Lula wata duniyar. Kulawa ta musamman Arman yake bawa Aira da cikinta taban mamaki saika rantse ba a tab'a haihuwa ba a duniya a kansu za a fara ga Mummy data daure musu kullum itama cikin kira take jin lafiyar Aira Ita kanta Aira abun har mamaki yake bata Dan ta zama wata y'ar gata ta musamman Tarairaiya kuwa ba a magana Dan Arman Ko nan Danan saiyace bazata taka ba sai dai ya d'auketa saida sukaje Asibiti ne ma awo dr yake cewa Hutu yayi mata yawa ta dinga exercises tukwana aka d'an samun saukin yake barinta tafiya da kanta cikin Aira ya shiga wata shidda Inda Yayi girma kamar Lokacin haihuwar ne A lokacin kuma wani kwadayi ne take na ban mamaki " yau ta tashi da son Cin d'an wake hada hawayenta ta kalleshi ta ce "Honey d'an wake nakesonci wlh" Cikin Sauri ya Mike ya ce "Karki damu Prince's sorry bani minti biyu " Mummy ya kira ya ce "Mummy Dan Allah ya ake d'an wake please koyamun cutie ce Ke son ci " Dariya Mummy tayi ta ce "Aifa abun nema ya samu Abu yazo ga ma iya" Sosa kai Arman yayi ya ce "Uhm Mummy ke nake jira" Cikin kankanin lokaci ta koya mashi Katse kiran yayi tare da nufar kitchen yaje ya fara hada d'an waken fulawa Mummy ko Aira ta kira Video call Bayan ta daga kallonta tayi cikin so da k'auna ta ce "Sannu daughter ya jikin naki normal ne dai ko har yanzu"murmushi Aira tayi ta ce "Lafiya Qalau Mummy Saidai Nauyi da nakeji sosai da motsi yayi yawa Kuma banajin dad'in hakan" ta fad'a cikin shagwaba "cike da kulawa Mummy ta ce " Sorry daugher Ai sai hakuri indai ciki ya fara girma Kidage da addua safe yamma dare karki sake da adduo I kinji sannan zanturama son adduoin da zai dinga tofa maki kinasha Insha Allah za a rabu lafiya Ga cikin naki naga yayi girma kamar mai yara biyu a ciki anyi scanning kuwa? Insha Allahu Mummy A a a ba ayi scanning ba ya hana ya ce Wai yafison Muga koma meye a surprise kuma Dr dinma yace ayi "girgiza kai Mummy tayi ta ce " Rabu dashi Allah saukeki lafiya Ai naso zuwa wlh hidimar Siyasa data taso ta hanamu zaune da tsaye Kinsan saura wata biyu zab'e to ko nace zanbar k'asar Daddynku bazai bari ba Har sai munga wucewar zabe lafiya insha Allahu ana gama zabe zan taho"Murmushi Aira tayi ta ce "Bakomai Mummy Allah yasa ayi zaben cikin nasara ya bawa Daddy nasarar komawa next level Insha Allahu" Ameeen ameeen Mummy tafada ta ce "Sai anjima ki kulamun da kanki" Murmushi kawai Aira tayi a haka ARMAN yadawo ya isketa tare da plate din Dan wake a hannunshi "sorry dia Sannu ko" Aira ta fad'a zaunawa yayi yana shafce zufa ya ce "ywwa my prince's Angama ci kawai ya rage" Amsa tayi tare da bud'ewa Masha Allah danwake yasha mai da yaji da Yanke yanke Shi da kanshi ya chakuda mata tare da Fara bata tanaci sosai taji dad'inshi Kallon Arman tayi tare da "Jinjina mai hannu Alamun good" Murmushi yayi ya ce "Thnks wiffey yayi dadi kenan?Uhm ai in ana salla ba a magana Honey Girkinka na musamman ne bantaba cin girki mai dad'in haka ba ta fad'a Dan yaji dadi " sosai yaji dadin yanda take yaba masa koda ya dandana yasan Dad'in bai kai chanba kawai tana fadane Dan ta faranta masa Wanda hakan sosai ya karajin kaunarta na k'ara shiga Ransa Shidai Ana cewa mutum Tara yake bai cika Goma ba Amma ya kasa gano Inda aibun d'ayan na Aira yake kodan kyawawan halayyarta sunyi yawa koma dakwai dayan ba za a tab'a ganewa ba. Sosai suka shiga sayayyar kayayyakin jarirai gadaje,kayan wasan yara,kekunan koyan zama,keken kwantar da yara da,Abun goya Yara a ciki,Keken tura yara,Kayayyakin sawa na ban AL ajabi a Gaskiya sayayyar da suke gaban mamaki ce saikace ba a San darajar kudi ba komai saya ake daki guda an cikashi da kayayyaki kayan sanyawa jariraine kawai basu saya da yawaba kuma komai da suka saya bibbiyune saboda Dr ya shaida twins ne a cikinta Kayan sanyawa na jarirai Guda bibbiyu suka saya Masu masifar kyau da tsada bangaren Mummy ma sosai take sayayyarta. Masha Allah anyi zabe cikin nasara Inda Daddy Ya koma Kujerarshi ta gwamna a yanzu hankali ya kwanta Mummy kuma yanzu Hankalinta ya tafi Wajen Yaranta So take.taje ta samu ganinsu. Cikin Aira Ya shiga watan haihuwa Sosai Arman ya linka kulawar da yake mata fiye da Ga wani irin girma da cikin yayi Dak'yal take tashi take zama yauma tana zaune Dak'yal ta yunkura zata mik'e ARMAN ya yi saurin tareta tare da mik'ar da ita ya ce "Sannu mummyn twins wlh tausayi kike bani Allah ya saukeki lafiya" Murmushin K'arfin hali Aira tayi tare da cije lebe ta ce "Ameen honey Allah harna k'agara na rabu da Cikin nan karkaga yanda nakeji" Shafa cikin yayi ya ce "Dan bakisan yanda nakejiba a raina cutie ji nake daman Wahalar ta dawo kaina Dan babu yanda zanyi ne nake ganinki cikin wannan halin kici gaba da hakuri da daurewa ankusa rabuwa insha Allahu" Gyada mishi kai tayi ta ce "Bacci nakeji muje ciki" Shiya kamata Dan bazai iya daukartaba tana rik'e da k'ugu suka shiga ciki Suna zuwa ta kwanta Gado Sosai take d'anjin sauyi a tattare da ita amma batason tayarwa da habibyn nata hankali hakan yasa ta yin shiru Dan abun bai matsa mata ba Sosai ba tana daijin bayanta na sarawa Koda ta kwanta Arman toilet ya shiga tare da Dauro alwala Inda ya shiga jera salloli Akan Allah ya sauke cutie d'inshi lafiya Aira ko bacci ne ya kwasheta Chan wajen Ukkun dare taji ciwon na k'ara yawa koda ta bud'e idonta ta ganta jikin Arman Yana bacci cije baki tayi tare da daurewa ta fara adduo I a haka dai har taji kuma abun ya lafa tukwana bacci ya sake daukarta Chan wajen Asuba taji Abu ya dawo sabo Wanda ya linka na d'azu "wayyo Allah na ciki na " ta fad'a yana rik'e kugu "Cikin kid'imewa Arman ya Mike Dan daman baccin baiyi nisaba cikin tashin hankali ya ce " me ya faru cutie "Cikinta ta nunamai tana yarfe hannu Tace " yaya cikina bayana kamar zai balle ta fad'a tana hawaye "Subhanallahi Sannu dia bari mu tafi Asibiti cikin Sauri ya lalubo Wayarshi ya kira Mummy ringing biyu ta daga Dan ta tashi Sallar asuba cikin kid'imewa ya ce " Mummy Aira ce ba lafiya Kingantanan cikinta da bayanta ke ciwo sai kuka take"Ku maza ku tafi Asibiti nak'udarce ku marmaza ganinan tahowa k'asar nima yanzu yanzu"Cikin rud'u Arman ya sanyawa Aira hijab da ta fara hada gumi ya sungumeta Sai mota koda suka isa asibitin har gari ya fara wayewa Labour room aka wuce da ita duk yanda Arman yaso shiga hanashi nurse sukayi zaunawa yayi ya rafka tagumi tare da Fara jera mata adduo I Mummy ko Cikin Sauri ta shirya kayanta akwati Lek'a Daddy tayi ta da mamaki ya Kalleta ya ce Ina zuwa da asubar nan "wata karyace tazo mata ta ce " Wlh habiby yanzu aka kira kanin mahaifinmu dake Yola ya rasu za ayi sutura karfe Tara shiyasa na maza na shirya "Subhanalla Allah ya jikansa Aida kin bari mun tafi tare " a a a dia Basaikajeba na wakilceka ai Sunsan yanayin da kake ciki na gajiyar siyasa "To shikenan Allah jikansa sannan ya mik'a mata check din kudi akan takai sadaka cikin Sauri Mummy tabar gidan duk ta rude koda ta isa airport ba jirgin da zaije London jirgin Lagos tahau Inda tana isa ta samu jirgi mai zuwa London cikin k'ank'anin lokaci ta gama clearing d'in komai jirginsu ya d'aga. Aira sosai take shan azabar da tunda uwarda ta haifeta bata tab'a shan irinta ba Cije baki kawai take tana Salati Tana kiran sunan duk Wanda yazo bakinta gashi likitoci sun duba sunga Haihuwar da saura sosai take Abu d'aya har Mummy ta Iso wajen 1 na rana Aira na Abu d'aya Koda Mummy tazo cikin k'arfin hali Arman yayi mata kwatancen asibitin a waya Tana shigowa cikin rud'u ta ce " Ina take "Arman kamar zaiyi kuka ya ce " Mummy tana ciki tund'azu taki haihuwa"Bata saurareshiba Mummy tayi cikin labour room d'in Inda ta sameta sai yarfewa take Wajenta Mummy ta nufa cike da tausayawa Dan daman tasan yanda Aira batayi laulayin cikiba zata iyashan wahala wajen haihuwa sosai ta tausaya mata Sannu ta shiga jera mata Aira bama tasan da wanzuwarta ba cewa ta ke "Zan mutu yaya kazo ka taimakeni yaya Airanka Ce fa Gashinan ina ganin mutuwa daman haka Zafin d'aukar rai yake bansaniba wayyo ni Aira Mamy ki yafemun na tuba Abba ka yafemun zanmutu yaya Arman kazo"Saida Mummy tayi hawaye kamata tayi ta ce " bazaki mutuba haka kowa yakeji ki daure kinji y'ata"Arman jin Haka bai saurari kowa ba ya Banko k'ofar Tare da zuwa ya Rungumeta Saikuma ya sanya kuka "Ikon Allah Kowa ke fad'a itadai Mummy tana mamakin yanda Arman akan Aira Duka jarumatarshi ta tafi Ada d'an nata ko hawayen shi baka isa ka ganiba" Tasoshi Mummy tayi ta ce "Haba son meye haka ka fita mana zata sauke lafiya insha Allahu" Cikin hawaye ya ce "Mummy bakiga yanda take shan wahala Mummy ba yanda za ayi cutie na sai shan wuya take" Airako jin Arman Sosai ta karawa rakinta volume Ta ce "Yaya karka tafi kaikadai ke sona mutuwa sukeso inyi Yaya Ka taimakeni Cikina" Kama hannunta yayi tare da durk'ushewa ya ce "Zaki sauka lafiya cutie kinji kiyi hakuri ki daure " Dak'yal Aka samu Arman ya fita Inda ya tafi masallaci ya shiga jera Adduo I Aira tana nan tana Abu har magriba Har ana shirin mata Aiki Mummy dukta fita hayyacinta Dan ta tsorata da wuyar da takesha ana shirin Tafiya da ita d'akin theatre ta haifo y'arta Kyakyawa Fara Sol "Hamdala kowa yayi musamman Mummy Bayan nan nakuda ta dawo sabuwa Inda Bayan Mintuna baifi goma ba ta k'ara haifo wata d'iyar itama fara Sol kamarsu d'aya da d'ayar rai da rai ba banbanci Nauyayyar Ajiyar zuciya Aira ta sauke Sai yanzu tajita ta dawo mutum Mummy ko hamdala tayi tare da godewa Allah Bayan anshirya yaran an sanya musu kayansu iri d'aya mik'o wa Mummy su akayi sosai Take farinciki ta ce " Alhamdulilla Allah na gode Maka wai yau nice rik'e da d’iyan Arman shida Aira Allah mai iko"Aira ko Bayan Angama shirayata Aka ajeta gadon hutawa Kallon Mummy tayi da take Ta murmushi tare da Yaran A hannunta Kallon nurse din tayi ta ce "Meye na Haifa Dr " Murmushi tayi ta ce mata "Twins Mata " Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da Yin hamdala Mummy ce ta mik'e tare da Yaran ta ajesu Gefenta ta ce "Daugher Kinga Abunda kika Haifa Ikon Allah kenan Twins lokaci guda kuma Duka mata masu zafin rabo " Kallon Yaran Aira tayi sosai taji wata irin soyayyarsu ta mussaman na shigarta dukda jariraine daka kallesu sak kaga ARMAN Saidai haskensu irin na Aira amma rai da rai Arman ne "Rungumesu tayi batasan lokacin da wasu hawayen farinciki suka zuba mata ba wai yau ita ce Da Yara yaranma har biyu lokaci guda kuma ita da masoyinta Arman suka haifesu Goge hawayenta tayi ta yi a hankali ta ce " Alhamdulilla Allah abun Godiya Allah ya raya munku bisa sunnar ma aiki"Ameeeen Mummy ta fad'a tare da daukarsu ta ce "Son baisan kin haihu ba bari naje na masa albishir Murmushi kawai Aira tayi tana karajin soyayyar Mummy koda ta fita Mummy da Yaran a hannunta daidai lokacin da Arman ya shigo harabar asibitin dawowarshi kenan daga masallaci cikin Sauri ya karaso Inda Mummy take da sai fara a takemai cikin zumudi ya ce " Mummy ta haihu?Mik'a mashi ta farkon Mummy tayi ta ce "Ta haihu congratulations son An samu twins duka mata kagansunan a hannuna.........✍🏿 *Ni da Yaya Arman nakudine akan naira #200 kachal ki biya ki karanta cikin kwanciyar hankali da nustuwa 07026166536* *_Miss Hajo ce_*🤙🏿 [7/17, 11:09] Hajo hajo: 🅿️.........*105&106* ...Ka gansu nan a hannuna "Cike da farinciki Arman ya ce " Alhamdulilla Mummy kina nufin Duka yaran nan nawa ne"Lakutar kumatunshi tayi ta ce "nakane son halak malak" mik'a mata d'ayar yayi tare da sujjudul shukur Yajima yana Godiya da yabo ga ubangiji itadai Mummy murmushi yaki barin fuskarta yana Dagowa Amsar d'ayar yayi ya ce "Allahu Akhbar Mummy kamata sukayo sak" Wlhko naga Duka Kaine ni harna rikice ma Bana banbancesu Inbanda naga ta farkon tafi K'aramar girma ta haka kawai na bambance su"Hawayen farinciki suka zuboma Arman amsar d'ayar yayi tare da rungumesu gabaki d'aya ya ce "Allah yayi muku albarka yarana" cikin Sauri ya ce Mummy ina cutie tana lafiya"lafiyanta qalau muje ka ganta Mummy tafada suna shiga Inda suka tarar da Aira kwance Tana hawayen farinciki cikin Sauri Arman ya nufi gadon tare da rungume ta tare da Yaran ya ce "Thnks You so much My cutie kin gama yimun komai a rayuwa kinbani abubuwan da bazan tab'a mantawaba dasuba ked'in haskece cikin rayuwata Allah yayi miki albarka ya baki lafiya" murmushi Aira tayi tana Goge hawayenta ta ce "Ameen hero" zaunawa yayi tare da kafe yaran da idanu Inda ya shiga musu Adduo i sosai yakejin k'aunar yaran na shigarsa ta musamman Bayan yayi musu addua jin sun fara kuka ya sanyashi kallon Mummy ya ce "Ba abunda za a basu Mummy " Zamzam ta ciro tare da Dabino mai laushin nan irin na makka ta mik'a masa tace tauna musu Kad'an ka basu saika basu ruwa daga nan zaka iya musu hud'uba "hakan yayi Bayan nan yayi musu hud'ubar kiran salla Kamar yanda manzon Allah ya koyar tukwana ya rad’a musu suna Dagowa yayi ya kalli Mummy tare da Yin murmushi " Kallonshi tayi ta ce "Me ka sanya musu" Mik'a mata Hasanar yayi ya ce "ga takwararki Fatima zahra d'ayar kuma Rahama"Cike da farinciki Mummy ta amsa ta ce " masha Allah Allah ubangiji ya raya manasu sosai Aira taji dad'in sunan da ya sanyawa yaran sunan mahaifiyarshi da nata Hakan ya mata dadi sosai nurse dinne suka bukaci da Akai Aira d'akin Hutu Dan yanda tasha wahala saita huta sosai haka ko akayi ita kadai aka bari ba b'ata lokaci bacci ya d'auketa Arman da Mummy suna waje sai liliyar yaran suke Dan yanzu sunyi shiru Har sha biyun Dare sunanan dak'yal Mummy ta lallaba Arman ya koma gida Bayan ya sayowa Aira abubuwan da zataci su Kaza fresh milk fruit Da sauransu Baiso ba ya koma Dan bayason abunda zaiyi nesa da yaranshi da yakejin kaunarsu ta musamman Mummy dakinda aka kwantar da Aira ta nufa da Yaran har lokacin Bacci take ga yaran sunfara kuka Alamun sunajin yunwa Haka nan tayi ta jijjigasu Inda Hasanar ta rude da kuka Wanda kukan ya tashi Aira har cikin Ranta takejin kukan yaran ganin ta tashi ya sanya Mummy saurin zuwa tare mik'a mata ita ta ce "Kinga tund'azu ita tafi rigimar" Amsarta Aira tayi tare da Fara jijjigata tad’an lafa da kukan Amma bata dainaba Alamun yunwa takeji sanyata Mummy tayi ta fito da Mamanta ta sanya mata a baki dukda kunyar da Aira takeji Amma me babu ruwa "Cikin Sauri Mummy ta hadawa Aira tea mai kaurin gaske Mik'a mata tayi Tasha Bayan nan ta zuba mata Farfesun naman da Arman ya sayo Shima tadanci sosai Fresh milk da Malta Mummy ta k'ara had'a mata marairaicewa tayi ta ce " Mummy wlh na k'oshi" a a a Aira daurewa zakiyi kisha Dan asamu abincin yaran nan yazo Kinga sai kuka suke ki daure jin Haka ya sanya Aira saurin shanyewa "yawwa to Mummy tafada tare da cewa " to gwada bata insha Allahu ruwan zaizo yanzu"cike da jin kunya Ta Kara gwadawa Tana sanya mata taji yazo ta kama ta fara tsotsa Sosai Aira taji wani irin zafi d'an k'ara tayi tare da saurin fusgewa "Tana hawaye ta ce " Mummy zafi"Matsawa kusa da ita Mummy tayi ta ce "Daurewa zakiyi ko so kike kibar yaranki na kukan yunwa Daga yanzu bazaki sakejiba " Jin haka ya sanya Aira mayar ma da Hasana taci gaba da sha Dukda zafin da takeji haka ta daure gashi yarinyar da ancire zata hau kuka tafi minti ashirin tana tsotsa Ganin d’ayarma ta fara kuka ya sanya Mummy saurin karbeta ta ce "ba d'ayar itama Amsarta tayi itama ta fara bata tanajin tana tsotsa tayi shiru Babbar ko kuka ta fara Jijjigata Mummy tafara ta ce " Haba takwara karfa kiyi Rashin hakuri Kinji "Sosai Mummy ta shiga jijjigata Inda ta samu har bacci ya d'auketa itama d'ayar tana cikinsha bacci ya d'auketa kwantar dasu kan gadon tayi itakuma Aira ta koma gefen karshen gadon ta kwanta. Washegari safko Arman ya buga musu a lokacin Aira sunfito Daga wanka Wanda mummy ta gargasata doguwar riga ta sanya tare da zaunawa kan kujera Lokacin shigowa yayi tare da kayan break fast d'aya shirya Bayan ya zauna Kallon Aira yayi ya ce " Sannu cutie ya jikin naki"Murmushi Aira tayi ta ce "Alhamdulilla" Mummy ina kwana "Lafiya qalau son ta fad'a tana d'aukar Rahama da ta tashi don yi mata wanka Plask din d'aya shigo dashi ya Tsiyaya ruwan tea din tare da sanya madara millo da bounvita a ciki sosai yayi kauri mik'a mata yayi ya ce " Amshi maman twins kisha"Wara idanu tayi kasa kasa ta ce "Uhm harna tashi daga cutie na koma maman twins kenan" Dariya yayi ya ce "Ai Duka sunankine my cutie " Amsa tayi tare da Fara kurba a hankali Inda take hadawa da wainar kwan da ya kawo kallon Mummy yayi da take yiwa Rahama wanka yace "Sannu Mummy ga break fast d'innan a hada maki ko saikin gama" Bari dai na gama tafada tana Tsaneta a towel Dan ta gama mata "Gado taje ta kwantar da ita tare da zaunawa kan chairs din dake d'akin Arman ya had'a mata tea din itama da wainar kwai tana cikin break fast Zarah ta kwala Kuka da duk saida suka Kalleta Cikin Sauri Arman ya d'auketa tare da Fara jijjigata ya ce "Mummy ko bata lafiya?Lafiyanta qalau wlh inajindai takwarar tawa zatayi kukan banza bata ta bata Tasha " sorry my Mummy karkiyi Rashin hakuri Kinji takwararki hakuri gareta ki taimaka "Arman ya fad'a yana kallonta " Duk Dariya sukayi har Aira data kusa kwarewa ta ce "Yaya kamar irin tanajin naka nan ko" Kallonta yayi da murmushi a fuskarsa ya ce "tanaji mana ai tasan daddynta tama Cemun bazata sakeba " Girgiza kai Mummy tayi tare da amsarta ta dorawa Aira kan cinyarta ta ce "Karki biyema mashiririncinnan Bata Tasha " Amsarta Aira tayi tare fara feeding d'inta Arman ko d'aukar Rahama yayi yana kallonta tare da Fara mata wasa Kallon Mummy yayi ya ce "Wai Mummy baza a sanya Musu Nick name ba" ku zan tambaya ai me kuka zaba musu"Kallon Aira yayi ya ce "Cutie wannan zab'inkine wani suna kike tunanin za a dinga kiransu dashi? Yaya duk sunan da yayi muku nima yayimun ku zaba kawai " Mummy ce ta ce "a a a baza ayi haka ba ke zaki zabawa yaranki ne Ai tunda yayi na farkon ke kuma saiki zab'i sunan da yayi maki ko zuwa kafin suna ne Kinga sai a sanya" Kasa tayi da kanta ta ce "To Mummy " Bayan tagama bata itama Amsarta Mummy tayi itama Bayan tayi mata wanka ta shiryata Nan Arman ya shiga yiwa yaran nashi hotuna masu kyau a waya ranar aka sallamesu Bayan sun koma gida Nan Mummy ta shiga kiran y'an uwa tana shaida musu haihuwar tare da tura hoton yaran groups d'insu na y'an gida kowa sai Farinciki yake Sosai yaran tun a hoto suka shiga ran mutane murjace ta kira Aira Bayan ta d'auka ta ce "Congratulation kawata Allah ubangiji ya raya mana twins wlh Kinga Dana gansu a hoto kamar na sace Ji nake kamar nayi tsuntsuwa na taho" murmushi Aira tayi ta ce "Ai gwara ki tahoma tun wuri karsuyi fushi da Mummyn su " ah suyi hakuri ina hanyar tahowa my twins ki shafa mun kansu Sis Zadai ki bani su kyauta ko Dan wlh ina sonsu"Hasina ce tayi saurin amshe wayar ta ce "Rabu da ita sis Me ya kaiki ba wannan mahaukaciyar yara Ni zaki bawa su yanda zankula dasu " Dariya Aira tayi tanajin irin yanda suke drama A waya Bayan sunyi bankwana hotonsu tahau what's App ta tura musu tana ganin yanda suke ta status Ana hadama yaran tiktok sak daka kalli yaran zakace musu turawa grps suka bude su hudu waidan tattaunawa akan sunan Aira ce tayi voice ta ce "Manyan iyayen twins wani suna kukeganin za a dinga kiransu dashi nidai wlh na kasa ganowa Ku zaba musu suna mai dadi" Voice maryam tayo ta ce "Gaskiya kam kyanta a naima musu nick name mai dadi bari hasina ta fito itace Gwanar sanin sunaye nima ita ta zabawa hanif" Hasina ce tayo voice bayan nasu ta ce "a gaskiya inaga a kirasu da Nihal da Naila ko ya kikace sunan yayi kuma Kunga baiyi yawa Ba sosai" kowa yayi na am da sunan Hakan yasa Aira ta ce "sunan yayi sis kawai a kirasu da hakan amma yaushe zakuzo" Insha Allahu zuwa jibi mukeson tahowa tare da su goggo"Sosai Aira tayi farinciki sosai take chat da su ana raha da Hira A lokacin Aira na Gado Arman ya shigo da Rahama dake Kuka mik'a mata ita yayi tare da zaunawa ya ce "wani sunan kuka zaba musu za a bugo musu abubuwan suna "Nihal & Naila yayi ko Yaya?Wow ya fad'a tare da Jinjina mata hannu ya ce " sunan yayi mom.twins "takwarar Mummy sai a kirata da Naila takwarar Mamy kuma Nihal ko " Eh my hero ta fad'a tana feeding d'in Nihal Kallonsu yake gwanin sha wa Shafa sajenshi yayi ya ce "Kinsan me cutie" Dagowa tayi ta ce "Saika fad'a hero" Nifa mamaki nake har yanzu Wai kece da yara saina tuna kema yarintataki gani nake kamar haka kece da kina yarinya"Dariya sosai Aira tayi tare da mik'ewa ta ce "Lallai hero Allah kana maidani baya da yawa sannan tayi Farr da ido ta ce " Me yafi son ranka Ganikwa dak'au kamar ban haihuba ko yanzu sai a dasa daga Inda aka tsaya"Dariya yayi ya ce "Au to bari na yi taste naji da gaskene zai chafkota ta ruga da gudu tayi palour "Rufamun asiri karki kadamun y'a ya fad'a yana binta a palour Kallon Aira da ta shigo da gudu Mummy tayi ta ce " Subhanallahi meye haka Aira Da yarinyar zaki dinga gudu Dan shirme jaririyar saikin kada ita kodai harkin manta zafin nakudar da kikasha ?Sosa kai Aira tayi ta ce "Yi hakuri Mummy bazan sakeba " Hararar Arman d'aya biyo bayanta Mummy tayi ta ce "Kaikuma Dan shirme na meye zaka biyota Wlh indai wannan shiririta zakuyi bazan yardaba wannan kunma iya kula da Yaran har yanzu baku Aje shirmeba" Sorry Mummy Arman ya fad'a tare da Kallon Aira ya kashe mata ido Alamun zasu hade gwalo tayi mishi tare da zaunawa gefen Mummy duk tana kallonsu girgiza kai kawai tayi Ywwa Mummy Sun zaba musu Nick name takwararki Naila za akirata dashi takwarar Mamy kuma Nihal sunan yayi ko?Masha Allah eh sunan yayi kam Allah ya raya"Mikewa Arman yayi tare da Kallon Aira ya ce "Jeki fito musu da kaya masu kyau mai hoton na waje zai shigo ya d'aukesu Ki fito musu da Kamar kala biyar biyar?to Aira ta fad'a tare da mik'ewa ta shiga d'akinta drawer da aka jera kayan Yaran ta fiddo Inda ta zaba musu masu kyau iri daidai ta fito dasu palour a lokacin har mai hoton ya shigo Mik'awa Mummy kayan tayi tare da zaunawa gefe Nan Mummy ta shiga shiryasu da anyi musu hoton su sauya musu wasu kuma sosai hotunan sukeyin kyau a haka har aka gama Mai hoton ya tafi sosai Mummy ta shiga tofe yaran da Addua Dan yaran nan a kyansu sai an dage da addu'a saboda bakin mutane Kallon Aira da Arman tayi ta ce " Karku sake Kuyi sake da Addu'ar nan Safe dare ko fita zakuyi dasu Karku kuskura ku tab'a mancewa Ta zauna a bakinku ku dinga Tofa musu "A'uzu bikalmatillahi tammati min sharrima halak'a " ku tofa musu a kansu sau Ukku ko sau Bakwai insha Allahu babu abunda zai samu Yaranku tundaga kan sharrin mutum da aljan ba abunda zai samu Yaranku sannan Karku dinga Dorasu a social media bakin mutane idan kasan wani bakusan wani dukda idan kun rik'e addu'ar nan babu Wanda ya isa yataba Yaranku koda maye ne kuwa Amma ance hanyar lafiya a bita da shekara Karku dinga d'ora Yaranku a social media Ya wuce what's app a barshi kunjidai na fad'a maku"To Mummy insha Allahu suka fad'a Sannan ta k'ara kallon Aira ta ja mata kunne cikin sigar wasa"Dan Kara Aira tayi ta ce "Auch mummy" Sannan ta d'an dankwasheta aka ta ce "kekuma na k'araga kina gudu da su a hannu Ko shan ruwan sanyi ko zaki ko yaji na hana" Dariya Arman yayi ya ce "Mummy kamar kinsan ta da shegen shan choculate gwara ki mata warning" Shima dankwashinshi Mummy tayi a ka ta ce "Kaikuma ina ruwanka d'an sa ido" Dariya Aira tayi mai tare da mashi gwalo Marairaicewa yayi ya kalli Mummy ya ce "Kinganta ko Mummy gwalo takemunfa" tayi maka d'in Mummy ta fad'a tana Kara masa dankwashi"Dariya Aira tayi sosai hada rik'e ciki Tare da Kara mashi gwalo ganin ya Mike Ya sanyata saurin Aje Nihal kan sopa tare da rugawa tayi ciki ya Mara mata baya"Girgiza kai Mummy tayi ta ce "Ana magani kai yana k'aba Allah ya shiryeku yaran nan kuma zakusha renon mashiriritan iyaye ta fad'a tana Dorasu kan kekensu na kwanciya Dan sunyi bacci tukwana ta mik'e ta shiga bedroom d'in da ta sauka tayi wanka ta shirya.tana tunanin yanda zata kankare da Daddy idan ta koma. Ana jibi suna y'an Yola suka tattaho sunfi su sha biyar hada Gwaggo Sosai Aira tayi farincikin ganinsu ita dasu Hasina tsalle sukayi suka Rungume juna suna farincikin had'uwa da juna Sosai suka tahowa da Aira dinkuna Wanda Mummy ta sanya a kai mata d'inkin a tafo dasu kala goma kuma Duka masu masifar kyau nanfa kowa ya shiga d'aukar yaran da riritarsu kowa ji yake inama nasune musamman su Hasina da suke zuba musu hotuna a wayar Aira saboda wayar badai camera ba idan ka kalli yaran saika rude kaji inama nakane (lol). Yau ta kama Friday ranar sunan twins manyan manyan raguna tirka tirka saida aka yanke takwas uwar jego Aira sosai tayi masifar kyau ita da yaranta Haka uban gayya Arman sosai aka shiga musu hotuna masu masifar kyau Mummy ma anmata hotuna masu kyau ita da y'an jikokin nata da takejin kaunarsu kamar ita ta haifesu sosai akayi bishasha a bikin sunan nan Anci ansha Sannan aka raba su calendar, bags kala kala na hotunan Yaran da sunansu jiki,su cups,memo,littatafai manya da hoton yaran jiki,sannan da kayan yara da aka buga da hotonsu jiki Babban Hall Aka kama Inda akayi lunch Akaci aka sha akayi hani an Hall din sosai ya cika da mutanen Arziki Dan abokanan Mamy dake nan London hada Wanda suke Dubai da aminanta dake 9ja manyan masu kudi saida sukazo sannan kowannensu saida ya cika jariran da kayan arziki Sosai na dinga kyalla idona naga ko zanga Ni da yaya Arman fans a bikin sunan nan amma shiru kakeji nace kaico Nasan kila jirgi suka rasa hakan yasa na d'auko musu rahoto yanda ya kamata anyi taro lafiya ankwashe lafiya kowa sai dai Sam barka........✍🏿 *nida Yaya Arman littafin kudine akan Naira 200 kachal ta wannan number* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/17, 11:09] Hajo hajo: 🅿️........*107&108* .....Washegari Bayan anyi soye y'an uwan Mamy wasu suka tattafi garage daga Murja sai Hasina da goggo sai Mummy kawai da dare Suna kan Gado su Ukku suna ta fira yayinda Hasina ke kalle_kalle a tiktok Amsar wayar Aira tayi ta ce " wai muga iktok d'innan ya yake " Amsa tayi tayi ta kallon videos da na kirkin da Wanda bana arzikiba saitaji abun ya burgeta kallon hasina tayi ta ce "Sis amma Wlh abun yayimun kyau ka d'ebe kewa " Wlhko ga kinci Dariya Ko na bud'e maki kuma Kinga kina d'ora hoton twins wlh zakiyi mamakin followers din da zasu jawo maki"Allah sis Saidai yaya Ya ce whats app kadai yakeson inayi ga karkiga yanda ya tsani tiktok d'innan"Yo sani zaiyi kinayi shida bayinshi yakeba bare yagani inaga yaya what's app kadai yake ki bud'e abunki wlh"Mik'a mata wayar Aira tayi ta ce "Anshi budemun " Amsa tayi ta bud'e mata account da Oum_twins_Naila&Nihal (Karfa Kuyi search fans k'irk'irarren account ne😂dan naga kun k'agu ku samu shiga wajen Aira lol😉😝) Ana gama bud'ewa ta d'ora mata hotunansu sannan ta nuna mata yanda akeyi ai Aira abun nema ya samu Nan tayi ta shiga Inda ta fara d'ora hotunan twins da photographer yayi musu rannan wa iya zubillahi fad'ar kyan da sukayi bata bakine walahaula ta tofa a hoton su kansu su Hasina saida suka d'auka suka daddaura a nasu shafin dan su kansu twins sun isa su janyo musu followers a cewarsu (Nima dai inaga hoton twins din Aira zankoma post Ko sunjayomun followers lol)Boye mata account din sukayi Inda bazai ganiba koya d'auki wayar. Washegari Suna zaune a palour ana fira twins na hannun Mummy da goggo Magungunan miyagu da na iska goggo ta mik'awa Aira ta ce "Amshi ku dinga turarawa duniyar nan ba yarda " Amsa Aira tayi tayi mata Godiya goggo Ce ta kalli Mummy ta ce "Ke yanzu fatima haka za abar yaran nan su kadai Nidai Dan kinji tawa amma da muntafi dasu idan tayi arba in sai ta dawo" jinjina kai Mummy tayi ta ce "Goggo bazaki gane bane yaran ne basuyi kwariba AC jirgi ba wasa bace illa zatayi musu sannan ayita yawo dasu da kafin ta haihu ne za ayi wannan din" Hakane.kuma to yanzu wa zai zauna wajensu kenan nidai Kinga jibi zamu wuce da ina da lfy da ni saina zaunama tunda dai ba ambar yarinya haihuwar farko ita kadaiba"goggo ni zan zauna daman har tayi arba'in din wa garesu Wanda ya fini "Haba Fatima dukga y'an uwanki nan da d'iyan yayyinsu har a rasa Wanda zai zauna saike ki zauna a a baza Ayi hakaba a kira hadiza ta dawo (kanwar Mamy ce tana Aure a Yola)saita zauna har suyi arba'in din?banki taki ba goggo amma kiyi hakuri na zaunadin nasan bawai mai rasa zaman akaiba a a nafison su samu kulawar tawane yaran Dan Yaran nan saina taka musu birki ta fad'a tana Hararar Arman " Dariya kawai sukayi ita Aira suna jinsuma amma hankalinsu nakan hirar da suke" jinjina kai goggo tayi ta ce "To shikenan amma gsky bazakiyi kwana arba'in ba mijinki baisan Inda kikeba kidaiyi sati biyu gasu Hasina nan Saisu zauna Har suyi kwarin" To goggo Hakanma yayi "Su Hasina da Murja ko tsallen murna suka daka Za a barsu Aira ma sosai tayi farinciki suka Rungume juna Dariya Mummy tayi ta ce " Uhm shirirta ai saita karu kuma"Dariya sukayi Naila ce ta tsala kuka dake hannun goggo saurin mik'awa Aira tayi ta ce 'ke amshi d'iyarki ni ban iyawa Haba yarinya sai jarabar kuka harta rika wani hakikicewa ita ga shak'iyiya"Duk Dariya sukayi Aira ta amsheta tare da mik'ewa sukayi Bedrom ita da su Murja hartabar wajen Arman na binta da wani mayen kallo suna shiga Gado suka baje Inda ta fara feeding Naila Wayarta ta bud'e ta ce Bari ma shiga Munsamu followrs Dariya sukayi tana d'agawa kuwa taga Uban followers tare da likes da 70 comment "Ihu tayi ta ce " Sis Kunga kuwa followers Dina farawa da iyawa daman sunsan anrina amsa sukayi sukayi ta karanta comment din mutane Wasu addua Allah raya wasu masha Allah sosai ake yaba yaran Nan wata Hartana Tayi kamun D'aya idan za a bata. Sosai Aira da twins d'inta suke samun kulawa daga wajen Mummy Inda Mummy sosai take gyara y'artata Dan sanyawa tayi aka kawo mata kayan gyara daga Sudan Sosai ta shiga gyara y'artata tuni Aira tayi zam kamar bata tab'a haihuwa ba Arman ko duk matse yake da Matar tashi satin Mummy Ukku a lokacin twins sunfara wayau sunyi b'ulb'ul abunsu ta tattara kayanta Dan komawa 9ja ba irin kukan da Aira batayiba akan Mummy ta zauna takiya tace Ai zata dinga zuwansu itama wajen mijinta zata koma Aira da Arman sai twins kadai suka mata rakiya airport Dan su Hasina suna gida "Suna filin jirgi jirginta zai tashi Naila dake hannunta ta mik'awa Arman tanajin kamar karta tafi Dan sosai take so da k'aunar jikokin nata Ta ce " Kuci gaba da kula dasu yanda ya kamata sannan dai Karku manta da adduoo Allah ya raya "Amsar ta Arman yanajin kamar yayi kuka Aira ko jikin Mummy ta fad'a tana kuka Lallashinta Mummy tayi ta ce " Haba daughter idan inazuwa zantafi kina kuka aisaikisa na daina zuwa insha Allah nan kusa zan dawo kodan nayi supervised d'inku inga kuna kulamun da jikoki kiyi shiru kinji y'ar Mummy"Goge hawayenta Aira tayi tare da kama hannun Mummy ta ce "To Mummy nadaina Dan Allah Mummy kidawo" murmushi tayi tare da ida Goge mata hawayenta ta ce "Insha Allahu daughter" cike da kewar juna Mummy ta hau jirgi har jirginsu ya tashi suna nan Saida sukaga dagawarshi sama tukwana suka koma mota Inda Aira duk tayi sanyi tunanin Mamy kawai take tanason jin koda muryar mahaifiyartata ne amma ba dama a motama kuka ta dingayi Arman Lallashinta sosai ta dingayi Dan a tunaninshi ko tafiyar Mummy Ce itako kewar Mamyntace yanzu ta addabeta tasan a yanda uwa takeson d'anta Dan ta haihu taji kalar soyayyar da takeyiwa twins d'inta Itamafa haka Mamy take mata Amma Yanzu basa tare tsawon shekara kusan biyu kenan Sai take ganin kamar batayiwa mamy adalciba sosai tayi sanyi danma Arman ya kwantar mata da hankali Dan son rage mata damuwa ya sanyashi kaita wajen shakatawa sosai taji dad'in wajen ita da twins d'insu d'aya na hannunta daya hannun Arman duk Inda suka gitta sai an kallesu sai magriba suka Koma gida. Mummy koda ta isa sosai suka sha dagu da Daddy hakuri sosai ta dinga bashi yana burkucewa yace ta rainashi hartatafi kusan wata guda ba waya ba komai sannan tayi mashi k'aryar mutuwa ashe da Inda zata hakuri Mummy ta bashi ta ce "Diyar yayata ce dake London ta haihu to damukaje suna bamai zama sai ni na zauna Dan na kula dasu cs ce akai mata kuma kaga ni nayi karatun health ga kula.da twins sai babba shiyasa harna zauna nakai haka Amma kayi hakuri Dan Allah habiby hakan bazata k'ara faruwa ba please" Sassautawa dady yayi ya ce "Amma wlh raina ya baci amma tunda kikace hakane bakomai Allah ya raya koni kika fad'awa haka aiba hanaki zanyiba Haushin da Naji da kika tafi ba izinina" Ai nazata bakaza bariba shysa amma dai kayi hakuri nidai bada hakuri nake "Daga nan suka shirya kunsan tsakanin mata da miji Da daddare tana d'aki suna Hira wajen 12 dasu Hasina twins na wajen Arman taji kiranshi "D'auka tayi cikin kasalalliyar murya taji ya ce " kizo Ki bawa su twins Susha santashi"Mikewa tayi Tare da cewa "Ina dawowa" A daki ta sameshi kwance rik'e da mararshi Twins na gadonsu suna bacci "wajenshi ta nufa tare da tsayawa ta ce " Honey lafiya naga kamar baka da lafiya fa Kuma naga baccima suke kace sun tashi" janyota yayi jikinshi tare da kwantar da ita gefenshi cikin k'arfin hali ya ce "I need you My wife please kiyimun dabarar da zan samu nutsuwa ya fad'a yana hade bakinsu Ita Aira saima ya bata tausayi Hakan yasa ta bashi Had'in kai sosai ta yi duk yanda zatayi ganin ta gamsar da mijin nata Har ta samu ya samu nutsuwa tukwana ya Rungumeta yana sanya mata Albarka A haka bacci mai dad'i ya kwashesu Cikin dare twins suka tashesu Madara suka basu tukwana suka koma suka kwanta cikin ikon Allah basu Kara tashi ba kusa har safe. Sosai Aira ke amfani da magungunan da mummy ta had'o mata ba kama hannun yaro ga kuma cima me kyau da takeci sosai sukayi b'ulb'ul da kyau itada Twins d'inta twins Nada wata biyu su Hasina suka koma 9ja Inda saida aka sha kukan rabuwa kafin su tafi Dan sosai suka shaku da Yaran ga shakuwar dasukayi da su Aira Bayan Tafiyarsu tare da Aira da Arman suke kula da yaransu Da safe shi yayiwa Naila wanka ita tayiwa nihal haka wajen shirya suma daman girki da gyaran Gidan kuku yakeyi hakan yasa Aikin bai wani chakude musu ba ranar da Aira fa tsarkaka Taji wuta wajen Arman Dan banbanci da first night d'insu kadanne sosai ta wahaltu aiki ya dawo mata sabo har dingishi saida tadingayi Kuka ko ta shashi kamar me haka rayuwarsu taci gaba da wakana cikin soyayya da k'aunar juna ga kullum cikin turawa Mummy hotunan twins ake da video d'insu a haka har twins sukayi wata biyar. Yau suna Video call da Mummy dake zaune Daddy na Kan sopa yana Danna laptop Twins na kekensu na koyan zama sai wutsil wutsiltu suke suna Dariya Aka haskawa Mummy su cikin farinciki Mummy ta ce "Ah lallai kuna kulamun da twins yanda ya kamata ji yanda suke Dariya da zillo Alamun dai akwai lafiya tattare dasu" Dariya Aira tayi ta ce "Mummy kindai gani muna kula miki dasu sune dai suke missing d'inki musamman takwararki idan tana gwalamgwamtu zaikiji tana muuum " Dariya sosai Arman da Mummy sukayi ta Cikin waya ta ce "Ah gsky dole nazo naga takwara tunda harta fara kiran suna na " Itako kamar tasan me ake Naila Sai Dariya take yana zullo zata kamo wayar Mummy ta ce "Ah na tabbatar gsky ganinan zuwa next week insha Allahu tsallen murna Aira tayi " Daddy ne dake sauraronsu Kallonta yayi ya ce "Dia kina daiji da twins d'innan sosai naga alama " Murmushi Mummy tayi ta Kalleshi ta ce "Sosaima dia saima ka gansu" Inda mu gaisa dasu daddy ya fad'a sosai Mummy tayi mamaki Kallon Aira tayi ta Cikin waya a hankali ta ce "Karku juyo fuskarku zasu gaisa da Daddynku Sannan karkiyi magana kunji" to sukace a tare Mikewa Mummy tayi da wayar a hannunta ta nufi wajen Daddy "Fuskar twins dake Dariya suna zillo Ta bayyana a jikin wayar Wanda sak kamanninsu suka k'ara fitowa da Arman Dan suna girma kamanninsu na bayyanuwa gaban daddyne ya fad'i sosai Ganin yara masu kama da tilon d'an nashi ga kuma wata soyayyar yaran da yaji ta tsargamai Lokaci guda baitabajin yara da suka shiga ranshi lokaci guda irin twins d'innan da yake ganiba " murmushi yayi musu ta Cikin waya ya ce "My twins yakuke" Kamar sunsan me ake cewa sukahau Dariya da zillo Shima dariyarsu ta manya yayi musu Bayan an katse kiran kallon Mummy yayi ya ce "ya akayi naga yaran nan suna tsananin kama da Arman?gaban Mummy ne ya fad'i tamaza ta fusge ta ce " wlh ko dia kowa haka yakecewa kamarsu d'aya sak kasan wasu su dangi suke biyowa kuma kaga Arman kama dani yafi daukowa to kaga Y'an gidanmu yawaici duk kakanninmu d'aya inaga shiyasa haka"jinjina kai Daddy yayi Alamun ya fahimta ya ce "Hakane Allah ya rayasu yayi musu albarka yaran suna da shiga rai Sosai Gaskiya Idan kinkira ina nan ki dinga banisu” Mummy ita kadai tasan farincikin da ta shiga Wannanma dama ce ta sameta babba ta ce "Angama ranka ya dad'e nan Mummy ta tuttura masa hotunan su Naila Inda ya shiga kallonsu har murmushi yake yanajin inama ace yaran nan daga gudan jininshi suka fito Dan har yanzu da soyayyar Arman a ranshi dukda kuwa fushin da yake dashi Saidai idan ya tuna girman laifin da yayi masa yakejin Haushi a ranshi amma sosai yake kewar Dan nasa Tundaga ranar Duk sanda idan yana gidan ake video call da twins tofa Shima amsa yake ayi tayi dasu sosai hakan yakeyiwa su Arman dad'i. Yanzu Aira ta Tara uban followers da suka haura 50k Likes da comment din da takesha a hotunan twins naban mamaki wani comment dinma bata tsayawa karantawa yau ta shiga Duba comment duk hoton data daura nasu na cikin satin nan taga wata lemart l Sadeq saitayi comment wasu ta ce " wow masha Allah bantaba ga yaran da suka burgeni irin yaran nan ba Allah dai ubangiji ya raya ya Kade bakin mutane "refly Aira tayi mata ta ce " Ameen sis Thnks"User din ta kurewa ido tasan y'an gidansu ne ke using da sunannan ko a school sosai tayi mamaki to ko akwai masu irin sunan daman haka dai ta kyale . Washegari tayi post din videon twins Inda Naila ke janyo Nihal daga zaune harta sanyata kuka Sai comment ake wata kawarta Rahama da suke kawance har chat suke sbd twins y'ar Kaduna ce ta ce "Gaskiya Naila zan zaneki Dan Kinga takwarata Nada hakuri shine kika rainata harkika sanyata kuka to zan rama mata ke kuma mom twins munbata tunda kika kyale waccen uwar fad'an ta zalintarmun takwara. Emogis din Dariya Aira ta tura mata ta ce " am sorry mumcy da yake haka take kiranta ta ce "Takwarar takice y'ar tsokana ce Bakigaba daga farko ba Ai ita ta fara ja mata gashi ba "" emogis din harara ta aiko mata ta ce "To ke kuma saiki kyale Allah ku kiyayeni duk Randa nazo zantafi da takwarata saiku nemu wacce zak'uwa" Dariya Aira tayi ta ce "To saikinzo kullum haka kike cewa Amma mundaiki ganinki kidaiyi zuciya ki taho ki tafi da takwarartaki mana" emogis din kuka ta turo ta ce "Ai k'watsam zaku ganni a London Zuwan bazata zan maku"Allah yasanya Aira tafada" Duk hirar da suke amma na saurara Dan tunda ta fara ga yaran taji sun shiga ranta ga mamakin ta na kamannin yaran da Arman da tagani Ta PC tayiwa Aira magana ta ce "Aslm mom twins ykk" Dubawa Aira tayi ta ce "Alhamdulilla auntyn twins ygd " Alhmdllh amma ta fad'a ta ce Wlh yaranki sun burgeni Aunty Ga kama da sukeyimun da wani cousin brother Dina wlh kamar harta b'aci"gaba Aira ne ya bada daram Mikewa tayi daga zaunen da take ta ce "Na shiga ukku Kardai amma ce cikin Sauri ta shiga profile d'inta ta duba ba post Ko d'aya tana shiga hoton data daura taga hotonta ita da ita Lokacin wata salla sosai sukayishi sunyi kyau sunsha ankonsu na dogayen riguna wasu ziraren hawaye ne suka zubo mata ta maza ta Goge a ranta ta ce " Allahsrk ashe y'ar uwatace Amma bazan tab'a nuna mata ni ce ba "Yadai sis kinyi shiru ta k'ara maido mata refly " Goge hawayenta Aira tayi ta ce "Allahsrk Kinsan duniya akwai kamanni da yawa" lemart:Hakane kam wlh ai Naji ma kamar London kuke ko? Aira:😅smile eh amma ba haifaffun Chan bane Aikine ya kaimu Chan Lemart:Allahsrk wace kasa kuke kenan Naji kuna hausa: Aira:9ja muke kefa sis:Lemart:wow Kasarmu d'aya kenan mom twins kice wataran zanga twins Dina wani gari kike a 9ja"Aira:insha Allah zakiga twins dinki har gida Auntynsu Yola nake kefa"Kano nake nikuma "Murmushi Aira tayi jin kukan Naila a palour ya sanyata saurin cewa " Bye sis Naila na kuka sai anjima"Ki shafamun kanta Y'ar uwa Sannan inba dmw turoman numberki ta what's app mudinga gaisawa"Typing number Aira tayi ta tura mata tare da saurin kashe datar ganin Arman ya shigo da naila hannunshi d'akin kallonta yayi ya ce "Bakijin kukan momcy Sweetheart kwanannan kin tarki Danna waya wlh " Sorry honey Tafada tana amsarta Ta ce "Sorry mummynmu "ammako cikin murna ta sanya number Aira tayi mata magana a what's app Mikewa tayi da wayar a hannunta d'akin mama ta tafi ta ce " Mama Kinga Wasu Yara masu kama ya yaya Arman kuwa diyan wata kawata ne dake London wlh yaran suna da kyau Ga shiga rai"Dan kullum idan Aira tayi post saita dauki hotunansu "Kallonsu Mama tayi ta ce " wlhko Kinga kama ikon Allah masha Allah dai yaran Akwai kyau "Wlhko mama ta fad'a tana tashi tare da nufar d'akin Mamy ta sameta tana Sanyawa Amer kayan islamiya Dan yanzu Amer an girma anshiga shekara hud'u Kallonta mamy tayi ta ce " ywwa amma gashinan ki mik'awa driver ya kaishi A hanya ya saya masa choculate ta fad'a tana mik'a mata 500 to Mamy amma ta fad'a tare da isowa ta ce "Mamy wani hoto ne zan nuna maki'ta fad'a tana zama gefenta tare da nuno mata hoton su Naila ta ce " Mummy kalli twins d'innan basa kama da yaya Arman"Kallonsu Mummy ta tsayayi gabanta na tsananta fad'uwa sosai yaran suka shiga ranta lokaci guda ta ce "suna kama sosai wlh ba Ama magana ina kika samesu ke kuwa" murmushi tayi ta ce "Wlhko Mamymamansuce kwt a London suke amma tacemun y'an Yola ne karkiga maman yaran tana da kirki" ta k'arasa fad'a tana nuna mata sauran videos din yaran tiktok dinma gaba daga tahau ta ce kalli Mamy uban comment da likes din da yarannan ke samu"kallonta Mamy tayi ta ce "Wai uwar yaran da kanta take dorawa koko wanine daban yake dorawa ya sunan maman tasu" Wlh Mamy bansan sunantaba Oum twins kawai ake cemata maman yarance ke dorawa mana Ta fad'a tana nuna mata fadansu na d'azu ta ce kalli Mummy yaran Akwai wayau ji kamar diyan turawa wannan mai fad'an ita ce "Naila d'ayar kuma Nihal" kallon videon Mamy ta tsayayi harya k'are itama yaran sun burgeta jinjina kai ta yi ta ce "Amma uwar yaran nan anyi mahaukaciya wlh bata da magaya Inbanda Rashin magaya tazo tana d'ora diyanta a bainar duniya haka kawai a cinye mata y'ay'a tama rasa Inda zata dinga dorawa sai tiktok to Allah ya kyauta ya k'are matasu amma wannan kam uwar bata da magaya da d'iyatace da taci ubanta wlh Shi mijin ko yana haukan me Mamy ta fad'a tana Jan tsaki" (Nikam nace d’iyar takice ma mamy)Dariya Amma tayi ta mik'e ta ce "Mamy kenan " Amma na fita da Amer Mummy tayi tagumi hawayen kewar y'artata na zubo mata batasan ya akayi ba Ganin yaran nan da tayi taji hankalinta ya tashi sosai Saida tagama kuka tukwana ta gode Allah ta ce "Allah tsaremunke a duk Inda kike y'ata Albarka ta na tare dake insha Allahu bana fushi dake Allah ya shiryeki..................✍🏿 *Ni da Yaya Arman ba free bane na kudi ne akan 200 to 07026166536* _*Miss Hajo ce*_ [7/18, 13:05] Hajo hajo: 🅿️..........*109&110* ...Bana fushi dake Allah ya shiryeki kasancewar yau Friday su Aysha Da Ummy sunzo Ummy da d'anta Khalil har an yayeshi Daukarshi Mamy tayi ta ce "To mai Gidan ina Goron Juma ata" Murmushi sukayi suka gaisheta Aysha ce dai har yanzu bata haihuba da ta samu ciki yake b'arewa sau Ukku tana bari kenan Hakan yasa hankalinta duk ba kwance ba danma dangin mijinta suna sonta basu tab'a ko gora mata ba haka mijinta bai damu da hakan ba yasan haihuwa ta Allah ce kuma idan da rabo suma zasu samu ga tunanin halin da y'ar uwarta da take ciki da ta sanya a ranta Suma Duka saida amma ta nuna musu hoton twins suma sosai yaran suka burgesu ga mamakin su na kamannin yaran da Arman ranar duk saida suka jajinta Rashin Aira a tattare dasu Amma da Aysha hada kukansu Ummy cema tayi hawaye kawai Sosai Aira da Amma suke chat batare da Amma ta gane Aira ba Dan bata yi mata voice koda wasa ko video call ta kira twins kawai take haska mata bata yarda ta ganeta a yanzu Twins Nada shekara guda Wanda Mummy ta kawo musu ziyara kwanakin baya tayi one week ta koma tuni sunfara Dan cin abinci ta tafiya jefi jefi ga dumur dumur da kyau da Yaran suke karawa sosai Aira take Kara samun followers Dan yanzu yaran tuni sun baza duniya duk mahalukin dake tiktok tofa yasan da zaman Naila_da Nihal har yanzu Arman baisan Aira tana d'ora masa yara a duniya ba. Da misalin Sha d'aya na rana Twins na wasansu a palour su janyo wannan sun janyo wancen an baje musu kayan wasa a palourn saiyi suke suna Dariya Iyayen ko na like da juna Suna Zuba love d'insu Yanda ya kamata wajen 12 sukaji Nihal ta k'walla k'ara ta zube a wajen cikin rud'u Suka nufi wajen cikin fitar hankali Arman ya sungumeta ya na jijjigata ya ce "Lafiya meya sameta " kafin ya rufe bakinsu Naila ma ta fara kakkarwa da kakkafewa ihu Aira ta fasa ta ce "Na shiga ukku meya samesu ta fad'a tana sungumarta da take kakkafewa Arman bai sauraretaba makullin mota ya d'auko Ya figa suka tafi Asibiti yaran a hannunsu a rude Suna zuwa cikin gigita sukayiwa dr bayanin abunda ke damunshi amsarsu yayi cikin gaggawa tare da wucewa da su Emergency durk'ushewa a wajen Aira tayi tana matsanancin kuka Kar dai wani Abu ya samu twins din nata " Suna zaune Dr ya fito Cikin gaggawa ya ce "Ana buk'atar Kara musu jini nawa za a d'auka" Cikin Sauri Arman ya ce "nau mana Dr Dan Allah ka taimakamun kar wani Abu ya samu yarana " Cikin gaggawa aka Auna jinin Arman akaga Yayi daidai Nan aka d'auka Inda likitan ya bawa su Naila Gado ya sanya musu a lokacin duk sume suke Shi kanshi yayi mamaki ace jinin yara ya zuke haka lokaci guda gashi yaran baiga Alamun Rashin jini a tattare dasu ba wani tunani ne ya fad'o masa Tabbas yaga yanda ake dora yaran nan a media Dan ya sansu shi kanshi farin sani Tabbas y'an shan jinine suke neman Shanye musu jini dayake musulmi ne Wani malaminshi ya kira Akan Dan Allah yazo yayi wani taimako ta Cikin wayar yayi mushi bayani da yake malamin mai taimakone ya ce gashinan zuwa su Aira sunyi jugum jugum sai risgar kuka take Arman shinema mai k'arfin halin Lallashinta Suna tsaye sukaga wucewar Malam Cikin office d'in Dr d'in binshi sukayi Dan sungaji da jira A tare suka shiga cikin kuka Aira ta ce. "Dr kar yarana su mutu Dan Allah Dr ina sonsu wlh ka taimaka mana" kallonsu Malam din yayi ya ce "Karku damu Kuyi musu addua Sannan ya kalli Dr Bayan sunyi musabaha ya ce " Ina yaran suke"Mikewa Dr yayi ya ce "Bari muje d'akin da suke a tare suka shiga d'akin harsu Aira Hango yaran nata yashe gadon marassa lafiya karasawa tayi ta fashe da kuka tana sabbatu Dak'yal Arman ya tadota Kallon Dr yayi yaa ce " akawo ruwa a cup"miko masa akayi ya jima yana tofa adduo'i a cikin ruwan kafin ya k'arasa Inda yaran suke ya yayyafa musu Nan take suka kawo numfashi tare fara kikkifewa Rikesu Malam yayi Inda ya shiga tofa musu Adduo i da karatu yayi minti Talatin a kansu dayake Babban malamine su Aira duk sai kallon ikon Allah suke Chan sukaji sun tashi tare da Fara tari sai kuma suka fara kuka "Cikin farinciki aira taje ta rungumesu tace " Alhamdulilla Allah nagode maka"Ajiyar zuciya Malam ya sauke ya ce " Alhamdulilla a Gaskiya yaran nan sun Auna arziki wlh inbanda dr kayi tunanin gane kan matsalar da Saidai wani ikon na ubangiji masu shan jini ne suka kamasu suka fara Shanye musu jini amma sun sakesu yanzu insha Allahu Saidai a cigaba da musu adduo'i Sosai sannan a kiyaye da yawa iyayen yanzu kuna sakaci da Yaranku saikiga yaro gashi bud'e ko anyi kitso yayi kyau an bud'e ko kaga ana d'ora yara social media Wanda hakan duk ba dacewa bace ta wannan hanyarce har ire_iren mutanen nan suke samun daman Shanye jinin Yaranku ku daina Sakaci da Addua Allah ya kiyaye gaba "Ameeen dr da Arman suka fad'a sosai suka shiga yiwa malamin Godiya Inda ARMAN ya bashi check din one million da farko kin karba yayi ya ce Ai aikin Allah ne yayi Dak'yal dai ya samu ya amsa Inda ya rubuta musu Adduo i sosai Wanda zasu dinga yiwa yaransu dasu kansu na tsaro. Bayan barin Malam wajen Kallon Arman Dr yayi ya ce " Bro Gaskiya Ku daina d'ora Yaranku a media baki da ido yayi musu yawa "da mamaki Arman ya ce " media kuma dr ai yaran nan bama Dorasu media Ko what's app ba Dorasu mukeba ko Ya fad'a yana kallon Aira dake feeding d'in yaran gabantane ya bada daram shikenan yau asirinta ya tonu"Kasa da kanta tayi gabanta na fad'uwa Lalubo Wayarshi Dr yayi ya shiga shafin Oum twins Naila&Nihal nan take Abubuwan yaran suka bayyana mik'awa Arman Wayar Dr yayi ya ce "Wannan ba su bane " Da mamaki Arman ya amsa Inda ya shiga Dubawa Tabbas sudinne Post d'insu yafi d'ari Ukku Kome suke ana d'auka ana dorawa Hatta shigarsu ta yau da safe yaga an d'ora sosai ranshi yayi mugun b'aci"idanunshi da har sun sauya launi ya kalli Aira datayi kasa da kanta ya ce "Uban waye yake doramun Yara a tsinannan abunnan " kasa tayi da kanta gabanta na fad'uwa ta kasa magana "Tsawa ya daka mata da ta mance rabon da yayi mata ya ce " nace ubanwa Yasa ki dinga doramun y'ay'a a duniya tallarsu nake ,ko me Da izininwa kika bud'e tiktok ?tuni Aira harta fara hawaye Cikin rud'u ta ce "Dan girman Allah yaya kayi hakuri?zuciyar ARMAN banda tafarfasa ba abunda take sosai ta bata masa rai to yanzu da yaranshi sun mutu fa a saboda dorasun da take har y'an shan jini zasu kashe musu yaya Tabbas saiya d'auki mataki bazai kyaletaba (hakan yana Faruwa sosai wlh Iyaye a dinga kiyayewa Allah ya kara kiyayewa ameeen)Tsawa ya daka mata ya ce " Ajemun yara na "Cikin rudu tana hawaye ta mik'e Dan baitab'a mata haka ba tsawon rayuwarsu tare da Jan baya hanyar kofa ya nuna mata ya ce " Get out."Yay....tsawar da ya daka mata ya sanyata saurin barin dakin hada tuntube tana kuka waje ta samu kofar D'akin ta durkushe tare da fashewa da kuka itakam ta bani Kenan yanzu da masu shan jini sun kashe mata yara bata tab'a tunanin hakanba ga ARMAN yanda taga yayi mugun fushi kuka take sosai Tana danasanin d'ora Yaranta da take Arman ko zuwa yayi ya Rungume yaran daman sunsaba da Daddynsu hakan yasa sukayi shiru jikinshi suna wasa da gemunshi yana musu wasa a haka har jinin ya k'are Inda Dr d'in yazo ya cire tare da rubuta musu magani Godiya sosai Arman yayiwa Dr d'in Inda ya amshi number shi Shima yayi mashi alkhairi sosai Rungume Naila datayi bacci a kafad'arshi yayi tare da d'aukar Nihal da idonta biyu ta lafe jikinshi yayi a haka ya fito Kallon Aira yayi data hade kai da guiwa tana kuka ya ce "Wuce mu tafi" cikin Sauri ta mik'e tana kuka ta ce "Dan Allah yaya....d'aga mata hannu yayi ya ce " banson jin komai daga bakinki Goge hawayenta tayi tare da bin bayansu zasu shiga mota mik'a masa hannu tayi zata amshi Naila tsaki yaja tare da kallonta ya ce "Ai bazaki Kara daukarsuba tunda bakya sonsu ni inason abuna kuma zan kula dasu daga yanzu kika k'ara daukarmun yara duk abunda na maki ke kikaja" Jan bakinta Aira tayi tana Hawaye Dan tasan sahibin nata yayi fushi sosai da ita a baya ya kwantar da Naila Inda ya na rik'e da Nihal ya shiga matuk'ar driver ya sanyata gabanshi yana tukawa ganin zai tada motar ya sanya Aira saurin shiga gaba tare da rufewa harsuka isa gida baice uffan ba itama sai hawaye take suna isa ya zagaya ya d'auki Naila da ta tashi ta fara kukan yunwa a palour suka baje Inda ya had'a musu madararsu ya basu daman suna sha sosai nan suka shiga sha a lokacin kasancewar magriba ya sanyashi Zaunar dasu yasa musu abun wasa yaje yayi alwala ya tada salla Yana gamawa yaje ya lalubo turaren da goggo ta taba basu basu taba amfani dashi ba na miyagu da iska nan ya hada boner ya sanya take dakin ya bide da kaurin maganin inda daya bayan daya ya turare yaran saida yaga sun fara tari alamun hayakin ya fara musu yawa tukwana ya dauke Aira ya kalla da duk tayi jugum tana hawaye ya ce "Bani wayarki ?Jikin charge ta cirota Dan daman tana chaji suka tafi mik'a masa tayi Daman ba security Tiktok din ya shiga ya shiga bincikawa yaga itadince duk gashinan ta daddora Wasu frnds d'inta yabi Wanda suma suka d'ora yaga wata Rahama ta d'ora yafi sau goma sai lemart da yaga ta d'aura sau Ukku sai wata Jannat Abuja Itama ta d'ora so biyu duk saida ya k'ara biccinkawa yaga su kadai suka d'ora Kallonta yayi fuska babu wasa ya ce " wacece Rahama Lemart Jannat?tana shashekar kuka ta ce "Kawayenane ?tsaki yaja ya ce " zoki amsa ki kirasu kice su sauke abubuwan yarana da suka d'ora yanzunnan"cikin Sauri taje ta amshi wayar tana kuka Rahama ta fara kira tana d'auka ta ce "Mom twins yau wata sabon gani kece hada kirana" Cikin muryar mai kuka Aira ta ce "Momcy Dan Allah hotunan su twins da kika D'aura ki sauke Yanzu Dan Allah a tiktok" lafiya mom twins nagama kamar kuka kike"Da sauki dai ki sauke Yanzu Tana gama fad'ar haka ta kashe kiran kallon Arman tayi d'aya kafeta da idanu Jannat ta dannawa kira itama ta fad'a mata haka A na lemart ne gabanta ya dinga fad'uwa karta ganeta Harararta yayi ganin takasa kiran d'ayar ya ce "jiran me kike" Goge hawayenta tai tare da Danna mata kira lemart na na d'auka sosai tayi mamakin ganin kiran Muryar da ba tataba Aira ta ara ta ce "Sis Dan Allah hotunan su twins da kika d'ora zaki hau yanzu ki sauke plx" subhanalla lafiya"da sauki ki sauke Dan Allah"too yanzu kuwa Amma meya faru Naji kina kuka"Bata bata amsa ba Aira ta katse kiran mik'awa Arman Wayar tayi da ya mik'o hannu amsa yayi tare da Kara shiga yana shiga Yaga Rahama. Da Jannat harsun sauke nasu tsaye tayi yaga saukewar na lemart itama tana nan yaga ta sauke ajiyar zuciya ya sauke Tare da shiga daman shi ya kware a computer a take ya lalata account din nata yayi harking dinsa yana gamawa Ya goge tiktok din gaba d'aya Tare da kashe wayar yasa a Aljihu D'aukar twins d'inshi yayi da suka fara bacci yayi ya wuce Bedroom d'insu Aira dai ta zama hoto dak'yal ta iya Jan kafarta ta shiga dayan bedroom d'in Sallar itama tayi har isha i da taji ankira Tana gamawa itama Sosai tayiwa yaran nata addu'ar neman tsari Tana nan zaune har 12 duk daukarta Arman zai huce da wuri Kodan susha abincinsu ai ya kawo mata su Amma taji shiru tunowa da bak'ar zuciyar Arman tayi ya sanyata saurin Mikewa ta fito d'akin ta shiga a hankali Inda ta samesu kwance akan Gado Arman a lokacin ba bacci yakeba yanajinta ya rufe idonshi Kamar mai bacci Ajiyar zuciya Ta sauke tare da Yin sanda a hankali taje ta d'auko Nihal tare da zama Gefen gadon Zage zif din rigarta tayi ta fito da Mamanta tare da sanya mata abaki Nihal da daman abunda take buk'ata kenan a take ta tashi tare da kamawa ta dinga tsotsa Dukda duhune hakan bai hana Aira yi mata wasa ba Takai 15 minutes tana sha tukwana taji ta saki Alamun tayi bacci a hankali ta yunkura Ta maida ita makwancinta tare da rufa mata bargo Arman duk yanajinta yana kallonta ta wutsiyar ido sosai yaji tausayinta Allah sarki y'a da uwa kenan ya fad'a yana jinjina kai Aira ko a hankali ta d'auko Naila Tana daukarta Ta yage baki zatayi kuka Cikin Sauri ta sanya mata abaki Wanda hakan yasa tayi shiru Ajiyar zuciya ta sauke daman yunwa Naila takeji nan tashiga tsotsa Sosai saida tayi 30 minutes tana tsotsa Aira harta fara gyangyadi Chan kuma taji ta saki Alamun tamayi bacci Daman Naila tafi Nihal tsotsa a hankali ta maida abunta tare da kwantar da ita Tana shirin Mikewa tabar dakin taji Arman ya janyota tare da rungumeta jikinshi Dan tuni zuciyarshi ta karye Yama fasa horata din da yace zaiyi Aira jin Haka kamar me jira ta sanyata sanya mishi kukan shagwaba ta ce "Yaya Dan Allah kayi hakuri Allah bazan sakeba nima nayi nadama dan Allah karkayi fushi dani bazan iya jurar fushinkaba yaya please ka yafemun"Rungumeta yayi ya ce " Na hakura my cutie nima ai bazan iya fushin dakeba ta maza ce nayi na daure amma kin b'atamun Raine Kinga yanzu inbanda Allah ya taimaka malamin nan yazo dafa zamu iya rasa yaranmu"Cikin kuka ta ce Bazan sakeba yaya "to my cutie na hakura ya fara yana fara romance d'inta Kamar basu tab'a fada ba daganan suka Lula wata duniyar ta daban. Twins Nada shekara daya da Rabi sosai suka Tashi da baki magana rai rai ga shegen wayau ga gudu ko ina Komai aka fad'a saisun maimaita A lokacin ne kuma Aira ta fara wani irin zazzabi da amai ga tashin zuciya arman yayida ita suje Asibiti ta kiya yauma tana kwance jikinshi Tana sauke ajiyar zuciya twins na tsaye suna wasa su biyu da teddy Shafa cikinta arman yayi ya ce " Cutie kodai nayi ajiya ne a cikin nan yake sanyaki amai da tashin zuciya"cikin shagwaba ta ce "Hero ka manta wancen cikin na twins banyi wani lauyayi ba sai nakega kawai ciwo ne fa " Naila ce ta rugo da gudu ta fad'a jikin Aira nihal kuma ta fad'a jikin Arman cigaba da hirarsu sukayi ARMAN ya ce "Amma ai saikanakega baizama lalle Duka biyun ya zama iri daya d'aukar cikinsu sainakega kowanne da banbancinsa nidai ban yarda ba cikine dake cutie" Uhm Nidai ka daina cewa haka hero ciwone kawai"Naila ce dake tsotsar yatsa Duka sunajinsu ta kalli Aira ta ce "Cuty(Cutie) itakuma Nihal ta kama Sajen Arman ta ce " Helo(Hero) Wara idanu a tare Aira da Arman sukayi Arman ya ce.....✍🏿 *Ki biya naki ki karanta cikin nustuwa da kwanciyar hankali akan Naira 200 kachal to 07026166536* _*Miss Hajo ce*_ [7/18, 13:05] Hajo hajo: 🅿️........*111&112* Ya ce "Chab Kwaiwayonmunefa sukayi?Dariya Aira tayi ta ce " Aidaman shirun nan danaga sunyi sunajin me akecewa "Dariya twins sukayi Naila ta kama rigar Aira zata d'aga ta kasa turo baki tayi ta Ce " Cuty mama ansha"Itama jin Haka ya sanya Nihal saurin Rugawa ta Dare Aira ta ce "Cuty nima ansha"Dariya sosai Aira da Arman suke Arman ya ce " Kinga yara karfa su sa mana suna"Dariya itama Aira tayi ta ce "Ai na yayeku tunda kuka iya gulma daga yau " kamar sunsan me tace sukahau kuka Arman da bayason kukan yaran nashi saurin yiwa Aira magana yayi akan tabasu susha tukwana ta basu tana jin haushin yanda Arman yaki bari ta yayesu gasudai tubarakalla saika d'auka sun haura shekara biyu ita har kunyar Shayar dasuma take wlh. Tundaga ranar twins suka sanyawa iyayen nasu suna ba irin yanda basuyiba su hanasu amma suka hanu saidai wani gamun sucewa Aira "Cutie mom" Shikuma Arman "Hero dad" sosai yanzu jikin Aira ya k'ara tsanani kome taci saita maidoshi Koda sukaje Asibiti gwajin farko likita ya tabbatar musu da tana d'auke da juna biyu na Wata biyu zokuga farinciki wajen wannan masoyan haka suka dawo gida suka ci gaba da rainon cikin su Wanda kuma lokacin Mummy da taji Aira Nada ciki ta yiwa Arman magana akan a yaye twins sun girma da kansu suka yaye yaran nasu daman sunacin abinci sosai hakan yasa basu sha wahalar yayensuba Mummy ma tazo ta duba jikin na Aira Inda taso tafiya da twins saboda rage musu wahala Amma sukak'iya subita suka dinga rafka kuka hakan yasa Mummy ta ajesu tace karma mutane suce satosu tayi daman iyayen baso suke ba Dan Aira bata nuna ba Amma Arman Saida ya nuna bayason Dan ko Kad'an bayason abunda zaiyi nesa da yaran nasu a lokacin ya kaisu school saboda shegen wayau da garesu da baki ya sanya malaman amsarsu Dukda sai ansha dagu suke zuwa school d'in musamman Naila danma sayayyar Choculate da kayan makuleshen da ya ninka saya musu ya sanya suka Dan yarda suke zuwa makarantar kullum idan zasu tafi sai sun tofe su da adduo'i Dan idan ka gansu da kayan makarantar zakayi mamakin irin kyan da sukayi yau Aira na kwance saman bed Dan da zazzabi ta tashi ga ciwon kai Arman ya bata maganin da Dr ya rubuta musu ta sha Rungumeta yayi akan bed Dan twins na palour suna wasa kasancewar yau weekend Yana shafa bayanta yace "sorry cutie Cikin nan Yana baki wahala da sauki d'auko" gyada mashi kai tayi tana Lafewa jikinshi dan bacci takeji"Kwantawa sukayi a tare Rungume da juna ya dorata saman ruwan cikinshi irin yanda akema yara idan sunaso suyi bacci tare da Daddab'a bayanta yana zuba mata kalamai masu zafi Itadai Uhm kawai take cemas shikam arman a hanksli ya dinga shafa ta tare da sanya hannunshi a rigarta yana mata wani irin salo twins ne jin iyayen nasu shiru ya sanyasu rugawa d'akin suna banka k'ofar suka samesu a haka Kallon juna sukayi tare da wara idanu Saikuma suka k'ara kallon iyayen nasu ido hud'u sukayi da Aira da Arman Saurin Juyawa sukayi suka koma palour Aira ko cikin saurin ta mik'e Ta ce "Yaya me suke nufi jifa kallon da suka mana" Shima Mikewa yayi tare da kama hannunta Suka fita a palour suka tarar dasu sun had'e waje guda suna kallo"Wajensu Aira ta nufa ta ce "My twins Kallo ake " banza sukayi da ita kallon Arman tayi tamai nuni da yazo yana zuwa Ya ce "my twins Me yasa kuka kyale mummynku naila uwar iyayi da tsiwa tana turo baki ta ce " Ba luwanmu daku mu"Wara idanu a tare sukayi suka kalli juna sannan suka kallesu Aira ta ce "Me mukayi muku" suna turo baki Nihal miskila ta kauda kai Naila kuma ta ce "ku Daina kaji Hero ba chauu"Kallon juna Arman da Aira sukayi saikuma Aira ta fusge Dan ta lura yaran nata abunda suka nufi tsaki taja ta ce " yara sai shegen sa ido mu wlh daman mummyn ta tafi dasu suka barmu muka huta ba damar Mu sake muda gidanmu yara sai gulmar tsiya "Dariya Arman yayi ya ce " ai shiyasa kikaga na sanyasu school a a gwara da Mummy ta barmu da abunmu ai sakacinmunema da muke barin d'akin bud'e"Turo baki Aira tayi tare da kallonsu ta daure fuska ta ce "Kuka k'ara shigo mana d'aki batare da kun nemu iziniba saina zaneku uban me ke hanaku knoking Dan iskanci ku fadowa mutane d'aki ba ko sallama haka nakoya muku?kamar jira suke Dan a rayuwarsu basason fad'a aiko suka fashe da kuka rungumesu Arman yayi tare da Hararar Aira ya ce " Kinga kin sanyamun su kuka wa yace ki musu fad'a "tab'e baki Aira tayi tare da barin palourn taje ta haye Gado tare da kwanciya Dan bacci takeji Arman ko sosai yasha dagu wajen bawa yaran nashi hakuri Dak'yal ya samu suka hakura Shima saida ya kaisu shan ice cream da wajen wasa tukwana suka sauko Aira a lokacin tana d'aki ta tashi dak'yal ta yunkura tayi wanka tana fitowa ta sanya rigar bacci ganin magriba nayi tana fitowa palour ta samesu suna shigowa da kayayyaki a hannunsu " tana ganin haka tasan wajen wasa ya kaisu Dan kullum suna hanyar park Sannu da zuwa tayi musu tare da kwantawa Sannu Arman yayi mata Twins ko sai kallonta suke sunason suje Wajenta suna tsoron karta musu fada irin na d'azu Take away din da yayo mata ya bud'e tare da nufar ta ya ce "Cutie bakici komai ba Yau ki daure kici ko Kad'an ne zakiji sauki" Hero amma kasan zan iya maidosa"girgiza mata kai yayi ya ce "Bazaki maidosa ba " Ya fad'a yana kai saitin bakinta Tare da Fara bata ci spoon hud'u ba Taji zuciyarta ta tashi da gudu ta mik'e kafinma ta isa toilet din palour ta fara amai sosai take yi kamar zata amayar da y'ay'an cikinta Arman yaje cike da tausayawa ya taimaka mata ta gyara jikinta shiya gyara Inda ta bata tare da sanya k'amshi twins ko sosai suka rude ganin mamansu cikin wannan halin musamman Naila da har ta fara kuka Wajen Aira data fito daga toilet din taje tare da Rungumeta tasa kuka Shafa kanta tayi tare da karasawa palourn ta zauna dasu a tare da ita Nihal ma jikinta ta fad'a tana hawaye a tare suka ce "Sorry cutie mom bazamu sakeba" Gyada musu kai kawai Aira tayi tare da kwantawa kan sopa "Jikinta suka haye Naila ta dinga shafa fuskar mamantata ta ce " Sorry mom sannu"Murmushi Aira ta sakar musu tare cewa "yawwa" Ganin sun damu sosai ya sanyata K'arfin halin nuna lafiyarta qalau ranar dak'yal ta samu sukayi bacci da anjima anjima saisu zo wajenta suna mata Sannu Aira saida tayi hawaye ganin yara dai kanana yanda suke tattalin uwarsu kamar wasu Manya '"Allah sarki d'a da uwa kenan sai Allah sosai itama ta shiga kogin tunanin tata mahaifiyar Arman ma sosai yake jera mata Sannu da tattalinta. Yau da lafiya gobe babu haka har cikin Aira yayi wata takwas Inda ya fito amma baiyi girma sosai ba Yau suna zaune a garden din gidan Su Duka Twins na Danna tab D'insu Mummy ce ta kira Arman Bayan sun gaisa yabawa Aira itama suka gaisa Jin Mummy da gudu twins suka amshe wayar suna rigen cewa "Mummy Mummy " murmushi bangaren Mummy tayi ta ce "Iye yaran Mummy yakuke " am Very fine mom how are you"Nihal ta fad'a cikin Muryar yara'alhmdllh Mummy ta fad'a "Naila ce ta amshe ta ce " Hello takwala "Dariya Mummy tayi ta ce " na am my takwala yakike "Lafiya qalau takwala yauce jakijo munyi missing d'inki" ni bazanzoba Saidai ku kuzo ganina Mummy ta fad'a "Shagwaba Naila ta dinga mata akan saitazo daga karshe danson kwantar mata da hankali ya sanya Mummy cewa 'to shikenan zanzo " tsallen murna Naila tayi tare da wulla wayar ta Dare Arman ta ce "Hero Mummy zatazo am very happy"shafa kanta yayi yana murmushi ya ce " kice takwararki ta kusa zuwa Me zaki shirya mata"Abinci me nice "Naila ta fad'a tana zillo jikin Arman " dauko wayarshi yayi da ta fashe dan tunda aka haifi twins waya kusan biyar suka fasa masa saidai ya sauya wata Nihal ko kuka ta fashe dashi Duk kallonta sukayi Aira ta janyota ta ce "Lafiya kukan me kike" Cikin kuka ta ce "Nima cutie ina takwala ta kullum takwalal Naila kadai take zuwa muke waya da ita ni hal yanju banga takwalata ba " Jikin Aira ne yayi sanyi harshi Arman Naila ce tayi mata gwalo ta ce "yeyeye yalinya to ai ke sunan maman cutie gareki Mummy maman Hero ce ko?ta fad'a tana kallon Arman?cikinsu ba Wanda yayi magana " Nihal ce cikin shagwaba ta kalli Aira da har ta fara hawaye ta ce "Cutie wai gaske sunan mom enki galeni?gyada mata kai Aira tayi tana Hawaye " a tare kamar sun had'a baki Nihal da Naila suka ce "Cutie ke ina mom En taki bamu tab'a ganinta ba mom En hero kadai muka sani sannan bamusan Dad enki ba Dad ein hero kadai muka chani "Aira kamar daman jira take Wani kududune taji tundaga zuciyarta sosai yaran Suka tayar mata da hankali bata tab'a jin tashin hankali tunda tabar gidansu ba irin na yau bata tab'a sha awar waiwayar gida ba sai yau kuka ta fashe dashi sosai Rungumeta Arman yayi ya ce " Subhanalla cutie meye haka kukanme kike"Sosai take kuka a jikinshi Inda twins duk suka tsaya suna kallonta suma harsun fara hawayen ganin mom d'insu na kuka Arman duk ya rud'e ganin irin kukan da Aira take ya ce "Kiyiwa girman Allah cutie kibar kukan nan daga yara sunyi magana zaki tashi hankalinki " Cikin kuka ta ce "Yaya Mamy nakeson gani Dan girman Allah ka kaini na ganta......✍🏿 *tofa ya kenan Twins sun Tayarma da Mummynsu hankali harta fara tunanin Gida* . _*Miss Hajo ce*_ [7/18, 17:31] Hajo hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN*🍏 _Hot love story_♥️ MALLAKAR Hajara L Sadeq *Bonus page*💃🏾😂 🅿️.......*113&114* ....Dan girman Allah ka kaini na ganta"ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka"Lallashinta ya fara ya ce "Kiyi hakuri cutie kibar maganar nan ki bari ba yanzu ba na kaiki ki ganta d'in amma ki bari saikin haihu" Mikewa Aira tayi tana Hawaye ta ce "Dole kace haka tunda bakai ne kake cikin halin da nake cikiba amma kasani ina k'aunar mahaifiyata kuma inason ganinta kamar yanda kowani d'a yakeji game da mahaifiyarshi Daurewa kawai nake tunda nake dakai na tab'a cewa ka kaini naga mahaifiyata yanzu nace ka kaini shine zaka k'i kaini" tana gama fad'ar hakan ta bar wajen tare da nufar hanyar Palour binta yayi yana kiran sunanta tayi mishi banza "Tana shiga Aira d'aki ta shige tare da rufewa da durkushe ta fashe da kuka abubuwan da suka faru a baya suka shiga dawo mata cikin kwalwarta kuka sosai take kamar ranta zai fita Arman da twins ba irin bugawar da basu mata ba dansu har sun fara kuka amma taki bud'ewa sai kukanta da suke juyowa sosai Hankalin Arman ya tashi palour ya koma Tare da dafe kanshi da yake Sara masa twins ne suna kuka suka ce " Hero kaba cutie hakuri bazamu sakeba mu muka chanyata kuka ko dad?rungumesu yayi ya ce "Ba ku kuka sanyata ba kuka My twins Karku Damu kinji" nan ya shiga Lallashin su har ya samu sukayi shiru duk sunyi sanyi Naila uwar iyayi harda tagumi "Arman ba irin yanda baiyiba Aira ta bud'e amma taki Mummy ya kira cikin damuwa ya fad'a mata abunda ke faruwa " Cewa tayi "ka lallab'ata Ta hakura ta Bari idan ta haihu saiku taho din yanzu ina zata da tsohon ciki" Cike da damuwa ya ce "to Mummy amma banajin zata hakura" ka jaraba idan Bata hakura ba saimusan yanda za ayi"To ya fada ranar Aira kulle ta kwan a d'aki tana kuka har bacci ya d'auketa su ARMAN ko a palour suka kwana shida yaranshi Da safe Bayan ta tashi idonta yayi jawur saboda kukan da tasha cikin k'arfin hali tayi wanka ta shirya cikin Doguwar Riga marar nauyi parasitimol ta b'alla Tasha saboda ciwon da kanta ke mata "bud'e d'akin tayi ta fito Inda ta samu Arman yana bawa yaranshi abinci a palour duk kallonta sukayi musamman Arman Cikin tausayawa ya ce " Sorry cutie Kintashi lfy "Alhamdulilla ta fad'a tana zama tare da kauda kai twins suka tashi sukaje suka hau kanta a tare sukace " Good morning cutie mom ya jikki"morning too my angels how was your night "ta fad'a tana shafa kansu" Very fine suka fad'a Sannan nihal ta marairaice ta ce "Cholly mom bazamu chakeba"murmushi Aira tayi musu " Arman ne ya taso ya ce "Taho muje kiyi breakfast" Kauda kai tayi tana shan magani ta ce "Na koshi" Amma dai kinsan bakici komai ba tun jiya banson irin haka cutie ki taho muje kici abinci kodan Abunda ke cikinki"ya fad'a cikin kulawa "kamar me jira tuni ta fara hawaye Cikin fushin da bata tab'a masa irinsaba ta juyo ta ce " nace na k'oshi bazanciba Ta fad'a tana Mikewa tana kuka tayi hanyar bedroom taku biyu tayi zatayi na Ukku ya ce "kika k'ara taku d'aya ban yafe maki ba " Chak ta tsaya bata juyoba Batayi gaba ba "Ajiyar zuciya ya sauke tare da Cewa dawo ki zauna muyi magana " ba musu ta janyo kafafunta tana hawaye ta dawo ta zauna "Matsawa Inda take yayi cikin damuwa ya ce "Meye haka cutie wani sabon salon ne kika samo Wanda baki dashi fushi kike dani me nayi maki?Kuka ta fashe dashi tare da Fad'awa jikinshi tana kuka ta ce " yaya na fad'a maka Mamy nakeson gani ka taimakamun ka kaini Wajenta Dan Allah na hadaka da girman Allah"sosai yayi sanyi Cikin sigar lallashi ya ce "Kiyi hakuri cutie idan kika haihu yanzu bakiga yanda kike Bafa k'aramar tafiya bace daga nan zuwa 9ja " Cikin kuka ta ce "Yaya Dan soyayyarka da Annabi Muhammad (S A W) ka kaini yanzu banajin komai ba abunda ke damuna nidai ka kaini na ganta"to shikenan Bar kukan insha Allahu zan kaiki shikenan ko" Dagowa tayi fuskarta jab'e jab'e da hawaye ta ce "da gaske " murmushi yayi mata ya ce "Ehmana cutie jibi insha Allahu saimu tafi" Cike da farinciki Aira ta Rungumeshi ta ce "Thnks you so much My husband " murmushi yayi yana shafa kanta Aira sosai taji farinciki Wanda harta k'agara jibin tayi koda Arman ya kira Mummy ya fad'a mata cewa tayi Allah ya kawosu lafiya Aira ko tun ranar ta fara shiri da parking d'in kayan twins kayanta kala biyar kawai ta zuba a akwati sauran duk na twins ne da kuma na Unborn da suka fara sayayya twins ma sai murna suke zasuje 9ja Washegari Arman ya bata wayarta da ya amshe tare da mata kashedin wani Abu ya k'ara faruwa ba ita ba k'ara rik'e waya cikin farinciki ta ce Insha Allah ba abunda zai k'ara faruwa yana bata tana bud'ewa what's app ta hau taga voice din mutanenta da kawayenta da suka had'u saboda twins Sai voice suke mata lafiya D'aya Bayan d'aya ta shiga ta dinga maida musu da alhmdllh "Rahama ce ta kirata " murmushi Aira tayi ta d'auka ta ce "My momcy ykk" Cikin murna Rahama ta ce "Haba daughter saikuma muka jiki shiru wlh karkiga yanda na damu kusan wata nawa anriga an saba Saina jiki shiru ga wayarki bata shiga kullum saina kira yanzuma ina gwadawa Naji ta shiga " Murmushi Aira tayi ta ce "Sorry my mom.wlh matsala aka samu ranar nan da na kiraku d'innan wlh kwana a gaba ya tayar da su twins masu shan jini suka kamasu To dadynsune da ya gano ina Dorasu ya b'ata account din sannan ya amshe wayar sai yanzu ya maidomun harma na hakura banyi zatoba nima nayi kewarki wlh" Cikin damuwa Rahama ta ce "Subhanallahi ai bamusan abunda ke faruwa ba Allah ubangiji ya tsare gaba ya k'are gsky gwara da aka lalata account din mutane ba gsky ina twins nasan yanzu an girma" murmushi Aira tayi ta ce Bari na had'aki dasu daga Inda take ta kwala musu kira da gudu Suka rigo Nihal ta ce "Cutie what happend? zaunar dasu tayi ta ce " ga Auntynku zaku gaisa"sannan ta fara karawa Nihal wayar ta ce "good Afternoon Aunty yakeke" Dariya Rahama tayi ta ce "Lafiya qalau my namesake ashe kunyi baki to ygd ya mom " tana lafiya ta fad'a tana shirin kada wa Aira waya ta maza ta amshe tana Harararta Dan ita ba Arman bace da zasu mata asara Naila ta karawa a kunne wayar na hannunta Bayan sun gama gaisawa ta ce oya to ku tafi Aje ayi wasa "ta cikin wayar Rahama ta ce" kai ji yanda yaran nan sukayi baki gsky anjima ba a hadu ba wlh k'ilama yanzu har anyi musu k'ani ko"Dariya Aira tayi ta ce "Zadai ayi musu gobe fa zamu shigo k'asar" Cikin farinciki Rahama ta ce "da gaske sis kice muna da manyan baki ina zaku sauka " Kano ina sa ran insha Allah"Allah ya kaimu insha Allah Ko bakizoba ni zanzo naga my twins har yanzu dai banga pic dinkiba bare inmun hadu mu gane juna"murmushi Aira tayi tare da tura mata pic d'inta me kyau ta what's app ta ce "Yau dai kinganni momcy" Sosai Rahama tayi mamakin yarinya ce ma Airar ashe "voice tayo "ta ce " wow daughter Ammafa kin hadu ba k'arya wlh dole twins suyo kyau dukda naga ba kamarki suke ba Ammafa bamai cewa kina da Aure wlh bare har ance kina da su Naila"murmushi kawai Aira ta yi ta tura mata da stiker Dariya Itama tambayarta tayi hotonta ta turo mata soi sannan taganta itama kyakyawa ce Masha Allah ga wayewa zatayi irin 21 years "voice Aira ta tura mata ta ce " Kaiii ashe dai momcyn tawa ba wasa Wajen kyau masha Allah insha Allah gobe damun Iso zankiraki da layin 9ja "Kawarta Jannat ta kira dake Abuja Itama sosai ta ja jinta shirun da tayi kamar yanda tayima Rahama bayani haka tayimata ita daman suna da hotunan juna Dan ita kadai Aira ta yarda take da hotonta itama Dan ta yarda da nutsuwartane Itama budurwace wayayya Nanko ta shiga murna Akan Aira idan tazo Itama zatazo ta ganta da twins amma ce da tayi mata message a what's app duk na jajanta ne take tura mata voice tayi cikin. Make murya tayi mata bayanin abunda ke faruwa " Sosai Amma ta damu kiranta a waya tayi Bayan sun gaisa ta ce "wayyo Allah ya k'ara kiyaye gaba wlh karkiga yanda na damu sosai wata da watanni ba a tare" Murmushi Aira tayi ta ce "Karki damu sis insha Allah kinkusa ganin twins dinki kusa dake" cike da zak'uwa amma ta ce "da gaske sis " Dariya Aira tayi ta ce "Kedai kisa ido kawai zamuyi surprise d'inki amma badan ta yarda ba Dan a tunaninta zolayanta ne take. Washegari Aiport na gano su Aira sosai tayi kyau cikin pink d'in Abaya Mai mugun tsada Fuskarnan tata ba komai sai asalin kyan da Allah yayi mata Ga cikinta d'aya turo saiya Kara yi mata kyauma hand bag rataye a hannunta Arman ke rik'e da k'aramar akwatinsu yana ja Twins ko wasa kawai suke suna tsalle A haka har aka fara kiraye kirayen suna Suka shishiga ba b'ata lokaci jirginsu ya d'aga 9ja Wanda Aira jinta take cikin Farinciki Twins ko a jirgima wasansu kawai suke suna harkar gabansu wasa suka dingayi da yara Wanda har maman wata noor suka k'ulla kawance da Aira saboda jinin yaransu da yazo d'aya harsukayi musayar number itama y'ar Abuja ce karfe d'aya tayi musu a 9ja kasancewar asubanci sukayo koda suka fito daga jirgin Aira jinta take cikin farinciki marar musaltuwa sai kuma fargabarta na had'uwa da Abba sosai gabanta ya fad'i Kasancewar a Lagos Suka fara sauka hakan yasa saida suka hau wani jirgin tukwana suka isa kano around 3 suna kano Sosai gaban Aira ga tsananta fad'uwa Hakanan ta fusge driver Arman ya kira ya kawo masa mota twins Sai tsalle suke suna murna zasuga Mummy "gaban Aira na tsananta fad'uwa ta kalli Arman ta ce " yaya ina muka nufa"gida cutie muje ki huta tukwana"Kasa tayi da kanta "Kai tsaye gidan Arman dake GRA suka nufa Bayan sunyi wanka sun huta Twins ne suka damu Arman da cewa " Hero ka kaimu muga mummy"Lallashinsu yayi ya ce "Sorry my twins ku bari sai gobe " Tuburewa sukayi hakan yasa ya kira Mummy wayarta kashe batamason zuwansu ba kallonsu yayi ya ce "Kunga wayarta a kashe ku kwanta ku huta Wanda ya Riga bacci shi zan fara kaiwa Wajenta " cikin saurin suka Haye kan sopa Tare da rumtse ido wai bacci yazo"Dariya Aira tayi kasa_kasa ta ce "Ai gwara da kayi mana maganinsu Dandananko baccin gaske ya kwashesu a lokacin ana isha I Aira salla tayi Bayan ta ciccibi twins ta kaisu bedroom Gado ta kwantar dasu Bayan tayi musu addua itama ta kwanta dandanan baccin gajiya ya kwashesu Arman koda ya dawo ya samesu Gado daya addua yayi musu tare da wucewa d'ayan bedroom d'in ya kwana. Washegari wajen 12 na rana Aira ta shirya ita da twins d'inta sosai tayi musu gayu cikin y'an kanti d'insu Riga da wando da suka matse red ba hula kansu sai Gashin kansu da akayi parking sai shek'i yake Itama shiryawa tayi cikin doguwar riga ta d'ora hijab d'inta mai hannu har k'asa green sosai hijab din tayi mata kyau A harabar gidan suka tsaya Arman ya fito da mota Suka shiga Kallonta yayi ya ce " ina muka nufa mom twins"gabanta na fad'uwa ta ce "Mu fara zuwa gidan Aunty Aysha hero" To ya fad'a tare da kama hanyar gidan Aysha Dan bai manta ba Suna isa suka fiffito da twins Kallonta yayi ya ce "zanshiga gari around 3 zanzo na daukemu" gyada mishi kai tayi a sanyaye tare da kama twins dake shirin nufa wani wajen knoking gidan ta fara minti Ukku taga anbude kallon mamaki Aysha ta dinga binta dashi ji take kamar mafarki itama Airar Kallon y'ar uwar tata ta tsayayi wara idanu Aysha tayi ta ce "Sis kece" Murmushi Aira tayi ta ce "Nice sis" Rungume juna sukayi a tare saikuma suka sanya kuka Aysha ta ce "Aira ina kika tafi kika barmu da kewa tsawon shekara Ukku da rabi" kasa magana Aira tayi sai kuka da take janye jikinta Aysha tayi tare da Kallon cikin jikin Aira wara idanu tayi ta ce "Sis ciki" Bata rufe bakinta ba taga twins Suna kallonsu"janyosu tayi tana mamaki taa ce "tare kuke sis" gyada mata kai tayi "D'aukar d'aya Aysha tayi tare da kama hannun Naila tace taho mu shiga ciki labarin nan sai anzauna kin sanyani a duhu da yawa" murmushin k'arfin hali Aira tayi suka shiga ciki a palour suka tarar da mijinta gaisheshi Aira tayi ya amsa mata cike da mamaki Bayan sun zauna Aysha ta kawo musu abun Tabawa twins ko tuni suka kama wasansu a wajen dining harsuna shirin yiwa Aysha b'arna tashi mijin aysha yayi yabar gidan dan yabarsu su sake kallon Aira tayi tare da kama hannunta ta ce "Sis yaran waye bani labarin abunda ya faru" Goge hawayenta Aira tayi tare da bawa aysha labarin komai da ya faru tundaga rayuwar gidanta ta Alh Yusuf har Zuwan Aurensu da Arman da yaran su Sannan sharrin da Akai musu Tayi mata rantsuwa akan basu tab'a aikata Alfasha ita da ARMAN ba"Aysha na kuka ta Rungume y'ar uwar tata ta ce "Allahsrk sis wlh na tausaya maki Abba mahaifinmune amma baiyi miki adalci ba Abba yana tsananta Abu da yawa fushinshi yana yawa yanzu Kinga ba bincike ba komai ashe haka abun yake"Aira na kuka ta ce " Sis Dan Allah fad'amun Gaskiya Bayan tafiyata Abba da Mamy basu tsinemun ba"Goge hawayenta Aysha tayi ta ce "basu tsine maki ba sis amma Abba ya Ce ya cireki a jerin yaranshi nan Tabawa Aira labarin komai da ya faru har Rashin lafiyar da Mamy ta dingayi a dalilinta" Sosai Aira ke kuka ta ce "Na shiga ukku ni Hajara sis ya zanyi da rayuwata wlh nayi nadama Yanzu kenan Abba ya cireni a yaranshi sannan ya rabaku dani" girgiza mata kai aysha tayi tana Hawaye ta ce "Sis fadarshi ta yarabamu bashi ke nuna zamu rabu dake ba muna tare da ke har gobe ke y'ar uwarmuce babu yanda zamuyi dake sannan koda ace zargin da aka maki Gaskiya ne bazamu rabu dake ba bare sharrine jibi da ikon Allah hada rabon yara Har biyu ga na Ukku " Sosai Aysha ta shiga Lallashin Aira harta samu ta daina kuka suka hirar yaushe gamo Waiwaye Aira ta dingayi ko zataga yaran Aysha amma shiru kasa daurewa tayi ta ce "Sis ina Yaran ko suna makaranta" Murmushi Aysha tayi ta ce "Bani da yara ko d'aya har yanzu sis Gaki k'anwarta ta Ukku hada yara biyu ga na Ukku Kinga ikon Allah Ko" Sosai Aira taji tausayin y'ar uwar tata cewa tayi "Allah ya baki kema me amfani sis"Ameen Aysha ta fad'a " rugowa Nihal tayi wajen Aira tare da hayewa kanta tana boyewa ta ce "Cutie Kinga Naila zata doken " Kallon Naila da ta biyota Da wayar chazar Aysha tayi sai huci take tana hawaye Aira tayi ta ce "naila bansan zalinci y'ar uwar taki zaki doka da abun nan Dan iskanci Ta fad'a a tsawace tare da amshe chazar tace " wuce kiban waje sarkin fad'a"kuka Naila ta fashe dashi tare da durk'ushewa ta fara burgima Aysha ce tayi saurin daukarta tana Dariya wai Aira ce da raba yara fad'a kallon Aira tayi ta ce "Ke kuma haka ake rabon fad'a saikiji me tayi mata kafin ki sasinta" Turo baki Aira tayi ta ce "Allah Aunty fad'ane da ita Dan taga ta fita k'arfi ita kuma sakaran tsorantama take ta fad'a tana dungurarwa Nihal kai data lafe jikinta " Dariya Aysha tayi tana Lallaba Naila harta samu tayi shiru ta ce "Uhm su Aira iyaye Ashe dai twins dinkine amma ta rude a kansu hhh kaji y’an soyayya yarankuma cutie suke cemaki kenan “Dariya Aira tayi ta ce "Ai har yanzu batasan ni bace sai ta ganmu k'watsam amma Aunty kina ganin naje gida ba matsala?Ajiyar zuciya Aysha ta sauke ta ce " bazance kije ko karkije ba sis amma zaki iya zuwa kidai je a b'oye kar Abba ya ganki firstly "Gyada mata kai Aira tayi wajen 3 Sukaji order Arman Bankwana Aira tayima Aysha Wanda twins harsun saba da ita suka fito Inda ta basu choculate sannan tacewa Aira Dan Allah ta dawo bayanin sanya mata number ta" da to Aira ta amsa mata cike da kewar y'ar uwar tata ta bar gidan suka shiga mota sosai gabanta ya fad'i koda suka shiga layin gidansu sosai gabanta ya shiga fad'uwa ta shiga jero duk addu'ar da tazo bakinta kallonta Arman yayi da suka kusa get d'in gidan ya ce "Kisa a ranki akwai nasara insha Allahu kinji my cutie" Cikin k'arfin hali ta gyad'a masa kai tare da bude kofar zata fita kallonta yayi ya ce "Da yaushe zanzo na daukeku "? Wajen 5 ko 6 ko?gyada mata kai yayi ya ce " ki kulamun da kanki Da my unborn nd my twins"murmushi ta sakar masa ta ce "kaima ka kulaman da kanka my hero a tare da twins suka fito da suke daka tsalle yau zasuga mom d'in Cutie Kallonsu tayi tayi murmushi ta kauda kai " Kallonsu yayi ya ce "My angels ba a yiwa hero bye bye" Dariya sukayi tare da d'aga masa hannu suka ce bye bye hero bakache mu gaishe maka da mom En cutie ba Kuma ma har dad enta yau jamu gani suka fada suna tsalle"y'ar Dariya yayi musu tare da cewa "To ku gaishemun da su" kama hannunsu Aira tayi tare da d'aga masa hannu ya wuce Tayi minti biyar tsaye tana tunanin yanda zata tunkari get d'in gidansu haka nan dai tayi shahada tare da nufar bakin get d'in gidan gabanta na tsananta fad'uwa Dak'yal ta iya d'aga hannunta ta yi knoking mai gadi ne ya leko tare da bud'ewa turus yayi ganin Aira gabanshi wara idanu yayi cike da mamaki ya ce "Hajiya kece da gaske" Murmushin K'arfin hali Aira tayi ta ce "Ni ce Baba Su Mamy na ciki?........✍🏿 *Tofah yau ga aira a gida me kuke tunanin zai faru ABBA zai yafe mata kuwa koko yana nan kan bakanshi*?? *Ni da Yaya Arman it’s for sale akan Naira 200 kachal to 07026166536 ki biya ki karanta cikin nutsuwa da kwanciyar hankali nida yaya Arman ko da kudinka saida rabonka har yanzu kuna da damar sayanshi akan garabasar da na saki 200 daga randa ya zama complete document zai koma 400 ne* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/20, 23:17] Hajo hajo: 🅿️........*115&116* ....Ni ce Baba Su Mamy na ciki"?Eh suna ciki Alhaji dai naga ya fita"Ajiyar zuciya Aira ta sauke jin Abba bayanan cikin Sauri ta shiga cikin gidan twins na biye da Ita "sosai take kallon gidansu tana jin wani dadi gidan da rabonta dashi shekara kusan hud'u A bud'e ta tarar da Palourn Cikin fargaba da shiga twins na biye da Ita suna surutansu Tana tura kofar amma da Mama Sai Haidar ta tarar a palourn ja tayi ta tsaya suma duk Kallon mamaki suke binta dasu amma Ce tayi k'arfin halin cewa " Sis kece da gaske ko gizau ne nake gani"Tuni hawaye suka wanke fuskar Aira gyada mata kai tayi "ai da gudu ta rugo ta Rungumeta Itama Rungumeta tayi tana jin kewar y'ar uwar tata sun jima suna kuka kafin suyi shiru wara idanu amma tayi ganin twins Bayan Aira da mamaki ta isa garesu tare da dukursawa ta ce "naila Nihal kune nake gani gabana kodai mafarki nake" Dariya Aira tayi ta ce "sunedai gabanki sis" da mamaki ta ce "me kike nufi Aira me ya hadaki da Yaran nan" Dariya tayi ta ce "Ai yarankine sis" Mama ko duk mamaki ya gama cika ta ga mamakinta na ganin Aira da wani cikin cewa tayi ta yi"mufa in sanyamu a duhu Aira Yaran nan dai ko ba a fad'a ba daka gansu kasan na Arman ne yaushe kika haihu bansaniba Bayan baki da Aure"Goge hawayenta Aira tayi tare da cewa "Mama ina yini" Haidar ne Shima da ya gama mamakinshi ya rugo suka Rungume juna yana hawaye ya ce "Yaya Aira me yasa kika tafi kika bar gida tsawon wannan lokaci" kama hannunshi Aira tayi ta na Goge hawayenta ta ce "Nima ba haka naso ba bro k'addarace ta zabamun haka Ina Mamy ta fad'a tana hawaye" D'akinta ya nuna mata Ai cikin Sauri Hartana hadawa da gudu Tayi d'akin tana turawa ta samu Mamy bakin Gado da gudu Aira ta Ruga tare da Fad'awa kan Mamy ta Rungumeta ta fashe da kuka Mamy da jin mutum kawai tayi a kanta ana kuka sosai tayi mamaki"Juyowa tayi ta duba fuskar aira taga ita d'ince wara idanu ta yi ta ce "Aira tace nake gani ko gizau" Tana kuka tana hawaye ta ce "Mummy Airankice Mamy Dan Allah ki yafemun " ta k'arasa fad'a cikin wani irin kuka "Itama Mamy kuka ta sa tare da Rungume y'artata tanajin soyayyarta har cikin ranta ta kasa koda magana Twins ne da suka shigo biyo mamansu Sakin rungumar Mummy tayi tare da dafa kafadar Aira Kare mata kallo Tayi Tare da Kallon cikin jikinta gabanta na tsananta fad'uwa ta ce " Aira ciki?meya hadaki da ciki Bayan ba Aure gareki ba"hawaye nabin k'umcinta Aira tayi k'asa da kanta twins ne suka zo suka D'are kanta Nihal ta ce "Cutie mom ina Mom en taki take"Nuna musu mamy tayi tana Hawaye tare da K'asa da kanta " Kallon mamy sukayi a tare Itama mamyn kallonsu take ta kasa koda magana Da zaka duba yanda zuciyarta Take tofa da kila tana Daf da fashewa saboda fargabar yaran nan nan da Cikin nan Kardai a waje ta samesu "cikin k'arfin hali ta ce " Aira ina kika samu yara da ciki keda ba Aure gareki ba fad'amun abunda ke faruwa kinsanyani cikin duhu"Goge hawayenta Aira tayi tare da kama hannun Mamy tana kuka ta ce "Mamy wlh duk abunda Alh Madugu ya fad'a muku wlh sharrine suka mana bantaba zina ba......Duka ta bawa Mamy labarin komai bata boye mata ba har zuwa Aurensu da iyayen Mummy suka hada har zuwa yaran da suka Haifa. Koda ta gama bata labarin Ajiyar zuciya Mamy ta sauke ta ce " Amma Gaskiya Hajiya Fatima ta cika uwa ta gari ba ku kadai ta taimaka ba ni kaina ta taimakeni Allah ya saka mata da gidan Aljanna yanzu Dan Allah ina da za a akai rabon yaran nan da Saidai ku haifesu a waje Allah na gode Maka da komai yazo yanda banyi tunanin ba sannan ta kalli twins tana fara a ta ce "Ina takwarar tawa da takeson Gani na " Nihal cikin Sauri ta Ruga tare da Rungume Mamy itama mamyn Rungumeta tayi ta ce "oyoyo takwara ta yau dai Gaki ga takwararki ko?gyada mata kai Nihal tayi Ta na mata Dariya tare da shafa Fuskarta " Naila ce ganin Mamy batayi mata magana ba ta fashe da kuka tare da Fara didiira kafa "duk kallonta suka tsayayi Aira ta ce " me aka miki Naila "Tana kuka ta nuna Mamy ta ce " ba mom enki bace ta kyaleni ta dauki takwalalta Nima ki kaini wajen mom tunda itace takwala ta kuma bazan kala zuwa nanba tunda ni bata so na"Dariya mamy tayi tare da janyota ta Rungumeta ta ce "Sorrry Mamy tayi laifi ayi hakuri ina sonki sosai kema kinji" Lokaci guda Naila ta fara Dariya tare da Fara tsalle jikin Mamy ta ce "I love you so much mom En cutie" Dariya mamy tayi tanajin soyayyar yaran a ranta ta ce "I love you too yaran kirki" Nihal ko Lafewa tayi jikin Mamy kamar daman ta Santa tana Tsotsar yatsa kallon Aira Mamy tayi ta ce "Karkiga yanda Halima ta rude kullum bata da zance sai Oum twins Da twins ashe dai yarantanema Akwai lokacin da ta nunamun hotonsu har ina fad'a ina cewa baki da magaya Aira me ya kaiki d'ora yaranki a media " Murmushi tayi ta ce "Mamy ai yanzu na daina" Ai tun lokacin da kika daina karkiga yanda ta damu lafiya dai ko"Wlhko y'an shan jinine suka kamasu twins nan ta bata labarin abunda ya faru"Subhanalla Mamy ta fad'a ta Ce "Aidaman nasan anrina Allah ya kiyaye gaba sannan ki dinga sanya musu hula in zaku fita jifa gashinsu waje tubarakalla sunyo gashinki Sai a cinye miki yara a banza " murmushi kawai Aira tayi tana wasa da yatsun hannunta Amer ne ya shigo Bayan dawowarshi daga Tahfex Wara idanu Aira tayi ganinshi da mamaki ta kalli Mamy ta ce "Mamy amer ne ya girma haka" Dariya Mamy tayi Dan yau cikin farinciki ta ke ta ce "Wlhko ai yaushe rabonki dashi" Amer ko kallon mamaki yakewa Aira Dan baisan taba wajen Mamy ya nufa Tare da Kallon twins dake cinyarta Dariya yayi musu Suma suka mayar masa kallon Mamy yayi ya ce "Mamy ina kika samo mana yara masu kyau" Dariya Mamy tayi tare da nuna masa Aira ta ce "yaranka ne auta kaga mamansu ka ganeta?Kallon Aira yayi da itama shi take kallo Ya girgiza kai ya ce " a a a Mamy bansan taba amma naga tana kama da Abba kuma ina ganin hotonta"to yayarkace itama Nina haifeta wannan kuma yarantane aidai kasan Ayra a baki ko?wara idanu yayi ya ce "Lah Mamy Aunty Ayra ce Sannan ya Ruga ya Rungumeta Itama Rungumeshi tayi ta ce " Ah lalle autan Mamy ya girma "Dariya yayi Inda yaje Yayi tayiwa Su twins wasa suna Dariya sunk'i sauka daga kan Mamy sai liliyarta suke Haidar ne ya shigo shida amma tare da plate a hannunsu Amma tazo ta zauna jikin Aira tana kallonta ta ce " sis oum twins ga abincinan kici ga ya Ummy na kirata hada saurinta ta ce tana hanya Ashe dai surprised Dina da akace za ai da gaske ne"Dariya Aira tayi ta ce "Ai cewa nayi a bazata zanyi maki yaudai gaki ga twins dinki"mikawa twins hannu Amma tayi tana musu murmushi Naila ce ta Ruga Wajenta Nihal ko tayi luf jikin takwararta daman ita uwar son jiki ce fita amma da Naila sukayi Kallon Haida Ayra tayi da yayi tsaye yana Danna waya ta ce "Hmmm su Haidar manya tunda nazo sai daddauremun kake" Mamy ce cikin fad'a ta ce "Rabu dashi uban bak'in hali kamaga y'ar uwarka ko farincikin ganinta bakayi ni wuce ka bani waje kazo kayima mutane tsaye kana Danna waya" Murmushi Haidar yayi ya ce "Sorry Mamy sannan ya kalli Aira ya ce " Tunfa a palour muka gaisa sis "Amsar wayarsa Aira tayi ta ce " Kayi waya kenan bari na d'auki number ka D'aukar number tayi save Shidai Haidar mamaki yake Inda Aira ta samu yara Suna haka Ummy ta shigo da gudu Suka Rungume juna itada Aira sai murnar ganin juna suke dukda abokiyar fadantace itama saida tayi mamakin jin twins yaran Aira ne Palour Aira ta fito Nan Mamy tayiwa Su Mama bayanin da Aira tayi musu sosai suka jinjina Abun kuma sukayi farinciki da abunda akayi tunani bashi bane Mama ma sosai tayi fad'a ta ce "da yanzu ina za akai rabon yaran nan Haidar ma sai yanzu yaji sanyi harma ya d'auki twins Dan dazun dukda yayi farincikin ganinta amma Yaji haushin Ace yayartashi tayi abunda ake zargi ashe ba haka ba nan aira ta tambaya ina inna akace mata batanan tayi tafiya kauye ziyarar yan uwa sosai aira taso ta hadu da inna Suna palour ana jajinta abunda ya faru Amma na bawa twins abinci Aira ce ta ce “sis wai Ina makarantar kin gama?Murmushi amma tayi ta ce “two months kenan da kammala degree dina sai jiran result kingani abunda nake fada maki yanzu fa bakinki sec sis Da yanzu kema kingama degree dinki “Dariya aira tayi ta ce “Ni kinga degree dina nan “ta fada tana nuna Twins duk Dariya akai Mamy tace “kujimun marar kunya’duk Dariya akai sosai aira ta tsinci kanta cikin farinciki ganinta cikin yan uwanta da mahaifiyarta ana wasa ana dariya ana haka Suka ji sallamar Abba sosai gaban Aira ya fad'i Ganin shigowar Abba Mikewa tayi a matuk'ar firgice Shima a mamaki Abba yake kallonta cikin tsananin b'acin rai ya nunata da yatsa ya ce Uban me ya kawo wannan abar gida na da izininwa " Tuni Aira ta fara hawaye Bayan Mamy ta boye ta ce "Dan girman Allah Abba kayi hakuri ka yafemun na tuba " Mama ce ta mik'e ta ce "Kayi hakuri Alh ka sauraremu’’ Tsawa ya daka mata Tare da nuna Aira da yatsa ya ce "Minti d'aya na baki ki fitarmun daga gida bana k'aunar ganin bak'ar Fuskarnan taki a cikin gidana " Sosai Aira take kuka ta ce "Dan girman Allah kayi hakuri Abba Mamy ma tana hawaye ta ce " Kayi hakuri Abbansu Ka yafe mata ka nutsu kaji komai a sannu"Tsawa ya daka mata ya ce "Na karajin bakin wani cikinku yana ban hakuri wlh zakuyi nadamar abunda zanyiwa mutum Sannan ya sakewa Aira Tsawa ya ce " bazaki kwashi rubabbun kafufunki ki barmun gida ba saina sauya maki kamanni y’ar iska a zatonki kingama yawon karuwancin naki zaki dawomun gida na karbeki ai nariga na dade da cireki a jerin yaran da na haifa ki gaggauta barmun gida ko na kira jami’an tsaro su fitarmun dake "Cikin Sauri Aira ta mik'e dak'yal tanajin zuciyarta kamar zata rabe gida biyu ta ce "Abba zan tafi kamar yanda ka koren kuma bazansake dawowaba har saika yafemun amma Bazan gaji da neman yafiyarka ba " Kallon twins tayi da duk sun rude ganin Abba na yiwa mom D'insu Tsawa ta ce "ku taho mu tafi" Da Sauri suka taho Wajenta suna boyewa Dan sun tsorata da Abba hanyar kofa ta nufa tana kuka Suma Duka y'an d'akin kuka suke musamman Mamy cikin kuka ta ce "Alhaji ba Inda zata fushinka bazai rabani da y'ata ba " Saidai ki bita Abba ya fad'a yana nuna mata hanya"Cikin fushi Mamy ta mik'e zuciyarta na zafi ta ce "Aira jirani wannan Karin bazan lamunta irin abubuwan da akayimun a baya ba na Shanye Saidai hakan ya zama silar lalacewar alak'armu tana gama fad'ar haka ta dauki hijab d'inta " Juyowa Aira tayi tare da girgiza mata kai ta ce "Dan Allah Mamy kiyi hakuri ki koma banason na zama silar Mutuwar aurenki kiyi hakuri zantafi ni kad'ai amma Dan Allah ki koma" girgiza mata mai Mamy tayi ta ce "Aira bazan yarda ki tafi cikin halin nan ba Ni uwace zan iya fuskartar ko wani irin Abu amma Bazan barki ki tafi ba " Durk'ushewa Aira tayi tare da fashewa da kuka ta ce"Mamy Dan Allah ki koma ni banason na dinga zama silar rugujewar farincikinku zan tafi kamar yanda Abba ya fad'a duk ranar da ya huce zan dawo tana gama fad'ar haka ta kama hannun twins tana kuka sosai ta fita daga gidan Gaba d'aya Mamy ko binta tayi dak'yal Mama ta lallabeta ta maida ita ciki ta hanata fita Sosai take kuka tanajin haushin Abba Aira ko na fita dakalin kofar gidansu ta zauna tare da fashewa da kuka sosai takejin zafi a cikin zuciyarta twins ma kukan suke sosai a jikinta Naila nacewa "Mom kiyi hakuli Mu tashi mu bal musu gidanchu Tunda Dad enki baya chonki muma I hate him kuma duk sanda na gilma saina rama maki" rufe mata baki Aira tayi tama kasa koda magana sai kuka Yaran abun tausayi suma kukan suke Ganin mamansu na kuka a haka ARMAN yazo ya samesu cikin wannan halin sosai Shima hankalinshi ya tashi a mota ma Aira kuka kawai take ta kasa koda magana Twins ne suka ce"Hero Dad en mom ne ya chanyata kuka sai sannan arman ya gane Dalilin kukan na Aira Lallashinta ya fara amma taki magana sai kuka kai tsaye gov house suka wuce saboda yayi waya da mummy ta ce suzo nan suna isa Bayan sunyi parking a harabar Part d'insu suna fitowa Aira na hawaye har lokacin a harabar gidan suka ci karo da Mummy da Daddy sun fito Da gudu twins suka Ruga suka Rungume Mummy itama rungumesu tayi tana farincikin ganin jikokin nata Daddy ko tsaye yayi yana binsu da Kallon mamaki Kallon Mummy yayi ya ce "me ya kawo wadannan gidana" Ajiyar zuciya ta sauke ganin cikin nutsuwa yayi maganar ta ce "zanyi maka bayani idan ka nutsu Wannan yaran da kake gani jikokinkane yaran Arman ne Wanda suka Haifa da Aira Yaran sunna ne kuma y'an halak "sosai dad yayi mamaki Nihal ce tazo wajenshi tana Dariya ta ce " Dad en hero"Murmushin k'arfin hali yayi mata tare da daukarta Dan yanason yaran sosai tun kafin yasan jinin shine amma hakan bai hanashi tunowa da abunda Arman yayi masa ba Kallonshi yayi ya ce "Fitarmun daga gida karna k'araga kafarka ka tako cikin gidan nan bani bakai na Riga na shafe da labarinki Ubanme ya kawoka gidana" Rumtse ido Arman yayi yanajin zafi a ranshi zuciyarshi na tafarfasa cikin zuciya ya kalli Aira ya ce "Shiga muje " Shiga tayi tana Hawaye Kallon twins yayi dake hannun iyayen nashi ya ce "Ku taho mu tafi" mak'alewa jikin Su sukayi Alamun basu zuwa Cikin fad'a Mummy ta ce "Banson iskanci Arman bazaka bawa mahaifinka hakuri ba kai uban zuciya shine ma zakayi fushi to ka tafi d'in ko warce yaran zakayi a hannumu ka nuna mana kai ka haifesu ba muba" Arman baicewa Mummy komai ba sai Juyawa da tayi tare da bude mota da karfi ya shiga tare da tada motar ya figeta da gudu Tsaki Mummy taja tanajin haushin Arman yanda taga Daddy Ya sauko da ya bashi hakuri zai iya hakura Daddy ko sosai ranshi ya b'aci fasa fitar da yayi yayi ya kalli mom ya ce "Muje ciki " suna shiga Mummy ta bashi labarin abunda ya faru na hada Auren su da tayi sosai Abun ya bashi mamaki yanda ta rik'a boye mai Abubuwa har a zuciyarshi baiji zafin Mummy na hada Auren nan da tayiba tunda gashi hada zuri a da dole dai sai an haifi yaran amma Yaji zafin Arman yanda yayi masa hakan yasa ya karajin zafi a ranshi Idan kuma ya kalli yaran sai yaji soyayyarsu a ranshi ga yanda Nihal ta lafe jikinshi kamar daman ta sanshi sosai Mummy taji dad'in yanda Daddy bai nuna wani b'acin ranshi ba sai shiru da yayi Yana nazarin abubuwa da dama Jin ana kiran Magriba ya sanyashi Aje Nihal zai tafi masallaci taki barin jikinshi murmushi yayi mata ya ce "Amaryar tawa uwar son jikice kenan salla zanje inyi" Dariya Nihal tayi kamar tasan me yake nufi ta ce "Dad en hero kai bazaka dinga yiwa hero fad'a ba shi dad en Cutie mugu ne Kuka ya sanya mom Kuma bama sonshi saina halbeshi da bindigata" Girgiza kai dad yayi tare yimata murmushi ya ce "Eh bari na dawo daga salla saimuyi labarin" Mummy ko girgiza kai tayi gsky abunda Abba yake baya kyautawa gashi har yara kanana zasu kullaceshi Nihal ko dining ta nufa tare da Fara b'arna da abinci Kallon Naila da tayi shiru kamar mai tunani Mummy tayi ta ce "My takwara me ya faru kinyi shiru yau ba surutun kenan" Hawaye Naila ta fara ta ce "Mom ina cutie zataje kuka take dad enta baya chonta ya sata kuka Please kije ki bashi hakuli kice Yadaina sanya mom enmu kuka kuma mu bajamu k'ala juya wajensa ba" Saida zuciyar Mummy ta karye jin yarinya k'arama na irin maganganun nan Gashi damuwa k'arara a fuskarta Goge mata hawayen tayi ta ce "Dad d'inta itama yana sonta Naila laifi tayi mashi shiyasa yayi mata fad'a kuma yanzu ya hakura sunje su dawo muje kici abinci Kinga y'ar uwarki wasanta take ko " ta fad'a tana nuna mata Nihal dake b'arna dak'yal ta samu Naila itama ta waske Inda take ta basu abinci sukaci sosai suka saki jiki da ita suka dinga mata surutu da labarai Wanda tare da Daddy suka dinga musu dimi Saidai suyi Dariya Dan labarin gida kowanne saisun basu. Arman ko cikin fushi kai tsaye hanyar Kaduna ya d'auka ranshi na Mashi mugun zafi shi abunda yafi damunshima irin yanda yaga cutie d'inshi hankalinta ya tashi sun wuce Zaria Aira ta farajin ciwon baya da mara tun tana daurewa har ta kasa cije baki tayi tana Salati da mamaki Arman ya ce "Kina lafiya cutie me ya sameki" Kallonshi tayi yana nukurkusa ta ce "Cikina yaya bayana kamar zai balle" Sosai ya shiga damuwa Cikin kid'imewa ya tsaida motar Mummy ya kira tana d'auka cikin tashin hankali ya ce "Mummy kinganmu nan hanyar Kaduna Aira ba lafiya bayanta da cikinta wai ciwo" Subhanalla Mummy ta fad'a ta ce "ku hanzarta isa Kaduna ka kaita Asibiti zankira Halima ta sameku nakuda ce take" Da mamaki ya ce "Amma Mummy ba watan Haihuwarta bane" Eh inaga tashin hankalin da ta shigane ya turo nakudar ka maza ku tafi karta galabaita"Cikin Sauri yace to mom tukwana ya tada motar harsuka isa Kaduna Aira na Abu d'aya suna isa ya wuce da ita wani private hospital.........✍🏿 *Ni da Yaya Arman littafin kudine akan 200 kachal ta wannan number 07026166536* _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/21, 09:47] Hajo hajo: 🅿️........*117&118* Wani private hospital suna isa kai tsaye labour room aka nufa da ita ya nan yana safa da marwa yaji kiran Mama Halima Bayan ya d'auka ya shaida mata asibitin da suke ba ayi minti goma ba sai gata cikin rudu ya nuna mata d'akin da take Kallonshi tayi ta ce "kun taho da kayan haihuwarne?a a Mama bamu taho da komai ba " To.ka maza kaje ka sassayo da abunda za asa jaririn da komai nikuma bari naje "To ya fad'a duk ya rud'e tare da tafiya neman abunda Mama Halima ta fad'a ita kuma ta shiga ciki Inda ta samu Aira na labour sosai Sannu ta dinga mata a lokacin Tara na dare Karfe sha biyu Aira ta haifo d'anta namiji kyakyawa dashi mai tsananin kama da ita Bayan ta haihu a lokacin Arman ya kawo jibgin kayan da ya sayo hamdala kawai yake da yaji ance ta haihu Bayan anshirya jaririn itama Aira anshiryata d'akin Hutu aka wuce da ita saboda galabaita da tayi Gashi kuma taso tayi ikilamsiya saboda jininta da yahau Allah dai ya kiyaye Arman sosai ya ji soyayyar yaron a ranshi koda ya daukeshi cikin farinciki Yayiwa Allah Godiya Yau shine da yara har Ukku Tambayar Mama Halima Aira yayi ta ce " bazai samu ganinta ba saita huta sannan ta amshi jaririn ta ce "sauran kayan da ka jibgo ka wuce dasu Gidana sannan kace Hafsa ta gyara d'akinsu " to Arman ya fad'a nan takura ya shaida wa Mummy haihuwar itama Sosai tayi farinciki marar musaltuwa Aira ko sosai ta huta duk galabaice take Dan bama tasan abunda ta Haifa ba Mama Halima Tabawa jaririn ruwa gashi baiyi kuka sosai ba ranar Aira kwana tayi tana bacci Dan Dr d'in saida yayi mata allurar bacci saboda jininta da yau ya sauka washegari itace bata tashi ba sai 10 koda ta tashi Su Hafsa sunzo duk Sannu suka dinga mata Har Arman da yake tausayawa cutie d'inshi ganin yanda tayi firi_firi Mama Halima tayi mata wanka ta gasata sosai Bayan sun shirya ta bata yaron akan tayi feeding dinshi sosai Aira ta tsaya Kallon Yaran tanajin soyayyar shi kamar yanda takeson twins a zuciyarta ta ce "Allah ya raya munkai " a fili kuwa shiru tayi saboda nauyin Mama Halima da takeji Bayan an b'ata tayi Kari me kyau A yammar ranar aka sallamesu ta koma gida duk tayi shiru bata son magana sosai saboda ciwon kan da take "Wanda saida aka rubuta mata magunguna akan ta dinga sha. Washegari Mummy tazo ita da twins a lokacin Aira na D'aki tana kwance Kanta banda ciwo ba abunda yake Dan tunda ta haihu take wannan ciwon kan Mummy ta shigo Tare da twins dak'yal ta tashi tana kirkirar murmushi ta ce " Sannu da zuwa mom"yawwa daughter ya jikin naki barka ko Allah ya raya k'asa da kanta Aira tayi Twins ne sukaje Wajenta Suna mata murmushi itama mayar musu tayi Naila ta ce "Sannu cutie mom ya jiki baby boy d'in da muka gani namu ne ko"? Itama Nihal cewa tayi " Mom ai boy dinmune ko wai Mama tace bazata bamu ba ta fad'a tana turo baki"Dariya Aira tayi ta ce "sarakan surutu " Dariya Mummy tayi ta ce "Kunga kubar maman taku ta huta" k'iyawa sukayi suka D'are Aira Girgiza kai tayi sannan ta Kalleta ta ce "Ki fad'a abubuwan da kike buk'ata a sunan daughter saina taho maki dashi Dan anan za ayi sunan tunda naga jikin naki ba adinga yawo dake ba " Kasa tayi da kanta ta ce "ba komai Mummy duk yanda Mummy tayi Aira ta fad'a abunda takeso kiyawa tayi ta ce komai ma ta yanke yayi " Ita Mummy duk sai ta bata tausayi ganin irin sanyin da tayi Lallashinta ta dingayi gami da nasiha Cikin hikima "Da yamma Mummy suka wuce tare da twins dan yanzu sunyi mugun sabawa da mum " da dare Aira na kwance tana kallon boy d'inta Arman ya shigo Dagowa tayi ta Kalleshi da murmushi a fuskarsa ya zauna tare da d'aukar jaririn ya ce "Sorry my boy yau bamu gaisa ba ko to ya jikin mom d'in taka" ya fad'a yana kallon Aira ya ce "ya jikin cutie" Murmushi ta masa ta ce "Alhamdulilla" "Allah ya k'ara maki lafiya uwar y'ay'ana yasa kaffarane " Ameen ta fada "Huduba tayima yaron Bayan ya gama Kallonshi Aira tayi ta ce " wani suna ka sanya masa "Aliyu Haidar " Munyiwa Bappa takwara Saboda shi ya zama silar samun wannan farincikin namu "Murmushi Aira tayi Tabbas hakane ta ce " Allah ya raya my hero ka kyauta kuwa "Sun tab'a Hira cikin so da k'aunar juna sai wajen 11 yabar D'akin da Haidar a hannunshi saboda yaron baida rigima Sosai Arman keson Haidar saboda kamannin cutie d'inshi da yayo " Hafsa ce ta shigo d'akin da farfesu a hannunta ta ce "Sis gashi Mama ta ce kisha karki sake tazo bakici ba" Dariya Kad'an Aira tayi ta ce '"Uhm my Mama kenan"Zaunawa Hafsat gefenta tana mata hira Bayan Aira ta cinye Kallon Hafsa tayi ta ce "Hafsa Dan Allah aroman wayarki zanyi kira banda layin nan k'asar" Mik'a mata wayar tayi number Aysha Ta dannawa kira Bayan ta d'auka "Aysha ta ce " Sis kina lfy dazu amma ke fad'amun Abunda Abba yayi maki wlh banji dadi ba yanzu kina ina?Goge hawayen da suka zubo mata Aira tayi ta ce "Ina Kaduna sis Na haihu ina gidan Mama Halima" Cikin farinciki aysha ta ce "Wow masha Allah me muka samu" Baby boy "ta fad'a kasa kasa" kai amma nayi farinciki wlh Allah ya raya insha Allah gobe Nida Ummy zamu taho har sai anyi suna tukwana bari nafadama honey Babban Albishir murmushi Aira tayi Bayan ta katse kiran number Mamy ta kira a lokacin Mamy sun gama fadansu da Abba tana d'aki Taga kiran Hafsa jin muryar Aira ya sanyata sauke ajiyar zuciya ta ce "Kina lfy Aira tunda kika tafi hankalina bai kwanta ba" Ajiyar zuciya Aira ta sauke ta ce "Ina lafiya Mamy ina Kaduna Ma gidan Mama Halima" Ajiyar zuciya Mamy ta sauke ta ce "Alhamdulilla gwara da kikaje Chan Dan Allah kici gaba da hakuri ki kwantar da hankalinki ba ason mai juna biyu na damuwa Kinga yanda kike " Murmushin K'arfin hali Aira tayi ta ce "Mamy ai na...sai kuma tayi shiru tanajin nauyin abunda zata fad'a " Dariya Hafsat tayi tare da Amsar wayar ta ce "Mamy so take ta ce maki ta haihu tun jiya mun samu baby boy" Cike da farinciki Mamy ta ce "Kai Alhmdllh amma nayi farinciki wlh Allah ya raya yanzu wannan cikin nata Har isa haihuwa nazata da saura " eh wlh Mamy Naji Mama tace ba watan Haihuwarta bane kawai tension ne ya kawo nakudar kuma ma tunda ta haihu bata da lafiya ciwon kai take kullum ikilamsiya taso ta sametama Allah ya kiyaye Amma yanzu da sauki "cikin tashin hankali Mamy ta ce " Subhanalla Oh ni Rahama Kenan Bata da lafiya bata wayar"Hararar hafsat Aira tayi ta ce "wa yace ki fad'a mata kinsan zata tashi hankalinta " A lokacin Mama ta shigo "Amsar wayar Aira tayi ganin yanda Mamy ta damu ta ce " Mamy lafiya ta fa qalau karya take"Sosai ta kwantarwa da Mamy hankali ganin yanda ta rude Hartana cewa kodai ta taho dak'yal ta samu hankalinta ya kwanta "Bayan sun gama wayar mik'awa Mama Halima wayar Aira tayi nan suka shiga gaisawa da Mamy Inda Mamy tayi mata Godiya Ta ce " bakomai ai Aira y'atake a Wajenta abunda zatayiwa Hafsat dole shi zata mata nan suka jajinta abunda ya faru a baya Mamy ta ce "Wai kina sanin kema bakisan abunda ke faruwa ba sai yanzu" Girgiza kai tayi ta ce "Wlhko banida masaniya komai Kawai sai kirana Hajiya Fatima tayi akan naje Asibiti sai jiya da tazo take fad'amun abunda ke faruwa na ce " ai da ta fad'amun tunda dai nima da Bayan goyon abun zan bada Allah dai ya kyauta ya kawo mana karshen AL amarin nan"Ameen Mamy ta fad'a Bayan sunyi bankwana Mama Halima ta Kali Aira ta. Ce "ki daina sanya damuwa a ranki Mamana jifa kin haihu keda zakiyi k'iba kiyi kyau amma ramewa kike " Kasa tayi da kanta ta ce "To Mama" Bayan fitar Mama kulli Aira ta kaiwa Hafsat ta kauce tana Dariya Hafsat ta ce "Wlh sis mamaki nake wai muna sa anni amma kece hada yara ukku" Dariya Aira tayi ta ce "me yafi son ranki kema ki fito mana da miji kawai musha biki" murmushi Hafsa tayi tana far da ido ta ce "Ah bakisan an sanya aure na ba ni da yaya omar" wara idanu Aira tayi ta ce "wanne yaya Umar din " Dariya tayi ta ce "naku mana " Sosai Aira tayi mamakin ashe soyayyar Hafsa da yaya omar kamar wasa ta zama gaske sosai kuma tayi farinciki da hakan suna cikin hirar ya kiraa Inda Hafsa daman ta fad'a masa komai a waya Aira Tabawa wayar sosai yayi farincikin jin muryar y'ar uwar tashi nan yayi mata barka tana jin kunya Daga karshe ta ce ya gaishe da Aunty Khady Dariya yayi ya ce "Abokiyar fad'ar taki zakice zataji insha Allah gobe zuwa jibi zanzo naga jikin naki kinji y'ar kanwata Allah ya raya mana boy" Dariya Aira tayi ta ce "To yaya Allah kawoka lfy tukwana ta mik'awa Hafsat wayar saida suka gama shan love d'insu tukwana suka yi bankwana Kallon Hafsa Aira tayi tana Dariya ta ce " zakici gidanku hannun basamudiyar Matar nan Dan wlh ta zauneki saikin hango k'abari ni zan baki labarinta"Sosai Hafsat ke Dariya hada rik'e ciki ta ce "yarinya kedai zatayiwa taganki haka kamar fara amma ni kam Saidai mu chashi juna sannan ma ina zan ganta muda ba gida d'aya zamu zaunaba ya ce " gida zai raba mana"Nan suka cigaba da Hira har bacci ya kwashesu . Washegari kamar yanda su Aysha suka fad'a ita da Ummy sukazo daga gidajen mazajensu Sosai Aira tayi farincikin ganin y'an uwan nata nan suka shiga d'aukar Haidar suna yabawa da kyan yaron Aysha ji take inama nata Har saida tayi hawaye a b'oye Mamy duk sanda taso tazo Abba ya hana Dan ta fad'a masa Aira ta haihu ya ce "bazataje ko ina ba cikin su Duk Wanda yaje a bakin aurenshi Mamy Kad'an Ya hana ta tafi in banda Aunty Ramlat da ta kira ta dinga mata nasiha akan ta zauna ita zasuje gobe ayi komai dasu ta kwantar da hankalinta a haka suka samu Mamy ta zauna Amma taso taje Amma ganin yanda Abba ya hana iyayensu ma zuwa ina ita ina tunkarar zuwa. Yayyun Mamy Duka saida sukaje kd din Har Matar Yayanta ana jibi suna sukaje Wanda hakan sosai yayiwa Aira dad'i koba komai wannan Karin akwai dangin mahaifiyarta da na mahaifinta a sunan y'an uwan mummy ma na yola duk sunzo Ranar suna yaro yaci suna aliyu Haidar k'aton sa Arman ya yankawa d'an nashi sosai a wannan sunanma yayi b'arin kudi Aira ko shigar da tayi ma fad'ar tsadar da kyaun kayan b'ata baki ne Sosai tayi kyau dukda bata da walwala saboda batajin dadi tunda ta haihu k'arfin hali ne kawai take haka akayi taron suna aka gama lafiya Bayan anyi bishshar kudi Mummy ma sosai ta taka rawar gani a sunan Haidar Wanda Daddy ma ya bata gudummawa mai tsoka da zata taho tare da twins sosai suka sha gayunsu nan aka shiga musu hotuna da dare Aira na kwance saboda hayaniyar mutane ya sanya kanta tsananta ciwo Mummy Ce tazo da kanta Tare da mik'ar da ita ta bata magani ta sha su Aysha tayiwa magana akan a barta ita kadai ta huta Haidar ma daukeshi Mummy tayi tare Madarar da aka fara basa ta ce "Shima bari mu kwana dashi Jinin naki ina ganin har yanzu yaki sauka kodai sai mun koma asibiti" girgiza kai Aira tayi ta ce "a a a Mummy ina ga hayaniyar mutane ce zuwa safe na kwanta zai sauka " saida taga kwanciyar ta tukwana Mummy ta mik'e tare da rufo mata dakin. Washegari koda ta tashi ciwon kan da sauki Bayan Angama soye soye y'an uwan Mamy da Mummy duk suka wuce Bayan ancikasu da Abubuwan arziki Arman ko yana Abuja Dan ya koma kan aikinshi Ganin irin jimawar da yayi bayanan kuma lafiya qalau komai nashi a normal ya sameshi hakan yasa bai samu daman lekowaba washegari dukda hankalinshi na kan Aira Cikin kwana biyu su Aysha Da Ummy suka koma Wanda Aira saida suka sha kuka da zasu tafi su Mummy ma sun tafi danma an bar Nihal taki bin Mummy yasa Tadanjin saukin kadaici Da dare tana kwance tana chat Inda Rahama tayi mata voice ta ce "nayi ta Kiranki bata shiga daughter kuma baki hawa online " voice Aira ta tura mata ta ce "Sorry momcy kinsan bani da layin nan Shiyasa bansamu na kira ba kina raina kuma albishirinki muna ma garinku anyima su twins k'ani shekaranjiya akai suna kunyi Aliyu Haidar" kasancewar rahma na online "cikin farinciki ta ce " wow congratulation daughter Allah ya raya kai amma wlh baki kyauta mun ba kina ma garinmu ashe turoman address din Inda kike gobe insha Allah gani nan zuwa "nan Aira ta tura mata address din gidan Wahshegari ko Aira na kwance akan sopa Mama Halima na rigima da Nihal Dan kullum saisun yi rigima Aira na Dariya Haidar ko na hannun Hafsat tana liliyarshi Suka jiyo knoking Mikewa Hafsat tayi da Haidar a hannunta tana bud'ewa turus tayi ganin kawarta Rahama da suka gama KASU tare " wara idanu tayi ta ce "Friendy kece yau a gidan namu ko gizau" itama rahamar mamaki tayi ashe gidansu Hafsat ce ma Aira ta sauka "Dariya tayi ta ce " muje ciki"suna shiga har kasa Ta duk'ursa ta gaishe da Mama ta amsa cikin mutuntawa Rungume juna sukayi da Aira sunajin farincikin had'uwa Barin d'akin Mama tayi Rahama ta kalli Aira ta ce "Kai daughter a fili kinfi kyau kin ganki kuwa" Dariya Aira tayi ta ce "Ai momcy kema a fili kinfi kyau kinganki kuwa " Dariya sukayi "Ganin Nihal Kallon Aira tayi ta ce " Takwarace ko uwar fad'a kinsan bana gane su daban daban "Dariya Aira tayi ta ce " takwararce "Wara mata hannu Rahama tayi ta ce " yaudai gani ga takwara da Oum twins fad'awa jikinta Nihal tayi tana Dariya kamar ta Santa daman"Hafsat ce ta ce "Wai ina kikasan juna nan Aira ta fad'a mata Inda suka had'u tukwana itama Hafsat din ta fad'a mata kawartace " D'aukar Haidar tayi ta ce 'masha Allah shi kuma kama da mom d'inshi yayi kenan Allah ya raya manasu"Ameen Hafsa ta fad'a Bayan an kawo mata kayan makuleshe Nihal ko duk ta hahhayeta Nan ta fito da uwar sayayyar da tayiwa twins hada Haidar sosiau Aira tayi mamakin kirkin Rahama Godiya tayi mata sosai ta ce Bakomai ai ana tare sai yamma Rahama ta tafi Wanda dak'yal Nihal Aka Bambareta jikinta Dan cewa tayi sai ta bita Bayan tafiyar ta Mama Halima taja kunnen Nihal ta ce "Mutane na zuwa kina cewa zaki bisu saina zaneki ko suna baki abu kina amsa ki bisu uwar kwadayi ja'ira a haka idan mugaye ne har a sace ta " Kuka Nihal tasa "Aira ko dariya tayi " Mama ta ce "Gaskefa ku dinga hanata wlh kwanaki haka y'ar wata nan k'asar layin mu Daga ganin wani a hanya ya bata sweet ta like mai Saita bishi a banza mutumin nan ya lalata musu y'a karshe sai gawarta aka kawo musu karkiga ba kyan Gani y'ar shekara shidda " Sosai Aira ta tsorata ta ce "wayyo amma duniya ba Gaskiya wlh insha Allah Mama zamu hanata daman itace Naila bata da likewa mutane " Aira sosai take samun kulawa daga wajen Mama Halima Wanda suke zuwa Asibiti akai akai har aka samu jinin nata ya sauka yanzu ciwon kan ma ta daina sosai Rahama ma kawarta me kirki tana zuwa akai akai Arman ko fashin kwana daya yake yau yazo gobe bai zuwa Mummy ko duk sati sai tazo wannan satin tazo zata tafi Nihal ta ce itama binta zatayi daman ba wasu kaya gareta ananba Mummy tace suje zasu shiga mota juyowa tayi ta dagawa Aira hannu ta ce "Cutie mom bye" Sannan ta kalli Hafsa ta ce "Aunty bye " Dariya Mama Halima tayi ta ce "Ni baza ayimun bye d'inba " Turo baki tayi tare da Harararta ta ce "Ke ai fad'a galeki ba ruwana dake ke da dad en Cutie " sosai kowa dake wajen ya kwashe da Dariya musamman Mummy kama hannunta tayi tana Dariya cikin zolaya ta kalli Mama Halima ta ce "Kinji yarinya k'arama ma tasan halinku na fad'a " Dariya Mama Halima tayi ta ce "y'ar yayatu ce Ai gwara kuje Chan ku karata Wannan iyayen Surutun " duk Dariya sukayi washegari Arman yazo dayake barin musu palourn ake idan yazo Suna mak'ale da juna kamar kullum Haidar na hannunshi yana mashi wasa yana Kallonshi yana Dariya Aira na mak'ale jikinshi marairaicewa yayi ya ce "Cutie yaushe zaki koma gidan ni d'aya ba dadi duk a takure nake "marairaicewa tayi ta ce " Uhm nima bansaniba hero gashi Mama batamayi zancen ba "cikin damuwa ya ce " Yanzu saura kwana nawa ayi arba'in d'in "Juya idanu tayi saikuma ta ce "yau dai satinmu hud'u "Ajiyar zuciya ya sauke ya ce " saura kwana goma kenan"gyada mashi kai tayi "cewa yayi Allah ya kaimu"daganan suka sauya Tasha sunjima suna Abu d'aya kafin Arman ya Mike ya tafi Bayan yayiwa su Mama bankwana Aira ko ciki ta koma tayi wanka tayi alwala tayi sallah Dan tun last week ta fara salla batason Arman ya sanine Dan karya dameta ". Inna koda ta dawo daga kauye aka bata labarin abunda ya faru sosai ta shiga Surfa ruwan masifa a gidan Inda ta shiga ba tanan take fita ba hada kukanta a lokacin Su Abba na wajen a palourn gidan ta ce " y'an jikokin nawa da nafiso su suka tsolewa mutane ido akewa sharri duk wani masifar mutum kansu ake dorawa to ta Allah ba ta mutum ba Kuma abunda akaso suyi din Alhmdllh basuyi ba mutum Saidai ya mutu Sannan kai kuma habu ka jima baka kori Hajara a gidan nan ba Ai ba wajen zama zata rasa ba Aikin banza aikin hofi sosai ta dinga bala I da masifa Shidai Abba bai tanka mata ba haka kowa dake wajen Mamy ko sosai taji dad'in yanda Inna tayiwa Abba Dan ko magana basayi dashi ita kwanciyar hankalinta ma da yanzu aka San Inda y'arta take. Su twins ko sosai suke samun kulawa daga wajen kakannin nasu Dan duk wani meeting da za ayi na manya dasu mummy take tafiya sosai manyan mutane suka San jikokin na excellency Wanda sosai ake musu kyaututtuka ganin Suna zaune a haka ya sanya Daddy nema musu makaranta me kyau wacce tafi ko wacce tsada da koyawa ya sanyasu sannan ya nema musu Tahfex sosai Kuma yaran suke ganewa da fahimta Dan sun tsaida hankalinsu waje d'aya Saidai Rashin ji fa akwaishi musamman Naila da Ake shan fad'a da ita a school y'an ajinsu duk tsoranta suke Nihal cema miskila Dan Yanda take daddagewa yara saikace wata babba wai ita ala dole Jan aji ne kar a rainata Sosai Malaman makarantar keson yaran kasancewarsu masu kyau da kokari gashi kuma jikokin governor guda hakan yasa ake nuna musu kulawa a school kuma hakan yasa sukeson zuwa makarantar har so suke su tafi. Aira ta na gama arba'in da sati Mama Halima ganin irin Rashin kunyar ARMAN tayi yawa yanzu kullum Yana nan kuma ya gwada matarshi yakeso ya sanya hada musu kayansu ta runkutasu ta ce Allah ya raka taki gona hakan ko sosai yayiwa Aira da arman dad'i ranar da ta koma suka bud'e sabon shafin soyayya suka dasa daga Inda suka tsaya Danma yanzu Arman na zuwa wajen Aiki ba kamar Lokacin da suke London ba kawarta maman noor da suka had'u a jirgima Tazo tayima Aira barka Dan jininsu ya had'u ranar yini tayi mata tana tambayar ina twins Noor Kullum saitayi zancensu"murmushi Aira tayi ya ce "Ai suna kano twins ina ma tunanin sun koma Chan da zama wajen kakanninsu " jinjina kai Mom noor tayi ta ce "Amma kinyi kokarifa sis kinganninan noor ta girma ma amma ban iya barinta ta tafi da kwana daya ma ai bazan iya bacci ba" Dariya Aira tayi ta ce "nikam Kinga banajin komai Saidai ma wani Karin ne nakejin kewarsu " Ai Dan kunsamu wannan shiyasa da ace ba kowa zakiji fin kadaici"eh kuma hakane noor ma Dan ita kad'aice shiyasa "Mik'a mata Haidar Mom noor tayi tare da Aje mata 20k ta ce " gashi mom twins ba yawa Ai bansaniba da har suna munje Allah ya raya"amsar Haidar tayi tare da ajeshi kan gadon shi Dan yayi bacci ta ce "Haba mom noor Dan Allah ki barshi sunyi yawa" Girgiza mata kai tayi ta ce "a a a kawata baza ayi haka ba sainaga kamar bakison kyauta daga waje na ne Ai anzama daya Dan Allah ki amsa" Badan Aira tasoba ta amsa ta ce "Angode har bakin get Inda tayi parking motarta Ta rakata tana mata Godiya sannan ta ce " insha Allahu duk ranar da su twins sukazo zasuzo tare "Bayan ta koma Daga mata rakiya ta samu missed call d'in mamy a sabon layinta na 9ja dayake suna waya " kiranta tayi Inda suka sha hirarsu sosai nan Mamy take fad'a mata irin fad'an da Inna tayi murmushi Aira tayi ta ce "Allahsrk my Inna inasonta sosai wlh Allah yabar mana Ita inason ganinta amma ba hali". Washegari Aira na yiwa Haidar wasa yana y'ar dariyar k'uda Arman ya shigo da Fara a fuskarsa " Mikewa tayi tare da tarbarsa ta ce "Yadai honey yau ka shigo cikin fara'a kama hannunta yayi ya ce " kin tuna promise d'in da nayi maki na haihuwar twins ?jujjuya idanu tayi sai Chan kuma ta ce "Na tuna hero " yawwa to muje ga tukucinki na farko "suna fita Aira taga dalleliyar mota Ja mai masifar kyau da d'aukar hankali wacce a k'alla zata haura 10 millions"batagama santin motar ba Taji ya mik'o mata makullin mota a hannu ya ce " ga motarki cutie ta iso"wara idanu Aira tayi ta ce "Hero kana nufin motar nan tawace " Gyara mata kai yayi yana murmushi "tsallen murna Aira ta daka tare da Rungumeshi Ta fashe da kukan farinciki ta ce " Thnks yo hero Thnks you so much ka gamayimun komai a rayuwa Allah ya saka da alkhairi ya k'ara budi"murmushi kawai Arman yake ya ce "Komai nayi maki ban isa na biyaki kwatar abunda kikayimun ba cutie kece kika gamayimun komai a rayuwa kika bani farincikin da babu wanda ya tababan kwatankwacinshi Komai nayi maki kin chanchanci fiye da hakan banason Godiya Da ni da duk abunda na mallaka naki ne keda yaranki ko kin manta" murmushi Aira tayi tana farinciki ta ce "Hakika kaid'in haskene a cikin duhu Mijina Da babu kamarsa a fad'in duniyar koda ina cikin bakincikin wani abun idan na tuna Da baiwar da Allah yayimun na mallakamun mijin da yafi na kowa so da k'auna da tattalina uwa uba kyauwun hali da kyawun fuska sai Naji dadi a raina Naji waccen damuwar ta gushe nagode mijina aljannata Allah ya barmu tare har a badan Abadan....✍🏿 *Ni da yaya Arman it's not free it's fore sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* *_Miss Hajo ce_* [7/22, 19:01] Hajo hajo: 🅿️........*119&120* Har Abadan Abadan sosai Aira ta shiga Jerawa mijin nata adduo i Dan sosai ya sanyata farinciki marar musaltuwa a ranar Ta shiga ta tuk'a mota Inda yana gaba Rike da Haidar Dan yaga yanayin tukin nata kuma masha Allah komai na tafiya normal Saidai Sam barka sosai masoyan nan suke rayuwarsu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali Sai fargabar su d'aya kawai Rashin daidaaito tsakaninsu da mahaifansu Anyi hutun school Wanda Mummy ta sanya aka kawo twins Dan suyima iyayen nasu Hutu da misalin Sha biyun rana Arman na wajen Aiki Aira na d'akinta tana gyara kayan Haidar da twins suka lalata shi kuma ta barshi a palour cikin net Twins da suka gaji da wasansu Wajen Haidar suka nufa tare da Fara liliyarshi suna mashi wasa Nihal ce ta ce "Naila bari kiga na iya d'aukar Haidar yalinya " Wara idanu Naila tayi ta ce "Mu daukeshi mom bazatayi fad'a ba " Eh mana ai bata nan "a tare suka had'u suka Chunkumeshi Jin damkar manya yaro ya kwala Kuka Wanda shi ya fito da Aira daidai suna shirin kadashi da gudu da ruga ta warceshi Cikin fad'a ta ce "Dan gidanku ban hanaku Tab'amun yaro ba kashemunshi kukeso Kuyi mugaye waye ya ce Ku daukarmunshi " ta fad'a tana jijjigashi tsuru tsuru sukayi Naila ta ce "Cutie Nihal ce ta ce Mu daukeshi" Cikin masifa Naila ta hayayyakowa Nihal ta ce "Munafuka Ba ke kikace mu daukeshi ba shine zakimun sharri" Harararta Nihal tayi ta ce "kece dai Munafuka muguwa kawai " Kallon Aira Naila tayi ta ce "Mom kinganta ko "? harararsu Aira tayi tana danna wayarta tana chat ta ce " Kuka k'ara sako suna na ma zakuyi mamakin abunda zan muku koba fad'a ba ku kashe kanku"sosai Naila ta kulu Aiko shako Nihal tayi nan suka hau Dambe Aira na jinsu ta musu banza ganin ihunsu ya isheta ma earpiece ta sanya Arman ne yashigo Ya ga twins na fad'a D'aya ta hau kan d'aya cikin Sauri ya shigo Tare da rabasu nihal dake Kuka tana saita rama Dakyal ya samu ya raba su Kallon Aira yayi da Hankalinta na kan waya ya ce "Ke yanzu Kina ganinsu suna fad'a bazaki raba su ba Saima zama kikayi kina Danna waya to idan d'aya ta jiwa d'aya ciwo fa kice me?Dagowa Aira tayi tare da turo baki ta ce " To Hero Akanme zan damu kaina Kaida kasan halinsu sarai barinsu nayi su gwada karfi nan gaba wacce taji jiki bata yarda su Kara fad'an ba Dan basu isa su doramun hawan jini da yarintataba "tana gama fad'ar haka ta sab'i Haidar tayi ciki girgiza kai yayi tare da d'aukar Nihal dake birgima take kuka ya ce " sorry my angel kiyi shiru idan ba haka ba Kuma na fasa kaiku wajen wasa"Lokaci guda ta Goge hawayen tace "hero da gaske" eh mana kuje Yanzu mom ta shiryaku anjima zamu fita sannan kice itama ta shirya kafin na shirya "Cikin Sauri Nihal tahau tsalle tare da Kallon Naila ta ce " Naila taho muje muyi Sauri mu shirya kinji dad zai kaimu wajen wasa"kama hannunta Naila tayi Ta ce "Nihal kiyi hakuri Bazan sake Dukanki ba kinji kema ki daina Jana" Gyada mata kai tayi ta ce "Nima nadaina" tukwana suka Ruga a tare d'akin Aira "murmushi Arman yayi yana jin soyayyar iyalan nashi tun suna yarinta ya lura zasu taso cikin Had'in kai da k'aunar juna danma Mummy Sun kwafsa musu sun amshe Su Gashi bazai iya amsar su daga wajen iyayen nashi ba Suna zuwa Suka samu Aira kan Gado Naila ta dareta ta ce " Cutie mom dad yace ki shiryamu kema da my boy ku shirya zamu fita unguwa Shima shiryawa yake"To aku sarkin surutu ta fad'a tana Mikewa "Dariya Nihal tayi ta ce " Mom yaushe zamuje naga takwarata"Harararta Naila tayi kamar wata babba ta ce "Ke baki da zuciya me zamuje muyi a wannan gidan Ai dad en Cutie mugu ne bazamu sake zuwa ba" Ta fad'a tana murguda baki"kallonta Aira tayi tare da hade rai Ta ce "magulmaciya Abban nawane mugu na k'arajin kin fad'a haka saina Bata maki rai Munafuka" Turo baki Naila tayi ta ce "To ai mugun ne tunda baya sonki nima bana sonshi kuma bazan sake zuwa gidan ba Har mom En takima bazanje naganta ba Tunda bata tab'a zuwa gidan muba shi kuma dad enki da bindigata zanje na harbe sa" Sakato Aira Tayi tana kallonta ji take kamar ta shakota Ja mata kunne tayi ta ce "Uban kine mugun ba uba na Dan Ubanki ubana sa ankine karki Kara zuwa gidan mana wani yace yanason ganinki yarinya sai shegen surutu to gobe_goben nan zaku tattara kubar mana gida Tunda Isgilallu ne ku munafukai" ta fad’a tana Kara ja mata kunne k'ara ta saki tare da fashewa da kuka Arman da ya shigo yaji suna dramar nan Dariya yayi tare da saurin zuwa ya d'auki Naila da take rafka ihu ya ce "Sorry momcy Yaudai kinjawa babanki zagi Kiyi shiru karna karajin maganar nan a bakinki"tana ihu tana kuka ta ce " Ance mugu ne "Tasowa Aira tayi da niyyar bugunta Arman ya ja gefe yana Dariya ya ce " Sorry mana my beautiful wife ayi mana hakuri bazamu sakeba "Naila dake Kuka ta ce " Dad saina sake mugu ne Ai "Cikin fad'a Aira ta ce " ka bari hero na daki yarinyar nan wlh ta rainani Kanaji ina fad'a tana fad'a ga sa'arta(Ohni su Aira manya)Dariya Arman yayi sosai Ya ce "To ai halinkine tayo na kafiya kinga ko idan ka tashi Gado ai linkawa kake" harararshi Tayi ta ce "Ni ba hali na ba tayo wannan ai gulmace take kuma Zakisan ni kika Zagarwa uba daga yau ba ruwana dake" Ta na gama fad'a ta zauna Kan Gado tana girgiza k'afa "girgiza kai Arman yayi ya ce " Yanzu dai yi hakuri tashi ki shiryasu mu fita"Turo baki tayi ta ce "Allah wlh kaji na rantse bazan shiryata ba Saidai kai ka shiryata" Dariya yayi ya ce "ta turo maki baki kema kinturomun kinga an fanshe 1-1 kenan to ni bari naje na shiryata kafin na shiryata kishirya sauran" Bata ko kallesu ba harya fita sai Haushi takeji a haka ta shirya Nihal da Haidar itama ta shirya sosai sukayi kyau gwanin burgewa nan d'akin Arman yazo ya shirya Naila dake like dashi kar Aira ta daketa A tare suka fito gwanin ban sha awa kai tsaye wani katafaran mall suka wuce Inda kowa ya jibgi abunda yakeso daga nan ya wuce dasu ya kaisu park sosai ya nishad'antar da iyalin nashi suka ci sukasha sannan sukasha hotuna sai wajen isha i suka koma gida har lkcn Aira zafin maganar Naila takeji ko magana bata mata abun ne ya isheta suna zaune a palour Naila da Nihal na Game a tab d'in d'insu suna gefen Arman Haidar ko na hannunshi yana masa wasa yana Dariya janyo wayarta Aira tayi ta lalubo number Mamy tana d'auka ta fashe da kuka sosai hankalin Mamy ya tashi ta ce "Lafiya Aira meya faru" Su Arman ma da twins duk kallonta suka tsayayi cikin kuka Aira ta ce "Mamy Dan Allah yaushe zakizo kinganninan har yara sun fara yimun gori wai iyayena bakwa sona ta k'arasa fad'a tana rushewa da kuka " Arman sosai yayi mamakin maganganunta ya k'ara tabbatarmai da airantashi dai har yanzu ta da d'ince dai "mamy ko cewa tayi wasu yaran ne suka maki gorin" Mamy Naila ce Hada cewa wai babana mugu ne "Tsaki Mummy taja ta ce " nazata ma wacen macen arzikice akan jariran yaran nan kikemun wannan kukan Allah ya shiryeki ni ban iya shiririta ba sanda kika dawo daidai munyi waya "tana gama fad'ar haka ta katse kiran " Fashewa da kuka Aira tayi sosai "Arman ne yaje tare da Rungumeta ya Ce " Haba Aira akan Naila ne duk zaki d'aga hankalinki kiyi shiru kinsan ba abunda na tsana sama da kukanki bazata sakeba daga yau"To ba kaibane ka goyi Bayan ta rainani ba kuma ko Ka bani hakuri"Murmushi yayi tare da "Goge mata hawayen ya ce " to yi hakuri bazamu sakeba"Nihal ce tazo tare da hayewa kan Aira tana Goge mata hawaye ta ce "Sorry mom " Goge hawayenta Aira tayi tare da d'aukar nilah ta ce "Na hakura yarinyar kirki Allah miki albarka" Amen Nihal ta fad'a tana Lafewa jikin Aira Naila ce ta taho tana Hawaye ta ce "Sorry mom bajan zakeba" Harararta Aira tayi tare da d'aukar Nihal tayi sama da ita ta ce "Muje mu kwanta my Beloved Daughter kuma Mummynah " Dariya Nihal tayi tana yiwa Naila gwalo Suna barin Wajen Naila ta fashe da kuka Lallashinta Arman ya dingayi amma ta tubure Dak'yal ya samu bacci ya d'auketa tana bacci Dakinsu yaje ya kwantar da ita Shikuma ya wuce d'akin cutie d'inshi . Washegari ayra Tarairaiyar Naila ta dingayi Dan Naila taji Haushi yanzu ma tana cinyarta tana bata choculate ta kunna mata game a wayarta tanayi Naila na gefe tana hawaye Ganin Haka ya sanya naila fashewa da kuka tare da zuwa taje ta haye Aira ta ce "Dan Allah mom kiyi hakuri Allah na daina bazan sakeba" Shafa kanta Aira tayi ta ce "Na hakura Amma kika sake me zan maki" Dagowa tayi tana Hawaye ta ce "Ki dakeni Mom Allah bazan sakeba " Murmushi Aira tayi tare da Rungumeta Itama ta ce "To yi shiru my prince's d'ina " Sosai Naila taji dad'i . Washegari Aira ta shiryasu sukaje gidan maman noor Bayan ta turo mata address din gidan Sosai Taji dad'in zuwansu a motarta Aira ta tuk'a sukaje Twins da noor kuwa Sai wasa suke Sai magriba sukayi mata bankwana Bayan ta cika twins da abun arziki Washegari kuma kawarta Jannat ta kawo mata ziyara itama ganin twins tazo. Hutunsu na karewa na makaranta Mummy ta aiko Aka tafi dasu Suka koma Inda Aira gidan yayi mata ba dad'i haka rayuwa taci gaba duk Hutu ana kawo twins suyo Hutu su koma A haka har Haidar yayi wata Bakwai Wanda yaron yayi wayau sosai ga kyau da shiga rai . Yau Aira tunda Arman ya tafi Wajen aiki takejin fad'uwar gaba Hakanan kawai takejin kamar wani Abu marar dadi zai faru Haidar ne dake Kuka ta hau jijjigashi Bayan ta bashi abincinshi ta samu yayi shiru tana nan zaune Taji shigowar motar Arman Bayan ya shigo cikin shigar kayan aiki ya Kalleta ya ce "My Prince's ya dai naga Sai wani k'ara kyau da k'iba kike kwanannan " murmushi kawai tayi tare da mik'a masa Haidar ta ce Hero.Wlh gaba na ke fad'uwa tun d'az...bata k'arasa fad'a ba sakamakon ruri da wayarta ta fara Duba mai kiran tayi taga bakuwar number d'auka tayi tare da karawa a kunne Muryar amma taji tana kuka ta ce "Sis ki maza duk inda kike ki taho yanzu " Innalillahi wa inna ilaihiraji'un meke faruwa sis wanine ya mutu "Aira ta fad'a tana dafe k'irji "Inna ce ba lfy muna asibitin Mallam aminu kano sunanki Dana yaya Arman kawai take ta fad'a a kira mata ku" Tuni Aira hankalinta ya tashi cikin kuka ta ce "Na shiga ukku sis gamu nan katse kiran tayi Arman da jira yake ta gama yaji meye cewa yayi " lafiya cutie ?ba lfy ba yaya kana ji Inna ce ba lfy kuma ni dakai take nema "Cikin rudewa Arman ya ce " Subhanalla maza maza sanyo hijab Cikin Sauri Aira ta Ruga ta sanyo hijab Haidar dake hannun arman ta amsa tana hawaye ta ce "Muje yaya muyi Sauri" Kai tsaye Airport suka nufa Cikin kankanin lokaci jirginsu ya tashi zuwa kano minti Talatin me kyau tayi musu a kano Inda Arman ya kira driver d'inshi yazo ya daukeshi Kai tsaye asibitin Mallam aminu kano suka nufa Duk sun rude Suna isa cikin kid'imewa Aira ta fito Inda ta Hango su Mamy ta nufa tana kuka duk kallonsu tayi ta ce "Mamy ina innar " D'akin Da take ta nuna musu itama tana hawaye ganin zata yadda Haidar ya sanya Mamy Amsarshi Tare da cewa "ki nutsu " Cikin Sauri Aira ta nufi d'akin Arman ma d'akin ya nufa batare da ya ma Gaishe da mutanen wajen ba Dan Duk ya rud'e Aira na shiga ta samu Inna Kan gadon marassa lafiya numfashinta na fita sama sama yayinda likita biyu a kanta cikin kid'imewa Aira ta nufi gadon tare da fashewa da kuka ta ce "Inna meya sameki Inna " Arman ma gadon ya isa ya kama hannunta ya ce "Sannu Inna meya sameki" Cikin murya ta marassa lafiya Inna ta murza hannunsu ganin tana motsa bakinta ya sanya su Matsawa saitin kunnansu suka saita bakinta Cikin dauriya ta ce "Allah yayi muku Albarka Allah yayi muku Albarka Ko yau na mutu Alhmdllh tunda burina ya cika na ganin kunzama ma'aurata kuma harda zuri'a Burina na karshe ne har yau ya kasa cika na Daidaituwar Iyayenku Ina fatan ko Bayan raina zaku zama silar Daidaituwar Iyayenku nasan tawa tazo karrshe kuyimun Alk'awarin zama tsintsiya d'aya Ku rik'e juna da amana Allah yayi muku albarka" tari ne yaci k'arfin ta Kuka Aira ta fashe dashi tare da Rungume Inna ta ce "Bazaki mutu ba Inna zaki tashi muci gaba da rayuwarmu zafin ciwo ne ki daina fad'ar zaki mutu Inna bazaki mutu ba " ta Kara'sa fad'a cikin kuka mai ban mamaki Arman ma ji yake kamar yayi kukan girgiza mata kai yayi ya ce "Inna bazaki mutu ba " Bayan tarin ya tsagaita Girgiza musu kai kawai tayi Dan muryarta harta fara chanzawa ta ce "Ina Aliyun yake " Kallon Amma Aira tayi dake tsaya wajen tana hawaye itama ta ce "Amma amso Haidar wajen Mamy" Amso Haidar amma tayi wajen Mamy ta shigo dashi Amsarshi Aira tayi tare da nunawa Inna ta ce "gashinan Inna " Shafa kanshi Inna tayi ta ce "Naganshi daman shine bansaniba Allah musu albarka y'an biyu ma dazu sunzo na gansu Allah ya raya muku zuri arku yayi musu albarka" Ameen Aira ta fad'a tana kuka sosai "kallon amma tayi ta ce “meya sameta sis”Amma na hawaye ta ce “Daga zazzabi kwana biyu yau da safe ana tashi mukaga tana cikin wannan halin shine aka kawota asibiti yanzu da saukima akan dazu tun dazu sunanku kawai take kira tana cewa a kira mata ku shiyasa na kiraku”Girgiza kai aira tayi tana kuka tace “Allah bata lfy”Murmushin karfin hali inna tayiwa aira da arman tare da cewa " Kabir da Abubakar ko bayan raina zanyi alfahari daku idan kuka zama silar daidaituwas....Tari ne Inna ta fara ba kakkautawa Tare da shakuwa sosai duk suka rude har Abba da Daddy da suka shigo tsaye sukayi kanta Aira ko hannunsu gam ta kasa saki kuka kawai take Dr ne ya shigo Tare da sanya mata oxygen ganin numfashita yana daukewa "Chan kuma sukaji shiru Ba motsi ba numfashi Hannunta suka ga ya saki Wanda yake rik'e da na Aira da Arman " A firgice kamar mahaukaciya Aira ta mik'e ta ce "Inna Inna bacci ne kikayi " Dr ne ya matso tare da cire mata na urori ya rufe mata fuska kallonsu yayi ya ce "kuyi hakuri Allah yayi mata cikawa Allah jikanta da Rahama yasa mutuwa Hutu ce yana gama fad'ar haka yabar wajen " Ai Aira jin Abunda Dr ya fad'a batasan lokacin da jinta da ganinta Ya daukeba sai ganinta sukayi a sulale a wajen summammiya......✍🏿 *Allahsrk rayuwa kulli nafsin za ikatul maut Mutuwa kenan mai yankan kauna Allah jikan musulmanmu da suka rigamu gidan gaskiya idan tamu tazo yasa mu cika da imani Allah ya sa muyi kyakyawan karshe*😭😭😭 *Ni da Yaya Arman it’s not free it’s for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* _*Miss Hajo ce_*🤙🏿 [7/22, 19:54] Hajo hajo: 🅿️.........*121&122* Summammiya su Mamy da su Aunty Aysha su ummy amma da Mummy da twins da sukazo Sosai Suka shiga kuka mutuwar Inna ta girgiza mutane da dama musamman Arman Daddy da Abba ko ba a magana Babban bakincikinsu da Inna ta mutu Da Jimamin Rashin jituwarsu A bakinta Tabbas basuyi mata adalci ba Mummy ce tayi k'arfin halin Daga Aira taji ta sume ruwa ta yayyafa mata amma bata kawoba Kallonsu tayi cikin k'arfin hali ta ce "Addu'a ya kamata muyi mata ba wai kuka ba Ta rigamu ne Saidai muyi fatan samun Rahama Inda taje dole kowa zaijeshi muma jiran tamu muke Allah sa mucika da imani Inna kuma yayi mata Rahama yasa ta huta mala'ikun Rahama su San da zuwanta" Ameeen duk suka fad'a "nan aka shirya tafiya domin ayi Jana izar inna itakuma Aira aka wuce da ita emergency Arman ko baka iya Tantance yanayin da yake ciki ba a tab'a yimasa mutuwar da ta shigeshi irin mutuwar Inna ba zuciyarshi ji yake kamar zata rabe gida biyu " Wajen ya samu ya zauna a waje yanajin zuciyarshi na masa zafi da zaiyi kuka ma shi da ya ji sassauci akan Abunda yakeji idan ya kalli masu kukan sai yaji inama shine ya samu kukan irin nasu Sosai yayi mamaki jin Daddy Ya dafoshi ya ce "Addu'a zamuyi mata Mujahid tashi mu tafi ayi mata Sutura" Kallon Daddy Arman yayi sai kuma zuciyarshi ta karye Ya fashe da kuka tare da Fad'awa jikin Daddy Ya ce "Daddy Inna ta rasu Daddy shikenan ta mutu" Rungume dan nashi dad yayi yanajin nadamar abubuwa da dama da yayi a rayuwa ya Ce"Adduarmu take buk'ata namiji da jarumta aka sanshi muje kaga antafi da ita muje ayi mata Sutura da wuri"Dak'yal Arman ya iya daidaita kanshi A tare da Dad suka shiga mota Cikin k'ank'anin lokaci aka shirya Inna Bayan anyi mata salla aka wuce da ita gidanta na Gaskiya( Inda kai da ni da ita da su da kowa zaije Saidai muyi fatan Allah ya sa mu cika da imani Wanda suka rigamu Allah ya jikansu yasa sun huta Mu dake raye kuma Allah bamu guzirin taddasu )Bayan an dawo daga Sutura Wanda dumbin mutane da dama suka Je suturar Dan kafin kace me labarin mutuwar Inna ya baza gari saboda d'iyan zumunta Mama Halima ma ta tarar da suturar Inda ta sha kuka kamar ba gobe Abba ko sosai daka Kalleshi shida dad zakasan mutuwar tana nukurkusarsu cikin gidan ma ansha kuka Inda daga karshe kuma duk aaka bita da addua sai Bayan magriba sai Sannan Mamy ta kawo a kanta Aira Na Asibiti Kallon Aysha tayi ta ce "Dawa aka bar Aira a Asibiti "Aysha da cikinta da ya fara girma ta ce " Wlh Mamy bansaniba duk nan muka taho "Mikewa Mamy tayi ta ce " Bari naje naga jikin nata "Mikewa itama Aysha tayi Ta ce " muje Tare Mamy a tare suka fito harabar gidan Daidai lokacin Abba ya dawo daga salla Kallonsu yayi da mamaki ya ce "Ina zaku" Aysha ce tayi k'arfin halin cewa "Aira ce zamuje mu gano a Asibiti ba a barta Da kowaba" ku jira na d'auko mota mu tafi tare suka tsinkayi Muryar Abba "Sosai sukayi mamaki da AL ajabi musamman Mamy Sakato tayi a wajen har Abba ya fito da mota har suka iso asibitin Mamy na.mamaki suna fitowa suka samu Amma rik'e da Haidar din Aira tayi jugum idanunta jawur a waje " Kallonta sukayi a tare sukace "Kina nan daman kenan to ya jikin nata" Juyowa Amma tayi tana jijjiga Haidar ta ce "Har yanzu basu bamu wani bayani ba Tunda suka shiga har yanzu shiru Kuma sunki barina na shiga na ganta" sosai suka damu musamman Abba da a fuskarsa zakaga tsananin damuwar da yayi Kallonta yayi ya ce "Dr din bai fito ba har yanzu" Gyada musu kai tayi "Suna nan tsaye Mummy da Arman sukazo suma daga wajen makokin sukayo nan Dan suga jikin nata Arman daka Kalleshi zakasan yana cikin tsananin tashin hankali ga mutuwar Inna ga kuma Aira ba asanma halin da take ciki ba nan suka zazzauna jiran Fitowar likitan aji halin da ake ciki " sai wajen 9 pm tukwana dr din ya fito yana shafce zufa duk wajenshi suka nufa tare da tambayar halin da take ciki"Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "Alhamdulilla munyi nasarar ceto rayuwata da d'an dake cikinta ta so ta samu heart attack ne Allah ya kiyaye Amma dai bata farka ba zata iya farkawa zuwa gobe haka Allah ya bata lafiya" Duk hamdala sukayi ga mamakin su na jin Aira wani cikin gareta Arman ne yayi k'arfin halin cewa "yanzu zamu iya ganinta" Eh ba damuwa zaku iya ganinta amma kar ayi hayaniya a kanta Dan Allah"Arman shi ya fara shiga d'akin Inda ya sameta kwance tana numfashi sama sama "Kama hannunta yayi ya ce " Allah ya baki lafiya my cutie"Duk shigowa sukayi suka duba jikin nata Har Abba Haidar ne da ke kuka hannun Amma Mamy ta amshe shi ta ce "Ko yunwa yakeji " Eh kila ai yanama da hakuri Tun dazu ruwa kawai na basa "Arman ne cikin k'arfin hali ya mik'awa Amma makullin mota ya ce " Ki bud'e Motar da mukazo da ita zakiga Madararshi a Pida"To ta fad'a tare da amsa ta fita Abba ne ya fita daga d'akin Bayan Amma ta dawo ta bawa Mamy Madarar Inda ta shiga bashi yana sha "Mamy kawai ta kwana wajen Aira Inda suaran suka koma gida Washegari Tun safe Arman a asibitin ya tare Dan jiran farkawartata Mummy Wajen 11 tazo tare da twins Suna ganin mamansu cikin wannan halin suka hau kuka Dak'yal aka dinga lallashinsu Haidar ko bawan Allah sai madara Mamy ta dinga bashi yanzuma yana bayanta ta goyashi yayi bacci suna nan zaune jugum jugum Sukaji farkawar Aira Cikin Sauri Arman yaje tare da kamata ya ce " Sannu Mom twins"Kallonshi Aira ta tsayayi tare da Kallon mutanen wajen da kuma Inda take abubuwan da suka faru ne suka shiga dawo mata Kuka ta fashe dashi tare da d'ora hannu a ka ta ce "Na shiga ukku yaya Dan Allah ka Cemun mafarki nake ba Inna bace ta mutu" Rungumeta Arman yayi ya ce "ki nutsu Aira baki da lfy Dukkan mai rai Mamacine Addua zakiyi mata Inna ta rigamu gidan Gaskiya" basuyi aune ba saiji sukayi ta buga uban k'ara tare da Kara sulalewa a wajen Duk rudewa sukayi Inda suka kira dr nan ya k'ara dubata Kallonsu yayi ya ce "Gaskiya mutuwar nan ta girgiza ta da yawa Ta Kara suma Allah ya kiyaye karta samu wata matsalar Allah Ya bata lfy ya fad’a tare da sanya mata Karin ruwa " sosai kowa hankalinshi ya tashi twins kuka suka sanya tare da hayewa kanta suna jijjigata sukace"Cutie mom ki tashi mom ki tashi mu tafi gida"Janye su Mamy tayi tare da Kallon Mummy ta ce "Ko Aysha ta wuce dasu gida" Mummy da duk tayi sanyi cewa Tayi Eh to a wuce da su din"Arman ne yayi saurin cewa "Mummy bari na kaisu gidan aboki na nan kusa ba nisa" Duk kallon mamaki suka bishi dashi "Mamy ta girgiza kai Mummy Ce ta harareshi ta ce " gidan abokin naka har yafi gidansu"Kiyi hakuri Mummy gwara na kaisu Chan saboda Chan din za a iya korosu Nan ko damun gama abunda muke zanje na d'aukesu "Duk Kallonshi suka tsayayi cikin b'acin rai Mummy ta ce " to ba Inda zaka kaisu"Mamy ce ta ce "Ki barshi ya kaisu Chan din Hajiya Ai yana da Gaskiya Abban su baida Tabbas ka kaisu Inda yafi maka kwanciyar hankali" Girgiza kai Mummy tayi Arman ko d'aukar yaranshi yayi ya fita dasu Dan bazai lamunta ba a wulakanta mai yara tunda baisan last time abunda Abba yayi musu ba har suke ce masa mugu Saida ya biya yayi musu sayayyar kayan ciye ciye Dan su kwantar da hankalinsu tukwana ya wuce dasu gidan wani abokinshi kasancewar akwai yara a gidan Tuni suka wartsake suka hau wasanninsu yinin ranar Aira Haka ta yini a sume. Washe gari ma.koda ta farka bata iya tuna komai saidae tabi mutane da ido ganin Abun nata Yana neman zama tab'in hankali ya sanya Mamy buk'atar a basu sallama Dan Aje kawai a dinga mata rokon Allah likitan bai musa ba ya basu sallama ranar Suka wuce gida Da ita Sosai Mamy tayi mamakin Abba da bai ce komai ba A.lokacin Aira bata ma cikin hayyacinta Abu saiya Zamewa mutanen gidan biyu da Jimamin mutuwar Inna ga Rashin lafiyar Aira Arman kasancewar bayanan aka bada sallamar koda Mummy ta fad'a masa an sallamesu an Wuce gidansu da ita sosai ya shiga f'ada Inda ya shiga ba tanan ya ke fita ba Ya ce "Akanme za a kaimun mata Chan bada izini na ba sanadin a kara bata mata rai ne Me yasa ba a kiraniba Ko so ake sai an k'ara wulakantamun ita tukwana hankali zai kwanta" Cikin fad'a Mummy ta ce "Kai baka da hankali ma to tatafi chandin kainan gani kake har kafi iyayenta sonta to ko su da kaga suna mata haka ba Dan basa sonta ba koshi mahaifin nata Yana son y'arshi daurewa ce yake ka duba kai soyayyar da kakeyiwa yaranka to haka ko wani uba yake yiwa y'ay'ansa Dan an kaita gidansu shine zakazo ba kunya kana kumfan baki to ankaita din kuma bazata dawo ba sai ta samu lfy" Shiru Arman yayi batare da ya k'ara cewa uffan ba Daga asibitin Mummy gida ta wuce ita da twins shi kuma Arman ya wuce Guest house d'inshi ko ya rage haushin da yakeji har a ranshi yaji haushin tafiya da Aira akayi gidan su Dan Ko kare ya cinye zuciyarshi bazai tab'a taka gidansu ba Dan ko zaman makokin Inna da akayi a Farfajiyar gidanta akayi bai lek'a ko bangarensu ba to shi yanzu ya zaiyi sun tafar mai da mata gashi baya ma da tabbacin Abbanta zai amsheta Da wannan tunanin ya yini zuciyarshi chunkushe duk ba dadi Aira ko bangarensu Sosai Aka baza malamai aka dinga mata rokon Allah Dan ta firgice ta zama kamar wata mahaukaciya a haka Aka samu take shan rubutu ko magana batayi Yayinda Mamy ta yaye Haidar ganin halin da mahaifiyarshi ke ciki Ga kuma ciki da Dr yace tana dashi madara da Abinciccikan yara aka shiga bashi y'an gidan sosai suke Son yaron lokaci guda suka shaku dashi abun tausayi Aysha Da Ummy ko kullum suna gidan Mama Halima da Aunty Maryam Bayan anyi sadakar Bakwai suka tafi gidajensu Yaya Omar ma ya koma wajen aikinshi Bayan Kwana goma da rasuwar yan uwan mummy ma da na mamy duk sun zazzzo gaisuwar daga garuruwansu har bappa da goggo sunzo sunyi gaisuwa ranar suka juya gidan ya rage sauran yasu yasu Aira ko har yanzu sauki Saidai na Allah Arman Kullum da damuwar abun yake kwana yake tashi gashi idan ya kira wayarta Saidai Amma ta d'auka a wajen amma nema yake sanin halin da ake ciki yau yana zaune a daki kadaici duk ya isheshi gana Aira ga na kewar twins ga mutuwar Inna duk ya rame kiran Daddy ne yaji ya shigo Wayarshi da mamaki ya d'auka "Nan Daddy Ya shaida masa yana nemansa a gidansa yanzu" Cikin Sauri Arman ya Mike tare da d'aukar key bai zarce ko ina ba sai gida Inda yana zuwa ya samu twins Gefen Daddy Alamun Kuka ma suka gama suna ganinshi suka Ruga da gudu tare da Fad'awa jikinshi suka sanya kuka Lallashinsu yayi tare da zaunawa kan sopa Ya ce "Ina yini Daddy " Lafiya qalau Daddy Ya fad'a yana sauke ajiyar zuciya "Shiru Arman yayi Ya rasa abun cewa ga twins dake masa kuka Jin Shima Daddy yayi shiru ya sanyashi Dagowa a hankali ya Kalleshi tare da Kallon Mummy da itama shid'n take kallo Da ido tayi masa sing da yaba Daddy hakuri Kallon Daddy yayi tare da Saukowa daga kan kujera ya Dirar da gwiwowinshi har k'asa cikin ladabi ya ce " Daddy Dan Allah ina neman yafiyarka akan abubuwan da nayi maka Kayi hakuri ka yafe mun badan niba Dan girman Allah"Ajiyar zuciya Daddy Ya sauke ya ce "Ka tashi Arman na jima da yafe maka Allah yayi maka albarka ya yafe mana baki d'aya Arman wani sanyi yaji cikin zuciyarshi Mikewa yayi tare da zuwa kujerar da Daddy yake ya ce " Nagode Daddy Allah ya saka Alkhairi ya k'ara girma hakika kaid'in ka cika uba na gari mai mahimtar iyalanshi Allah ya k'ara maka lafiya da nisan kwana"Cikin murmushinshi na manya daddy ya ce "Ameen my son Tare da Rungumeshi yanajin soyayyar yaron nashi na k'ara ratsa shi ta bangaren Arman ma haka yaji sosai soyayyar mahaifin nashi na k'ara fisgarsa.........✍🏿 *Ni da yaya Arman its not free its for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* _*Miss Hajo ce_*🤙🏿 [7/23, 23:37] Hajo hajo: 🅿️..........*123&124* Sosai soyayyar mahaifin nasa ke Kara fisgarsa Mummy ko hamdala tayi tare da d'aga hannu ta godewa Allah da ya nuna mata wannan babbar ranar da ta jima tana tsumayi "Bayan sun tsagaita Daddy Ya kalli Arman ya ce " Naji ance Ita Matar taka tana gidansu Kaje kaga jikin nata"A a a Daddy Banje ba Banajin zanje"shiru Daddy yayi bai Kara cewa uffan ba Mummy ko ta lura akwai magana a bakinsa ya kasa furtawa ne kawai twins ne sukaje wajen Mummy Naila na hawaye ta ce "Mummy ki kaimu wajen mom asibiti mu ganta" Nihal kuma ta ce"Mummy ki kaimu wajen cutie Mom da Haidar bata da lafiya karta mutu"shiru Mummy tayi tana Nazarin yanda zatayi da Yaran nan wata dabara ce ta fad'o mata ta ce "Mamanku ta warke tana London Ita da Haidar sunje suyi maku sayayya "shiru twins sukayi kamar masu nazari basu Kara cewa uffan ba Mummy ko tana so taje taga jikin na Aira Tana tunanin Daddy Dan ya hanata shiga gidan saboda ko zaman makokin Inna da Akai bakinsu part din inna Batace uffan ba Daga ranar ARMAN ya dawo gidansu da zama Wanda Bayan sati guda Daddy Ya ce " ya koma kan Aikinshi Ba dan ya so ba ARMAN ya koma Ba abunda ke damunshi irin. Kewar cutie d'inshi da Rashinta a kusa dashi gashi har yanzu idan ya kira amma Saidai tace masa bata magana Twins ko sunkoma makarantarsu Inda yanzu basu da walwala irin ta da Dabara Mummy tayi musu tace Aira ta koma Abuja tare da Dad d'insu Idan sukace ta kira musu ita sai tace Wayarta ta lalace a haka take musu dabara. Tsawon wata biyu kenan Aira na kwance ba a gane kanta dan likita ya ce "ta dan samu loosing memory ne sai a hankali zata dawo daidai insha Allah Kullum Mamy saitayi mata kuka ga cikinta da ya fito sosai yau ma tana kwance idonta bud'e Mamy na gefenta Amma na goye da Haidar tana jijjigashi Kallonta Mummy tayi ta ce "Ki tashi kici abinci Aira tun jiya rabonki da abinci ?juya kanta Aira tayi tare da rufe idonta " Girgiza kai Mamy tayi tare da zubo abincin nan ta tirsasata taci Saida tayi hawaye ganin halin da y'artata take ciki ta zama kamar wata mai tabi nan ta bata rubutun da ake yo mata Tasha tukwana ta gyara mata kwanciyarta. Yau Arman yazo daga Abuja yana isowa twins suka tareshi da murna ya d'aukesu d'aya Bayan daya Yana musu Dariya Waiwaye suka fara suga ina Aira amma basu ganta ba Kallonshi sukayi suka ce "Hero ina cutie?Gaban Arman ne ya bada daram Dan daman abunda ya kawoshi kenan Dan hakurinshi ya k'are Gwara a bashi matarsa ya nema mata lafiya Dan kwanakinnan duk cikin 'kaya ya yisu Mummy ce ta Kalleshi dake tsaye ta ce " Yaran nan Dan Allah a kaisu suga mamansu ni wlh tausayi suke bani"Ajiyar zuciya ARMAN ya sauke ya ce "Bari idan na huta na kaisu amma ki fara tambayar Daddy idan ya yarda " murmushi Mummy tayi ta ce "Zan tambayesa dukda nasan bazai hanaba saboda na lura tundaga mutuwar Inna dad d'inku baida walwala yayi sanyi duk ya sauke wani Abu dake kanshi" Bayan Arman ya huta Mummy ta shirya twins da sai murna suke yau zasuga mom d'insu Mummy koda ta tambayi Dad cewa yayi akaisu suga Mahaifiyarsu tunda ma weekend ne su yi kwana biyu a Chan"Bayan Arman ya shirya misalin hud'u na yamma ya d'auki yaranshi a mota Inda saida ya biya ya jibgo uwar sayayya su Malta cartoons madara,Custard, Juice kala kala Da sauransu saida aka cika boot din motar da kaya Tukwana ya nufi gidan su Aira suna isa Kallon Twins yayi ya ce "Ku shiga to kuga mom din taku gobe zanzo na Daukeku" Naila ce ta zaro ido ta ce "Hero mom ai bata nan dad enta da mukaje ya kolemu" Danne zuciyarshi Arman yayi ya ce "Ku je tana ciki yanzu bazai kore ku ba" ya fad'a yana fitowa tare da kama hannunsu Ya kaisu Har bakin Kofar gidan saida yaga shigarsu Yana musu bye bye tukwana ya koma Almajirai ya samu suka shiga da kayan cikin gidan dafe ganshi yayi dake mugun saramai ji yake kamar shiga ta fito da matarsa da yaronsa dake gidan Wayarshi ya lalubo tare Danna kiran layin Aira Amma na d'auka ya ce "Fitomun da Haidar Ina kofar gidanku" To ta fad'a A lokacin da twins suka shiga palourn gidan Sosai akayi mamakin ganinsu Aysha ta taryosu ta ce "oyoyo my twins yau kune a gidan" Shiru sukayi suna kalle_Kalle So suke suga Aira amma basu ganta ba Mamy ce ta fito ta ce "Ah yau manya garemu a gidan kenan " Duk shiru sukayi basuce komai ba sai waige waige da suke "Mama ce ta ce " Yau ba a y'an maganar kuke ba kenan?Naila ce ta fara hawaye tare da Kallon Mamy ta ce "Mom ena cutie " Nihal kuma ta fara kuka ta ce "Ina mom d'inmu" kama hannunsu Mamy tayi tare da kaisu d'akin da Aira ta ke Inda suka sameta kwance da gudu Suka ruga Wajenta tare da hayeta suka fara girgizata suna mom ki tashi"Hayaniyarsu ta tayar da Aira Kallonsu ta dingayi da ido su kuma Rungumeta sukayi suna murnar ganin maman tasu "Mummy na tsaye a kansu Amma ce ta fito daga toilet Bayan tayiwa Haidar wanka ta shirya shi Kallon Mamy tayi ta ce " Mamy babanshi ya ce na kaishi Bari na kaisa"ARMAN dinne ya kawo yaran kenan"Eh Mamy "Bazai shigo ba kenan" Girgiza kai tayi ta ce "Wlh bansaniba" Ki kai masa shi "Mamy ta fad'a " Su mamy nan sukaga ana ta shigowa da uwar sayayya suna gani suka san arman ne ya aiko Fita amma tayi da Haidar a hannunta da yake ta zillo a gaban mota ta samu Arman Inda ta gaisheshi Ya amsa cikin mutuntawa Mik'a masa Haidar tayi ta ce " Gashi yaya"Amsarsa yayi ya ce "Nagode Sis Ya jikin cutie din da sauki" da sauki yaya yanzu tana samun sauki bazakaje ka ganta ba?Girgiza kai Arman yayi ya ce "Allah ya bata lafiya Dan Allah ku dinga kula da ita sosai ga twins nan zasuyi kwana biyu shi kuma Haidar ki cewa Mamy na tafi dashi yayi mana kwana biyu Idan nazo daukarsu saina Maidosa ki gaishe da y'an gidan to amma ta fad'a tare da yiwa Haidar bye bye Dan sosai ta shaku dashi a Rashin lafiyar da Aira tayi ita ta zame masa uwa twins sosai suka lafe jikin Aira wacce ta kasa daga baki tayi musu magana ganin tayi shiru ya sanya Nihal shafa Fuskarta ta ce "Mom bazaki mana magana ba ko munyi miki laifi kiyi hakuli bazamu sake ba" Naila ce ta fara hawaye ta ce "Mom kiyi magana" Saida Mamy ta Goge hawayen tausayin yaran "Magana suka dinga mata wanda hakan yasa aira taji kanta ya fara juyawa saiji sukayi ta fasa.k'ara tare da sulalewa wajen summammiya Sosai y'an gidan suka nufo d'akin hankali tashe twins ko kuka suka sanya suka hau jijjigata suna mom.ki tashi karki mutu ki tashi mu tafi Abba ne da ya shigo duba jikin na Aira dan yajiwo ihunta ya samesu a haka suna ganin Abba Suka rude suka hau jijjigata suna cewa " Mom ki tashi Ga dad enkinan Ki tashi mu tafi karya dakeki ki tashi mu koma gidanmu"Mamy ce dak'yal ta samu ta banbaresu daga jikin Aira suna kuka Naila Abba ya yunkura ya d'auka Dan baiji dadi ba har ranshi yanda yaran suke tsoronshi sosai Naila ta k'ara yiwa kukanta volume Lallashinta Abba ya fara cikin sigar Lallashi da kwantar da hankali "Harya samu tayi shiru ta lafe a jikinshi Nihal ko kuka ta ke ta kalli Mamy ta ce " mom en Cutie a kaita hospital karta mutu"Kallon Abba Mamy tayi ta ce "Ko Asibiti ake kaita Abbansu?Shiru Abba yayi kamar mai nazari sai kuma ya ce " Bari na kira dr din yazo ya duba ta a gida haka ko akayi Dr d'in har gida yazo Inda ya duba ta Sosai sukayi jugum jugum yana gamawa Ya juyo Ajiyar zuciya ya sauke tare da Yin hamdala ya ce "Alhamdulilla Ta dawo daidai ne data tashi Insha Allah zata dawo yanda take Saidai a dinga Lallashinta Sannan kar a dinga tuno mata da Abubuwan da suka wuce Dan Gaskiya a tunani na ba tension din mutuwar nan kawai ya sanya ta samu matsalar nan akwai damuwa sosai a tattare da ita Wanda a age d'inta kwalwarta bazata d'auka ba Allah kiyaye gaba " Hamdala kowa ya sauke Sukace ameeen sosai suka yiwa dr din Godiya Abba ne ya ce "Yanzu zuwa yaushe zata farka" ?zuwa gobe zata iya farkawa a barta ta huta kar ayi hayaniya a kanta "Godiya duk sukamai Abba ya ce Duk a firfita a barta ta huta Shi ya fita da twins da suke kuka ya lallashesu Bayan ya bawa Haidar ya sayo musu choculate Aiko nan suka D'are Abba Suna murna Take suka waske suka fara masa surutu Sosai hakan yawa Abba dadi koba komai dai yanzu yaran sun daina tsoronshi dukda har yanzu baisan ta yanda aka samun yaran nan har Ukku ga cikon na hud'u " Arman daga gidan su Aira wani mall ya biya ya jibgowa yaron nashi sayayyar kayan sawa da kayan wasa gidan Mummy ya wuce Amsar Haidar Mamy ta yi ta ce "Lale marhaban mai Gidan har gida" zaunawa Arman yayi tare da sadda kai ya dafe kanshi"Kallonshi Mummy tayi ta ce "Lafiya dai son"? d'agowa yayi ya ce " Mummy wai yaushe zasu bani mata ta?Shiru Mummy tayi ta ce "Inason naje ma naga jikin nata wlh amma bari anjima muyi magana da Dad dinka in ya bari jibin sai naje na ganta Ka bar maganar dawowarta Arman ka bari ta samu sauk'i kuma tunda mahaifinta ya fara Saukowa ka bari su sasinta da mahaifinta kamar yanda ka sasinta da mahaifinka muyi mata adalci itama Mu bari iyayenta suma suyi iko da y'arsu tunda wancen lokacin munyi musu haka koni kaina sainaje na nemu yafiyar mahaifinta saboda bamubi yanda shari a ta tanadar ba a aurenku mu samu mu warware matsalolin nan Inajin a jikina komai yazo karshe" Ajiyar zuciya Arman ya sauke Tabbas maganar Mummy Gaskiya Ce soyayyar da zai nunawa Aira a yanzu ita ce Ta sasinta da mahaifanta da dare Mummy ta samu Daddy da maganar zataje taga jikin Aira cewa yayi zata iya zuwa amma akayi mata wulakanci ba ruwanshi cewa Mummy tayi ta yarda tunda dai ya amince taje din da sauki. Washegari kamar yanda Dr ya fada tunda safe y'an gidan suka sanya Aira gaba Suna jiran farkawartata har Naila dake jikin Mamy Suna wajen Abba ma yana d'akin Nihal na jikinshi Dan tun jiya ta like mai A hankali ta fara bud'e idonta da sukayi mata nauyi harta k'arasa budesu saukesu tayi akan y'an gidansu kowa Ajiyar zuciya ya sauke Sukace alhmdllh Naila da Nihal da gudu sukaje suka Fad'a kanta sukace "Mom kin tashi" Kallonsu Aira tayi d'aya Bayan daga abubuwan da suka faru suka dinga dawo mata a kwalwa rumtse idonta tayi tare da budesu wasu zazzafan hawaye ne suka shiga zubo mata kallon Mamy tayi ta ce "Mamy wai da gaske ne Inna ta mutu?Kama hannunta Mamy tayi ta ce " Hakan da kikayi ayra ba soyayya bace kike nuna mata Shi mamaci a koda yaushe addua yake buk'ata bawai Dan anyi mutuwa ka shiga tashin hankaliba Wannan din kamar Rashin tawakkaline karfa ki manta mutuwa na wuyan kowa kuma muma bamu wuce ta d'auke muba a kowani lokaci kema Da mu jiranta muke addua zaki mata ba kuka ba kinji"hawaye ne suka zubowa Aira ta Goge ta ce "Allah ya jikanki Inna yasa kin huta ked'in kinyimun komai a rayuwa halinki na gari ya biki Tabbas nayi Babban rashi Inna shakuwarmu da mukayi shekara da shekaru shikenan yanzu kin tafi kin barni" Rungumeta Mamy tayi ta ce "Is okay kukan ya isa Haka kiyi mata addu'a kinji" Saida Aira tayi kuka sosai jikin Mamy kafin ta hakura tayi shiru Dagowa tayi ta kalli Mamy ta ce "har an binneta mamy"?,Yanzu watan Inna Biyu da rabi Ayra tunda ta mutu kika zautu sai yau Kika dawo hankalinki " Sosai Ayra tayi mamaki Ace wata biyu kenan da rasuwar Inna ji take kamar yau ne duba jikinta tayi taga ciki jikinta ya fara girma sosai tayi mamaki ita dai ko lokacin nan bata San tana da ciki ba "Nihal da Naila ne sukaje Wajenta suka Rungumeta suka Ce "Sannu mom " Rungumesu Aira tayi tare da Kallon Mamy Dan bata lura da Abba dake dakinba ta ce "Mamy bari muyi Sauri mu tafi kar Abba ya dawo ya samemu Ta fad'a tana yunkurawa tacewa twins ku taho mu tafi" Ba Inda zaki koma ki zauna Mamana "Suka tsinkayi Muryar Abba " Sosai Ayra tayi mamakin jin kalaman Abba da batayi tsammani ba Bama ta San yana wajenba Kallonshi tayi hawaye na zubowa daga idonta sai kuma tayi k'asa da kanta ta ce "Dan Allah Abba kayi hak....shit Abba ya fad'a tare da cewa " banason jin komai ki huta Sannan ya kalli Mama ya ce "A bata abinci taci sannan Tasha magani " To Mama ta fad'a Abba na gama fad'ar haka yabar palour kowa saida yaji dadin ganin saukowar ta Abba Bayan fitarsa Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da Kallon Mama ta ce "Allah yasa Abba ya yafemun" murmushi kawai ta mata nan kowa ya shiga yi mata Sannu Inda Amma Cikin farinciki ta kira Aysha Da Ummy ta fad'a musu samun lafiyar ta Ayra A lokacin da Aysha Tazo sosai Ayra tayi farincikin ganinta da tsohon ciki nan suka Rungume suna suna murna Ummy ma tana da wani k'aramun cikin Dan d'anta harya girma Itadai Aira shiru tayi tana son ta tambaya ina Haidar d'inta tana jin nauyi ga ARMAN da takeson taji yana ina Dan bata gansa ba Da dare Suna daki ita da Amma suna ta hira Ta ce "Sis wai ina Haidar " yana wajen babanshi jiya da ya kawo twins Ya tafi dashi gobe zai maidosa ya ce Ai kullum saiya kira ta wayarki ni nake d'auka yaji halin da kike ciki"Shiru Aira tayi tana nazari kenan Arman wata biyu bai ganta ba kenan Tasan Tabbas daman indai tana gidansu ne bazai tab'a taka kafarshi gidan ba yanda yake da bak'ar zuciya Shiru tayi bata Kara cewa komai ba washegari tunda Safe Abba ya sanya Driver ha kaisu Aira Asibiti Wanda Mama tayi mata rakiya Inda akai checking lafiyarta da abunda ke cikinta Alhmdllh komai normal Jikinta yanzu watanshi biyar Ya shiga na shidda nan aka rubuta musu magunguna suka dawo gida Suna zazzaune twins na bangaren Abba Suka jiyo sallama Amsawa sukayi Haidar babba ya je ya bud'e Mummy ce ta shigo Tare da Haidar A hannunta sosai Su Mamy suka tarbeta cikin girmamawa da mutuntawa Nan aka shiga gaisawa sosai Mummy tayi farincikin samun lafiyar na surukar tata Sosai tayi hamdala nan suka Rungume juna ita da Aira Haidar ko Amma ta amsheshi Dan tayi kewarshi sosai Nan aka shiga jajinta abunda ya faru Aira dai na like da Mummy Arman ko yana kawo Mummy yajuya ya koma A hankali Aira take kallon Haidar d'inta taga Ya girma masha Allah ga ya k'ara wayau ganin Yanda ya lafe jikin Amma kamar itace mamansa "Murmushi tayi musu Tana kallonsu Shima ita d'in yake kallo" Amma ce ta nuna masa ta ce "Ga Mom je ku gaisa" Lafewa yayi jikin Amma yana tsotsar yatsa Alamun bazaijeba "Murmushi Aira tayi sosai taji dad'in yanda taga y'ar uwar tata tana kula mata da d'anta Dan yanda taga ya like mata to Ta tabbata ba k'aramar kula ta bashiba a kwanciyarta. Da Mummy zata tafi Bayan ta Aje sayayyar da tayo Sosai tayi wa su Mamy Godiya sannan ta ce a rakata su gaisa da Abba Mamy ita ta rakata har part din Abba Suna tafe Mamy nayi mata Godiya akan Abubuwan da Aira ta bata labarin ta dinga mata cewa tayi ba komai ai Ayra da Arman duk d'aya suke a waje na " Suna isa palourn Abba Inda suka tarar twins Na cinyarsa suna Danna laptop suna ganin Mummy da gudu Suka tashi tare da Rungumeta "daukarsu d'aya Bayan daya tayi ta ce " Oyoyoy yaran Mummy ya weekend din "Alhmdllh suka fada a tare da tsallen murnar ganinta Mamy ta Ce " to ku bar mummyn taku ta zauna ko "Sai sannan suka bar Mummy ta zauna " Kallon Abba tayi da ita yake kallo ta ce "Ina yini Yaya munsameku lafiya" Lafiya qalau Fatima ya Gida"Alhmdllh Abba Mummy ta fad'a tana sauke ajiyar zuciya jin ga Alamun Abba zai saurareta "Madalla " ya fad'a Mamy ce ta fita tare da twins Dan su basu wuri su tattauna "Bayan fitarsu cikin ladabi Mummy ta ce " Daman hakuri muka zo baka yaya akan laifin da mukayi maka ni da yarana Dan Allah kayi hakuri ka gafartamana "shiru Abba yayi kamar mai nazari sai kuma ya ce " ai babu abunda zance kin tab'ayimun na b'acin rai Fatima tsakani na dake Sai mutunci da mutuntawa bakiyimun komai ba Allah yafe mana tare"a a a yaya Munyi maka laifi babba Wanda nice mai laifin ma dai a Gaskiya Dan ni na had'a Auren yaran nan bada saninku ba ?Aure!!!!Abba ya fad'a mamaki k'arara a fuskarsa "Shiru Mummy tayi Chan kuma ta ce " Eh Yaya Aure.....tas ta basa labarin abunda ya faru a yola Har zuwa yanzu "Sosai Abba ya shiga kogin tunani kenan yaran nan yaran sunna ne " a fuska bata iya Tantance yanayin da yake ciki b'acin rai ko akasin haka amma a fili cewa yayi "Allah yasa haka shi yafi zama alkhairi " Ameeeen Mummy ta fad'a tare da Yin shiru ganin Abba bai sake cewa komai ba ya sanyata rasa abun cewa Mikewa tayi ta ce "To zan wuce Yaya mungode Allah Kara girma zan wuce da twins Gobe za a koma makaranta" Ai nazata zasu kwanan mana biyu to shikenan Allah tsare hanya "Ameen Mummy ta fad'a tare da fitowa bata gane dai abunda Abba yake nufi ba Tana fitowa Mamy ta kira a waya ta ce " Twins su fito mu wuce ?To gasunan Mamy ta fad'a tare da Kallon Aira ta ce "Zata tafi da su Naila saboda Makaranta daman weekend ne suka zo mana " To Mamy Ayra ta fad'a tare da mik'ewa ta sanya k'atuwar hijab d'inta ta kama su Suka fito a harabar gidan ta tarar da mummy na jiransu Murmushi ta sakar mata tare da dafa Aira ta ce "Ke kika fito da kanki kenan daughter Aida kin huta saboda yanajin jikin naki" Murmushi Ayra tayi tana kasa da kanta ta ce "Ai da sauki Mamy a gaishe da su Dady ta fad'a tana mik'a mata kayan su twins " Ansa tayi ta ce "zasuji me kike buk'ata na bada driver ya kawo maki" Murmushi tayi ta ce "bana buk'atar komai Mummy nagode Allah saka da alkhairi" Duk yanda Mummy tayi Aira ta fad'a abunda take so kin fad'a tayi "To tunda kinki fad'a na bada sako yanzu akawo maki" Mummy ta fad'a tana kama Nihal dake shirin sillewa ta ce "Ku wuce mutafi sarakan wasa" Murmushi Aira tayi tare da musu bye bye "suma bye bye suka mata Naila ta ce " Mom bakice a gaishe da Hero enki ba"Dariya Mummy tayi itama Airar Dariya tayi Tare da girgiza kai ganin sun fita ya sanyata komawa Ciki ta na tunanin sahibitin nata.........✍🏿 *Ni da Yaya Arman it’s not free it’s for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* *_Miss Hajo ce_* [7/24, 12:52] Hajo hajo: 🅿️..........*125&126* Tana tunanin sahibin nata Koda Mummy ta koma ta fad'awa Arman samun lafiyar Aira zokuga farincikin da ya shiga Kiran wayarta yayi tayi a lokacin wayar na silent bata gani ba Da dare Aira na zaune a palour suna Hira da y'an gidansu Dukda ba wani sakewa take sosai ba Amer yazo ya ce "Ya Ayra Abba yace kije" Saida gaban Ayra ya fad'i cikin dauriya ta mik'e ta sanya hijab d'inta Kallon Mamy tayi Gyada mata kai tayi Alamun ta je gabanta na fad'uwa ta isa part din da Sallama ta yi knoking ya bata izinin shigowa tana shigowa kasa ta samu ta zauna nesa dashi tare da Yin kasa da kanta ta ce "Ina yini Abba" Lafiya qalau ya jikin naki"Alhmdllh "ta fad'a masa kasa-kasa" Jim yayi kamar bazaiyi magana ba saikuma ya ce "d'ago ki kalleni zamuyi magana dake kuma kika kuskura kikamun karya kinsan zanganeki Gaskiya nake so ki fad'amun Dazu Hajiya Fatima tazo munyi magana da ita ta fad'amun komai na shirya aurenku Da tayi to ni wannan bai daman ba Sosai Saidai Annunamun ban isa dake ba Wanda ke kika bada kofar yin haka to wannan ya wuce tunda Allah ya kadarta auren ba wanda ya isa ya Hana tunda gashi hada rabon yara Maganar da zamuyi akan Aurenki Da Alh Madugu tun lokacin da abun ya faru Ya kirani yake sanarmun Sunje Asibiti Anga ciki Jikinki Bayan nan sun kamaki keda Mujahid daki daya " To abun nan har yanzu shi yafi mun ciwo Gaskiya nakeson ki fad'amun shin maganar Gaskiya Ce haka take ko Ko?Tuni Idon Aira harya cika da k'walla ta ce "Wlh tallahi Abba ko da Al'kur ani zan iya rantse maka wlh ban tab'a zina ba Da kowa ba bare kuma *NI DA YAYA ARMAN* sharri ne kawai suka mana sannan babu wani ciki a lokacin Typord ne ke damuna suka mun sharri sukace ciki" ta k'arasa fad'a tana fashewa da kuka"Shiru Abba yayi na d'an wani lokaci yana nazarin maganganunta A yanda tayi maganar yasan Tabbas Gaskiya take fada Cewa yayi "Kin tabbatar maganar haka take" Tana kuka ta ce "Wallahi Abba idan akwai karya a maganar nan kar Allah ya maidani Cikin gida lfy" Sosai ran Abba ya b'aci kenan sharri ne Madugu yayiwa y'arshi kenan shiyasa bai Kara kiranshi akan maganar ba Aiko cikin b'acin rai ya lalubo wayarsa tare da dannawa Alh Madugu kira Ring biyu ya d'auka tare da cewa "Alhaji Abubakar kana lafiya " Cikin fushi Abba ya fara magana da cewa "Daman kai ba mutumin kirki bane na d'auke ka na baka y'a saboda yarda da kuma amintar mu da na duba ka rasa Dame zaka sakamun saida b'acin suna Ka k'ullawa y'ata sharrin zina da kuma sharrin ciki to bari kaji wlh baka isa kaci lilis ba Saina makaka a kotu ka kawo shaidun Inda ka kamata mutumin banza da wofi kawai"Sosai Alh Yusuf ya rikice cikin waya ya fara cewa " Dan girma Allah ka tsaya ka saurare Alhaji Duka abunne yazo a wani iri Rashin bincike da zurfafa bincike yasa aka samu matsalar wannan wlh banyiwa y'arka sharri ba Daga asibitin ne suka bada result d'in ba daidai ba muma saidaga baya suke shaida mana mistake ne aka samu aka bata result d'in wata ita waccen Aka bata nata ashe typord ke damunta sannan ni bani da shaidar da zance na kama yarka tana iskanci duk Rashin bincike ne ya kawo haka har yanzu nima ina nadamar abunda na aikata Inajin kunyar zuwa na baka hakuri sannan nayi bikonta Dan wlh inason mata ta har yanzu”sosai ran Abba ya k'ara b'aci ashe Gaskiya ne kenan Aiko cikin fad'a ya ce "Zaka maimaita Duka wannan bayanan a gaban alkali mutumin banza Sannan Kai bakaji kunyar na k'ara maido maka y'a ba a karo na biyu to idan baka sani ba ka sani tun sanda ka saketa tayi Aure yanzu haka Yaranta Ukku Dan haka kaida ita har abada sannan saina nema mata hakkinta na b'ata mata suna da kayi ka jirayi sammaci Abba na gama fad'ar haka ya katse kiran sai huci yake saboda b'acin rai Aira Duka taji abunda Alh Madugu ya fad'a Dan a hands free Wayar take sosai taji dad'in yanda Abba yayi mishi kuma ya nuna zai nemo mata y'ancinta bata gama wannan tunanin ba ta tsinkayi Muryar Abba da cewa " tashi zaki iya tafiya gobe kiyi sammako Mu tafi court saina maka Dan iskan mutumin nan a gaban hukuma "Mikewa Ayra tayi ta ce " To Abba Tare da dukursawa ta ce "Dan Allah Abba ka yafemun irin Abubuwan da nayi maka a baya nayi nadama Kuma na tuba na shirya yi maka biyaya akan duk abunda ka bani umarni a kansa amma Dan Allah ka yafe mun"Taso da ita Abba yayi ya ce " Na jima da yafe maki Mamana Allah yayi maki albarka ya shirya miki yaranki Na yafe maki duniya da lahira ko yanzu kika mutu baki mutu Da hakkin mahaifi a kanki ba sannan nima ki yafemun irin abubuwan da nayi miki na rashin Adalci zafin zuciya ne da fushi ya rudeni harna dinga maki abubuwan da namaki ki yafemun nima na yafe maki duniya da lahira Allah maki albarka mamana "Ayra harta ta manta yaushe rabon da tashiga cikin farincikin da ta shiga ba irin na yau Ai batasan lokacin data Rungume Abba ba ta ce " Nagode Abba Allah ya saka da alkhairi Tabbas kaid'in ka cika uba na gari bakayimun komai da zan yafe maka ba duka laifi nane na rashin maka biyayya da nayi nagode Abba “ta k'arasa fad'a tana hawayen farinciki Sosai Abba yakejin ninkin soyayyar yaratshi na shigarshi Dan har yanzu Aira ta daban ce a cikin yaranshi son da yake mata na daban ne"Da gudu Aira ta saki Abba Tare da rugawa part d'insu Dan tayiwa y'an uwanta da Mamy albishir tana zuwa Cikin farinciki ta Ruga ta Rungume Mamy daka Kalleta kasan tana cikin farinciki " Kallonta duk sukayi tare da cewa "Lafiya Ayra cikin " Tsananin farinciki ta d'ago ta ce "ku tayani murna Abba ya yafemun duk abunda nayi masa da bakinsa yanzu ya fad'a ya ce ya yafemun duniya da lahira" Cikinsu babu Wanda baiyi farinciki ba duk hamdala sukayi "Nan Aira ta basu labarin yanda sukayi Da Alh Madugu Dariya Mamy ta yi ta ce " Ai gwara da suka k'are a hakan shi aminta dadi hada d'aukar Y'a sukutum ka aurawa tsoho ai yanzu an k'are. Tsiya tsiya wani kotu kuma Bayan Allah ya bayyana Gaskiya "Dariya Ayra tayi Jin maganar da Mamy tayi ta ce " ai gwara a kwatomun hakkina na b'atamun suna da yayi ta fad'a tana Mikewa taja hannun Amma suka nufi daki Dan su Kara labatarwa "Mamy ko da Mama tattaunawa suka dingayi akan Lamarin Sannan sukaje suka samu Abba dak'yal suka samu suka shawo kanshi akan yayi hakuri ya barsu da Allah sakayyar Allah tafi ta kotu A haka suka samu harya hakura ya janye maganar Karan . Aira na komawa daki wayar Ta ta lalubo nan ta shiga kiran y'an uwanta su Aysh,ummy,Aunty Maryam,Mama Halima duk tayi musu albishir da Abba ya yafe mata zokuga farincikin da y'an uwanta sukayi musamman Mama Halima daman Arman Daddy Ya yafe masa yanzu Abu d'aya ya rage Daidaituwar Abba da Daddy Shima kuma suna sa ran insha Allah zasu shirya. Sai sannan Ayra ta duba wayarta taga missed call d'in da Arman yayi mata Tana cikin liliyar wayar taji yana kira saida taja aji tukwana ta d'auka tana turo baki" Daga bangaren Arman Ajiyar zuciya ya sauke ya ce "My cutie " Turo baki Ayra tayi ta ce "Uhm ba wani cutie ashe duk Rashin lafiyar nan da nayi bakazo ka ganni ba " Am Sorrry Matar aljanna farincikina Uwar yayana Macen da babu kamarta a fad'in duniyar nan tauraruwa mai Haske a cikin taurari kiyimun Afuwa sannan kiyimun uzuri kinsan dai ason samune bazanso muyi second d'aya batare da juna ba Wlh inason zuwa ganinki ina tsoron Wulakancin da Abba zaiyimun shi ya hanani zuwa Kinsan dai bazai barni na shigo cikin gidansa ba ni kaina kwanakinnan a kaya na yisu"Uhm kawai tace "Cikin damuwa ya ce " Fushi zaki yi dani My nurul khalbi kiyi hakuri Kinsan Gaskiya nake fad'a maki"cikin shagwaba ta ce "Na hakura Hero " Ajiyar zuciya ya sauke har tana ji daga waya ya ce "To ykk ya jikin naki my cutie " Alhmdllh hero "Masha Allah haka nakesonji Allah ya k'ara maki lafiya ya my unborn" Turo baki tayi ta ce "Ameeen wai ashe yaya ciki ne dani bansani ba Gashi harya girma Haidar fa ko shekara baiyi ba Yaya kamar wata kaza" ta fad'a tanajin kamar zatayi kuka "Arman saida yaso yayi Dariya Amma Dan kartaji Haushi ya fusge tare da marairaicewa ya ce " wayyo sorry cutie d'inmu Aike jaruma ce So nake ai ki cikamun gidan da kyawawan yara kamar 30 haka ba yawa"Wara idanu tayi kamar yana ganinta ta ce "Chab Yaya 30 fa saikace wata Akuya" Sosai Arman ya sanya Dariya daman Dan ya dara yayi maganar Ayra ko turo baki tayi ta ce "Dariya ko ai dole kayi Dariya tunda baka tab'a shiga labour room ba kaidai kawai ganinsu kake " daidaita dariyarshi yayi ya ce "Sorrry Oum twins d'inmu kece kika bani Dariya to yanzu dai ayi hakuri a cigaba da kulamun da unborn Allah ya saukeki lafiya Yanzu yaushe zan ganki" ameen ta fad'a tare da cewa "Albishirinnka honey tun d'azu nake son nayi maka Albishir farinciki ya hana " Cike da zak'uwa ya ce "Goro my prince's wannnan wani Babban Albishir ne " Tana murmushi ta ce "Yaya Abba ya yafemun Duniya da lahira " Arman yana daga kwance saida ya Mike ya ce "Da gaske kike cutie " Wlh kuwa yaya nan ta bashi labarin abunda ya faru"Ajiyar zuciya nauyayya ya ce "Alhamdulilla Alhmdll Allah nagode maka Tabbas komai yayi tsanani akwai sauki Nan gaba Ashe muma saukin namu na kusa Amma nayi farinciki marar musaltuwa cutie shikenan yanzu nidake gaba d'aya Bamuda hakkin iyaye a Kanmu Duka sun yafe mana Amma nayi farinciki" tana murmushi Ayra ta ce "Wlh nima nayi farinciki Sosai yaya Inajin a jikina komai yazo karshe yanzu saura Daddy da Abba kawai shiryawarsu ta rage " Insha Allahu suma zasu shirya saboda tundaga mutuwar Inna naga sun yi sanyi Allah ya nuna mana wannan ranar da cikar burin Inna "Ameen Ayra ta fad'a " Sun tab'a Hira sosai cikin so da k'auna Wanda saida bacci ya d'auke Ayra bata ma saniba tukwana Arman ya kashe kiran Washegari aka kira aka shaida musu Aysha ta haihu ta haifi y'arta mace zo kuga farincikin da wannan iyalan suka shiga kodan Aysha ta jima bata haihu ba Musamman Ayra da ta rasa Inda zata sanya ranta saboda Farinciki sati na zagayowa yarinya taci suna Halimatu ana cemata Shukura anyiwa mariganyiya Inna takwara Wanda koda yaushe Ayra da Arman Cikin waya suke da juna ba yanda Arman baiyiba Akan Mummy ko dad suje akan maganar dawowar Ayra dan baigane nufinsu ba Rik'e amsa mata ba Amma Duka sukace bazasu je ba A bari ubanta yayi iko a kanta Kuma Sosai Arman yakejin haushin Dan koda ya koma wajen aikinshima hankalinshi ya raba biyu rabi yana Wajen Ayra Gashi itama ta kiya masa Dan duk lokacin da yace kawai ta shirya ta taho su komawarsu gidansu Sai ta ce "a a a yayi hakuri aga abunda Abba yake nufi A yanzu cikin Ayra ya k'ara girma sosai Inda bikin Hafsat da yaya Omar ya rage wata hud'u kenan tun yanzu amfara shiga busy din hidimar biki Dan su Ayra Abu biyu bangaren ango bangaren Amarya Danma dadinta d'aya Lokacin bikin sannan ta haihu dan yanzu cikinta watanshi Bakwai saura wata biyu ta haihu twins ko duk week end Mummy take badawa akawosu A maidasu Wanda hakan sosai yake yiwa Ayra Dad'i Ana haka Itama Amma aka sanya Aurenta da Wani Saurayinta AL_Ameen tun a B U K suka had'u Wanda aka had'e bikin rana d'aya da na Hafsa zo kuga farinciki wajen Ayra duk ta rasa Inda zata sa ranta Dan murna Yau Arman yazo kano Wanda Hakurinshi ya soma karewa so yake ya had'u da Cutie d'inshi a kofar gidansu yayi parking tare da hade rai irin ba wasa d'innan ya Danna mata kira tana d'auka ya ce " Ki fito ina kofar gidanku"Dariya tayi har yana jinta ta ce "Hero yau kuma zolaya kakeji" ba wasa ba ki fito yanzu karki bata mun lokaci ya fad'a yana katse kiran "Dariya Ayra tayi Jin yanda yayi maganar nan irin ba wasa d'innan hijab d'inta ga zira tare da takalmi Mamy ce ta Kalleta ta ce " Ina zuwa kuma"Sosa kai tayi ya ce "Uhm Dadyn su twins ne yazo zamu gaisa " Mamy batace uffan ba Ganin haka ya sanya Ayra fitowa tana bud'e get d'in gidan ga mamakin ta kuwa ta hangoshi tsaye jikin mota ya Rungume hannayenshi Fuskarnan tashi a had’e"Dariyarta ta Had'iye tare da nufar Inda yake Arman ko tundaga nesa ya k'are mata kallo Sosai ta k'ara masa kyau da kwarjini a y'an kwanakin da yayi bai ganta ba ga cikinta da yaga yayi wani irin girma na ban mamaki baisan lokacin da ya sakar mata murmushi mai narkar da zuciya ba Itama mayar masa tayi da kalar nata murmushin tare da karasawa garesa ta ce.........✍🏿 _*Miss Hajo ce*_🤙🏿 [7/24, 12:52] Hajo hajo: 🅿️........*127&128* _*Semi Final*_💃🏿🥹 Ta ce "Ashe da gaske kake my hero I miss you so much Wlh " Ta fad'a tana marairaicewa "kama lallausan hannunta yayi Cikin kasalalliyar murya ya ce " Naki a baki ne cutie ba k'aramun kewarki nayi ba "Uhm ai naga harka rame wlh yakake ya zaman gauranci ta fad'a tana Dariya" Hararar wasa yayi mata tare da shigar da ita mota Shima ya zagaya ya shiga ya ce "dole kicemun gauro Tunda dai an maidani na karfi da yaji" Kama hannunshi Ayra tayi ganin yana shirin tada mota ta ce "Yaya ina kuma zamu please ka tsaya " Bai saurareta ba sai Tada motar da yayi ya ce "Allah baki isa ba Yau saina Rage zafi ya fad'a yana Jan motar da karfi " Duk yanda Ayra ta firgice amma bata nuna masa a fili ba "Uhm kawai ta ce " Cikin zuciyarta kuwa tsoro ne fal a ranta Dan batasan Inda zai kaita ba gidansu dake nan kano taga ya nufa haka yasa ta Dan kwantar da hankalinta suna isa daukarta yayi ba tare da jin nauyi ko wani Abu ba bai dire ta ko ina ba sai Bedroom d'inshi Ayra na ganin hakan tasan yau Kuma saita Allah tutturo baki ta dingayi ta ce "Yaya Banda lafiya fa har yanzu" Hararar wasa yayi mata ya ce "Ai zaki warke yanzu zan baki magani......Bayan komai ya lafa Ayra sai nishin wahala take Dan ta gurzu ba Kad'an ba wanka ta yunkura tayi tare da fitowa ta sanya Kayanta da Tazo tashi dukda sunyi squeeze Kallonshi tayi da shidinma ita yake kalla yana k'are mata kallo ta galla masa harara ta ce " ai saimu tafi gida ko"Mirginawa yayi tare da kwantawa ya ce "Akwai gidan da ya wuce wannan kin dawo gidanki ai" D'ora hannu aka Ayra tayi ta ce "Na shiga ukku yaya so kake Su Mamy su tsigeni To wlh nidai ka maidani gida " Dariya yayi mata tare da mik'ewa ya ce "Kina da gidan da yafi na mijinki daman" Kuka ta sanya masa hada diddira kafa ta ce "Daman kasan wayau zakayimun shiyasa " sosai take zuba masa ruwan shagwaba shiko Dariya kawai yake mata tana nan har yaje yayi wanka ya shirya cikin shigar K'ananan kaya da sukayi mugun Amsarsa Suka Kara fito masa da ainahin kyawunsa Ita kanta Ayra da ta Kalleshi saida ta yaba A zuciyarta ta ce "Nidai nayi sa ar miji baida makusa ta ko ina ga iya d'aukar wanka " Irin Kallon da take masane ya sanyashi hure mata ido ya ce "Yadai y'an mata ko wankan yayi miki ne " Firgit ta dawo cikin hayyacinta ta ce "Uhm wankan yayi kyau sosai hero Saidai ina kishin Ace ka fita da shigar Dan Banason Ana kallemunke miji " ta fad'a tana turo baki"rungumota yayi ta baya Tare da rada mata a kunne cikin sexy voice dinsa mai dad'in sauraro ya ce "Mujaheed na Hajara ne ita kad'ai Ki daina kishinsa da yawa Dan kinriga kinyi babakere a cikin zuciyarsa babu gurbin wata dagake ba k'ari kece ta farko kece fari sannan kece karshe Kin kulle zuciyata da Soyayyarki a cikinta Wanda Kika jefar da Makullin a ruwan maliya Babu wacce ta isa ta sameshi " Sosai farinciki ya mamaye zuciyarta Ayra Tasan Gaskiya mijin nata yake fad'a mata Dan Bata tabajin tunda take a rayuwarta ba Inda akace ga budurwar Arman ko da kuwa a yarintane hakan yasa Daraja da martabar mijin nata Koda yaushe take karuwa a cikin zuciyarta cikin jin dad'i ta ce "Nasan da haka mijin da babu kamarsa kaid'in na musamman ne a cikin mazajen duniya Har gobe ina Kara godewa Allah na mallakamun kai da yayi a matsayin miji kuma uban y'ay'a na anan duniya da ma lahira insha Allahu" Sosai suka dinga zubama juna kalamai masu dad'in sauraro Nanma saida suka shagala suka k'ara ruftiyawa kogin wata soyayyar Sune dai basu gama soyayyarsu ba har magriba ganin haka ya nusar da Ayra tun Ukku rabonta da gida hakan yasa hankalinta yayi gida Bayan sun Sake wanka Ta sanya hijab d'inta hannunsu mak'ale Dana juna harsuka isa parking space Inda ya fito da motarsa a hanya saida ya biya yayi mata sayayyar kayan ciye ciye da Kaza da su juice tukwana ya wuce da ita gida a lokacin amma kusa isha i cike da kewar juna suka rabu Aira ko tana shiga cikin farfajiyar gidansu saita tuno da a da lokacin da idan suka fita da Arman da rayuwar da sukayi a baya da dramar su a gidan Inna batasan lokacin da wasu hawaye suka zubo mata ba ta ce "Bazan tab'a daina kukan rashinki ba my Inna Allah jikanki da Rahama " Goge hawayen tayi tare da shiga cikin Amma da Mamy kawai ta tarar a palourn Haidar na hannun Amma tana masa wasa "Kallon Mamy tayi ko zata nuna mata wani Abu saitaga tama kauda kanta wajen amma ta k'arasa Haidar na ganinta Ya mik'a hannu d'aukarsa tayi tare da cewa " Wannan k'aunar Sis keda Haidar zanga idan Kikayi Aure yaza ayi"Dariya amma tayi ta ce "Ai dashi zan tafi Shima Ai ya al-Ameen din ya San da wannan zancen " Dariya Mamy da Ayra sukayi Mamy ta ce "Aiko harya koroki keda d'an naki" Korama tun tana da sauki Mamy Ina aka tab'a kai amarya da d'a"Dariya amma tayi ta ce "akanmu za a fara sannan ta daga Ledar da taga Ayra ta shigo da ita ta ce " My k'anwas me aka samo mana"Dariya Ayra tayi ta ce "Sai Naji wani iri ma wlh wai my kanwa ko kunya ma baki jiba Ni yanzu ai Yayarkice tunda Harda yara Ukku " Harararta Amma tayi ta ce "Kujimun yarinya nanfa jinki kike daidaima kike da kowa To ko dai kiki ko kiso Ko d'iya d'ari kikayi Nice dai gaba dake ta fad'a tana Kai kaza baki" Dariya ayra tayi sosai ta ce"Kici a hankali karki kware uwarson girma"Mamy ce ta ce "waini Ayra ya maganar Karatu zakici gaba kuwa Dan naga amfara registration na Jamb d'in this year naga ma ke kwata kwata kamar karatun baya gabanki" k'asa tayi da kanta Ayra tayi ta ce "Ba haka bane Mamy Ni wlh wahalar ce Nake tsoro Ga Haidar Kinga Ko shekara fa Baiyi ba Yanzu idan nace zanjona karatu zansha wahala kuma ma shi baiyi mun maganar makaranta ba har yanzu bamuyi maganar dashi ba" Tab'e baki Mamy tayi ta ce "Ai karatu baya hana kula da yara Ni Ina goyonki Nayi NCE Dina Hankali kwance kuma" Dariya ayra tayi ta ce "Mamy Ai Inna tace Lokacin baki iya komai ba ita ke Reno na Ke ai y'ar dad'in Inna ce a bulus kika sameni" pillow mamy ta d'auka tare da nufar ta dashi zata Jefa mata ta kauce tana Dariya ta ce "ja ira da yake ke kikayi nak'udar kika haifi kanki ko" Dariya ayra tayi tana barin Palourn bedroom dinsu ita da Amma ta nufa sosai tayi hawaye tunowa da irin labaran da Inna ke basu Da dramar da ake sha a part d'inta Haidar ta sauyawa Kaya ta sanya masa pampas amma ce ta shigo da indomie A hannunta a plate Marar yaji ta zauna tare da cewa "Miko na basa yaci baici Ta dare ba " Mik'a masa shi ayra tayi ta ce "Zaki barmu da aiki fa kika tafi sis kin saganta yaron nan da yawa ace kullum sai an dafa masa indomie sau kusan hud'u Jiyafa Da na kwana dashi Cikin dare ya dingamun kuka na basa komai yakici saifa Mamy ta ce " sai na dafa masa indomie Itace kawai yake ci yanzu komin dare haka kike tashi ki dafa masa "Murmushi amma tayi ta ce " Yaronne dole a dage masa da abinci wlh ni tausayima yake ban Ace an yaye ka tun 7months da haihuwa danma hakuri garesa wlh baya da kukan banza"Jinjina kai Aira tayi ta ce "Wlhko Yana da hakuri kam ba kamar su twins ba Ai cikin nan yamun cikas wlh Afa lissafin da nayi yana da 4 months na samu wani cikin Ina ta haukana bansaniba Jifa Dan Allah wai wannan Dan yaron wata sha d'aya za ayiwa k'ani kamar wata kaza" Harararta Amma tayi ta ce "Ki godewa Allah wlh Wasu Nema ma suke da kud'in da komai Su hana idonsu bacci suna rokon Allah akan ya basu Amma ke kinsamu shine zaki butulce masa " Shiru Ayra tana Nazarin hakane kam Astaghfurilla ta fad'a tare da Kwanciya kan Gado ta cire hijab d'inta ta ce "Nikam na kwanta saida safe na gaji wlh " ba dole ki gaji ba Tun rana Kinje kuna Abu d'aya"jin abunda amma tace ya sanya Ayra bata Kara cewa komai ba kenan kowa yasan Abunda sukayi Tsaki taja a ranta ta ce "Aidai miji na ne kuje Kuyi ta zargin naku"ba bata lokaci bacci yayi awon gaba da ita.. tun daga ranar Arman ya samu kofar zuwa ya kirata itakam bata kin fitowa suyi Tafiyarsu suje su shakatawarsu ya maido ta Ayra ko sosai taji dad'i ganin ba Wanda ke hanata Fita Abba ma akwai lokacin da har ganinsu yayi amma baice komai ba Arman da yazo da niyyar kwana Ukku ya koma shine saida yayi sati kafin ya koma wajen Aiki tunda ya tafi kullum suna waya da video call Su raba dare Suna baza soyayyarsu A yanzu cikin Ayra ya shiga watan haihuwa Inda Yayi wani irin girma sosai Kamar lokacin da take Da cikin twins Sosai gidan ake kaffa kaffa da ita Mummy ma duk sati tare suke zuwa da twins taga jikin nata Ranar wata Alhamis Ayra ta tashi da nakuda sosai kai tsaye Asibiti aka wuce da ita Sosai Tasha wahala Tun safe ita ce bata haihu ba sai Bayan magriba Inda ta haifo twins d'inta Duka maza kyawawan gaske kowa yazo saiya yaba yaran Bayan an sallamesu daga asibiti koda aka kira Arman aka fad'a masa haihuwar sosai ya shiga farinciki washegari tun asuba ya baro Abuja Amma ta fito masa da Yaran Wanda yakejin soyayyarsu ta musamman Dan d'ayan kamarsu D'aya da Dad d'inshi d'ayan kuma kamanninshine sak Nanfa Arman ya shiga bishashar kudi sati na zagayowa ranar suna Yara sukaci suna Kabir da Abubakar "Sadeq da Shuraim" suma sosai akasha bishsha a sunan nasu dangi ko ta ko ina sunxo hatta Iyayen Mummy dake Yola saida suka zo har Bappa Saidai Bappa tafiyar biyu ne ta kawoshi a wani gidan daban suka sauka haka akasha bikin suna lafiya aka gama lafiya cikin kwanciyar hankali Da dare Ayra duk ta gaji Nan itada da y'an uwanta suka shiga fiddo abubuwan da ta samu bata tab'a samun alkhairi irin na haihuwar yaran nan ba kodan an haifesune cikin danginsu ba kamar haihuwar twins ba Naila ce ta shigo tana mik'a Gado ta haye ta ce "Mom bacci zanyi" Harararta Aira tayi ta ce "A nan d'akin kike kwana daman ki tafi Wajen Mamy Inda Nihal take "Turo baki Naila tayi ta ce " Ni anan zan kwana bazan kwana Chan ba"Kama hab'a Ayra tayi ta ce "Wlh idan baki tashi kintafi ba Dukanki zanyi" Kara turo baki Naila tayi ta ce "Ai daman cutie tunda aka Haifi Haidar kika daina Sonmu Nida Nihal Yanzu ma Dan An haifi wadannan Yaran shine har zakice zaki dakeni bazan kwanta gadonki ba to Kema Da su Allah bazaku kwanta ba ta fad'a tana Mikewa tare da barin d'akin " Duk da ido suka bita Aysha Da Amma suka kwashe da Dariya Amma ta ce "Wlh waccen yarinyar Sak kece Ayra kafiyar tsiya gareta ga jaraba Harta linka ki " Aysha ma tace "Ai tunda na ganta nasan Ayra ce " Tsaki Ayra taja ta ce "Wlh nema take duk ta rainani ban isa na mata magana tabi ba saidaga baya tazo tana bada hakurin munafurci" Dariya Duk sukayi Ummy ta ce "Ai kedince kema ai haka kike kizo kina hawaye kina yarfe hannu Kiyi Hakuri Mamy bazan sake ba na tuba Allah bazan sake ba " ta fad'a tana kwaikwayan yanda take magana duk Dariya suka kwashe da ita "Suna cikin Hira Ayra juyawar da zatayi wajen twins Taga kunama kusa dasu " Innalillahi ta fad'a tare da saurin d'auke Sadeq ta sauka daga gadon da hannu d'aya ta d'auke shureim "Ta ce " Na shiga ukku kunama a d'akin nan"?duk Kallon wajen sukayi da mamaki Aysha ta ce "Kunama kuma meya kawo kunama d'akin nan " Mik'a mata Sadiq Ayra tayi tana hak'i ta ce "Wlh nima bansaniba " Ummy da mamaki ta ce "Ayra twins na kwaffi daman ?Girgiza kai Ayra tayi ta ce " Nidai ban tab'a ga sunyi ba wlh "Chab Aiko wlh Naila ce Zata fito da kunamar nan kin manta tace kuma bazaku kwanta gadon ba" dafe k'irji Ayra tayi ta ce "Na bani Ni Ayra Kuma fa basu tabayiba wlh" Aysha ce ta ce "Kila k'inyi ne kawai suke " suna cikin hirar suka nemu kunamar suka rasa Dak'yal suka koma gadon suka zazzauna da anjima anjima saita k'ara fitowa ba arziki Duka suka bar d'akin sai a palour suka kwana Aira dukta tsorace washegari koda Naila ta fito ta gansu a palour nan ta dinga Musu Dariya Harararta Ayra tayi tare da Jan tsaki ta ce "Yau d'innan zaku bar gidan nan wlh tunda har kika iya mugunta babu ruwana dake dagayau Nihal ce kad'ai y'ata" Jin hakan ya sanya Naila fashewa da kuka tare da rugawa ta fad'a jikin Ayra ta ce "Kiyi hakuri mom bazan sake ba Dan Allah karkice Nihal ce kad'ai y'arki bazan sake ba " Shafa bayanta ayra tayi ta ce "To nahakura amma kika sake me.zan maki?Ki yankani Na yarda Allah mom" Dariya Ayra tayi ta ce "To shikenan na hakura my prince's jeki Kuyi break fast " Tsalle Naila tayi ta ce "Thnks cutie d'in hero " ta fad'a tana wucewa dinning Duk Dariya sukayi Ummy ta ce "Wlh kun b'ata yarannan Wai wani cutie din hero Suma sun shaida dai iyayensu y'an soyayya ne " Dariya Ayra tayi nan sukaci gaba da Hira da y'an uwan nata cikin raha da annashuwa Ranar akayi soye Inda wasu daga cikin y'an uwa suka tafi Aunty Maryam da Mama Halima ne a bakin kawai basu tafi ba sai gwagwo da Baffa da Bayan isha I Bappa ya shigo gidan Palourn Abba aka saukesu Inda aka Girmamasu sosai aka cika musu da abun arziki Inda Ayra Bayan taje ta Gaishesu ta Aje musu twins Bappa ne ya kira Mummy da Daddy da Arman akan suzo su sameshi a gidan Abba yanzunnan sosai sukayi mamakin me zasuyi Daddy ko dak'yal Mummy ta samu ya yarda suka tafi Dan acewarshi baiga abunda zaiyi gidan d'an uwan nashi ba karfe takwas da rabi Duka palourn ya cika da mutane Tundaga kan Daddy Abba,Mama Halima,Mamy,Mummy,Mama,Arman,Aira ,Aunty Maryam,Yaya omar,Aysha,Ummy,Amma,Haidar ,Hafsat,Twins,Little Haidar,dake hannun Hafsat,Hatta Amer dukansu Iyalan Saida Bappa ya had'a Bayan an bud'e taro da Addu'a ya far'a da cewa "Ba komai yasa Muka hadu a wannan wajen ba saidan sasunci a matsayina na babba kuma Wanda nake ganin Dukanku nan zan iya yin iko da ku Kallon Abba yayi ya ce " Da farko zamu fara baka hakuri a bisa Auren da muka d'aurawa y'arka bada masaniyarka ba munyi hakane badan komai ba saidan Kaucewa wacce matsala shi Aure da haihuwa da kake gani na Allah ne ba a fiya zakewa a Lamarin Aure ba saboda rabo Har kashewa yake yanzu duba ka ga Cikin k'ank'anin lokaci da auren zuri'ar da suka fara Tarawa yara har biyar Wanda da koda Aure ko babu sai an haifesu yanzu da ace a waje suka haifi yaran nan Dan Allah ya zakaji a cikin ranka zakayi tsantsar nadama to zandai gajarta maganar Yanzu dai muna neman yafiyarka Akan kuskuren da mukayi maka"Cikin girmamawa Abba ga d'ago ya ce 'Bakuyimun komai ba Bappa nine ma ya kamata na nemu yafiyarku sannan nayi muku Godiya akan Abun nan da kukayi Tabbas na sake da Lamarin ubangiji Nasan yaran nan da a yanda na hana Su auri junansu tofa yaran nan da a waje za a haife su kaga ko ai ni ya kamata nayi muku Godiya Allah ya saka da alkhairi ya k'ara girma banida da bakin da zan gode muku Saidai nayi muku fatan gamawa da duniya lafiya"Amen Baffa ya fad'a sosai yaji dadi maganar da Abba ya fad'a Bayan nan ya d'ora da cewa "Sai magana ta gaba kuma da itace ginshikin haduwar mu a wannan wajen magana ce ta tsakaninku kai da d'an uwanka ya fad'a yana nuna Daddy a Gaskiya banji dadi ba Kuma kowama dake karkashinku na tabbata basajin dad'in irin wannnan D'aurarriyar gabar da kuka daura akan Abunda baikai ya kawoba Maganar ce dai ta farko zata dawo Shi aure da haihuwa da kuka gani Abu ne mai wuyar AL amari tun ran Gina ran Zane Kowace mace a duniya da kuke gani Allah ya Riga ya Zab'a mata mijin da zata aura Wanda alk'awarin Allah baya tashi kowace mace da kake gani da mijinta wani bai isa ya auri Matar wani ba Auren Rahama da Abubakar yayi dukda ance ana barin halak kodan kunya tofa ku sani shi silar tashi haduwar da Matar tasa ne tazo ta silar d'an uwanshi ko da Kabir baiga Rahama ya ce yana so ba dole Abubakar Zai Aure ta Komai Yana da Sila ne su nasu silar ne yazo da haka ta dalilin d'an uwansa Wanda abunda ya kamata ayi shine tawakkali da Allah to duk bakuyi haka ba kai Kabir saika dauri gaba da d'an uwanka Wanda hakan bai kamata ba har yakai ga kunfito takara to yanzu dai bazamu tsaya tashe tashe ba Duka abunda ya wuce ya Riga ya wuce ya kamata kuyiwa kanku fad'a tun kafin duniya tayi muku Rayuwar Duka nawace Duka cikinmu damu da ku babu Wanda zai maimaita shekarunshi na baya an riga an cinyesu tsufa na kama ku mutuwa na kusantomu ta na iya riskarkar kowannenmu a kowani lokaci yanzu ko mutuwar Inna bata isheku ishara ba ta mutu Da bakincikin gabar da kuke Sannan koda Mahaifanku dake k'asa na tabbata suna bak'inciki da wannan AL amarin Har koda yaushe burin wannan baiwar Allah bai wuce taga kun hade kanku ba kun shirya Amma kuka kasa cika mata wannan burin har saida ta bar duniya wannan kadai bai isheku ishara ba "Nidai ina mai baku shawara ne akan ku shirya ku sasinta junanku Dukanku nan kuna da Ilimi kuma Duka cikinku kowa yasan girman laifin da kuke aikatawa Yanke zumunci ba Abu bane mai wasa Wanda Allah s w a da kansa ya ce Zumunci rik'e take da al'arshi banda girman laifin yanke zumunci Kuma kuka had'a da laifin gaba Wanda Annabi MUHAMMAD s a w ya ce " Daga kwana Ukku Sallar mutum bata karbuwa wannan wace irin rayuwa ce kuke wacce babu Wanda ya isa ya fad'a muku Gaskiya mecece duniyar bare abunda ke cikinta Wlh duk Wanda ya d'auki duniya ma wani Abu ya maza ya sauke Dan Rayuwar nan da muke cikinta ba komai bace Dole zamu tafi mu barta ko muna so ko bama so kuma mutuwar nan dai da muka sani ba sallama take ba baka ta tabbacin zaka ma iya k'ara second d'aya a duniya Me zaisa duniya ta dinga ribatarmu Wanda duk abunda kake tak'ama dashi kudi,mulki,sarauta,izza,tak'ama,muk'ami,girman kai,dukansu a nan Inda kazo haka zaka tafi ka barsu kai kad'ai za a sanyaka k'abarinka da ga kai sai halinka sai abunda ka aikata alkhairi ko sab'anin haka Itafa duniyar nan da kuke gani makaranta ce In maka misali da Kamar matafiya ne muna cikin tafiya Muka tsaya yada zango mu huta Kafin wuce to kamar haka ne Mezaisa mu shagaltu da duniya Gidan aro Duniyar da ba komai bace Muyi kokarin mu Gina lahirarmu tun anan kafin lokaci ya kure mana Dan duk Wanda ya shagaltu da duniya to wlh ya Riga da ya gama tab'ewa a lahira lahira itace Matabbata Inda rayuwar ta Chan ce dindindin Har Abadan Abadan muyi kokari wajen mun Zage damtse mu gyara lahirarmu tun Anan har yanzu lokaci bai k'ure muku ba Tunda kuke da rai kuma kuke numfashi tofa kuna da ikon da Zaku daidaita kuma ku nemi Allah yafiya a take ya yafe muku,Nidai nasiha ce nake muku gami da bada Shawara sauran kuma ya rage naku "Ba Daddy da Abba Hatta kowa dake wajen saida yayi sanyi sosai nasihar bappa tayi tasiri a cikin zuciyarsu hada masu hawaye Daddy ne ya Mike tare da zuwa ya Rungume d'an uwan nasa ya ce " Ka yafemun Yaya nasan Nafi kowa laifi a al'amarin nan da banyi tawakkali na barwa Allah komai ba Tun ba yanzu ba nayi nadamar k'iyayyar da muka kulla Nayi tsantsar nadama a rayuwa Dan Allah ka yafemun Har yanzu ina sonka ina maka soyayyar da muke yiwa juna tun yarinta "Rungume Dan uwannashi Shima Abba yayi sosai yanajin tsananin soyayyarsa na dawo masa ya ce " Ni zan nemi yafiyarka na fara yi maka laifin da nayi d'an uwana na fika nadamar abunda nayi a rayuwa nima ina neman yafiyarka ka yafemun "Daddy harda hawayen farinciki ya ce " Na yafe maka duniya da lahira Dan uwana Allah yafe mana tare "Nima na yafe maka duniya da Lahira " Sosai suka k'ara Rungume juna sunajin wata nutsuwa na shigarsu wacce rabonsu da ita harsun manta Sosai mutanen dake palourn Sukayi farinciki Hada Masu hawayen farinciki Kowa Alhamdulilla kawai yake fad'a Arman ma Da Aira nauyayyar Ajiyar Zuciya Suka sauke a tare suka kalli juna suka sakarwa juna murmushi Da Hannu Aira Ta jinjinawa Arman alamar jinjina "Kashe mata ido d'aya yayi" Dariya tayi tare da K'asa da kanta Farincikin da suka shiga b'ata bakine Bayan an tsagaita Bappa ya ce........✍🏿 *Ni da Yaya Arman it’s not free it’s for sale #200 for more information contact me on my phone number as follows 07026166536* *_Miss Hajo Ce_*🤙🏿 [7/24, 15:41] Hajo hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN*🍏 ```MALLAKAR``` *Hajara L Sadeq* *Bonus page*💃🏿 *THE END*🔚🔚🔚🔚 🅿️......*129&130* Ya ce "Alhamdulilla Allah mungode maka da ka nuna mana wannan Rana Allah ubangiji ya k'ara had'a kanku Ya shirya muku zuri arku sannan ya k'ara muku Had'in kai da k'aunar juna" Ameeeen kowa ya fad'a a lokacin da Zaka kalli fuskar kowa zakasan suna cikin farinciki Mama Halima ma zuwa tayi ta Rungume y'an uwan nata ta ce "Alhamdulilla Allah nagode maka Allahsrk Inna da da ranta nasan da zaitafi kowa farincikin wannan Rana Allah ya jikanta Da Rahama nasan ko yanzu ruhinta zai kwanta cikin salama An cika mata burinta dadadde da ta mutu dashi " Duk ameen suka fad'a Bappa ya kalli Ayra da Arman da Murmushi a fuskarsa ya ce "Allah yayi muku Albarka kuma kun sauke nauyin dake kanku Allah shirya muku Yaranku" Ameen suka fad'a "Mama Halima ce ta ce " Bappa bamu gane ba "Murmushi Baffa yayi ya ce " ai sune silar zuwana garin nan Su suka kirani suka yimun bayani akan d'an Allah nazo na taimaka musu nayiwa iyayen nasu nasiha Dan nine kadai Babban da kila idan nayi musu magana za a iya cin nasara gashi kuma alhmdll anci nasara Allah yayiwa kowa Albarka "Sosai kowa yayi farinciki Da abunda Ayra da Arman sukayi Nan aka shiga sanya musu albarka Daddy ko da Abba Hannunsu cikin na juna wani sabuwar soyayyar y'an uwanta ka na fusgarsu Bayan komai ya tsagaita Bappa ya Ce " To saura magana ta gaba Yaushe Hajara zata koma gidanta ?Ya fad'a yana kallon Abba 'murmushi Abba yayi ya ce "Bappa duk sanda kace ai kai mai ikon kowane kuma duk hukuncin da ka zartar ya wadatar" Bappa yanajin dad'in yanda Abba ke girmamasa da kuma daukarsa tamkar uba cewa yayi "to shikenan Idan tayi arba in saita koma gidanta tunda kula dole sai iyaye musamman ita da har yanzu akwai yarinta tattare da ita hakan yayi ko'Duk sunyi na am da hakan Arman ko Haushi yaji ji yake cewa xa ayi ya tafi da matarsa Ganin yana gunguni ya sanya Mummy harararsa tamai nuni da kar yayi magana " Daren ranar kowa kwanan farinciki yayi Daddy ko da Abba daki daya suka kwana su na ta hirar yaushe gamo su kansu sai yanzu sukejinsu cikin nutsuwar da ta jima da tafiyar musu "Washegari su Baffa suka juya Bayan an cikasu da Abubuwan arziki Fly suka hau Ayra Nan tacigaba da samun kulawa a gidan nasu Wanda Arman kullum sai yazo Dan yanzu har palourn gidan yake shigowa Baya da haufi akan komai Bar musu daki ake susha soyayyarshi shida Airanshi a yanzu hankalinsu ya kwanta sosai twins nayin b'ulb'ul abunsu suna samun kulawa sosai Koda Ayra tayi ar ba in a lokacin saura sati Ukku bikin Su Hafsat hakan yasa Taki tafiya nan suka shiga Hidimar biki ba kama hannun yaro gashi Mama Halima ma ta dawo a nan za ayi bikin gaba d'aya saboda kar zaryar tayiwa mutane yawa hakanko sosai yayiwa mutane dadi amarya Amma da Hafsat sosai sukeshan gyara na musamman dan wacce tayiwa ayra gyara Mummy ta d'auko daga Sudan Inda aka hada da Ayra aka shiga musu gyara sosai suka fito musamman Ayra da ta saje dasu baka tab'a cewa ta haihu kamar Budurwa Haka aka fara hidimar biki cikin kwanciyar hankali Arman ma yazo Inda duk Inda zasu suna mak'ale da juna dan twins ma Har jariran Aje su Ayra tayi take shan gayunta Wanda Sosai Arman ya rikice ya rude Dan ta dawo masa kamar amarya Ranar da akayi kamu ma sosai Ayra tayi kyau cikin Ankon lace d'insu da yayi bala in kyau shikuma ARMAN ya shirya cikin dakakkar shaddarsa kalan lace din nata sosai aka shiga Zuba musu hotuna tare da twins Mata mazan bama tasan Inda suke ba (Su Ayra manya anshiga busy an yadda d'iya😂)sosai suke bala in kyau Dan twins ma gayun da sukasha saikunyi mamaki duk Inda suka gitta ana kallonsu Ayra ko Zage jiki tayi ta chashewa a bikin Yayyun nata amma saida taga Arman yabar wajen Dan hanata Yayi haka aka gama kamu lafiya aka k'are washegari ranar Juma a dunbin AL Umma suka shaida d'aurin Auren *Hafsat Zubair Sambo Tare da Angonta Umar Abubakar Umar Saikuma na Halimatu Abubakar Umar tare da Angonta AL_Ameen Sani* Akan sadaki Naira Dubu D'ari d'ari Da yamma angwayen sukayi walima Da dare aka kai kowacce gidan Mijinta Inda Hafsat Aka kaita sabon gidanta Wanda Ya Omar ya Gina Dan bazai had'asu da Khady ba Dan Y'ar jaraba ce a auran nan Ma da zaiyi yajinta hud'u gidansu dandai taga abun yafi karfinta kuma iyayenta sukayi mata fad'a hakan yasa ta zubama sarautar Allah ta dauki hakurin dole Sosai Aka sha kuka Da amaren Aira ko k'in kuka tayi ta ce "ba wani kuka da zatayi Haka aka sha taro lafiya aka k'are lafiya Saidai Fatan nema musu zaman lafiya Ayra ko banda tsiya ba abunda take musu " Bayan biki da kwana biyu Aira suka tafi Ita da Mijinta Abuja Daga su sai twins Dan Haidar ma Mamy ta barwa shi Dan su sake Soyayya Suka dinga zubawa fiye da ta da Ga Aira da kullum sabuwa take komawa Arman har yanzu bata girma jikinta yanda yake Saidai kyau da murjewa da take karayi da wayewa Twins d'insu na samun kulawa sosai Dan Nanny suka d'auka mai kula dasu duk hutu har yanzu Twins nazuwa iyayensu hutu su koma Haidar ma Idan zasuzo hutu tare ake tahowa dashi sai a maidashi dan shi yafi sabawa da gidan Abba saboda yanda Uncle Haidar Da Uncle Amer ke kula dashi da wasa da suke masa danma yanzu Haidar babba yabar kasar yana america yana karatu Makarantarsu d'aya da su twins inda shima Amer chan aka maidashi rabi suna gidan mummy rabi suna gidan Mamy. kwana a tashi ba wuya a wurin Allah a yanxu twins Har an yaye su sun tashi suma da wayau Dan yaran su Aira dukansu masha Allah badai wayau da baki ba (Nikan nace Gado sukayi) Aysha ko ta kara haihuwar y'arta mace inda aka sanya mata Hajara ana ce mata Little Ayra karkuga irin bazan kudi da ayra da arman sukayi a sunan dan sosai yaji dadin yiwa cutie dinshi takwara da aysha tayi ayra ko ba a magana dan akwatinan da tayiwa takwarartata ma b'ata baki ne Hafsat ma ta haihu ta haifi d'anta namiji Sosai yaya omar ya shiga farinciki da kara kaunar matar tasa Khady ko har yanzu shiru danma Mijinta na nuna Mata kulawa Kuma yanzu ta hakura sun hade kansu da Hafsat dukda ba gidansu daya ba amma suna zaman lafiya amma ce dai take da tsohon ciki bata haihu ba. Ayra ganin har an yaye twins Kuma bata samu wani cikinba Ya sanya hankalinta komawa kan karatu Yanzu kuma karatu take so tayi a d'aki ta tarda Arman yana Danna laptop Wajenshi ta rufa tare da D'ora kanta kan kafadarsa ta ce "Sannu da Aiki my hero " Murmushi yayi mata ya ce "Yawwa Ai aiki ya k'are ma tunda Gaki ya fad'a yana linke Laptop din.murmushi tayi ta ce " Dan Allah magana nakeso muyi hero Makaranta nake so na koma kaga duk Sa anni na sunjima da Gama degree d'insu yanzu an kusa fara registration din Jamb "Lokaci guda taga ya had'e fuska ya ce " ba yanzu ba Nifa ina kishin Makarantar nan Me kike nema a karatu turanci dai Kin iya babu Wanda bazaku gagara dashi ba Kina da iliminki daidai gwargwado Arabi da boko kina da wayewarki Kudi Alhmdllh baki da matsalar komai me zakiyi da karatu"Lokaci guda hawaye suka zubowa Aira ta ce "Shikenan yaya tunda bakaso na hakura ta fad'a tana Juyawa tare da kwanciya" Sai yaji ta bashi tausayi amma dukda haka shi dai kishin matarsa ya ke bayason Karatun "Aira ko saida ta Goge hawaye Dan harga Allah yanzu burinta na karshe kuma bai wuce Karatu ba Tunda komai yanzu Alhamdulilla basu da matsalar komai Kenan ita Haka zatayi ta zama ba wani cigaba haka dai tayi ta tunane tunaninta irin abunda taji Arman ya fara mata ne Ya sanya ta fusge dukda barinshi tayi shi d'aya yake rawarshi da tsalle Wanda baiji dadin hakan ba Sosai Ya lura kamar ma fushi take. Washegari cikin sanyi Aira ta tashi Arman ko baice mata komai ba Ganin yanda take fuska Twins Ya Kalla da suke wasa ya kalli Aira ya ce " Cutie kina ganin ba ansanya yaran nan school ba "Yanda ka gani hero amma da anbari sunyi 2yrs tukwana " Hakane kuma ya fad'a wayar Aira ce tayi ringing d'auka tayi tana karawa a kunnanta muryar Hafsat taji cikin d'oki ta ce "Albishirinki Sis" Goro Aira ta fad'a tana sonjin Menene"Amma ta haihu yanzu Ta haifi baby boy Karki ganshi masha Allah "Cikin farincikii Aira ta ce wow masha Allah Kice Kano tayi kira wlh nayi farinciki Allah ya raya ban ammar mu gaisa " nan ta mik'awa Amma wayar Inda Ayra ta mata barka Tana zolayarta ya labour room Dariya tayi ta ce "Kedai bari na azabtu kam har mala iku na dinga ganin sunamun kamar gizau tsabar azaba" Dariya sosai Ayra tayi Ta ce "Amma kinban Dariya wlh to ni me haihuwa Ukku nace me " Dariya Amma tayi ta ce "Ai sai yau na tabbatar ke jaruma ce Wlh " Dariya sosai Aira ta dinga yi hada rik'e ciki Arman na jinsu Ya girgiza kai Bayan sun gama wayar cikin murna ta Kalleshi ta ce "Yaya Amma ta haihu yanzu munyi baby boy " masha Allah na mana murna gsky Allah ya raya sai yawa muke karawa"Dariya Ayra tayi tanajin farinciki ta ce "Wlhko yaya gobe zantafi ko?Hararar wasa yayi mata ya ce " Chab ina zan yarda ki tafi ki barni ai ko kina zuwa sai ana gobe suna"Diddira kafa da kukan shagwaba ta fara ta ce "Uhm Uhm Allah honey ban yarda ba yaushe rabo na Da Kano Shine zakace rayya gobe suna" Dariya Arman ya dinga mata itakuma tana narke masa Dak'yal ta samu ya yarda A jibi suna zata tafi Haka ko akayi ana jibi suna Suka shirya harshi suka taho kano bayan sun jibgarwa mai jego da jariri uwar sayayya Gidan Mummy suka fara sauka Inda sosai ta shiga tarbarsu Dan sun kwan biyu basu zoba a lokacin twins na school Bayan an cika musu gabansu da Abinci Suna cikin Hira Mummy Ce ta ce "Wai ni Daughter ya maganar makarantarki Anfa fara registration Jamb tun last week" shiru Aira tayi tare da Kallon Arman saikuma tayi k'asa da kanta "Kallonsu Mummy tayi ta ce " bakicemun komai ba "Dagowa Aira tayi kamar me shirin yin kuka ta ce " Ya hana Mummy ya ce bazanyi ba wai "lallaima Aiko bai isa ba wlh Mummy ta fad'a tana Hararar Arman ta ce "wannan ne baka isa ba wlh saitayi karatunta kamar kowa " Amma Mummy Cikin maza fa "ya fad'a yana marairaicewa " Eh cikin mazan Matarka ce kad'ai cikin mazan kuma ma ina ruwanta dasu ita da karatu taje Kuma Bana shakkar Aira a ko ina Yarinyace mai kamun kai da nutsuwa Koda tana budurwa batayi Shiririta ba bare da Aurenta Dan haka wlh karatu zata jona barima ka gani na kira Suje tayi registration Jamb "Shiru Arman yayi jin Mummy ta fara fad'a Aira ko sosai tayi farinciki taji dad'in zuwansu Gwalo tayiwa Arman dake hade rai " wara idanu yayi tare da nuna kanshi"gyada mishi kai Tayi tana Dariya "Cije baki yayi tare da karkada hannu Alamun zata gane kuranta Gwalo ta k'ara masa Hada yi da hannu Marairaicewa yayi tare da Kallon Mummy ya ce " Mummy Kinga gwalo take yimun"Harararshi Mummy tayi ta ce "Tayi maka d'in " Dariya Ayra tayi Ganin haka ya sanya Arman tashi zai chafkota tayi saurin Mikewa tare da zuwa ta lafe jikin Mamy tana Dariya "Kudai bazaku daina shiriritaba wlh kun girma harda yara amma Abunda yaran suke Shi kuke Allah shiryeku ta fad'a tana Kiran Wanda zai fara yiwa Aira registeration din cikin sa a ko ta sameshi A ranar Aka je da Aira tayi registration din jamb sai murna take Daga nan gidansu ta wuce Bayan sun gaisa da y'an gidan Ta wuce gidan Amma Inda aka shiga Firar yaushe gamo cikin y'an uwanta Ranar suna yaro yaci suna Sani ana ce masa Sultan Haka akayi taron suna Lafiya aka gama lafiya Inda Aira ta koma gidansu a lokacin twins Sunje suna ganinta da gudu Suka ruga suka Rungumeta suna oyoyoy cutie D'aya Bayan d'aya ta daddagasu ta ce " oyoyoy my Angels "I miss you mom Suka fad'a a tare " Miss you tooo "ta fad'a tana sama da Haidar dake Dariya ya ce " Mom amma dai Kindawo nan ko"Dariya tayi ta ce "Sarkin wayau nufinka na dawo nan ku bazakujeba Chan kenan Saidai ku ku koma Chan badai ni ba " Mak'ale kafada yayi yayi ya ce "um um nidai bazan koma ba Saidai ke ki dawo" Dariya Ayra tayi ta ce "nak'i wayan " dak'yal Aira ta samu ta zauna saboda yanda suka yayyabeta Mamy da Mama ta Gaida suka Amsa cikin mutuntawa Mamy ta ce "Y'an suna sai yau ake ganinki tun Randa kikazo" Dariya Aira tayi ta ce "Wlhko Mamy hidima ta boyemu Ina su Sadeq da shureim " sai yanzu ma kike Tambayarsu Dan gidanku Kawai daga zuwa ki tafi kibar yara suta Rafkawa mutane kuka saidai babansu na kira Yazo ya d'aukesu kinsan k'iyiwa ce dasu daman zaki barsu ke raguwa Biyun ma kin kasa kula dasu tsabar ragwanci ai wlh naso ace Biyar d'innan hannunki suke muga ta tsiya"Dariya Ayra tayi ta ce "Chab Mamy Ai bazan iya dasu ba Kuma kunsani shiyasa kuka amshesu ina ni ina Iyawa da Yaran nan Ai Saisu ida doramun hawan jini Kinga idan sukaje Hutu suka had'u Su Biyar d'innan Kullum da ciwon kai nake yini Dan B'arna da Irin tijarar da suke mun kare baici wancen hutun fa k'atuwar plasma d'inmu ta palour wlh Suna fad'a suka fasata saida tayi ragwa ragwa kuma Da gangan Wancen uban zuciyar ya fara fasata ta fad'a tana nuna Haidar saida muka sake sabuwa"girgiza kai Mamy tayi ta ce " Sun aika Wlh Shiyasa da na gansu kaffa kaffa nake da kayana b'arna yaran nan garesu Allah dai ya kyauta "Ameen Aira ta fad'a ranar ta kwana gidansu tukwana tayi musu bankwana Ta wuce gidan Mummy Dan yau zasu wuce tana zuwa ta samu Arman da Twins suna ganinta suka Ruga suka Tareta daukarsu tayi tare da zaunawa ta ce " Shine kukayi tayiwa Mamy kuka ko"Dariya sukayi suna wasa da Sarkar gold din jikinta shureim ya ce "Mom mu chafi(tafi)Dariya Mummy tayi ta ce " bagwaran nan Baisan mutane ja iri tunda sukazo saidai babansu wai dole.sai an tafi gida"Dariya Aira tayi ta ce "Wlh Mamy sarkafa garesu shiyasa Na gudu ba dasu ba " Harararta Arman yayi ya ce "Ai wlh sa a kikaci ina y'an mutuncin da kaimiki su zanyi kawai kika tafi kika barmun yara Suna kuka Kika kashe wayarki saini Mamy ta kira " Dariya Aira tayi ta ce "To ayi hakuri ai gwara da kake a y'an mutunci ba y'an tsiyarba ta fad'a tana Dariya" Shima dariyar Arman yayi ya ce "Mummy zamu wuce " Okay Allah ya kiyaye Amma bamu minti biyu ta fad'a tana kama hannun Ayra bedroom d'inta ta nufa da ita Bayan ta rufe kallonta tayi ta ce "Shawarace nayi akan karatun da zaki Fara idan kika samu wani cikin zakusha wahala Shiyasa na sayo Allurar planning zanyi maki ta shekara Ukku Kina ganin ba matsala?Ajiyar zuciya Ayra ta sauke Dan daman a tsorace take karta kuma samun wani cikin Dan data samu ko tasan ko giyar wake Tasha Arman bazai barta tayi karatu ba cikin farinciki ta ce " Mummy kawai kiyimun nima inaso"To Mummy ta fad'a tare da had'a allurar ta ce "Karki kuskura ya sani nima bazan fad'a masa ba " Insha Allahu Ayra ta fad'a Nan Mummy tayi mata allurar A tare suka fito Arman bai damuba Dan Mummy da Aira An saba sirri har parking space Mummy ta rakasu tare da musu bye bye. *After 5 years* Cikin shekarun nan Aira ta kammala degree dinta a nan abuja tayi inda bayan gamawarta ta k'ara haihuwar y'arta kyakyawa Aka sanya mata halimatu takwarar inna ana ce mata Amal. *** A hankali suke Saukowa daga matattakalar jirgi k'aramar baby da bata wuce 5months ba a hannunta Kyakyawa mai tsananin kama da Ita Ansha mata gayu babyn tare da mata two babies sosai tayi kyau Uwar kuma sanye take cikin shigar doguwar Riga Blue ta yafa beilt din rigar sosai tayi kyau ta fito kamar wata baturiya Dak'yal na gane ta saboda wani kyau da fresh da wayewa da ta k'ara Arman ne a gefen ta hannunsu cikin na juna Shima sosai yayi kyau cikin Farar shaddarsa da tayi masa bala in kyau Ta Kara fito da kyawunsa suna tafe suna hirar soyayya har suka sauko suna Saukowa sukaji a rungumesu su Duka an zagayesu "Murmushi sukayi Ganin yaran nasu ne su biyar suka rungumesu Cikin farinciki Arman ya shiga daukarsu d'aya Bayan daya banda twins da suka girma yanzu sun tafi shekara Tara shagwaba suka fara Naila ta ce " Dad saurani "Dariya yayi tare da d'agata itama ya maidota tana Dariya Sannan itama Nihal ya d'agata Naila ce Ta Rungume Aira ta ce " Highly wellcome my cutie mom "Dariya Aira tayi Wanda ya fito da fararen hakoranta Dake d'auke da zinarin hakorin makka sosai naga ya k'ara fito nata da wutar kyanta Ta ce " Thnks my angels "Nihal ce itama ta matso ta ce " Sannu da zuwa mom ya makka"Dariya itama ayra tayi mata ta ce "Yawwa my angel makka Alhmdllh" Amsar Amal Naila ta mik'a zatayi Yarinyar ta mak'ale jikin uwarta "Turo baki Naila tayi ta ce " rabu da ita wai ita nan ji take ta dawo daga makka shine zatayi mana rainin wayau to tun kafin kije mu muka fara zuwa Y'ar rainin hankali"Dariya iyaye sukayi Sai sannan suka Hango Mummy mamy da Daddy tare da Abba Wajensu suka nufa d'aya Bayan d'aya suka rungumesu kowa nayi musu Sannu da dawowa suna amsawa Mummy ce cikin fara a ta ce "Masha Allah yaudai su Aira anzama Hajiya" Dariya Aira tayi tare da murmushi ta ce "Ai jina nake cikin farinciki Mummy ashe duk zuwan da zakayi idan ba hajji kayiba bakajinka cikin nutsuwa kamar haka nidai Alhmdllh yanzu kuma banida da wani sauran buri anan duniya Duka burika na Sungama cika Saidai Fatan samun aljanna kawai Sannan ta juya ta kalli Mijin nata ta ce " ka gama yimun komai a duniya my hero Kaid'in miji ne da kowace mace zata so samun irinsa Allah ya barmu tare har mutuwa "Ameen Arman ya fad'a yana lakutar kumatunta kamar ba gaban iyayensu suke ba ya ce " Nima kingamayimun komai my cutie matata a duniya kuma a Aljanna uwar y'ay'ana Allah ya biyaki da gidan Aljanna Alhmdllh nima bani da wani saurin buri a duniya burina kowanne ya gama cika Saidai kuma fatan samun aljanna Allah ya had'amu a aljanna baki d'aya mudaku "ameeeeeeen duk suka Fad'a Zuwa Aira tayi ta Rungume Mamy Itama Rungumeta mamyn tayi ta ce " Highly wellcome my Beloved daughter Alhmdll ko buri ya gama cika "Murmushi Aira tayi tanajin gumin mahaifiyartata ta ce " Thnks Mamy na Yanzu kam bani da wani sauran buri duka burika na sungama cika tsakanina da ubangiji har kullum sai Godiya Saidai kawai muce Alhamdulilla Allah ya barmu tare har mutuwa *Ni da Yaya Arman*.......✍🏿 _Laifin dad'i karewa_😭😭 *Nima Miss Hajjo anan nake cewa Alhamdulilla* *TAMMAT BI HAMDULILLAH ALHMDULILLAH INA GODIYA GA ALLAH (S W A) DAYA BANI IKON FARA WANNAN LITTAFI LAFIYA NA GAMA LAFIYA A YAU NE NI HAJARA L SADEQ NA KAWO KARSHEN WANNAN LITTAFI MAI TAKEN NI DA YAYA ARMAN KURA KURAN DA NAYI A CIKINSA ALLAH YA YAFEMUN ALLAH YA BAWA AL UMMA DAMAR AMFANUWA DA FADAKARWAR DA NAKESON ISARWA* *SAKON GAISUWA DA JINJINA GAREKU NI DA YAYA ARMAN FANS A GASKIYA BABU ABUNDA ZANCE GA MASOYA SAI GODIYA NAJI DADI SOSAI YANDA KUKA AMSHI LITTAFIN NAN HANNU BIBBIYU KU KA SOSHI KUKA KAUNACE SHI DA YANDA KUKE NUNAMUN TSANTSAR SOYAYYA NAGODE NAGODE ALLAH YABAR ZUMUNCI DA KAUNA KU SANI NI HAJARA L SADEQ INA KAUNARKU FIYE DA YANDA KUKESON LITTAFINA DA WANDA SUKA SAYA SUKA KARANTA DA WANDA BAMA SU SAYA BA SUKA KARANTA DUKA INA GODIYA KUMA KU SANI INA MUKU SON FISABILILLAHI LOVE YOU ALL MY FANS IRIN SOSAI DINNAN WOLLA INAJI DAKU HAR CIKIN KOKON ZUCIYATA ALLAH YABAR KAUNA DA SOYAYYA* *SAIMUN HAD'E A SABON BOOK DINA MAI TAKEN AUREN WATA TARA WANDA ZAI FARA ZUWA MUKU RANAR 20/AUG/2022 WANDA INA DA TABBACIN SHIMA ZAKU SOSHI BAZAN KODASHI BA SABODA KUNSAN ANCE WAKA A BAKIN MAI ITA TAFI DADI AMMA DAI NASAN KUNSANI ZAZZAKAN ALKALAMIN MISS HAJO BAYA RUBUTA LABARIN BANZA KUDAI KAWAI ACIGABA DA GASHI GA MAI BUKATAR SHIGA GROUP DINA NA WHATS APP KO SHARHI,KO TAMBAYA HANYA A BUDE TAKE KU TUNTUBE NI AKAN NUMBER WAYATA KAI TSAYE 07026166536* *ALBISHIRINKU MASOYA HAJARA L SADEQ TA SHIRYA GIVE AWAY NA MURNAR KAMMALA WANNAN KASAITACCEN BOOK DIN NA NI DA YAYA ARMAN KOWA DA KOWA YANA DA DAMAR SAMUN WANNAN GARABASA ZAKUYI SAVE D'IN NUMBER TA KUYIMUN MAGANA KAI TSAYE ZANYI SAVE NUMBERKU ZAN D'AURA GARABASAR KATIN MTN A STATUS A YAU K'ARFE 8:00 NA DARE WANDA ALLAH YA BAWA SA AR CI ZAICI ALLAH YA BAWA MAI RABO SA A AMEN GA NUMBER WAYAR DA ZAKUYI MAGANAR 07026166536* *Littafin Ni Da Yaya Arman ya kammala ya zama complete document zaku sayeshi cikin farashi mai rahusa ga mai buk'atar sayan cmplt document na Ni DA YAYA ARMAN ku tuntub'eni akan number wayata 07026166536* *Sayan na gari maida kudi gida* *_MA'ASSALAM MISS HAJO CE_*🤙🏿