🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE SHI🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 1 Bismillahir rahmanir rahim,Ina godiya ga Allah daya bani damar fara wannan littafi ,bayan kammala littafin soyayyata.Allah kasa yadda na fara lafiya naga bayansa lafiya ameen. Gargadi banyarda wani ko wata ya juyamin wannnan littafi ta kowace sigar ba. _______________Wata kyakkyawar yarinya na hango sanye da kaya irin na Fulani ,wato rigar saki dakuma zaninta,duka duka rigar da kadan ta wuce cibiyar ta,saidai kuma ta daura zanin ya rufe mata cikinta ta yadda ba wanda zai ga jikinta awaje. Farace irin mai sirkin yallow -yellow din nan,tana da doguwar fuska mai kyan tsari dauke da dogon siririn hanci har baka,bakinta dan karami kamar gidan tsutsa,tana da irin manyan idanunnan masu kamar tana jin barci,ga gashin ido zara -zara. Girarta kuwa ,kamar wacce aka dora Mata ita dan saiti,gaban goshinta wasu yan kananan gashine kwance lub lub kamar na jarirai. Masha Allah yarinyar ta lafiya ta hadu ,dan doguwace marar jiki saidai fa Allah ya hore mata hips Kai kace wata babbar macece Sannan akwai alamun girma akirjinta , ma'ana dai akwai dukiyar Fulani dasuka fara tasawa akirjin nata. Duka duka wannan yarinyar bata wuce shekara 15/16 ba ,amma kallo daya zaka yi mata kasan Allah yayi halitta agurin. Sandace irin ta Fulani ahannunta tana dagawa sama ,da alama tana son hada kan wasu tarin sha'nun dake kiwone wani kayataccen jeji ,dan kuwa ciyawace agurin Kore sharr da ita ,sha'nun suna ta cin abarsu . Tafiya ta farayi gurin shanun dake dan nesa da ita ,dan ita tana daga jikin wata bishiya ne tana kallon yadda suke kiwo abinsu. Kanta ta daga ta kalli yadda garin ke hada wani irin hadari baki kirin dashi ,kuma da alama koda yaushe ruwa na iya saukowa. "Kuzo mu tai gida abokaina kada ruwan nan ya sauko ya taba mu banin son nai mura aradu" Cikin Yaren fulatanci take musu magana ,tana daga sandarta .aikuwa kamar wanda suke jin me take fadi suka fara yin hanyar gida . Murmushi tayi tana mai binsu tana kara daga sandarta . Tafiya suke cikin jajen ita kadai daga ita sai wadannan garken shanun ,sam ba alamun tsoro tattare da ita,yar wakar tama take tana daga sandar sama. Kusan tafiyar minti biyar sukayi ,sannan na fara hango bukkokinsu dake can gaba kadan . AHankali naga duk wani annurin dake kan fuskar yarinyar ya dauke ,nan da nan damuwa ta maye gurbin nishadi da take ,sosai naga jikinta yayi sanyi har suka karasa wata bukka dake farkon rigar da alama nan ne gidansu. Garken shanun ta fara zuwa ta daure su tsaf sannan ta nufi cikin gidan,bakinta dauke da sallama. Lokacin har anfara yayyafi . Ba kowa a tsakar gidan nasu ,hakan yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da nufar wata bukka cikin sauri. Saidai kafin ta karasa kofar bukkar aka daka mata wata uwar tsakar da saida sandar hannunta ta fadi kasa. Afirgice ta juyi jikinta na rawa sosai kamar dan mazari.da sauri ta karaso gurin matar data daka mata tsawar, "Gani gwagwgo"ta fada cikin rawar murya. Kallon matar nayi sai na tarar da matar farace saidai kuma kazanta da rashin kulawa yasa tayi wani irin baki baki fari fari,sannan tana da jiki sosai sam fuskar ta ba alamun rahama a cikinta. Tana tsaye a kofar bukkar ta tana hararar yarinyar dake durkushe gabanta. Cikin masifa da bala'i matar ta fara magana da hausarta marar kyau. "Da kake kokarin shigewa dakin,ubankane zai debi ruwan? Ko kin ajiye bawanki ne a gidan?matar ta fada cikin zaro ido. Kan yarinyar akasa jikinta na rawa ta fara magana "Allah hukkumu hakuri gwagwgo naga ruwa na don sauka ne shiyasa ban deboba"ta fada cikin rawar murya da tsoro. Wani wawan mari matar ta kai mata cikin rashin imani da tausayi cewar yanzu ta dawo daga kiwo kuma ko abinci bata ci amma take kokarin sake turata rafi. "Shegen yaro mai bakin hali wllh yanzu koke kidobo min ruwan nan dan ubanki karuwa kawai"matar ta fada tana mai hankade yarinyar . Faduwa tayi sosai hannunta ya bugu da wani dutse dake ajiye tsakar gidan da alama na zama ne. Kara ta saka cikin azaba tana mai dafe hannunta dake mata wata irin azabtar zafi. "Wayyo handi ɗin boni lalashewa gwagwgo hannu na ta ɓalle" ya rinyar ta faɗa cikin azaba. "Shege wllh dama zai karye danafi kowa jin dadi yarinya kamar aljana,ace kinfi kowa kyau arugarnan? Na tsaneka fatto saina bata wannan shegen fuskan baki.maza ki tashi kona shakeki agurin ki mutu kowa ya huta" cewar matar cikin bala'i da tsantsar nuna tsana ga dattin. Cikin hanzarin ta mike ta zari wani boket din roba ta fice tana kuka sosai. Tafiya mai nisa tayi kafin tazo rafin, har zuwa lokacin kuka take hannunta sai zogi yake mata, ruwan ta debo cike da sauri dan kuwa ruwan da ake ya fara karfi. Saidai me ?tana juyawa tayi arba da wani murtukeken maciji katon gaske ya fasa kai yana huci. Wani irin mugun tsorone ya kamata nan da nan jikinta ya kama rawa har batasan lokacin da boket ɗin ya fadi kasa ya fashe ba. Tashin hankali kenan wanda ba'a sa masa rana ,iyakar rushewa da tashin hankali yarinyar nan ta shiga. Hannu ta ɗora aka tana mai kara ƙarfin kukanta. "Wayyo ni fattu bukar na mutu na lalashe ya zanyi da rayuwata nashi zai karni wayyo baffana wayyo Allah ,taimaka min" Ta faɗa tana kallon boket ɗin dake tarwatsa,dama kuma rana ta gama cin ubansa. Shi kuwa macijin nan ganin yadda ta tsaya tana kallon sa kuma tana kallon fasashshen boket ɗin ta ,sai taga kamar neman makami take ,dan haka afusace yayi kanta Ihu ta kwalla mai karfin gaske tare da zubewa agurin sumammiya dan ganin yadda macijin nan yayi kanta baki bude. Masu karatu ya kukaji? Meye ra'ayinku akan wannan Nobel ɗin? Ina bukatar comment dinku idan buk din nan yayi muku dadi muci gaba. Takuce har kullum anty mammy Msr babi💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE SHI🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 2 _______________Ihu ta kwalla mai ƙarfin gaske ,tare da zubewa agurin sumammiya,dan ganin yadda macijin nan yayo kanta baki buɗe . Hakan ba ƙaramin tsorata ta yayi ba . Dai dai lokacin ne kuma wani katon macijin ya nufo wannan macijin da gudun gaske ,yana zuwa ya sarkeshi suka fara kaiwa juna sara .hakan shi ya hana wannan katon macijin ya sami damar karasawa inda fattun ke kwance asume. Sosai macizan nan ke kaiwa junansu sara suna murdewa cikin jikin juna.ko wanne na ƙoƙarin illata dan uwansa. Ahankali fattu ta fara bude idanunta da sukayi mata mugun nauyi tana kuma lumshesu,hannunta ta daga da nufin dafe kan nata,saidai wani azababben zafi da radadin ga wani irin zugi dataji hannun yana mata ,shine ya sanyata sanya kara tare da fashewa da kuka."washhhh hannuna wayyo kaina"ta fada cikin kukan tana mai dafe kan da dayan hannun marar ciwon. Sai kuma ta zabura cikin azama ta zauna tana mai zare idanu da rarraba su,sakamakon tunowa da katon macijin da yayo kanta dazu.saidai kuma can ta hangi macizan biyu suna ta artabu,gaba daya sun jima kansu ciwo jini yana ta zuba akikkunansu,amma sunki daina fadan. Tsoro ,fargaba ,tashin hankali da rudewa suka saka fattu kurma wani uban ihu tare da yunkurawa ta felle da mugun gudu tana ihu cikin rudewa dan ganin macizan sun zama biyu wato har fada suke akan waye zai cinyeta. Duk da irin ruwan da ake zugawa mai ƙarfi ga iska ,haka tayi ta cin uban gudu ko gabanta bata gani.ikon Allah ne kawai ya kawota gidansu lafiya. Kai tsaye ta danna cikin gidan da gudu ta shige dan dakin dayake amatsayin nata,cikin rawar jiki ta janyo wasu karare dogaye guda hudu ta kara a kofar,dan sune Matsayin murfin kofar tata. Dakin ba komai sai wata yar yaloluwar taburma ,wacce kallo daya zaka mata kasan cewa taga duniya,dan gaba daya ta ciccinye kuma tayi lakwam da ita.sai wani zani dake gefe daure ,da alama kayanta ne acikin. Tana tsaye atsakar dakin ,har lokacin jikin ta rawa yake ,ga ruwa sai zuba yake ajikinta yararara!!! Kallo daya zaka mata kasancewa afirgice take sai kif-kifta ido take tana kallon kofa,gani take kamar macizan nan zasu biyota.tayi kusan minti biyar acikin wannan halin ,kafin ta fara cire kayan jiki ta dake yararin ruwa."masha Allah nace,sakamakon ganin wani uban dogon bakin gashi mai santsi akanta,lokacin da take zame dan kwalin dake kanta .an raba kan biyu an daure ko wanne bangare sai kuma aka nannade ko wanne abarinsa kamar gammo.hakan da akayi shine ya hana mu ganin gashin nata tun farko. Daurarren zanin nan ta kwance ta dauko wani zanin irin wanda ta cire da rigarsa ,saidai kayan fa sun sha jiki sosai ,sun kode sun jeme sunyi wani fari,sai wata hula baka irin ta sanyin nan ta dauko ta ajiye kusa da kayan ,sannan ta mike tsaye ta cire rigarta ta ajiye ta gefen ta barmar ahankali ta warware tsangalallen zanin shima ta ajiye gefe,ya zama daga ita sai wani kodadden pant Wanda kana gani kasan shima yaga rayuwa.kallonta nayi tun daga sama har kasa kawai nace Masha Allah.dan sura kam Allah ya halicce ta agurin fattu jikintahar wani sheki yake kamar yar masu kudi wacce ke rayuwa cikin jin dadi. Haka ta dauki kayan ta saka ajikinta tanayi tana kuka abin kwanon ban tausayi. Bayan ta kammala sanya kayan ne kuma saita dauki wanda ta cire ta matse sannan ta makalasu ajikin karan dake jingine akofar dakinta. Zama tayi akan yar tabarmarta ta dukunkune jikinta tana kuka.abubuwa dayawa ke dakinta ahalin yanzu,na farko tsantsar tsoron macizan data gani dan bata taba ganin irin wadannan macizan ba,dan dayan kam jikinsa mai matukar shekine da kyau,sai kuma hannunta dake mata azabar ciwo uwa uba kuma yunwa,rabonta da abinci tun safe data sha nono har kawo yanzu da magrib ta sanyin kai ba abinda taci. Sosai take tausayi rayuwarta, tabbas rashin uwa babbar gibine arayuwa,yanzu da innarta na kusa da ita data rungumeta ta fada mata damuwarta,amma rashin dace ta daya shine sam batasan koda fuskar innarta ba ,bata sani Bama kotana raye koya mutu Allah shine masani. Tana cikin wannan halin taji an ture kararan data rufe dakinta dashi. Azabure ta mike tsaye tana shirin sanya ihu. "Ke fattu nutsu mana nine fa ,nine baffanki"wani dattijo ne fari mai dan tsayi yake maganar,yana sanye da riga da wando na wani yadi mai arha sai takalmin sau ciki na roba,da hula irin mai malafar nan.ya shigo cikin dakin da wani kwano hannunsa. Ajiyar zuciya ta sauke sakamakon ganin baffan nata ,da sauri ta karasa kusa dashi tace "baffan usee wollahi na tsorata ne"ta fada idonta akan kwanon dake hannunsa. Murmushi yayi yace "hoo fattu akwai tsoro,sannu maza karbi wannan tuwon ka shinye nasan kanajin yunwa,kayi sauri kar hansai ta gani"yana fadin haka ya mika mata kwanon yayi saurin fita,dan kar matar tasa ta fito ta ganshi ya shiga uku. Cikin sauri _sauri fattu ke cin tuwon nan kamar zata kware, tas kuwa ta cinye ta side kwanan, da sanda tafice tsakar gidan ta wanke kwanon ta ajiye akicin sannan ta sha ruwa tayi alwala ta koma daki. Sallar la'asar tayi da magrib dan tuni an kira. Har zuwa lokacin ruwa ake saidai bai kai ƙarfin na farko ba.tana zaune cikin zullumin matakin da gwogwgo zata dauka akanta ,na fasa mata boket har akayi ishsha tayi salla sannan ta kwanta tana mai karanta addu'a ,nan da nan barci yayi gaba da ita,har baffanta ya shigo ya duba ta yaga tayi barci addu'a yayi mata cikin tausaya wa halin kuncin da take ciki kafin yayi saurin fita. Gwagwgo kuwa tana daki ita da yaranta suna ta hira suna cin gyada ,ba ruwansu da wane halin fattu ke ciki,shin ta dawo gidanma ko yaya taci abinci ko bata ciba?sam ba wanda ya damu ,kuma ba wanda yayi Sallah a cikinsu. Can cikin dare fattu na barcinta damuwa da tsoro dan kuwa mafarkin macijin nan take ,saidai kuma ba na farkon bane yazo mata yanzu wannan mai kyakyakywan jikin ne,saidai gaba daya jikinsa jini yake zubarwa,ga wani irin hayaki da tururi dake fita ajikinsa, sai burkima yake yana wani irin kuka da wata murya mai amon sauti,kuma yana nufota da ƙoƙarin hawa jikinta . Wani razanannen ihu ta kwalla tare da mikewa zaune afirgice ,tana mai waige waige,ba abinda take iya gani saboda duhun dakin ,hakan yasa tayi saurin komawa ta kwanta tare da karanta addu'a kala_kala,hannu ta mika dan janyo zaninta ta rufe jikinta dashi ,saidai kuma hannun nata taji ya sauka akan wani abu mai dan karen sanyi da santsi. Cikin tsoro take shafa abun dan jin ko menene,tabbas MACIJINE dan kuwa ta tabo har kansa .... Masu karatu badai macijin ne ya biyo fattu da gaske ba? Wane hali fattu zata shiga ? Muje zuwa yaki ce dai anty mammy Mrs babi💘💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE SHI🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 3/4 ________________Cikin tsoro take shafa dogon abun dan jin ko menene,tabbas MACIJINE dan kuwa har kansa ta taɓo. Aikuwa da hanzari ta janye hannunta cikin kidima ta fara ja baya tare da fasa wani irin gigitaccen ƙara, "Ahhhhhhhh wayyo Allah baffa maciji!maciji !!maciji!!!"gaba ɗaya ta kidime abinda take iya faɗi kenan jikinta na rawa kamar ɗan mazari. Allah Sarki baffa dama ba wani barci yake yi ba ,dan yana kula da ɗakin fattu ,kasancewar ɗakin yana gaf da ƙofane,dan haka jin ihunta da yayi ,yasa shi tashi agigice ya nufi ɗakin nata. Haskawa yayi da tocila can ya hangota jikin bangon ɗakin ta duƙunƙu ne tana ta ihu,da alama batama cikin hayyacinta. Da sauri ya nufeta yana kiran sunanta"fadimatu !ke fadimatu menene ?ya isa haka gani akusa dake baffanki ne kinji daina ihun "baffa ya faɗa cikin ƙasa ƙasa da murya dan karya ƙara tsorata ta. Ita kuwa gaba ɗaya ta rikice kawai kira take "baffa maciji zai sareni baffa wayyo Allah na" Ganin halin da take ciki ne yasa baffa ya fara tofa mata addu'a ,cikin minti biyu kuwa tayi shiru sai rawa da jikinta ke famanyi,ahankali ta daga kanta ta sauƙe kyawawan idanunta akan baffan nata,kawai saita saki kuka tana mai cewa"baffa MACIJINE yake son sarina aradu da idonsa na ganshi anan"ta faɗa tana nuna masa gurin dataga macijin. Kallon gurin baffa yayi ,shifa ba abinda ya gani agurin ,kawai yana tunanin ko mugun mafarki tayi,dan haka cikin ƙokarin kwantar mata da hankali yace "shike nan fattu ya tafi maza koma ki kwonta kiyi addu'a ba abinda zai sameka kinji"ya faɗa cikin yanayin Hausar su ta Fulani. Cikin kuka take girgiza masa kai "aradu baffa dawowa zaiyi tun daga rafi suke son cinyeni baffa ,bazan iya kwonshiya Ni kaɗai ba"ta ƙarasa tana mai matsowa kusa da baffan. Shiru yayi yana tunanin mai ya kamata yayi,dan gaskiya yaga ta tsorata da yawa,dan haka cikin ƙarfin hali yace "tashi muje gurin hansai saiki kwonta shan ko"ya faɗa cikin tausaya wa. Ai kafin ma ya rufe bakinsa ta kai ƙofa,dan ita kam babban burinta ta bar ɗakin nan,tama manta da gurin wa baffan yace taje. Ahankali baffa cikin ɗan tsoro yake tura murfin ɗakin na hansai harya buɗe shi duka.suna kwance abinsu kan gado ita da yaranta su uku,na miji ɗaya sai mata biyu Dukansu basu kai fattu shekaruba, da alama na mijin zaiyi shekara sha uku,matan kuma basu fi sha daya ba. Kuma dan rashin tsari irin na goggo hansai da ita da yaranta duka suke kan gadon ,har na mijin. Ahankali baffa ya karasa yana dan bubbuga fillon da hansai ke kwance ,sai uban munshari take zabgawa,banda wari ba abinda dakin keyi. "Hansai!hansai!!"baffa ya faɗa cikin Muryar tsoro,dan yasan idan ta farka saitayi masa bala'in ya tashe ta tana barci. Juyi tayi tare da goge yawun barcin dake zuba abakinta taci gaba da barcinta.ahankali ya fara kiran sunanta da ɗan karfi "Hansai ! Hansai!!" Har sau biyu. Buɗe ido tayi ahankali ta sauke su akan baffa dake tsaye ,buɗe idon tayi sosai cikin bala'in ta tace "to jarabarce ta motsa haka da cikin dare zakazo ka dameni?to wllh garama ka koma inda ka fito dan ba abinda zaka samu agurina ,wannan jaraba dame tayi kama ,ko sati biyu bakayi da saukemin jarabarka ba shine yanzu ka ƙara jajiɓo jiki kazo ka sake ko ?to wllh banda lokacinka kaficemin daga ɗaki"ta faɗa cikin masifa tana juya masa baya. Girgiza kai yayi cikin jin kunyar fattu ,dan yasan taji abinda gwogwgo take faɗi ,kuma ai ita ba yarinya bace bare ace bata san me hakan ke nufi ba,tunda tana karatun addini. Cikin sanyin murya yace "ashsha Hansai ba wannan ta kawoni ba ,dama ina neman alfarmar fattu ta kwana anan ne daku,dan bazata iya kwana ita kadai ba ,atsorace take "ya faɗa cikin shakkun zata amince ko yaya. "Kan ubannan yau kuma da wannan sabon munafurcin kuka zo ?fattu ta kwana aɗakina ,lallai in baka mutu ba zakaga ikon Allah,da can da ubanwa take kwana? sai yau zakace ta kwana aɗakina?yarinyar mayya wato cikin dare ta lashemu ko?kai baka da asara,to ku ficemin aɗaki ,Allah yasa abinda yake tsoratatan ya cinyeta ta mutu kowa ya huta "tana gama faɗin haka ta juya taci gaba da barcinta. Sosai maganganunta suka ɓatawa baffa rai ,saidai bashi da damar magana ,kai kawai ya girgiza yace "muje fattu" Kuka sosai fattu keyi na tausayin su ita da baffanta ga wannan matsalar dake ƙoƙarin Kunno mata kai ,basu da gata sai Allah kawai. Suna fita baffa yace "shiga ɗakina ki kwanta fattu,Ni bari na je ɗakin naki kinji"ya faɗa cikin sanyin murya. Girgiza kai tayi tace "baffa Zan koma ɗakin nawa In kwanta kaima kaje ɗakinka ,idan gwagwgo tasan na kwana aɗakinka yanka Ni zata yi,dan ta hanani shiga ɗakin"ta faɗa tana mai share hawayenta tare da nufar ɗakin nata ,gabanta naci gaba da bugawa. "Kiyi hakuri fattu komai yana da iyaka kinji,Allah zai miki sauyi Na alkairi"baffa ya faɗa yana mai mika mata tocila ya ce ki haska ki kwanta kinji ,kiyi addu'a" Karba tayi tare da ɗaga masa kai ta koma cikin ɗakin. Daga bakin ƙofa ta tsaya tare da haska ɗakin ko ina ,ba abinda tagani aɗakin ,hakan yasa tayi zamanta bakin ƙofar ɗakin da tocilan ɗin ta ko yaya taji motsi saita zabura ta haska . Sam awannan daren bata sami damar runtsawa ba ,ga sanyi da garin ya ɗauka sakamakon ruwan da aka zabga jiya. Sai gabannin asuba sannan barci ɓarawo ya saceta. Wani irin azababben sanyi daya ratsa ƙasusuwan tane sakamakon ruwan sanyin da gwagwgo ta kwara mata ,shine ya sanyata zabura ta miƙe da sauri tana haki,kafin ta gama dawowa cikin hayyacinta kuma taji duka yana sauƙa ajikinta ta ko ina ,ihu ta fara tana neman taimako amma ba wanda yazo dan taimakon nata,dan baffa yana masallaci kasancewar shine limamin rugar, "Wayyo Allah na gwogwgo kiyi haƙuri wllh bazan ƙara ba ,tsautsayine yasa na fashe miki bokati, dan Allah kiyi haƙuri gwogwgo"abinda fattu ke daɗi kenan cikin azaba dan ko ina na jikinta ciwo yake mata barin ma hannunta daya kumbura sosai ,alamun tayi targaɗe a hannun kenan. "Wllh yau saina kasheni Shegiyar yarinya muguwa, kafin baƙin cikinki ya kasheni ,na Tsaneki fattu bana ƙaunar ganinki arayuwata, kinsan nawa nasai bokatin nawa?kika je kika fashemin shi? Murtala huɗu da nairagoma fa na siya,wllh saina daki kuɗina kuma kije duk inda zaki samo min kuɗin bokatina ki samomin dan bazan ɗauki asarar ba"gwogwgo ta faɗa tana haki,kuma bata daina jibgar fattu ba ,kamar ta sami jaka. "Wayyo gwogwgo dan Allah kimin rai hannuna zai karye, wllh bada gangan na fashe miki bokati ba,macizaine suka biyo ni zasu cinyeni shine na gudu amma bada gangan nayi ba wllh"ta faɗa cikin azaba dan tuni ƙarfinta ya kare ko iya ɗaga hannunta bata yi. "Allah ya tsine muku keda mashizan shegen yaro karuwa ,ina ruwana da macizai ?dama sun cinyeki kowa ya huta mai baƙin hali marar farin jini har yanzu kin kasa auruwa ,dama shegun macizan sun.......kasa ƙarasa magannarta tayi sakamakon wani ƙaton abu dataji ya faɗo kanta jifff !!!kamar buhun hatsi. "Wayyo Ni Hansai menene wannan ɗin yake zagayemin jiki?ta faɗa cikin firgici da tashin hankali tana mai jefar da iccen hannunta.aikuwa carab idanunta suka sauka akan ƙaton macijin daya nannaɗeta ko motsi bata iya yi,kuma ya fasa kai a saitin fuskarta sai huci yake yana Filato da harshe. "Wayyo Allah na Ni hansai yau me zan gani ?na shiga ukuna malam kazo fattu ta min ture maciji zai kasheni ka taimakeni, handi ɗin bonu lalashewa ni yar nan wayyo malam"ta faɗa cin tsantsar tsoro da razani da ƙyar take magana dan ba ƙaramin shaƙar mata jiki macijin yayi ba har wuyanta. Tsoro,fargaba da tashin hankali sune suka daɗa kashewa Fattu jiki ,dan faɗuwa tayi ƙasa warwas ko motsin kirki bata iya yi,shikenan Tata ta ƙare yana gamawa da gwogwgo tasan kanta zaiyo ,Allah Sarki innarta ,yanzu shikenan zata mutu bataga innarta ba,batasan ya fuskarta take ba ?bare tasan dangin innarta?,amma Gara ta mutumma ta huta da wannan baƙar azabar da take sha agurin gwogwgo. Shikuwa macijin nan ƙara matse gwogwgo yake sosai ,gaba ɗaya ta fice daga hayyacinta,dan ko magana ma ta kasa ,idanunta sunyi jajur sai nishi take numfashinta na ƙoƙarin ɗauke wa. Saida macijin nan yaga gwogwgo bata motsi alamun ta suma,kafin ya sake ta ta hanyar janye jikinsa daga gareta. Da gudu kuma yayi kan fattu wacce ke kwance cikin tashin hankali ganin yadda macijin nan ya kashe gwogwgo.runtse ido tayi da mugun ƙarfi tana salati da sallama da duniya,ko motsin kirki batayi ,dan da kyar take iya jan numfashi ma. Shikuwa macijin nan yana zuwa gareta ya tsaya saitin fuskarta ya fasa kai yana huci,sai kuma ya fara zagayeta cikin sauri da sassarfa, kafin kuma ya fara hayewa kan ruwan cikinta........ Masu karatu mezai faru da fattu ? Me macijin nan yake nufi da ita ne? Anya ma macijin ne shi? Saimun haɗe next page in Sha Allah taku har kullum anty mammy Mrs babi💘💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing.Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LsrDragdsZn2UMCRLPA7uv Banda maza Please mata kawai . By mammy kabeer 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE SHI 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 7/8 ________________Ihu jauro ya kurma mai ƙarfin gaske ya faɗi can gefe yana burbura tare da rikan "wayyo haroji jaurota zai cinyemin ka taimakeni zan mutu wayyo maciji "ya ƙarasa faɗa da kyar sakamakon wata danƙa mai ƙarfi da macijin nan yayiwa jauronsa har saida numfashinsa ya ɗauke . Haroji kuwa ya mugun tsorata ganin halin da jauro ke ciki,ga wannan ƙaton macijin daya kanannadeshi yana ƙoƙarin karya masa ƙasusuwa. Cikin kiɗima ya rarumo wani ƙaton dutse yayi kan jauro da wannan macijin,yana zuwa baiyi wata wata ba ya ɗaga dutsen ya kwaɗawa macijin nan abayansa. Aikuwa nan da nan bayan macijin ya fashe jini yayi tsartuwa har kan fuskar haroji,wani ihu haroji ya kwala ,sakamakon sauƙar jinin macijin nan akan fuskarsa ji yayi kamar an watsa masa ruwan batir,nan da nan gurin ya sale kamar wanda ya ƙone sai turiri gurin yake. Jifa haroji yayi da dutsen hannunsa yana ihu yana faɗin"wayyo Allah idona bana gani wayyo kwayar idona ta zazzage na shiga ukuna "abinda yake daɗi kenan yana ihu da tsalle. Shikuwa macijin nan silalewa yayi daga jikin jauro ya koma gefe guda tare da kwantar da kansa akasa ,dan kuwa sosai haroji ya kwada masa dutsen nan,kuma da alama ya shige shi . Gaba ɗayan abinda ke faruwa akan idanun fattu ,tana kwance tana kallon ikon Allah,tabbas zuwa yanzu ta gama yarda cewa macijin nan bashi da biyar cutar da ita ,saima taimakon ta da yake,shin wanene wanan macijin?meye alaƙarta da shi?me yake nema agurinta?anya ma MACIJINE wannan ?kodai aljanine yake zuwa mata asiffar macijin? Wadanna sune tarin tambayoyin da fattu ke yiwa kanta tana daga kwancen wanda bata da amsarsu. Saidai kuma gaba ɗaya hankalinta ya tashi ganin yadda macijin nan ya kwanta lamo kamar ya mutu.nan da nan tsoro ya mamaye zuciyarta ,cikin dauriya da jarumta ta yunƙura ta miƙe tsaye tana yamutse fuska,hannunta mai ciwon yana riƙe aɗaya mai lafiyar. Gurin macijin ta nufa gabanta na ci gaba da faɗuwa,dan tsoro take kar ita kuma yayi mata wani abu.tana ƙara sawa ta durƙusa ahankali dai dai inda haroji ya buga masa wannan dutsen ,hannu ta sanya ahankali ,cikin karkarwa jiki ta ɗan shafa gurin ciwon.ai tana ɗora hannunta agurin macijin nan yayi wata irin juyowa tare da fasa kai kamar zai sareta, cikin tsoro da fargaba ta cire hannunta tare da matsawa baya da sauri tana zare ido tana kallon macijin. Shima yana juyowa yaga fattu ce ,sai ya tsaya yana kallon ta,tare da komawa yadda yake ,wato ya sassauta fusatar da yayi ,kawai ya tsaya yana kallon ta. Itama kallonsa take cikin tsoro da bugawar zuciya,ahankali macijin ya fara tahowa ,har ya zo gareta ,runtse idanu tayi tana karanta addu'ar Allah ya tsareta. Ga mamakinta kawai saitaji macijin ya hau kan cinyarta ya kanannaɗe jikinsa ya dora kansa a saman gammon da yayi da jikinsa. Ahankali ta buɗe idanunta tana kallonsa,shima ita yake kallo saidai idanunsa na zubar da hawaye kuma na jini . Jikinta kawai rawa yake cike take da tsantsar tsoron abinda zai faru .juyawa tayi tana kallon haroji dake ta faman ihu yana yaɗuwa kasa.sannan ta kalli jauro wanda yake kwance ba alamun numfashi atare dashi,ga jauronsa nan tayi wani irin kumbura na ban mamaki sai jini ke zuba . Tsorone ya ƙara kamata cikin azama ta yunƙura tare da mikewa tsaye, ture macijin tayi daga jikinta ta kwasa da gudu tayi gida tana kuka . Koda taje gidan, da sanɗa tayi saurin shiga ɗakinta tana kuka,zama tayi akan tabarmarta tare da kife kanta a tsakanin cinyoyinta tana kuka.damuwace fal cikin ranta,wai meke shirin faruwa ne da rayuwarta?wacece mahaifiyarta?waye wannan macijin da yake ɗaukan hukunci akan duk wanda yayi nufin cutar da ita?tanasan sanin wannan macijin waye shi,kokuma waye ya aikoshi gareta.tana cikin kukanta ne kawai taji abu yana hawa jikinta silililili!!! Afirgice ta ɗago kanta tana kallon macijin daya gama hawa jikin nata. kansa ya ɗora akan wuyanta yana fidda wani irin huci ,shiru tayi tana sauraron yadda macijin ke huci,sanan jikinsa yayi wani irin zafi sosai.duk yadda akayi bashi da lafiya ,kuma dukan da haroji yayi masane solar hakan. Tausayinsane taji yayi mugun kamata,ahankali cikin tsoro ta miƙa hannunta tare da riƙo saitin wuyansa ahankali ta janyoshi, ko motsi baiyi ba bare ya hanata abinda yake yi ɗin. Akan tabarmar ta ɗorashi tare da ci gaba da kallonsa,cikin muryar kuka tace "bawan Allah kai waye?meke tafe dakai?waya aikoka zuwa gareni?meyasa kake ƙoƙarin daukar mataki akan duk wanda ya zalumceni?dan Allah karka cutar dani, bani da kowa sai baffana,dan Allah kayi tafiyarki ,idan mutanen garin na suka farga da kai zasu kasheka ,bazan so hakan ba dan Allah na roƙeka ka tafi"ta ƙarasa maganar tana haɗa hannunta cikin kuka. Shidai macijin nan ko motsi baiyi ba sai huci da yake yi sosai, Ahankali ta kalli gurin da yaji ciwo dazu sai taga gurin yana turiri kuma yayi wani fari fat.shiru tayi tana kallonshi ,yanzu ya zata yi masa ne?dan da alama fa yana jin jikine, data rasa abinyi kawai saita lulluba zanin sallarta ta fara karatun Alqur'ani mai girma.cikin abinda bai wuce sakwan biyar da fara karatunta ba kawai macijin nan ya fara wata irin murmurɗewa yana sauya kala, da farko yayi jajur dashi,sai kuma yazo yayi baƙiƙirin sosai ,wani irin hayaƙi na fita daga jikinsa . Duk abinda yake sam fattu bata kulaba ,dan ta ɗaga kanta sama ne tana karatun ,kuma idanunta na zubda kwalla. Shikuwa macijin nan burburwa ya ci gaba dayi yana murɗewa jikinsa na turiri tare da sauya kala.can kuma ya fara wani irin ƙara mai kama da gurnanin zaki.cikin tsoro fattu ta dawo da kanta ƙasa tana kallon macijin , sakamakon wannan sautin ƙara da taji yanayi.sai lokacin hankalinta ya kai kanshi taga abinda ke faruwa. Tsorone ya kamata ƙarara "innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shikenan ta tabbata wannan ba maciji bane tabbas aljanine ,ko kuma aljanine ya shiga jiki sa,na shiga uku ni fattu ya zanyi da rayuwata?meke shirin faruwa dani" ta faɗa cikin muryar tsoro da shiga ruɗu. Shikuwa macijin nan tana daina karatun saiya daina burburwar da wanann gurnanin,ahankali kuma jikinsa ya dawo yadda yake . Ya jima kwance lamo kafin ya fara motsi,kansa ya ɗago tare da fasa kan yana kallon fattu,gaba ɗaya idanunsa sun koma baƙiƙirin dasu sannan wasu irin ƙananan layoyi suka bayyana kusan guda uku aƙasan kanshi, sai wani irin motsi suke kamar ya'yan tsutsa. Karkarwa jikin fattu keyi kamar an saka mata shokin, lamarin ya matukar bata tsoro ,meye wannan ɗin haka suka bayyana jikin macijin nan? Me yasa daga fara karatun Alqur'ani gaba daya ya sauya kama?tabbas akwai wani boyayyen al'amari game da wannan halittar dake gabanta,kuma zata ci gaba da bibiyar macijin nan sannu kan hankali har saita gano menene tattare dashi. Tana nan maƙale jikin katangar karanta kamar ƙadangaruwa dan tsabar tsoro da shiga shock ,idanunta ƙuri akan macijin ,wanda shima ita yake kallo ,kusan minti biyar suna haka ,taga macijin ya sulale ya bar ɗakin ta wannan hanyar tashi. Rarraba idanu ta farayi tana dafe da ƙirjinta ,yau kam tana ganin ikon Allah kala kala ,anya kuwa bata janyowa kanta masifa ba?waima meye alaƙarta da wannan halittar ne?ko dai baffanta zata sanarwa halin da ake ciki ne?kai a'a ba yanzu ba tukunna ,ya kamata ta zama jaruma tayi wanann aikin koba komai zata taimaki rayuwar macijin,dan ta fahimci akwai boyayyen al'amari atareda shi. Su haroji kuwa gaba ɗaya ya fice daga hayyacinsa sai ihu yake yana faɗuwa ƙasa ,ahaka ya nufi gidan lamiɗon garin ,wanda shine mahaifin jauro ,yana ihu yana tumami, har yaje gaban lamiɗo ya faɗi yana "wayyo idanuna ,wayyo fuskata lamiɗo ka taimaka min. Ruɗewa lamiɗo yayi wanda yake tsaye jikin wata sanuwa yana bata ciyawa, lamiɗo bashi da imani ,azalumine sosai ,kuma mutanen garin suna matuƙar tsoronsa, dan haka yake mulki na zalumci agarina,ganin halinda haroji yake ciki"kai haroji menene hakan ?ina jauro?me yasameka?sune tambayoyin da lamiɗo ya jerowa haroji Cikin azabar ciwo da fitar hankali haroji yace "jauro ya mutu maciji ya cinye masa jauronsa yana bakin rafi" Ai dajin wannan batu hankalin lamiɗo ya tashi ,nan da nan yayi kan haroji yana faɗin wane macijin ?me kake cewa ?jauro ya mutu?ƙaryane badai agarina ba ,ba wanda ya isa ya zo garina ya kashe min ɗana."lamiɗo na gama faɗin haka ya kira mazan garin ,ya sanar dasu maza aje bakin rafi ataho da jauro. Aikuwa cikin ƙanƙanin lokaci aka ɗauko shi kamar gawa . Nan da nan lamiɗo ya nemi haroji ya sanar dasu abinda ya faru . Nan ya sanar dasu iya abinda idanunsa suka gani,dan shima yana cikin mugun halin mutuwa ko rayuwa dan tuni gurin da jinin nan na macijin ya taɓa ajikinsa yayi wani irin kore shar yana zubar da wani yallow ɗin ruwa . "Lamiɗo fattu ce ta Turo mana macijin nan ,shine ya kashe jauro"abinda haroji ya faɗa kenan ya sume. Nan da nan mutanen gurin suka fara maganganu Suna faɗin da "da hansai ta faɗa tace mayyace yarinyar ,tunda har ta fara kashe mutane ba zasu yarda ba sai an hukunta itama. Ran lamiɗo ya ɓaci sosai ,dan dama yana jin haushi yarinyar da ubanta,ya shirya neman aurenta amma sam taƙi yarda wai karatu take,yanzu kuwa dama tasameshi da zai hukunta su ita da tsohon nata.dan haka cikin bada umarni yace lallai lallai aje ataho da fattu da ubanta . Nan da nan fusatattun maza suka nufi gidan malam bukar dan aiwatar da ƙudurin lamiɗo........ Masu karatu meke shirin faruwa ne ? Wane hukuncin lamiɗo zai zartar akansu fattu? Mai zai far nan gaba? Muje zuwa yaki ce dai anty mammy Mrs babi💘💘💘 Share and comments fisabilillah. More comments More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Page 9/10 __________________Nan da nan fusatattun rugar suka nufi gidan malam bukar ,dan aiwatar da ƙudirin lamiɗo. Allah Sarki fattu kuwa a wanann lokacin tana ɗakinta cikin jimami da tunanin abinda ta gani yau ɗin nan,haka nan ta tsinci kanta da son sanin menene wannan abubuwan dake motsi aƙasan wuyan maciji? wanda tun daɗewa bata taɓa ganinsu ba sai yau,waya sani ma ko wani akayiwa asiri ajikin macijin ?tabbas zatayi iya ƙoƙarin ta dan ganin ta raba macijin nan da wannan abubuwan ,ta yadda koda wani aka yiwa asiri ta hanyar macijin, to asirin zai karye .sannan tana fargabar gwogwgo ta gano cewar tana gidan kuma bata ɗebo ruwan ba.kuma ahalin da ake ciki yanzu bazata iya komawa rafin nan ba ,.dan ta tsorata dasu jauro . Hayaniyar mutane ce ta cika gidan nasu fattu ,wanda haka yasa gwogwgo hansai fitowa dole badan ta soba, Dan har lokacin nan ita da yaranta ba wanda yayi sallar asuba. "Kai su waye haka suka zo suka cika mana gida da ihu kamar ana yaƙi?"cewar gwogwgo hansai tana gyara daurin ƙirjinta dake ƙoƙarin kuncewa bayan ta fito daga ɗakin. "Aa meye hakan arɗo ?lafiya na Ganku da yawanku kun shigo?ta tambaya lokacin da idanunta ya sauka akan mutanen da suka cika gidan,kusan duk mazan garin ne. Cikin masifa wanda aka kira da arɗo yace "wllh yau saimun ɗauki mataki akan bukar da fattu ,haka kawai yarinya ta fara kashe mutane ,kuma ta rasa ta kan wa zata fara sai ɗan gidan lamiɗo ?wllh yau sai mun kashe Shegiyar yarinyar nan"ya faɗa yana wani zazzaro idanu kamar zararre. Eh wllh afito mana da ita kawai mukaita gurin lamiɗo ya bamu izini mu kashe mayya.gaba ɗayan mutanen gurin suka faɗi haka cikin nuna fusata da ƙosawa abasu fattun . Wani irin farin ciki da jin daɗine ya kama gwogwgo hansai ,shikenan zata rabu da alaƙaƙai cikin sauƙi Allah yasa akasheta kowa ya huta ,dama su haɗa da bukar ɗin da yake ɗaurewa fattu gindi ,koba komai shanunsa sun zama nata.gwogwgo hansai ta faɗa cikin ranta.kafin ta kalli arɗo da sauran mutanen tace "aikuwa idan aka kasheta an kyauta ,dan nima nan wllh so take ta cinyeni nida yarana, jiya da kyar mukasha data maƙuremin wuya wai saita cinyeni, ku ɗan jira kaɗan yanzu zaku ganta shegiya gantalalliya,banma san inda ta tafiba, dama haka takeyi kullum inta fice yawon iskanci bata dawowa da wuri,tana can gurin maza"gwogwgo hansai ta ƙarasa maganarta tana mai buga hannu acinya. "Aikuwa yanzu zamuje mu nemota ko ina ta shiga,wasu sutafi bakin rafin wasu sushiga jeji, mukuma zamu jira ana "cewar arɗo kenan yana kafe sandarsa akasa,sannan ya gyara tsayuwarsa. Duk wannan abunda ke faruwa akan kunnen fattu, tana jin komai ,saidai tashin hankali,firgici tsoro da kuma ruɗewa sun hanata koda yin kwakwkwaran motsine . Numfashinta ma da ƙyar yake fita tsabar ruɗewa. Ta shiga uku !shikenan yanzu kasheta za'ayi?laifin me tayi da za'a kasheta?me baffanta yayi ake nemansa shima? Dama jauron mutuwa yayi ? innalillahi !!!yanzu ya zatayi. Wani kukane ya kubce mata cikin sauri ta toshe bakinta tana kuka sosai kamar ranta zai fita,ji take dama tana da ikon ɓacewa, tabbas da ba abinda zai hanata ɓacewa ta bar duniyar ma gaba ɗaya. Ahankali ta miƙe cikin sanɗa ta leƙo da kanta ,ba ƙaramin tsoro tajiba lokacin da taga mutanen da suka zo tafiya da ita.shikena kawai ta mutu,yanzu shikenan bazata cika burinta na ganin innarta ba?wayyo "Allah ka kawomin ɗauki "ta faɗa cikin raunananiyar muryarta mai cike da tsantsar tsoro. Ahankali ta ƙara leƙo da kanta waje ,cikin rashin Sa'a kuwa sukayi ido huɗu da dan gidan gwogwgo hansai umaru.wanda hayaniyar mutane tasa suma suka farka. "Laaaah aradu gwogwgo ga fattun can cikin ɗakinta tana leƙowa"ya faɗa yana nuna ɗakin da Fattu ke ciki .cikin hanzari fattu ta koma cikin ɗakin tana mai runtse idonta ,tare da dafe ƙirjinta."shikenan sun ganni wayyo Allah na baffa,wayyo MACIJINA kana ina kazo ka taimakeni zasu kasheni wayyo ni fattu"fattu ta faɗa tana mai leƙa hanyar nan da macijin Kebi idan zai bar ɗakin nata inya zo kamar Zariya haka take bankada hanyar macijin da hannunta. "Munafuka ,mayya dama kina ji ana neman ki shine kika ɓuya nan?to fito yau dubunki ta cika ,mutuwa zakiyi wllh saikin bar duniyar nan yau nima na huta da ganinki ,maza arɗo zoka tafi ta ita gata nan"gwogwgo hansai ke faɗin wannan maganar tana daga bakin ƙofar dakin Fattu,dan tun lokacin nan da tasha matsa agurin maciji bata ƙara shiga ɗakin Fattun ba. Aikuwa kafin ta rufe baki su arɗo sukayo kan Fattu suna janta. "Wayyo Allah gwogwgo karki bari su tafi dani zasu kasheni ,wllh ban aikata komai ba wayyo Allah na gwogwgo ki taimaka min"abinda Fattu ke faɗi kenan tana miƙawa gwogwgo hannu cikin kuka mai tsanani. "Ai wllh dana taimakeki gara hannuna ya karye Shegiyar yarinya ,kutafi da ita can ku kashe banza" gwogwgo ta faɗa tana kaɗa hannu irin yadda ake korar kaji ,cikin farin ciki take maganar. Ihu Fattu keyi tana kuka,amma haka suke janta kamar akuya aƙasa, suna cikin tafiya ne ,saiga baffa aguje yazo gabansuu ya tsaya riƙe da sanda yana ta haki,dan yana can bayan gari ya sami labarin abinda ke faruwa acikin garin da gidansa,shine ya rugo yazo . Aikuwa Fattu na ganin baffa ta ƙara fasa ihu tana cewa" wayyo baffana ka taimakeni zasu kasheni" ta faɗa tana miƙa masa hannu,abin tausayi dukta susuce tayi buju buju da jiƙaƙkiyar ƙasa.kallonta baffa yayi Cikin bacin rai mai tsanani ya ce. "Sakarmin yarinya arɗo, kona rotsa maka sandar nan akanka" baffa ya faɗa cikin hargowa da ƙaraji, Kasancewar baffa kowa ya sanshi arugar mutumin kirki ne ,sam ba ruwansa da shiga harkar wani,sanan kuma shine ke ja musu jam'i ,hakan yasa suke ɗan ganin girma da mutuncinsa, dan haka cikin Turo baki da hura hanci arɗo yasaki hannun Fattu wanda ke mata azabar ciwo da raɗaɗi,yana mai cewa"ato lamiɗo ne dai yace mu taho daku,dan haka ya zama dole ayiwa lamiɗo biyayya"ya faɗa yana hararar gefensa, dan yaji haushin sakin wannan hannun na Fattu mai shegen laushi da daɗin taɓawa da baffa yasa yayi.lol Fattu kuwa yana sakar mata hannu ,da rarrafe ta ƙara so gurin baffa ta rirriƙe shi tana kuka da faɗin"wllh baffa ba abinda na aikata,ban kashe jauro ba " ta faɗa cikin matsanancin kuka da tsoro, jikin ta sai rawa yake. Riƙota baffa yayi cikin tausayawa yace "na sani Fattuna,baki kashe jauro ba ,kuma ba wanda zai kasheki, Allah na tare dake kinji"?ya faɗa cikin sigar rarashi,sannan ya kalli arɗo yace"kai arɗo ka kiyayeni ,karka ƙara ƙoƙarin sake aikata irin wannan dabbacin akan ƴata, saboda baka da hankali shine zaka rinƙa janta aƙasa. Kamar wata dabba ?jahilan banza jahilin hofi,muje gurin mai garin zanji idan shiyasaka wannan ɗanyen aikin"baffa ya faɗa cikin mugun bacin rai yana mai riƙe Fattu suka nufi faɗa. Lamiɗo na hangosu ya fara lasar baki ya kure fattu da idanu kamar maye , yana kissima abubuwa da dama cikin ransa.... Manage please yau ina busy,Dan banyi niyar typing bama yau wllh. Masu karatu me lamiɗo ke nufine shima? Hmmmmmm kubiyoni mu hade bayan sallah danjin yadda zata kaya. Kafin nan ina mana fatan yin salla lafiya,sannan aci Nama ahankali kar azo ana ....... Taku anty mammy Mrs babi,💘💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 11/12 Ta ƙabbalallahu Minna waninkum. Slm, ƴan uwa masoyan littafin MACIJINE, ina miƙo gaisuwa tare da Barka da Sallah ,Allah ya maimaita mana,yasa munyi karɓaɓɓiyar Ibada. ________________Kai tsaye su baffa suka nufi gurin lamiɗo,hannunsa riƙe da na fattu ,wacce ke tafiya ahankali cikin azabar raɗaɗin da hannunta keyi,dakuma ciwon jiki.yayinda su arɗo ke mara musu baya burinsu kawai suga wane irin hukunci lamiɗo zai ɗauka akansu fattu ,cikin zuciyarsa arɗo yake fatan inama lamiɗo ya kori su fattu daga rugar ,inyaso su bisu hanya suyiwa fattun fyaɗe,dan su kashe ƙishirwarta dake cin ransu. Shikuwa mai gari tun daga nesa ya hango su fattu,gaba ɗaya nutsuwarsa ta bar jikinsa,ƙureta yayi da ido guri!!yana haɗiyar yawu da lasar leɓe kamar tsohon maye. Kallonta yake yana ji kamar yaje ya kamota yayi ɗaka da ita. haba malam ,yarinya bul-bul da ita kamar nunannen tumatur,lallai yau zai sha shagali.lamiɗo ya faɗa cikin ransa yana mai kallon fattun. Baffa kuwa suna ƙarasowa gaban mai gari ya nemi guri ya zauna tare da zaunar da fattu kusa dashi,wacce gaba ɗaya arikice take ,tsorone ƙarara shinfiɗe akan fuskarta.tayi luƙus ajikin baffanta jikinta sai rawa yake, ta kasa ɗaga kanta ta kalli kowa ,sai hawaye take sharewa. Kowa yanemi guri ya zauna ,masu tsayuwa suka tsaya , da ƙyar lamiɗo ya iya saita kansa ya aro nutsuwa ya yaɓa akansa, tare da ɓata ransa ya kalli baffa yace "malam bukar kana sane da irin abinda ƴarka take aikatawa awannan garin ?lamiɗo ya faɗa cikin kakkausar murya . Ahankali baffa ya gyara zama kafin yace ,naji anata wai wai agari cewar ƴata tayiwa su jauro turen maciji ,amma sam ban yarda da wannan magana ba,dan kuwa ƴata ba mai kashe mutane bace ,sannan ba mayya bace kamar yadda ake faɗa"baffa ya faɗa cikin ɗaure fuska . Cike da ɓaci rai lamiɗo ya fara magana. "To wllh malam bukar bazan ɗauki wannan abun agarina ba,yanzu ace abun nata ya wuce kan kowa sai kan ɗana ?sannan kuma kace wai baka yarda da zancen ba ?kana nufin nayi maka ƙarya ne?to bari kaji dole ne saina ɗauki mataki mai ƙarfi akanka da ƴar taka ,dan ka nuna rashin ɗa'a a gaban fada.bayan kuma kowa yaga abinda ƴarka tayiwa yaranmu, Dan haka bazan yanke hukunci yanzuba sai zuwa gobe ,idan yaranmu sun sami lafiya,dan haka yanzu za'a shiga da ita cikin gida anan zata zauna cikin wancan bukkar da ake ajiye masu laifi . Dan haka kowa ya watse sai zuwa gobe da la'asar adawo nan dan jin hukuncin da zan yanke"mai gari yana gama faɗin haka ya jingina da jikin kujerar da yake zaune akai. gaba ɗayan mutanen dake gurin sunyi na'am da wannan hukuncin nacewar fattu ta zauna a gidan mai gari ,dan karta gudu. Kuka sosai fattu ta sanya tana riƙe hannun baffa "wayyo Allah na baffa ka taimakeni,dan Allah karka bari akulleni adakin hukunci ,wllh bani nayi musu haka ba ,kuma sunzone da nufin keta min haddi baffa ka kalli Yadda ya famamin targaɗe na wllh ba laifi na bane" fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka kamar zata shiɗe. Cikin tashin hankali baffa ya riƙe hannun Fattu ,ji yake kamar ya fasa ihu,aduniya ba abinda ya tsana irin yaga Fattu cikin damuwa,"kiyi haƙuri fattu ba abinda zai sameki,in Sha Allahu Allah zai saka mana dan wannan mugunta ce ake son yi mana ,kuma Allah yana bayan mai gaskiya"yana gama faɗin haka ya juya gurin mai gari yace "lamiɗo ina neman alfarmar abarmin fattu mu tafi gida ,zamu dawo da ita zuwa goben,dan bata da lafiya kuma barinta ita kaɗai akwai matsala" ya faɗa cikin damuwa da alhinin wannan rashin adalci da ake ƙoƙarin aiwatar musu. Cike da mugunta lamiɗo yace "kai bukar ina ganin girmanka karkasa in daina gani ka iya bakinka a faɗa kake,kasan idan na riga yanke hukunci ba mai ja dani ,dan haka ka tashi ka bani guri tun kafin raina ya gama ɓaci kuma yanzu zansa aje anemomin macijin duk inda ya shiga daga nan zuwa safiya ,"lamiɗo ya faɗa yana mai kiran wasu matasa yace su shigar da fattu cikin bukkar. Kuka fattu keyi tana faɗin"wayyo baffana wayyo Allah ka taimakamin zasu tafi dani wayyo Baffa na karka bari su nemo shi zasu kasheshi. "amma haka suka tura ƙeyarta suka tafi da ita ɗakin hukunci.baffa yana ji yana gani ,hawayene masu zafi suka silalo daga idon bawan Allah ,zuciyarsa kamar ta faso ƙirjinsa yakeji, ashe ma ƙoƙarin keta masa haddin ƴa akayi?amma saboda rashin imani da adalci aka ɗora mata sharri,ba komai Allah zai saka musu. Juyawa yayi ya nufi gida ransa amatukar jagule,yanzu idan wani abun ya sami yarinyar fa?idan wasu suka ƙara yunƙurin cutar da rayuwarta fa?"ya Allah ka karemin yarinyar nan Allah ka duba matsalolin dake kanta da wanda suke shirin samunta.ya Allah ka sauƙaƙa mata ƙalubalen dake gabanta.haka yayi ta mata addu'a harya ƙarasa gida kwata kwata hankalinsa baya jikinsa. Yana shiga gidan gwogwgo hansai ta sanya dariya cike da mugunta harda riƙe ciki tana nuna baffa da hannu."wllh malam Gara ka cire wannan yarinyar daga zuciyarka, inba haka ba kana tsaye zaka yanke jiki ka faɗi ka mutu.ba ruwa na bani da asara, ai wllh banso lamiɗo ya kyaleta wai har sai gobe ba,daya sani yasa anyanke mata kai yau -yau ɗin nan ,da mun huta da nauyinta akanmu" ta faɗa tana turo wani baƙin ɗan kwalinta mai shegen datti zuwa gaban goshinta. Kallon ta kawai baffa keyi ,cikin zuciyarsa yake kissima iri saɓawa gwogwgo da zaiyi dan yau zai nuna mata matsayin fattu azuciyarsa ,sai dai yana yunƙurowa da nufin maida mata martani,kawai yaji bakinsa yayi nauyi,wani irin shayinta da tsoro ya mamaye zuciyarsa.kai kawai ya girgiza ya wuce ɗakinsa ,wato itama gidan mai garin taje kenan?ba komai akwai Allah. Fattu kuwa tunda aka turata cikin ɗakin nan banda kuka ba abinda takeyi, ita damuwarta ma yanzu bai wuce na rashin ganin macijinta ba,duk wannan abunda ke faruwa baizo ba.anya kuwa lafiya?kodai wani abu ya sameshi ne? "Ya Allah ka kare wannan bawan naka ,ka bashi kariya daga sharrin mugayen mutane . Shikuwa maciji adaidai wannan lokacin yana gidansu fattu yaje nemanta bai ganta ba yayi ta zagaye aɗakinta amma bata nan,tun lokacin datayi masa karatun nan daya fita yaje can jeji ya kwanta ,sam bayajin daɗin jikinsa sosai yake jin ciwo ta ko'ina ajikinsa,sai da lokaci yaja sannan ya nufi gidansu fattu ,ahankali yake tafiya cikin ciyawa da jikin katanga, harya ƙarasa gidansu fattu. Koda yaje yaga bata nan saiya yi ta zagaye ɗakin yana nemanta ,amma bata nan. Kwanciya yayi akan ɗaurin kayanta yayi lamo kamar ya mutu.saidai hawayene ke zuba cikin idanunsa . Can kuwa gidan mai gari ,da misalin ƙarfe bakwai na dare sosai hadari ya haɗu agarin, dan haka kowa ya shige cikin gida dan gudun zubowar ruwan,da akowane lokaci yana iya sauƙa. Daidai wannan lokacin kuma fattu na duƙunƙune cikin ɗakin hukunci sai kuka take zuciyarta tayi mata ƙunci ga yunwa dake addabar ta rabo ta da abinci tun madarar da baffa ya bata da safe.hannunta sai zagi yake mata. Ahankali taji ana turo kofar ɗakin hukuncin,da alama shigowa za'ayi,ga duhu aɗakin. Zabura tayi cikin sauri ta miƙe tsaye jikinta na karkarwa,kar dai ace su jaurone suka dawo ?wayyo Allah na " ta faɗa tana dafe ƙirjinta ,zuciyarta kamar zata fito dan tsoro da firgici. Cikin rawar murya tace "wa...w....ayee." Ahankali cikin murya mai kama da raɗa,yace "ke kwantar da hankalinki,nine nan lamiɗo" Ya faɗa yana mai haska tocilan ɗinsa . Cikin zubar da hawaye tace "dan Allah lamiɗo ka fitar dani daga gurin nan ,wllh ban aikata komai ba,bani na kashe jauro ba"ta faɗa cikin kuka. "Kinga ki nutsu jauro bai mutu ba yana raye ,kuma idan kika bani haɗin kai muka yi komai cikin sirri ,to zan kyale ki ki tafi gida abinki"lamiɗo ya faɗa yana matsowa gareta. Ja tayi da baya cikin sauri tace "me kake so nayi maka ?dan Allah ka gyaleni na tafi gida ,an fara ruwa"ta faɗa cikin kuka,dan ta gano manufarsa ,irin tasu jauro ce ,wato fyaɗe yake son yi mata. Matsowa lamiɗo yayi tare da ruƙo hannunta yana mai cewa"Ayya fattu yarinya mai kyau da kyan jiki ki yarda dani mana duka -duka minti nawa ne ba dayawa zanyi ba kinji ki taimaka min"ya faɗa yana mai janyota jikinsa sosai . "Wayyo Allah na baffa kazo ka taimakeni,dan Allah lamiɗo kayi haƙuri wllh ba kyau kaji tsoron Allah ka tausaya min na roƙeka"fattu ta faɗa cikin rawar jiki da matsanancin kuka,tana mai tureshi daga jikinta,banda warin tsufa ba abinda yake yi. "Ke dan ubanki ki tsaya ko saina miki ta ƙarfine?Shegiyar yarinya haka zamu zuba miki ido muna kallonki kin cika kinyi tunjum dake amma ba mai morarki,ki tsaya dan ubanki"lamiɗo ya faɗa yana mai ɗauke fattu da wani gigitaccen mari Wanda saida ji da ganinta suka tsaya na wucin gadi.kusan minti biyu kafin kwakwalwar ta ta dawo aiki,kuka ta sake fashewa dashi mai tsananin gaske lokacin da lamiɗon ya Kaita ƙasa yana ƙoƙarin dage yar ficiciyar rigar dake jikinta ,wacce jiƙaƙƙiyar ƙasar nan ta gama bushewa . "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un wayyo Allah na baffa wayyo mai taimako kana ina?kazo gareni,ina buƙatar taimako ka ahhhhhhhh "fattu ta kwalla wani irin ƙara mai ƙarfi lokacin da lamiɗo yayi......... Tofa masu karatu me lamiɗo yayiwa fattu ne ? Muje zuwa kuci gaba da bin alƙalamin anty mammy. Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJINE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 13/14 ____________________"Wayyo Allah na Mai taimako kana ina?kazo gareni,ina buƙatar tallafinka,ahhhhhhhhh !!!fattu ta kwalla ƙara mai tsananin ƙarfi lokacin da taji hannun maigari na ƙoƙarin taɓa mata dukiyar fulani tana mai buge hannunsa daga kan ƙirjinta. Ɗaga hannu maigari yayi cikin fushi ya sake ɗauke fattu da wani gigitaccen mari,dan ya fuskanci tana ƙoƙarin kawo masa cikas akan ƙudurinsa,shikuwa ya rantse yau bazai bar wannan damar ta wuce shi ba. "Dan ubanki ki tsaya nayi- nayi abinda ke gabana,wllh yau ko ubankine bukar zai zo gurin nan bai isa ya hanani aiwatar da ƙudirina akanki ba"mai gari ya faɗa yana ƙara ƙoƙarin maida hannunsa gurin dake tsole masa idanu,wato breast ɗin fattu. Saidai kafin hannunsa ya sauƙa ga inda yayi nufin ,yaji wata irin shaƙa da tunda yake arayuwarsa bai taɓa tsintar kansa cikin irin makamancin wannan shaƙar a aduniya ba. Ta ko ina yaji shi aɗaure dam-dam kamar ƙullin buhun goro. Cikin azaba da fizgar magana mai gari yace "wayyo Allah hannuna,na shiga uku wayyo zan mutu" ya faɗa idanunsa azazzare kamar zasu fito tsabar azaba. Cikin hanzari fattu wacce idanunta ke rufe, ta riga ta gama fitar da rai ta sadaƙar cewa yau shikenan ta rasa budurcinta ,dan ta san ba mai zuwa ya ceceta ,koda tayi ihu ba mai jin sautin ihunta,sakamakon ruwan saman da ake tsugawa.ba zato ba tsammani tajiyo ihun maigari lokacin da maciji yayi sama dashi ya cilla shi can gefe guda ,bayan tabbatar da cewa mai gari ya suma.ji kake ƙasss-ƙasss,hannu da ƙafar mai gari na bangaren dama sun karye. Da sauri fattu ta kalli inda akayo jifa da mai gari dan tabbatar da cewar shiɗin ne kokuma yaya.aikuwa cikin wani irin farin ciki da murna ta yunƙura da ƙyar ta zauna tana kuka da dariya,sai kuma ta tafi gareshi cikin rarrafe tana zuwa inda macijin ke tsaye yana huci ya ƙure mai gari da ido,da alama yana son ganin maigari ko zaiyi wani motsin ne yaje ya ƙarasashi,duba da yadda yake ta uban huci ya kafe mai garin da ido. Fattu na zuwa ta wani kwaƙume macijin zuwa jikinta ,ta ƙanƙameshi tana kuka kamar ran ta zai fita,kukanta na dalilai biyu ne,dalili na farko shine ganin macijinta na nan araye ba mutuwa yayi ba,kuma masu neman shi basu ganshi ba.na biyu kuma yadda yazo ya kawo mata ɗauki adaidai lokacin da ta fidda rai da cewar zata rasa abu mafi muhimmanci arayuwarta. "Ina ka shiga mai taimakona?na shiga damuwa na rashin ganinka, naji tsoron ko sun kamaka sun kashe ,dan Allah karka ƙara yin nesa dani na tsawon lokaci irin haka,kalli yadda suke son kawar min da budurcina, bansan me na tsare musu ba ,kowa nufinsa ya cutar dani,kai kadai ke sona,sai baffana ,bana son na rasa ɗaya daga cikinku ,kune rayuwata,farin cikina da jin daɗina,mai taimakona ina sonka har cikin zuciyata, ba ruwana da kasancewarka wata halitta ta daban,Dan kafiyemin halitta irin tawa sau dubu"duk cikin kuka fattu ke faɗin Waɗan nan maganganu,yayi da take ƙanƙame da macijinta kamar zata maida shi cikinta.yadda ta ƙanƙameshi, kai kace uwace ake ƙoƙarin rabata da ɗanta. Ahankali macijin nan ke sauƙe wani irin numfashi kamar yana hurawa fattu iska mai sanyi ,da alama dai rarrashinta yakeyi,dan yadda yake huro iskar yana wani rufe ido da buɗewa shine zai fahimtar da kai cewar rarrashinta yake . Zare jikinsa yayi daga ƙwaƙwumar da fattu tayi masa ya zagaye west ɗinta ,Amma Sam bai matseta ba ,sannan ya shigo da kanshi ta ƙirjinta yana kallon fuskarta yadda hawaye yayi faca -faca kan kyakkyawar fuskar tata.kallon -kallo ake tsakanin fattu da macijinta ,kallo yake mata irin na tausayawa dan abin mamaki ne sosai idan kaga yadda ya wani marairaice fuska yana ƙifta idanunsa tare da ɗan matso da kansa saitin fuskarta,sai kuma ya kwantar da kan nashi saitin da hawayenta ke tsiyaya, ta ɓangaren dama, sannan yayiwa ɓangaren hagun ma haka. "Dariya mai haɗe da kuka fattu take yi cike da tsantsar ƙaunar wannan halitta ,hannu ta sanya ta share hawayen daya ƙara zubowa tace "na daina kukan mai taimako tunda baka so ,bazan ƙara ba ka gani ma ko "ta faɗa tana mai ƙara shafe idanunta ,saidai wasu hawayen na ƙara zubowa. Zare jikinsa yayi yana mai hawa kan wuyanta zuwa kanta saiya leƙo da kansa ta saman kanta ,idan ta ɗago da nufin kallonsa saiya silale ya koma wuyanta ya ɓoye kansa abayanta. Dariya fattu take cikin farin ciki da ganin cewar wai wasa yake mata dan ta sami nutsuwa ta daina kukan ,dan haka lokacin daya ɓoye abayanta sai tace "wayyo ni fattu mai taimakona ya ɓata, ya zanyi da rayuwata ,ina kake abinsona shikenan masu son cutar dani zasu sami dama akaina wayyo ga mai gari nan ya taso"ta faɗa cikin yanayi kamar tana son yin kuka .aikuwa cikin sauri macijin nan ya haye kan cinyarta yana mai fasa kai da wani kalle -kalle ya miƙa kansa can ya dawo dashi can yana huci. Dariya fattu tayi tace "nima ramawa nayi tunda ka boyemin " ta faɗa cikin shagwaɓa kamar wacce ke gaban baffanta ko innarta. Juyowa macijin yayi yana kallonta sai kuma ya ɗora kansa daidai saitin zuciyarta yayi lamo ,tare da rufe idanunsa.ahankali ta sanya hannu tana shafa kyakyakywan jikinsa mai matuƙar santsi da laushi.kusan minti biyar suna haka,yayinda ake tafaman zuga ruwan sama ,can gefe kuma mai garine shame shame akwance baya motsi.kallon mai gari fattu tayi ,sai taji tsoro ya cika zuciyarta,kodai shima mutuwa yayi, dan ita tama manta da batunsa aɗakin sam,idan kuma ya farka ya ƙara dawo mata fa ,gara fa su gudu daga ɗakin nan tun kafin jama'a su ankare dasu. Cikin muryar tsoro tace "mai taimako ya kamata mu gudu gida karya farka ko wani yazo ya gammu dashi ahaka"ta faɗa tana kallon macijin dake kwance akan ƙirjinta,da alama kuma yana jin daɗin kasancewarsa ahakan. Ahankali ya ɗago kansa tare da silalewa ƙasa yayi hanyar ƙofar fita daga bukkar,wacce mai gari ya barta abuɗe tsabar jaraba na cinsa. Binsa fattu tayi da sauri ,harta fita saikuma ta dawo ta ɗauke tocilan nan ta mai gari ,dan taga garin yayi baƙi ƙirin kuma har lokacin ruwa ake. Suna fita fattu ta kama sauri -sauri gudu-gudu ,tana tafe tana haska tocilan ɗin nan ,yayinda mai taimako ke biye da ita cikin salon nashi gudun ,saidai suna tafe yana zagayeta ,dan bata kariya ta kowacce kusurwa. Suna zuwa gida kai tsaye fattu ɗakin baffa ta nufa,tana zuwa ta shiga ɗakin ahankali tana haska tocilan ɗin hannunta.Allah sarki baffa yana kan sallaya ya ɗaya hannunsa sama yana ta addu'a,juyowa yayi dan ganin hasken da ake haskowa. "Waye anan"ya faɗa yana kunna tashi tocilan ɗin. Ai da sauri ya miƙe tsaye yayi kan fattu,yana mai cewa"fattu kece alhmdllh fattu na ba abinda ya sameki,?ina mai garin?waye ya fito dake?baffa ya jero mata waɗannan tambayoyin alokaci guda yana mai shafa kanta cikin farin ciki . Ahankali fattu ta kalli gefenta ta ƙasa inda macijin nan ke nannaɗe ya fasa kansa yana kallon baffa.tace "baffa wannan ne ya taimakeni, kuma shine macijin daya hukunta su jauro "ta faɗa tana haska macijin da tocilan. Da sauri baffa yaja baya yana faɗin"subhanalla fattu wannan ai MACIJINE ,meye haɗinki dashi,matsa daga gareshi maza karya cutar dake" baffa ya faɗa cikin tsoro yana mai kamo hannun Fattu. "Baffa ka kwantar da hankalinka ,ba abinda zai min ,domin mun jima tare dashi,zauna baffa in baka labarin haɗuwata dashi ,sannan baffa macijin nan yana cikin matsala ,dan da alama anyi amfani dashi wajen yiwa wani asiri. Zama baffa yayi ahankali kan sallarsa ,idonsa akan macijin nan ,daya matso kusa da fattu wacce ke zaune kusa da baffanta,kallon ikon Allah baffa keyi, yadda macijin nan yayi kane-kane akan cinyar fattunsa ya waniyi lub kamar jariri akan cinyar mahaifiyarsa. Kallon fattu baffa yayi ,yaga ko ajikinta saima hannu data ɗora akan bayan macijin tana shafawa. "Ina jinki fattu faɗa min komai dan hankalinta ya kwanta" Nan fattu ta fara bashi labari tun daga farko har kawo yanzu. Sannan ta ɗora da cewa "baffa dan Allah mu taimaki wannan macijin dan wllh yana cikin matsala ,bakaga yadda ya koma ba lokacin dana ke masa karatu,mu cire masa wannan masifar dake jikinsa"ta faɗa tana nunawa baffa waɗannan layun dake wuyan macijin. Cike da mamaki da al'ajabi baffa ke kallon macijin ,wanda ya ƙara kafewa jikin fattu yana kallon baffa da kuma fattu.baffa yace "haƙika akwai wani ɓoyayyen al'amari dangane da wannan macijin ,kuma in sha Allah zamu taimaka masa iyakar ƙarfin mu,tun kafin mai gari ya farfaɗo ya ɗauki matakin kashe macijin nan ,yanzu kije kiyi alwala ki dawo,dan mu fara aiki akansa. Cike da ɗoki fattu ta amsa da" to baffa na ina godiya agareta sosai"sannan ta ajiye macijin gefen baffa tace "mai taimako ai kasan baffana ko?to katsaya agurinsa yan zu zan dawo kaji"ta faɗa cikin murmushi tana shafa bayansa. Kallo ta kawai yayi kafin ya kwantar da kansa ajikin gangar jikinsa dake nannaɗe. Bayan fattu tayi alwala ta dawo dakin ne ta gabatar da sallolin dake kanta ,sannan tayi addu'ar samun nasara akan ceton macijin nan ta shafa.sanna ta juyo gurin baffa wanda ke ta tofa addu'a cikin wata ƙwarya ,zama ta gyara tana mai kallon baffa da jiran ya kammala addu'ar sa. Shikuwa macijin nan yana ganin fattu ta zauna ya silalo ya dawo kan cinyarta ya kwanta,gaba ɗaya jikinsa asanyaye yake,kamar wanda yake tsoron faruwar wani abu.kallonsa fattu tayi tace "mai taimako ba abinda zai sameka ka kwantar da hankalinka ,in Sha Allahu zamu cire maka duk wani sihiri da akayi amfani dakai wajen yinsa"ta faɗa tana mai shafa lallausan san jikinsa mai santsi. Miƙa mata kwaryar nan baffa yayi yace karɓi wannan fattu ki yayyafar masa ajikinsa ,kinayi kina karanta ayatul kursiyyu da falaƙi da nasi, duk abinda zaki gani karki tsorata kinji ?"baffa ya faɗa yana mika mata kwaryar,dan shikam ya gama fahimtar abubuwa da dama aka. Macijin nan. Karɓa fattu tayi cikin nutsuwa ta fara karatun tana kuma shafa masa ruwan rubutun nan ajikinsa. Ikon Allah,ai da fara shafa masa ruwan nan ajikinsa ya fara wani irin motsi da jijjiga ,yana murɗewa ,baffa kuma saiya ci gaba da addu'a yana tofa masa. Ahankali hannun Fattu ya kai kan waɗaɗan na layin dake wuyan macijin nan,aikuwa damƙarsu tayi da Bismillah ta fizge da ƙarfin gaske. Wata irin ƙara da guguwa ne suka turnike dakin gaba ɗaya baka iya ganin komai sai duhu..... Masu karatu mutara gaba dan jin ya zata kaya. Takuce dai Mrs babi💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 15/16 Albishirinku masoya,ga dama ta samu ga mai buƙatar a tallata mata hajarta,to ashirye nake dan tallata mata cikin farashi mai sauƙi,dan haka idan kin shirya sai kiyimin magana . ________________Wata irin ƙara da guguwa ne masu matuƙar ƙarfi da firgitarwa , suka cika dakin.ta yadda koda tafin hannunka baka iya gani tsabar duhun da ɗakin yayi,ga guguwa sai juyawa take aɗakin. Ko kaɗan hakan bai tsorata baffa ba ,saima cigaba da yayi da karanto ayoyin shifa daga cikin alƙur'ani mai girma yana tofawa asaitin dayasan macijin nan yana gurin ,duk da duhun daya mamaye ɗakin. Fattu kuwa wani irin tsorone da fargabar suka baibayeta , jin yadda macijin nan yake wata irin murɗewa da sakin wani sautin ƙara mai ban tsoro ,sannna kuma sai takejin yana ƙara mata nauyi sosai akan cinyarta. Cikin tsoro da ruɗewa ta lalubo hannun baffa tace " wayyo baffa tsoro nakeji,wllh kamar yana rikiɗewa ne zuwa wata halittar ,yayimin nauyi akan cinyata baffa, baffa ina tsoron kar wani abu ya faru"Fattu ta faɗa cikin rawar murya mai cike da tsoro. Hannunta baffa ya riƙe shima cikin yanayi na son kwantar mata da hankali yace"karki damu Fattu ba abinda zai faru sai alkairi,kici gaba da karanto addu'oi kina tofa masa in Sha Allah komai yazo ƙarshe "baffa ya faɗi hakan tare da ci gaba da karanto zafafan addu'oi yana tofawa macijin. Fattu ma ɗaurewa tayi taci gaba da karanto addu'ar tana tofamasa, jikinta sai rawa yake,yadda takejin alamun sauyin halittar da macijin nan keyi.idanunta arufe gam-gam. Kusan shuɗewar mintina biyar zuwa bakwai, duhun nan ya fara yayewa ,ahankali hasken tocilolin su baffa ya fara gauraye dakin. Salati baffa ya farayi da ƙarfi da kiran sunayen Allah yana mai kabbara. "La'ilaha illallah muhammadur rasulullahi sallallahu alaihi wasallam,ya Allahu Ya rahmanu ,ya hayyu ,ya ƙayyum,Allahu akbar, Allahu akbar "abinda baffa keta faman faɗi kenan cike da ta'ajibi da jinjina wa ƙudurar Ubangiji,cikin hanzari ya janyo zanin rufuwarsa ya lulluɓawa maciji ,daga cikinsa zuwa ƙasansa dan ba kaya ajikinsa. Jin yadda baffa ke tafaman kabbara da salati ne ,yasa Fattu buɗe idanunta cikin nutsuwa da kuma jarumta ,har zuwa lokacin bata fasa karanto addu'oi ba.akan fuskar baffa ta sauƙe idanunta ,gaba ɗaya baffa ya shiga al'ajabi da mamakin abinda idanunsa suka gane masa.dan har lokacin yana kallon macijin ne ƙuri kamar ya sami talabijin. Ahankali Fattu take sauƙe idanunta zuwa kan cinyarta,wata irin bugawa zuciyarta tayi ,lokaci ɗaya komai nata ya tsaya cak. Sai wata irin rawa da jikinta ya kama kamar zata karkarye,ta ɗauki kusan minti biyu cikin wannan halin kafin taja wani dogon numfashi tana mai buɗe baki tace"ba.....f..ff..fa ...mumm.......tttuummm....nnnee.....a..Mamman.cc.....iiii.....sai kawai ta sulale ta faɗi ƙasa daga zaunen da take. Ba komai bane ya sanya Fattu shiga cikin wannan halin ba , face ganin wani zankaɗeɗen haɗaɗden saurayi ,fari ƙal-ƙal da tayi kwance ya kifa cikinsa akan cinyarta,maimakon macijin dake kwance akan cinyar ta ta. Kuma wannan shine dalilin salati da baffa keta rafkawa cikin kushu'i da tsarkake baiwa da buwayar mahalicci.lallai duniya ta zama abinda tazama ,yanzu mutum ne aka mayar dashi dabba?maciji?kuma ga dukkan alamu wannan ba ɗan yankin nan bane ,dan ko kaɗan baiyi kama da mutanen mu ba. Ahankali baffa yayi kokarin janye shi daga kan cinyar fattu ya kwantar dashi rigingine akan tabarmar. Hannu baffa ya sanya ya gyara masa zanin daya lulluɓa masa dan rufe masa al'aurarsa.sannan ya ture gashin daya lulluɓe fuskar mutumin. "Masha Allah ,watabarakallahu fi ahsanil kaliƙin"baffa ya faɗa adaidai lokacin da yayi arba da fuskar kyakyakywan matashin mai cike da haiba da kwarjini,ga kyan zati. Kallonsa baffa yake ƙuri yana jinjina kai cike da mamaki da alhini,lallai duniya abin tsoroce, rayuwa bata da tabbas,Allah ka karemu,ka rabamu da sharrin maƙiya da mahassada. Baffa ya faɗa acikin zuciyarsa yana kallon bawan Allahn. Ruwa baffa ya ɗebo ya yayyafawa fattu ,ahankali ta fara motsi tana buɗe idanunta ,tar ta buɗe idanun ta sauƙesu akan baffa, kusan minti biyu tana kallon baffa. "Sannu Fattu kinji?tashi ki zauna kiga ikon Allah ,tashi kiga taimakon da kikayiwa rayuwar wannan bawan Allahn. Baffa ya faɗa yana nuna mata inda macijinta yake kwance. Zabura tayi ta tashi zaune cikin tsoro tana kallon inda baffa ya nuna mata,da sauri ta matso kusa da baffa ta riƙe shi gamm! Jikinta sai rawa yake tace "na shiga uku baffa wllh aljani ne wannan ba mutum bane, daga maciji ya koma siffar mutum ,baffa wllh bamu san me zai koma ba nan gaba ,baffa atsorace nake"ta faɗa idanunta yana zubar da hawaye. Ahankali baffa ya kamo hannunta yace "habaFattun baffa ,kin manta ne?macijin nan ne fa ,wanda yake taimakonki cikin hukuncin ubangiji, shine kuma kikejin tsoro yanzu?kin manta da halaccin sa gareki?meyasa bazaki tsaya tare dashiba?alokacin da yake buƙatar taimakonki kema?ki kwantar da hankalinki Fattu ina ji ajikina wannan bawan Allah shine zai zame miki bango kuma tsanin da zai haɗaki da innarki"baffa ya faɗa cikin yanayi na son kwantar mata da hankali. Murmushi Fattu tayi cikin kwarin guiwa tace "hakane baffa ,kuma zan kula da bawan Allahn nan in Sha Allahu ,harya sami lafiya"ta faɗa cikin kwarin guiwa,saidai har zuwa lokacin tsorone fal cikin ranta.ahankali ta matsa kusa da macijin saidai can nesa kaɗan dashi ta zauna . Kallonsa take cike da mamakin tsantsar kyan da Allah yayiwa wannan bawan nashi, ita kam tunda take arayuwarta, bata taɓa ganin wani mutum mai kyan wannan bawan Allah ba. Dan duk kyanta da ake faɗa ,tayi imani bata kama koda ƙafar wannan bawan Allahn ba. Ahankali ya fara motsi yana ɗan juya kansa hagu da dama.sai kuma ya fara ɗan fizge fizge kamar yana ƙoƙarin tuna wani abunne ko kuma yana son farkawa daga wani mummunan mafarkin . "Baffa kaga abinda yake "Fattu ta faɗa cikin zabura tana kallon baffan. Wata yar jarka baffa ya ɗauko ya buɗe ,ahankali yafara shafa masa ruwan dake cikin jarkar. ahankali maciji ya sauƙe wata ajiyar zuciya mai ƙarfi yana sauƙe numfashi ahankali ahankali. Addu'oi baffa yake tayi cikin wasu magunguna kala-kala yana shafawa bawan Allah nan da yake kwance ,wanda zuwa yanzu jikinsa yayi sanyi,ba kamar dazu da yayi zafi ƙau-ƙau ba. Tun daga ƙafafuwansa Fattu ke kallonsa har zuwa fuskarsa,masha Allah. Wannan mutumin ya haɗu ta ko ina ,anya ma wannan ba haushene?ko bafulatanine irin mu?kai gaskiya wannan bayajin Hausa ko fulatanci,ohhh Ni Fattu yanzu wanann macijina ne haka ?dama da mutum nake ma'amula ashe?waye wannan bawan Allahn?su waye sukayi masa wannan shirin haka?me yayi musu ?inane garinsu?meye sunansa?waɗan nan sune tambayoyin da Fattu ke buƙatar amsarsu ,saidai ba mai bata amsar sai wannan bawan Allah. Baffa ma tunani yake wannan bawan Allah daga ina yake? ,waye yayi masa wannan sihiri?koma dai menene yayi masa maganin da duk sihirin mutum bazai yi tasiri akanshi ba da yardar Allah. Suna nan zaune jigum jigum, cike da fatan Allah yasa ya farka ba tare da wata matsalar ba,kawai suka ga ya fara motsi karo na biyu,saidai wannan karon ba fizge -fizgen yake ba ,kawai dai ya ɗan riƙe kansa yana kuma yatsina fuska. Ido suka ƙura masa ba wanda yayi magana ,daga Fattu har baffa,kowa yayi shiru yana kallon ikon Allah. Ahankali bawan Allahn nan ya fara bude idanunsa yana ɗan lumshesu ,kafin ya buɗe su tar kamar lantarki dan tsananin haske da sheƙin da suke yi. Ƙur ya ƙure rufi bukkar dakin baffa da idanu,baya ko ƙiftasu,tunani yake ina ne nan?waye ya kawo shi nan?kuma yaushema suka zo nan ɗin? Yunƙurawa yayi ya tashi zaune ahankali yana cije light pink lips ɗinsa .kallon ɗakin yake cike da mamaki ,har ya juyo zuwa inda su baffa ke zaune shida Fattu sunyi masa ƙuri suna kallonsa,baffa ya fara kalla cike da rashin sani. "Sannu bawan Allah ka tashi ?meke maka ciwo yanzu ?me kake ji ajikinka" baffa ya faɗa lokacin da suka haɗa ido da bawan Allahn . Ahankali bawan Allahn ya lumshe idanunsa tare da jingina da jikin bangon ɗakin.yana mai dafe kansa ,dan ciwo yake masa sosai. "Ayya Fattu inaga fa wannan bayajin hausa ,kuma bayajin filatanci miƙamin wannan kwaryar In bashi magani ,da alama kanshi ke ciwo. Cewar baffa kenan, dayaji yayi magana amma bawan Allahn bai bashi amsaba. Ahankali Fattu ta miƙe ta ɗauki kwaryar ta miƙawa baffa ita ,tana mai cewa "baffa gashi,kuma kamar ma yana jin yunwa ko ?kaga yana shafa cikinsa"ta faɗa tana kallon yadda bawan Allah ke shafa cikinsa zuwa ƙirjinsa wanda gashi yayi kwance luf-luf akai. Ahankali bawan Allah ya ɗago kansa yana kallon saitin dayaji sassanyar muryar Fattu na tashi. Aikuwa karaf idanunsa suka gauraye cikin na juna ,wata irin faɗuwar gabace ta ziyarcesu alokaci guda, da sauri bawan Allahn ya kawar da kansa yana mai dafe ƙirjinsa,dan sosai ƙirjinsa ya buga. Bangaren Fattu ma kuwa,wata irin bugawa ƙirjinta yayi, wacce har saida taji numfashinta ya ɗauke ,wani jiri ne ya ɗebeta ,tayi baya luuuuuuu zata faɗi,ƙara ta kwalla cike da jin tsoro tana mai runtse idanunta, saidai kuma kafin ta kai ƙasan taji ta faɗa kan wani lallausan abu mai kama da katifa tsabar laushi. Ahankali ta buɗe idonta ta sauƙesu akan......... Muje zuwa masu karatu yanzu muka fara. Taku ce dai anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 17/18 ______________Ƙara fattu ta kwalla cike da tsoro,dan ta saddaƙar kawai ta gama faɗuwa,saidai kuma maimakon tajita akan ƙasa ,saitaji ta faɗa kan wani abu mai matuƙar taushi kamar katifa. Da sauri ta buɗe idanunta dan ganin inda ta faɗa,cikin mamaki take kallon bawan Allah nan,dan hannunsa ta faɗo, lokacin da yaga tayi baya zata faɗi ,bai ma san lokacin daya zabura yayi kanta ba ,tare da tareta ta faɗo akan hannunsa . Kallon kallon sukewa juna basa ko ƙiftawa, yayin da bawan Allah ya zazzaro idanu waje ,irin wanda idan mutum yaga abin tsoro ɗin nan. Ita kuma fattu mamaki take yaushe ya taso yazo gareta harya tare ta ?bata kai ga faɗuwa ƙasa ba? Baffa ne yayi gyaran murya tare da faɗin "subhanallah,fattu sannu, Allah ya taƙaita wahala da tuni kin faɗin ƙasa ,bawan Allah sannu kaji,kana fama da kanka amma zuciyarka mai tsafta bazata bari wani ya cituba,ina mai godiya gareka"baffa ya faɗa cike da jinjinawa bawan Allah nan,lallai akwai wani abu da Allah ya ɓoye tsakaninsa da fattunsa, haƙiƙa fattu kam,zuwa yanzu ta sami mai taimako,kuma yanzu ne ya kamata su fara neman dangin Fattu ,dan zuciyarsa na raya masa wannan bawan Allah alkairine ga rayuwar fattunsa. Ahankali bawan Allah ya miƙar da fattu tsaye ,yana kallon ta sai dai fuskarsa sam ba walwala ,da alama dai irin mutanen nan ne marasa yawan fara'a . Fattu kuwa da sauri ta juya baya tana mai dafe ƙirji ,dan hango zanin da baffanta ya lulluɓawa mutumin a ƙasa,kuma da alama bai ma san zanin ya daɗi ƙasanba. Da sauri shima ya ankare cewar ba zanin fa ajikinsa ,wato yana tsaye tsirara ne.cikin azama ya durƙusa ya ɗauki zanin yana cukuikuyewa ajikinsa, idonsa akan fattu yana fatan Allah dai yasa wannan yarinyar bata ganshi haka ba,dan ma dakin ba wani haske sosai.dan tocilolin sun kalli wani direction ɗin ne da ban. Zama yayi cike da jin haushin yadda zanin jikin nashi ya daɗi kasa,wai ma to ina kayansa ne?me yasa y ganshi haka ba kaya ne? Daga kanshi yayi yana kallon baffa daya miƙa masa kwaryar da fattu ta miƙa dan abashi magani. Karɓa yayi shikam nadan yasan menene aciki ba , kallo yabo kwaryar dashi,yana jin wani irin tashin zuciya ,dan kwaryar ta tsufa sosai ,tayi baƙi saboda ruwam rubutun da ake zubawa a cikinta. "Maza ka shanye bawan Allah zakaji sauƙin ciwon kan"baffa ya faɗa yana nuna masa alamun ya sha da hannunsa ,dan gani yake kamar bayajin me suke faɗi. Kafa kansa yayi yana shan maganin ,bayan ya runtse idanunsa.saida ya ɗansha da yawa kafin ya miƙawa baffa kwaryar. Saidai ko minti ɗaya baiyi da sha ba ,ya kama yunƙirin amai.aikuwa tasss ya mayar da maganin nan,sannu kawai baffa ke masa. Juyowa fattu tayi lokacin daya fara aman, dan tunda ta juya musu baya bata ƙara juyowa ba,saida taji yana aman. Ahankali ta buɗe bakinta tace "sannu hamma"ta faɗa ahankali. Kallonta yayi ,tare da kawar da kansa can gefe yana jingina da jikin katangar karan,ba tare da yayi magana ba .itama bata damu da sai yayi maganar ba,dan su tunaninsu bayajin me suke faɗi. Cikin nutsuwa fattu ta gyara gurin da yayi aman,kanta aduke ,har zuwa lokacin gabanta yaɗuwa yake .shi kuwa bawan Allahn nan yana daga jikin bango Ya lumshe idanunsa ,kamar mai barci.saidai duk abinda fattu keyi idonsa na kanta,mamaki yake da irin kyan da yarinyar ke dashi,gata da nutsuwa komai nata gwanin burgewa.tana da hankali bata da rawar kai duk da ƙaranci irin na shekarunta.dan ya san wannan bata wuce 14/15ba amma Masha Allah,tana kyan diri irin na cikakkun mata ,kalli hips ɗinta kamar wanda aka ɗora mata shi Dass abinta. Jikin fattu ne kawai ya bata cewar kallo ta mutumin nan keyi,dan haka ahankali ta ɗago kanta ,shikuwa daidai lokacin ya ɗan ƙara buɗe idanunsa yana kallon ɗan ma dai-dai cin lips ɗin ta, masu taushi , sai sheƙi suke.aikuwa carab ta kama shi yana mata kallon ƙurillah. Ɗan hararar ta yayi tare da kawar da kansa ,aransa yace "wannan ta cika kallon mutane " Kuji fa masu karatu ?ko tsakanin shi da fattun wake kallon wani? Da sauri fattu ma ta kawar da kanta,azuciyarta tana mai cewa "kuji min mutum shi yana kallon mutane amma kuma baya son akalleshi" "Abba waye yakawoni nan?kuma me nakeyi anan?sannan kuma ina kayan? Baffa da fattu suka ci tsinkayi murya mai shegen daɗi da amon sauti cikin nutsuwa.da mamaki gaba ɗaya suka bishi da kallon ,ba wanda yayi magana dan sai sukaga kamar bashi yayi maganar ba ,dan yana yadda yake bai ko buɗe idonsa ba lokacin da yayi maganar. Jin sunyi shuri ba wanda yayi magana ne ,yasa bawan Allah buɗe idanunsa da suka ɗan yi ja kaɗan yana kallon baffa,sannan ya ƙara maimaita tambayarsa cikin Hausarsa da bata fita sosai. "Ashsha -ashsha ikon Allah yaro ashe kana jin Yaren Hausa ?Alhmdllh.sannu kaji bari na baka kaya saika saka,inyaso zuwa wayewar gari nayi magana kaji"baffa ya faɗa yana mai buɗe wata tsohuwar bakonsa ,kaya ya daukowa bawan Allah nan ,waɗanda dasu yake zuwa sallar juma 'a .wani yaɗi ne yollow share dashi ,anyi masa ɗinkin riga da wando dogaye .miƙa masa baffa yayi yace "kasa Waɗan nan tukunna yanzu kaji" Karɓar kayan yayi yana mai ƙare musu kallo,to ina nashi kayan da za'a bashi Waɗan nan kayan wani iri dasu haka?ɗari kansa yayi ya kalli baffa yana son yayi magana ,amma sam ya kasa,dan ba ɗabi'arsa bace yawan magana ,yana matuƙar jin wahalar yin magana ,shiyasama tun farko yaƙiyi musu magana . Kallon fattu yayi wacce ke zaune can nesa dasu kanta aduƙe,tana wasa da yatsun hannunta ,sannan ya kalli baffa ,ya kalli kayan hannunsa kuma . Fahimta baffa yayi cewar ,yana son saka kayan ne ,kuma yana buƙatar fattu ta bar gurin,dan haka baffa yace "fattu muɗan bashi guri ya kimtsa ko"baffa ya faɗa yana mai kama hannun fattun sukayi wajen ɗakin. Bayan fitarsu daga ɗakin,shikuwa kallon yabo kayan dashi yana juyasu ahannunsa, kusan minti uku kafin ya saka rigar ,dube dube yake ko zaiga boxern sa ,saidai ba alamun boxer aɗakin nan,dan haka ya saka wando yana mai turo baki da ɗan yamutse fuska.sauƙinsa ma ɗaya kayan wanke suke tas ɗasu,sai ƙamshin kilin suke.lol. Koda ya saka kayan zamansa yayi a inda ya tashi tare da lumshe idanunsa ya faɗa duniyar tunani ,shikam a iya tunaninsa baisan meye dangantakar da da Waɗan nan mutanen ba,abinda zuciyarsa tafi yarda dashi shine,wata ƙila yayi hadarine suka ganshi suka taimakeshi. Baffa ne yaji shiru baice musu ya kammala saka kayan ba,kuma ga fattu sai rawar ɗari take, dan zuwa wannan lokacin an jima da ɗauke ruwan saman da ake tsugawa,dare ya raba sosai. Dan haka saiya ɗan leƙa cikin ɗakin.aikuwa azaune ya hangoshi ya jingina kansa da jikin katanga ,sannan idanunsa alumshe . "Ayya ashe ma ya ida shiryawa fattu, shigo daga ciki kar mura ta mamaki naga kinata rawar sanyi,bana so kije ɗakinki ki kwanta saboda hansai idan ta ganki zata je ta sanar da lamiɗo kina nan"baffa ya faɗa yana mai tura ƙofar dakin nashi ya rufeta. "Sannu bawan Allah"baffa ya faɗa cike da tausaya wa. Jinjina kai kawai bawan Allah yayi ,ba tare da ya buɗe idonsa ba. Zama baffa ya gyara ya ƙara cewa"ko zaka iya tuna wani abu daya danganci rayuwarka"?ya faɗa cike da fatan cewar bawan Allah nan bai manta komai na rayuwarsa ba. "Ikon Allah ,saikace wanda yayi lossing memery zan manta da rayuwata "bawan Allahn ya faɗa cikin ransa,amma a zahiri ,ɗan buɗe idonsa yayi ya kalli baffa,sannan ya maida idonsa kan fuskar fattu wacce itama shi take kallon kamar ta sami talabijin. "Kai wannan yarinyar ta cika kallo wllhda wani idanunta masu kama da ruwan Gwale"ya faɗa cikin zuciyarsa yana mai hararar fattun ,kafin ya ɗauke idanunsa daga kanta ya maida kan baffa . Saida ya kai kusan minti biyu kafin ya buɗe baki ahankali kamar baya so yace "my name is ADEEB MUHAMMAD ASHRAF "ya faɗa yana jinjina kansa tare da kallon baffa.gani yayi baffa yana kallonsa alamun kamar bai fahimceshiba. Lumshe idonsa yayi cike da gajiya ,sannan yace "sunana ADEEB MUHAMMAD ASHRAF"yana faɗin haka ya mayar da kansa ya jingina tare da lumshe idanunsa. "To- to masha Allah malam Adeeb ina ne garinku ? Baffa ya faɗa cikin gamsuwa da jin cewar shiɗin musulmine. Dan da yana ta kokwanto shin musulmi ne shi ko arne? Amma zuwa yanzu ya sami nutsuwar jin cewa shiɗin musulmine. Shiru yayi kamar bazai yi magana ba, kafin ya buɗe baki yacewa baffa"nidan MISRA ne" ya faɗa yana kallon yadda baffa yayi zugum cike da tunanin ina yakejin Misra? "Ikon Allah malam adeeb duk da dai Ni ba sanin Misra a ina take nayi ba,amma nasan garine mai matuƙar nisa ,to zahiri gaskiya nan kana Nigeria ne ,cikin ƙauyen ƴar ruga dake jahar Gombe"baffa ya faɗa yana kallon Adeeb wanda mamaki ya mamaye ilahirin fuskarsa , Nigeria kuma ?yaushe yazo Nigeria?bayan rabo da da Nigeria tun last year? "Who brought me hare"?ya faɗa cikin mamaki da sanyin murya.sai kuma ya ɗan rufe idonsa tare da dage kansa kafin yace "waye ya kawoni nan? Shiru baffa yayi ba tare da yace komai ba,na tsawon lokaci ,kafin ahankali ya nuna masa fattu yana mai cewa"haƙika wannan yarinyar itace solar haɗuwar mu dakai ,kuma anan garin ta ganka -----nan dai baffa ya bashi labarin abinda ya sani ,da kuma abinda ya faru yanzu harya koma asalin halittar da. Tunda baffa ke magana Adeeb ya saki baki yana kallo da sauraron baffa,mamaki yake wai shine ya zama maciji?as how ? Me ya faru dashi ?waye ya maida shi hakan?ya Allah who's known how long yake cikin garin nan,ko yaya ƴan gidansu? Ko wane hali suke ciki yanzu?yasan yanzu haka hankalin amminsa yayi matuƙar tashi fiye dana kowa ,lallai dole ya bar garin nan ko ta halin ƙaƙa. "Na gode sosai da taimakon rayuwata da kuka ,amma bani da wani masaniya akan abinda ya sameni, ina don barin garin nan gobe-dan akwai gagarumin abinda ke gabansa,saidai i promise you I will get you back,zan dawo gareku"ya faɗa cikin wani irin yanayi na ban tausayi,dan gaba ɗaya jikinsa asanyaye yake ,sannan damuwa ta cika fuskarsa taf! Da gani maganar ta shiga jikinsa sosai . Cikin murmushi baffa yace ba komai malam Adeeb Allah yayi mana jagora ,saidai ina neman alfarma agareka"baffa ya faɗa cikin damuwa. "Ba komai Abba ka faɗi duk abinda kake don faɗi and I promise zanyi maka shi"ya faɗa cikin sanyin murya mai cike da tarin damuwa. "So nake ka tafi da ƙanwarka can garin naku ,domin ka taimaka mata wajen saduwa da asalin iyayenta baffa ya faɗa cikin tsantsar damuwa yana mai kallon fattu,wacce taji maganar baffa kamar sauƙar aradu ....... Masu karatu mu tara next page Taku ce anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 19/20 https://www.facebook.com/groups/1627491150723081/?ref=share_group_link Masu amfani da face book sai kuyi join wannan group ɗin . _______________"So nake ka tafi da ƙanwarka can garin naku,dan taimaka mata wajen gano iyayenta na asali"baffa ya faɗa yana kallon fattu ,wacce tunda baffa ya fara maganar take jin wani irin matsanancin faɗuwar gaba ,ji tayi maganar tasa ta sauƙa acikin tsakiyar kanta ,kamar sauƙar aradu,"wace irin magana baffa keyi ne haka" anya kuwa yasan me yake faɗi?kai a'a gaskiya bai gane me yake faɗi ba shima. Fattu ta faɗa cikin zuciyarta,tana mai sauƙe ajiyar zuciya ,dan ta fahimci baffa yana nufin innar ta kenan,saidai kuma bata da wani dalilin bin mutumin da bata sanshi ba,Gara tayi zamanta agurin baffanta ,inyaso innar tata inhar ta damu da ita ,zata zo gareta. Ahankali fattu ta buɗe bakinta tace "baffa ina ganin babu buƙatar saina bishi wani garin ,dan neman innata,zan zauna anan ɗin idan da rabon zamu gana wata rana zata zo gareni baffa"fattu ta ƙare maganarta cike da mugun bugawar zuciya ,dan har lokacin kalaman baffa na mata yawo akanta. Ajiyar zuciya baffa ya sauƙe cike da alhini abinda zai faɗa wa fattun ,kafin yace"ayya fattu amm ki saurareni, da kyau ,ki nutsu ,kuma ki sani kowane bawa da yadda ƙaddararsa ke zuwa masa. Haƙiƙa Ni malam bukar bani ne na haife ki ba na tsincekine tun kina yarinya ƙarama "baffa ya faɗi hakan yana mai sunkuyar da kansa cike da tausayin fattu. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un baffa me kake faɗi ne haka?dan Allah baffa kayi haƙiri idan nayi maka wani laifin ne,amma karka ƙara nesanta alaƙarka dani, baffa bazan iya jura ba,bansan kowa ba sai kai ,kai kaɗai ne gata na baffa dan Allah karka rabu dani "fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka marar sauti sosai. Shide Adeeb kallonsu kawai yake cike da mamaki,how can that be possible ace wai ya tafi da wata yarinya har can ƙasar su ,yace a ina ya samota ?kuma ta yaya ma zai fara neman ahalin yarinyar .shifa gaba ɗayama lamarinsu ɗaure masa kai yake ,basu sanshi ba,ba wata alaƙa atsakaninsu dashi,amma yana ƙoƙarin bashi yarinya ya tafi da ita. Kallon baffa yayi lokacin dayaji yana magana da cewa"nasan zaki shiga ruɗu da damuwa Aduk lokacin da kika sami wannan labarin fattu,saidai bani da yadda zanyi,yazama dole insanar dake gaskiyar abinda ke wakana,kisani fattu ina ƙaunarki fiye da ƴaƴan dana haifa na cikina dan kin fiyemin su sau dubu.amma son da nake miki bazai sa in cutar dake ba ta hanyar ƙin faɗa miki gaskiya fattu , kisani ahalin yanzu zamanki arugar nan akwai haɗari ,idan mai gari ya farka,kinsan hukuncin da zai zartar akanki bazai mana daɗi ba .dan haka kiyi haƙuri wllh badan cutarwa yasa nace tafi dake ba,saidan ko da baya nan to nayi niyar barin garin nan dake Dan tseratar da rayuwarki" Baffa ya faɗa hawaye na zubowa daga idanunsa. Kuka fattu kawai take cike da wani irin baƙin ciki marar misaltuwa, wannan wace irin ƙaddara ce ?yanzu shikenan bata ga tsuntsu bata ga tsarki,baffan da take gani matsayin mahaifinta ashe shima ba mahaifinta bane?kenan ita bata da kowa?tunda ta taso take cikin bakin ciki da damuwa ,amma ta kwance zamanta cikin wannan bakin cikin akan zuwan wannan ranar.kuka take irin wanda yake fitowa kai tsaye daga zuciya ba abinda take fata ahalin yanzu kamar ace ta farka taga ashe barci take ,tayi wannan mummunan mafarkin.to suwaye iyayenta?me tayi musu suka yarda ita?shin basa son tane ko yaya?tambayar da take tayiwa zuciyarta kenan,jikinta kuwa nan da nan ya ɗau ɓari,kan kace me tuni zazzaɓi mai zafi ya kamata. Ahankali Adeeb ya kalli baffa na tsawon lokaci kafin ya buɗe baki cikin salonsa na rashin son magana yace "amma Abba ta yaya zaka bani ƴarka i tafi da ita ?bayan baka Sanni ba,bakasan koni ɗin waye ba ,infact baka saniba ma koniɗin mugune ,Amma kake don bani ƴarka in tafi da ita why?Adeeb ya faɗa yana kallon baffa. Dan murmushi baffa yayi,irin wanda yafi kuka ciwon nan,kafin yace "na yarda da kai nasan bazaka taɓa cutar min da fattu ba ,dan tun kana wata halittar wacce ta kasance muguwa kake taimakonta, bare yanzu da kake cikakken mutum.sannan na jima ina addu'a akan Allah ya kawo wanda zai zama silar farin cikin fattu ,sai haka Allah ya kawo ka,alokacin da mu bamuyi tsammani ba,kuma kallo ɗaya nayi maka zuciyata ta aminta da kai ,nasan Allah ne ya karɓi addu'a ta.dan haka bani da wani kokwanto akanka." Baffa ta faɗa cikin nuna yanayi na gamsuwa akan hukuncin daya yanke. Ahankali fattu ta rarrafe zuwa kusa da baffa ,hannunsa ta kama ta riƙe gamm!cikin nata ,kafin tace "baffa su waye iyayen nawa?me yasa suka yarda Ni?a ina ka tsinceni?ta faɗa cikin kuka tana mai jan majina. Kallon ta Adeeb yayi cike da tausayawa,dan sosai yaji ta bashi tausayi, she's too young ace ta fuskanci wannan babban ƙalubalen. Baffa ne ya fara magana da cewa"kafin na auri hansai na auri wata kanwata,yar gidan tayar babata. Inda muka kasance duka marayune daga i har ita.itace matata ta farko ,minyi aurene irin na haɗin zumunci,tana da haƙuri da kawaici ,muna zaune cikin aminci da mutunta juna,har Allah ya bata ciki. Munyi murna sosai da samun wannan cikin ,tare da addu'ar Allah ya sauƙeta lafiya. Wata rana kuwa naƙuda ta kamata,ganin yadda take shan wahala ,saina tafi jeji dan ɗebo mata maganin gargajiya tasha,ina cikin tafiya nayi nisa sosai da rugar nan,kwatsam saina fara jiyo kukan jariri,haka nayi ta bin sautin kukan harna cimma gurin. Kwance na iskeki kinata kuka gaba ɗaya jikinki yayi ƙura, sannan kin kukkurje dan ga jini jini nan ma ajikin rigar dake jikinki, Addu'a nayi tare da ɗaukoki na dawo gida . Koda na dawo gida na iske matata tana kuka ga gawar jaririya nan gabanta.wato ƴar da ta haifa ta koma. Munyi baƙin ciki sosai da rashin yarinyarmu,amma haka muka haƙura muka mikawa Allah lamarinmu. Nan na bata labarin samoki da nayi,sai naga tana ta murna da farin ciki,batayi wata- wata ba ta karɓe ki ta fara shayar dake,koda nayi magana saitace"Allah ne ya dawo mana da farin cikinmu.dan haka zamu rikeki matsayin ƴarmu da muka rasa,idan kuma munji anyi cigiyarki saimu bada ke. Nan da nan nima na yarda da shawarar ta ,dan lokaci ɗaya Allah ya samun ƙaunarki raina. Haka na gayyato mutane akayi suturar ƴarmu,yayinda nake faɗawa Mutane cewar ƴan biyu matata ta haifa ,ɗayar ta koma sai ɗayar. Lokacin da muka tsinceki akwai wani sarƙa awuyanki,wacce da alama zata yi matukar tsada ,dan haka sai muka cire muka ajiyeta haɗe da rigar dana tsinceki da ita. Munsha tambaya akan ya akayi baki biyo ko ɗaya daga cikinmuba,dan kin kasance kyakyakywa wacce kaf rugar nan ba wanda ya kama ƙafar kyanki,sannan gashinki ba irin namu bane.haka dai muke samun amsar da zamu rufe bakin mutane da ita. Shekararki biyu a duniya ,Maryama ta koma ga Allah.munyi kuka daga ni harke na rashinta, kafin daga bisani muka haƙura. Lokacin ne na auri hansai ,wacce ta kasance ba abinda ta iya banda mugunta da baƙin hali,sam bata ƙaunar ki ,da idan tayi miki wani abun nakan yi magana ,saidai daga baya kuma sainake kasa yin maganar,koda na yunƙuro da nufin yin maganar bana iyawa. Wannan shine taƙaitaccen tarihinki fattu na.amma na tabbata ko ba daɗe ko ba jima zaki haɗu da asalin iyayenki,jikina yana bani kun kusan haɗuwa. Wanda idan har kikaci gaba da zama cikin rugarnan, hakan bazata faru ba.zan nemeki Aduk inda kuke fattu na "baffa ya faɗa cikin kuka abin tausayi. Fattu ma kuka take sosai kamar ranta zai fita ,"baffa ina sarƙar take "fattu ta faɗa cikin rawar murya irin ta mai zazzaɓi. Tashi baffa yayi ya buɗe cikin jakarsa ta kaya ya ɗauko wata leda ya kunce,saiga wata sarƙa mai tsananin sheki da ɗaukar ido,sai wata ƴar riga mai kyau fara ta yara.miƙawa fattu kayan baffa yayi . Ahankali ta karbi kayan ta rungume ajikinta tana kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro. Kallonsu kawai Adeeb yake ,dan zuwa yanzu ya gama ɗaukarwa kansa alƙawarin taimakawa fattu ta kowace fuska ,har saita ga iyayenta. Baffa kansa kukan yake ,yana jimamim rabuwa da Fattun sa. Tashi Adeeb yayi ,cikin tafiyarsa ta izza da cike jarumta ya ƙarasa kusa da fattu ,tsugunmawa yayi akusa da ita ,yana kallon fuskarta dake ta faman kuka ,gaba ɗaya tayi jajur da ita. Hannunsa ya sanya ya ɗago habarta ya kura mata ido,buɗe idanunta tayi itama ta sauƙe cikin nashi,sun ɗauki kusan mintuna uku suna kallon juna,kafin Adeeb ya sauke wani kwauron numfashi ,sannan ya sanya babban ɗan yatsanshi ya share mata hawayen dake zuba a idonta.girgiza mata kai yayi alamun ta daina kuka.amma sam ta kasa dainawa. Sarƙar hannunta ya karɓa yana kallo,sarkar zallar daimond ce sai sirin kwal,da gani wannan sarƙar ta doshi millions ,koma ina yarinyar nan ta fito to tabbas ƴar gidan manya ce,in Sha Allah zai haɗata da iyayenta na asali. Sarƙar ya buɗe tare da nufar wuyanta wanda yake nan zafi ƙau da zazzaɓi,ya ɗaura mata sarƙar.nan da nan sarƙar ta ɗauki wani sheƙi da walwali. Dawo da kallonsa yayi kan baffa wanda yake kallon duk abinda ke faruwa,zuciyarsa tana masa wani irin ƙuna da ciwo. Saida ya ɗauki kusan minti biyar kafin yace "Abba nayi maka alƙawarin zan taimaka wajen neman asalin iyayen yarinyarka,zamuiyi amfani da wannan sarƙa in Sha Allah everything is gonna be ok"ya faɗa cikin muryar sa mai daɗin amo . Hannunsa baffa ya kama cikin farin ciki yace "na gode Allah yayi maka albarka,ka kulamin da fattu karka bari ta cutu " Jinjina kai yayi shima yana mai riƙe hannun baffan, akaro na farko ya ɗanyi murmushi.masha Allah masu karatu bakuga yadda yayi wani sihirtaccen kyau ba,Dan murmushin ba ƙaramin kyau ya ƙara masaba. Kwanciya fattu tayi akan sallaya ta juya bayanta tana ta kuka da rawar zazzaɓi,shikenan yanzu haka zata bi wannan bawan Allah da batasan koshi waye ba,meyasa iyayenta suka yarda ita?me tayi musu haka da zafi?dama baffa ya fasa ƙidurinsa na cewar saitabi wannan bawan Allah mana. Baffa ne ya miƙe tsaye da sauri tare da leƙawa ƙofar ɗakinsa, dan tabbas yaga gilmawar mutum,aikuwa yana leƙawa ya hango zanin gwogwgo hansai tana shigewa ɗakinta. Ya Salam kenan taji duk abinda suke tattaunawa ?lallai dole su bar gidan nan kafin gari ya gama wayewa.dan yanzu kam asuba ta kawo kai, Da sauri ya koma ɗakin yace "Adeeb akwai matsala,yanzu yanzu zaku tashi ku dau hanya,dan kuwa hansai taji duk abinda muke tattauna,kuma na tabbata ko bari bazata yi gari ya gama wayewaba zata je ta sanar da mai gari" Baffa ya faɗa cikin tashin hankali da damuwa. Shikuwa Adeeb ko ajikinsa ƙara gyara zama yayi ,dan bazai iya kwanciya anan gurin ba ,kafin ya kalli baffa ya ɗan taɓe baki yace "and so what idan ta faɗa masa"? Ya faɗa cikin ko in kula. "Bazaka gane zalumcin lamiɗo ba Adeeb zai iya sawa kashe fattu ,dan Allah ku tashi muje In fitar daku hanya ku tafi, ka taimaka min ka ceci rayuwar yata"baffa ya faɗa cikin kuka yana durƙusa akan gwuiwoyinsa. Da sauri Adeeb ya tashi ya kama baffa ya miƙar dashi yace "is ok Abba zamu tafi yanzu.ya faɗa yana mai kamo hannun fattu ya miƙar da ita tsaye. Ita kuwa fattu yadda yake jin zuciyarta bayani ace mai gari yasa a kasheta Bama,koba komai zata huta da ƙuncin zuciya da damuwa.tana mikewa tayi baya zata faɗi,dan gaba ɗaya ba ƙarfi ajikinta.da sauri Adeeb ya tallafi ga zuwa jikinsa,kallon fuskarta yayi wacce ta kumbura ,sai rufe idanu take tana buɗe wa,da gani tana shan jiki sosai. "Muje bawan Allah ,fattu daure kinji"baffa ya faɗa cikin ruɗu ,ba abinda yake ɓukata irin yaga sun bar rugar nan. Ganin fattu zata ɓata musu lokacine yasa Adeeb ya ɗagata sama tsak!kamar ƴar tsana ya saba akafaɗarsa yacewa baffa" muke Abba" Wata leda Baffa ya dauko,tare da rigar nan ta fattu ya cusa ciki,sannan yayi waje suka rufa masa baya...... Masu karatu me zakuce game da rabuwar baffa da fattu? Mrs babi ce💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 21/22 _______________Wata leda Baffa ya ɗauko ,ledar da ɗan nauyi ,alamun wani abune acikin ta .sannan ya ɗauki wannan rigar ta fattu ya cusa acikin ledar,safin yayi waje ,Abeed ya rufa masa baya. Ahankali baffa ke takawa Abeed na biye dashi,saɓe da fattu akafaɗarsa,wacce ke cikin matsanancin hali na zazzaɓi,da damuwa. Tafiya suke cikin sauri bayan sun bar gidan ,cikin ikon Allah basu haɗu da kowa ba ,har sukayi nisa da garin sosai,saida baffa ya fitar dasu kan kwalta kafin ya tsaya . Har zuwa wannan lokacin fattu na saɓe akan kafaɗar Abeed ,duk da irin uban nisan dake tsakanin rugar da kwalta. Ahankali Abeed ya sauƙe fattu ya ɗan jingina ta da jikinsa,dan yaga bazata iya tsayuwa ba . "Malam Abeed karɓi wannan wasu yan kudadene da nake tarawa saboda irin wannan ranar,nasan zasu toshe muku wata kafar,dan Allah ka riƙe min alƙawari, ka kulamin da fattuna,karka bari wani ko wata ya cutar da ita,sannan kayi iyakar ƙoƙarin ka wajen sadata da magaifanta. Kaima zaka sami lada"baffa ya faɗa yana kallon bayansa ,hanyar da suka baro ,dan tsoro yake kar yaje ko anbiyosu,dan yasan zuwa yanzu labari ya isa kunnen lamiɗo,tunda gari yayi haske an kusan shiga sallah. "In Sha Allahu Abba zan kula da amanar ka,na gode da taimakon da kukayimin, sannan zan dawo gareka very soon"Abeed ya faɗa cikin nutsuwarsa da rashin son magana,akwai abubuwan da yake son faɗa amma tsabar rashin son maganarsa bazai iya ba dan haka yayi shiru daga wannan maganar. Hannun fattu baffa ya kama yariƙe gam-gam cikin nashi,kallon ta yayi yayinda itama take kallonsa cikin kuka wanda muryarta ko fita batayi sosai, shima baffa tuni zuciyarsa ta karaya ,sai hawaye sharrrr!! "Allah ya shiga lamarin ki fattu, Allah ya karemin ke ka yasa damu da alkairi,ki kula da kanki,ki kama mutuncinsu.Allah yayi miki albarka"baffa ya faɗa cikin kuka sosai,abin tausayi. "Baffa bana son tafiya ,dan Allah kace na zauna ,Ni nafison zama da kai akan iyayena ma asali,baffa karka tafi ka barni "Fattu ta faɗa cikin kuka harda shashsheka kamar zata shiɗe. Kafin baffa yayi magana saiga wata mota zata wuce ,da alama daga cikin Jos take . Da sauri baffa yayi musu hannu alamun su tsaya.tambayarsu yayi ina suka nufa ,mai motar yace Kano. Kallon Adeeb baffa yayi yace "duk da bansan inane Kanon ba amma Gara kubi wannan motar kafin tawagar mai gari su fito nemanku. Kai kawai Abeed ya ɗada,tare da kamo hannun fattu suka nufi motar,hannunsa ɗaya riƙe da ledar da baffa ya basu. Kuka fattu take harda ihu tana faɗin"wayyo baffana ,banason tafiya,dan Allah baffa kace na dawo wayyo baffa am wayyo Allah na ,wayyo rayuwata " Baffa kam ko magana ya kasa tsabar kuka sai daga musu hannu kawai yake yana juya kai. Abeed ne ya sanyata cikin motar tare da riƙe ta ,ɗan sai ƙoƙarin fitowa take ,haka mai motar nan yaja motarsa yayi gaba,dan kaya zaije ɗaukowa. Baffa yana tsaye har saida yaga ɓacewar motar ,sannan ya sauke wani kwauron numfashi yana mai share hawayen idanunsa,"Allah ga amanar ƴata nan na miƙa lamarin ta ahannunka ,ya ubangiji kazama majiɓancin al'amarinta "baffa ya faɗa yana mai juya dan koma gida ayi wacce za'ayi. Aikuwa tun kafin ya ƙarasa cikin garin ,ya hango cincirindon mutane aƙofar gidansa,jinjina kai yayi,dan dama yayi tsammanin hakan . Suna hangoshi sukayo kan suna wllh koya fito da ƴar Shegiyar daya ɗauka matsayin ƴarsa ,da kwarton ta da suka ajiye agida,ko kuma su kashe shi yanzun nan. Kallonsu yayi cikin kamala da dattako yace "ikon Allah me kuma mukayi dazaku kashemu?wace yarinyar kuke nema?bayan wacce mai gari ya riƙe agurinsa?baffa ya faɗa kai tsaye ba nuna alamun tsoro. Nan wani lawwali yace masa"ai jiya yarinyar nan saida ta bari dare ya raba sannan ta sami lamiɗo tayi masa jina jina,gaba ɗaya ƙafafunsa sun ƙarye,ga hannun damanshi ma ya ɓalle baral, sannan ta gudu,kuma munsan tabbas tana gidan nan,dan kuwa hansai ta kai labari, Kuma ta fayyace mana komai game da yarinyar ,ashe Shegiya ce ka tsinto ka kawo gidanka,sannan ka ajiye mata wani gardin suke lalata dashi,dan haka gaba ɗayanku yau sai hukunci ya hau kanku,dan lamiɗo yana nan banda ihu ba abinda yake yana kiran maciji zai kashe shi,fattu ce tayi masa ture.sannan arɗo ma yana can hannunsa guda ya shanye ya zama kamar sillan kara ,kuma duk aikin fattu ne ,dan haka yau wllh saimun kashe fattu"lawwali ya ƙare zancensa yana mai ɗaga sandarsa sama. "Toh me yasa baku shiga kun duba fattun ba ?idan nan ta dawo,ita wacce ta kai muku rahoton saita faɗa muku inda fattun take"baffa ya faɗa yana ƙoƙarin shigewa gida. "Ƙarya yake wllh, saidai in ya boyesu ,ko kuma sun gudu ,dama naji yana cewa su gudu dan haka karku taga masa " na tsinkayo muryar gwogwgo hansai na faɗin haka ,dan taji mugun haushi da ba'a sami su fattu cikin gidan ba. Aikuwa baffa yana tsaye Ba zato ba tsammani yaji sun rufeshi da duka ta ko ina. Har saida suka kaishi ƙasa.sannan suka taitayeshi sai gurin. Mai gari.suna zuwa suka tarar ana yiwa mai gari ɗori sai ihu yake yana kuka.dan haka can ɗakin hukunci suka jefa baffa,wanda yayi kaishi sosai dan ya daku. Allah Sarki baffa ,Allah ya saka maka. Fattu kuwa tsabar kuka har muryarta ta dashe,can jikin ƙarshen motar ta koma tare da haɗe kai da gwuiwa tana kuka marar sauti ,jikinta sai rawa yake ,fuska ta kumbura suntum tayi jajur ,abinka da farar fata. Abeed yana daga gefe yana kallonta ,sosai yake jin kukanta har cikin ransa,haƙiƙa yarinyar tana fuskantar ƙalubalen rayuwa and she's to Young to handle the situation.amma ya zatayi?dole ta ɗauki ƙaddara yadda yazo mata. Kallonta yayi yadda jikinta ke ta rawa tana shashsheƙar kuka,yaso ace ya iya rarrashi, daya rarrasheta ,koba komai itaɗin yanzu amanarsace,amma Gara tayi kuka ,koba komai zata rage jin raɗaɗin da taleji cikin zuciyarta. Tafiya suke sosai ,Dan drivern gudu yake tsulawa,kasancewar safiya ce hanyar ba motoci sosai,sai jifa-jifa suke cin karo da motocin. Abeed yayi shiru ,tare da jingina kansa jikin kujerar da yake zaune,ba abinda ke yawo cikin zuciyarsa,sai labarin da baffa ya bashi na cewar wai shiɗin amaciji suka ganshi,to ta yaya?yaushe hakan ta faru,me yasameshi? Tabbas idan har abinda baffa ya faɗa gaskiya ne baya raba ɗayan biyu cewar sharrin Amma ne wannan ,dan ita kaɗai yake tunanin zata iya cutar dashi ,tunda afili take nuna masa ƙiyayya, amma zaibi abin ahankali harya gano mugun ƙullinta akansa kafin ya ɗauki mataki. Ya rasa me ya tsareta Amma arayuwa sam bata ƙaunarsa ,kullum burinta ta cutar dashi,tun yana ƙarami yake fuskantar tsangwamarta,har kawo yanzu bata fasa ba ,amma akwai lokacin da ko ance tayi masa wani abun bazata iyaba. Juyowa yayi ya kalli inda fattu ke zaune ,har zuwa wannan lokacin kuka take ,banda rawa ba abinda jikin ta keyi.wani tausayine yaji ya kama zuciyarsa ,wannan kukan yayi yawa zai iya haifar mata da matsala.dan haka ahankali ya ɗan matsa kusa da ita ,ƙureta yayi da ido ,yana son yayi mata magana amma baisan me zaice mata ba. Kusan minti uku yayi yana kallonta da yadda jikinta ke rawa sosai,kafin ya sanya hannunsa ahankali ya dafa kanta . Da sauri fattu ta ɗago kanta agalabaice ,idonta ya mugun kumbura yayi jaaa!sosai lips ɗinta sai sheƙi yake .kallonsa tayi wani sabbin hawayen na kwararowa daga idanunta. Dan yatsansa ya sanya ya share hawayen dake zuba daga idanunta,amma wasu na ƙara zubowa. Da gyar ya buɗe bakinsa cikin hausarsa da bata fita sosai yace "menene"ya faɗa yana kallon cikin idanunta ,gabansa sai bugawa yake,ya rasa mai yasa inhar zai sanya idonsa cikin nata ,to gabansa yayi ta bugawa kenan. Cikin dasashshiyar murya wacce kuka ne yasanya ta dashe fattu tace "Baffana" cikin yanayin shagwaba irin na masu kuka tayi maganar. Wani yummmmmm!!!Adeeb yaji tun daga tsakiyar kansa har babban dan yatsan ƙafarsa.dan yanayin yadda tayi maganar sai yaji wata irin kasala ta kama shi. Ahankali ya kumshe idanunsa yayi jimmm!kafin ya buɗe su ya ɗora akan fattu"is ok ki daina kuka"ya faɗa ahankali yana mai janyowa zuwa jikinsa ,dan shikam hakan kaɗai yake ganin zai yi mata tayi shiru. Allah Sarki fattu kuwa tayi luƙus akan faffaɗan ƙirjinsa sai ajiyar zuciya take sauƙewa,kuma cikin ƙanƙanin lokaci ta fara jin zuciyarta nayi mata sanyi, tana nan kwance ajikinsa barcin wahala yayi gaba da ita. Shikuwa Adeeb gaba ɗaya jinsa yake wani irin,sam ya kasa samun nutsuwa jinta da yayi cikin jikinsa ,gaba ɗaya yaji yanayinsa na sauyawa zuwa kasala da jin wani abu mai kama da feeling ,ahankali ya jingina kansa jikin kujerar ,tare da kumshe idanunsa yana mai ƙara gyara mata kwanciyarta. Tunanin Abie ya fara yi aƙokarinsa na kawar da abinda yake ji acikin jikinsa ,dan aganinsa wannan yarinyar tayi ƙanƙantar da har zai rinƙa jin wani abu akanta,saidai sam jikin nashi yaƙi bashi haɗin kai,dan ji yayi lamarin na ƙara rikice masa,ganin ba sarki sai Allah yasashi cire ta daga jikinsa ya jingina ta da jikin kujerar da suke kai. Ajiyar zuciya ya sauƙe yana mai kallon kyakyakywar fuskarta ,wacce ta ƙara wani jaaa!sosai ,ahankali ya sauƙe idanunsa zuwa lips ɗinta waɗanda ta ɗan turosu Baga cikin shagwaɓa kamar kamar yadda yara keyi idan suna son yin kuka. Haka kawai ya tsinci kansa da sakin wani murmushi mai ƙayatarwa, hannu yasa ya gyara mata hulɗar kanta,wacce ta ɗan zame har gashinta na gaban goshi yasami damar fitowa . Bai ankara ba yaji driver na cewa sun iso Kano,kallon garin yake ,yana tunanin inda zasu sami hotel ,dan su ɗan huta sannan ya sai kaya ya cire wannan na jikin nashi,dan sun matuƙar takura masa. Tambayar drivern yayi nawane kuɗinsa ya faɗa masa ,bashi yayi cikin wanda baffa ya basu da zasu taho, sannan yace wa mai motar dan Allah hotel yake son zuwa . Nan mai motar ya tare musu dan adaidaita yace ya kaisu hotel mafi kusa. Ganin fattu na barci yasa Adeeb bai tashe ta ba kawai ɗauki ta yayi kamar ƴar tsana ya shiga adaidaita ya zauna ,sannan itama ya zaunar da ita.kuma ko buɗe ido batayi ba ,dan barcin sosai ya kamata. Bayan sunje ne ya kama musu ɗaki, sannan ya nufi ɗakin ,har lokacin kuma fattu na rike ahannunsa dan baya don tashi ta daga barci. Da hannu ɗaya yayi amfani wajen bude dakin sannan ya shiga,kwantar da ita yayi akan gadon ya lulluɓawa da ƙarin bargon dake kan gadon,sannan ya ɗan zauna shima yana mai lumshe idonsa ,gaba ɗaya agajiye yake jinsa , dan bai saba irin wannan tafiyar haka ba. Fita yayi ya siyo musu kaya a store ɗin cikin hotel ɗin sannan yayi musu odar abinci ya dawo,fattu nata barci taji laushin gado da katifa ga ƙaton bargo .lol Tashi yayi ya shiga bayi yayi wanka,ya faɗa sosai kafin ya fito,agurguje ya sanya kayan daya siyo ,riga da wando ne na jins da boxers and singlet, sai turare ,sannan yayi sallar asuba. Masha Allah duk da bayani shiri yayi ba ,amma karkuso kuga irin kyan da Adeeb yayi ,sosai ya ƙara zama cikakken Balarabe mai tsananin kyau,sai ƙamshi yake zubawa. Kwankwasa ƙofar dakin akayi, ahankali ya tashi yaje ya buɗe ,abincin da yayi odar ne aka kawo,kaɓar yayi ya dawo ciki. Kallonta yayi yaga bata tashi ba ,dan haka ya zauna yana cin abincinsa.kaɗan yaci ya tashi ,da alama bashi da yawan cin abinci sosai. Gadon da fattu ke kwance ya nufa ,ahankali ya ɗan yaye bargon daya rufa mata,hannunsa yasanya saman goshinta,har lokacin jikinta da zafi sosai. Filin da take kai ya ɗan bubbuga sau uku, ahankali ta buɗe idonta tana mai turo baki ,sai kuma tayi saurin tashi tana ƙarewa ɗakin kallo ,wai aljanar duniya nan ɗin shine gidansu hamma Adeeb ?lallai yan gayune su,ji laushin gado kamar auduga.fattu ta faɗa cikin zuciyarta tana mai ƙarewa dakin kallo. Ji dan Allah yadda take ta wani kallon daki kamar bata taɓa ganin daki ba "Adeeb ya faɗa cikin zuciyarsa yana ɗan kallonta. "Go and get your shower" Adeeb ya faɗa ahankali yana mai kawar da kansa . Kallonsa take ƙuri tana rarraba ido,dan bata fahimci me yake cewa ba. Jin bata tashiba yasa shi dan juyowa yana kallonta. "Ɗan harararta yayi kafin yace " nace kije kiyi wanka ne"ya faɗa fuskarsa aɗaure ba walwala. Tashi fattu tayi sumi-sumi ta nufi hanyar fita ,tana zuwa bakin ƙifar taja ta tsaya tare da juyowa yana kallonsa. Shima kallonta yake cike da jin haushi ko ina zata kuma?nace take tayi wanka. Ganin irin kallon da yake mata ne yasa tace "bazan iya budewa ba"ahankali tayi maganar cikin dasashshiyar muryarta kanta aƙasa. Harararta yayi cike da jin haushin wai yaje bakin ƙofar fita, kuma tana faɗin bazata iya buɗewa,sai kace nan ne toilet ɗin. Tashi yayi ya nufi bakin ƙofar toilet ɗin ya buɗe sannan ya juyo yana kallonta. Shiru tayi itama tana ɗan kallon nasa,dan bata gane nufinsa ba. Wata iska ya furzar mai zafi yana lunshe idonsa,kafin yace "zo kishiga "ya faɗa yana kallonta ,fuskarsa sam ba walwala,shi wllh ya gaji da wannan shirmen nata fa. Kanta adurƙushe tazo ta shige toilet ɗin , kayan daya siyo mata ya ɗauki tare da ɗan kwankwasa toilet ɗin ya buɗe kadan yace "take" Fattu kuwa da tun shigar ta toilet ɗin ta saki baki galala tana kallon ikon Allah,anya kuwa yasan inda ya buɗe mata yace tazo tayi wanka?yo wannan ai Dakin kwanan ne,kalli da harda wani ƙaton gado mai rami,to ma ta a ina zataga ruwan bare har tayi wankan? Juyowa tayi tana kallon farin hannunsa daya miƙo mata leda.ƙarasawa tayi kusa dashi ta karɓi ledar sannan tayi saurin cewa "inane banɗakin? "What " ya faɗa yana mai buɗe kofar gaba ɗaya ,sannan ya kalli fattun ko fara wankan ma batayi ba. Cikin faɗa -faɗa yace "do you expect me to West my time here?Ina jiranki?"ya faɗa yana zaro mata manyan fararen dara-daran idanunsa. Nan da nan jikin fattu ya kama rawa ,tsoro ya kamata ,har kayan hannunsa saida suka faɗi ƙasa" duk da batasan me yake cewa ba ,tabbas ta san faɗane yake mata ,cikin muryar kuka tace"dan Allah hamma kayi haƙuri bansan a inda zabga ruwan ba"ta faɗa tare da fashewa da kuka tana mai toshe bakinta. Shiru yayi yana kallonsa,lokaci guda kuma tausayi ta ya kamashi, sai yanzu ya tuna daga inda ya taho da ita,ba abin mamaki bane idan tace bata san ya zata yi ba.dan haka cikin sanyin murya yace "is ok daina kuka "ya fadi yana mai ƙarara shigowa toilet ɗin. Idan kina son yin wanka nan zaki danna ruwa zai zubo, sannan idan kina biyan buƙata nan zaki zauna ,In kin gama saiki dannan nan ,wannan na wanke bakine and ga soso da soap kin gane "ya faɗa yana kallonta . Kai ta ɗaga masa alamun ta gane , Hanyar waje ya nufa sannan ya juyo yace mata "kiyi sauri yanzu zamu wuce"yana faɗin haka yayi waje. Zama yayi abakin gadon yana mai dafe kansa,ciwo yaji kansa nayi , sakamakon wannan doguwar maganar da yayi, gaskiya kula da yara akwai wahala ,ji yadda tasa masa ciwon kai rana ɗaya kawai. Fattu kuwa bayan ta cire kayanta na gado ,wato rigar fulaninta ƴar dingila da zanin ta ,kai tsaye gurin soso da sabulun nan ta nufa ta ɗauka sanna tazo ta tsaya saitin gurin da akace idan ta danna ruwa zai zo ,dannawa tayi tana jiran taga ta ina ruwan zai zubo,ai ba zato ba tsammani kawai taji ruwa akanta shaaaaaa!!! Wata zabura da fattu tayi tare da watsar da soso da sabulun nan ta kurma uban ihu iya ƙarfinta ta nufi kofar fita ba komai ajikinta "wayyo Allah na hamma wayyo kazo ka buɗe ni na shiga uku dakin yan shan jini ka kawoni ana min ruwan jini akaina wayyo hamma am" abinda fattu ke faɗa kenan cikin rikicewar da tashin hankali gaba ɗaya jikinta rawa yake kamar ɗan mazari. Adeeb na kwance a gefen gado yayi nisa cikin tunani kawai ya biyo ihunta ,ai baisan lokacin daya zabura da mugun sauri yayi toilet ɗin ba,yana zuwa ya buɗe kofar da da sauri ya danna kansa ciki. Kicibis sukayi da fattu abakin ƙofar, tayo gunsa ga gudu tana kuka. Wani irin bugawa ƙirjin Adeeb yayi kansa ya hau juyawa ,sakamakon ganin da yayiwa fattu haka zirr ɗin ta ba kaya.tunda yake arayuwarsa yau ya taɓa ganin mace data fara girma haka ba kaya agabansa. Cikin hanzari ya juya bayansa yana mai dafe ƙirjinsa dake barazanar fashewa."innalillahi "ya faɗa cikin sassarfa lokacin dayaji fattu ta kankameshi tana kuka. "Sosai shima jikinsa ya hau rawa kamar ɗan mazari,cikin rawar murya yake faɗin"le..a...ve. me... Lea....ve... M....e" yana kasa nutsuwa yayi mata magana. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,wannan wace irin masifa ce haka?wane irin gida ya kawota ,za'a cinyeta ya sama. Runtse idanun Adeeb. Yayi da mugun ƙarfi yana ambaton sunan Allah ,ya ɗauki kusan minti biyu cikin halin ruɗewa da rawar jiki.gaba ɗaya jikinsa yayi wani iri,kafin yayi ƙarfin halin sanya hannunsa dake rawa ya fizgota daga bayansa tare da tureta can gefe guda,yana mai sauƙe numfashi cikin sauri ,kawar da kansa yayi daga gareta yana mai cewa"kisa zani ki rufe jikinki Please. Fattu kuwa cikin rawar jiki ta ƙara matsowa gareshi sam tama manta da batun wasu kaya,"dan Allah ka fitar dani daga ,Ni gurin baffana zani "ta faɗa cikin kuka. "Kisa zani nace miki"ya daka mata tsawar data ƙara hargitsata.tsugunnawa tayi tare da ƙanƙame jikinta tana kuka. "Ni ka kaink gurin baffana dan Allah ka maidani gurin baffa "abinda take daɗi kenan cikin kuka da rawar jiki ,gaba ɗaya ta gama tsorata . Zanin nata Adeeb yaje ya yayumo cikin lalube,dan ko gani batayi sosai .yana zuwa ya lulluɓa mata sannan,ya fice daga bayin, da gyar ya iya ƙarasawa kan gadon yana zuwa ya faɗa kan gadon tare da duƙunƙune jikinsa yana rawar sanyi ...... Masu karatu mutara next oage. Ina ganin comments ɗinku masoya ta ko ina ,ina matukar jin daɗi da ƙaunarku ga wannan novel ɗin . Na gode sosai Allah ya bar ƙauna , And I love you guys where ever you are🥰🥰🥰🥰 Anty mammy ce Mrs babi💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 23/24 https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share _________________Kwanci Adeeb yayi akan gadon ,tare da duƙunƙunewa guri ɗaya ,jikinsa kuwa banda rawa ba abinda yake ,idanunsa arufe ruf! Ba abinda yake gani cikin idanunsa face hoton surar fattu. "Ya Salam ! Ya Allah save"Adeeb ya faɗa ahankali yana mai riƙe matarsa data ke masa wani ciwo na lokaci guda. Fattu kuwa tana jin fitarsa da sauri itama ta fito tana kuka.jikin madubi taje ta tsaya tana kallon yadda ya faɗa kan gadon tare da dunƙulewa yana rawar sanyi,cikin ranta take rayawa kodai baida lafiya ne ?ko shima zazzaɓin yake ? Ganin idan ta tsaya zancen zuci saita shekarar agurin,gashi batayi sallaba. Dan haka cikin tsoro da fargaba ta fara takawa zuwa jikin gadon ,tana zuwa taka ta tsaya ,tare da sanya bayan hannunta ta share hawayen daya silalo daga cikin idanunta. Cikin sanyin murya tace "hamma zanyi sallah" ta faɗa kanta a ƙasa. Yana jinta yayi shiru abinsa, yana ci gaba da jin yadda matarsa ke masa ciwo tana ƙullewa,ahankali yake karanta addu'oi cikin ransa ,fatansa kawai ya daina jin wannan azabar da kuma yanayin dake bibiyar ilahirin jikinsa. Kusan minti biyar fattu na tsaye kanta aƙasa ,jifa jifa tana share hawayen dake zubowa daga idanunta.aranta kuwa cewa take "wannan hamma wllh baida kirki ,san ba bakinsu ɗaya da macijina ba,dubi yadda nayi masa magana ya wani shareni. Shikuwa Adeeb yana kwancene yana ci gaba da ambaton sunan Allah,harya samu marar ta kafa masa ,sai wani uban gini dake karo masa agishinsa ,duk da sanyin a.c dake ɗakin hotel ɗin. Ahankali yake sauƙe ajiyar zuciya yana ɗan kumshe idanunsa.kafin ya tashi zaune yana mai dafe da kansa. Ganin ya tashi zaune yasa Fattu ɗan ja da baya,dan ita tsoronsa ma takeji yanzu ,dan wllh da gani masifaffene. Kallon gefen ta yayi ba tare da ya lalle ta kai tsaye ba,sannan ya ɗan ja tsaki yana mai yamutsa fuska da turo baki,kamar wani mace ,sannan ya miƙe ya shiga bayin ,ruwan wanka ya haɗa mata cikin boket dan yasan ba iya shiga kwamin wannan zata yi ba, sannan ya ɗauki sisi da sabulu ta ajiye mata .ya ratsa makilin acikin sabon burush sannan ya ɗan leƙa cikin ɗakin .tana tsaye kamar gunki ,har lokacin share hawaye take ,kumshe ido yayi yana mai cewa, wannan ta cika kuka ,cikin ransa. Kafin ya buɗe baki ahankali yace "zo" ya faɗa kamar baya so.badan Allah yasa Fattu mai saurin ji bace da bazata ji me yace ba. Ahankali take takowa cikin yanayi na tsoro,dan dai tana tsoron masifarsa ne da ba abinda zai sa ta koma wannan ɗakin da ake ruwan jini. Shiga tayi tare da tsayawa tana kallonsa.jikin sink ya matsa tare da miƙa mata burush ɗin yana mai cewa "oya wash your mouth" Shiru fattu tayi tana kallonsa tare da kallon burush ɗin data karɓa daga hannunsa. Kallon ta yayi shima fuska aɗaure yace "wanke baki" ya faɗa cikin ƙosawa ,yana jinjina ƙauyanci irin na fattu wai ko burush bata sani ba. Ita kuwa fattu kallonsa tayi tare da kallon burush ɗin ,cikin ranta tace ikon Allah ,su nan da wannan abun suke wanke baki,mutuwa saidai hawaye da gishiri.ƙara kallonsa tayi suka haɗa ido,da sauri kowa ya kawar da kansa ,cikin shagwabar da fattu batasan tana da ita ba tace "hamma Ni ban iya wanke baki da wannan ba"ta faɗa tana miƙa masa burush ɗin. Wani yarrrrr yaji ajikinsa, saboda salon yadda tayi maganar ,saiyaga kamar da gangan take wani abun.harara ya salla mata kafin ya karɓi burush ɗin yace "open your mouth" Gurun fattu tayi tana kallonsa ba tare da ta buɗe bakin ba. Runtse ido yayi cikin ciwon rai yace da ɗan ƙarfi"haaaaaa"ya faɗa yana bude dan madaidaicin bakinsa. Buɗe nata bakin tayi kamar yadda taga yayi, wanda yake nan ɗan mitsitsi kamar gidan tsutsa ,haƙora ta farare tass dasu,ajere reras. "Masha Allah "Adeeb ya faɗa cikin rashin sanin ya furta hakan. Saida ya faɗa kafin ya ankare.kallon fattu yayi suka haɗa ido,harara ya watsa mata yana mai cewa"kaki cinyeni da wannan lulu eyes ɗin naki"Adeeb ya faɗa yana mai sanya burush ɗin cikin bakin fattu. Ahankali yake wanke mata haƙoran nata masu kyau da ɗaukar hankali,yana wanke wa yana kallon fuskarta,ita kuwa ta rufe idanunta ƙam!wani irin takeji bakin nata,gashi abun da shegen zaƙi, anya kuwa ba abin sha bane ya manta yace na wanke baki ne? Aikuwa wllh saita ɗan sha taji ya faɗinsa yake.Adeeb bai sankara ba kawai yaga ta tattara kumar bakinta ta haɗeye ƙut! Zaro ido yayi tare da buɗe baki cike da mamaki yace "what!!" Kin shanye kunfar?oh my God" ya faɗa yana zare burush ɗin daga bakinta. Yace "oya fito dashi"ya faɗa yana zare mata idanu. Shagwabar fuska fattu tayi kafin tace "ai na shanye zaƙi gareshi" ta faɗa tana mai sunkuyar da kanta. Girgiza kai kawai Adeeb yayi,baice komai ba ya kunna fanfo yace ta tara ta kuskure bakin, Hannu ta saka ta tari ruwan sannan ta kuskure bakinta.wani fayau taji bakin nata yayi ,sosai taji yayi mata daɗi ga kamshin strowberry da bakin keyi. Nuna mata ruwan wanka yayi yace tayi wanka ,yanzu ta fito yana jiranta. Kai ta daga masa,tana nufar gurin da boket ɗin yake ajiye. Harya kama handle ɗin kofar sai kuma ya juyo yace "kiyi alwala anan"ya faɗa yana nuna mata jikin sink din tare da ficewa. Zama yayi abakin gado bayan fito daga toilet ɗin ,haka kawai yaji yana cikin farin ciki,sai murmushin yake,abinda ba al'adar shi bace yawan fara'a. Fattu kuwa ko minti biyar batayi ba ,sai gata ta fito sanye da Kayan ta data cire . Kallon ta Adeeb yayi yace " ina kayan dana baki?" Miƙa masa al'adar tayi tana mai cewa"bazan iya sawa ba harɗe Ni zasu yi" Kallon ledar yayi sannan ya lalle ta, karba yayi tare da budewa ya zazzage,doguwar rigar baƙa mai dan faɗi sai ɗan kwalin rigar shima baki,kuma yana da girma.wai amma sune bazata iya sawa ba ' "Take it ,ya faɗa cikin hade fuska. Kallonsa tayi, tare da karɓar ledar,bawai dan ta ji me yace ba ,saidan taga yana miƙa mata ledar . "Wuce kije kisa"ya faɗa ba alamun wasa afuskarsa. Juyawa tayi sumi"sumi ta koma toilet ɗin ,amma bata rufe ƙofarba ,ta yadda dataji burum,zata arce. Haka ta cire kayanta ta sanya wanna doguwar rigar ,masha Allah rigar tayi mata kyau sosai ,saita fito ras da ita.maimaiko ta lulluɓa dan kwalin ,sai kawai ta daura akanta.,sannan ta sanya kayanta wanda ta cire cikin ledar sabon kayan. Fitowa tayi tana tattare rigar ,dan harga Allah jinta take aharharde,tafi don tsangalallen ,zaninta. Tana fitowa Adeeb yabi ta da kallon,aransa yana mai yaba irin Khan da tayi ,amma jibi yadda yake wani dage rigar. "Hamma a ina zanyi sallar?ta faɗa tana kallon gefensa. Shiru yayi yana kallon ta kafin yace "zo nan" Cikin tsoro take takowa har zuwa kusa dashi,tana fatan kar yayi mata faɗa irin na ɗazu. Mikewa yayi tare da zare ɗan kwalin kanta,ya warware shi tare da yi mata rolling irin yadda yaga amminsa da ƙannansa nayi. Masha Allah ai nan danna fattu ta fito abalarabiya sak, tayi kyau sosai da sosai,kamar ba fattu yar fillo ba. "Kije can kiyi sallah"ya faɗa yana nuna mata kan dardumar da yayi Sallah shima. Bayan ta idar da sallar Adeeb yana kallon ta,masha Allah ba wani kuskure cikin sallar Tata,dan fattu tana da ilimin addini sosai. Abinci ya nuna mata yace tayi sauri taci zasu tafi.bata wani ciabincin kirki ba,dan ji tayi sam abincin baiyi mata daɗi ba,tafi son tuwo ko madarar shanu. Shima bai wani damu ba ,dan yaga bataci abinci ba sosai.tashi yayi yace mata suje . Yayi gaba tana binsa abaya. Riƙe da rigarta, hannun dayan kuma tana riƙe da ledar kayanta. Suna fita daga hotel ɗin kai tsaye gurin masu saida waya ya nufa , wata ƙaramar waya ya siya da layi,ba tare da ya tambayi kuɗi su ba ,naga ya bada duka kuɗin nan dake cikin leda,dan dama suna hannunsa,wanan rigar kawai ya cire daga ledar,sosai naga mai saida wayoyin yana ta murna da godiya har kasa ya durƙusa yana godiya. Haɗa wayar Adeeb yayi tare da sanya layin ,kati ya karɓa gurin mai saida wayar ,aikuwa da sauri ya ɗauki mata na dari biyar ya mika masa. Wata number naga ya daddana cikin wayar,bayan ya gama sanya katin acikin wayar. Magana ya farayi cikin harshen larabci,bayan anɗaga wayar daya kira.ni dai ba dan me yake cewa a,saidai naga kamar yana kwatancen inda yake ne. Bayan ya kammala wayar ne yana ƙoƙarin sanyata cikin Aljihu,kawai yaji mutum yana ƙwaƙwumarsa kamar za'a shige cikin jikinsa. Da sauri ya kalli gefen hagunsa ,inda tanan yake jin alamun mutum ɗin,aikuwa fattu ya gani tsaye ta kama gefen rigarsa,jikinsa har rawa yake tana ɓoye fuskarta ajikinsa. Hannunsa ya sanya tare da kamo hannunta ya dawo da ita zuwa gabansa. Saida ya ɗan harareta kafin yace "menene kuma"ya faɗa cikin salon maganarsa kamar baya so. Ahankali fattu ta nuna masa wasu matasa kusan su goma da suka tsaya suna kallonsu.tace "waɗan can ne ke kallona "kallon gurin matasan yayi,yaga yadda suka kafesu da idanu,kuma ba akowa suke kallo ba face fattu,nan da nan yaji wani irin ɓaci rai da ciwon zuciya ya turnuƙeshi, Cikin hanzari ya maida fattu bayansa yana mai hararar matasan nan,zuciyarsa kamar zata fito dan tsabar ɓaci rai.gaba ɗaya yaji gurin yayi masa baƙi kirin,Bama yason tsayuwa agurin, dan haka cikin zafin nama ya fizgi hannun fattu suka fara tafiya daga gurin,mai saida wayoyin yana ta masa godiya da Allah ya kiyaye amma ko sauraransa baiyi ba. Can wani guri ya koma tare da tsayawa ,shi kaɗai dai huci yake,dan me zasu tsaya suna kallon ta ,shifa saiyaga kamar ma ɗaya ƙirjin fattu yake kallo. Cikin sauri ya juyo tare da kallon fattu tun daga sama har ƙasa.ba wani abu daya bayyana ajikinta ,wanda za'ace shigarta batayi daidai ba ,saidai fa idan ka ƙura mata ido zaka iya gane ba bra ajikinta. Lallai ke nan bata sanya bra ajikinta? "Ke meyasa baki saka wannan abun ba kafin kisa rigarnan" Ya faɗa cikin fushi da bakin rai. Kallonsa fattu tayi cikin rashin fahimta dan bata gane me yake nufi ba,kawai saita sunkuyar da kanta ƙasa tace "kayi haƙuri Ni banga komaiba inda rigar ba"ta faɗa Muryar har ta fara rawa,alamun zata yi kuka. Harya buɗe baki zaiyi magana yaji wayarsa na ringing,tsaki yayi kafin ya ɗaya call ɗin. Shiru yayi na tsawon lokaci kafin yace "Yes i sawa them"ya kashe wayar . Dan fitowa yayi daga gurin dasuke tsayen naga ya ɗaga hannunsa . Wata tsuleliyar mota naga ta taho gareshi,suuuuuu,baka ko jin ƙagarta,kallon ɗaya zakayiwa motar kasan anɓadda Naira agurin,farking motar tayi agabansa,kafin mai riƙon ya fito cikin sauri yana mai faɗin "your highly well come back sir"mutumin ya faɗa yana mai durƙusawa har kasa gaban Abeed. Kafadar mutumin Abeed ya dafa tare da miƙar dashi tsaye,sannan ya ɗan rungumeshi yana mai bubbuga bayansa. "Let go hisham"Abeed ya faɗa yana mai nufar motar ,da sauri wanda aka kira da Hisham ya budewa Adeeb motar ,shikuma ya shiga gidan baya ya zauna. "Hamma " fattu ta faɗa cikin sauri tana mai ƙarasowa jikin motar ganin ya shige cikin motar yana ƙoƙarin barcinta. Adeeb kuwa da gangan yayi banza da ita ,intaga dama ta ƙara so ta shiga motar,dan haushinta ya keji sosai ,ai da gangan ta wani tsaya har wasu ba zaune ke ƙare mata kallo. Hisham ne ya kalli fattu yace "yan mata lafiya kuwa? Shagwabe fuska fattu tayi tana kallon Adeeb tace "gurin hamma zani gashinan acikin nan"ta faɗa tana nuna mai Adeeb ,wanda ya wani ɗauke kai . "Yallaɓai this ... "Let her in"Adeeb ya faɗa cikin katse Hisham . "Yes sir"Hisham ya faɗa cikin bin umarni,ya kauce daga bakin ƙofar motar yana mai cewa fattu"shiga" Da saurinta kuwa ta shige kusa da Adeeb ta zauna ,harda sauƙe ajiyar zuciya. Ahankali ta sanya hannunta tare da riƙe gefen rigar Adeeb ta kalle- kallen motar.banda faɗuwa ba abinda gabanta keyi. "Yallaɓai where are we going now" Hisham ya tambaya cikin girmamawa. "Abuja" Adeeb ya faɗa tare da kwantar da kansa jikin kujera ,ac na ratsa shi ta ko ina. Nan Hisham ya kunna mota suka cilla sai Abuja. Ko daga Abuja kuma sai ina ? Ga dai Hajiya fattu cikin mota mai a.c ana baza idanu. Muje zuwa ku biyoni sannu kan hankali. Domin samun wannan littafin daga farko sai ku danna bulun dake kasa 👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.aihausanovels.com.ng/2022/07/macijine-shi-page-5-6-hausa-novel.html Anty mammy ce Mrs babi💘💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MICIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 25/26 https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share ________________Tafiya suke cikin motar Ba tare da kowa ya ƙara cewa komai ba,ba abinda ke tashi cikin motar dai sanyi a.c da daddaɗan kamshi, gefe guda kuma ƙira'ar sudais ke tashi cikin suratul mulk. Gaba daya zuciyoyinsu,sun sami nutsuwa,irin wacce mai sauraron Alƙur'ani ke samun tago mashi da ita. Adeeb yana kwance cikin kujerar, idanunsa alumshe ,ahankali yake ɗan motsa bakinsa yana bin ƙira'ar,al'adar sa kenan dama shi,inda yana cikin mota ,to karatun alƙur'ani yake sauraro. Yayin da can ƙarƙashin zuciyarsa yake jin wani irin farin ciki da annashuwa,duk da baisan tsawon lokacin daya ɗauka cikin yanayi na wata halittar ba,amma yana ji ajikinsa cewa yayi kewar ahalinsa fiye da yadda yake tunani.ba abinda yake fata da buri irin ace yaganshi kusa da abie da ammi.ko wane yanayi zasu shiga idan suka ganshi? Tunanin da Adeeb yayi tayi kenan cikin zuciyarsa.hakan ya hana masa fahimtar halin da fattu ke ciki.wato ta takure jikinsa sosai,sai rawar sanyi takeyi, sosai sanyin motar ke damunta, ga wani irin yanayi na kewar baffanta dake taso mata, sosai ta ƙunaci Jikin Adeeb ,aƙoƙarinta na samun gurin da dataji ɗumi. Ahankali ta ɗan zakuɗa kadan zuwa jikinsa,ta yadda har kafaɗarta na gugar tasa.kuma har zuwa wannan lokacin tana riƙe da gefen rigarsa. Shikuwa Adeeb jin anɗan bugeshi ,yasa shi buɗe idanunsa ahankali, ɗan juyowa yayi yana kallon fattu, wacce tayi lugus ajikinsa tana karkarwa. "Ke matsa daga jikina"ya faɗa cikin salon maganarsa ba tare da ya motsaba. Da sauri fattu ta ɗan matsa ,daga jikin nashi,dan ita atunaninta dama yayi barcine. Kallonsa tayi tare da marairaicewa tace "Hamma sanyi nake ji,kodai cikin ƙanƙara muke tafiya"ta faɗa zuciyarta ɗaya,tana ɗan gwabe fuska. Kallonta yayi tare da harararta yace "dake baki san acikin ƙanƙara muke tafiyaba?ya faɗa cikin gatse. Zato ido fattu tayi tare da dafe ƙirji,"na shiga ukuna Ni fattu ,dan Allah Hamma kayi min rai,mu canja wata hanyar wllh mutuwa zanyi idan naci gaba da jin sanyin nan"fattu ta faɗa cikin marairaita tana rawar sanyi,gaba ɗaya ta gama tsorata,idanunsa kuwa harya fara kawo ruwa. Bamza Adeeb yayi da ita tare da maida idonsa ya rufe,wannan gaskiya ɓaci ƙauyencima akwai shirye atattare da ita,kamar ba tare suka shiga motar ba, ko ina taga alamun ƙanƙarama bare tace akanta suke tafiya? Fattu kuwa ganin ya maida idanunsa ya rufe sai tsoro ya ƙara makata,da sauri ta cusa kanta tsakanin hannunsa da kujera, ta kara ƙanƙame gefen rigarsa tana kuka. "Wayyo Hamma sanyi nakeji yana shiga cikin ƙashina ,jinina daskarewa yake" fattu ta faɗa cikin kuka,tsakaninta da Allah take kukanta. Dafe kai Adeeb yayi tare da kallon Hisham yace "switch up that a.c" ya faɗa kamar baya so. "Ok sir" Hisham ya amsa tare da kashe a.cn yana mamaki,yau yallaɓai ne da kansa yace akashe a.c? Fattu kuwa ahankali taji ta daina jin sanyi da take ji,dan haka share hawayenta tayi tana mai cewa aranta."anya kuwa Hamma ba so yake ya kaini gurin yan shan jini su tsotsemin jini ba? Ahankali ta dago kanta tana kallon fuskarsa ,shagala fattu tayi da kallon kyakyakywar fuskarsa ,barin ma light pink lips ɗinsa da gashin baki yayi masa ƙawayan,ga gemunsa mai kyau sai sheƙi yake,hanci kuwa kamar wanda aka ɗora masa,gaskiya Hamma akwai kyau ,inama nike da kyansa,aikuwa danasha gayu. "Ke meye kika ƙuramin ido haka?karki cinyeni" Adeeb ya faɗa yana mai tsare fattu da idanunsa masu tsananin haske. Dan duk yadda ta ƙuresa da ido yana kallonta ,dan ba duka ya rufe idon nashi ba . Ɗan zabura fattu tayi ta matsa baya tana soso kai,dan ba ƙaramin kunya taji ba,ashe yana kallonta ta ƙuresa da ido haka? wayyo Allah Ni fattu .ta faɗa cikin ranta tana mai kwantar da kanta jikin kujera cikin kunya. Tun daga lokacin ba wanda ya ƙarayin magana a cikinsu. Adeeb yana cikin tunaninsa yaji fattu ta langaɓo kansa,dan dubawa yayi saiyaga ashe ma barci tayi.kafeta yayi da idanuwansa yana kallon zallar kyau irin na fattu,duk da ƙarancin shekarunta ,amma Allah yayi mata baiwar kyau,irin kyanda sai kana kallon mutum kake ƙara ganin kyan nashi . Gyara mata kwanciyar yayi agefen kafaɗarsa ,duk da yadda yake jinsa atakure,kasancewar kusancinsu yayi yawa ,amma haka ya daure ya barta akan kafaɗar tashi taci gaba da barcinta. Fattu na cikin barci taji ana dan taffing kumatunta, Ahankali ta buɗe idanunta da sukayi mata nauyi saboda barci. "Dagani malam duk cin batani da yawun barci ko" Adeeb ya faɗa yana hararar fattu Wacce ke kif-kifta idanunta tana mai daga masa kafaɗa,kallon kafaɗar tashi tayi,amma ita bata wani ga yawu agurin ba. Suna fita daga Motar fattu ta gansu kusa da wani ƙaton jet ,Aida sauri ta kamo hannun Adeeb ta rike ƙam cikin nata tana mai zaro ido. Fizge hannunsa Adeeb yayi yana hararar fattu "stop touching please" ya faɗa yanayin gaba binsa. Da sauri fattu ta mara masa baya,tana binsa ƙafa ƙafa.tab yaushe zata tsaya kusa da wannan abu mai kama da girman duniya?haka kawai ya fado kanta ta mutu ? Wani farin Balarabe ne ya fito daga cikin wata ƙofa,dake ɗan nesa da inda jet ɗin ke tsaye. Da gudu naga ya taho ya ruƙunƙume Adeeb yana sunbatarsa,kuma yana hawaye. "Habeebi ina ka shiga ?me yasameka?kasan irin tashin hankalin da muka shiga?kowa na gida yana cikin damuwa,abie yana nan akwance ba lafiya tunda aka rasaka"Balarabe ya faɗa cikin harshen larabci. Murmushi kawai Adeeb yayi yana mai shafa kan wannan balaraben ,sannan yace " where is the imam? Cikin share hawaye mutum yace "yana ciki kai kawai muke jira. Kallon fattu Adeeb yayi yace "jirani ana karki biyoni" ya faɗa cikin hade fuska.kafin yayi gaba. Da sauri fattu ta kamo hannunsa cikin marairaita tace "tsoro nakeji Hamma dan Allah karka gudu ka barni"ta faɗa cikin kwabe fuska. Zare hannunsa kawai yayi baice komai ba suka shige cikin dakin da wanann balaraben ya fito. Zama fattu tayi akan wata kujera dake gefen ta,da alama kujerar sassaƙata akayi dan zama agurin,tagumi tayi rungume da yan kayanta,tunani take yanzu idan Adeeb ya gudu ya barta anan yazatayi? Gurin wa zata?dan ita dai yadda take ganin garin nan da zungura- zunguran gidajen dake cikin garin ,zaiyo wahala idan ba shan jini akeyicikin gidajen ba.shikenan ba ita ba ƙara ganin baffanta. Daga kanta tayi ta kalli inda aka daka motar da suka zo cikinta amma watan bataga motar ba,saidai taga wasu tarin motocin can gefe guda arufe da wani abu. Ƙila duk waɗanda aka kawo su cikin motocin can an shanye musu jininsu.yanzu itama haka za'a shanye nata jinin idan Hamma ya gudu?"wayyo ni fattu naga rayuwa "ta faɗa tana mai leave fuska da waige waige . Shikuwa Adeeb koda suka shiga ƙofar nan, Kusan minti talatin suka ɗauka cikin dakin kafin suka fito, ,lokacin fattu hatta fara kuka, tana ganinsa taji wani sanyi cikin ranta,da hanzarin ta ta miƙa tare da nufarsa tana kuka,tana zuwa ta kama hannunsa cikin kuka take cewa"Hamma harba fara kuka ,nayi tunanin gudawa kayi ka barni, anan ado a shanye min jinina, dan Allah Hamma karka ƙara tafiya ka barni" fattu ta faɗa tana mai ɗora kanta akan damtsen hannunsa. Wani irin yanayi na tausayinsa Adeeb yaji yana ratsa zuciyarsa,Allah Sarki,yasan ahalin yanzu bata da wani gata saina Allah saikuma shi,shi kaɗai ta sani,zaiyo iyakar ƙoƙarin sa ,wajen kula da ita har su cimma burin su. hannunta kawai Adeeb ya kama , tare da nufar cikin jirgin nan. Noƙewa fattu ta farayi cikin rawar jiki tace"Hamma na tuba Dan Allah karka sani cikin wannan abun mai kama da kifi" fattu ta faɗa tana mai ƙoƙarin zare hannunta daga cikin nashi. Tsayawa yayi tare da kallon wannan balaraben yace tareeƙ ka shiga ciki "ya faɗa cikin harshen larabci. Jinjina kai tareeƙ yayi tare da kama ɗayan hannun Adeeb ya sunbata kafin ya shige cikin jet ɗin. Kallonta Adeeb yayi yaga yadda gaba ɗaya ta firgice,sai ƙoƙarin zame hannunta take cikin nashi. Ahankali ya sanya hannunsa ya kawota jikinsa,yayi mata side hug,kana yace " ki nutsu kinji,ba abinda zai miki zamu tafi gidane acikinsa" ya faɗa yana mai shafa kanta. Jinjina kai fattu tayi tare da cewa"Ni bazan bikaba Hamma kamaida Ni gurin baffa ,bazan shiga wannan abunba tsoro nakeji,kifine da,muna shiga haɗiyemu zaiyi Hamma"ta kai ƙarshen maganarta cikin kuka. Murmushin Adeeb yayi akaro na farko tun tasowarsu daga Kano,wai haɗiyesu zaiyi ,kifine.kai wannan yarinyar akwai ƙauyanci. Ganin dai da gaske fattu atsorace take, sai kawai ya juyo da ita zuwa gabansa ,bai jira komai ba ya haɗar da jikinsa ya rungumeta cikin faffaɗan ƙirjinsa,ahankali yake shafa kanta zuwa kafadunta . Shiru fattu tayi sakamakon wani irin nutsuwa mai cike da sa annashuwa dataji tana ratsa dukkan sassan jikinta,luɓ tayi cikin jikinsa ta daina wannan rawar jikin,idanunta kawai ta kumshe tana shaƙar daddaɗan kamshi da Adeeb keyi. Kusan minti uku Adeeb ya bata ajikinsa,yayinda shima yake jinsa cikin wani irin yanayi na samun nutsuwa da peace of mine ,ji yake kamar suyi ta zama ahakan, amma tunowa da yayi da abinda ke gabansa yasashi saurin ɗagota daga jikin nashi,ƙara komawa fattu tayi ta kwantar da kanta akan ƙirjinsa,ba tare da tasan tayi hakan ba,.cibiya ya karatu kafin yace "to dagamin jiki karki karyani"ya faɗa daidai saitin kunne ta. Wani yuuuuuuu fattu taji ,jiri na neman dibanta, lokacin da iskar bakin Adeeb ta bugi kunnenta,da sauri ta rike damtsensa tana mai runtse idanunta,saida suka sake ɗiban minti kusan biyu,kafin Adeeb ya ɗagota,wanna karon bayi musu ba,saidai kanta na ƙasa cikin jin kunya. "Ya isheki haka ko kina don daɗi?"Adeeb ya faɗa yana kallon fuskarta. Shiru tayi kanta a ƙasa ba tace komai ba. Hannunta Adeeb ya kama suka fara taka matakalar. Taku ɗaya biyu kawai fattu tayi luuuuuu zata daɗi ƙasa ,da sauri cikin azama Adeeb ya ruƙota ,yana mai zato idanu waje. Fattu kuwa ji tayi kanta yana juyawa sosai,tace "Hamma ka rikeni zan faɗi "ta faɗa tana mai kumshe idanunta. "Ina tare dake ba abinda zai sameki"Adeeb ya faɗa ,yana mai ɗaya fattu kamar ya ɗauki jaririya ya shige cikin jet din. Wow wato shi kansa cikin jet ɗin abin kallo e ,tsayawa fasalta yadda ya tsaru kuma bata lokacine,na barku kawai ku ƙiyasta tsaruwar jet ɗin. Sin yanufa ya zauna tare da rungume fattu cikin jikinsa,yana shafa kanta ahankali. Belt ya ɗaura musu kafin ya ɗanan wani ɗan guri saiga kujerar ta mike ,yadda mutum zai iya kwanciya akai. Wata har danja ya latsa ,nan danan mai tuƙin wato tareeƙ ya tada jirgin sukayi kula sukayi sama. Ƙara gyarawa fattu kwanciya Adeeb yayi ajikinsa yana mai kallon fuskarta dake cike da tsoro,idanunta arufe gam, da hannunta shima ta rukunkume Adeeb dasu, idanunta kuma na tsiyayar da ruwan hawaye . Ahankali Adeeb ya sanya hannunsa yana mai share mata hawayen bakinsa ya kai daidai goshinta kamar zaiyi mata kiss saikuma yayi saurin dauke kansa . Ajiyar zuciya Adeeb yayi yana mai kallon sararin samaniya cike da jin wani irin shauƙi cikin zuciyarsa Manage please my people, Banda caji wllh nefa ya sami matsala. DOMIN SAMUN COMPLETE NOVEL DIN KU TABA BULUN RUBUTUN DAKE KASA 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 https://www.aihausanovels.com.ng/2022/07/macijine-shi-page-23-24-hausa-novel.html Mrs babi ce💘💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy Elegant online writers📚📚 Free book Page 27/28 ________________Tafiya suke cikin sararin samani,yayin da Fattu ke ruƙunkume da Adeeb jikinta naci gaba da rawa,kuma har lokacin idanunta akulle suke. Ɗan juyowa Adeeb yayi yana mai kallonta ,shi mamakin tsoro irin na fattu yake,sam baiga abun tsoro ahawa jirgi ba,dubi yadda ta wani uzzurawa kanta,ko idanu ta kasa buɗe wa. Ni kuwa nace malam Adeeb fattu fa ko ganin jirgi baya taɓa yi ba ,bare ta hau,ai dole ta shiga cikin cakwakiya,akaranta na farko. Kallon fuskarta Adeeb keyi kamar bai taɓa ganin taba,haka kawai yake jin wani bakon al'amari tare dashi, jin yadda fattu ta ruƙunƙumeshin nan ,sai yake jin hakan yayi masa daɗi sosai,saidai yana tsoron abinda zuciya da gangar jikin sa ke ɓuƙatar aikatawa,idanu ya kirawo lips ɗinta ƙuri,cikin wani irin mugun son ya sunbacesu,gabansa sai bugawa yake,har wani lasar lips ɗin da yake ,yana hasko yadda zai sunbaci lips ɗin fattun.iyakar ƙokari Adeeb yayi dan hana kansa aikata abinda zuciyarsa ke tsananin muradi, amma ya kasa,dan jinsa yayi gaba ɗaya yanayinsa ya sauya ,ahankali cikin mugun son isar da saƙon zuciyarsa ya nufi ɗan bakin na fattu, har wani rawa bakinsa keyi, Yana gan da kai bakin nasa cikin nata ne ,fattu tayi waral!da idanunta,ma'ana ta buɗe idanun nata ba zato ba tsammani,karaf kuwa idanunsa ya sarƙe dana juna,da sauri Adeeb ya runtse idanunsa tare da kawar da kansa can gefe,saidai bai daga daga rankwafowar da yayi ba,jikinsa gaba daya yana manne dana fattun,wani irin abu yakeji mai kama da mayen karfe ,yana fusgarsa zuwa ga aiwatar da burinsa, kiss fa only kiss Adeeb you can do it ,dan ka samawa kanka mafita daga yanayin da kake ciki. Zuciyar Adeeb ke bashi wannan shawarar,ahankali ya ƙara bude idanunsa wanda suka fara sauya yanayi daga fari tas zuwa wani irin sirkin jaaa da wani ratsin pink. Kallon fattu yayi wacce itama shi take kallo tana wani rarraba idanu,Ita dai batasan me yake nufi ba,taga ya kwanto jikinta ne ,ƙila ahaka ake tafiyar ,amma kuma me yasami idanunsa haka,idan bata mantaba ,yanayin da idanunsa ya shiga yanzu,kusan kalar da idanunsa yake ne lokacin da yake macijinsa, kodai macijin zai ƙara zama ne?na shiga uku na idan yazama maciji yanzu yazanyi?ina zamuje cikin wannan halittar mai kama da kifi?nan da nan tsoro ya kama fattu ƙara rikoshi tayi sosai cikin muryar tsoro tace "Hamma menene?dan Allah karka ƙara zama maciji kai kadai nake dashi,idan ka koma maciji ya zanyi,waye zai fitar dani daga wannan cikin kifin da muka shi?ta faɗa cikin salon shagwaɓa taba mai zubda hawaye. Da ƙarfin gaske Adeeb ya runtse idanunsa, yana mai furta "ya Salam wannan yarinyar zata kashe ni fa"dan yanayin yadda tayi maganar ba ƙaramin tasiri yayi akan Adeeb ba,hakan saiya ƙara masa jin wani iri ajikinsa,gani yake kamar da gangan tayi hakan ma. Kansa banda juyawa ba abinda yake,yayinda zuciyarsa ke ta bashi shawarar kawai ya sunbaci fattun .cikin rashin sanin abinyi Adeeb ya ɗora bakinsa kan na fattu,ba tare da ɓata lokaciba ya fara kissing ɗinta kamar ya sami lolli pop,zaro idanu fattu tayi cike da tsantsar tsoro da mamaki,meye hakan kuma Hamma keyi?me yasa yake shan bakina?kodai shima yana cinye mutane ne?shikenan Ni fattu naga ta kaina ,wayyo Allah na,daga cikin fiki saikuma shanye baki?nan da nan fattu ta fara rawar jiki fiye da da,cikin zuciyarta tana take ta faman haure haure da ƙoƙarin ture Adeeb,amma kuma azahiri ta kasa koda ɗaga dan yatsanta ne bare tayi yunƙurin kwacewa. Shikuwa Adeeb ɗora bakinsa kan bakin fattu keda wuya ,gaba ɗaya haddarsa ta zube,tuni ya nemi inda kansa yake ya rasa,kissing ɗin bakin fattu kawai yake kamar Mayunwacin zaki. Kusan minti shida zuwa bakwai Adeeb na abu ɗaya,cikin kwancewar kai da rasa tunani,fattu kuwa tun tana jin abinda yakeyi kamar waiwayi yake mata har ta fara jin wani azababben zafi da raɗaɗi ,dan ji tayi kamar zai tsinke mata lips,tuni ta fara kuka tana ɗan bubbuga damtsen hannunsa. Hankali da tunanin Adeeb ne suka dawo jikinsa lokaci ɗaya,kuma ya fahimci abinda yake aikatawa da Fattun, cikin wata irin azama da hanzari ya dago kansa tare da cire bakinsa daga cikin na fattun. Da sauri ya zareta daga jikinsa yana mai mikewa cikin hanzari ya nufi wani daki,yana layi kamar ɗan maye. Yana shiga ɗakin ya kulle ƙofar tare da zamewa ajikin ƙofar ya zauna dabas. Dafe kansa yayi yana mai runtse idanunsa."meye hakan ?me na aikata kenan?wane irin kallo yarinyar zata rinƙa min yanzu?ohh my God ,why Adeeb !why am I losing my control over her?"Adeeb ya faɗa Afili yana mai tsakumo sukar kansa wacce ke kwance lub-lub. "Me ka aikata ba dai-dai ba Adeeb bakayi laifin komai ba ,kuma ba abin ƙi kayi ba just colm down"wani sashe na zuciyar Adeeb ne ke sanar dashi wannan maganar cikin yanayin rarrashi. Ahankali ya sauƙe wata ƙaƙkarfar ajiyar zuciya yana mai rarrafawa ya kwanta akan wani ƙayataccen gado dake cikin ɗakin.kwanciyar rigingine yayi tare da kumshe idanunsa.ba abinda ke masa gizo sai moment ɗin daya kasance cikinsa yanzu nan.tabbas bai taɓa jinsa cikin wata ni'imtacciyar rayuwa makaman iyar wadda ya fito daga cikinta ba yanzu,wannan yarinyar da yake mata kallon baby he can't imagine ace wai just kissing ɗin ta zai sanya shi cikin wannan yanayin ba. Kusan minti goma Adeeb ya ɗauka a kwance yana ta saƙa da warwara,gaba ɗaya ya kawowa kansa matsala,yana zaman zamansa ,yanzu inbanda amsawa ba abinda mararsa keyi. Tsaki yayi akaro na barkatai kafin ya mike cikin ƙarfin hali ya buɗe wata ƙofa ya shiga, wanka yayi ya tsarkake jikinsa kafin ya fito sanye da wata jallabiya, danaga ya buɗe wani guri ya zarota. Zama yayi abakin gadon daya kwanta dazu,yana tunani,me Yakamata yayi yanzu? Gara kawai ya fuske ya fita,idan ba haka ba yarinyar zata rinka masa wani iri. Kallo ne.dan haka mikewa yayi tare da ɗaure fuskarsa sosai kafin ya fito daga ɗakin. Fattu kuwa lokacin da Adeeb ya zareta daga jikinsa ,zama tayi atsorace kan kujerar jirgin tare da ƙanƙame jikinta,wani irin abu yakeji ajikin nata wanda bata san menene ba,gefe guda kuma lips ɗin ta dataji yana mata zugi,hannu ta kai tare da taɓa lips ɗin ta ,aikuwa jinsa tayi yayi tauri gurin,alamun ya kumbura kenan. Hannu ta sanya tare da share hawaye ta ,sannan ta kira kanta akan cinyarta tana kuka. Ita sam batasan meye hakan da Hamma yayi mata ke nufi ba,kuma gaba ɗaya jikinta yayi wani irin ,sam bata jin ƙarfi ajikinta,gashi har lokaci ji take kamar bakin Hamma nata yana cikin nata bakin.tana cikin wannan halin ne taji buɗe kofarsa . Firgigit tayi tare da zabura tana kallon inda taji ƙarar.haɗa ido sukayi da Hamma nata kallonsa take ƙuri ,ganin har kaya ma ya canja ,ko a ina ya sami kayan oho" Shikuwa Adeeb ganin sun haɗa idanu ya wani galla mata harara yana nufar kujerar dake dayan bangaren. Binsa da kallo fattu tayi tana mai son zuwa inda yake , amma tana tsoron yadda taga ya haɗe fuska. Ɗan juyowa Adeeb yayi jin cewar idanun fattu na kansa. Harara ya ƙara zabga mata cikin basarwa yace " karki cinyeni da ido fa,bayan kin gama cinyemin baki"ya faɗa yana saurin kawar da kansa,dan shi kansa saida yaji kunyar abinda ya faɗa.tunda yasan shine marar gaskiya . Fattu kuwa shiru tayi tana tunani,yaushe ta cinye masa bakin?kodai hankalin mutum yana gushewane idan yana cikin wannan abun,har yayi abu bai sani ba.dago kai tayi tana mai kallon Adeeb kafin cikin muryar mamaki tace "Hamma to meyasa na cinye maka bakin?kuma amma ai naga ga bakinka anan ajikinka, saidai ma ni nawa bakin dake min zafi " fattu ta faɗa cike da mamaki. Dariya ce taso kama Adeeb amma ya manne sannan ya kalleta yace" inaga kina da aljanu ko?haka kawai ki ka kama shamin baki kamar kin Sami sweet , shine zakice min bakinki na miki ciwo? "Na shiga ukuna Ni fattu Wllh Hamma bansan nayi ba ,nima kawai ganinki nayi kana shamin bakina kagani nan gurin ma ya kumbura ciwo yakemin"fattu ta faɗa tana ɗan turo kanta tare da nuna masa lips ɗinta na ƙasa wanda ya tasa. Kallon lips ɗin Adeeb yayi cike da jinjinawa wauta irinta fattu,sam bata da wayo ko kaɗan,kafin yace "maganinki ai garin don banzarki kika kuwa kanki ciwo ,Ni ba ruwana, kuma saikin faɗamin inda kika koyi wannan abunda kikayimin"Adeeb ya faɗa yana hararar fattu. Allah Sarki fattu kuwa tuni idanunta sun kawo ruwa,marairaicewa tayi tana mai juya kai,"Ayya Hamma nisa ba mayya ba ina zanyi wannan aikin mayyun,wllh bansan nayi maka ba dan Allah kayi haƙuri,nima bansan menene hakan yake nufi ba,amma idan kaji haushi ka rama kawai"fattu ta faɗa tana mai shashsheƙar kuka tare da goge wahaye,tsakani da Allah ita ina tasan ma tayi masa wannan abun,ita ba mayyaba ba komai ba ina ita ina shan bakin wani,ai ƙazantane ma wannan. Lallai ma yarinyar nan wato shine maye kenan ?hmmmm zakiyi bayanin maye.Adeeb ya faɗa cikin ransa yana mai jingina kansa da jikin kujera,dan sosai yaji kansa na ciwo wanan doguwar maganar da yayi. Bai ƙara cewa komai ba sai kumshe idanunsa da yayi ya jingina jikin kujerar,ba abinda yake gani sai lips ɗinsa cikin bakin fattu,ahankali yake sakin murmushi, ta gefen bakinsa,haƙiƙa al'amarin yayi masa daɗi sosai . Fattu kuwa ganin ya lunshe idanunsa yasa ta ɗan juya ta kalli window. Kan bala'i me zata fani,?gani tayi kamar ta saka hannunta ta kamo gajimare ,kuma saitaga kamar asama suke. Ɗan Dada leƙa kanta tayi sosai,yadda zata hango da gaske a sama suke ko a ƙasa,aikuwa wllh asaman suke,hana wani wawan ihu da fattu ta kurma tare da buga tsalle ta fito daga kan kujerar nan tayi kan Adeeb,ba Adeeb kadai ba ,hatta tareeƙ saida ya jiyo ihun fattu. Arazane Adeeb daya lula duniyar sa ta nishaɗi ya buɗe ido tare da mikewa tsaye cikin tsoro,kawai saijin fattu yayi ta fado kansa tana ihu"wayyo Allah na Ni fattu na shiga ukuna ,Hamma ka taimakeni,wllh duniyar sama suke tafiya ,dama saida nace bazan shiga cikin wannan kifin ba amma saboda mugunta ka shigo dani gashinan sai sama akeyi damu, wayyo Allah Hamma ka fitar dani daga nan wayyo baffa an,e....a.yyy.y..oooo ga....ji...immarr,sai kawai ta tafi luuuu tayi baya zata faɗi.alamun ta suma. Da sauri Adeeb ya dariya zuwa jikinsa,kumatunta yake ɗan bugawa yana faɗin"hey! hey!! wake up HULWA wake up please,Adeeb ya faɗa cikin mugun damuwa ,komawa yayi ya zauna tare da riƙe ta ahannunsa, dan bubbuga kumatunta yake yana kiran HULWA !HULWA,amma ina HULWA kam tayi kisan zango. Gefensa ya danna wata yar jar danja ,saiga wata ƙaramar ƙora ta buɗe ,ruwane da lemuka kala kala aciki da alamu dai fridge me,robar ruwan ya ɗauko tare da budewa,Ahankali yake tattara mata ruwan yana shafawa akan fuskarta amma ko motsi batayi ba. Hankalinsa yayi mugun tashi,sosai hannunsa ya kai saitin zuciyarta ya taɓa,da sauri kuma ya zare hannun nashi,sakamakon karo da yaci da tudun ƙirjin fattu. Ɗagota yayi tare da ɗora bakinsa kan nata ,sannan ya toshe hancinta,ya fara hura mata iska ,amma nan ma shiru,bayi motsiba, Cikin mugun tashin hankali Adeeb ya ƙanƙame fattu ajikinsa yana faɗin "AM sorry HULWA Please wake up " ya faɗa yana mai kara ƙankameta ajikinsa.nan da nan idanunsa suka fara rikiɗewa zuwa kaloli daban daban ,wani irin huci yake yana zazzage idanu jikinsa ya kama bari.idan kaga Adeeb a wanna lokacin tabbas zaka shiga cikin kuɗu da tsantsar tsoro ,dan gaba ɗaya kamaninsa sun sauya. Shiba mutum ba Shiba aljan ba. Cikin wanan halin suka sami isowa Misra,kai tsaye wani guest haose ɗin Adeeb na sirri Tareeƙ ya nufa ,suna sauka kuwa ,Adeeb ya kinkimo fattu da gudu yake sauka akan jirgin,kai tsaye yana zuwa jikin ƙofar ya fara daddanna wasu nonbobi jikin wata ƴar na'ura,cikin second kofar ta fara budewa tana faɗin well come back prince Adeeb Muhammad Ashraf , long time no see" kota kanta baibiba yayi cikin gidan da gudu,kai tsaye wani daki ya shiga ,yana zuwa bai jira wata wata ba daddanna wani guri tare da shigewa cikin wani ɗan banzan haɗaɗden jacuzy mai matuƙar girma da kyau,ruwane ya fara zubowa daga samansu, mai sanyi sosai,wanda idan haka kawai aka zubawa mutum ruwan nan tabbas sai yayi jinya. Bubbuga kumatun fattu yaci gaba dayi yana kiran sunanta"HULWA ! HULWA!! HULWA!!! Har sau uku,Ahankali fattu ta fara bude idanunta tana lumshewa, kafin ta buɗe su duka, da sauri kuma ta ƙankame Adeeb tana mai cewa"dan Allah Hamma kafitar dani dana cikin kifin na wllh tsoro nakeji,Hamma, fattu ta faɗa tana mai rawar jiki. Janyota Adeeb yayi zuwa jikinsa yana mai sakin wata kakkarfar ajiyar zuciya,"AM sorry HULWA ba abinda zai sameki ina tare da ke ,Please karki ƙara suma irin haka,saura kaɗan zuciyata ta buga" ya faɗa cikin rashin sanin abinda yake faɗi. " Hamma mufita dan Allah" fattu ta sake faɗa. Ahankali Adeeb ya riƙe kumatun fattu yana kallonta kafin yace "ki nutsu HULWA ba acikin jirgin muke ba yanzu,mun fita kalli kigani we are in toilet now ,bazan taɓa barin wani abu ya samekiba ,domin kuɗin mallakina ce kuma amanata, sannan ma....saikuma yayi shiru ,tare da cire hannunsa daga kan fuskar ta,fitowa yayi daga cikin ruwan ,sannan ya kamo hannunta ya fito da ita ,sai rawar sanyi yake,wani ɗaki ya kaita tare da zaunar da ita akan wani makeken gado,a baidamu da yadda jikinta ke jiƙe ba,wani ƙaton bargo ya dauko ya lulluɓa mata,sannan ya nufi jikin wani bango,nidai naga ya danna wani guri,kawai naga bango Ya dare,kaya sun bayyana.ehe mana bango Ya dare zance,tunda idan ka kalli gurin bazaka taba tsammanin akwai wata ƙofa dazata bude ajikinsa ba. Wasu kaya naga ya dauko masu kama dana sanyi riga da wando sannan. Ya dawo kusa da fattu da ke binsa da kallo yace "kisa wannan kayan ,kinji,zanje in shirya nima yanzu zan dawo " ya faɗa yana mika mata kayan. Karba tayi cikin rawar hannu tana mai binsa da kallo harya fice daga ɗakin. Bin dakin fattu tayi da kallo,ikon Allah wai nan ɗin ɗakin mutum ne ,saikace wanda aka tattaro duk kayan jin daɗin duniya aka ajiye aciki. Ahankali ta mike ta cire kayan jikinta sannan ta sanya riga da wando da Adeeb ya bata,kayan sunyi mata kyau sosai,saidai wando yayi mata tsayi rigar ma haka,kasancewar Adeeb dogone sosai,hakan yasa rigar ta sauƙo ta rufe mata manyan mazaunanta.sanna kuma rigar tana da hula,hmmmmm nan da nan fattu ta koma wata irin ƴar balarabiyar nan tayi mugun kyau cikin kayan . Kayan data cire ɗin ta dauka tare da rikews ahannunta tana tsaye ,tana waige waige kallo ɗaya zaka mata kasan afirgice take. Bude ɗakin Adeeb yayi bayan yayi noking yaji shiru, "Masha Allah " shine abinda Adeeb ya iya faɗi lokacin da yayi arba da fattu cikin kayan nan. Shima yana sanye da wata farar jallabiya ajikinsa da hirami akansa.yayi kyau sosai cikin shigar tasu ta larabawa. Cikin ɗakin ya nufa yana mai jure fattu da idanu,ita kuwa kanta na ƙasa,riƙe da jiƙaƙkun kayanta. Cikin wata irin murya mai kama da mutum na jin barci Adeeb yace "Hulwa" Ahankali fattu ta daga kanta tana kallon bayan Adeeb ɗin dan gani ta ina hulwar zata fito..... Muje zuwa masu karatu, Mrs babi ce💘💘💘[21/07, 9:44 am] +234 704 353 5214: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 29/30 _________________Cikin wani irin salo da murya mai maka da yana jin barci,Adeeb yace "Hulwa" Ahankali fattu ta dago kanta tana mai kallon bayan Adeeb ɗan ganin ta ina hulwar zata fito. Rarraba idanu take ,amma bataga kowa ba,ikon Allah ko ina hulwar take ?bisani Banga kowa abayansa ba ,kuma ba kowa cikin ɗakin nan, fattu ta faɗa tana mai waige bayanta ,dan ita dai bataga hulwa anan ba. Duk abinda take Adeeb na kallonta,kuma ya gane me take nufi,wato suna daya faɗa shine bata ganeba,take neman mai sunan. Juyowa fattu tayi ta kalli Adeeb ɗin cikin rashin fahimta tace "Hamma Ina hulwar take ?naga ba kowa cikin ɗakin nan ? Kallonta yayi tare da ɗan zafi ido yace "yanzu ke bakuga hulwar tawa ba anan?" Ya faɗa yana mata kallon tuhuma. Waigawa fattu ta sakeyi bayanta,amma wllh ita kam bataga kowa ba,juyowa tayi tace "alƙur'ani banga kowa ba" ta faɗa tana ɗan buɗe hannayenta dan tabbatar masa da cewar ba kowa aɗakin. Yaɓe baki yayi yace "matata ce hulwa kuma gata nan akusa dani idan ke bakya ganinta toni ina ganin abata,ya faɗa yana ɗan kallon kusa da gadon da fattu ke tsaye. Ai fattu najin haka wani irin tsoro ya kamata,da gudu ta watsar da kayan hannunta ta taho gareshi ,tana zuwa ta biye abayansa tana tsuma, ahankali take masa faɗa cikin kunnensa,"aradu Hamma aljanna kake gani ba matar ka ba,dan ba kowa acikin ɗakin nan,Ni dama tun dazu nakewa dakin kallon na aljanu,dan wannan ɗakin baiyi kama dana mutane ba ,kyanshi yayi yawa aradun Allah" fattu ta ƙare magannarta cikin kunne Adeeb da sunan tana masa raɗa dan kar Hulwa tajisu. Tunda ta fara masa magana akunne ya wani lumshe idanunsa,har cikin ƙwaƙwalwar sa yake jin sautin maganarta, yayi da yake jin tana zaga dukkan ilahirin jikinsa, wani yuuuuum yakeji ajikinsa har kamar zai faɗi.ahankali ya buɗe idanunsa,jin ta kai aya akan maganar tata. Wacce shidai yaji farkon,amma sam bai fahimci me take fadi ba daga ƙarshen. Yana shirin yin magana ne yajiyo ƙarar na'urar sanarda mutum yayi bako tana faɗin tareek na jikansa afalo. Dan haka ya fasa yin maganar ,kawai saiya juyo yana kallon fattun da tunanin idanunsa,ahankali ya buɗe baki da gyara yace "wait for me here I will be back" ya faɗa yana ƙoƙarin buɗe kofar,ai carab fattu ta kama hannunsa ta riƙe cikin nata gam!tana kallonsa. Kallonta yayi shima da nuna alamun menene? Turo baki tayi tace " Ni ma zan bila Hamma,dan naji ka kira sunan wasu mutanen da yawa,bayan waccan hulwar Ni wllh tsoro nake ji" fattu ta faɗa tana mai kallon fuskarsa. Hannunsa data rike cikin nashi,yabi da kallon,kafin ya ɗago yana kallonta,waima shi yaushe ya kira sunan wasu mutane kuma?ahankali ya sanya hannu ya zare nata hannun daga nashi kafin yace"bazaki bini ba, kuma Ni nace ne ki Kijirani kawai"ya faɗa yana harararta tare da bude ƙofar,yana sanya ƙafarsa waje fattu ma ta fito jikinta sai rawa yake,juyowa yayi yana kallonta fuska ba walwala yace " koma" Marairaicewa fattu tayi kafin tace " wllh tsoro nakeji,dan Allah kaje dani,wannan hulwar fa tana ciki" harara ya Banka mata kafin yace "get in I said ,hulwar ta cinyeki" ya faɗa yana turata ciki dakin yana ƙofar ya kulle. Hauka yake yaje da ita gurin tareek cikin wannan shigar?ai wllh idan tareek ya ganta ahana,inaga saina kusan mutuwa dan baƙin ciki.cewar Adeeb kenan yana nufar madaidaicin falon daya gaji da hadewa,zama yayi yana kallon tareek ɗin cikin yanayinsa ya haɗe fuska. "Yallaɓai me yake faruwa ne ?naga ka shigo cikin tashin hankali?"tareek ya faɗa cikin harshen larabci yana kallon Adeeb ɗin. Ajiyar zuciya Adeeb yayi kafin ya jingina kansa jikin kujera ,kusan minti biyu kafin ya buɗe baki dagyar yace " ta tsoratane ,shine ta suma" shima cikin harshen larabci yayi maganar. "Ya Salam, yallaɓai koka sanar da ita wanann maganar ne?" "No ban faɗa mata ba" cewar Adeeb . Shiru suka ɗanyi na wani lokaci, kafin tareek yace "yallaɓai abie baisan da dawowarsa,bansanar da kowa ba kamar yadda ka buƙata" Ɗagowa Adeeb yayi daga kwanciyar da yayi jikin kujera,kafin yace " Yes,bana son ya sani yanzu,sai dare yayi zamuje gurinsa, ka shirya komai da komai,yanzu zanje na rage suman nan ne" Adeeb ya faɗa yana mai shafa dogon lallausan gashin kansa zuwa gefen fuskarsa da gemunsa. "Ok me kake ɓukata yanzu yallaɓai " tareek ya faɗa cikin ladabi. "Kaje ka kawo mata kayan buƙata duka, sannan ka tahomin da wayoyi ayi duk abinda ya kamata" yana faɗin haka bai jira me Tareek zaiceba ya miƙe tare da nufar wani ɗakin da ban. Fattu kuwa Adeeb yana kulle ƙofar taji wani mugun tsoro da fargaba, wayyo Allah,yanzu ya zanyi idan hulwar nan mai shan jini ce ? Kuma gashi bana ganinta ? Zama tayi agurin tare da ƙanƙame jikinta tana kuka sosai harda shashsheka,Allah Sarki baffanta ,ko wane hali yake ciki yanzu?ko wane hukunci mai gari ya ɗauka akansa? Allah dai ya kare mata baffanta Aduk yanayin daya tsinci kansa. Tana nan zaune sai waige waige take ,ta gaji sosai ga yunwa ,ga barci,gashi tana sonyin salla dan rabonta da abinci tun wanann jakwalkwalon da Hamma ya bata awanann gidan.tana zaune shiru kawai taga wasu labulaye masu suna saukowa ahankali daga kowane bango na ɗakin.wata zabura da tayi cikin tsoro ta kwallah ihu tana mai komawa tsakiyar dakin ,banda rawa ba abinda jikinta keyi"wayyo Allah ma hulwa dan Allah kiyi haƙuri,karki cinyeni ,wllh ba abinda nayi miki,Hamma ne ya kawoni gidanki"abinda fattu ke fadi kenan tana rawar jiki da karkarwa,tana juye juye atsakiyar dakin,ta kalli wannan bangon ta kalli wancan.. Sukuwa labulaye ,sai sauka suke kasa,kuma basu tsayaba ,saida suka dire har aƙasa. Sai kuma taga hasken ɗakin ya sauya kala ,daga farin haske zuwa dim light,kuma daga can gefe wata bishi sai walwali take . Kuka sosai fattu keyi cikin tsoro da rashin sanin abinyi,yaukan yasan kwananta kawai ya kare kamar wacce akace kalli can ,tana juyowa wajen da sif ɗin nan take ,kawai taga abubuwa kamar malam bude mana littafi, suna ta yawonsu ajikin sif ɗin. Wata irin numfashi fattu ta jaa da ƙarfi,kafin kuma tayi ƙasa sululu ta faɗa kan gadon asume. Shikuwa Adeeb yana shiga wannan dakin kwanciya ya ɗanyi akan lafiyayyen gadon dake ɗakin,so yake ya ɗan huta,dan gaba ɗaya yarinyar nan ta gama gajiyar dashi ,yana kwanciya sai yayi tunanin ai baiyi Sallah ba,dan haka tashi yayi tare da sake wanka sannan yayi Sallah,ya koma toilet ɗin ya gabata fuskarsa,sosai naga kyansa ya ƙara fitowa ,ashema kyanshi ya wuce yadda nake tunani,dan kallo daya idan kayi masa ,kuma kuka haɗa idanu ,bazaka iya ƙara yarda ku haɗa ido ba,dan yana da wani irin kwarjini da haiba. Wannan karon ƙananan kaya ya sanya,riga da wando ne na jins, rigar light blue ce ,yayinda wando kuma ya kasance blue ne sosai.kansa ya taje, sannan ya fashe jikinsa da tauraruwa masu masifar ƙamshi, danaga ya buɗe wata loka guda ,duka turarukane acikin lokar tunda ga sama har ƙasanta. Wata lokar ya buɗe naga agoguna ,masu azabar kyau da tsada,wani agogon kwal ya dauko ya daura ahanannunsa, sannan ,sannan ya buɗe bangaren takalma,nidai gefe na koma na zama yar kallo.dan abun yafi karfina, daki guda duka na kayan Amfanin mutum ɗaya?wani aikin sai amasar. Yana gama shiryawa ,dakin ya dauki wani ƙamshi mai rikitarwa da sanya nutsuwa,kanshi ya taje sannan ya shafa mayuka kusan kala biyar akan nashi,tuni kan ya dauki walwali da sheƙi, Fitowa yayi daga ɗakin ya nufi kitchen,masu karatu kuzo kuga kitchen ,aini kodaga nam aka barni ,tabbas na more,dan iya tsaruwa kitchen ɗin nan ya tsaru. Wani irin tea naga ya haɗa ,sannan ya siya kwai tare da imdomie,shikam arayuwarsa baida wani abinci daga tea sai imdomie saiko nama, Yana gama haɗawa ya tsaya yana kallon abincin daya haɗa ɗin cikin wani kayataccen faranti, mamakin kansa yake ,wai yau shine da haɗawa wata abinci,kuma shi zai kai mata da kansa.koda yake ai itaɗin amanar sa ce,kuma dole ya kula da ita. Ɗaukar tiren yayi ya nufi dakin da Fattun ke ciki, Kwankwasawa yayi kafin ya dannan wani guri sai ga kofar tana komawa gefe guda,harya buɗe gaba ɗaya ɗaya . Kansa ya kunna cikin dakin yana mai kallon yadda komai ya canza,wannan alamun e na lokacin barcinsa yayi ,dama haka dakunan aka shiryasu suke sauya komai da kansu,idan lokacin barcin rana ne kona dare ,kokuma safiya . Ajiye tiren yayi yana mai kallon ta ina zai hangi fattu,can ya hangota kwance akan gado ,saidai da'alama kwanciyar bata daɗi bace, dan haka da sauri ya nufeta, kamar yadda yayi tsammani kuwa suma tayi,cike da fargaba ya ɗagota yana mai kiran sunanta ,"Hulwa !hulwa!!amma bata ko motsaba,ajiye ta yayi tare da bude fridge ya dauko ruwa mai sanyi yana yayyafa mata.amma bata ko motsaba ,wai wannan suman na menene haka?duka duka yaushema ta dawo hayyacinta ne ?gashi yanzu ta ƙara suka. Huci kawai yake yana kallon fuskarta,zuciyarsa kamar zata fasa ƙirjinsa ta fito,sam baya ƙaunar ganin fattu cikin wani mugun yanayi,waima menene yayi silar wannan suman nata ne?kallon dakin yayi yana mai jinjina kai ,ba shakka tayi arba da yadda dakin nan ke sauyawa ne,wani irin runtse idanunsa yayi tare da dafe kansa,duk laifinane dana fita da ita da duk haka bata faru ba.bude idanunsa yayi wanda suka juye zuwa na macizai sak, ahankali jikinsa ya kama wata irin girgiza yana hayaƙi,kan kace me saiga ɗakin ya turnuƙe da hayaƙi, kusan minti biyar dakin yana wanann yanayi hayaƙi da wata irin ƙara,kafin hayaƙi ya baje, saiga wani murtukeken maciji mai girman gaske ya fasa kai yana huci. Cikin tafiyar macizai macijin nan ya fara sauƙa daga kan gadon ,bangon dakin ya kama tare da fara lauye jikin wanan haɗaɗdun labulayen yana nannadesu tare da fesa musu wani irin ruwa daga bakinsa,da zaran ya fesa ruwan sai kaga labulen yana hayaƙi tare da murmushewa, haka yayi tayi saida ya bata gaba dayan labulayenan sannan ya fara bugun kwayayen dakin dake bada hasken nan mai ban sha'awa da jelarsa.tas saida ya gama fashesu, sannan ya nufi kan gadon,yana zuwa ya hau kan cikin fattu dake kwance ,cikin halin suma,zagayeta ya farayi tare da shigewa ciki rigarta sosai,yana goga mata sanyin dake jikinsa. Aikuwa sanyin yana fara ratsa fattu ,ta fara bude idanunta ahankali,tana mai dafe kanta tare da yamutse fuska. Abu taji yana fitowa sululu daga cikin rigarta,da sauri ta tashi zaune tana mai daga rigarta sama,daidai lokacin shikuwa macijin ya gama fitowa daga jikin nata. Saƙare fattu tayi tana kallon macijin cike da tsantsar mamaki,shima macijin kallonta yake ido cikin ido. Masu karatu meke faruwa ne? Wannan macijin kuma waye? Shin Adeeb dama bai daina zama macijin ba? Muje zuwa takuce anty mammy Mrs babi💘💘💘 Share and comment Fisabilillah. More comments More typing. [21/07, 5:07 pm] Haddy: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 29/30 _________________Cikin wani irin salo da murya mai maka da yana jin barci,Adeeb yace "Hulwa" Ahankali fattu ta dago kanta tana mai kallon bayan Adeeb ɗan ganin ta ina hulwar zata fito. Rarraba idanu take ,amma bataga kowa ba,ikon Allah ko ina hulwar take ?bisani Banga kowa abayansa ba ,kuma ba kowa cikin ɗakin nan, fattu ta faɗa tana mai waige bayanta ,dan ita dai bataga hulwa anan ba. Duk abinda take Adeeb na kallonta,kuma ya gane me take nufi,wato suna daya faɗa shine bata ganeba,take neman mai sunan. Juyowa fattu tayi ta kalli Adeeb ɗin cikin rashin fahimta tace "Hamma Ina hulwar take ?naga ba kowa cikin ɗakin nan ? Kallonta yayi tare da ɗan zafi ido yace "yanzu ke bakuga hulwar tawa ba anan?" Ya faɗa yana mata kallon tuhuma. Waigawa fattu ta sakeyi bayanta,amma wllh ita kam bataga kowa ba,juyowa tayi tace "alƙur'ani banga kowa ba" ta faɗa tana ɗan buɗe hannayenta dan tabbatar masa da cewar ba kowa aɗakin. Yaɓe baki yayi yace "matata ce hulwa kuma gata nan akusa dani idan ke bakya ganinta toni ina ganin abata,ya faɗa yana ɗan kallon kusa da gadon da fattu ke tsaye. Ai fattu najin haka wani irin tsoro ya kamata,da gudu ta watsar da kayan hannunta ta taho gareshi ,tana zuwa ta biye abayansa tana tsuma, ahankali take masa faɗa cikin kunnensa,"aradu Hamma aljanna kake gani ba matar ka ba,dan ba kowa acikin ɗakin nan,Ni dama tun dazu nakewa dakin kallon na aljanu,dan wannan ɗakin baiyi kama dana mutane ba ,kyanshi yayi yawa aradun Allah" fattu ta ƙare magannarta cikin kunne Adeeb da sunan tana masa raɗa dan kar Hulwa tajisu. Tunda ta fara masa magana akunne ya wani lumshe idanunsa,har cikin ƙwaƙwalwar sa yake jin sautin maganarta, yayi da yake jin tana zaga dukkan ilahirin jikinsa, wani yuuuuum yakeji ajikinsa har kamar zai faɗi.ahankali ya buɗe idanunsa,jin ta kai aya akan maganar tata. Wacce shidai yaji farkon,amma sam bai fahimci me take fadi ba daga ƙarshen. Yana shirin yin magana ne yajiyo ƙarar na'urar sanarda mutum yayi bako tana faɗin tareek na jikansa afalo. Dan haka ya fasa yin maganar ,kawai saiya juyo yana kallon fattun da tunanin idanunsa,ahankali ya buɗe baki da gyara yace "wait for me here I will be back" ya faɗa yana ƙoƙarin buɗe kofar,ai carab fattu ta kama hannunsa ta riƙe cikin nata gam!tana kallonsa. Kallonta yayi shima da nuna alamun menene? Turo baki tayi tace " Ni ma zan bila Hamma,dan naji ka kira sunan wasu mutanen da yawa,bayan waccan hulwar Ni wllh tsoro nake ji" fattu ta faɗa tana mai kallon fuskarsa. Hannunsa data rike cikin nashi,yabi da kallon,kafin ya ɗago yana kallonta,waima shi yaushe ya kira sunan wasu mutane kuma?ahankali ya sanya hannu ya zare nata hannun daga nashi kafin yace"bazaki bini ba, kuma Ni nace ne ki Kijirani kawai"ya faɗa yana harararta tare da bude ƙofar,yana sanya ƙafarsa waje fattu ma ta fito jikinta sai rawa yake,juyowa yayi yana kallonta fuska ba walwala yace " koma" Marairaicewa fattu tayi kafin tace " wllh tsoro nakeji,dan Allah kaje dani,wannan hulwar fa tana ciki" harara ya Banka mata kafin yace "get in I said ,hulwar ta cinyeki" ya faɗa yana turata ciki dakin yana ƙofar ya kulle. Hauka yake yaje da ita gurin tareek cikin wannan shigar?ai wllh idan tareek ya ganta ahana,inaga saina kusan mutuwa dan baƙin ciki.cewar Adeeb kenan yana nufar madaidaicin falon daya gaji da hadewa,zama yayi yana kallon tareek ɗin cikin yanayinsa ya haɗe fuska. "Yallaɓai me yake faruwa ne ?naga ka shigo cikin tashin hankali?"tareek ya faɗa cikin harshen larabci yana kallon Adeeb ɗin. Ajiyar zuciya Adeeb yayi kafin ya jingina kansa jikin kujera ,kusan minti biyu kafin ya buɗe baki dagyar yace " ta tsoratane ,shine ta suma" shima cikin harshen larabci yayi maganar. "Ya Salam, yallaɓai koka sanar da ita wanann maganar ne?" "No ban faɗa mata ba" cewar Adeeb . Shiru suka ɗanyi na wani lokaci, kafin tareek yace "yallaɓai abie baisan da dawowarsa,bansanar da kowa ba kamar yadda ka buƙata" Ɗagowa Adeeb yayi daga kwanciyar da yayi jikin kujera,kafin yace " Yes,bana son ya sani yanzu,sai dare yayi zamuje gurinsa, ka shirya komai da komai,yanzu zanje na rage suman nan ne" Adeeb ya faɗa yana mai shafa dogon lallausan gashin kansa zuwa gefen fuskarsa da gemunsa. "Ok me kake ɓukata yanzu yallaɓai " tareek ya faɗa cikin ladabi. "Kaje ka kawo mata kayan buƙata duka, sannan ka tahomin da wayoyi ayi duk abinda ya kamata" yana faɗin haka bai jira me Tareek zaiceba ya miƙe tare da nufar wani ɗakin da ban. Fattu kuwa Adeeb yana kulle ƙofar taji wani mugun tsoro da fargaba, wayyo Allah,yanzu ya zanyi idan hulwar nan mai shan jini ce ? Kuma gashi bana ganinta ? Zama tayi agurin tare da ƙanƙame jikinta tana kuka sosai harda shashsheka,Allah Sarki baffanta ,ko wane hali yake ciki yanzu?ko wane hukunci mai gari ya ɗauka akansa? Allah dai ya kare mata baffanta Aduk yanayin daya tsinci kansa. Tana nan zaune sai waige waige take ,ta gaji sosai ga yunwa ,ga barci,gashi tana sonyin salla dan rabonta da abinci tun wanann jakwalkwalon da Hamma ya bata awanann gidan.tana zaune shiru kawai taga wasu labulaye masu suna saukowa ahankali daga kowane bango na ɗakin.wata zabura da tayi cikin tsoro ta kwallah ihu tana mai komawa tsakiyar dakin ,banda rawa ba abinda jikinta keyi"wayyo Allah ma hulwa dan Allah kiyi haƙuri,karki cinyeni ,wllh ba abinda nayi miki,Hamma ne ya kawoni gidanki"abinda fattu ke fadi kenan tana rawar jiki da karkarwa,tana juye juye atsakiyar dakin,ta kalli wannan bangon ta kalli wancan.. Sukuwa labulaye ,sai sauka suke kasa,kuma basu tsayaba ,saida suka dire har aƙasa. Sai kuma taga hasken ɗakin ya sauya kala ,daga farin haske zuwa dim light,kuma daga can gefe wata bishi sai walwali take . Kuka sosai fattu keyi cikin tsoro da rashin sanin abinyi,yaukan yasan kwananta kawai ya kare kamar wacce akace kalli can ,tana juyowa wajen da sif ɗin nan take ,kawai taga abubuwa kamar malam bude mana littafi, suna ta yawonsu ajikin sif ɗin. Wata irin numfashi fattu ta jaa da ƙarfi,kafin kuma tayi ƙasa sululu ta faɗa kan gadon asume. Shikuwa Adeeb yana shiga wannan dakin kwanciya ya ɗanyi akan lafiyayyen gadon dake ɗakin,so yake ya ɗan huta,dan gaba ɗaya yarinyar nan ta gama gajiyar dashi ,yana kwanciya sai yayi tunanin ai baiyi Sallah ba,dan haka tashi yayi tare da sake wanka sannan yayi Sallah,ya koma toilet ɗin ya gabata fuskarsa,sosai naga kyansa ya ƙara fitowa ,ashema kyanshi ya wuce yadda nake tunani,dan kallo daya idan kayi masa ,kuma kuka haɗa idanu ,bazaka iya ƙara yarda ku haɗa ido ba,dan yana da wani irin kwarjini da haiba. Wannan karon ƙananan kaya ya sanya,riga da wando ne na jins, rigar light blue ce ,yayinda wando kuma ya kasance blue ne sosai.kansa ya taje, sannan ya fashe jikinsa da tauraruwa masu masifar ƙamshi, danaga ya buɗe wata loka guda ,duka turarukane acikin lokar tunda ga sama har ƙasanta. Wata lokar ya buɗe naga agoguna ,masu azabar kyau da tsada,wani agogon kwal ya dauko ya daura ahanannunsa, sannan ,sannan ya buɗe bangaren takalma,nidai gefe na koma na zama yar kallo.dan abun yafi karfina, daki guda duka na kayan Amfanin mutum ɗaya?wani aikin sai amasar. Yana gama shiryawa ,dakin ya dauki wani ƙamshi mai rikitarwa da sanya nutsuwa,kanshi ya taje sannan ya shafa mayuka kusan kala biyar akan nashi,tuni kan ya dauki walwali da sheƙi, Fitowa yayi daga ɗakin ya nufi kitchen,masu karatu kuzo kuga kitchen ,aini kodaga nam aka barni ,tabbas na more,dan iya tsaruwa kitchen ɗin nan ya tsaru. Wani irin tea naga ya haɗa ,sannan ya siya kwai tare da imdomie,shikam arayuwarsa baida wani abinci daga tea sai imdomie saiko nama, Yana gama haɗawa ya tsaya yana kallon abincin daya haɗa ɗin cikin wani kayataccen faranti, mamakin kansa yake ,wai yau shine da haɗawa wata abinci,kuma shi zai kai mata da kansa.koda yake ai itaɗin amanar sa ce,kuma dole ya kula da ita. Ɗaukar tiren yayi ya nufi dakin da Fattun ke ciki, Kwankwasawa yayi kafin ya dannan wani guri sai ga kofar tana komawa gefe guda,harya buɗe gaba ɗaya ɗaya . Kansa ya kunna cikin dakin yana mai kallon yadda komai ya canza,wannan alamun e na lokacin barcinsa yayi ,dama haka dakunan aka shiryasu suke sauya komai da kansu,idan lokacin barcin rana ne kona dare ,kokuma safiya . Ajiye tiren yayi yana mai kallon ta ina zai hangi fattu,can ya hangota kwance akan gado ,saidai da'alama kwanciyar bata daɗi bace, dan haka da sauri ya nufeta, kamar yadda yayi tsammani kuwa suma tayi,cike da fargaba ya ɗagota yana mai kiran sunanta ,"Hulwa !hulwa!!amma bata ko motsaba,ajiye ta yayi tare da bude fridge ya dauko ruwa mai sanyi yana yayyafa mata.amma bata ko motsaba ,wai wannan suman na menene haka?duka duka yaushema ta dawo hayyacinta ne ?gashi yanzu ta ƙara suka. Huci kawai yake yana kallon fuskarta,zuciyarsa kamar zata fasa ƙirjinsa ta fito,sam baya ƙaunar ganin fattu cikin wani mugun yanayi,waima menene yayi silar wannan suman nata ne?kallon dakin yayi yana mai jinjina kai ,ba shakka tayi arba da yadda dakin nan ke sauyawa ne,wani irin runtse idanunsa yayi tare da dafe kansa,duk laifinane dana fita da ita da duk haka bata faru ba.bude idanunsa yayi wanda suka juye zuwa na macizai sak, ahankali jikinsa ya kama wata irin girgiza yana hayaƙi,kan kace me saiga ɗakin ya turnuƙe da hayaƙi, kusan minti biyar dakin yana wanann yanayi hayaƙi da wata irin ƙara,kafin hayaƙi ya baje, saiga wani murtukeken maciji mai girman gaske ya fasa kai yana huci. Cikin tafiyar macizai macijin nan ya fara sauƙa daga kan gadon ,bangon dakin ya kama tare da fara lauye jikin wanan haɗaɗdun labulayen yana nannadesu tare da fesa musu wani irin ruwa daga bakinsa,da zaran ya fesa ruwan sai kaga labulen yana hayaƙi tare da murmushewa, haka yayi tayi saida ya bata gaba dayan labulayenan sannan ya fara bugun kwayayen dakin dake bada hasken nan mai ban sha'awa da jelarsa.tas saida ya gama fashesu, sannan ya nufi kan gadon,yana zuwa ya hau kan cikin fattu dake kwance ,cikin halin suma,zagayeta ya farayi tare da shigewa ciki rigarta sosai,yana goga mata sanyin dake jikinsa. Aikuwa sanyin yana fara ratsa fattu ,ta fara bude idanunta ahankali,tana mai dafe kanta tare da yamutse fuska. Abu taji yana fitowa sululu daga cikin rigarta,da sauri ta tashi zaune tana mai daga rigarta sama,daidai lokacin shikuwa macijin ya gama fitowa daga jikin nata. Saƙare fattu tayi tana kallon macijin cike da tsantsar mamaki,shima macijin kallonta yake ido cikin ido. Masu karatu meke faruwa ne? Wannan macijin kuma waye? Shin Adeeb dama bai daina zama macijin ba? Muje zuwa takuce anty mammy Mrs babi💘💘💘 Share and comment Fisabilillah. More comments More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free book Page 31/32 _________________Saƙare,fattu tayi tana kallon macijin cike da tsantsar mamaki, kamar yadda macijin ke kallon fattu shima ido cikin ido. Ahankali fattu ta lumshe idonta,tana mai ambaton sunan Allah,abin da ya bata mamaki shine,sam bataji tsoroba, saima bin jikin macijin da tayi da kallo,tabbas wannan macijin ta ne na yar ruga, kenan hakan na nufin Hammanta ne ya ƙara zama maciji? innalillahi ,yanzu yazatayi kenan?awane matsayin take idan bai dawo mutum ba? Ahankali ta furta "Hammana" hawaye na zubowa daga cikin idanunta. Shikuwa macijin yana ganin hawayen nan nata,ya taho zuwa gareta,yana zuwa ya hau kan cinyarta tare da nannaɗe jikinsa ya ɗora kansa akan kafaɗunta. Lumshe ido fattu tayi cikin kuka tace " dan Allah HAMMA karka zauna cikin wannan yanayin,bazan iya rayuwa Ni kadai cikin wannan gidan mai aljanu ba, dazuma saida Hulwarka tazo ta tsoratani, gaba daya ta sanja duniyar wannan dakin ,ya koma wata kala,kalli kagani yanzu yadda ya koma,Hamma inajin tsoro"fattu ta faɗa tare da ɗora hannunta akan macijin tana shafawa. Dagowa macijin yayi tare da zuba mata idanu,itama kallonsa take hawaye na zubowa daga idanunta. Jikinta ya fara zagayewa yana yana nannaɗeta,kafin kuma yayi baya da ita akan gadon,kwanciya fattu tayi tare da runtse idanunta . Ita kam tariga ta gama sallama wa rayuwa, tasan idan har macijinta bai dawo mutum ba to mutuwa zatayi, ahalin da ake ciki yanzu tana jinsa ne har cikin ranta,kome takeyi shi take gani,ba abinda take bukata akullum kamar tajita kusa dashi,ta san duk ransa wani ya ganshi matsayin maciji ,to za'ayi ƙoƙarin kashe mata shine,wanda tayi imanin duk randa aka kashe Hamma, to tabbas da gawarsa za'a binnesu. Shikuwa maciji bayan ya kwantar da fattu saiya zare jikinsa daga nannaɗetan da yayi,sannan ya kamo bargon dake kan gadon ya lullaba ajikin fattu,duk abinda yake kallonsa fattu keyi cike da tausayawa,ace mutum yana komawa wata da bar daban?kuma mai haɗari wacce kowa ke gudunta.saukowa yayi daga kan gadon tare da tsayawa daga can gefenta yana kallonta, itama kallonsa take ,kusan minti uku suna kallon juna,yayin da fattu ke zubda hawaye,juyawa yayi tare da nufar ƙofar dakin. "Dan Allah Hamma ka dawo mutum,kada ka tafi ka barni,ina don kasancewa tare da kai,bani da kowa awannan sabuwar duniyar saikai"abinda fattu ta faɗa kenan lokacin da taga yana ƙoƙarin ficewa daga ɗakin. Aikuwa tsayawa yayi kamar wanda yake sauraron me take faɗi .saida ta kai aya azancenta,kafin ya kalleta da idanunsa masu naunuka daban daban,sannan ya fice daga ɗakin. Kuka sosai fattu ta fashe dashi,tana daga kwancen nan,shikenan komai yazo mata ƙarshe,idan Hamma ya tafi ya barta,ita ahalin yanzu ma, ta fara tunanin kodai duniyar aljanu ya kawo ta? Haka tayi ta kukanta tana daga kwance har barcine wahala yayi gaba da ita. Shikuwa Adeeb yana fita kai tsaye dakin daya baro ya nufa ,ahankali yake jan jikinsa , harya kai kan gadon ,hawa yayi tare da kwantawa lamo kamar baya nunfashi,rufe idanunsa yayi yana nishi da gyar, kafin kuma jikinsa ya kama girgiza sosai yana hayaƙi, sosai dakin ya turnuƙe da hayaƙi kafin ya washe. Ikon Allah Adeeb na hanga kwance akan gadon nan,ya duƙunƙune jikinsa,sai rawa yake kamar mai jin sanyi,ahankali ya ɗaya hannunsa dake ta faman rawa ya dage kansa,yana mai yamutse fuska ,da alama kan ke masa ciwo,kusan minti goma ya ɗauka cikin wanan halin kafin naga ya miƙe jiki ba kwari,ya nufi toilet ,wanka yayi tare da sake kaya,ya fito cikin fara tass ɗin jallabiyya. Zama yayi akan wata kujera dake gaban gadon,kujerar tsabar kyanta ,kai kace da zallar kwal akayita.sai ƙamshi yake bugawa, kallon ɗakin yake yana mai mamakin shidai yasan ya fita zuwa kitchen kuma har yayi girki,bayan nan kuma ya nufi dakin Hulwa, kuma... Da sauri ya mike yana mai zafi ido,tabbas asume ya ganta aɗakin ,amma kuma me yasa shi yaganshi ana ?me ya dawo dashi ɗakinsa. Da sauri ya nufi ƙofa yana ficewa daga dakin,saidai yana fita kafin ya kai dakin nata,yaji sanarwar zuwan tareeƙ,kallon kofar Tata yayi sannan ya nufi bakin ƙofar shigowa falon, yana ɓudewa ya ga tareeƙ da kaya riƙi-riƙi ahannunsa. Kallonsa tareeƙ yayi yace "yallaɓai lafiya kuwa? Ahankali Adeeb ya lumshe idanunsa kafin ya jinjinawa tareek din kai,alamu lafiya ba komai. Shigowa tareeƙ yayi da kayan ya ajiye yana mai cewa"yallaɓai idan an duba sai afadamin abinda babu aciki." Nan ma dai kai kawai Adeeb ya daga sannan ya kalli kayan ,ledojine kusan guda goma manya-manya. Kallon Tareeƙ yayi na dan wani lokaci kafin yace "an shirya komai na zuwan gurin mai Abie"? " Eh yallaɓai komai ya kammala ,lokaci kawai muke jira" cewar tareeƙ kenan cikin girmamawa . Jinjina kai Adeeb yayi kafin yace " U can go" "Ok yallabai" Tareeƙ ya faɗa yana mai barin falon . Kayan da tareeƙ ya ajiye Adeeb yayi da kallo kafin ya ɗauki leda ɗaya yana ɗan leƙawa, idanunsa ne suka sauka kan inner wear masu bala'in kyau da tsada,da sauri ya rufe ledar yana ɗan kallon ƙofa, dan sosa kansa yayi kafin ya dauko bra guda ɗaya da hannunsa yana mai kallonta,shiru yayi yana tunanin lallai zatayiwa fattu daidai,dan ahalin yanzu yana kallon abubuwan ta daya taɓa gani a toilet,murmushin yay tare da dan sosa kansa kafin ya ɗauki ledojin duka ahannunsa yayi dakin fattun. Yana tura ƙofar kuwa ya jiyo ƙinkishin kukanta,tana zaune a tsakiyar gadon ta haɗa kai da gwuiwa tana kuka.dan bata wani jima tana barcin ba ta farka kuma ita tsoro takeji taje ta taɓa kofar wannan hulwar ta kuma tsoratata. Da sauri ya ƙarasa cikin dakin yana kallonta,tsayawa yayi akanta bayan ya ajiye ledojin dake hannunsa,sosai yake jin tausayin fattu cikin zuciyarsa,sam baya kyaunar ganinta cikin damuwa,yanzu zaiji zuciyarsa tayi masa zafi sosai. "Hulwa " Adeeb ya furta cikin muryarsa mai sanyi da nutsuwa. Da sauri fattu ta ɗago kanta ,sakamakon jin Muryar Adeeb da tayi, Ai bata san lokacin data diro daga kan gadon nan ba ta wani ƙanƙame Adeeb da iya ƙarfinta tana kuka, "Hammana dama nasan bazaka gudu ka barni ba, Hamma na shiga damuwa sosai lokacin danaga ka koma macijin nan,nayi tunanin guduwa zakayi ka barni Hammana dan Allah karka rabu dani"fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka,wanda zamu iya cewa na farin cikine. ahankali Adeeb ya lumshe idanunsa,tare da sakin ajiyar zuciya"har abada bazan taba rabuwa dake ba,ina tare dake komai rintsi komai wuya hulwatee" abinda Adeeb ya faɗa kenan , cikin zuciyarsa,amma azahiri kawai rungume fattu yayi shima ,yana mai shafa bayanta ahankali. Kuka sosai fattu keyi tana kara rungume Adeeb,bazata iya faɗin irin farin cikin da take cikiba, " Ya isa haka kukan " Adeeb ya faɗa yana mai ɗago kanta.komar da kan nata tayi tare da kara kwanciya akan faffaɗan ƙirjinsa. Murmushi kawai Adeeb ya tsinci kansa dayi,yana mai shafa bayan fattu,sosai yake jin wani nishadi idan fattu ta ruƙunkume shi nan ,ji yake kamar su tabbata ahaka. Bangaren Fattuna dai hakan ne ,ji tayi bata don rabuwa da jikin Adeeb ɗin,dan ba ƙaramin nutsuwa take samu akan wannan ƙirjin nashiba. Kusan minti goma suna rungume da juna ,kafin Adeeb yayi karfin halin cire ta daga jikinsa yana mai cewa" waike bazai sakeni ba saikin karyani?kin fiye son jiki fa" ya faɗa yana ɗan harararta . Kai ta duniyar ƙasa kafin tace "Hamma yunwa nakeji" kallon inda ya ajiye abincin dazu yayi kafin ya janyo table ɗin zuwa gaban gadon, " Zauna "yace mata. Zama tayi abakin gadon tana kallonsa,farin ciki fal cikin ranta. Tea ya haɗa mata sannan ya mika mata flate ɗin kwan da bread zuwa gabanta.wani bowl ya mika mata ta wanke hannunta,kafin ta fara cin abincin,lallai fattu na jin yunwa ,dan kuwa tass ta kawar da abincin nan,shidai kallonta kawai yake,azuciyarsa yace "wannan badai ciba" tana gamawa tayi hamdala tana mai lashe lips ɗinta,ɗago kai tayi suka haɗa ido da Adeeb ,saikuma kunya ta kamata,ganin yadda ta kawar da uban abincin nan. Shikuwa Adeeb cewa yayi " kin koshi ko zaki ƙara dan naga kedin akwai ci kamar Gara" Dan shagwabe fuska tayi kafin tace "Allah Hamma abincinne ke wuce silik -silik,ba dan ma na cinyeba.ta faɗa tana kallon farantin. Ƙureta kawai yayi da ido yana kallonta baice komaiba,dagowa tayi suka haɗa ido ,harararta yayi yace "zaki fara kallonsa ko" girgiza kai tayi tare da maida kanta ƙasa."zanyi sallah Hamma"ta faɗa kanta a ƙasa. Nuna mata toilet yayi da hannunsa ,ba tare da yace komai ba. Mikewa tayi yake bakin ƙofar ta tsaya tare da juyowa. Yana kallonta baice komai ba,dan yasan me take nufi,ita komai bata iyaba Saida yayi jimmm!kafin ya mike ya ƙarasa jinkin ƙofar, ya murda handle ɗin yace "kin gani haka ake yi"jinjina kai tayi tare da mamakin wai ƙifama sai anwani murɗata kamar kan fanfo" Maida ƙurar yayi ya kulle sanan yace "buɗe"kallonsa tayi kafin ta kalli ƙofar, hannunta ta sanya tayi kamar yadda yayi aikuwa saiga ƙofa ta bude.wata dariya ce ta kwacewa fattu ganin tayi nasarar buɗe kofar tace " hahhahhh laaaah Hamma dan Allah kaga abin sauƙi wllh kuma budewa daɗi"ta faɗa tana kara sanya dariya cikin farin ciki. Shikansa Adeeb dariyar tayi har saida fararen haƙoransa suka bayyana.jijjiga kai yayi kafin ya wuce ciki yana faɗin"Allah ya shiryeki" Komai saida ya nuna mata ,sanan yasa ta kunna da kanta,aikuwa fattu gaba ɗaya yau ta zama kamar wata shasha ,data kunna abu yayi zata kama dariya,wataran harda ɗan tsallenta takeyi. Shidai fitowa yayi ya barta dan tayi wanka da alwala. Bude kayan da tareeƙ ya kawo yayi ,wata doguwar pink ɗin riga ya dauko da mahaifinta ya ajiye mata,sannan ya dauko wani fant da bra ya ajiye akan gadon,sannan fice. Bayan fattu tayi sallah ne taga kaya akan gado,ɗauka tayi tana kallon kayan,sunyi mata kyau a ido sosai ,amma saita ajiye da sauri tace "ƙilama na hulwar tasane ,Ni wllh na tsani wannan hulwar" ta faɗa tana hararar kayan. Adeeb me ya shigo cikin dakin da sallama can ƙasan maƙoshinsa. Tsayawa yayi yana kallon fattu ganin bata sake kayan daya ajiye mata ba. " Baki Ga kaya bane kika maida wannan. Dan ƙazanta" Adeeb ya faɗa tana hararar fattu. "Kayi hakuri Hamma nayi tunanin a hulwar taka ne ai" fattu ta faɗa tana daga kayan, "Hamma wannan fa " ta faɗa tana daga bra ɗin nan. " Baki san me ake yi da itaba maza ki shirya ina jiranki" ya faɗa harararta tare da ficewa daga ɗakin. Fattu kuwa data rasa ya zatayi da bra ɗin na sai kawai ta sanya kayanta haka tayi waje . Tana fitowa Adeeb ya biya da kallo ganin bata sanya bra dinba ,yace ........ Mu hade next page banda cajine. Mrs babi ce💘💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 33/34 ________________Fattu kuwa data rasa inda zata maƙala wannan abun ,sai kawai ta sanya kayanta haka ta yi waje gurin Adeeb, kafin ta fita daga ƙofar saida ta buɗe ta rufe kusan sau biyar,idan buɗe saitayi dariya ta ƙara rifewa, sannan ta buɗe,murna take sosai itama yanzu ta iya buɗe kofar yan wata duniyat. Tana fitowa kuwa Adeeb ya bita da kallo, so yake yaga ko tasaka wannan abun,saidai kamar yadda ya tsammata ,bata saka ɗin ba kuwa,dan haka kallonta yayi tare da dalla mata harara yace " kingama shiryawa kenan?" Kai fattu ta daga masa tana gyara lullubin da tayiwa matakin kamar wata amarya,ta rufe kusan rabin fuskarta ,sannan ta kama wuyan ta rike ƙam da hannunta. Shiru yayi yana ɗan wani tunani,shi baisan ta yaya zai faɗa mata cewar tasaka bra ɗin ba,dan haka sai yace" ina wannan abun da kika tambayeni na menene?"ya faɗa yana kallonta. Itama kallonsa tayi kafin tace " na barshi agurin ne ,dan bansan a ina ake sakawa ba" ta faɗa tana ƙara riƙe wuyanta, dan kar mayafin ya faɗi. Kallonta yayi har zaiyo magana sai kuma ya fasa ,wayoyin da tareeƙ ya taho masa da su ya ɗauki daya daga ciki , ya daga tare da kiran tareeƙ . Yana dagawa yace "ka tahomin da make up artist yanzu ta shirya yarinyar nan" "Ok sir " tareeƙ ya faɗa yana mai kiran wata number. "Koma daki" Adeeb ya faɗa yana mai mikewa shima ya bar gurin.juyawa tayi ta koma tana mai tunanin kodai tayi masa wani abunne ? Taji yace ta koma ɗauki?zama tayi bakin gado tana mai cire mayafin nan ,dama duk ya isheta.gashin kanta ta shafa,tun wannan daurin dake kanta ,shine har yanzu,kuma kan nata ƙaiƙayi yake mata amma Indai ta zata ƙaramin wanka saita nemi omo ta wanke kan dashi . Ba komawa saiga tarin ya shigo gidan,waya ya kira Adeeb yake sanar dashi sun karaso. Cewa Adeeb yayi ya nuna mata ɗakin farko shikuma yashigo ɗakin hutu. Kasancewar ba inda tareeƙ bai sani ba acikin gidan,dan haka ya nunawa matar wacce take balarabiya ce dakin yace tayiwa yarinyar ciki duk abinda ya dace . Shikuma ya shiga dakin da Adeeb ke ciki. Da sallama ya shiga dakin,Adeeb na kwance akan gado, ba barci yake ba ,amma idanunsa alumshe suke .zama tareeƙ yayi yana mai cewa" yallaɓai fatan dai kana cikin ƙoshin lafiya" Ahankali Adeeb ya yunƙura ya tashi zaune,kallon tareeƙ yayi kafin ya sauke ajiyar zuciya yace " tareeƙ ina tunanin abinda nayi ne ,kada yarinyar nan taga kamar na cutar da itane"Adeeb ya faɗa yana kallon tareeƙ da yanayin damuwa akan fuskarsa. "Ko kaɗan yallaɓai,idan har tayi tunani zata gane baka cutar da itaba, kuma Allah yaga niyyarka, kayi hakan ne dan kare martabarta da kiyaye hakkin Allah, amma yallaɓai mai zai hana kasanar da ita abinda ke faruwa ,dan gudun samun matsala nan gaba"tareeƙ ya faɗa yana mai kallon ogan nashi . Shiru Adeeb yayi na kusan minti biyu kafin yace" no tareeƙ ,she's too young ace munyi wannan maganar da ita,is better mubar maganar atsaninmu har zuwa lokacin da Allah zai bayyana iyayenta,inyaso saina basu ita ahannunsa,sannan kaga tayi free . "Shikenan yallaɓai amma yanzu kana ganin ,zaka kaita can gidane,ko kuma zata zauna anan?"tareeƙ ya faɗa yana kallon Adeeb da jiran jin me zaice. Kusan minti biyu Adeeb ya ɗauka kafin yace" ko zamanta anan tare dani akwai matsala tareeƙ bana so wataran zuciya ta Kani ga aikata wani abun da zai zamo na cutar da ita,zan kaita can gida gurin ammi ne tunda nima mafi zama can din" ya faɗa yana mai lumshe idanunsa. " Hakan yayi yallaɓai, Allah ya baka nasara akan kudirinka na alkairi" tareeƙ ya faɗa cike da ƙaunar ogannasa. "Ameen "Adeeb ya amsa ahankali tare da kwanciya. Ita kuwa wannan matar mai make up,kasancewar tareeƙ yayi mata bayanin komai tun kafin su zo gidan,dan haka da sallama tashi ga cikin dakin,juyowa fattu tayi da sauri tana kallon matar. Murmushi matar tayi tare da kama hannun fattu ta miƙar da ita tsaye tana murmushi, Kallonta kawai fattu keyi cikin tsoro da rashin sanin ko itaɗin wacece? Cikin harshen larabci matar ke cewa" kai masha Allah yarinya mai kyau da daukar hankali,gaskiya kina da sihirtaccen kyau,ƴata, zanyi Mali kwalliya mai kyau kamar ke" ta kai karshen magannarta tana murmushi. ita dai fattu kallon matar take tana tunanin wannan ɗin kuma daga ina ?wacece?kodai itace hulwar? Ahankali matar ta kama fattu ta zaunar da ita bakin gadon,gashin fattu ta fara warwarewa, " kai masha Allah,kina da gashi mai tsananin kyau,samun irin gashinki ba kowacce mace ba,larabawan ma" matar ta faɗa cikin harshen labarci, Ita dai fattu tayi gurum cike da tsoron matar,gashi kuma ta kasa koda yunƙurin gudawa ne bare ta tsere.haka matar ta kama fattu sukaje toilet ta wanke mata kanta tass,sanann suka fito. Gaban madubi ta kai fattu tare da ɗauki handryer ta busar da kan na fattu,mayuka kala-kala ta shafawa fattu akanta,kan kame tuni kan fattu ya ɗauki wani sheki da ƙamshi, ita kanta fattu wani sawai takejin kan nata. Gyara mata kan tayi sosai sannan ta ɗaure mata shi da wani ƙaton ribom mai kyau. Kwalliya tayiwa fattu cikin nutsuwa ba mai yawa ba,daga powder sai lips da kwalli ta sawa fattu a idonta,irin sakun nan da larabawa keyi,kusan rabin ido. Kai fattu fa tayi mugun kyau fuskar nan Tata kamar farin wata dan haske,kwalliyar ta karbi fuskarta sosai,kodan ba tabayin kwalliyar tayi ba oho? Ledojin nan mata ta buɗe tare da ɗauko wata bakar doguwar riga,dama kuma kayan duk dogayen riguna ne masu kyau da sutura jiki. Har zata dauko su bra,sai taga wata akan gadon ,dan haka sai bata daukoba. Wani ƙaton towel ta ɗauko ,dake gefen kofar bandakin asaƙale ,mikawa fattu tayi tare da cewa ta cire kayan jikinta ,saita sanya bra ɗin sannan tasa kayan nan.cikin harshen larabci matar ke magana.dan bata san cewa fattu bata jin larabci ba,dan kuwa ita tayi tunanin fattun ƴar Misran ce itama. Kallon fattu tayi gurum! Kamar kurma,dan bata san me matar ke faɗi ba.ganin fattu bata karɓi towel ɗin ba tana zaune kawai yasa matar tunanin kodai kurmace? Kwatance ta farayiwa fattu da hannu,cikin ikon Allah kuwa fattu ta gane wai rigar zata cire ta ɗaura towel din .karɓa fattu tayi tare da daura towel din asaman ƙirjinta.murmushi matar tayi tare da ɗaukar bra ɗin ta mikawa fattu.kallon brar fattu tayi tare da kallon matar" tab Ni nasan me zanyi da wannan abun da kina wani mikomin" fattu ta faɗa cikin ranta tana mai turo baki tare da kauda kanta. Murmushin matar tayi tana mai rayawa aranta ,kodai fattun kunyar saka bra ɗin take?dan ga dukkan alamu wannan ne karonta na farko asaka bra ɗin. Cikin hikima da dabara matar ta sakawa fattu bra bayan sun sha artabu,dan fattu sam ƙin yarda tayi da farko, aganinta wannan hulwar so take ta gane mata abubuwa,amma cikin hikima matar tayiwa fattu munin ba ganin jikinta zatayi ba tana son rufe mata jikinta ne,sannan ta dagawa fattu rigar jikinta tare da nuna mata itama ta saka irinta.sai lokacin fattu ta fahimci inda ake saka bra ɗin.ikon Allah wato suma waɗannan abubuwan harda jakar da ake boyewa?lallai zakaga abu da yawa idan baka mutuba. Aikuwa tsif bra din tayiwa fattu ajikinta,Dan dama koda tareeƙ yaje karbowa cewa yayi budurwa yar kimanin 16 za'a haɗawa kayan, Saidai fanties ɗin duk sun mata kaɗan sosai,da gyar matar ta samo mata wani mai kama da gajeren wando sannan tasaka. Da kanta ta sanya rigar ajikinta,masha Allah masu karatu duk wanda yaga fattu awannan lokacin zaiyi tunani wata fattun aka sake,dan tayi kyau har ta gaji da yin kyan. Tauraruwa matar ta fadawa fattu ajikinta masu daɗin ƙamshi,sannan tayi mata rolling ta ɓame da wani kyakykyawan abinda ake riƙe mayafi dashi dan gudun zamewa. Sosai matar ke yaba kyan da Fattun tayi , ga sarƙarta sai walwala take,matar sai kallon sakar take cike da jinjina irin kuɗin da aka batar wajen siyanta,kafin ta kama hannun fattun ta juya da ita gaban madubi.saida gaban fattu ya faɗilokacin datayi arba da kyakyakywar fuskarta jikin madubi,hannu tasa tare da shafa fuskartata,dan tabbatarwa itaɗince kuwa. Ƙuri!! Fattu ta kure kanta da kallo ta jikin madubi,wai dama haka take ko kuma dai ba ita bace wannan ɗin?anya matar nan ba sake mata fuska tayi ba ?dan dan ita bataga tsohuwar fuskarta ta da ajikin madubin ba. Murmushin tayi lokacin data ɗan mintsini hannunta kadan,kuma taji zafi. Wllh nice ,nice fattun baffa, gaba daya na zama ƴar gayu aradu zan tsula tsiya, wayyo Allah na ,ina Hamma yazo ya ganni ,yaga yadda na koma fattu ƴar gayu. Juyowa fattu tayi tana kallon matar nan, fuskarta dauke da murmushi, itama matar murmushin tayi tana yaba kyau da Allah ya ba faytu. Wayar matar ce tayi ƙara hakan yasa ta dauka ba tare da tace komai ba ta kara akunnenta, "To yallaɓai ganin nan" Shine abinda matar ta faɗa tana mai haɗa jakarta ,sallama tayi fattu bayan ta rungume fattun. Koda matar ta fita tsayawa fattu tayi jikin madubin nan tana ƙara kallon kanta,tajita nan ta juya can tana dariya ƙasa -ƙasa. Adeeb ne ya shigo ɗakin sanye da farar jallabiya mai tsananin kyau da ɗaukar ido,kansa kuma hiramine sai wannan baƙin abun da suke ɗorawa asaman hiramin, ba ƙaramin kyau yayi ba sai sheƙi fuskarsa keyi. Tsak !ya tsaya abakin ƙofar yana mai faɗin "masha Allah,watabarakallahu fi ahsanil kaliƙin" lokacin da yayi arba da ƴar gayu fattu,wacce Bama tasan yana gurin ba,kallon kanta kawai take ,ta taɓa nan ta taɓa can. Saida yayi gama ƙureta da kallo,yaga dai idan ya biye ta kallonta to zasu kwana anan ba tare da ya gaji da kallon nata ba,dan haka sai yayi ɗan gyaran murya kafin yace " idan kin gama kalle madubin zo mutafi. Sai lokacin fattu ta an kare da Hammana nata na gurin" cikin jin daɗi ta nufeshi tana murmushi," Hamma kalli yadda matar nan ta sauya min fuska? Wllh gani nake kamar bani ba "fattu ta faɗa tana dariyarta mai burge wa da ban sha'awa. Kallonta kawai Adeeb yake ,dan shikam ya rasa bakin magana ma,gaba ɗaya fattu ta sanya shi cikin wani yanayi na ruɗewa da zallar kyanta. Ita kuwa tana tsaye gabansa sai rangaji take ,jinta take kamar sarauniya yau ɗin nan. Ahankali Adeeb ya kai kallonsa kan waɗan nan abubuwan na fattu, ajiyar zuciya ya sauke ganin yanzu kam ta saka wannan abar.dan haka hannunta kawai ya kamo sukayi waje. Sai lokacin fattu ta sami damar kallon tsarin falon,sama gidan baki ɗaya . Suna tafe amma fattu na waige waige,ikon Allah Allah garin daɗi na nesa,ashe su amaƙabarta suke,anya kuwa wannan gidan ba aljannar duniya bane.ahankali tace " kaikuwa Hamma dan Allah wannan gidan na waye?"ta faɗa tana kallon yadda yake danna nonbibin bude ƙofar. Kallonta yayi bayan sun fito farfajiyar gidan,kafin ahankali yace "nawa ne" Baki fattu ta buɗe cike da mamaki kafin tace " ikon Allah, to Hamma a ina ka sami kudin gina wannan gidan, dan nasan aradu zai kai kusan dubu saba'in ko tamanin " ta faɗa tana irin jinjina kan nan na ta kwaso kudi da yawa. Dariya ce ma ta kama Adeeb ,saidai kasancewarsa ba mai yawan dariya ba yasa yayi murmushi kawai ,kafin yace " ki tara kuɗin da kika faɗa kibani na baki gidan" ya faɗa cikin nishadi,haka kawai yake jinsa cikin wani irin nishaɗi dajin daɗi Kama baki fattu tayi cikin zato ido tace"woooooh Ni ɗiyar baffa,ina zanga wannan uban kuɗaɗen? saidai idan kaina san siyar insamu, Ni wllh bazan gina gida irin wannan ba ma,haba saikace wanda zan zauna da aljanun duniya acikin" ta faɗa tana wani dan taɓe baki irinna rufamin ashirin nan. Kallonta Adeeb ya ɗanyi, yadda take ta zuba masa surutu,ashe dama tana da surutu haka?yanzu ta sake dashi sosai,kuma ya fuskanci idan suna tare sam bata fiye lura da wasu abubuwan da zata gani taji tsoroba. Dai dai nan suka kawo wajen ajiye motoci,kafin su karasa saiga tareeƙ ya fito daga cikin wata rantsatstsiyar mota Black,mai baƙin gilasai,motace yar ubansu wacce kana gani kasan anyi barin kuɗin agurinta. Bude musu motar yayi yana ɗan satar kallon fattu,wai zuƙi haka yarinyar take dama,gaskiya yana fatan Allah yasa wanan alherin da suka ƙalla karya kunce . Harararta Adeeb yayi cikin jin haushi yadda ya kafawa fattu idanu yace " to yi da gaske ka cinyeta" ya faɗa cikin harshen larabci yana hararar tareeƙ . Dan sosa kai tareeƙ yayi yana murmushi,azuciyarsa yana faɗin lallai yallaɓai irin wannan kishi haka kiri-ƙiri?hmmmmm . Shiga motar sukayi fattu na ta kallon yadda motar take wani sukuf da ita ,kamar siffar wani kwaron, Kallon Adeeb tayi wanda ya jingina kansa da jikin kujera as usual idanunsa alumshe. "Hamma wai a wannan duniyar da mukazo, acikin kwarya ake yawo ne?"ta faɗa tana mai riƙe haɓa. Idonsa daya ya buɗe tare da kallon ta ,yana rasa mai zai ce mata dan takaice wai motace ƙwaro,kai fattu sai gyaran Allah. Ganin yayi shiru ta kuma cewa "Hamma yanzu kuma wace duniyar zamu?" Kai Adeeb ya dafe cike da gajiya surutu yace " duniyar cinye mutane masu surutu" ya faɗa yana harararta. Allah Sarki fattu dagalo!!tayi tana kallonsa cikin mutuwar jiki ,kafin ahankali ta ɗan matsa kusa dashi tare da kamo hannun rigarsa ta rike tayi kalar tausayi sosai ,ashe duk murnar da take dama duniyar cinye mutane zasu koma,?shikenan bazata ƙara ganin baffanta ba? Ahankali tace "Hamma baffa.... "Hihhhhhhhh" Adeeb ya fada yana mai ɗora danyatsarsa akan bakin fattu,sannan ya kwanto da kanta zuwa kafaɗarsa. Kwanciya tayi lamo cike da tunani kala kala aranta . Tafiya sukayi mai ɗan nisa kafin naga sunzo gaban wani irin makeken gida mai matukar girma da ƙasa,girman gidan yayi haɗa anguwanni manya guda uku,get suka nufa ,suna idan akaga tareeƙ sai abude masa cikin girmamawa,ba wanda ya kula da Adeeb dake bayan motar,dan glass ɗin bakinsa sosai. Saida suka wuce manyan get bakwai ,kafin suka nufi wani get mai matukar kyau da girma,wani irin walwali get ɗin keyi kai kace da zallar kwal akayishi. Daga samansa kuma wasu danjojine masu ruwan kwal ke rubuta, Well come to the King palace cikin manyan baki. Ahankali get din ya buɗe bayan wata doguwar na'ura ta danno kai ta haske ko ina cikin motar . "Yallaɓai mun karaso" tareeƙ ya faɗa yana ɗan juyowa kadan. Shiru Adeeb yayi yana mai jin wani irin kewa da damuwa azuciyarsa." Tareeƙ how long na dauka ba'asan inda nake ba?Adeeb ya tambaya cikin sanyin murya. "Yallaɓai 5 months 3days" tareeƙ ya faɗa cikin jimami. Runtse idanu Adeeb yayi tare da budewa ,da sauri kuma ya yunƙura tare da dauke kan fattu daga kafaɗunsa,wacce tayi lamo kamar mai barci tsoro duk ya gama cika mata ciki. Fitowa yayi daga motar kafin ya fara takawa cikin nutsuwa da jin kewar iyayensa. Da sauri fattu ta fito daga mota ita ta riga da gudu tabi bayan Adeeb,Allah yasa flat shoe ne akafarta.saurin kamo gefen hiraminsa tayi ta riƙe gan cikin hannunta.yana jinta baice mata komai ba ,har suka kai bakin ƙofar. Ahankali ya nuna fuskarsa jikin wani dan madubi,wani dogon layine naga yana zagaye fuskar tashi,kafin kofar ta buɗe da kanta,yana sanya kafa cikin wani tafkeken falo ,naji wata murya ta dauki Magana," Well come home prince Adeeb Muhammad Ashraf ,your hinest you have a big surprise to see " Masu karatu fattu fa gaba ɗaya ta tsure da ganin irin duniyar da suka shigo,wani irin mahaukacin falone ,wanda ta ko ina matsalar benece acikinsa, ga wani dan banzan sanyi da ƙamshi dake dukan hancin ta.nan da nan jikinta ya kama rawa. Ta rike hannun Adeeb gam-gam cikin nata. Kamo hannun nata yayi tare da kanta zuwa cikin tsakiyar falon,wanda da gyar fattu ke taka ƙafarta dan wani irin kaishi da taji a ƙasa dakin. Zaunar da ita yayi yana mai kallonta, "Ki zauna anan, za'a shigo dake yanzu." Adeeb ya faɗa yana mai kallon yadda jikinta ke tsuma. Hannunsa ta kara damkewa kafin tace "Hamma tsoro nakeji sosai" ta faɗa cikin rawar murya. Hannun nata ya kama ahankali ya kai bakinsa ya sunbata, kafin ya shafa gefen fuskarta ,yace kijirani kinji " yana faɗin haka yabi matakalar dake tsakiyar falon yayi sama. Kallo fattu tabishi dashi cike da tsantsar tsoron wannan guri.hawayene ya zubo mata sharrrrr!! Daga idanunta,ahankali ta sanya hannu ta share wahayen . Shikuwa Adeeb wani haɗaɗden part ɗin naga ya nufa asaman,hadimaine birjik farfajiyar gurin kowa da abinda yake ,tafiya yake cikin sauri da sassafar,ba abinda yake so da buri illa yayi ido hudu da abinsa.wata baiwa ce ta ankare da Adeeb,cikin hanzari ta zube ƙasa tana faɗin Takawarka lafiya ,dan sarki jikan sarki,yarima mai jiran gado,alherin Allah ya kai maka. Da sauri duka suka ankare da abinda baiwar nanke fadi,cikin azama da tsantsar farin ciki sauran ma suka zube ƙasa suna kwasar gaisu da murnar ganin Adeeb,ba wanda Adeeb ya kula kai tsaye dakin mahaifinsa ya nufa. Ahankali ya buɗe kofar cikin sanyin murya yayi sallama. Wani farin Balarabe dattijone kwance akan wani lafiyayyen gado irin na sarakuna masu ji da kansu,gefensa kuma wani likita ne ke ƙoƙarin daura masa ruwa ahannunsa, Sai wani mata guda biyu dattijai, sunsha ado da gwala-gwalai na alfarma ,ko wacce tana inbakiyi bani guri, Sai wani farin matashi zaune kusa da dattijon nan,ya riƙe hannunsa. Cikin azama dattijon ya wani zabura tare da sauƙowa daga kan gadon yana mai goge idanunsa,kafin cikin rawar murya yace " habeebee Adeeb " Ya faɗa tana nuna gofar dakin ,inda Adeeb ke tsaye ,cikin shaukin ganin mahaifin nashi. Gaba dayan yan dakin ne suka biyo suna kallon ƙofar dakin,aikuwa Adeeb ne ya dawo,prince Adeeb ya dawo gida. Da gudu Adeeb ya karaso cikin dakin tare da rungume dattijon nan ajikinsa tsantsan yana mai faɗin," habeebe rurh cikin kuka" Shima kuka kawai dattijon nan yasa tare da ƙanƙame Adeeb ajikinsa. Matan nan kuwa kallon kallo naga sun fara cikin rudewa da shiga kokwanto. Masu karatu muje zuwa yau dai ga fattu cikin gidan sarautar Masar,koya zata kasance? Ga kuma Adeeb jikin mahaifinsa . Sai mun hade next page. Anty mammynku ce Mrs babi💘💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 35/36 _______________Kallon- kallo naga matan nan nayi atsakaninsu, ko wacce tana jifar ƴar uwarta da mugun kallo, yayi da zuciyoyinsu ke buga cike da mamaki . " Habeebee ina kashiga? Me yasami rayuwarka? Na shiga damu matuƙa lokacin da muka wayi gari an nemeka anrasa ba ƙasashen da bamu zagaye ba wajen nemanka, na sanya ƙudede, kadarori,dama kanfanunuwa na ga duk wanda ya kawo min koda labarin in da kake ne,amma bamu sami komai da ya shafeka ba,meke faruwa habeebee?"dattijon nan ya faɗa yana mai shafa fuskar Adeeb hawaye na zuba daga idanunsa. Ahankali Adeeb ya kamo hannun mahaifin nashi ,tare da sumbatar hannunsa ,sannan yace " abie wasu abubuwan basu buƙatar afadesu,saidai kawai mubarsu cikin zuciyarmu, sannan muyi ta kallon azzaluman dake neman ganin bayanmu da bakin halinsu." Adeeb ya faɗa yana mai kallon daya daga cikin matan dake tsaye aɗakin. Kallone irin na duk abinda kike aikatawa akaina, na sani kuma ki kiyaye ranar haduwarmu. Ahankali naga matar cikin ruɗewa da irin kallon da Adeeb ke mata,ta sanya gefen mayafin dake kanta tana goge zufa daga goshinta ,kanta a ƙasa. Ita kuwa ɗayar mata cikin sassarfa ta karaso gaban Adeeb ,hannu tasa akan kumatunsa tana shafawa, hawaye ya gama wanke mata fuska. "Hayatee nayi kewarka fiye da yadda zan fadamaka, naji daɗi da Allah ya kuɓutar dakai daga sharrin mahassada" matar ta faɗa cikin kuka tana mai rungume Adeeb. " Ammina" Adeeb ya faɗa cikin wata irin murya mai cike da kewa ,yana mai rungume matar daya kira da amminsa. Matashinnan kuwa gaba daya ya haɗe fuska ,ba alamun fara'a ko murnar dawowar Adeeb gida atare dashi.zamu iya cewa ma bakin ciki yake da ganin Adeeb ɗin. Zama sukayi abakin gadon ,shida mahaifin nashi,fuskokinsu dauke da mafificin farin ciki da ɗauki ganin juna. " Habeebee ka bani labarin abinda ya faru" mahaifinsa ya faɗa yana mai kwantar da kan Adeeb ɗin akan cinyarsa. Kwanciya Adeeb yayi tare da kamo hannun mahaifin nashi kafin yace " abie ,zan baka labarin komai daya sameni ,amma yanzu baka da lafiya ka huta kayi barci abie na" Adeeb ya faɗa yana sumbatar hannun mahaifin nashi. Dariyar farin ciki abie yayi tare da shafa kan Adeeb yace " ai naji sauki yanzu kam ,wanda yayi silar kamuwa da cutar yazo ya bani magani,bana jin ciwon komai habeebee likita ,zaka iya tafiya" abie ya faɗa yana mai kallon likitan cikin fara'a . Godiya likitan yayi cikin garmamawa ,yana mai taya sarki murnar dawowar Adeeb ɗin gida,dan kowa yasan da batun bacewar Adeeb ɗin. Dubawa nayi cikin dakin naga ya rage daga sarki sai Adeeb da ammi,amma ɗayar matar da saurayin nan tuni sun bar ɗakin. Fattu kuwa tana nan zaune afalon wannan matar ta sauko daga saman sarki cikin wani irin yanayi ,dan ko lura da fattu batayi ba, sai ƙoƙarin kiran waya take . Ba jimawa kuma,saiga wannan kyakyakywan saurayin shima ya fito cikin fushi da bacin rai,kallonsa fattu keyi taba dan hango yanayin kama da sukayi da Adeeb,saidai ko kama ƙafar kyan Adeeb baiyi ba. Harya gota inda fattu ke zaune ,sai kuma ya dawo da sauri ya tsaya akanta. Fattu kuwa da sauri ta mike tsaye tana kallonsa.ganin irin yadda ya tsaya mata akai ƙerere. Shikuwa saurayin nan mai suna,Rashad ,wani irin. Shegen kallo yake bin fattu dashi,tunda ga sama har kasa,wow wannan kayan fa ?daga ina haka?ya faɗa cikin zuciyarsa yana mai kashewa fattu idanu. Haɗe fuska fattu tayi tana mai turo baki tare da kawar da kanta gefe. "Hi babe !" Rashad ya faɗa yana mai ƙoƙarin kamo hannun fattu. Da sauri fattu tayi baya tana mai turo baki tare da biye hannunta abayanta. Murmushin gefen baki yayi tare da shafa gefen fuskar fattu yace " yanzu ina cikin hanzari amma zan nemeki,dan kin kwanta araina kuma yawuna ya tsinke" ya faɗa yana mai wucewa bayan ya sunbaci hannun daya taɓa fuskar fattu dashi. Duk zancen da yake da larabci yake yinsa,dan haka ba abinda fattu ta fahimta cikin zancen nasa.taɓe baki tayi tare da binsa da harara , tana faɗin" Allah ya isa taɓa min fuska da kayi" ta faɗa afili tana mai murguda baki,sannan ta koma ta zauna. Tana nan zaune shiru -shiru agurin nan ,tunanin take ko ina Hamma ya shiga ya barta anan?karfa taje tana zaune kawai taji anfara yankan naman jikinta,ga shegen sanyin falon duk ya isheta. Wani irin ƙamshine ya doki hancin fattu,cikin sauri ta lumshe idanunta tare da budewa tana mai kallon ta inda tajiyo ƙamshin, Masha Allah,wata kyakyakywar budurwace mai tsananin kyau da gayu,taci ado da wata doguwar riga baƙa ,mai tsayin gaske ,dan saida wasu yammata kusa su shida dake Binta abaya suka riƙe kasan rigar,gaba daya wuyanta da hannunta hatta gashin kanta anyi masa ado ne da kwal,tayi kyau matukar gaske,kallo daya zakayi mata kasan tana cikin farin ciki,dan kuwa sai murmushi take,tana tafiya ɗas-ɗas cikin salo da yanga. Kallonta kawai fattu keyi cike da tunanin wannan ɗin ko wacece?amma gaskiya ƴar gayuce ta gaske,nima nan gaba irin wannan kwalliyar zan riƙayi inji ta yanga abina.fattu ta faɗa cike da murmushi tana kallon budurwar. Ita kuwa budurwa tana karasowa tsakiyar falon ,idonta ya sauƙa akan fattu,dammmm !taji gabanta ya faɗi, wannan ɗin kuma wacece?daga ina haka?me takeyi acikin babban falo?budurwar ta faɗa cikin zuciyarta ,tana mai jin wani irin tsabar fattu cikin zuciyarta,dan saitaga duk yadda take taƙama da kyau wannan yarinyar tafita,saidai kawai tafi wannan wayewa da sanin duniya. Kallon -kallo aka fara tsakanin fattu da wannan budurwa,ba abinda ya ƙara batawa budurwar nan rai irin yadda fattu ta tsareta da ido,wato ko shakkar ta ma batayi. Cikin takunta na isa da rangwada ta ƙarasa gurin da Fattun ke zaune, Kallon wulaƙanci take yiwa fattu tana wani yamutse fuska. " Wacece ke? Budurwar ta faɗa cikin harshen larabci. Kallonta fattu tayi ba tare da tace komai ba,dan bata san me take cewa ba. Ran budurwar ne ya ɓaci sosai,hannu tasa tare da fizgo fattu ta kama kwalar rigarta, cikin isa da gadara take faɗin" ke kinsan komi wacece ina miki magana kika shareni?ke ƴar uban waye marar kunya?"budurwar ta sake faɗa cikin fushi, Fattu kuwa cikin jin zafin abinda budurwar tayi mata ta ballawa budurwar harara tare da ture hannun budurwar daga wuyanta,tana mai murguda baki. Gaba daya hadiman da suka taki budurwar nan zato ido sukayi,cikin tsoro da tausaya wa fattu ,dan ta tabka babban kuskure. Zato ido budurwar tayi itama tana mai kallon fattu ," kee!!! Ni kika turewa hannu?lallai minti babban kuskure.budurwar ta faɗa tana mai ɗauke fattu da wani lafiyayyen mari, kafin fattu da gama dawowa cikin hayyacinta ta sake jin wani zazzafan marin a dayan kumatunta. Wani irin azabar raɗaɗine ya ziyarci fuskar fattu,cikin hanzari ta dafe duka kumatunta tana kallon budurwar nan,nan da nan zuciyar ƴaƴan Fulani ta motsowa fattu, ai batasan lokacin data ɗaga hannu itama ta shararawa budurwar nan matuka har biyu ba....... Manage please my fans, Wllh am seek. Mrs babi ce💘💘💘🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 37/38 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din ________________cike da zallar madarar mamaki budurwar nan ke kallon fattu,tunda take arayuwarta ba wani mahaluƙin daya taɓa daga hannu da sunann ya faɗa mata koda baƙar magana ne, amma wai yau itace tsaye gaban wata kucakar yarinya,sannan agaban bayinta ,dafe da kunci,wai da sunan an sharara mata maruka har biyu? Lallai wannan yau ko ƴar gidan uban waye saita gane kurenta, zata san cewa ni Zulaihat nafi ƙarfin awulaƙantani ,kuma azauna lafiya. Gaba ɗaya barorin gimbiya Zulaihat atsorace suke ,kuma kawunansu sunkuye a ƙasa, yayin da zuciyoyinsu ke bugawa cikin tsoro da fargabar abinda zai biyo baya. Fattu kuwa tana tsaye riƙe da ƙugu,ta ƙurawa gimbiya Zulaihat idanu,kamar yadda itama ke kallon fattun,lokaci ɗaya fattu taji mugun tsabar Zulaihat cikin zuciyarta,haka kawai zata wani daga hannu ta dallamin uban mari?ai wllh saidai acinyeni agidan nan,amma idan wannan banzar tayi min abu saina rama dan ba tsoronta nakeji ba ehe.fattu ke wannan zancen ,cikin zuciyarta tare da murguda baki bayan ta kammala zancen zucinta. H Ahargitse gimbiya Zulaihat ta fara juye-juye ,can ta hango wani ƙarin flower vase na tangaran,da hanzari tayi gurin da tare da rarumoshi tayi kan fattu tana huci. Tsorone ya gama kama fattu,yanzu idan ta jibga mata wannan ƙaton abun akai ,ai wllh sai kanta yayi raga-raga,tab yaseen bazata tsaya ba.baya fattu ta farayi cikin tsoro tana mai kallon gimbiya Zulaihat, Ita kuwa gimbiya zulaihat ganin fattu na ƙoƙarin gudawa yasa ta dakawa hadimanta tsawa akan su riƙe mata fattu,wani irin zafi takeji cikin zuciyarta,wllh zata iya kashe fattu yadda takejin tsanar fattun cikin ranta,dan haka tayi rantsuwa yau saita illata fattu,ta yadda ko hannunta bazai ƙara moruwa ba,bare ta sake gigin marin wani. Cikin azama kuwa suka tsakumi fattu suka riƙe ta,ihu fattu ta fara cike da tsoron abinda matar nan zata mata," wayyo Allah na Hamma kazo, zasu cinyeni danya da raina ,wayyo hammana!wayyo Hamma kana ina!! Fattu ta faɗa cikin ihu,lokacin da tajita ahannun waɗannan manyan yan matan masu shegen ƙarfi. Zulaihat kuwa cikin rashin imani da tsana take faɗin,"wllh yau saikin komi wacece ,kin siya babban kuskuren taɓa Zulaihat,kuma yau zaki girbi abinda kika shuka" Zulaihat ta faɗa cikin fushi tana daga wannan flower vase ɗin da iya ƙarfi ta zata sakarwa fattu. "Zulaihaaaatttttt!!!!" Aka kwalla kiran sunan gimbiya Zulaihat din ,cikin wani irin sauti mai ƙarfin gaske ,wanda saida dukansu suka tsorata . Afirgice Zulaihat ta saki flower vase ɗin nan daga hannunta ya fadi ƙasa. Ba kowa bane yayi mata wannan bahagon kiran face Adeeb ,wanda ya fito ne dan shigowa da fattu gurin mai martaba,lokacin ya gama basu labarin irin taimakon da fattu da baffanta sukayi masa ,da kuma dalilin tahowa da ita nan ɗin .shine mai martaba yace ya shigo da ita ciki. Dama kuma yana zaune ne ,amma zuciyarsa tana can gurin fattu,dan yasan ta da shegen tsoro,abu kaɗan ne zai firgitata. Dan haka cikin sauri yake tafi lokacin daya fito daga part ɗin sarki, Yana doso babban farko kuwa ya fara jin ihuj fattu tana kiran sunansa.dan haka da gudunsa ya ƙaraso cikin falon,yana zuwa idanunsa sukayi masa mummunan gani,Zulaihat na ƙoƙarin illata masa Hulwa. Cike da tsoro bayin nan suka saki fattu tare da zubewa kasa suna gaida Adeeb. Wani shegen kallo da Adeeb ya watsa musune yasasu ficewa daga falon da gudu cike da tsantsar tsoro . Fattu kuwa da gudu ta nufi Adeeb tana kuka,cikin sauri shima yake saukowa daga matakalar benen, uku -uku,hurhuɗu yake tsallake step din, atsakiya falon suka hade da fattu,tana zuwa ta faɗa ƙirjinsa tare da ƙanƙame shi tana kuka."Hamma mutafi daga gidan nan,tsoro nakeji,wannan matar muguwace daga zuwa ta ta mareni har sau biyu,kuma tasa wadancan doyoyin suka rikeni wai zata baremin kai" fattu ke faɗin haka cikin kuka tana kwance akan ƙirjin Adeeb. Wani irin tausayin fattu ne yake mamaye ilahirin jikin Adeeb,tare da tsantsar jin haushin Zulaihat cikin ransa. Ahankali yake shafa bayan fattu yana shiiiiiiiii da bakinsa alamun rarrashi. Idanunsa sun kada sunyi mugun jaaaa ya kafesu akan fuskar Zulaihat,wacce tayi mutuwar tsaye tana kallon wannan yarinyar kwance akan ƙirjin Adeeb,wanda ita bata taɓa samun wannan damar ba.banda bugawa ba abinda zuciyarta keyi,lallai akwai gagarumar matsala,wacece wannan yarinyar?meye alaƙarta da Adeeb? Cikin daukewar tunani da tsananin kishi daya rufewazulaihat idanu,kunsan matan larabawa da bakin kishi,Zulaihat ta nufi kansu Adeeb gadan -gadan.tana zuwa ta sanya hannu tare da ƙoƙarin fizge fattu daga jikin Adeeb. Wasu zafafan marukane guda biyu suka sami gurbin zama akan fuskar Zulaihat ɗin,wanda sun fitowa daga hannun Adeeb. Kusan minti biyu Zulaihat ta dauka kafin ji da ganinta sudawo daidai. Ihu ta kurma cikin azaba tana mai dafe kumatunta" habeebee nika mara?akan wannan jakar?wacece ita?meye alaƙarka da ita ? Da har zata kwanta akan ƙirjinsa,kaikuwa kana rarrashinta?Zulaihat ta faɗa cikin kuka da rikicewa. Wani matsiyacin kallo Adeeb yayi mata, yana mai gyarawa fattu kwanciyarta akan ƙirjinsa kafin yace " ita ɗin mutumce mai matukar muhimmanci arayuwata,mafi kusanci da zuciyata wacce zan iya aikata komai akanta,ki kiyaye nan gaba,hukuncin da zan miki bazaiyiwa kowa daɗi ba " Adeeb ya faɗa cikin wata iriyar murya mai kama da ta basasa,yana mai nuna Zulaihat da hannunsa. Cikin karawa kukanta ƙarfi Zulaihat tace" kana nufin harni,tafini muhimmanci agareka?" Ta faɗa cikin ruɗu. Wani banzan kallo Adeeb ya wurgawa Zulaihat kafin yace " ke wacece?wane matsayi kike dashi agareni,karki ƙara haɗa kanki da Hulwa banza shashasha marar zuciya da kamun kai " Adeeb ya fada yana mai juyawa da fattu suka fara tafiya zuwa sama. Cikin kuka kamar zata shiɗe Zulaihat tace " wacece ita" Saida sukayi taku kusan uku ,kafin Adeeb ya juyo cikin murtukakkiyar fuskarsa yace " MATA TACE ita" ya faɗa yana mai tsare Zulaihat da idanu. Wani wasan ihu Zulaihat ta kwalla tare da ficewa da gudu ta nufi waje. Harara Adeeb ya bita dashi kafin ya juya suka ci gaba da tafiya ,duk abinda suka faɗa fattu batasani ba, dan da Yaren larabci sukayi maganarsu. Saida sukaje bakin ƙofar part ɗin sarki sannan Adeeb ya tsaya tare da gogewa fattu hawayenta.yace "kinga duk kin bata kwalliyarki da hawaye, kiyi shiru zamuje gurin abie ne yanzu kinji?karki damu bazata ƙara yi miki komai ba"ya faɗa yana mai riƙe kumatunta. Kallonsa fattu keyi tare da shagwabe fuska tace " Hamma Ni tsoro nakeji" "Ba abinda zai sameki ,bagani ba?" Ya faɗa yana kama hannunta suka shiga dakin abie. Zulaihat kuwa tana ficewa daga falon,kai tsaye mota taje ta shiga tana kuka kamar ranta zai fice,da mugun gudu take tafiya hatta bar cikin masarautar ,kai tsaye wani hotel ta nufa tana zuwa dama akwai dakin dake amazaunin nata cikin hotel ɗin. Fridge ta buɗe tare da ɗauko wata kwalba ta buɗe cikin sauri tare da kafa kai ,saida ta shanye abinda ke ciki tass kafin ta jefar da kwalbar. Waya ta dauka tare da kiran wata number tace tana jira. Ko minti biyar ba'ayin saiga wani saurayi kyakyakywa ya shigo ɗakin ,yana zuwa lokacin harta fara fita daga hayyacinta ,tana surutai," saina kasheta ,saina ranta da yarimana ,nawa ne Ni kadai. Rungume saurayin tayi suka fara aikata alfasharsu,subhanallah,Zulaihat Allah ya shirya. Adeeb kuwa suna shiga dakin abie ,fattu ta kama gefen rigarsa ta rike gan! Cikin hannunta .ammi ce ta ƙaraso tare da kamo hannun fattu tana murmushi tace "ƴata yar albarka sannu kinji" ammi ta faɗa tana mai rungume fattu. Abie ma murmushi taye yana mai kallon fattu ,lokaci ɗaya yaji yarinyar ta kwanta masa arai tana da hankali da nutsuwa. Nan ammi tace agurinta fattu zata zauna ,ita zata kula da ita ,sannan zata taya Adeeb cigiyar mahaifan fattun. Bayan sati guda Sarki ya hada wani gagarumin taro na farin cikin dawowar babban dansa magajin faɗa,wanda aka gayyato sarakuna daga kasashe daban -daban. Kuma nan da kwana biyu taron zai gudana,dan haka gyara ake yiwa masarautar sosai.ko ina ka kalla an gyara shi yayi mugun kyau, Adeeb kuwa shima yanzu ya shiga busy,yana ɗan bin kamfanoninsa na kasashe daban -daban yana duba yadda harkokin ke tafiya,dan haka yau kwana hudu baya gida .kuma basu hadu da fattu ba . Gaba ɗaya fattu ta shiga damuwa,kullum tana cikin dakinta da aka bata mai shehun kyau,saidai akawo mata abinci taci ,tayi wanka ta kwanta. Ko falo baya fita.itama ammi gaba ɗaya bata zama tana ta uzuri. Gashi bata ita tare su ba,Gara ammi wataran takan dan yi mata Hausa kadan kadan. Yau dai fattu tana zaune shiru ,tace bari ta fito falo dan yasan huta kuma ta duba Hammana. Tana sanye da doguwar riga milk mai fadi kanta yanke da mayafin rigar,ba kwalliya akan fuskarta amma tayi kyau sosai. Falon ta fito tana binsa da kallo,ya hadu iyakar hafuwa, sai ƙamshi ke tashi ta ko ina. Tana ɗan zagayenta afalon ,taji anbude kofa. Juyawa tayi ɗan ganin waye ya shigo, Rashad ne ya shigo ɗakin shida zulaihat.suna tafe suna dan magana ,da alama kuma rarraba jin Zulaihat ɗin yake. Turus suka tsaya suna kallon -kallo atsakaninsu su ukun. Ita dai fattu kallonsu take tana tunanin,dama wannan matar agidan nan take ?tun ranar bata sake ganinta ba,sannan Kuma ta gane wannan. Saurayin,shine wanda ya taba mata kumatu awancan ɗakin,dan haka da sauri fattu ta kawar da kanta gefe tare da hade fuska, nemar guri tayi ta zauna akan lumtsuma luntsuman kujerun da suka yiwa falon ƙawanya. "Kai !!Rashad me wannan fitsararriyar keyi anan?aikuwa wllh saina koya mata hankali"Zulaihat ta faɗa tana ƙoƙarin ƙarasawa kusa da fattu. Da sauri Rashad ya riko hannunta yana mai faɗin "haba -haba ke matsala ta dake gaggawa ,ba yanzu muka gama magana dake ba,zaki taimakeni,nima zan taimakeki, cikin sauƙin kowa ya sami abinda yake so. Idan kika yi wani abu yanzu ,to shirin mu ga zai wargaje,kuma kinsan wancan horon bashi da sauƙi ko kaɗan.ba dai jini ne za'ayi taron nan ba? Rashad ya faɗa yana mai sakin wani shegen murmushi. Jinjina kai Zulaihat tayi tana mai hararar fattu. Cigaba Rashad yayi da maganarsa"to ki kwantar da hankalinki, ranar zamu aiwatar da ƙudirinmu akanta ,zamu tarwatsa koma menene ke tsakaninsu,Ni sam na kasa gane inda ammi ta dosa ,bata bamu goyon baya kamar yadda ya kamata,amma zamuiyi komai da kanmu. Kedai kawai ki danne zuciyarki akan komai har zuwa jibin" Rashad ya faɗa cike da ƙarfafawa Zulaihat gwuiwa. Jinjina kai tayi cikin murmushi tace " nasanka nasan halinka,kuma zaka iya Allah ya nuna mana lokaci, amma wllh na tsani yarinyar nan sosai acikin raina" Zulaihat ta faɗa tana hararar fattu. Fattu kuwa murguda mata baki tayi itama tana mai cewa cikin ranta" oho dai saidai kiyi ta hararata amma wllh baki isa ki doke in gyaleki ba ,ba ruwana da wani kin girmeni ehe" fattu ta faɗa tana mai dan dukan cinyarta har saida ƙaran ya fito sukaji. Kallonta sukayi gaba dayansu ,Zulaihat tace ka "gani ko dukda batasan me muke cewa ba,amma kalli abinda take ?wllh daka barni na tattara yarinyar nan,ai Prince baya gida bare yace wani abu"Zulaihat ta faɗa cikin muryar bacin rai. "No karki fara,ko baya gida yanzu ai kinsan zai dawo ko?kuma ma gaskiya bazan bari ki taba min kayana ba,dan gaskiya ina hango hutu agurin man sosai " Rashad ya faɗa yana wani kashe ido tare da kallon fattu. " Wllh Ni haushi ma kake bani ,akan wannan kucakar zaka wani tsaya bata lokacinka,me zaka samu jikin wannan banzar?"cewar Zulaihat cikin haushi. " Ke wllh ƙarya kike kinsan wannan yarinyar tafiki komai na mata ,kalleta mana da kyau ki gani ,aikinsa ba karya ,malam komai yaji yadda ake bukata" cewar Rashad cikin wani irin shegen voice . Tsabar haushi daya kama Zulaihat tashi tayi afusace ta bar falon tana ƙunƙuni. Adeeb yana can ƙasar farin yana gudanar da binciken kasuwanci sa ,gefe guda kuma ya dage sosai wajen neman iyayen fattu,yasa hoton sarkar nan Tata da rigarta tare da nuna yana neman wanda yasan waɗan nan kayan,saidai bai yarda ya nuna wata alama da zata nuna shike neman wanda yasan wani abu game da kayan ba,dan nunawa yayi shidin talaka ne sosai . Kullum suna waya da ammi yana tambayarta fattu ,sannan yace ta rinƙa koya mata Yaren larabci ,kuma ammi tana kokarin koyawa fattun ,dan yau take son kawo tsohuwa salima ,ta zauna tare da Fattun dan ta koya mata Yaren sosai,tunda ita ta iya hausa sosai.kuma kusan ahannunta Adeeb ya girma ,ita tayi renonshi. Wai ina batun baffa ne? Allah Sarki baffa lokacin da aka kaishi dakin hukunci ,saida yayi kwana biyu basu wai-waiceshiba,yana can yana fama da zazzabi sakamakon dukan da sukayi masa.sau daya ake kawo masa abinci. Ranar kwana na biyun ne da yamma aka fito dashi dan zartar da hukunci,lokacin mai gari ya danji dama -dama an gyara masa karayar daya samu har uku .jauro kuma yana nan cikin halin bakin ciki,dan kuwa jauronsa ta lalace ,bazata ƙara amfanuwa ba,ta motse ta zama ƴar ririya kamar sillen kara. Shiruwa abokin ta'asar tashi,yanan ido daya ya tsiyaye ,rabin fuska ya zagwanye ,ya zama kamar horo,arɗo ma hannu ya shanye ya zama kamar lauje. Cikin fushi da bacin rai tare da bakin ciki mai gari yace , sakamakon ta'adda cin da baffa da yar shegen daya kawo musu cikin gari sukayi,an karbe duk wasu shanayensa da tumakai harda gidansa ,matsayin diyyar abinda mayyar daya kawo gidansa tayi,sannan ankoreshi daga garin ,saboda ƙarya da cin amanar yan garin da yayi ,na cewa fattu yarsace. Baffa yayi kuka sosai,akan wannan rashin adalcin da akayi masa.amma haka ya haƙura ya miƙawa Allah lamarinsa. Koda ya dawo gida tuni labari ya isa kunne gwogwgo hansai,dan haka yana shigo taci kwalarsa tace ya bata takardar ta bazata iya zama da faƙiri ba. Nan take kuwa baffa yayi mata saki daya .kuma sam ta hana ƴaƴan ta subi baffa. Shi kadai ya bar garin cikin mawuyacin hali. Allah Sarki baffa ,Allah ya saka maka wannan zalumcin da akayi maka. Acan misra kuwa ,amma na hango zaune akan wata ƙayatacciyar kujera , da waya ahanunta ,magana take cike da nuna yanayi na jimami, masu mata hidima na can gefenta azaune. " Zanyi duk iya ƙoƙarin na,ɗan ganin naja yarinyar ajikina, in Sha Allah muke da nasara" amma ta faɗa tana mai ajiye wayar. Murmushi tayi kafin tace" Maryam zaki san koni wacece ,zanyi abinda saiya girgizaki,saina rabaki da dan da kike takama dashi" amma ta faɗa tana mai gutsirar apple. Amma dai itace kishiyar mahaifiyar Adeeb,wacce lokacin da Adeeb yazo ta bar ɗakin mahaifin Adeeb cikin ruɗani. Washe gari da safe fattu ta tashi da wani irin matsanancin ciwon mara,sai kuka take tana riƙe da cikinta. Tsohuwa salima nata rarrashinta tare da bata haƙuri,dan tana tunanin period me zai yiwa fattun. Sosai fattu ke jin mugun ciwon mara,sai murƙususu take cike da azaba tana kiran " Wayyo Hammana zan mutu " Wani irin amai ne ya yunkuro mata,da gudu ta mike ,da nufin zuwa toilet ,saidai taku daya biyu, jiri ya kwasheta ta tafi luuuuuuuu tayi kasa..... Masu karatu masoya,ina godiya da addu'ar ku gareni ,kuma jiki alhamdulillah naji sauƙin sosai , Na gode sosai da kulawa, Much luv sosai da sosai. Mrs babi ce 💘💘💘 Share and comments Fisabilillah. More comments More typing.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 39/40 ________________Wani irin amaine ya tasowa fattu,dan haka da gudu ta mike tana mai riƙe baki,sannan ta nufi toilet.saidai taku ɗaya -biyu tayi kiri ya kwasheta,baya tayi luuuuu!!!zata faɗi.da sauri ta runtse idonta tana mai saki wani ɗan siririn ihu,gaba daya ta gama saddaƙarda cewa ta fadi ,jira kawai take taji ta ina zata fara jin raɗaɗin.saidai maimakon tajita aƙasa,sai taji ta faɗa jikin mutum,wani irin ƙamshine ya ziyarci hancinta mai daɗin gaske,da sauri ta buɗe idanunta dan ganin jikinwa ta faɗa. ido hudu sukayi da Hammanta, dan shigowarsa kenan dakin ya hangota zata faɗi ,shine yayi saurin tarota, dama yana sauka afadar ko gurin mai martaba baijeba yayi sashin ammi,duk kuwa da cewar maimartaban yana ta kiransa awaya akan ya dawo gida . Dan kumshe ido fattu tayi cikin azabar ciwon da mararta keyi ,sannan ta buɗe idonta ,tare da saukesu akan Hammanta,so take ta gasgata shiɗin ne ko gizo idonta keyi. Aikuwa shine wllh Hammanta ne ya dawo,cikin azama kuwa fattu ta rungume Adeeb tare da sakin kuka,dama kuma kukan take. " Hamma ina katafi ka barni?inata nemanka amma banganka ba?dan Allah Hamma karka ƙara tafiya ka barni,kaga bani da lafiya cikinsu ciwo yake min sosai" fattu ta faɗa tana mai cusa kanta aƙirjin Adeeb . Ahankali Adeeb ya lumshe idanunsa tare da rungume fattu shima tsan-tsam ajikinsa,dan kuwa tabbas ba karya yayi kewar fattu sosai ,kullum da ita yake kwana yake tashi,kwana uku da yayi baya ganinta ,jinsa yake kamar mara lafiya. " Is ok stop crying hulwa,ai gani na dawo ko?"ya faɗa yana mai ɗago kanta . Buɗe baki tayi da nufin yin magana ,amma gaba daya aman nan ya taho mata ,aiku ba ɓata lokaci ta wanke Adeeb tass!! Da aman nan ajikinsa. Shikuwa Adeeb ko ajikinsa ,bai damu da aman da tayi masa ba ,ya riƙe ta sosai ajikinsa yana mai shafa bayanta,tausayinta yake ji har cikin ransa,bata da lafiya sosai dole ya kira likita adubata. Tsohuwa salima ce ta karaso garesu tare da faɗin"ayya sannu fateema kinji,maza kawota kaje ka wanke jikinka, wllh tun jiya take fama da ciwon cikin nan,nace yaro kodai girma ne zaizo mata?tsohuwa ta faɗa tana mai kallon Adeeb, Dan sunkuyar da kansa yayi ƙasa yana mai sosa kai,dan ya gani abinda tsohuwa ke nufi,ita haka take dama ba ruwanta idan zata faɗi magana,kai tsaye take faɗi. " Ammm nanny bari na kira likita ya dubata. Ya faɗa yana nufar toilet riƙe da fattu,wanke mata jiki yayi tare da bakinta, shima ya wanke inda ta batashi,sannan ya dawo da ita cikin ɗakin, kwantar da ita yayi akan gado tare da shafa gefen fuskarta yace"sannu yanzu za'a baki magani kinji?"ya faɗa cike da tausayawa,ji yake kamar ya maida ciwon jikinsa. Lumshe ido fattu tayi tare da kamo hannunsa ta rike gam cikin nata tace"Hamma karka tafi dan Allah" fattu ta faɗa tana mai lumshe idanunta . Hannun nata ya riƙe da ɗayan hannunsa kafin yace "ba inda zani zan sake kaya in dawo yanzu" ya faɗa yana mai mikewa tare da ficewa daga dakin. Tare suka dawo shida likita,wadda ta kasance likitar gidan ce , mai duba mata. Sosai ta duba fattu ,kuma ta gane period ke don zuwa mata ,kuma farkon yine shiyasa take jin ciwo. Dan haka bayani tayiwa Adeeb tare da bashi magungunan da Fattun zata sha.sannan ta lika always Jikin pant taba nanny akan idan jinin yazo saita bata tasanya. " Yawwa Ni dama nayi tunanin ko girma ne zatayi ,dan ciwon yayi yawa,Allah Sarki ashe kuwa shine ,bari na haɗa mata tea mai zafi ta sha"nanny ta faɗa cikin tausayawa tana mai nufar kitchen. Shidai Adeeb yana zaune bakin gado,tunda yaji abinda ke damun fattu,baice komai ba ,kawai yana kallonta dan ta ɗan sami barci . Cikin girmamawa likitar tayiwa Adeeb sallama ta fita akan zata dawo anjima . Kai kawai ya ɗaga mata ba tare da ya kalletaba. Kusan minti biyar saiga nanny ta dawo riƙe da wani kyakykyawan kofi sai turiri yake ,mikawa Adeeb kofin tayi tana mai cewa" ungo magajin faɗa tashe ta maza ta sha zatayi daɗi,kuma jinin zai sauko da wuri" ta faɗa tana mai nufar ƙofa again tana cewa " bari i ke in kula da farfesun can dana ɗora mata,kasan shima yana taimakawa mace idan tana jini"ta faɗa tana ficewa. Kallo Adeeb ya bita dashi,yana mai girgiza kai,yana son tsohuwar nan ,saidai tacika surutu da sanya mutum jin kunya. Ahankali ya ɗan shafe fuskar fattu da tayi wani fayau da ita ,sai kyalli take,ahankali ta buɗe idanunta tare da saukewa akan kyakykyawar fuskar hammata. "Hamma" ta furta ahankali tana kallonsa. " Tashi Kisha tea maza" ya faɗa yana mai taimaka mata ta zauna bayan ta sanya mata fillo abayanta. Da kansa yake bata tea ɗin abaki,saida tasha kusan rabi sannan tace ya isheta, ajiye sauran yayi yana mai kallonta kafin yace" ya kike jin jikin naki?" " Da sauki Hamma saidai jikina ba kwari ,kuma har yanzu inajin ciwo anan dina"fattu ta faɗa tana mai nuna masa saitin marar ta. Kawar da kai yayi da sauri yana mai cewa" is ok zai daina " " Hamma zanyi fitsari" fattu ta faɗa ahankali. Dan kallonta yayi kafin yace " zaki iya zuwa toilet ɗin?" Kai ta daga masa tana mai yunkurawa ,tashi tayi tsaye tana ɗan yamutse fuska. Sai taji kamar lema ajikinta,juyawa tayi tare da kallon inda ta tashi,zato idanu tayi lokacin data jini agurin,da sauri ta kai hannunta ta shafo bayanta ,tana mai kallon hannun,aikuwa jini ne kuma daga jikinta ya fito,ƙara zato idanu tayi cikin tsoro tana mai faɗin" na shiga ukuna Hamma jini ,jine yana zuba ajikina,wayyo Allah Hamma jini"fattu ta faɗa tana mai nuna masa hannunta ,jikinta na rawa sosai kamar ana kada mata gangi, Kallonta Adeeb yayi da sauri ,yana mai kallon hannun nata ,lumshe idanu tayi yana mai jin wani iri ajikinsa,tausayi fattu ke bashi,ita bata san komai ba ,yanzu meye abin damuwa akan wannan ga yadda jikinta ke rawa kamar ana yankata.? Ahankali ya mike tsaye tare da dafa kafadun fattun yace " ki nutsu mana ,wannan ba wani abun damuwa bane kinji dama hakan na faruwa ga ko wace mace data kai shekaru irin naki" yayi shiru yana ɗan sauke nunfashi ahankali. Fattu kuwa kuka take tana cikin tashin hankali,sam Bama tajin me Adeeb ke faɗi,sai cewa take " Hamma jini ajikina, dan Allah kace ya daina zuba ,na shiga uku jinina zai kare wayyo baffana" abinda take fadi kenan jikinta na rawa . Gaba daya Adeeb yana rasa me zaicewa fattu,dan haka kallonta kawai yake cikin damuwa,suna cikin haka saiga nanny ta shigo, ajiyar zuciya Adeeb yayi tare da kallon nanny amarairaice. " Aa meke faruwa ne haka magajin faɗa?(da yake haka take kiransa) taci gaba ,naga fateema na kuka ,kaikuma ka tasata gaba da kallo kaima kamar salati kukan?nanny ta fada tana mai karasowa cikin dakin. Ahankali Adeeb yace "nanny kiyi mata bayani kuka take, wai bata so" ya faɗa kamar zaiyi kuka. "Yau naga ikon Allah fateema meye baki so?ko maganin ne baki don sha?kiyi haƙuri ai lafiya ake nema miki kinji ?kuma da kinsha jinin zai....sai kuma tayi shiru tare da bin gadon da fattu ta tashi da kallo,to kace jinin ne yazo ,wato shi tagani take cewa bata so,Allah Sarki ai zaki saba dayake wannan ɗin na farko ne ,zo muje In gyara miki jiki yi shiru" nanny ta faɗa tana mai kamo hannun fattun suka nufi toilet. Kallonsu Adeeb yayi tare da sauke ajiyar zuciya ,sannan ya fice daga ɗakin,bayan ya janye zanin gadon daga kan gadon,ya ajiye gefe guda,tare da shimfida wani. Kai tsaye gurin mai martaba ya nufa,yana shiga ya tadda mai martaba tare da amma, zama yayi kusa da mahaifin nashi,bayan ya jefa wa amma wani kallon na tsana . Kawar da kai amma tayi tare da sakin murmushin gefen baki tace yaro yarone ,cikin zuciyarta. " Habeebee Barka da dawo ,yanzu nake ƙoƙarin sake kiranka,ai najika shiru,kasan yanzu bana son koda da minti ɗaya ka ƙara nisa dani"abie ya faɗa yana mai shafa kan Adeeb. Murmushi Adeeb yayi tare da sumbatar hannun mahaifinsa kafin yace " abie wancan karon ma ,kaddarace ta sameni,har Allah ya ba maƙiya nasara akaina,saidai ahalin yanzu kar nake kallon,kowa sannan ba abinda mutum ya isa yayimin na cutarwa in Sha Allah" Adeeb ya faɗa yana mai kallon ammi cike da tsana . Itama ammi kallon Adeeb take ,tana mai suna maganganunsa ,kafin ta sauke ajiyar zuciya tayi sallama da mai martaba tare da ficewa daga ɗakin. Waya ta dauko tana mai kiran wata number tace " mu hadu yanzu-yanzun nan" sannan ta kashe wayar. Adeeb yana fitowa daga ɗakin abie ya nufi bangaren da amminsa ke hutawa, Wayace akunnenta kuma da alama wayar da take mai muhimmanci ce ,saidai tana hango Adeeb ya tunkarota tayi saurin katse wayar tana mai cewa " zan kira -zan kira" bata jira amsar dayan vangaren ba ta kashe wayar. Zama yayi kusa da ita tare da kamo hannunta ya sumbata, kanshi ta shafa taba faɗin Allah yayi maka albarka. Ya jima suna dan hira ,kuma duk akan kunyar fattun ne ,kafin ya mike yace zaije ya huta. Ƙura mata ido naga ammi tayi ta baya ,kuma fuskarta amugun hade ,kafin kuma tayi wani murmushi tana mai jinjina kanta.... Masu karatu manage , Yau naje gidan suna ne. Saida na dawo nayi wanna typing ɗin. Much luv. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 41/42 _______________Adeeb yana barin gurin saiga rashy ya ƙaraso,zama yayi kusa da mahaifiyar tasa tare da sumbatar hannunta, Kansa ta shafa tana faɗin ",magajin faɗa prince Rashad Muhammad ashraf"ta faɗa cike da jin dadin sunan. Turo baki Rashad yayi tare da kallon ammi yace " ammi ta yaya zan zamo magajin fadar?bayan kinƙi yin wani abu akan wannan al'amari,ki dubafa,Adeeb ya dawo gida,kuma cikin ƙoshin lafiya yake,kina tunanin abie zai bar Adeeb ne,sannan Ni ya ɗorani akan karagar? Shiru ammi tayi tana kallon Rashad har ya kai ƙarshe azancensa,kafin tayi wani murmushi kana tace " Rashad kenan,kasan dai Adeeb yana jin maganata,sannan baya tsallake umarnina, yanzu akwai Abinda nake tunani akan yarinyar can ,daya zo da ita. Ina son tabbatar da wani abu ne game yarinyar ,wannan sarƙa ta wuyanta tabbas nasan iyalan dake da irin sarƙa,kuma sun rasa yarinyar su tsawon shekaru, Amma idan har na tabbatar da zargina akanta,to zanyi iyakar ƙoƙarina na ganin bata haɗu da ahalin nata ba,dan haduwarsu da ahalin babban koma bayane agareni. Masanin ido kawai ,zakaga abinda zanyi akan wannan al'amarin. Murmushi Rashad yayi tare da jin wani sanyi cikin ransa,dan yasan tabbas mahaifiyar tasu zatayi ƙoƙarin akan wannan al'amarin. "Amma ammi Zulaihat fa?kinsan yadda take ƙaunar Adeeb ,kada ta bamu matsala"cewar Rashad kenan yana gutsirar dabino . "Barni da zulaihat,bana jinta ko kaɗan ,yarinyar da ba wani hankali ta cika ba,itama bazan bari ta auri Adeeb ɗin ba ,lokaci kawai nake jira in maidata can gida"ammi ta faɗa cike da murmushi akan fuskarta. Sun jima suna tattauna ita da Rashad agurin ,kafin suka koma cikin gida. Fattu kuwa suna shiga toilet nanny ta hada mata ruwan wanka mai zafi,tace tayi wanka maza. Bayan tayi wankan ne ,nanny ta bata wannan pant din tasa ajikinta ,sannan suka fito,har zuwa lokacin kuka fattu keyi,har yanzu jinin bai daina zubowa ba,yanzu idan jinta ya kare ya zatayi?mutuwa fa zatayi kenan. Nanny sai rarrashinta take akan taci farfesun nan tasaha magani amma taki,kuma har lokacin marar ta ciwo take mata. Suna cikin haka saiga Adeeb ya shigo ɗakin,tana ganinsa jikinta ya ƙaru.tun kafin ya zauna ta fara magana. " Hamma na shiga uku har yanzu jini na zuba yake ,tsoro nake karya kare In mutu,dan Allah Hamma ka taimaka min" fattu ta faɗa tana mai miƙa masa hannu cikin kuka sosai. Da ɗan sauri Adeeb ya ƙaraso kusa da ita ya zauna,kallonta yake cike da tausayi,kafin ya riƙe hannunta wanda take miƙa masa yana ɗan murzawa kana yace" kina so ya daina zubowa " ya faɗa cikin sanyin muryarsa. Da sauri fattu ta jinjina kai tana hawaye. " To kiyi shiru,ki daina kuka, sannan ki nutsu kici abinci Kisha magani,zakiga ya daina zubowa" Adeeb ya faɗa yana mai share mata hawaye wasu na zubowa. "Hamma da gaske idan na daina kukan zai daina zubowa Ni tsoro nakeji kar jinina ya ƙare" ta faɗa cikin muryar kuka tana mai shagwabe fuska. Jinjina mata kai yayi yace " sosai ma kuwa,kuma jininki bazai ƙare a idan kika daina kuka" Ahankali fattu ta sanya bayan hannunta ta share hawayen,tana mai kallon Hammana nata. Farfesun ya karba ahannun nanny ya fara ɗiba da cokali yana bata abakin,haka take cin farfesun kamar magani,kusan lokaci shida tayi tace ta koshi. Bai takura mata ba,ya ajiye flate ɗin ,magungunan ya bare tare da miƙa mata.yamutse fuska tayi tana mai turo baki,alamun bata so. Kallonta Adeeb yayi kafin yace " ok baki son abun ya tsaya kenan?" " Ina so Hamma amma Ni bana son wannan abun aradu" ta fada cike da shagwaba, kafeta yayi da idanunsa masu matuƙar haske da ɗaukar hankali,wani irin yakeji idan tana masa shagwabar nan,nan take zaiji jikinsa yayi week, kasala ta lullubeshi ,gara yayi ya bata maganin nan kar ayi abin kunya gaban nanny. Hannunsa yaji fattu ta kama cikin nata tattausan hannu ,wani yuummmmm!! Yaji gaba ɗaya jikinsa ya ɗauka ,ahankali ya lumshe idanunsa yana mai sauke ajiyar zuciya. " Hamma zansha to kabani"fattu ta faɗa tana mai ƙara damke hannun Adeeb cikin nata. Ƙara damke idanunsa yayi tamau yana mai fidda wani sauti da ɗan sauri,kusan minti biyu idanunsa na runtse ,kafin ya budesu,har sun sauya kala daga fari tas zuwa ɗan jaa kadan. Ahankali ya zare hannunsa daga cikin nata,jikinsa sam ba kwari,maganin ya mika mata ,buɗe baki tayi ya saka mata maganin sannan ya bata ruwa.da gyar ta hadiye maganin tana ƙoƙarin yin amai. Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungume ta tsam-tsam ,yana ɗan shafa bayanta slowly. Lumshe idanu fattu tayi tana mai shaƙar daddaɗan kamshi jikin Adeeb,lokaci guda kuma taji ciwon marar ta na raguwa sosai. Shima Adeeb idanu arufe yake shafa bayan fattu,yana mai jin wani yanayi atattare dashi ,dadinsa ma nanny ta bar ɗakin tuni.dan haka gyara zama yayi ,tare da jingina bayansa jikin gado.sosai yake jin dadin yanayin da suke ciki ahalin yanzu,gaba daya yanayinsa ya sauya.sosai yake jin kansa cikin hali na buƙatuwa,wanda har wani hucin iska yake fesarwa daga bakinsa. Ahankali ya dago kan fattu tare da ƙura mata idanu,itama kallonsa take ,dan wani iri takeji ajikinta,bata san me takeji ba,amma kawai tana so hammanta yayi ta shafa mata bayanta. Ahankali Adeeb ya kira sunanta" Hulwa"can cikin makoshinsa,kallonsa take jin ya kira sunan Hulwa kuma yana kallonta. Bai damu da kallon da take masa ba yaci gaba da magana " me kike buƙata yanzu?ina ne yake miki ciwo" ya faɗa kamar mai yi mata rada asaitin kunnen ta. Da sauri ta ƙanƙame dantsen hannusa tana mai lumshe idanunta,dan wani irin abu dataji yana mata yawo cikin jikinta,lokacin da sautin muryarsa tare da iskar bakinsa suka doki kunne ta. "Hammmma" ta furta ahankali cikin jan sunan. Kallonta yake tare da karantar yanayin da take ciki,ko shakka babu yasan tana jin makamancin abinda yake ji ajikinsa,saidai shikam baida niyyar cutar da fattu,ko kaɗan dole yake nesanta kanshi daga gareta ,dan gudun faruwar wani abu. Ahankali ya ƙara maimaita mata tambayar ,saidai wannan karon bai kai bakinsa saitin kunnenta ba. "Hannunsa fattu ta kamo tare da ɗorawa asaitin mararta" marar Tata kuwa tayi zafi sosai ,kallon fuskarta Adeeb yayi wacce har yanzu idanunta ke rufe, "Nan ke miki ciwo" Adeeb ya faɗa ahankali muryarsa na dan rawa. Jinjina kai fattu tayi ba tare da ta buɗe idanunta ba. Ahankali ya kwantar da ita akan gadon,sannan ya ɗan daga doguwar rigar dake jikinta,nan take santala -santalan farare cinyoyinta suka bayyana,kallo Adeeb yabo cinyar Tata dashi,yana mai ambaton sunan Allah cikin ransa. Ahankali yake ɗan shafa marar Tata tare da dan dannawa kadan kadan ,kamar yana mata tausa , shiru fattu tayi tana jin wani irin sanyi da daɗi na ratsa dukkan sassan jikinta,sosai take jin dadin abinda Hamma ka mata,dan kuwa tuni ta nemi ciwon mararta ta rasa,sai wani nishi take ahankali tana mai riƙe zanin gadon .kwantowa Adeeb yayi tare da ƙurawa lips ɗin ta idanu,buɗe ido fattu tayi tana mai kallon fuskarsa, Kusan minti biyu suna kallon juna,kafin Adeeb yaji bazai iya ɗaurewa ba kawai ya hada bakinsu guri ɗaya ya fara kissing ɗin fattu. Kusan mintina biyar zuwa bakwai suka ɗauka cikin wannan halin,gaba daya Adeeb ya fice daga hayyacinsa ,Banda nishinsa ba abinda kake juyowa aɗakin,yayinda fattu kuwa tayi lakwas tana amsar sakonsa, da alama dai itama tana karbar sakon yadda ya kamata. Kamar wanda aka tsikara,Adeeb yayi saurin zare bakinsa tare da mikewa yayi hanyar fita daga dakin yana tangadi kamar ɗan giya. Fattu ma saurin juya bayanta tayi tare da runtse idanunta,wani irin abu takeji yana yawo ajikinta ,kuma bataso hamma ya daina mata wannan abun ba sam. Adeeb yana fitowa daga dakin fattu sukayi kiciɓis da Rashad shikuma yana shigowa babban falon, Baki sake tashar ke kallon Adeeb ,ganin yanayin da yake ciki,kar dai ace Adeeb zagayawa yake gurin yarinyar nan fa? Dan kallo daya Zakayiwa Adeeb kasan yana cikin hali na buƙatuwa. Kodai dama kafuwarta ce bamu sani ba ?yace taimakonsa tayi shima yake son taimakonta?(Dan ba Wanda yasan meye alaƙar dake tsakanin fattu da Adeeb ,hatta mai martaba ,sam Adeeb bai fada masa ba. Shikuwa Adeeb ko kallon inda Rashad take baiyiba ,yayi ficewarsa daga ɗakin,Dan shikadai yasan meke damunsa. Kai tsaye Rashad ya nufi dakin da fattu ke ciki,tana kwance har lokacin bata ko motsaba, kallonta yake cike da tsantsar sha'awar ta ,abun tayi ta ko ina kalli hips ɗin ta kamar zai fasa rigar nan,ahankali ya Rashad ya ƙarasa bakin gadon yana mai karewa fattu kallo ,wani irin kashe ido yake yana mai jin kamar ya ruƙunkumeta ajikinsa,hmmmmm Allah ya kamu gobe ,ko kaɗan bazan saurarawa babyn nan ba,Rashad ya faɗa yana mai miƙa hannu da nufin taba abinda ke taimake masa idanu ajikinta. " Kai- kai ɗan nan menene haka?me zakayi mata ajikin nata ?zo maza ka fice" nanny ta faɗa tana nuna masa hanyar waje. Dan sosa kai Rashad yayi yana mai hararar nanny kafin ya fice daga dakin yana faɗin "wllh tsohuwar nan ta fiye samun guri,duk wannan banzan ne ya bata dama ,amma zanyi maganinta ne.ya faɗa yana mai ficewa daga ɗakin. Ammi kuwa waya ta dauka tare da kiran wata number,bugu biyu aka daga ,murmushi ammi tayi tana faɗin " ƙawatafatan dai kina hanya ,zakizo gurin taron namu ?" Ta can daya bangaren bansan me akacewa ammi ba ,na dai ji tace "hmmmmm ke dai ki bari kawai saikinzo dan akwai gagarumar matsala sosai" Shiru ta ɗanyi kaɗan kafin tace " shikenan Allah ya kawoki lafiya dole mu san abinyi" ta faɗa cike da daure fuska. Ajiye wayar tayi tare da yin shiru ,da'alama tayi zurfi cikin tunanin mafita. Adeeb kuwa yana shiga part dinsa ya zube akan kujera,ko takalmin bai iya cire wa ba ,kwanciya yayi rub da ciki akan kujerar ,idanunsa alumshe ya dafe mararsa da hannun damarsa ,fuskarsa ayamutse. Sai huci yake sauƙewa. Wayarsa ce take ta faman ringing ,Amma ya kasa ɗagawa,haka tayi ta ƙara harta tsinke. Dole ya ɗauki mataki ,dan gaskiya yana cikin matsala ,idan haka taci gaba da kasancewa to zai shiga damuwa matuka. Ajiyar zuciya sauke arako na ba adadi,yana mai kara damke mararsa,ba abinda yake ji dagani sai fattu kwance kan ƙirjinsa,yayinda yanayinsa ke kara yin nisa. "Washhhh " ya furta ahankali yana mai dantse lips ɗinsa na ƙasa. Nan da nan jikinsa ya kama rawa zazzaɓi mai zafi ya rufeshi ruff.. Muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment Fisabilillah.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 43/44 _______________Adeeb yana barin gurin saiga rashy ya ƙaraso,zama yayi kusa da mahaifiyar tasa tare da sumbatar hannunta, Kansa ta shafa tana faɗin ",magajin faɗa prince Rashad Muhammad ashraf"ta faɗa cike da jin dadin sunan. Turo baki Rashad yayi tare da kallon ammi yace " ammi ta yaya zan zamo magajin fadar?bayan kinƙi yin wani abu akan wannan al'amari,ki dubafa,Adeeb ya dawo gida,kuma cikin ƙoshin lafiya yake,kina tunanin abie zai bar Adeeb ne,sannan Ni ya ɗorani akan karagar? Shiru ammi tayi tana kallon Rashad har ya kai ƙarshe azancensa,kafin tayi wani murmushi kana tace " Rashad kenan,kasan dai Adeeb yana jin maganata,sannan baya tsallake umarnina, yanzu akwai Abinda nake tunani akan yarinyar can ,daya zo da ita. Ina son tabbatar da wani abu ne game yarinyar ,wannan sarƙa ta wuyanta tabbas nasan iyalan dake da irin sarƙa,kuma sun rasa yarinyar su tsawon shekaru, Amma idan har na tabbatar da zargina akanta,to zanyi iyakar ƙoƙarina na ganin bata haɗu da ahalin nata ba,dan haduwarsu da ahalin babban koma bayane agareni. Masanin ido kawai ,zakaga abinda zanyi akan wannan al'amarin. Murmushi Rashad yayi tare da jin wani sanyi cikin ransa,dan yasan tabbas mahaifiyar tasu zatayi ƙoƙarin akan wannan al'amarin. "Amma ammi Zulaihat fa?kinsan yadda take ƙaunar Adeeb ,kada ta bamu matsala"cewar Rashad kenan yana gutsirar dabino . "Barni da zulaihat,bana jinta ko kaɗan ,yarinyar da ba wani hankali ta cika ba,itama bazan bari ta auri Adeeb ɗin ba ,lokaci kawai nake jira in maidata can gida"ammi ta faɗa cike da murmushi akan fuskarta. Sun jima suna tattauna ita da Rashad agurin ,kafin suka koma cikin gida. Fattu kuwa suna shiga toilet nanny ta hada mata ruwan wanka mai zafi,tace tayi wanka maza. Bayan tayi wankan ne ,nanny ta bata wannan pant din tasa ajikinta ,sannan suka fito,har zuwa lokacin kuka fattu keyi,har yanzu jinin bai daina zubowa ba,yanzu idan jinta ya kare ya zatayi?mutuwa fa zatayi kenan. Nanny sai rarrashinta take akan taci farfesun nan tasaha magani amma taki,kuma har lokacin marar ta ciwo take mata. Suna cikin haka saiga Adeeb ya shigo ɗakin,tana ganinsa jikinta ya ƙaru.tun kafin ya zauna ta fara magana. " Hamma na shiga uku har yanzu jini na zuba yake ,tsoro nake karya kare In mutu,dan Allah Hamma ka taimaka min" fattu ta faɗa tana mai miƙa masa hannu cikin kuka sosai. Da ɗan sauri Adeeb ya ƙaraso kusa da ita ya zauna,kallonta yake cike da tausayi,kafin ya riƙe hannunta wanda take miƙa masa yana ɗan murzawa kana yace" kina so ya daina zubowa " ya faɗa cikin sanyin muryarsa. Da sauri fattu ta jinjina kai tana hawaye. " To kiyi shiru,ki daina kuka, sannan ki nutsu kici abinci Kisha magani,zakiga ya daina zubowa" Adeeb ya faɗa yana mai share mata hawaye wasu na zubowa. "Hamma da gaske idan na daina kukan zai daina zubowa Ni tsoro nakeji kar jinina ya ƙare" ta faɗa cikin muryar kuka tana mai shagwabe fuska. Jinjina mata kai yayi yace " sosai ma kuwa,kuma jininki bazai ƙare a idan kika daina kuka" Ahankali fattu ta sanya bayan hannunta ta share hawayen,tana mai kallon Hammana nata. Farfesun ya karba ahannun nanny ya fara ɗiba da cokali yana bata abakin,haka take cin farfesun kamar magani,kusan lokaci shida tayi tace ta koshi. Bai takura mata ba,ya ajiye flate ɗin ,magungunan ya bare tare da miƙa mata.yamutse fuska tayi tana mai turo baki,alamun bata so. Kallonta Adeeb yayi kafin yace " ok baki son abun ya tsaya kenan?" " Ina so Hamma amma Ni bana son wannan abun aradu" ta fada cike da shagwaba, kafeta yayi da idanunsa masu matuƙar haske da ɗaukar hankali,wani irin yakeji idan tana masa shagwabar nan,nan take zaiji jikinsa yayi week, kasala ta lullubeshi ,gara yayi ya bata maganin nan kar ayi abin kunya gaban nanny. Hannunsa yaji fattu ta kama cikin nata tattausan hannu ,wani yuummmmm!! Yaji gaba ɗaya jikinsa ya ɗauka ,ahankali ya lumshe idanunsa yana mai sauke ajiyar zuciya. " Hamma zansha to kabani"fattu ta faɗa tana mai ƙara damke hannun Adeeb cikin nata. Ƙara damke idanunsa yayi tamau yana mai fidda wani sauti da ɗan sauri,kusan minti biyu idanunsa na runtse ,kafin ya budesu,har sun sauya kala daga fari tas zuwa ɗan jaa kadan. Ahankali ya zare hannunsa daga cikin nata,jikinsa sam ba kwari,maganin ya mika mata ,buɗe baki tayi ya saka mata maganin sannan ya bata ruwa.da gyar ta hadiye maganin tana ƙoƙarin yin amai. Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungume ta tsam-tsam ,yana ɗan shafa bayanta slowly. Lumshe idanu fattu tayi tana mai shaƙar daddaɗan kamshi jikin Adeeb,lokaci guda kuma taji ciwon marar ta na raguwa sosai. Shima Adeeb idanu arufe yake shafa bayan fattu,yana mai jin wani yanayi atattare dashi ,dadinsa ma nanny ta bar ɗakin tuni.dan haka gyara zama yayi ,tare da jingina bayansa jikin gado.sosai yake jin dadin yanayin da suke ciki ahalin yanzu,gaba daya yanayinsa ya sauya.sosai yake jin kansa cikin hali na buƙatuwa,wanda har wani hucin iska yake fesarwa daga bakinsa. Ahankali ya dago kan fattu tare da ƙura mata idanu,itama kallonsa take ,dan wani iri takeji ajikinta,bata san me takeji ba,amma kawai tana so hammanta yayi ta shafa mata bayanta. Ahankali Adeeb ya kira sunanta" Hulwa"can cikin makoshinsa,kallonsa take jin ya kira sunan Hulwa kuma yana kallonta. Bai damu da kallon da take masa ba yaci gaba da magana " me kike buƙata yanzu?ina ne yake miki ciwo" ya faɗa kamar mai yi mata rada asaitin kunnen ta. Da sauri ta ƙanƙame dantsen hannusa tana mai lumshe idanunta,dan wani irin abu dataji yana mata yawo cikin jikinta,lokacin da sautin muryarsa tare da iskar bakinsa suka doki kunne ta. "Hammmma" ta furta ahankali cikin jan sunan. Kallonta yake tare da karantar yanayin da take ciki,ko shakka babu yasan tana jin makamancin abinda yake ji ajikinsa,saidai shikam baida niyyar cutar da fattu,ko kaɗan dole yake nesanta kanshi daga gareta ,dan gudun faruwar wani abu. Ahankali ya ƙara maimaita mata tambayar ,saidai wannan karon bai kai bakinsa saitin kunnenta ba. "Hannunsa fattu ta kamo tare da ɗorawa asaitin mararta" marar Tata kuwa tayi zafi sosai ,kallon fuskarta Adeeb yayi wacce har yanzu idanunta ke rufe, "Nan ke miki ciwo" Adeeb ya faɗa ahankali muryarsa na dan rawa. Jinjina kai fattu tayi ba tare da ta buɗe idanunta ba. Ahankali ya kwantar da ita akan gadon,sannan ya ɗan daga doguwar rigar dake jikinta,nan take santala -santalan farare cinyoyinta suka bayyana,kallo Adeeb yabo cinyar Tata dashi,yana mai ambaton sunan Allah cikin ransa. Ahankali yake ɗan shafa marar Tata tare da dan dannawa kadan kadan ,kamar yana mata tausa , shiru fattu tayi tana jin wani irin sanyi da daɗi na ratsa dukkan sassan jikinta,sosai take jin dadin abinda Hamma ka mata,dan kuwa tuni ta nemi ciwon mararta ta rasa,sai wani nishi take ahankali tana mai riƙe zanin gadon .kwantowa Adeeb yayi tare da ƙurawa lips ɗin ta idanu,buɗe ido fattu tayi tana mai kallon fuskarsa, Kusan minti biyu suna kallon juna,kafin Adeeb yaji bazai iya ɗaurewa ba kawai ya hada bakinsu guri ɗaya ya fara kissing ɗin fattu. Kusan mintina biyar zuwa bakwai suka ɗauka cikin wannan halin,gaba daya Adeeb ya fice daga hayyacinsa ,Banda nishinsa ba abinda kake juyowa aɗakin,yayinda fattu kuwa tayi lakwas tana amsar sakonsa, da alama dai itama tana karbar sakon yadda ya kamata. Kamar wanda aka tsikara,Adeeb yayi saurin zare bakinsa tare da mikewa yayi hanyar fita daga dakin yana tangadi kamar ɗan giya. Fattu ma saurin juya bayanta tayi tare da runtse idanunta,wani irin abu takeji yana yawo ajikinta ,kuma bataso hamma ya daina mata wannan abun ba sam. Adeeb yana fitowa daga dakin fattu sukayi kiciɓis da Rashad shikuma yana shigowa babban falon, Baki sake tashar ke kallon Adeeb ,ganin yanayin da yake ciki,kar dai ace Adeeb zagayawa yake gurin yarinyar nan fa? Dan kallo daya Zakayiwa Adeeb kasan yana cikin hali na buƙatuwa. Kodai dama kafuwarta ce bamu sani ba ?yace taimakonsa tayi shima yake son taimakonta?(Dan ba Wanda yasan meye alaƙar dake tsakanin fattu da Adeeb ,hatta mai martaba ,sam Adeeb bai fada masa ba. Shikuwa Adeeb ko kallon inda Rashad take baiyiba ,yayi ficewarsa daga ɗakin,Dan shikadai yasan meke damunsa. Kai tsaye Rashad ya nufi dakin da fattu ke ciki,tana kwance har lokacin bata ko motsaba, kallonta yake cike da tsantsar sha'awar ta ,abun tayi ta ko ina kalli hips ɗin ta kamar zai fasa rigar nan,ahankali ya Rashad ya ƙarasa bakin gadon yana mai karewa fattu kallo ,wani irin kashe ido yake yana mai jin kamar ya ruƙunkumeta ajikinsa,hmmmmm Allah ya kamu gobe ,ko kaɗan bazan saurarawa babyn nan ba,Rashad ya faɗa yana mai miƙa hannu da nufin taba abinda ke taimake masa idanu ajikinta. " Kai- kai ɗan nan menene haka?me zakayi mata ajikin nata ?zo maza ka fice" nanny ta faɗa tana nuna masa hanyar waje. Dan sosa kai Rashad yayi yana mai hararar nanny kafin ya fice daga dakin yana faɗin "wllh tsohuwar nan ta fiye samun guri,duk wannan banzan ne ya bata dama ,amma zanyi maganinta ne.ya faɗa yana mai ficewa daga ɗakin. Ammi kuwa waya ta dauka tare da kiran wata number,bugu biyu aka daga ,murmushi ammi tayi tana faɗin " ƙawatafatan dai kina hanya ,zakizo gurin taron namu ?" Ta can daya bangaren bansan me akacewa ammi ba ,na dai ji tace "hmmmmm ke dai ki bari kawai saikinzo dan akwai gagarumar matsala sosai" Shiru ta ɗanyi kaɗan kafin tace " shikenan Allah ya kawoki lafiya dole mu san abinyi" ta faɗa cike da daure fuska. Ajiye wayar tayi tare da yin shiru ,da'alama tayi zurfi cikin tunanin mafita. Adeeb kuwa yana shiga part dinsa ya zube akan kujera,ko takalmin bai iya cire wa ba ,kwanciya yayi rub da ciki akan kujerar ,idanunsa alumshe ya dafe mararsa da hannun damarsa ,fuskarsa ayamutse. Sai huci yake sauƙewa. Wayarsa ce take ta faman ringing ,Amma ya kasa ɗagawa,haka tayi ta ƙara harta tsinke. Dole ya ɗauki mataki ,dan gaskiya yana cikin matsala ,idan haka taci gaba da kasancewa to zai shiga damuwa matuka. Ajiyar zuciya sauke arako na ba adadi,yana mai kara damke mararsa,ba abinda yake ji dagani sai fattu kwance kan ƙirjinsa,yayinda yanayinsa ke kara yin nisa. "Washhhh " ya furta ahankali yana mai dantse lips ɗinsa na ƙasa. Nan da nan jikinsa ya kama rawa zazzaɓi mai zafi ya rufeshi ruff.. Muje zuwa masu karatu. Anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment Fisabilillah.🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Aunty mammy ) Elegant online writers📚📚 Free book Page 47/48 Rashad ne keta kaiwa da komowa a daki ya rasa abinda ke mai dadi ga bakin cikin abinda adeeb ya mashi a dayan jefen kuma ya wutar son fattu da sha'awar sa dake ruruwa a zuciyarsa ya rasa Inda zai sa kanshi ana bacci barayo shidai ko rintsi yakasa yana sakawa da warwara har garin Allah ya waye. Adeeb.............................. Sai ayi hakuri Ajira aunty mami nide nayi nan💃💃💃 Allah tashe mu lafiya. [30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 49/50 _______________Tashi Adeeb yayi cikin nutsuwa, da takunsa irin na jaruman maza ,ya nufi ɗakin da fattu ke ciki. Fattu na zaune abakin gado, tayi shiru kamar mai tunanin wani abu,Adeeb ya turo ƙofar da sallama ɗauke abakinsa,saidai idan ba ka kasa kunne ba ,to bazakaji me yake faɗi ba. Dago Kai fattu tayi jin muryar Adeeb datayi,baki buɗe take kallon Adeeb ,tunda take arayuwarta,zata iya cewa bata taɓa ganin mutum mai kyau irin na Adeeb ba ."masha Allah"fattu ta faɗa tana mai mikewa tsaye fuskarta ɗauke da murmushi,ta ƙure Adeeb da ido kamar yau ta taɓa ganinsa. Ƙarasowa Adeeb yayi cikin ɗakin,shima idonsa na kanta ,dan haka kawai yaga tayi masa kyau shima . Ɗan harararta yayi kafin yace " Please karki cinyeni da kallo mana"ya faɗa yana ɗan wani gwabe fuska cikin shagwabar da baisan yayi ba. Da sauri fattu ta sanya hannu tare da rufe fuskarta tana ɗan dariya ,dan kunya taji da yadda yayi salon maganar tasa. "Hamma kayi kyau sosai ,kai mai kyaune" fattu ta faɗa kanta a ƙasa tana ɗan mirza hannunta. Wani irin sanyi ne yake ratsa zuciyar Adeeb, sosai yaji daɗin maganar fattu ,dan haka cikin wani irin shauƙi ya mika hannunsa tare da dago habarta .kallon juna suke ido cikin ido,murmushi Adeeb yayi kafin yace "kin tabbata nayi kyau a idonki?wankana yayi miki kyau?" Ya faɗa yana mai kallon lips ɗin fattu ,wanda yake ji kamar ya cinyesu. Lumshe ido fattu tayi tare da jinjina kai tace " Hamma bantaɓa ganin mutum mai kyan ka ba,kuma Ni kullum ma kyau kakemin" ta faɗa tana ɗan riƙe lips ɗin ta na ƙasa da haƙoranta. Wani irin abu Adeeb yaji yana masa yawo ajikinsa,sosai yake jin yana son rungumar fattu ajikinsa ,duk lokacin da yake tare da ita yakan tsinci kansa cikin wani irin shauƙin son kasancewa da ita . Murmushi yayi tare da shafa gefen fuskarta yace " to me zaki bani matsayin kyautar dazan fita gurin taro da ita?" Ya faɗa idanunsa akan lips ɗin ta. Shiru fattu tayi tana ɗan rarraba ido,to ita me take dashi ma ?dazata ba Hamma? "Hamma Ni bani da komai fa ,bansan me zan baka ba. Kallonta yake baya ko ƙiftawa ,ajiyar zuciya ya sauke yana faɗin " shikenan tunda ba abinda zaki bani,zan tafi,amma karki fito ko ina kinji?ki kwanta kiyi barci da zaran mun tashi daga gurin taro zanzo in ganki "Adeeb ya faɗa yana mai kallon fuskarta. Jinjina kai fattu tayi tana mai kallon Adeeb ɗin,sai taji bataji daɗi ba ,ace ya tambaye ta wani abu ita kuma bata bashi ba,kuma duk abinda take dashi ma ai shine ya siya mata,to mezata bashi?fattu ta faɗa cikin zuciyarta ,fuskarta ɗauke da yanayin damuwa. Ahankali Adeeb ya fara takawa zuwa bakin ƙofar fita daga ɗakin haka kawai yake jinsa wani iri, sam baya don rabuwa da fattu yau ɗin nan.ganin yana neman fita yasa Fattu ta tako da sauri tare da rungumeshi ta baya. Dammm!dammmmm!!dammmm!!!gaban Adeeb ya bada wani sauti na bugawa. Cikin hanzari ya runtse idanunsa,dan yadda yaji fattun ajikinsa ,abin yazo masa cikin bazata. "Hamma kayi haƙuri wllh bani da abinda zan baka ,amma indai na tara kuɗina zan siya maka cin-cin burodi,nima baffa ke siyomin idan yaje gari, ka fadi abinda kake so nayi maka yanzun" ta faɗa tana mai gyara kanta dake kwance tsakiyar bayan Adeeb. Cikin dauriya da jarumta Adeeb ya sanya hannunsa ya jawo fattu zuwa gabansa.bude idanunsa yayi dasuka fara rinewa sai wani lumshewa da budewa yake . Ido ya ƙura mata na wani lokaci,kafin ya matso da fuskarsa zuwa gareta,ta yadda numfashinsa ke sauka akan Tata fuskar. "Kin amince Ni na ɗauki Abinda nake ganin yayi amatsayin kyauta ta " Adeeb ya faɗa cikin voice ɗinsa mai kama da yana mata raɗa. Da sauri fattu ta gyada kanta ,dan yadda yayi maganar saiya sata jin wani iri atare da ita. Lips ɗinta Adeeb ya kalla cike da tsantsar son jinsu cikin bakinsa.bai jira komai ba ya ɗora nasa lips ɗin nata. Gaba ɗayansu sun shiga wani irin yanayi mai wuyar fassaruwa ,cikin salo da narkar da zuciyar mace Adeeb ke kissing fattu ,yayi da ita kuma take jin abin da yake mata har cikin ranta.idonsu alumshe yake sun lula wata duniyar ,dan tuni Adeeb ya mance da batun taro ,ya sami lips ɗin fattu kamar ya sami lollipop. Bugun da akeyiwa ƙofar ne yasa Adeeb saurin dawowa cikin hayyacinsa,ahankali ya zare lips ɗin sa daga bakin fattu yana kallonta .har lokacin idanunta alumshe suke ,sai sauke numfashi take cikin sauri,jikinta yana bari. Bakin gado Adeeb ya zaunar da ita,tare da shafa gefen fuskarta yace " wannan ma ya isheni nishaɗi har agama taron ,antee sururi Hulwa" Adeeb ya faɗa yana mai juyawa ya bar ɗakin. Saƙare fattu ta zauna abakin gadon kamar wata butumbutumi,haƙiƙa tana jin Hamma har cikin ranta,wani irin shauƙi takeji game dashi,sannan ko kaɗan bata jin damuwa idan tana tare dashi,lallai Hammanta shine farin cikinta,ga shi aduk lokacin da Hamman nata ke sha mata baki tanajin wani irin nishaɗi sosai,ko me yasa ma yake sha mata bakin oho? Murmushi tayi tare da shafa lips ɗin ta ,tanaji kamar har yanzu hamman na shan lips ɗin nata. Taro yayi taro ta ko ina ka ƙalla jama'ane Malik a haɗaɗden dakin taron dake cikin masarautar,abie na zaune kan wata kyakykyawar kujera ta zinare, yayinda Adeeb ke gefensa shima zaune kan wata kujera mai shegen kyau da ɗaukar hankali. Gaba ɗaya yan gidansu Adeeb suna zaune kan kujeru masu kyau,sai baki sarakuna da matayensu,kowa kagani yayi ado na kece raini, Yan mata sai kaiwa Adeeb hari suke da idanuwansu da jikinsu, amma ba wacce ta ishe shi kallo acikinsu. Anata jawabai da taya abie murnar dawowar ɗansa bayan tsawon lokaci da aka dauka ana nemansa. Ammi na zaune ita da tawagarta,yayinda gimbiya suhaimat ke kusa da ita ,sai sauran baƙinta, hakama amma na zaune tare da Tata tawagar cikin ado mai kyau.wata matace zaune agefenta tana ɗan kallon ammi,kafin ta juyo da kallonta ga amma tace " Dole saikinyi da gaske kafin ki gama da matar can,makircin ta yayi yawa,ina tsoron kaidinta" Kallon ammi itama amma keyi kafin ta sauke ajiyar zuciya tace " karki damu Maryam,ninasan ta inda zan bullowa al'amarin nan,akwai Abinda ke ɗauremin kai sosai,game da gimbiya suhaimat, ina don gano asalin gaskiyar abin kafin nayiwa ammi kwaf ɗaya,amma zanyi bincike sosai akan lamarin. "Shikenan zan ci gaba da baki goyon baya ,Abdul lokacin da kike buƙatar taimakona ƙofa abude take" cewar matar. Godiya amma tayi mata cikin murmushi, Nan dai suka ci gaba da tattauna akan yadda zasu ga bayan ammi. Rashad na hango zaune cikin wani kaya masu kyau irin na sarauta,fuskarsa ɗauke da murmushi,ya kafe Adeeb da ido baya ko kiftawa.wayarsace tayi ƙara dan haka ya ɗauka tare da karawa akunnensa, har lokacin idonsa na kan Adeeb,wanda shima hankalinsa yayo kan Rashad ɗin,kallonsa yake cike da tsana, tun lokacin da ya zaune yake kallon Rashad ɗin yana kula da duk wani motsinsa. Dan kwata-kwata zuciyarsa bata yarda da Rashad ɗin ba,gani yake kamar akwai wani makircin da yake ƙullawa. Dan haka ya sa tareeƙ ya kula da Rashad sosai. "Ya kamata fa kaje ka aiwatar da abinda zakayi, kafin lokaci ya ƙure " ammi ta faɗa tana ɗan kallon gefen da Rashad ke zaune,waya kange akunnenta,da alam ita ta kira Rashad ɗin. Wata dariya Rashad yayi kafin yace " ammina ta kaina ,ina sane da lokaci,yanzu zan tashi domin cike burina, yau saina hana Adeeb barci da irin aika -aikar da zanyi masa" Rashad ya faɗa idanunsa ƙur akan Adeeb, wanda ya Dan rangwafo kusa da mai martaba ,da alama suna magana ne. Kashe wayar ammi tayi tare da sauke wata ajiyar zuciya mai ƙarfi,kafin ta kalli gimbiya suhaimat tace " Ni kuwa suhaimat ina wannan sarƙar taku ta ahali, bana gajiya da kallonta ko kaɗan ,naga banganta atare da ke ba" ammi ta faɗa tana mai kallon gimbiya suhaimat. Murmushi matar tayi kafin tace " har abada bazan taɓa rabuwa da wannan sarƙar ba,dan kuwa itace shaidar dazata sadani da ƴata, Aduk inda take,ina ji ajikina mun kusa haduwa da juna kuma nayi alƙawarin saina ɗauki fansar rabani da ita da akayi na tsawon shekaru,akan koma waye keda hannu cikin al'amarin " ta faɗa idanunta cike da kwallah.kafin ta ɗan daga mayafin jikinta ,saiga sarƙar ta bayyana ,ƙurawa sarƙar idanu ammi tayi,tabbas wannan irin sarƙar wuyan yarinyar can ce ,hakan na nufin fattu itace ɗiyar suhaimat da suka rasa shekarun baya?innalillahi wa'inna ilaihir raji'un.banga ta zama ba. Cewar ammi cikin zuciyarta. Da sauri ta miƙe tana mai faɗin "suhaimat ina zuwa "bata jira amsar taba tayi gaba. Rashad ma ganin ammi ta mike yayi saurin bin bayanta dan zuwa ga fattu,yau kam za'ayi ta ta ƙare. Zulaihat dake zaune cikin ƙawayenta tana ta zuba izza da iyawa ,ganin su duka biyun sunyi waje hakan yasa itama ta mike cikin sauri ta rufa musu baya, dan kuwa tare zasu aikata mugun nufin nasu akan fattu, tana son ganin komai ya wakana akan idonta , Ko ina zasu kuma oho? Muje zuwa masu karatu, Manage please har yanzu muna cike da alhini. Na gode sosai da addu'ar ku garemu,waɗanda suka kirani,da waɗanda sukayi min ta waya. 🙏🙏 Anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. [30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 51/53 _________________Abakin ƙofar hall ɗin Zulaihat ta tarar da Rashad ,yana tsaye da waya ahannunsa ,da alama kira yake ƙoƙarin yi,saidai yana ganinta ya maida wayar cikin aljihunsa yana mai faɗin,"yawwa dama ke nake ƙoƙarin kira,sai gaki kin fito. Ƙarasowa Zulaihat tayi kusa dashi ta tsaya" ya ake ciki ne ?" Ta faɗa tana ɗan waigen bayanta. "Yau burina zai cika ,zan sami abinda ke hanani barci,kuma zanyiwa Adeeb illah,saina rama dukan da yayi min akan yarinyar da yake iƙirarin yar amanar da ce,bayan kuma Ni nasan dadironsa ce ,kawai kishine da mugunta sukayi masa yawa,shine ya hanani Nima in ɗana"cewar Rashad yana mai kallon Zulaihat. "Kaga Rashad karka ƙara cewa dadiron my Prince ce,karkayi masa sharri,dan kuwa nasan halinsa nasan koshi waye,wllh bazai taba ajiye yarinyar nan dan biyan buƙatarsa ba,mutumin da har maganin sha'awa nake saka masa alemo,dan kawai yayi tarayya dani,amma duk yadda ya galabaita bazai koda rungumeni ba. Dama dai kaine akace ka ajiye ta dan biyan buƙatarka,to wannan kam na yarda dan nasan kai din namamajo ne " Zulaihat ta faɗa tana mai galla masa harara,dan taji haushin sharrin da yayiwa adeeb,ita da take burin ace itace zata fara bude Adeeb aledarsa ina zataso jin wannan batu. Wani shegen kallo Rashad ya watsa mata kafin yace " banza yar tasha ,ke har Ni zaki cewa na mamajo? Ai duk iskancina ban kaki ba,kefa ƴar maye ce sannan jarababbiya, Ni kaina sau nawa ina taimaka miki ?ina ce wataran har guduwa nake saboda jarabarki ?zaki raina min hankali wawiya kawai" Rashad ya faɗa cikin faɗa. Haushi sosai ya kama Zulaihat ,ranta ya ɓaci da kalaman Rashad gareta ,wato har gori zaiyi mata ,dan ta neme shi kusan sau uku ?ba komai zai gane kurensa wllh. "Ni kakeyiwa gori Rashad ?to wllh kasani bazan taimaka maka akan ƙudirinka na yauba ,saidai kayi kai kadai ,banza marar mutunci" Zulaihat ta faɗa cikin ɓaci rai tana mai barin gurin cikin sauri. Tsaki Rashad yayi yana mai faɗin"aikin banza ,da me zaki iyamin agurin banda kema kice kina so intaimaka miki ,Ni kuwa ranata ta yau duka ta fine baby ce,yar ƙwaya kawai " ya faɗa yana mai nufar part ɗin ammi. Ammi kuwa tana zuwa part ɗinta cikin ɗakinta ta nufa ,ƙullewa tayi tare da zama bakin gado,tana tunani iri iri cikin ranta, wata akwati ta ɗauko dake can ƙasan gadon ta tare da budewa, Tana buɗewa wani hayaƙi yayo sama baƙiƙirin dashi,banda wari ba abinda ke tashi cikin hayaƙin nan,da sauri ammi ta toshe hancinta, tana mai zaro ido waje,abayyane ta furta " na shiga ukuna ba dai kwalbar nan ta fashe ba? Shikenan ta faru ta ƙare ,dama nasan hakan zata faru wayyo Allah na" ammi ta faɗa tana mai bin wata kwalba yar gajeriya da ta tarwatseda ido,wani farin abu mai kauri yana ta motsi kamar tsutsa. Bugun ƙofar da ammi tajine yasata saurin rufe akwatin ta tura can kasan gado,saita kanta tayi cikin ɗauriya ta nufi ƙofar . Rashad ta gani tsaye abakin ƙofar ,"ammi ya ake ciki ne ?ta yaya zan ɗauki yarinyar ne ?kinsan ba aɗakin ta zan aiwatar da ƙudirina ba,dan wancan mayen zai iya zuwa ya cin mini" ya faɗa yana kallon fuskar ammi . "Ka tafi can ɗayan part ɗina ka jira zan kawo maka ita da kaina ,ina son kayi mata abinda nan da wata guda ma bazata san inda kanta yake ba,bana son ka tausaya mata ko kaɗan"ammi ta fada fuskarta ahaɗe. "Kada ku damu ammi bazan taɓa baki kunya ba,nayi alƙawarin saina yi mata abinda Bama ki tsammata ba"Rashad ya faɗa yana wani irin killer smile. Ficewa ammi tayi tare da nufar part ɗin su fattu.ba kowa afalon,dan kuwa nanny ta ɗan leƙe gurin taron ,ganin fattu kwance tana barci. Cikin ɗakin ammi ta shiga ,tsaye tayi agaban gadon da fattu ke kwance ,idanunta arufe kamar mai barci,amma idanunta biyu,hammanta kawai take tunani. Kusan minti uku ammi tayi tana kallon fattu dake kwance ,tabbas ko tantama batayi ,wannan yarinyar gimbiya suhaimat ce ,dan kuwa sai yanzu take ganin tsantsar kamannin dake tsakaninsu,amma ta yaya suka haɗu da Adeeb?har ya taho da ita nan?wannan shine abinda take son sani. Ganin fattu ta ɗan motsa ne yasa ammi ta ɗan kira sunanta " fateema tashi" Ammi ta faɗa tana ɗan shafa kan fattu. Ahankali cikin nutsuwa fattu ta tashi zaune tana ɗan mika ,dan ta jima akwance. Murmushi tayiwa ammi tare da sunkuyar da kanta ƙasa cikin kunya . "Fateema Sarkin kunya,ke kadaice aɗakin ne"ammi ta faɗa cikin Hausa ,dan kuwa ta iya Hausa sosai itama. Jinjina kai fattu tayi tana wasa da ƴan yatsunta. Murmushi ammi tayi tana shafa kan fattu kafin tace " to ya jikin naki,?" " Da sauƙi inna"fattu ta faɗa cikin yar karamar muryarsa mai dadi. "Kinga bai kamata ki zauna ke kaɗai anan ba kowa ba,dan haka maza ki tashi ki koma can ɗaya part ɗin sauki kwanta kiyi barcinki kinji?kafin tashi daga taron" ammi ta faɗa tana mai kamo hannun fattu cikin nata ,suka fice daga ɗakin. Binta fattu tayi ba tare da ta musaba, dan tana tsananin jin kunyar ammi,saidai haka kawai taji gabanta na faɗuwa,gashi hammanta yace karta fita ko ina ,karya dawo bai ganta ba ransa ya ɓaci. Haka dai tabi ammi har zuwa wancan part ɗin da Rashad take ciki. Wani ɗaki ammi ta kaita tare da zaunar da ita akan kado,tace cikin murmushi"ki zamanki anan kinji,idan kina jin barci saiki kwanta,akwai abubuwan ci ,acikin fridge idan kinji bukatar ci" ammi ta faɗa tana mai kallon fattu ,fuskarta ɗauke da murmushi. Jinjina kai fattu tayi kafin tace "inna !Hamma yace karbaje ko ina ,karya dawo kuma bai ganni ba"ta faɗa kanta aƙasa. Wata uwar harara ammi ta bankawa fattu,kuji yar iyayi shegiya mai kama da aljanu,zaki gane kurenki, ne yau zaki yabawa aya zaƙinta,dagake har Adeeb ɗin. Da sauri ta saki fuska tana murmushi,ganin fattu ta ɗago kai tana kallonta,"karki damu habeebtee zan sanar da Adeeb nina kawoki nan kinji?"ammi ta faɗa tana sumbatar goshin fattu .kafin ta fice daga ɗakin. Rashad ta ci karo dashi abakin ƙofar ,daga shi sai wando iya gwuiwa da singlet,kallonsa ammi tayi cike da murmushi,tana mai faɗin"Rashad kenan,wannan zumuɗin haka?,nidai ka kula da maganata banson asami matsala" ammi ta faɗa tana mai kamo kunnensa. Murmushi yayi yace "baki da matsala ammina,ke dai kawai kijira sakamako"ya faɗa yana mai murmushin mugunta. "Amma ka jira sai an jima kadan,zan kulle ƙofar ta baya,inka gama sauka fice ta ɗayan ƙofar" jinjina kai Rashad yayi cikin zaƙuwa da son ammi tayi ta fice daga ɗakin. Adeeb yana zaune kusa da abie ,saidai haka kawai yakejin gabansa na faɗuwa ,sosai yake jin faduwar gaban.fattu kawai yake tunani yana ji cikin ransa yana buƙatar ganinta ahalin yanzu. Kallonsa ya kai inda Rashad ke zaune,saidai ba alamunsa agurin.gabansa ne ya ƙara mugun faɗuwa,ina Rashad ya nufa?yaushe ya bar gurin? Da sauri ya yunƙura zai mike,dan zuwa ya duba fattu,saidai gurin taron ne ya kara de da kiran sunansa Adeeb,ana buƙatar yayi jawabin godiya ga baki . Kallon abie yayi cikin yanayi na marairaita ,amma abin ya jinjina masa kai alamun yaje yayi jawabin. Haka Adeeb ya karbi lasifikar nan badan ransa yaso ba,burinsa kawai yaje gurin fattu. Adaidai wannan lokacin kuma Rashad ya kulle ƙofofin ɗakin daga falon har zuwa toilet duka,ɗakin da fattu ke ciki kawai ya bari abuɗe .kai tsaye ya kunna kansa cikin ɗakin. Fattu na zaune abakin gadon inda ammi ta zaunar da ita,zuciyarta sam bata aminta da zaman ɗakin nan ba, sai kalle kalle take, Da sauri ta juyo atsorace jin kamar mutum atsaye akanta. Ido huɗu sukayi da Rashad tsaye abakin ƙofa yana kallonta ,fuskarsa ɗauke da murmushi irin na yan duniya, Da sauri fattu ta miƙe tsaye jikinta na rawa,me wannan mutum yake yi anan kuma?ba innar Hamma tace nan ma ɗalibta bane?innalillahi,wayyo hammana kana ina?fattu ta faɗa cikin ranta jikinta na rawa matuƙa. Murmushi Rashad keta famanyi,yana takowa cikin ɗakin bayan ya kulle ƙofar,cikin harshen larabci yake faɗin"yan mata meye na tsorata haka?nimafa nazone nayi miki abinda wancan wawan yayan nawa ke miki,ki nutsu yarinya musha daɗinmu tare ,dan kuwa yau wllh ko mutuwa zakiyi saina kwashi daɗi" ya faɗa yana mai karasowa bakin gadon. Kuka fattu ta fara tana mai yarfe hannu, dan kuwa sosai take fahimtar yaren yanzu,dan haka ta fahimci da dama abubuwan daya faɗa, "Wayyo Allah na kayi hakuri dan Allah ,wllh niba yar iska bace ,kuma Hamma baya min komai,kayi min rai dan Allah"fattu ta faɗa cikin kuka sosai tana ja da baya. Zagaye suka fara ita da Rashad,yana ƙoƙarin kamota,ita kuma tana zillewa cikin kuka tana masa magiya,akan ya barta karya mata komai. Ganin zata ɓata masa lokaci ne kawai yayi wani tsalle tare da damko gashin kanta cikin fushi ya wanka mata mari tare da hankaɗata kan gadon. "Dan ubanki ki nutsu wllh idan kika ɓatamin lokaci,saina yi miki fata-fata anan gurin,kina abu kamar baki san me nake sanyi ba ,ko irin baki taba yi ɗin nan ba,shi wancan wawan idan yazo haka kike masa?Rashad ya faɗa cikin tsawa yana mai haurowa kan gadon. Cikin azama fattu ta mirgina can karshen gadon tana kuka,tare da kiran "wayyo hammana kazo ,Hamma kazo ka taimakeni" Ran Rashad ne ya ƙara ɓaci ganin zata ɓata masa lokaci,da sauri shima ya bita ya damko gashin kanta,ya ƙara wanke ta da mari, nan da nan gefen bakinta ya fashe jini ya fara zuba. Ihu fattu ta kwalla cikin azaba tana kuka tare da riƙe hannunsa daya damko gashin kanta . Ƙoƙarin Rashad yake ya haɗe bakinsa dana fattu ,amma sai kauda kai take tana kuka tare da juya kai. Bakinta Rashad ta matse da karfin gaske ,gaba ɗaya kamaninsa sun sauya ,ba abinda yake so da buri illa yabiya buƙatarsa da fattu.gashi sai neman bashi matsala take. Hannunsa ɗayan ya ɗora akan ƙirjin fattu ,zaro ido fattu tayi cikin tsantsar razana da jin hannunsa inda ba wanda ya taba ɗorawa,da karfi ta dunkule hannunta tare da buga masa aciki. Ihu Rashad ya kwalla Dan kuwa ta bugeshi sosai acikinsa. Hankaɗata yayi jikin bango ,aikuwa ta buga kanta ajikin bangon ,ji kake gummm!!ta gwara kanta. Ihu ta kwalla cikin azaba tana mai dafe goshinta da jini ya wanke ,tsabar azaba numfashinta har ɗauke wa yake. Ko tashi ta kasayi,da rarrafe ta nufi bakin ƙofa jini na zuba agoshinta. Cikin mugun bacin rai Rashad ya nufota, rigarta ya kamo ta baya ya fizgota baya. Mari yayi ta sauƙe mata har guda hudu,sannan ya cilla ta kan gadon, Gaba ɗaya fattu ta fita daga hayyacinta ,ko hannunta bata iya dagawa,numfashinta sai kaiwa da kawowa yake, Rashad kuwa cikin rashin imani ya zare wando sa tare da singlet yayi kan fattu gadan -gadan ,yana zuwa ya janye gadon tare da kama rigar fattu ya yagatadaga sama har ƙasa ,sannan ya........... Wayyo fattu ,Hamma kana ina kazo ka ceci fattunka,shikenan Rashad zai cutar da fattunka . Da gudu na fice dan nemo inda Adeeb yake .saiki biyoni muje nemansa tare. Taku ce anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 53/54 ________________Gaba ɗaya Rashad ya zama kamar wani mahaukaci,ba abinda ke gabansa face biyan buƙatarsa. Gaban rigar fattu ya kama da karfin tsiya ya tsargeta ,tun daga sama har ƙasa. Nan da nan farar best ɗin fattu da baƙin skin tite ɗin ta suka bayya, Allah ma yasa wandon har ƙasa yake. " Wllh yau ko da zaki mutu ,saina ida nufina akanki,banga wanda zai iya karbarki daga hannuna ba" Rashad ya faɗa cikin wata irin murya ta azzalumai,waɗanda suka manta da cewar Allah yana kallonsu duk abinda suke aikatawa. Da gyar fattu ta iya buɗe rinannun idanunta ,wanda tsabar mari da kuka suka sanya idanun kumbura sosai. Ahankali take daga lips ɗin ta magana take amma saiƙa kura mata ido zaka fahimci me take cewa."wallahu galibun ala amrina" shine abinda take ta maimaitawa abakinta. Ƙoƙarin zare skin tite ɗin Rashad keyi amma sam ya kasa,jikinsa sai rawa yake,yana jin kamar wanda ake jona masa shocking,Amma tsabar masifa da jaraba ,yaki fasa abinda yakeyi, Cikin haushi,ya ƙara kaiwa kumatun fattu mari mai zafi da shiga jiki."Dan ubanki me kikasa ajikinki?idan na taɓaki nakejin kamar ana zuƙemin jini?"Rashad ya faɗa yana mai kai fuskarsa saitin Tata,bakinsa ya ɗora akan na fattu,aikuwa ba wata wata fattu ta gartsa masa cizo alips ɗinsa.kara ya kwalla yana mai komawa gefe dafe da lips ɗin sa na ƙasa "kai -kai -kai Ni kika ciza Dan uwarki?zaki gane kurenki ,wllh yau saina kusan kasheki Shegiyar yarinya mai taurin kai"Rashad ya faɗa yana mai danƙo gashin fattu ,wanda yayi buju-buju. Fattu fa ko motsin kirki bata iyayi,gaba ɗaya jikinta ya saki,tunda take a rayuwarta,bata taɓa shiga tashin hankali da azaba irin na yauba. Sunan Allah kawai take ambata cikin ranta. Adeeb kuwa cikin gaggawa yayi jawabinsa tare da godiya ga baƙin da suka zo dan tayashi murnar dawowa gida cikin ƙoshin lafiya.sosai ƙirjinsa ke mugun bugawa zuciyarsa kamar zata fito waje,idanunsa sunyi jajur dasu,wani irin ɗaci yakeji cikin zuciyarsa,sannan ko dana second ɗaya ne fattu taƙi barin tunaninsa. Gefen da Rashad ke zaune Adeeb ya ƙara kai dubansa, baya gurin har zuwa yanzu,kai gaskiya akwai Abinda ke faruwa ,dole yaje ya duba Hulwa. Dan haka cikin hanzari ya mike tsaye ,kallonsa abie yayi tare da tambayar ina zashi haka ?ya mike cikin hanzari,sanar da abie yayi cewar kansa ke ciwo yana son yaje ya kwanta. Sanin da abie yayi cewar ,sam Adeeb yana son hayaniyane,yasa shi cewa yaje ya kwanta sannan yasha magani,akwai maganar da zasu yi zuwa dare. Cikin sauri da sassarfa Adeeb ya nufi ƙofar barin hall ɗin,yana ɗan kallon gefen da tareeƙ ke zaune,saidai baiga tareeƙ agurin ba.dan haka ficewa yayi daga hall ɗin yana mai takawa da sauri sosai. Bangaren nanny ya nufa kai tsaye,yana shiga ya tarar da tareeƙ da nanny atsaye cirko -cirko,gabansa ne ya ƙara faɗuwa ,da sauri ya karasa gurin nanny yana kallonta,"nanny Ina Hulwa?"ya faɗa cikin muryar damuwa. Kallonsa nanny tayi itama da alamun damuwa akan fuskarta tace " to magajin fada,nan da ka ganmu wllh ita muke nema,naje gurin taron can kenan,na barta tana barci,kuma ina dawowa naga bata ɗakin,na duba ko ina cikin bangaren nan banganta ba,saiga tareeƙ kuma yana tambayar ko Rashad ya shigo nan" Da sauri Adeeb ya nufi ɗakin da fattu ke zaune gabansa naci gaba da bugawa da ƙarfi. Ko ina ya duba amma bata nan,to ina taje?yasan dai ba yawo takeyi ba ,ba inda ta sani cikin fadar nan,ko part ɗin sa ma sau ɗaya ya kaita,da sauri ya juyo yana kallon tareeƙ," Ina Rashad yayi?"ya tambayi tareeƙ cikin wata irin murya mai kama da ta basawa. "Yallaɓai ina zaune naga lokacin da Rashad ke waya,kuma saiya fito waje,hankalina bai kwanta da fitowar sa ba,dan haka saina biyoshi,ina fitowa na hangesu shida Zulaihat,dan haka na buya ina sauraron me zasuce,yallaɓai amma banji me suke tattaunawa ba,saidai ga dukkan alamu akwai abunda suka ƙulla tare, sai dai kuma basu sami jituwa ba,dan kuwa cikin fushi suka rabu. Nayi ƙoƙarin bin Rashad Dan ganin inda ya nufa amma ban ganshi ba" tareeƙ ya faɗa yana kallon Adeeb cikin damuwa. Dafe kai Adeeb yayi zuciyarsa na masa zafi,lallai idan har wani abu Rashad ke ƙoƙarin aikatawa akan Hulwa ,to zai gane kurensa wllh azeem,saiya ɗanɗani kudarsa. Cikin sauri Adeeb ya nufi ƙofar fita daga part ɗin,tareeƙ ya na biye dashi,ganin zasu fice yasa nanny tayi saurin bin bayansu dan bazata iya zama ba. Suna fita daga part din, kai tsaye Adeeb part din ammi ya nufa,ko fattu can ta tafi,saidai suna gab da shiga ya tsinkayi Muryar ammi na kiran sa,tsayawa yayi harta ƙaraso,"lafiya na ganku haka afujajan?gashi ka bar gurin taro ba'atashi ba?"ammi ta faɗa tana karantar yanayin Adeeb. Ahankali Adeeb ya sauke wata ajiyar zuciya mai zafi,tare da lumshe idanu kana yace "ammi mun rasa inda yarinyar nan tayi ne ,shine zamu duba ko tana party ɗinki" Adeeb ya faɗa cikin yamutsar fuska kamar zaiyi kuka. "Hmmmmm ji dan Allah wai akan wannan Shegiyar yarinyar suka tada hankalinsu haka,dan kawai basu ganta ba. Tukunnama wllh sai kunga yadda rayuwarta ta koma yanzu,dan nasan Rashad ya kammala aikinsa"ammi ta faɗa cikin zuciyarta,amma azahiri, Cikin hanzari ta riƙo hannun Adeeb tana mai zaro ido." Ikon Allah ina kuma ta nufa?dan gaskiya bata part ɗina, sai dai kuma ɗazu naga Rashad yana shawagi tsakanin part ɗina Dana nanny,Allah yasa bashine yayi mata wani abu ba" cewar ammi tana mai dafe kai cikin nuna tsantsar tashin hankali. Gaban Adeeb ne ya fadi ,shikenan dama yasan hakan zata iya kasancewa, dan kuwa sam yau bai yarda da Rashad ba dama ,"innalillahi "Adeeb ya faɗa cikin ruɗu da tashin hankali. Da sauri ya kunna kansa cikin part ɗin na ammi,suka rufa masa baya. Saidai nan ma sunyi iya bincike su amma bata nan,wasa -wasa fa sune har part ɗin Rashad Amma bashi ba Hulwa,zuwa wannan lokacin Adeeb ya shiga tsantsar tashin hankalin da bazai misaltuba,gaba ɗaya fuskarsa tayi jaaa kamar manja, idanunsa sun koma kala kalan nan,idan ya buɗe baki har wani turiri zakaga yana fitowa daga bakin nasa. Hankali kowa ya tashi,tsakanin ammi ,tareeƙ ,nanny dakuma amma ,wacce ta tsincesu abangaren Rashad,Dan itama nemansa tayi ta rasa agurin taron,shine tazo dubawa ko part ɗin sa ya dawo. Sai kuma ta riskesu suna dubansa.sosai tashiga tashin hankali,karfa Rashad ya janyo mata wata sabuwar matsalar,amma tasan ma bai zama lallai abinda suke zargi ya kasance ba. Cikin wani irin voice Adeeb ya juyo yana kallon amma tare da fara magana " wllh !wllh!!wllh!!! idan wani abu ya sami hulwa ta silar ɗank,i nayi alƙawarin saina illatashi,ta yadda ke kanki bazaki so ganinsa ba" Adeeb ya faɗa yana mai nuna amma da ɗan yatsanshi, tsabar masifa da bala'i kumatunsa har rawa suke. Cikin tsoro amma ta ja baya tana mai dafe ƙirjinta ,dan kuwa ta tsorata da yanayin na Adeeb,tana kuma fatan Allah yasa ba hannun Rashad aɓatan fattu. Can kuwa wajen taro ,anyi addu'oi,kuma anci ansha taro ya tashi lafita,abie yana ta tunanin ina iyalin nashi suka nufa ,dan baiga kowa agurin taron ba,zuciyarsa na raya masa akwai Abinda ke faruwa ,dan haka kai tsaye bayan ya sallami baƙinsa ya nufi bangaren sa ,jakadiyarsa ya tura cikin gida dan ta gano masa ko lafiya. Adeeb yana gama korawa ammi warning yayi waje cikin zazzafar zuciya da jin jikinsa yana masa wani irin rawa,idanunsa gaba ɗaya ya rine zuwa kalar na macizai.tsoro sosai ya kama su ammi da nanny,hatta tareeƙ atsorace yake,dan bai taba ganin yallaɓan nashi cikin wannan yanayin ba. Part ɗin sa ya nufa kai tsaye,saidai yana zuwa saitin ɗaya part ɗin na ,ammi yaji zuciyarsa ta tsananta da bugawa ,cak yaja ya tsaya tare da ƙure ƙofar part ɗin da idanunsa.zuciyarsa na raya masa ya shiga ya duba,saidai yana tunanin ammi bata fiye amfani da bangaren nan ba ,kuma me zai kawo Rashad nan ma ? Idan kuma yazo nan ɗin da Hulwa dan kawar da tunaninka fa ?ɗayar zuciyar ta bashi amsa.dan haka ba bata lokaci ya kama handle ɗin kofar ya murza da zummar shiga,saidai kuma akulle yaji ƙofar ,hakan ya matukar bashi mamaki,dan kuwa kullum part din nan abuɗe yake ,koda ammi bata ciki akwai hadimai acikinsa.amma how comes yau zai kasance akulle haka.nan take zuciyarsa ta bashi lallai Hulwa na cikin part ɗin nan.daidai lokacin su ammi suka ƙara so gurin.kallon tareeƙ yayi cikin wata irin murya yace " na tabbata Hulwa na cikin nan,saidai ina mamakin yadda part ɗin ya kasance akulle karon farko" ya faɗa yana kallon ammi,wacce tayi wiƙi -wiƙi tsoro ya ɗan bayyana akan fuskarta. Dan kuwa Adeeb ya kafeta da mayun idanunsa.sam ba zargin ta yake ba,kawai yana tunanin yadda aka yaudareta ne itama har akayi amfani da part ɗinta.dan baya raba ɗaya biyu cewar Rashad na cikin part ɗin. Cikin in-ina ammi tace "habeebe a.a.a...k.wai spy ..kk...eyy " ta faɗa cikin jan numfashi. Kallonta tareeƙ yayi cike da zargi,dan shikam harga Allah tun farko ita ya zarga dan yasan bakin nufin ta akan abun daya shafi Adeeb sarai. Amma ma kallon ammi take cike da tuhuma,karfa tuggu ta haɗawa Rashad Dan kawai tana son ganin bayanta? " Wai wannan wane irin wandone kika sa ?kusan minti nawa ina ƙoƙarin cirewa amma na kasa?wllh idan ma wani siddabarun kikayiwa wandon nan yaƙi fita,to zanyi abuna ahaka, dan ubanki yau ɗin nan nayi alƙawarin ,sai Adeeb yayi kwanan baƙin ciki "Rashad ya faɗa yana hankaɗa fattu kan wani ƙaton tebur dake ajiye gefen gado ,da alama an ajiyeshine ɗan ɗora kofuna ko abinci idan bukatar hakan ta taso. Aikuwa tana fadawa ta fada kan wani glass cup, nan da nan ya tarwatse gaba ɗaya ya sossoketa aƙirjinta da wuyanta.wani marayan ƙara fattu ta sanya ,wanda koshi Rashad baiji sautin ƙaranba, dan kuwa muryarta tayi mugun dashewa.ahankali idanunta ke lumshewa yana budewa,gaba ɗaya jini ya bata farar best ɗin dake jikinta.amma bako imani bare tausayi haka Rashad yake ƙoƙarin keta mata haddi, ba tare da ya cire koda wannan skin tite ɗin ba. Wata irin zabura Rashad yayi sakamakon ƙaran da fattu ta kwalla,wanda yayi daidai da ƙarar faduwar kofar dakin . ”RASHAD!!!!!!............" Aka kwallah kiran sunan Rashad Wanda saida Rashad ɗin ya buge kansa ajikin tebur ɗin nan tsabar razana da yayi da wannan kiran sunan nashi da akayi...... Hmmmmm masu karatu,nima tsabar tsoro bansan sanda wayar hannuna ta fadi kasa ba,mutara zuwa gobe idan na ɗauki wayar .fatana dai wayata bata fashe ba. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 55/56 _________________"RASHAAADDDD" Aka kwallah kiran sunan Rashad,Wanda saida ɗakin ya amsa.gaba dayan mutanen da suka shigo ɗakin saida suka tsorata ,saboda yadda amon Muryar ya fito da mugun ƙarfi da sauti mai firgitarwa. Ahankali fattu da ke neman macewa ta buɗe kunburarrun idanunta da gyar,ta saukesu akan fuskar hammanta, wata shashshekar kukace ta zo mata ,numfashinta na hawa da sauƙa ,da gyar ta daga hannunta tana mikawa Adeeb , Da wani irin mugun sauri Adeeb yayi kanta yana mika mata nashi hannu,saidai kafin ya ƙara so tuni hannun nata ya koma ƙasa sharaff!! Ahankali kuma idanunta suka kulle ,duk wata jijiya dake jikinta tasaki,ataƙaice dai fattu ta sume. Wani irin ƙara Adeeb ya kwalla mai matukar firgitarwa ,hayaƙi na fita ta bakinsa da hancinsa, hannun fattu ya kama ya riƙe cikin nashi tare da damkewa kamar zai balla hannun nata. Jikinsa gaba ɗaya rawa yake kamar ana kaɗa masa gangi,ɗago da kansa yayi afusace ya sauke idanunsa akan Rashad,Wanda tsabar tsoro ya kasa koda matsawa daga kan table ɗin gashi tsirara haihuwar uwarsa. Da sauri Rashad ya runtse idanunsa,numfashinsa na wani irin hawa da sauka kamar shima zai shide tsabar tsoron ganin yadda idanun Adeeb ya koma,ga wani irin bakin hayaƙi daya fara cika ɗakin, Wani ƙaran Adeeb ya sake kwalla,wanda yafi na farko sanya tsoro da razani,gaba ɗaya dakin yayi wani irin bakiƙirin ,baka ko ganin hannunka bare na kusa dakai. Su ammi da amma,nanny tareeƙ ,jakadiya,da Zulaihat wacce zuwan ta kenan,bangaren dan ta sami labari gurin yan s.i.d ɗinta.gaba daya tsoro ,firgici da tsantsar mamakin abinda ke faruwa yasa sun kasa koda motsine agurin ,bare suyi wani abu. Sun ƙanƙame juna jikinsu yana wani irin bari,nanny Banda sunan Allah ba abinda take ambata"innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, meye wannan ke shirin faruwa haka,tareeƙ kana ina bana ganin komai fa " nanny ta faɗa tana ƙanƙame tareek dake kusa da ita. Shi kansa tareeƙ jikinsa rawa yake ,sam ya kasa magana sai rungume mahaifiyarsa da yayi sosai ajikinsa. Ƙaran rashad ne ya karaɗe dakin ,cikin wani irin sauti na azaba,wanda kana jinsa kasan wanda ke wannan karan yana cikin azaba da halin ƙunci. Kuka kawai amma ta sanya ,dan tasan yau kam ɗan ta sai abinda hali yayi,shikenan yau abinda ake shukawa agidan ya dawo kansu. Ahankali ɗakin ya fara washewa daga tsantsar duhun da yayi ,kusan minti uku suna cikin halin tsoro da razani kafin ,suka fara ganin komai tar-tar . "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shine abinda Dukansu suka haɗa baki wajen faɗa,sakamakon ganin wani narkeken maciji mai girman gaske nannade da Rashad ,Wanda kallo ɗaya zakayiwa Rashad kasan cewa ba alamun numfashi atare dashi. Kallon kallo ake tsakanin mutanen dake cikin dakin,wanda suka shiga tashin hankali fiye dana farko,dan kuwa ba Adeeb aɗakin sai wannan narkeken macijin,wato dai Adeeb shine ya zama wannan macijin. Jikin nanny Banda rawa ba abinda yake ,haka ammi da amma,jakadiya da Zulaihat wacce tuni ta jiƙa jikinta da fitsari,tana tsaye ƙanƙame da amma wacce itama ta ƙanƙame Zulaihat ɗin. Sun kasa magana sai kallon ikon Allah suke. Macijin nan yana tsaye nannade da Rashad ya fasa kai yana wani irin huci da fesar da wani irin bakin abu daga bakinsa.juyi ya farayi da ƙarfi kafin ya maka rashad ajikin bango,ji kake timmmm!!Rashad ya baje akasan tyles,tuni jini ya fara zubowa daga kansa.hakan bai ishi macijin nan ba ya kara zuwa ya nannade Rashad tare da kara makashi jikin bango. Ihu suka farayi ganin macijin nan na ƙoƙarin tarwatsa kasusuwan Rashad. Da gudu jakadiya ta juya tayi waje tana ihu ,ta nufi part ɗin mai martaba,tana faɗuwa tana mikewa,gaba ɗaya bata cikin hayyacinta. Zulaihat ma silalewa tayi agun ba alamun numfashi atare da ita. "Wayyo jama'a ku taimaka min ,zai kashemin yarona,wayyo Allah na na shiga uku ku taimaka min"amma ta faɗa cikin ficewar hayyaci,dan tsabar tsoro gadan gadan take nufar cikin dakin gurin da Rashad ke kwance ayashe, aikuwa kafin ta ƙarasa kaiwa inda Rashad ke kwance, saijin wani abu tayi mai kama da bulala ya fyadeta a gadon bayanta,wani ihu amma ta kurma tare da faduwa sakamakon azabar raɗaɗin da taji gadon bayanta ya ɗauka.da rarrafe ta koma inda take tsaye. Jikinta na rawa . Ammi fa tsoro ya gama kasheta,dan ko tsayuwar kirki ta kasayi, sam batayi tsammanin haka abin yake ba,ashe dai da gaske mutum yana iya komawa wata halittar ta hanyar asiri?lallai yau taga abinda ya fi ƙarfinta , sam bata tsammaci abun haka yake ba, amma dole tayi wani abu dan gudun zargi.dan haka cikin bugawar zuciya da tsananin tsoro ta fara takawa zuwa gurin da Adeeb ke tsaye yana zagaya Rashad yana huci. "A...a.ddd..ee.e.bbb."ammi ta kira sunansa cikin tsinkewar numfashi, shikuwa baiko kalli inda take ba ,burinsa kawai yaga Rashad yayi motsi ya kara karairaya masa inda bai gama lalacewa ba. "Ka nutsu Adeeb ɗana,.n...i.cce ammin ...ka, ka ...ka...ji."ta faɗa tana matsawa cikin tsoro da firgici. Ai kuwa jin takunta da adeeb yayi ,afusace ya juyo tare da kai mata tsafka, cikin sa'a kuwa ya damketa,ihu ta farayi tana neman taimako,"wayyo Allah na taimako jama'a taimako"ammi ta faɗa lokacin da Adeeb ke nannaɗeta kamar buhun goro.saida yagama naɗeta sannan ya fasa kansa saitin fuskar ammi yana huci.tsabar firgici tuni ammi ta sume ,kura mata ido Adeeb yayi kafin ya fara dakinta ahankali ,ta faɗa kan gado. Gurin fattu ya koma tare da hawa gadon bayanta, nade ta yayi tare da mirgina ta ta juyo rigingine,kallon fuskarta yake wani irin farin Ruwa na zubowa daga idanunsa ,kwanciya yayi akan cikinta yayi lamo yana mai juya kansa ,tare da yin wani irin ƙara yana bude bakinsa. Al'amarin yayi matuƙar tsorata dukkan wadanda ke cikin dakin,dan nanny ma tuni ta sume ,amma ce kawai mai ƙarfin hali ,dan tana zaune riƙe da bayanta da tasha bulala. Tareeƙ kuwa hawayene ke zuba daga idanunsa.yana matukar tausayawa yallabai ɗin nasa. Ana cikin wannan halin ne,abie ya shigo dakin tare da waziri da manyan faɗa ,sai Shaikh lateef ,babban malamine dake koyar da ilimin addini sannan masani akan abinda ya shafi jinya da maganinta, ya ƙware sosai wajen magance abun daya shafi sihiri. Lokacin da jakadiya ta kaiwa abie labarin,shikuma suna tare da su waziri suna ɗan tattauna wata magana mai muhimmanci,shine suka garzayo gaba ɗayansu, ɗan ganin abinda ke faruwa. Ba ƙaramin kaɗuwa abie yayi ba,lokacin da ya wannan kumurcin macijin amatsayin Adeeb ɗinsa,hawaye ne kawai ke zuba cikin idanunsa, ya ƙurawa Adeeb ɗin ido.tunanni kawai yake ,waye wanda yayiwa adeeb wannan aika -aikar?me yatsarewa wanda yayi masa haka?ace yaro mai gata dan sarauta kamar Adeeb yana zama maciji?duk yadda Adeeb ya kasance mai tausayi da taimakon al'umma ,amma ashe wasu suna can suna shirya masa mugunta.lallai dole ya tsaya tsayin daka ,wajen bawa yaronsa abin sonsa kariya ta ko wacce siga.yasan ammi na ƙoƙarin wajen yiwa adeeb addu'a ,kuma tana sawa ayi masa kamar yadda take faɗa amma dole shima ya dage ta bangarensa. Abie ne ya kalli Shaikh lateef,cikin damuwa da zubar hawaye yace "Shaikh kaga Adeeb ga ,kaga halin da yake ciki,menene abinyi ?abie ya faɗa yana mai share kwalla. Shaikh lateef kuwa wanda tun shigowar su yake kallon Adeeb,kallo na tsinake,sai lokacin yayi ajiyar zuciya kana ya kalli abie,yace" ranka shi daɗe lallai Adeeb yana cikin tsaka mai wuya ,da tuggun maƙiya ,amma In Sha Allah komai yazo ƙarshe,yanzu dai ayi ƙoƙarin diban bayin Allah dake kwance dan akaisu ga likita,sannan sai musan abinda ya kamata muyi"Shaikh lateef ya faɗa yana mai kallon abie. Nan da nan kuwa aka kwashe su ammi da nanny,Zulaihat ,sai dai ko yaya akayi yunƙirin zuwa inda Rashad ke wance kamar gawa,take macijin nan zaiyo kan mutum afusace. Ganin haka ya sanya abie cikin ƙarfin hali ya tunkari Adeeb dake fagen fattu yana fasa kai,ya kasa ya tsare, Ahankali abie ke kallon Adeeb da idanuwansa masu fidda hawaye kafin yace"habeebee kayi hakuri adauke dan uwanda,dan asuba lafiyarsa, koma me yayi maka nine nan,zan ɗaukar maka mataki,bazan taɓa yarda da zalunci ba"Abie ya faɗa cikin sanyin murya yana kallon Adeeb. Huci kawai Adeeb keyi yana kallon Abie kafin ya maida kansa ga fattu yana kallonta,sannna ya ɗago kai ya kalli abie, Jinjina kai abie yayi cike da fahimtar Adeeb ɗin yace "na fahimta habeebee,dole zan ramawa yarinyar nan abinda rashad yayi mata,dan kasan ba'a zalumci amasarautata" abie ya faɗa yana mai ƙara sawa kusa da Adeeb ɗin ahankali ya sanya hannunsa yana shafa bayan Adeeb. Shikuwa Adeeb sai huci yake yana guri da wata iska mai matukar zafi.haka aka samu aka lulluɓawa Rashad Abu ajikinsa kafin kayi waje dashi, amma duk yadda akayi ƙoƙarin ɗauke fattu Adeeb ya hana ,dan hatta mai martaba ,da yayi yunƙurin daukar ta saida Adeeb ya kai masa tsafka.haka suna ji suna gani ba yadda suka iya,sai lulluɓe mata jiki da sukayi itama ,dan kuwa yaƙi barin jikinta ma. Shaikh lateef ne zaune gaban Adeeb yana karanto wasu addu'oi yana tofa masa,lokaci guda jikin Adeeb yayi laushi, gaba ɗaya baya ko kwakwkwaran motsi,sai huci da yake fiddawa ,ya dora kansa akan ruwan cikin fattu dake lulluɓe,jikinsa sai wani bakin hayaƙi ke fita. Ci gaba Shaikh lateef yayi da addu'ar sa yana tofawa Adeeb,yayin da su abie ke gefe guda suna kallon ikon , Allah,dan zuwa lokacin murƙususu kawai macijin nan keyi,kafin wannan hayaƙin ya turnuke dakin,baka iya ganin komai tsabar duhu. Su abie suma addu'a suka fara,lokacin da suka ga wanan hayaƙin,dan Shaikh lateef yace karsuji tsoron komai ,duk abinda zasu gani kawai suyi addu'a. Can kusan wucewar mintuna biyar suna ta addu'oi ,dakin ya fara haske yana washewa har ya gama washewa tar, kamar ba shine yayi wannan duhun ba. Adeeb ne durƙushe agaban wannan table ɗin da fattu ke kwance,kansa har lokacin yana kan cikin fattu. Hamdala Abie da su waziri sukayi,ganin Adeeb ya dawo asalin halittarsa, dan abie yayi matuƙar tsorata, kar ace ahaka Adeeb ɗin zai zauna. Ahankali Adeeb ke buɗe idanunsa ,da har zuwa lokacin basu gama komawa normal ba. Kanshi ya daga da gyar yana ɗan yatsine fuska tare da dafe kan,dan ciwo yake masa sosai. Sai kuma yayi saurin zabura ya mike tsaye "Hulwa" shine abinda ya faɗa cikin daga murya yana waige waige, " Habeebee ka nutsu kaji ga hulwar taka nan kusa da kai "abie ya faɗa yana mai mikewa shima tare da riko kafadun Adeeb. Sai lokacin Adeeb ya ga su abie aɗakin,kallon abie yayi kafin ya kalli inda abie ke nuna masa,zaro ido yayi ganin hulwarsa kwance kamar gawa,"Hulwa " Adeeb ya faɗa yana mai girgiza fattu,amma ina Hulwa tayi nisan zango. Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungumeta tare da fashewa da wani irin kuka mai tsanani ciwo da zafi.irin kukan da Adeeb keyi kaɗai zai fahimtar da kai yadda yake jin Hulwa da kuma ciwo acikin ransa. "Rashad ! Rashad !! Rashadddd!!!ka tabka babban kurkuren ƙoƙarin tabamin mata,kayi kurkure,idan Hulwa ta mutu"yayi shiru yana mai goge hawayen dake kwatanta cikin idanunsa,kafin ya ɗago idanunsa da suka yi wani irin mugun jaaa,ya kalli Abie sannan yaci gaba"wllh billahi,saina kashe Rashad ,idan har matata ma mutu sanadin sa"Adeeb ya faɗa cikin karfafa murya da nuna gaskiyar abinda yake fadi har cikin ransa. Kallonsa kowa keyi acikin ɗakin,dan kuwa sun zama speechless,matarsa yake ta kira,kodai yarinyar nan amatsayin matarsa take?ko kuma yana nufin ita zai aura? Shine abinda yake ta yawo cikin zukatan su Abie. "Ya kamata akai yarinyar asibiti yanzu,nikuma zanje gida domin yin bincike akan larurar prince ranka shi dade"cewar Shaikh lateef yana mai mikewa tare da shafa kan Adeeb,dan yana tausayawa yaron sosai. " Haka ne Shaikh bari akaita asibiti yanzun nan " cewar abie yana mai kallon Adeeb dake ƙankame da Hulwa kamar zai maidata cikinsa. Kafin su ankara tuni Adeeb ya sungumi fattu yayi hanyar barin dakin da ita." Habeebee kayi hakuri akai yarinyar asibiti,kaima fa ba cikakkiyar lafiya gareka ba" cewar abie kenan ,ganin Adeeb na ƙoƙarin ficewa daga ɗakin. " Ba wanda zai kara tabamin mata abie ,domin itaɗin mallakina ce mata tace ta Sunnah,hakkin kula da ita yana kaina,dan haka bana bukatar taimakon kowa,karka manta ,likitanci bangarenane" yana faɗin haka yayi waje da fattu rungume aƙirjinsa. Kai tsaye fart ɗinsa ya nufa da fattu ,yana zuwa ya shimfiɗeta akan lafiyayyen gadonsa, kallo yabi jikinta dashi,cikin wani irin zafi da ƙunar zuciya,gaba ɗaya glasses sun maƙale ajikinta ,jini duk ya bata mata jiki.hatta fuskarta baka ganewa. Gimbiya suhaimat ce tsaye tana bin Adeeb da kallon sabe da yarinya akafadunsa,haka kawai gabanta ke tsananin bugawa,so kawai take taga yarinyar, Ko menene ya sameta oho?ahankali ta juya taci gaba da tafi zuwa dakin ammi,dan su basu san abinda ke faruwa ba. Zuciyarta gaba ɗaya taki samun nutsuwa ,ba abinda take son gani sama da wannan yarinyar,gaskiya bazata iya jurewa ba dole taje taga yarinyar,sannan ta san meke damunta?me yasame haka gaba ɗaya jikinta jini... Masu karatu ku biyoni dan jin gimbiya suhaimat zata je ganin fattu ne ko yaya? Taku anty mammy Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment more typing [30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 59/60 ________________Ahankali nanny ta ke kallon Adeeb,kafin ta sauke ajiyar zuciya,tunani take ta yadda Adeeb zai karbi wannan magana,ta yaya zata sanar dashi cewar,amminsa itace silar faruwar komai?shin zai amince da abinda zata faɗa masa ko yaya? Wane irin kallo zai musu idan yasan cewa amminsa ce ta kashe sarauniya Nazli da yaranta tare da baban tareeƙ,kuma abakinsu?anya kuwa basu barowa kansu aiki ba? "Nanny kiyi magana mana kinyi shiru, ki sanar dani wake da hannu akan hadarin nan?" Da sauri nanny ta dawo daga dogon tunanin data tafi,kallon tareeƙ tayi cike da karayar zuciya ,amma cikin ƙarfafa gwuiwa tareeƙ ya kalli nanny yana mai jinjina kai da nuna alamun ,kwantar da hankali. Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe Tana mai kallon fuskar Adeeb,kafin ta fara magana. "Magajin fada kamar yadda na faɗa maka,wasu abubuwan muna kallonsu ne ba a yadda suke ba,ka sani abinda zan faɗa maka ba ƙarya ,ba kuma cutarwa.shiru ta ɗanyi tana jinjina maganar kafin taci gaba"ba kowa ya shirya wannan hadarin ba, face Amminka"nanny ta faɗa tana mai kure Adeeb da ido. Da wani irin slow Adeeb ya mike tsaye bakinsa bude,zuciyarsa na wani irin bugawa kamar guduma, ji yayi kunnensa ya ɗauki wani ƙara ƙuuuuuuuu!!! Sai yake jin maganar ta nanny Tana rarrabewa,kamar baiji me take faɗi daidai ba,jikinsa rawa ya kama,ta yadda yana mikewa tsayen yaji kamar zai fadi dan haka da sauri ya koma ya zauna,idanunsa ƙuri,akan fuskar nanny, Cikin in-ina ya ke cewa"na...nan.,...y mek....Ike ..son....f..a...ɗ..I n..ee." ya faɗa numfashinsa na rarrabewa,ji yake kamar zuciyarsa zata fito tsabar yadda take bugawa. Da sauri nanny ta ƙaraso kusa da Adeeb ta zauna ,cikin nutsuwa take shafa bayansa tare da kallon fuskarsa cikin tausayawa,dole yaji maganar tazo masa kamar saukar aradu."ka nutsu Adeeb domin Abinda nake faɗa maka yana buƙatar nutsuwa,tabbas Amminka itace ta shirya wannan hadari,tare da taimakon wani ma aikaci dake cikin gidan nan,mai kula da harkokin motocin gidan"nanny ta faɗa cikin sanyin murya tana jin zafin rashin mijinta da uwar dakinta kamar yau abin ya faru. Kallonta Adeeb yake cikin wani irin yanayi na mamaki ,al'ajabi,tsoro,ruɗu dakuma firgici,ji yake kamar zuciyarsa zata iya fashewa ako wane lokaci,wannan wane irin magana nanny keyi?anya kuwa tana cikin hayyacinta?yaushe nanny ta koma maƙiyarsa ta hanyar hade kai da amma?dan su shiga tsakaninsa da amminsa? Dan kuwa yana tabbatar da cewa wannan shirin amma ne,lallai duniya ba tabbas .cikin zuciyarsa yake wannan maganar,kafin a fili ya kalli nanny ,sannan ya kalli tareeƙ,sai kuma yayi murmushi wanda yafi kuka ciwo ,sannan ya miƙe tsaye yana mai sanya hannunsa cikin aljihu,sannan ya fara magana bayan ya juya bayansa yana kallon bango" ban taba tsammanin cewa matar data raineni tun ƙuruciya zata iya hade kai da makiyana,ɗan ganin sun shiga tsakanina da ammina ba ,yau na kara tabbatar da cewa lallai wanda kake kallonsa matsayin masoyi ,to shine makiyinka aboye, amma bantaba tsammanin haka daga gareki ba nanny;Adeeb ya faɗa cikin zazzafar murya yana mai juyowa ,idanunsa sun kada sunyi mugun jaa, kallo ɗaya zaka masa kasan cewa zuciyarsa akaraye take.ci gaba yayi da cewa"nanny why ?why nanny me yasa zaki canja daga yadda na sanki?me yasa zaki so ganina cikin damuwa?na dauke ki tamkar mahaifiyata,duk wani abinda ya dameni ina zuwa gareki dan samun mafita,ammina tana kula dake da duk wani bukatun ki,amma meyasa kika hada kai da maƙiyanta?me yasa kika saida kanki dan bata alaka tsakanin da da mahaifiya?nanny why?tareeƙ me yasa nanny zatayi min haka?Adeeb ya faɗa yana mai riƙe kafadun tareeƙ idanunsa na zubda kwalla ,gaba ɗaya jinsa yake kamar ba shiba, wani sashen na zuciyarsa yana son karbar maganar nanny,saidai sashe mafi rinjaye na zuciyarsa na tunatar dashi wacece ammi agareshi,dan me zai yarda da batun nanny?. Cikin damuwa da alhini tareeƙ ya kama hannun Adeeb ,cikin murya mai nuna tabbatarwa ,tareeƙ ke fadin, "yallaɓai ka kwantar da hankalinka,kuma kayiwa maganar nanny kyakykyawar fahimta,da sannu zaka gano gaskiyar dake cikin batunta, yallaɓai munsan abubuwa da dama wanda kai baka sansuba,amma da sannu zaka gane da kanka"tareeƙ ya faɗa cikin marairaita yana kallon Adeeb. Fizge hannunsa Adeeb yayi tare da dafe kansa da yake jinsa kamar zai tarwatse,kafin ya kalli tareeƙ yana mai jinjina kai"well na gane ,na gane tareeƙ kaima kana bin bayan mahaifiyarka ko?da kai aka hada baki,am disappointed tareeƙ" Adeeb ya faɗa yana girgiza kai cikin karayar zuciya,idanunsa na fitar da hawaye mai tsananin zafi da ƙuna.ahankali ya juya ya nufi ƙofa yana dafe kansa . Cikin damuwa da zubda kwalla nanny ta miƙe da sauri tana kiran Adeeb" magajin fada karkayi saurin yanke hukunci akan maganata kana bukatar nutsuwa da bincike dan Allah ka yarda dani ɗana, bazan taɓa cutar da kaiba."nanny ta fada cikin zubda hawaye . Ko waiwayowa Adeeb baiyi ba ya fice daga ɗakin ,cikin sauri, dan ko ganin fuskar nanny baya sonyi ahalin yanzu.zuciyarsa na tafarfasa ,ji yake kansa kamar zai kama da wuta.kai tsaye part ɗin ammi ya nufa ko zai sami salama cikin zuciyarsa. "Tareeƙ ka gani ko?kaga Abinda nake faɗa maka,Adeeb ya riga ya makance,baya ganin laifin ammi ko kaɗan,yanzu bansan wane kallo zai rinƙa yi mana ba"nanny ta fada cikin kuka. Kamata tareeƙ yayi ya zaunar da ita akan kujera ,hannunsa ya sanya yana share mata hawayen dake zuba daga idonta,kafin yace " ummee na,ki kwantar da hankalinki,dama shi aikin alheri haka yake,dole saika fuskanci ƙalubale,nasan yallaɓai zaiyi fushinsa na wani lokacin kafin ya sauko,kuma nasan daga yau zai fara bincike akan abinda kika sanar dashi,In Sha Allah muke da nasara ,tunda akan gaskiya muke"tareek ya faɗa cikin yanayin ƙarfafawa mahaifiyar sa gwuiwa. "In sha Allah tareeƙ ,Allah ya datar damu"nanny ta fada tana share hawayenta. Ameen yace ,kafin suka ci gaba da tattaunawa akan matsalar. Kai tsaye ya shiga part din na ammi,ko kula gaisauwar da hadimanta keyi baiyi ba,dan zuciyarsa ba abinda take sai tafarfasa,bai taɓa tsammanin haka daga su nanny ba,lallai mutum bashi da tabbas. Afalo ya ci karo da sarauniya suhaimat,tana zaune da yaranta,suna cin apple da ya'yan itaceya ,gefe guda kuma suna kallo. Da gudu su zayyad suka taso suka rungume Adeeb suna murnar ganinsa,kansu kawai ya shafa tare da rungumarsu,shima. Kallonsa sarauniya suhaimat keyi,dan kuwa taga tarin damuwa cikin idanunsa. "Sannu yarima ,ya jikin naka?dana yarinyar ?"sarauniya suhaimat ta fada cikin yanayi na nuna damuwa . Lumshe ido Adeeb yayi cikin damuwa da yanayinsa na rashin son magana yace "da sauƙi" atakaice . "Allah ya bata lafiya " ta fada da yanayi na damuwa. "Ameen" Adeeb ya faɗa ahankali. "Ammin naka tana ciki"sarauniya suhaimat ta fada cikin kulawa. Kai kawai Adeeb ya jinjina mata kafin ya wuce zuwa cikin dakin. " Bangane ba ?kamar ya nayi sakacin da kwalbar ta fashe,bayan irin kulawa da ita da nake?kasan irin kuɗin dana kashe akan akwatin da aka ƙera na sanya kwalbar ciki? Shiru tayi ,da alama tana sauraron abinda ake faɗane daga can bangaren. "Shikenan ,yanzu muna cikin alhini ne na wannan abun daya faru,dan haka kajira nan da kwana biyu,zan nemeka,dan awannan karon aiki nakeso ayimin na ban mamaki,bana kuma son asami matsala " ammi ta faɗa cikin wani yanayi mai nuna ta shirya mugunta mai zafi cikin ranta. Gaban Adeeb ne yayi wata irin faɗuwa da har saida ya dafe ƙirjinsa,wane akwati ammi ke magana akai?wace kwalbar ce ta fashe?da wa ammi ke waya?waɗan nan sune tambayoyin da Adeeb ke yiwa kansa,saidai bashi da amsar ko daya daga ciki. Ganin ammin ta gama wayar kuma tana ƙoƙarin juyowa ne ,dan ta ba ƙofa baya,yasa Adeeb saurin saita kansa yayi sallama tare da shiga. Da sauri aɗan razane ammi ta juyo tana kallon Adeeb ɗin,dan batayi tsammanin ganinsa yanzu ba, saidai da alama baiji me take faɗi ba,itafa wllh tsoronsa ma ta fara ji yanzu,amma saita maze ta saki murmushi,tare da miƙa masa hannu,alamun ya ƙaraso gareta. Ahankali Adeeb ke takawa har yaje bakin gadon ya zauna,dan jikinsa sam ba kwari,murmushin ƙarfin hali yayiwa ammi yana kallon fuskarta, "Habeebee ya jikinka? na tsorata sosai da yanayin dana ganka ɗazu"ammi ta faɗa tana mai janyo Adeeb zuwa jikinta. Sam yau Adeeb ji yayi baya wani jin dadin kwanciya akan cinyarta,Dan saiyajisa kamar akan ƙaya, dan haka da sauri ya tashi daga kwanciyar da yayi,kafin ya dan saki murmushi,yana mai cewa"ƙalau nake ammi,kada ki damu,ya naki jikin?"ya faɗa sam fuskarsa ba walwala. "Shafa kansa tayi kafin tace naji sauki dana karka damu"ta faɗa tana kallon fuskarsa ,dan kuwa sam ba haka yake mataba,yau kam ba wannan shaukin da yake nuna mata idan suna tare. Mikewa yayi yana mai faɗin ammi zanje in duba yarinyar can zan dawo anjima" yana faɗin haka yayi waje abinsa. "Yawwa yarima ,ina son in duba yarinyar nan "sarauniya suhaimat ta fada tana mikewa lokacin da Adeeb ya zo zai wuce. Shiru yayi yana ɗan nazari,akwai bukatar ta duba ta ,tunda likita ce itama ,kuma fannin mata ta karanta. Dan haka yace "ok muje ,tana part ɗina" Ficewa sukayi tare suka nufi part din Adeeb. Toh masu karatu ,mubi su Adeeb dan duba Hulwa. Sai mun hade next page. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing.m [30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 57/58 ________________Gimbiya suhaimat ta gama tsara cewa data huta zataje part ɗin Adeeb dan ganin yarinyar nan, Saidai shigarta part ɗin ammi da yanayin da taga ammin yasa ta saurin,ƙarasawa cikin dakin ,cikin damuwa take faɗin"ukktee meke damunki? Yana ganki akwance?gimbiya suhaimat ta faɗa tana kamo hannun ammi ,wanda ba'a daura mata ruwa ajikinsa ba. Ahankali ammi wacce tayi nisa cikin tunani ta buɗe idonta tana kallon gimbiya suhaimat,kafin ta sauke ajiyar zuciya tare da lumshe ido ta buɗe" ke dai bari suhaimat,yau naga abinda ban taba gani ba arayuwata,nan ta bata labarin abinda ya faru,saidai ta boye mata asalin labarin fattu,sai cewa tayi wata baiwa ce Rashad ɗin yayiwa fyade,dan ita atunanninta Rashad yayiwa fattu fyaɗen. Sosai gimbiya suhaimat ta tausayawa yarinyar,sannan tayi Allah wadai da halin Rashad,zuciyarta na tsananin bugawa ,har cikin ranta take jin tausayin yarinya.kuma tayi alwashin ,saitaje taga yarinyar nan kafin ta bar ƙasar. Rashad kuwa kai tsaye aka wuce dashi,lafiyayyen asibitin dake masarautar,emergency akayi dashi,cikin gaggawa likitoci suka duƙufa akansa dan ceto rayuwarsa. Dan da dama cikin likitocin , sunyi tunanin hatsari ya samu mai muni. Karon farko ruwa suka fara ɗauka masa,kafin suka fara bincikarsa,karayama kusan biyar ce ajikinsa, bayan munanan raunuka dake jikin sa,sannan since kansa ya bugu ,dole sai sunyi bincike akwakwalwarsa, dan tabbatar da lafiyarta. Amma kuka take sosai cike da tarin damuwa da baƙin ciki ,meyasa Rashad zaiyi mata haka?me yasa gaba ɗaya halayyar Rashad ta sauya ne?da ɗan ta mai hankaline da nutsuwa ,sannan yana bin maganarta,amma daga baya ya fandare ya zama gagararre,yanzu ga irin abinda ya jama kansa.karaya har biyar ajikin mutum.Nan dai taci kukanta ta ƙoshi,tana zaune gefen ɗan ta. Nanny ma ta farfaɗo ,hankalinta amatukar tashe ,tana zaune hawaye na zuba cikin idanunta,yayin da tareeƙ ke rarrashinta cikin kwantar da murya. "Kayya tareeƙ abinnan na magajin faɗa,ya isheni yaron nan tun yana ƙuruciya yake haɗuwa da tuggun maƙiya,har zuwa girmansa,yaushe ne zai sami salama shima,kadufa wai Adeeb ne ya zama wannan ƙaton macijin,wanda idan awani gurin ka ganshi,sai inda ƙarfi ka ya ƙare wajen ceto rayuwarka. Yanzu idan haka ta faru dashi awani gurin yunkurin kasheshi fa zasu yi"nanny ta ƙarasa cikin kuka tana fyace majina. Hannunta tareeƙ ya kara damƙewa cikin nashi,kafin yace " wai ummeee yaushe zasu sanar da gaskiyar da muka jima da sanine?yaushe zamu taimakawa yallaɓai mu haska masa hanya danya gane irin haɗari dake bibiyarsa arayuwa?na gaji da boye gaskiya ummeee kiyi wani abu"tareeƙ ya faɗa cikin damuwa. "Tareeƙ baka san masarautar ya take ba,idan baka iya kama ɓarawoba ,to shi zai kama ka,dole mubi komai asannu,akwai lokacin bayyana gaskiya kaji?kayi hakuri"nanny ta faɗa tana mai shafa kan ɗan nata. Yanzu ya jikin ɗiyata yake ?shikenan yanzu yaron nan ya lalata nata rayuwa?ya karbi budurcinta awulaƙance sannan tana cikin al'ada ?kai ban taba ganin fajiri irin Rashad ba,Allah ya saka miki ɗiyata"nanny ta faɗa cikin kuka sosai,tana tausayawa fattu. Tareeƙ ma runtse ido yayi zuciyarsa na masa zafi,dan kuwa yasan ahalin yanzu Adeeb yana can cikin bakin ciki da damuwa,saidai shikam yana ganin kamar Rashad ɗin bai sami damar yiwa fattu fyaɗen ba suka karaso, yana kuma fatan Allah yasa hasashensa yazama gaskiya. Akan gado Adeeb ya shimfida fattu,wacce ke kwance kamar gawa,bata ko motsi,gaba ɗaya jini ya wanke mata fuska,jikinta ko ina raunine ,dan kuwa ba ƙaramin azaba Rashad ya gana mata ba,lips ɗin ta sun bushe idanunta ya kumbura sosai. Runtse ido Adeeb yayi lokacin da idanunsa suka sauka kan wuyanta zuwa ƙirjinta ,fasassun kwalabe duk sun soketa, zama yayi abakin gadon,cikin wata irin karaya da zafin zuciya.ji yake kamar yaje ya kama Rashad yayi gutsin-gutsin dashi, Hannunta ya kama na dama ,ya riƙe cikin nashi,gam-gam .jikinsa sai rawa yake ,yama kasa aikata komai akanta.wai hulwarsace kwance agabansa kamar gawa. "Why Rashad ?why ?duk matan dake cikin fadar nan sai matata?me yasa zaka aikata haka agareni?Adeeb ya faɗa afili yana mai kaiwa bango naushi, ji yake kamar zuciyarsa zata kama da wuta. Da sauri ya mike tare da ɗauko first aid box ɗinsa, dan Adeeb cikakken likitane akan fannin lafiya yayi karatunsa . Farar vest ɗin fattu data yage kaɗan daga sama ya kama,wacce ta rine da jini, ya cire mata ahankali,nan da nan albarkatun ƙirjinta suka bayyana,cikin faduwar gaba Adeeb ya kawar da kansa ga barin kallonsu,zuciyarsa na ci gaba da bugawa. haka ma ya zare wannan dogon wando dake jikinta ya ajiye gefe,ya rage daga ita sai pant Wanda shima gaba ɗaya yayi stairs saboda yadda jini ya ɓalle mata ,tsabar yadda ta shiga ruɗu da razani. Hannun Adeeb karkarwa yake ya kasa aikata komai,dan haka cikin sauri ya janyo ƙaton bargonsa ya lulluɓe fattu dashi,iya saman ƙirjinta zuwa kanta ya bari abuɗe. Sosai ya tausayawa fattu lokacin da yake cire mata kwalaben nan,dan kuwa taji ciwo da yawa,ko yaya ya taba gurin da kwalbar take saita zabura kamar zata farfaɗo. Haka dai ya gama cire mata kwalaben nan,tas yayi mata dressing ɗin duk inda ya kamata, ya sami ruwan zafi da towel ya goge mata jikinta .sai dai kuma ba wani kayan da pant da kuma pad ɗin dazai canja mata. Dan haka rigarsa ya ɗauko fara ƙal ,doguwar ya zura mata, kafin ya dauko mata kayanta,dan kuwa yana tunanin ta dawo nan part ɗinsa da zama kenan. Ƙarin Ruwa ya sanya mata ,kafin ya nufi ƙofa, kai tsaye ya kulle ƙofar ya fita zuciyarsa kamar wuta haka yake jinsa,ya nufi part ɗin nanny. "Tareeƙ na roƙeka kada kace zaka sanar da magajin faɗa komai ahalin yanzu,dan kuwa bamu da kwararan hujjoji akan hakan ,ka bari nan da lokaci kankanin shida kansa zai gano komai,zamu nuna masa hanya ta yadda zai fahimci abubuwa da dama" nanny ta faɗa tana rike da hannun tareeeƙ. Umme wllh zuciyata zafi take,Aduk lokacin dana ga yallaɓai cikin wani halin,yana zagaye da maƙiya ,amma bai sani ba,shi yana zaune dasu zuciya ɗaya .... "Su waye maƙiyan nawa?sannan wace gaskiyar ce ake boyemin?" Suka tsinkayo Muryar Adeeb yana faɗin haka cikin sautin da ba wasa acikinsa. Da sauri suka juyo gaba ɗayansu, dan basu tsammanci ganin Adeeb ɗin awannan lokacin ba. "Magajin faɗa yaushe ka shigo?ya jikin naka?ina ɗiyata take ?"nanny ta faɗa cikin inda-inda da son n kawar da zancen. Ƙura mata ido Adeeb yayi cike da tuhuma ,gaba ɗaya ta daburce.da alama akwai abunda take boyewa ita da tareeƙ .kallonsa ya dawo dashi kan tareeƙ wanda kansa ke ƙasa ,shi yaji dadin jinsu da Adeeb yayi,fatansa ɗaya ayi komai yau akare. "Tareeƙ, what wrong me kuke ɓoyemin? Dama akwai Abinda zaka iya boyemin tareeƙ ?na dauke tamkar kanina da muka fito ciki daya,why tareeƙ?" Adeeb ya faɗa yana kallon tareeƙ. Kallon nanny tareeƙ yayi,yana jin ba dadi cikin ransa,dama yasan watarana hakan zata iya faruwa,shi baiga amfanin biye boyen ba , amma suna haɗa ido da nanny tayi saurin girgiza masa kai,alamun karya ce komai. "Tareeeƙ,am tolking to you me kuke hidden mini?kada kusa na fara zarginku fa,Please nanny,bayan ammina da abie, ku kadaine mutanen dana yarda dasu arayuwata,ku kaɗai ne waɗanda nake ganin bazasu taba cutar dani ba,karki karyamin zuciya nanny, Please me kuke ɓoyemin?" Adeeb ya faɗa cikin wata kalar murya mai cike da tsoron kar ace nanny da tareeƙ suma suna daga cikin maƙiyansa . "Ka kwantar da hankalinka magajin faɗa,wllh har abada bazamu taba cutar da rayuwarka ba,saidai mu bata kariya, amma kasani akwai mutanen da kake kallo matsayin maƙiyanka,saidai sam,ba haka abin yake ba. azahiri kake ganinsu matsayin maƙiya,amma abaɗini sune masoyanka na haƙika. Su kuma wadanda kake kallo matsayin masoya,suke son ganin bayanka, sune waɗanda suke cin dunduniyarka,Adeeb ka kula kazamo mai lura da mutanen da kake tare dasu " nanny ta faɗa tana mai riƙe da hannun Adeeb,fuskarta ɗauke da damuwa. Kallonta kawai Adeeb keyi,tunda ta fara maganarta ,me take nufi kenan?su waye ya yarda dasu ,kuma suke cin dunduniyarsa? Sannan suwaye yake wa kallon maƙiya ,alhalin sune masoyansa na asali?kallon nanny yayi cike da tarin tambayoyi zuciyarsa na harbawa da gudu. "Nanny ban fahimceki ba,me kike nufi da kalamanki? Please kiyimin bayanin da zan gane"Adeeb ya faɗa yana kallon nanny,idanunsa sun kada sunyi jajur dasu. Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe mai ƙarfin gaske,sannan tace magajin faɗa ,idan baka manta ba,shekaru kusan sha takwas mijina da kuma gimbiya nazli sunyi haɗari suka mutu,sanadiyyar wuta data kama motar da suke ciki,harda yaranta mata su biyu,nanny ta faɗa tana kallon Adeeb, Runtse ido Adeeb yayi da mugun ƙarfi,har abada bazai taba mantawa da wannan baƙar rana ba ,ranar data zamo mafi muni arayuwarsa. Bude idonsa yayi wanda suka cika da kwalla yana kallon nanny kafin cikin rawar murya yace " tabbas nanny bazan taɓa mantawa da wannan rana ba,domin itace rana mafi muni arayuwata" ya faɗa yana mai lumshe idanunsa hawaye suka ziraro sharrrt. "To kasani wannan haɗarin ba afkuwa yayi ba ,shiryashi akayi" nanny ta faɗa tana mai kallon Adeeb , Azabure Adeeb ya bude idanunsa,da suka gama zama jajur dasu,kallon nanny yake cikin kiɗima da ruɗewa" nanny kamar ya ban gane ba,me kike nufi da shiryashi akayi?waye ya shirya?kuma meye dalilin shiryawa?"Adeeb ya faɗa aruɗe. Kamo hannunsa nanny tayi ta zaunar dashi akan kujera dan kuwa gaba ɗaya jikin sa rawa yake. "Tareeƙ maza jeka kulle mana ƙofar nan"nanny ta faɗa cikin damuwa. Ahankali tareeƙ ya nufi ƙofar tare da kullewa, yana jin sanyi aransa,koba komai yau zasu sauke nauyin da yayi musu bake bake acikin zuciya. " Nanny kiyi saurin sanar dani, domin zuciyata gab,take da tarwatsewa,dan kaɗuwa" Adeeb ya faɗa cikin tsantsar zaƙuwa . Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace " ina son ka saurari maganata da kunnen basira ,sannan kayi min kyakykyawan fahimta,kasani bazan taɓa cutar da kaiba, kuma duk abinda nayi nayine don tsiratar da rayuwarka" nanny ta faɗa hannunta riƙe dana Adeeb. "Please nanny go street to the point kina kara sani cikin wasi-wasi" Adeeb ya faɗa cikin muryar damuwa ,jikinsa na rawa ,ba abinda yake son ji sai wanda ya shirya wanann haɗarin. Mikewa nanny tayi tare da zuwa jikin window ta tsaya ,kallon Adeeb take tare da karantar yanayinsa, kamar yadda shima yake kallonta cike da ƙosawa. Ahankali ta buɗe baki tace"ba kowa bane ya shirya wannan hadarin face .......... Wayyo masu karatu cajina ya kare ,amma karku damu mu tara anjima, Nice dai anty mammynku. Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:56] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book page 61/62 ________________Ficewa sukayi daga part ɗin ammi zuwa na Adeeb, haka kawai gaban sarauniya Nazli ke faduwa,sam ta kasa gane kan wannan faɗuwar gaban nata,saidai kawai ta alaƙa ta hakan da tunanin halin da zata ga yarinyar data sanya tausayi ta cikin zuciyarta. Su zayyad ma biyo ta sukayi,dan sunce suma son gannin marar lafiyar ,kuma zasuyi wasa agurin uncle Adeeb ɗin. Suna zuwa Adeeb ya dannan lambobin securityn daya sanya lokacin da zai fice,nan take ƙofar ta bude suka shiga. "Tana cikin daki" Adeeb ya faɗa yana kallon sarauniya suhaimat wacce ke tsaye cikin faduwar gaba. Kallonsa tayi cikin tausayawa, tare da jinjina kai . sam zuciyarsa Adeeb da jikinsa basa masa daɗi, yana cikin matsananciyar damuwa ,abubuwa sunyi masa yawan da har yana rasa me Yakamata yayi. " Ku zauna anan maza kafin na fito kunji" ta faɗa tana shafa kan yaran nata,kafin tabi bayan Adeeb zuwa cikin dakin. Tana kwance kamar yadda ya barta,ruwan daya ɗaura mata ya kusan karewa. Jiki asanyaye sarauniya suhaimat ta karasa bakin gadon da fattu ke kwance .sosai bugun zuciyar sarauniya suhaimat ya tsananta. Zama tayi tare da ƙurawa fattu idanu,lokaci guda taji wata masifaffiyar kaunar yarinyar tana ratsa dukkan sannan jikinta,ji take kamar bata taɓa son abu makamancin yadda take jin son yarinyar na shiga lungu da sako na jikinta ba. Hannun fattu ta kamo tare da riƙewa gam-gam cikin nata,wani sanyi taji yana ratsata lokacin data kama hannun fattun,batare da saninta ba kawai ta rungume hannun fattu aƙirjinta ,tare da runtse idonta.wani irin shauƙi takeji yana shiga jikinta irin na ƙaunar dake tsakanin ɗa da uwa.haƙika takamu da matsananciyar kaunar yarinyar lokaci guda. Kallon fuskar fattu take bata ko ƙifta idanunta,Adeeb na tsaye agefe guda yana kallonta ,mamakin yadda yaga fuskarta ta nuna so da kaunar fattu yake,koda yake haka Allah ke al'amarinsa.ganin ta kasa cewa komai kawai tana rungume da hannun fattu ta kura mata ido yasa shi sauke ajiyar zuciya yana mai faɗin"anty lafiya kuwa naga kinyi shiru "ya faɗa yana mai kallon fuskar sarauniya suhaimat. Sai lokacin tadanyi firgigit ta ɗago kai tana kallon Adeeb,ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi kafin tace "wllh Prince haka kawai naji ina kaunar yarinyar har cikin raina ,sosai nake jin tausayinta, yanzu ka dan bamu guri inason na dubawa"ta fada ta na mai shafa kan fattu. Kallon fattu Adeeb yayi cike da tausayawa,zuciyarsa na masa wani irin ɗaci ,kafin ya sauke ajiyar zuciya kana yayi falo gurin su zayyad da yazeed. Sosai sarauniya suhaimat taji mugun daɗi lokacin data gane fattu period ma take,kuma babu alamun Rashad yayi mata wani abu,hamdala tayi ga Allah tana jin zuciyarta wasai, murmushi kwance kan fuskarta take kallon fattu,wacce ta fara dan motsi tana yamutsa fuska. Hannunta sarauniya suhaimat ta kara riƙewa da kyau tana mai faɗin"princess buɗe idonki ki ,kalleni kinji" tana faɗin haka tana ɗan buga kumatun fattu. Ahankali fattu ke buɗe idanunta da suka yi wani irin jaaaa kamar jini ya taru a cikinsu,har ta bude idon fess,tare da kafe silin da ido,bata ko ƙiftawa.da alama tana son tuno wani abune, shiru sarauniya suhaimat tayi tana bin idanun fattu da kallo. Kusan minti ɗaya fattu tana kallon silin ,kafin ta zabura tare da kwalla kara tana kokarin tashi,da sauri sarauniya suhaimat ta cire mata karin ruwan dan dama ya kare . "Wayyo Allah na ,wayyo hammana kazo ka ceceni,zai lalamin rayuwa,wayyo baffana,wayyo innata kizo ,dan Allah ka bari wllh niba yar iska bace karkamin bana so banaso wayyoooooo!!!" Abinda fattu ke faɗa kenan tana fizge -fizge ,dan gani take kamar lokacin Rashad ke ƙoƙarin yi mata fyade,janyota sarauniya suhaimat tayi da sauri ta rungumeta tsam-tsam ajikinta ,cikin mugun tausayinta,tana faɗin"ki nutsu princess ba kowa buɗe idonki ki gani,nice ba Rashad bane ya tafi kiyi shiru ya isa"abinda take faɗi kenan tana shafa kan fattu ,wacce ilahirin jikinta ke rawa ,ta rufe idanunta ƙam -ƙam taƙi budewa. Da hanzari Adeeb ya ƙaraso cikin dakinz su zayyad ma bishi sukayi da gudu ,jin ihu da fattu ta kwalla,har neman faduwa Adeeb yake tsabar sauri,yana zuwa ya zauna abakin gadon tare da kamo hannun fattu ,da sauri ta fizge hannunta tana mai sakin ƙara ,"ahhhhhh,wayyo ni kasakeni banaso ,wayyo hammana kana ina? wayyo Hamma kazo ka taimakeni" fattu ta faɗa tana kokarin zamewa daga jikin sarauniya suhaimat. Cike da damuwa Adeeb ya ƙara kamo hannunta ya rike cikin nashi ,duk yadda take ta ƙoƙarin kwace hannun nata,amma yaƙi saki, "Hulwa ki nutsu kinji ,nine hammanki,buɗe ido ki kalleni ,ba Rashad bane nine Hamma" Adeeb ya faɗa cikin sanyin murya yana mai shafa kan fattu. Jin muryarsa da fattu tayi yasata saurin buɗe kunburarrrun idantuna ,ta sauke akan fuskar Adeeb,ɗan kafeshi tayi da ido,gabanta na faɗuwa kamar zai fado kasa. "Nine ,hammanki ne Hulwa kalleni ki gani ,nine Hamma Adeeb " ya faɗa yana ɗan matso da fuskarsa saitin Tata. Ahankali tace "hammana" "Na'am Hulwa is me "Adeeb ya faɗa yana mika mata hannu. Da sauri ta fada ƙirjinsa tare da fashewa da wani irin kuka,mai matukar ban tausayi,kukane irin na wanda ke cikin tashin hankali kuma ya sami mai taimakonsa. "Hamma ina kaje ka barni?wannan mai kama da kai ɗinne yazo zaiyi min fyade,Hamma dan baki yarda shine yayi ta dukana,ya fasamin baki,ya bugamin kaina ajikin katanga,Hamma bana sonshi,bana son ganinsa ,dan Allah Hamma ka fitar dani daga gidan nan bana so"fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka muryarta har wani yankewa take kamar numfashinta zai dauke. Ƙamm ƙamm,Adeeb ya rungumeta ajikinsa,yana jin wani irin zafi akirjinsa, mugun tausayinta ne yake zaga dukkan wata kofa dake jikinsa,haushin kansa ma yake ji,wai me yasa ma ya tafi gurin taron ya barta anan?me yasa bai tafi tare da itaba? Ahankali yake shafa kanta,yana mai faɗin"am sorry Hulwa,kiyi haƙuri laifinane,dana tafi na barki,na miki alkawarin ba wanda zai sake ƙoda miki kallon banza ne bare hakan ta kara kasancewa,ki yafemin hulwata ,an sorry "ya faɗa yana kara ruƙunkumeta ajikinsa,wasu hawaye Masu zafi suna zirarowa daga idanunsa. Zuru su zayyad sukayi suna kallon fattu,dan yazeed ma tuni ya fara kuka ,dan shi yana da mugun tausayi. Sarauniya suhaimat na zaune ta kura musu ido,cikin tausayi take zubda kwalla itama,ji take kamar yarta akayiwa wannan zalumcin ,Allah Sarki Adeeb ya cika dan halak dan ga dukkan alamu yana kula da yarinyar nan,duk da kasancewarta ma aikaciya agidansu,kuma tabbas taga zallar kaunar yarinyar cikin idanun Adeeb. Sun jima cikin wannan yanayin,har saida Adeeb ya tabbatar Hulwa ta sami nutsuwa ta hanyar daidaiton da yaji bugun zuciyarta yayi,sannan ya rabata da jikinsa. "Sannu princess hulwar Adeeb"sarauniya suhaimat ta fada ,fuskarta ɗauke da murmushi. Sai lokacin fattu ta juya tana kallonta .rassa!rassa!!rassa!!! gaban fattu ya yanke ya fadi,ƙurrr ,ta kure sarauniya suhaimat da ido,lokaci guda taji ƙaunar matar na ratsata fiye da yadda tayi tunani,duk kunya irin ta fattu,da bata yarda kuyi ta haɗa ido da ita,amma yau kam ta kafe sarauniya suhaimat da ido bata ko ƙiftawa. Murmushi sarauniya suhaimat take sakarwa fattu,kafin tace" baki sanni ba ko? Ta fada cikin yanayi na murmushi. Kamar wata doluwa haka fattu ta daga kai idonta akan fuskar sarauniya suhaimat. "Daga yau nice innarki ,danaji kina faɗi kinji "ta faɗa tana mai shafa kan fattu. Ahankali fattu ta matsa kusa da ita tare da ɗora kanta akan cinyar sarauniya suhaimat tana mai faɗin "innata"ahankali tare da lumshe idonta. Kallonsu kawai Adeeb keyi,zuciyarsa na darsa masa abubuwa da dama,wannan wane irin shakuwace ta lokaci ɗaya?gaba ɗayansu sun kamu da kaunar juna daga haduwar farko,anya ba wani al'amarine mai ƙarfi atsakinsu ba ?. Hammmmm mudaije zuwa. "Sannu anty "zayyad ya faɗa cikin tausayawa. Ahankali fattu ta ɗago kai tana kallon yaran masu tsananin kama, Lokaci guda yaran suka shiga ranta. Masha Allah kyawawa dasu. Jinjina kai tayi tana kallonsu cike da kauna. "Maza kuje falo ko anty zatayi wanka" cewar suhaimat. Kama hannunsu Adeeb yayi suka fice zuwa falon. Saida Sarauniya suhaimat ta taimakawa fattu tayi wanka ta gyara mata jikinta sosai,ta bata abinci taci ta sha magunguna sannan ta kwanta barci .kafin ta bar ɗakin akan zata kara dawowa ta duba ta.har ta kai bakin ƙofa fattu ta ce"innata" da sauri sarauniya suhaimat ta juyo ,dan har cikin ranta taji sunan ya shigeta. "Zaki dawo "fattu ta faɗa tana kallonta . Jinjina kai tayi tana mai yiwa fattu murmushi tace "tabbas zan dawo ƴata"murmushi fattu tayi cikin karfin hali tare da rufe idanunta.ba ɓata lokaci barci yayi gaba da ita.dan kuwa harda maganin barci acikin wanda ta sha. Koda sarauniya suhaimat ta koma bangaren ammi,zaune ta tarar da ammin ta buga uban tagumi,duk sallamar da take sam ammin bata jiba,dan tayi nisa cikin duniyar tunani,saida ta tabata kafin ta san da zuwanta gurin. "Suhaimat ina kikaje ?na duba baki afalon? Ammi ta faɗa da kokarin kawar da samuwar dake kan fuskarta. Zama suhaimat tayi susa da ammi tace ,wllh yarinyar nan da abin nan ya faru da ita naje na gani,dan kuwa sosai lamarinta ya tsayamin araina ji nake kamar inada wata alaƙa da yarinyar" suhaimat ta fada tana mai lumshe idonta. Azabure ammi ta kalli sarauniya suhaimat tana mai dafe ƙirji"na shiga ukuna ,suhaimat gurin yarinyar kikaje?me kika gani?da wa kikaga tana miki kama?ammi ta faɗa cikin rudewa da tashin hankali,dan bata taba tsammanin suhaimat zataje gurin fattu ba. Kallon mamaki suhaimat ɗin ke bin ammi dashi ,kafin tace "uktee ,yanaga kin rude haka?daga jin cewar naje gurinta?kuma dawa kike tsammanin zanga tana kamar?ta fada cikin mamaki tana kallon ammi,da sai lokacin ta fahimci tayi baran -barama kuma tana son bada kanta. Cikin sauri ta saita kanta,kafin tace "ai nayi mamakin yadda kika damu da baiwane,har kikaje dan ganinta"ammi ta faɗa cikin basarwa. Murmushin suhaimat tayi kafin tace "wllh yadda nake jin yarinyar nan cikin raina ,ko su zayyad bana jinsu haka"ta faɗa cike da shauki akan fuskarta. Wani shegen kallon ammi ta jefa mata ,tana mai faɗin ,aikuwa saidai kiyi ta jin wannan shaukin cikin ranki,amma keda ƴarki har abada,bazan ƙara bari ki ganta ba,dan kuwa kashe shegiya zanyi kowa ya huta.ammi ta fada cikin ranta. Amma afili saitayi murmushi tana faɗin,"ke dai suhaimat kina nan da son jama'a har yanzu,sukuwa mutane ba abin yarda bane ,Gara ki kula" Jinjina kai suhaimat tayi kafin tace "ai idan har kana abu tsakaninka da Allah ,to tabbas Allah zai zama gatanka, kuma bazai taba ba maƙiya Sa'a akanka ba,kuma kinsan shi sharri dan aikene,idan ka cutar da wani to kana zaune zakaga sakayyar Allah"cewar sarauniya suhaimat kenan cikin murmushi take bayaninta. Kallonta ammi keyi,cike da sanyin jiki,sai take ganin kamar magana suhaimat ke faɗa mata afakaice,amma ai tasan suhaimat bata san komai game da halayyar ta ba ,bare tayi mata shagube.dan haka ta Badar da maganar sukaci gaba da hira. "Ranka ya dade ,hakika al'amarin Adeeb babban abune,wanda Allah shine kadai zai iya kareshi,domin kuwa sihirin da akaiwa yaron nan,badan ƙarfin addu'ar dake tare dashiba, to tabbas mutuwa zaiyi,domin kuwa sihirin anyi shine badan ya rayu ba,saidai akasheshi. Dan haka ba abinda zamuyi face addu'a domin Allah ya kareshi da duk wani mai nemansa da sharri" Shaikh lateef ya faɗa ,yana mai kallon mai martaba , Shiru abie yayi cike da tsantsar mamakin waye yayiwa ɗansa wannan aika aikar,kallon ƙaninsa waziri yayi cikin damuwa yace "ɗan uwana kanaji? Kana jin abinda Shaikh ke faɗi, me Adeeb ya tsarewa jama'a ?yaro mai hakuri,hankali da hangen nesa,ba ruwansa da kowa bai tsarewa kowa komai ba,amma ana neman ganin bayansa,Allah ka karemin ɗana ,ka raba shi da sharrin makiya,yanzu Shaikh menene abinyi. ?"abie ya faɗa cikin damuwa yana jin kamar ya zubda hawaye. Jinjina kai Shaikh lateef yayi yana Jan carbinsa dake maƙale adan yatsansa. "Ranka ya dade ba abinda zamuyi masa daya wuce addu'oi,sannan zan hada masa maganin karya sihiri wanda zai sha yayi wanka dashi,amma fa kasancewar samutum akoda yaushe abune mai matukar wahala,dan kuwa Aduk lokacin da ya shiga yanayi na ɓacin rai mai tsanani to tabbas akwai yuwuwar komawarsa macijin " Shaikh ya faɗa yana mai kallon abie. Wazirine ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Shaikh cikin damuwa kafin yace "yanzu ba wata hanya da Ya kamata abi,Dan arabashi da wannan iftila'in?ta yaya za'ace mutum yana komawa wata halittar? Shaikh aduba dai "waziri ya faɗa yana kallon Shaikh. Murmushi Shaikh yayi yana mai girgiza kai,kafin yace ,tabbas da 'ace akwai hanyar da zanbi dan ganin na raba yaron nan da wannan al'amarin ,to danabi ,kamar yadda na faɗa muku, anyi amfani da mugayen aljanu waɗanda suka samo macizan da ba irinsu afadin duniyar nan,kafin aka hada lakanin da akayi masa sihirin dashi, dan haka addu'a itace kadai mafitarmu" Ajiyar zuciya abie ya sauke ,zuciyarsa kamar zata fashe tsabar damuwa da ɓacin rai,sosai yake jin tausayin Adeeb,waye wanda ke son ganin bayan Adeeb? Me ya tsarewa mutane haka? Dole ya tsaya sosai ya kula da rayuwar dansa ,ta hanyar bashi kariya ta kowace sigar. "Shikenan Shaikh Allah ya shige mana gaba ,ya bamu Sa'a akan abinda muke nema"cewar abie yana mai lumshe idonsa lokaci guda damuwarsa ta baya ta dawo masa ,yana tuna abinda ya faru shekarun baya,sam baya son abu makamancin abinda ya faru a baya ya sake faruwa. "Yanzu ranka shi dade,ina son aturomin yarima zuwa anjima dan akwai abubuwan da zamu tattauna dashi"Shaikh lateef ya faɗa yana mai mikewa dan barin dakin. Bayan fitarsa waziri ya kalli abie wanda yayi shiru fuskarsa gaba ɗaya ta sauya ,ta koma kalar damuwa sosai, "Ranka ya dade ka kwantar da hankalinka,In Sha Allahu komai yazo ƙarshe,ba abinda zai sake samun yarima"waziri ya faɗa cikin kwantar da murya aƙokarinsa na kwantarwa da abie hankali. "Allah yasa waziri,amma abin yana damuna ,kasan yadda nake son Adeeb ,bana son abinda zai tabashi komai ƙanƙantarsa,domin shine magajina" "Ba komai ranka ya dade mubar komai hannun allah."cewar waziri. Jinjina kai abie yayi kafin yace ,sai kuma wannan matsalar ta Rashad,Dole in ɗauki mataki mai ƙarfi akansa,jira nake kawai ya sami lafiya" "Haka ne yaya dole ahukunta Rashad ,Dan yana don bata mana suna" cewar waziri cikin damuwa.nan dai sukaci gaba da tattaunawa akan matsalar. Rashad yana nan har yanzu kwance kamar gawa ,ko motsi bayayi, gaba ɗaya kamanninsa sun sauya ,abin tausayi,kullum amma cikin kuka take tana tausayawa halin da ɗan nata ke ciki, Gimbiya Zulaihat ma tun daga wannan ranar bata kuma ganin Adeeb ba,dan tsoronsa take ji sosai,amma har lokacin tana nan akan bakanta na son aurensa. Adeeb kuwa yana dakin da fattu ke kwance tana barci,kallonta yake cike da tausayi,gefe guda kuma wayar da ammi tayi gaba ɗaya ta tsaye masa arai,ga maganar da nanny ta fada masa,shi gaba ɗaya ma ya shiga ruɗu baisan me Yakamata yayi ba,yanzu gurin wa zai je neman shawara?waye zai sanarwa da damuwarsa?yanzu tsoron mutanen fadar nan yake ,dan kuwa cike take da mutane marasa amana da gaskiya. Ahankali ya shafa gefen fuskar fattu tare da sumbatar goshin ta kafin ya mike tare da ficewa daga ɗakin. Kai tsaye amma ta fito daga part ɗin Rashad bayan ta gama kukanta ta koshi,tunani tayi kan cewar ya kamata akawo karshen wannan al'amarin dake dukunkune cikin fadar nan,dan haka tana da bukatar magana da nanny Dole taje tayi magana da ita yanzu . Dan haka can ta nufa ,cikin sa'a ta tarar da nanny zaune afalo, kallo ɗaya zakayi mata kasan tana cikin damuwa da alhini.tana ganin amma ta mike tana mata maraba cikin girmamawa. Zama amma tayi tare da kallon nanny tace"zauna nanny inason muyi magana dake . "ta fada tana mai kallon nanny ,wacce itama kallonta take.zama nanny tayi jikinta asanyaye kafin tace "wace magana kike son yi dani ranki ya dade?inaga da kin aiko ankirani nazo gurinki dan gudun zargi ,idan aka ganki anan"nanny ta fada cikin damuwa. "Ajiyar zuciya amma tayi kafin tace ,ya kamata mu daina boye-boye nanny akan abinda muka san menene gaskiyarsa,ki duba halin da ɗana yake ciki ?kuma duk akan wannan makirar matar ,nasan cewa kome ya faru shirinta ne,meyasa zamu zauna mu zuba mata ido tana aikata abinda taga dama?dan haka dole mu kawo ƙarshen zalunci ta"amma ta faɗa cikin ɓacin rai da damuwa. Ajiyar zuciya nanny ta sauke mai ƙarfi kafin tace "ranki ya dade wannan abun fa abune mai matukar hadari ,dakuma tarin ƙalubale,domin nayiwa magajin fada maganar hadarin sarauniya Nazli, na sanar dashi wanda ke da hannu akan hadarin, amma sam bai yarda dani ba yayi fushi mai tsanani.tunda ya fita bai sake dawowa ba.dan haka ina ganin mudan jinkirta zuwa wani lokaci,har wannan abinda ya faru yayi sanyi" Jinjina kai amma tayi cike da gamsu,tace "wannan gaskiya ne ,dan kuwa nasan mai martaba ma jira yake Rashad ya farfaɗo ,kafin ya yanke hukunci akan abinda ya aikata .Allah shine kawai zai fitar damu " ta fada kwalla na cika idonta. "Kiyi haƙuri ranki ya dade ,komai yayi farko, yana da karshe ina sha Allah muke da nasara"cewar nanny cike da damuwa akan fuskarta. "Shikenan nanny Bari na koma can gurin Rashad din"Amma ta faɗa tana mikewa. Biyota nanny tayi tana mata sallama ,har farfajiyar gidan suka fito nanny na kara kwantarwa da amma hankali. Daidai lokacin kuma Adeeb ya fito daga part ɗinsa ,idonsa ne ya sauka akan nanny tsaye tare da amma. Kallonsu yayi cike da tsantsar mamaki,da kara tabbatar da zarginsa akansu. Suma kallonsa suke cikin yanayi na damuwa da rashin jin dadin ganinsu da yayi . Tafiya amma tayi daga gurin ,ganin irin kallon da Adeeb ke mata. Nanny kuwa jikinta ne yayi sanyi sosai.da hanzari ta nufi gurin da Adeeb ke tsaye........ Hmmmmm masu karatu muhaɗe next page . Takuce anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:57] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 65/66 ________________"Ki sanar dani dalilin da yasa baki son zuwana gurin yarinyar nan? Me alaƙarki da ita ?ko ince me ta tsaremiki uktee? Sarauniya suhaimat ta fada cikin haɗe fuska ,dan tasan kadan daga aikin ammi ta hanata zuwa gurin fattu. Zaro ido ammi tayi tana mai kallon suhaimat ,dan sai lokacin ta fahimci tana kokarin bada kanta,cikin in-ina ta fara magana "su...hai..mat,wane dalilin ne zaisa kuwa in hanaki zuwa gurinta?kawai ina gudun ace ko wata munaƙisar muka ƙulla yasa kike ta zarya,kinsan tunda wannan abun ya faru to komai ma laifi zai zama , amma bayan wannan bani da wani dalili"ammi ta fada tana kafe suhaimat da idanu. Murmushi suhaimat tayi ,kafin tace "Indai dan wannan ne karki damu ,ai kowa yasan Ni likitar matace,kuma ba laifi bane idan naje duba marar lafiya,kuma ma mace"suhaimat ta fada cikin yanayi na rashin damuwa.kafin ta juya ta bar ɗakin. Harara ammi ta biya da ita ,kamar idanunta zasu fado ,haushin suhaimat takeji fiye da tunanin mai tunani,wllh badan tana tsoron faruwar wani abu ba ,data gama da suhaimat ,dan itace silar shigar ta ko wace irin damuwa.amma ba komai muje zuwa sannu sannu bata hana zuwa,saidai dade ba'ajeba. koda sarauniya suhaimat ta koma bangaren Adeeb, kwance ta tarar da fattu adaki, idanunta alumshe kamar mai barci,yayinda Adeeb ke falo yana amsa waya. Bayan sun gaisa yake sanar da ita fattun tana cikin daki, dan sosai yake jin dadin yadda take kula masa da fattu. Tana shiga fattu ta buɗe idonta,da sauri sakamakon jin muryarta,dan dama tana kwancen nan, tunaninta Sarauniya suhaimat kawai take. Da murna ta tashi zaune tana murmushi,tare da kallon suhaimat, Itama cikin farin ciki ta karasa gareta ta zauna. Ahankali fattu tace "inna nayi tunanin bazaki dawoba,ina ta tunaninki araina"ta fada fuskarta ɗauke da annuri. Shafa fuskar fattu tayi kafin tace "ƴata kenan ,tunda nace zan dawo ,ai dole na na dawo naga kaykykyawar fuskar nan taki,ya jikin naki"suhaimat ta fada cikin murmushi. "Da sauki "cewar fattu. "Masha Allah,haka ake so ki kula da shan magungunanki kinji"cewar sarauniya suhaimat. Jinjina kai fattu tayi kafin tace "ina yan biyu " Murmushi suhaimat tayi kafin tace "suna can suna shiryawa ,Basu san nazo nan ba da kin gansu sun biyoni, dan sun damu dake sosai" ta fada cikin murmushi. Fattuna murmushin tayi, tana wasa da ƴan yatsunta. Sun jima suna hira da fattu,duk da tana ɗan jin kunyar sarauniya suhaimat din,amma zakayi mamakin yadda ya sake suke ta hira ,harda dariya . Anan ne take sanar da ita cewar yau zasu tafi garinsu. Lokaci guda fattu ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka, "Ayya inna meyasa zaki tafi?dan Allah ki zauna anan,bana son ki tafi "fattu ta faɗa tana mai kallon sarauniya suhaimat. Ahankali suhaimat ta kamo hannun fattu ta rike cikin nata tana ɗan murmushi,duk da itama sam batason rabuwa da Fattun,amma dan ta kwantar mata da hankali sai tayi murmushi tace"karki damu my princess ai zan rinka zuwa ina ganinki,kuma wataran zance yarima ya kawomin ke muyi hutu,ko bazaki zoba"?ta fada tana kallon fattu. "Zanzo mana inna dama bana son zama agidan nan tsoron wannan mai kama da hamman nawa nake"ta fada cikin yanayi na damuwa, idanunta har ya kawo kwalla. Cikin damuwa itama suhaimat ta tallafi kumatun fattu,tana mai cewa"ki kwantar da hankalinki ƴata, ba abinda zai miki kinji,ki daina tsoronsa,yanzu haka yana can akwance cikin halin mutuwa da rayuwa,kuma hammanki yana tare da ke"ta fada cikin salon kwantar da hankali. Jinjina kai fattu tayi tana mai kallon suhaimat ɗin. Murmushi suhaimat tayi tana mai kallon wayarta dake ringing ,lokaci ta duba taga harta kara minti biyar akan time ɗin da zasu tafi,dan ma private jet ne.kuma mijinta bai sami halartar gurin ba saboda wani meeting da suke mai muhimmanci. "To ƴata zan tafi saina ƙara dawowa zan dawo mutafi tare dake ,kinji"suhaimat ta fada tana jin ba dadi cikin ranta,ji take kamar zata rabu da abu mafi muhimmanci arayuwarta. Ahankali fattu ta daga mata kai, idanunta na zubda kwalla,sam bata son suhaimat ta tafi,"Allah ya tsareku,ya kaiku lafiya inna ,saikin dawo"fattu ta faɗa tana ɗan kwantar da kanta jikin suhaimat. Rungumeta suhaimat tayi cikin alhinin rabuwa da ita .Adeeb ne ya shigo dakin da sallamarsa,da alama wanka yayi dan ya cire kayan dazu ya sanya riga da wando blue and white yayi matuƙar kyau sosai,sai ƙamshinsa yake kamar kullum. Kallonsu yayi yadda ko wanne ke zubda kwalla ,lallai lamarin Allah abin kallone,dubi yadda lokaci ɗaya shakuwa ta shiga tsakanin bayin Allahn nan?kamar sunsan juna.murmushi yayi yana kallon suhaimat kafin yace "anty suhaimat har yanzu kina nan da tausayi da kuma saurin kuka " ya faɗa yana kallonta.shikam tun sanin da yayi mata haka bakinta yake ,akwai tausayi da son mutane bata da kyamar dan adam. Share hawayen idanunta tayi kafin tace "prince wllh da zaka bani yarinyar nan dana tafi da ita can Ghana munyi zaman mu ,dan Allah ya doramin kaunarta cikin raina sosai" ta fada tana shafa kan fattu. "In baki ita ku tafi?Ni kuma inyi yaya,haka kawai ,ki tafimin da mata?inaaa"Adeeb ya faɗa cikin zuciyarsa.amma zahiri saiyace "karki damu watarana zata zo " "Allah yasa da gaske kake,yanzu dai kayi mana hoto dan tarihi"sarauniya suhaimat ta fada tana mai janyo fattu jikinta. Luuuf!! fattu tayi ajikin suhaimat tana mai jin wani irin sanyi acikin zuciyarta.hotuna Adeeb yayi musu kusan kala biyar awayarsa, hakama yayi musu awayar Sarauniya suhaimat ɗin. Da gyar suka rabu da juna cikin kewa da kaunar juna, fattu sai kuka take ta rungume Adeeb lokacin da suhaimat ta tafi rarrashinta yayi tayi da gyar ya samu tayi barci. Ammi kuwa sosai taji dadin tafiyar suhaimat,dan hankalinta sam bai kwanta ba ,gani take kamar zata iya gano wani abu game da fattu Yanzu damuwarta daya shine yadda ,zata bullowa lamarin Adeeb. Rashad ya farfaɗo ,saidai gaba ɗaya ankasa gane kansa ,dan kullum haka zaka ganshi shiru baya magana saidai kallo,abin yana matukar damun amma,haka zatayi ta kuka tana kallonsa,saidai kawai kaga hawaye yana bin fuskar Rashad din,ya rame sosai,dan baya wani cin abinci,ga karaya ajikinsa ta ko ina likitoci suna ta binciken kwakwalwarsa dan suna tunanin tanan ya sami matsala.saidai muce Allah ya bashi lafiya. Sam yanzu Adeeb baya kula tareeƙ ,haka zai zo yayi ta bashi haƙuri amma Adeeb bazai ce masa ko ci kankaba.duk da yadda yayi kewar tareeƙ ɗin cikin zuciyarsa. Abin yana yiwa tareek ciwo ,haka zai je gurin nanny yayi ta kuka ,saidai tabashi hakuri. Alhamdullah jikin fattu ya warke sosai,dan duk tabon ciwukanta ma babu,sosai shakuwa ta kara shiga tsakaninta da Adeeb,dan kuwa ya dawo da ita bangaren sa gaba ɗaya ,ya siyo mata sabbin kayan sawa ,da duk wani abu datake bukata. Yayin da gefe guda yake ci gaba da bincikensa akan al'amarin su Nazli da kuma sarƙar nan ta fattu,akan ammi ,saidai har yanzu ya kasa samun wata kwakwkwarar hujja da zai kama ammi da ita .dan haka ya kara yarda cewar hadin bakine na amma da nanny ,suke son hadashi da ammi. Bangaren rashad kuwa ,abin ba'acewa komai,dan har yanzu yana nan jiya iyau, baya uhhhm bare uhm -uhm .magani ta ko ina yi masa ake ,mai martaba da kansa abin yana damunsa,. Haka ma Adeeb yana jin ciwon abinda yayiwa ɗan uwan nashi,saidai koma menene shiyajawa kansa.kuma hakan bai hana shi neman masa magani ba . Shaikh lateef ya bawa Adeeb magungunan da zai rinka amfani dashi,kuma yana amfani dasu yadda ya kamata.zamu iya cewa yanzu abubuwa sun dan lafa agidan. Yanzu haka fattu ana mata lesson kullum ,zakuyi mamakin yadda fattu ta iya Yaren larabci sosai,tana ji kuma tana iya mayarwa, dan fattu akwai ƙwaƙwalwa,shikansa mai mata lesson yana mamakin hazaka irin ta fattu. Adeeb kullum yana kara nuna mata abubuwan da bata game ba.tayi kyau sosai ta goge idan ka ganta bazaka taba cewa itace ba. Kullum saisunyi waya da sarauniya suhaimat,sun shaku da juna sosai. Gimbiya Zulaihat ma tana nan tana nata shirin,dan yanzu kam tana ganin fattu na neman zama wata abar alfahari agidan,dan ta kereta ta ko ina,Shegiyar yarinya kyau kamar yar aljanu. Wannan kenan. Ammice zaune ƙaton falonta tana waya,dawowarta kenan daga gurin mai martaba,tana masa maganar ya dace ace zuwa yanzu Adeeb yayi aure ,dan shekaru na tafi kuma shine magajin fada. Dan haka abie yace ta zaba masa matar da zai aura ,tunda itace amminsa ,kuma yasan Adeeb bazaiki zabin ammin nashi ba.tun da dai shi ba kula yan mata yake ba. Cikin farin ciki kuwa ammi ta dawo ɗakinta ta kira kawarta. "Ƙawata ,albishirinki? Ammi ta fada cikin ɗoki. Bansan me akace mata ba ta dayan bangaren naji dai taci gaba da cewa"ai mai martaba ya bani damar zabawa Adeeb matar da zai aura,kuma ba kowa na zaba masaba face yar wajenki,maryam.kinga mun sami hanya cikin ruwan sanyi,da zamu cika burinmu akansa" ta fada cikin doki tana murmushi. Shiru na ɗan wani lokaci kafin taci gaba"ki rabu dashi, kawai ,nasan barazana ce yake min,amma kinsan bazan taɓa yarda Zulaihat ta auri Adeeb ba,dan kuwa ubanta zatayi wa aiki ba muba, Batun yarinyar da yazo da ita kuwa,na boye duk wata hanya danasan zai gane suwaye iyayenta na asali,kuma nasanya boka ya hana uwarta zuwa gasar nan ma gaba daya , Kinga har abada bazasu taba haduwa da junaba. Abu na gaba da zamuyi shine ,da zarar anyi auren nan,zamu sa ta kashe dan banza kowa ma ya huta, zan san yadda zanyi in shawo kan wancan mugun ya yarda ayi auren saimu kashe Adeeb din" Shiru ammi tayi tare da sauraron abinda ake fadi aɗaya bangaren. Kafin taci gaba"wllh ƙawata Ni kaina yarinyar nan na tsaneta ,bana don ganinta,Aduk lokacin dana ganta fuskar uwarta nake gani ,kuma ina tunano abinda ya faru abaya,dan haka itama kawar da ita zanyi kowa ya huta ,duk dana ɗauke sarƙar nan Tata,amma na nemeta na rasa ,kuma banganta awuyan yarinyar ba,dan haka ina tunanin bata koma gareta ba,ƙila dai nice na sauya mata gurin ajiya na manta" Shiru ammi ta sake yi ,kafin tace shikenan sai kinzo ma karasa maganar. Jikin fattu banda rawa da bari ba abinda yake ,zuciyarta sai neman tarwatsewa take , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!!wanann wace irin masifa ce haka,yanzu ammi tasan su waye iyayena dama ?kenan kashe Hamma zasuyi?me hakan ke nufi? kenan ammi ba itace mahaifiyar Adeeb ba?dan kuwa tasan ba ta yadda za'ayi uwa tayi yunkurin kashe ɗan ta, wai meke faruwa ne?wannan ɗin wane irin badakala ce kuma? Tsabar rawar da jikinta yakeyi bata san lokacin data buge wani flower vase dake ajiye agefenta ba ,ya fadi kasa ,jikake toshshs!! Ya fashe . Cikin tsoro da tazana fattu ,tayi sauri buya ajikin ƙofa tare da runtse idanunta. Ammi kuwa da sauri ta taso Dan ganin waye yayi mata labe ,har yaji sirri ta. Da mugun ƙarfi aka fizgi fattu akayi waje da ita ,buɗe baki fattu tayi da nufin kurma ihu,taji an toshe mata bakinta..... Waye ya dauke fattu? Me zai faru nan gaba? Muje zuwa anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:57] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 67/68 _______________Da sauri ammi ta taso cikin tashin hankali da fargaba,dan kuwa tabbas tasan wani yaji me take cewa. Fattu kuwa tsabar ruɗewa da shiga tashin hankali tama rasa ina zata dosa,tsoro ya cika mata zuciya ganin ammi ta nufo inda take ,saidai cikin wannan yanayin ne taji an fizgeta da mugun ƙarfi anyi waje da ita.nan take tsoronta ya kara rubanya.buda baki tayi da nufin kurma ihu ,dan atunaninta masu kashe tan ne suka kamata.saidai gam!aka rufe mata baki,bata yadda zatayi ihu.kuma cikin wani irin sauri mai kama da gudu akayi waje da ita,ta wata hanya da bata nan ta shigo ba. Ammi kuwa tayi iyakar dubanta ,amma bata ga kowa ba,kuma tabbas tasan anshigo cikin dakin nan,to waye?dan duk ta kora yan aiki can farfajiyar gidan dan tasami damar yin wayarta. Ko dai Adeeb ne?kai bashi bane ,dan kuwa Adeeb baya zuwa gareta ba tare da yayi sallama ba.toko nanny ce ?kai idan nanny ce zan iya cimma ta kafin ta gudu,wai waye wannan yake son shiga rayuwata ne?waye yake son bakuntar lahira kwana kusa?na rantse da Allah idan na gano ko waye saina hukuntashi, hukunci mai tsanani.yanzu dole mu sake sabon tsari dan wannan kam ya rika ya lalace"ammi ta fada cikin zafin zuciya da kunar rai. Tana nan tsaye Zulaihat ta shigo dakin ba ko sallama,kawai ammi sai ganin mutum tayi bukut ya shigo cikin falon.guri ta nema ta zauna tare da ƙurawa ammi ido. Harara ammi ta Banka mata tana tunanin koma dai Zulaihat ɗin ce ta shigo dazu da tasan Zulaihat ba hankali gareta ba? "Ke Zulaihat kece kika shigomin daki dazu kina Min labe?"ammi ta fada cikin haɗe fuska. Wani shegen kallon Zulaihat ke jifan ammi dashi,kafin ta fara magana "lallai ma ammi har kina tunanin akwai wanda zan zauna inayiwa labe?to me zan labe naji,bayan duk wani tuggun da ake ƙullawa ina sane dashi,me kuma za'a boyemin ?kinsan Ni bana munafurci kai tsaye nake Abunda naga dama "Zulaihat ta faɗa cikin rashin kunya tana wani juya ido. Kallonta ammi tayi cikin tsantsar ɓacin rai da tsanar halayen ta na rashin kunya kafin tace " yanzu kina Min wannan gatsalin kike son na aura miki Dana?to wllh gara ki nutsu Dan bazan yarda ki auri Adeeb da wannan shegen halin naki ba,domin shirme zakiyi tayi mana,idan mun saki aiki"ammi ta fada cikin faɗa -fada. Wata irin dariya Zulaihat tayi tana kallon ammi kafin tace "Kinga ammi ki daina min tsawa keba uwata bace,ko iyayena lallaɓani suke ,kuma da kike cewa zan bata muku aiki,ku atunaninku idan anyi auren biye muku zanyi in cutar da abin sona,?wllh garama ku nutsu daga ke har daddy na Dan kuwa rungumar mijina zanyi musha soyayya ,kuma duk wanda yayi yunkurin cutar da shi ,wllh saina kashe mutum,kinsan nima na iya dabancin"Zulaihat ta faɗa cikin gadara tana kallon ammi ido cikin ido. Baki buɗe ammi ke kallon Zulaihat,lallai yarinyar nan ta wuce yadda suke tunani,Gara ta lallabata,karta jika mata aiki,dan haka cikin dan murmushin yake ammi tace "kai ƴata dadina dake baki san wasa ba,yanzu saiki maida abu gaske,ki kwantar da hankalinki,kinsan nima bazan taɓa bari a cutar min da Adeeb ba, dama nayi tunanin bakinsu ɗaya da mahaifi ki,shiyasa na fadi hakan"ammi ta fada cikin murmushin yaƙe tana hararar Zulaihat ƙasa ƙasa. "Ato Gara dai mutum ya kula wllh ,dan zan iya komai akan abinda nake so"Zulaihat ta faɗa tana mai gyara zamanta zuwa kwanciya,tare da lumshe idonta kamar zatayi barci. "Zanyi makaganinki daga ke har uban Maki shegiya"ammi ta fada cikin zuciyarta,tana shigewa daki,cike da tunanin mafita. Ba'a dire fattu a ko ina ba, sai cikin wani daki mai dan duhu, wanda kana iya ganin mutum ,amma bazakaga fuskarsa kai tsaye ba. Koda aka direta sam ba'asakar mata baki ba. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,sai ƙoƙarin cire hannun mutumin take daga bakinta, ammata kasa . Cikin nutsuwa da kwantar da hankali ya fara magana "ki nutsu ,niba cutar dake zanyi ba,koda na bude miki baki to karkayi ihu " Cikin hanzari fattu ke jinjina kanta idonta yayi zuru zuru ,burinta kawai tajita free. Ahankali ya dannan makunnar dake gefensa,nan take dakin yayi haske ta yadda kana iya ganin komai. Da sauri fattu ta daga idanunta tana kallon mutumin, "Hamma tareeƙ"ta fada cikin rawar murya,"ka bani tsoro Hamma tareeƙ,meke faruwa cikin gidan nan,wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana?fattu ta faɗa cikin muryar kuka tana kallon tareeƙ. Shima kallonta yake zuciyarsa na masa zafi ,yayi fatan ace Adeeb da kansa yaji wannan maganar ba wani ne yaji ba. "Ki kwantar da hankali ki fateema,da sannu zaki fahimci komai " Ya fada tare da ɗauko wayarsa yayi kira. "Ummee kuzo ina nan cikin dakin baya"haka kawai ya faɗa ya kashe wayar. Kallonsa fattu keyi jikinta har lokacin rawa yake ,tana cikin shock da zallar mamaki,kujera tareeƙ ya nuna mata tare da cewa"ki zauna anan fateema " jiki ba kwari fattu tabi bango ta zauna aƙasa ba tare da ta hau kan kujerar da tareeƙ ke nuna mata ba.zallar mamakin ammi da al'ajabi ta ke ɗawainiya da fattu,yanzu duk zaman da sukayi dama ammi tasan asalin iyayenta?kuma ita ta sace sarƙarta wacce take matsayin shaidar da zata sadata da iyayenta na asali?amma menene ribar ammi nayin hakan?wane amfani zata samu?lallai dole ta sanar da Hamma wannan maganar . Bude kofar da akayi ke ya katsar mata da tunaninta ,da sauri cikin tsoro ta kalli bakin ƙofar,nanny ce ta shigo ita da amma. Da sauri fattu ta mike cikin rawar jiki ta ƙanƙame nanny tare da sakin kuka mai ciwo da radadi," nanny wai zasu kashe min hammana ,kuma nima zata kasheni ,sannan tace tasan asalin iyayena ,amma bazata bari muhadu dasuba.nanny wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana,anya kuwa itace ta haifeshi ?fattu ta faɗa tana mai dago kanta tare da kallon nanny. Cike da tausayin fattu nanny ta riketa ajikinta Tana mai shafa bayanta ,alamun rarrashi,kafin tace "ki kwantar da hankalinki ɗiyata,ba abinda zai sameku da yardar Allah,kuma yau zan sanar dake alakar dake tsakanin Adeeb da amminsa" cewar nanny Tana me zaunar da fattu akan kujera. Amma kuwa tana tsaye ta kafe fattu da idanu,tabbas hasashenta ya tabbata ,dan kuwa ba tun yau take zargin cewa fattu yar sarauniya suhaimat bace,dan kuwa tasha ganin irin sarƙar wuyan Fattu atare da iyalin suhaimat,bayan nan sai kayi duba na tsanake zaka gano tsantsar kamar dake tsakanin fattu da suhaimat ɗin.aikuwa insha Allahu yau ba sai gobe ba zata sanar da fattu wacece ammi. Cikin kuka fattu ke kallon nanny kafin tace "Dan Allah nanny ki sanar dani ala'akar dake tsakanin hammana da kuma ammi,ko zuciyarta zata sami salama,ji nake kamar zan mutu,banson wani abu ya sami hammana nanny Ina kaunar hammana fiye da yadda nake son kaina idan wani abu ya sameshi wllh mutuwa zanyi"fattu ta faɗa cikin kuka mai ban tausayi. Hawaye nanny ta goge tana mai kallon fattu kafin tace "In Sha Allahu ba abinda zai sami magajin fada ki kwantar da hankalinki ɗiyata. Hannun fattu amma ta kamo cikin sanyin murya tace "kiyi shiru ,ki kuma kwantar da hankalinki,dan yau zaki san abubuwan da baki sani ba abaya,dan haka ki adana hawaye ki zai miki amfani nan gaba "cewar amma tana kallon fattu cikin tausayawa. Share hawayen kuwa fattu tayi tare da kafe nanny da ido,zuciyarta na bugawa kamar ana. Kada ganga. Ahankali nanny ta fara magana"ammi ba itace asalin wacce ta haifi Adeeb ba,amma itace wacce ta rike shi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararararmmmm gaban fattu ya bada sautin karar da saida ta kusan faduwa tana daga zaune. Ai Ni kaina saida na tsorata na jefar da wayar nan dan tsoron jin abinda nanny zata faɗa . Muje zuwa masoyan fattu da Adeeb . Sai mun haɗe anjima in Sha Allahu. Anty mammy ce Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free book Page 67/68 _______________Da sauri ammi ta taso cikin tashin hankali da fargaba,dan kuwa tabbas tasan wani yaji me take cewa. Fattu kuwa tsabar ruɗewa da shiga tashin hankali tama rasa ina zata dosa,tsoro ya cika mata zuciya ganin ammi ta nufo inda take ,saidai cikin wannan yanayin ne taji an fizgeta da mugun ƙarfi anyi waje da ita.nan take tsoronta ya kara rubanya.buda baki tayi da nufin kurma ihu ,dan atunaninta masu kashe tan ne suka kamata.saidai gam!aka rufe mata baki,bata yadda zatayi ihu.kuma cikin wani irin sauri mai kama da gudu akayi waje da ita,ta wata hanya da bata nan ta shigo ba. Ammi kuwa tayi iyakar dubanta ,amma bata ga kowa ba,kuma tabbas tasan anshigo cikin dakin nan,to waye?dan duk ta kora yan aiki can farfajiyar gidan dan tasami damar yin wayarta. Ko dai Adeeb ne?kai bashi bane ,dan kuwa Adeeb baya zuwa gareta ba tare da yayi sallama ba.toko nanny ce ?kai idan nanny ce zan iya cimma ta kafin ta gudu,wai waye wannan yake son shiga rayuwata ne?waye yake son bakuntar lahira kwana kusa?na rantse da Allah idan na gano ko waye saina hukuntashi, hukunci mai tsanani.yanzu dole mu sake sabon tsari dan wannan kam ya rika ya lalace"ammi ta fada cikin zafin zuciya da kunar rai. Tana nan tsaye Zulaihat ta shigo dakin ba ko sallama,kawai ammi sai ganin mutum tayi bukut ya shigo cikin falon.guri ta nema ta zauna tare da ƙurawa ammi ido. Harara ammi ta Banka mata tana tunanin koma dai Zulaihat ɗin ce ta shigo dazu da tasan Zulaihat ba hankali gareta ba? "Ke Zulaihat kece kika shigomin daki dazu kina Min labe?"ammi ta fada cikin haɗe fuska. Wani shegen kallon Zulaihat ke jifan ammi dashi,kafin ta fara magana "lallai ma ammi har kina tunanin akwai wanda zan zauna inayiwa labe?to me zan labe naji,bayan duk wani tuggun da ake ƙullawa ina sane dashi,me kuma za'a boyemin ?kinsan Ni bana munafurci kai tsaye nake Abunda naga dama "Zulaihat ta faɗa cikin rashin kunya tana wani juya ido. Kallonta ammi tayi cikin tsantsar ɓacin rai da tsanar halayen ta na rashin kunya kafin tace " yanzu kina Min wannan gatsalin kike son na aura miki Dana?to wllh gara ki nutsu Dan bazan yarda ki auri Adeeb da wannan shegen halin naki ba,domin shirme zakiyi tayi mana,idan mun saki aiki"ammi ta fada cikin faɗa -fada. Wata irin dariya Zulaihat tayi tana kallon ammi kafin tace "Kinga ammi ki daina min tsawa keba uwata bace,ko iyayena lallaɓani suke ,kuma da kike cewa zan bata muku aiki,ku atunaninku idan anyi auren biye muku zanyi in cutar da abin sona,?wllh garama ku nutsu daga ke har daddy na Dan kuwa rungumar mijina zanyi musha soyayya ,kuma duk wanda yayi yunkurin cutar da shi ,wllh saina kashe mutum,kinsan nima na iya dabancin"Zulaihat ta faɗa cikin gadara tana kallon ammi ido cikin ido. Baki buɗe ammi ke kallon Zulaihat,lallai yarinyar nan ta wuce yadda suke tunani,Gara ta lallabata,karta jika mata aiki,dan haka cikin dan murmushin yake ammi tace "kai ƴata dadina dake baki san wasa ba,yanzu saiki maida abu gaske,ki kwantar da hankalinki,kinsan nima bazan taɓa bari a cutar min da Adeeb ba, dama nayi tunanin bakinsu ɗaya da mahaifi ki,shiyasa na fadi hakan"ammi ta fada cikin murmushin yaƙe tana hararar Zulaihat ƙasa ƙasa. "Ato Gara dai mutum ya kula wllh ,dan zan iya komai akan abinda nake so"Zulaihat ta faɗa tana mai gyara zamanta zuwa kwanciya,tare da lumshe idonta kamar zatayi barci. "Zanyi makaganinki daga ke har uban Maki shegiya"ammi ta fada cikin zuciyarta,tana shigewa daki,cike da tunanin mafita. Ba'a dire fattu a ko ina ba, sai cikin wani daki mai dan duhu, wanda kana iya ganin mutum ,amma bazakaga fuskarsa kai tsaye ba. Koda aka direta sam ba'asakar mata baki ba. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,sai ƙoƙarin cire hannun mutumin take daga bakinta, ammata kasa . Cikin nutsuwa da kwantar da hankali ya fara magana "ki nutsu ,niba cutar dake zanyi ba,koda na bude miki baki to karkayi ihu " Cikin hanzari fattu ke jinjina kanta idonta yayi zuru zuru ,burinta kawai tajita free. Ahankali ya dannan makunnar dake gefensa,nan take dakin yayi haske ta yadda kana iya ganin komai. Da sauri fattu ta daga idanunta tana kallon mutumin, "Hamma tareeƙ"ta fada cikin rawar murya,"ka bani tsoro Hamma tareeƙ,meke faruwa cikin gidan nan,wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana?fattu ta faɗa cikin muryar kuka tana kallon tareeƙ. Shima kallonta yake zuciyarsa na masa zafi ,yayi fatan ace Adeeb da kansa yaji wannan maganar ba wani ne yaji ba. "Ki kwantar da hankali ki fateema,da sannu zaki fahimci komai " Ya fada tare da ɗauko wayarsa yayi kira. "Ummee kuzo ina nan cikin dakin baya"haka kawai ya faɗa ya kashe wayar. Kallonsa fattu keyi jikinta har lokacin rawa yake ,tana cikin shock da zallar mamaki,kujera tareeƙ ya nuna mata tare da cewa"ki zauna anan fateema " jiki ba kwari fattu tabi bango ta zauna aƙasa ba tare da ta hau kan kujerar da tareeƙ ke nuna mata ba.zallar mamakin ammi da al'ajabi ta ke ɗawainiya da fattu,yanzu duk zaman da sukayi dama ammi tasan asalin iyayenta?kuma ita ta sace sarƙarta wacce take matsayin shaidar da zata sadata da iyayenta na asali?amma menene ribar ammi nayin hakan?wane amfani zata samu?lallai dole ta sanar da Hamma wannan maganar . Bude kofar da akayi ke ya katsar mata da tunaninta ,da sauri cikin tsoro ta kalli bakin ƙofar,nanny ce ta shigo ita da amma. Da sauri fattu ta mike cikin rawar jiki ta ƙanƙame nanny tare da sakin kuka mai ciwo da radadi," nanny wai zasu kashe min hammana ,kuma nima zata kasheni ,sannan tace tasan asalin iyayena ,amma bazata bari muhadu dasuba.nanny wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana,anya kuwa itace ta haifeshi ?fattu ta faɗa tana mai dago kanta tare da kallon nanny. Cike da tausayin fattu nanny ta riketa ajikinta Tana mai shafa bayanta ,alamun rarrashi,kafin tace "ki kwantar da hankalinki ɗiyata,ba abinda zai sameku da yardar Allah,kuma yau zan sanar dake alakar dake tsakanin Adeeb da amminsa" cewar nanny Tana me zaunar da fattu akan kujera. Amma kuwa tana tsaye ta kafe fattu da idanu,tabbas hasashenta ya tabbata ,dan kuwa ba tun yau take zargin cewa fattu yar sarauniya suhaimat bace,dan kuwa tasha ganin irin sarƙar wuyan Fattu atare da iyalin suhaimat,bayan nan sai kayi duba na tsanake zaka gano tsantsar kamar dake tsakanin fattu da suhaimat ɗin.aikuwa insha Allahu yau ba sai gobe ba zata sanar da fattu wacece ammi. Cikin kuka fattu ke kallon nanny kafin tace "Dan Allah nanny ki sanar dani ala'akar dake tsakanin hammana da kuma ammi,ko zuciyarta zata sami salama,ji nake kamar zan mutu,banson wani abu ya sami hammana nanny Ina kaunar hammana fiye da yadda nake son kaina idan wani abu ya sameshi wllh mutuwa zanyi"fattu ta faɗa cikin kuka mai ban tausayi. Hawaye nanny ta goge tana mai kallon fattu kafin tace "In Sha Allahu ba abinda zai sami magajin fada ki kwantar da hankalinki ɗiyata. Hannun fattu amma ta kamo cikin sanyin murya tace "kiyi shiru ,ki kuma kwantar da hankalinki,dan yau zaki san abubuwan da baki sani ba abaya,dan haka ki adana hawaye ki zai miki amfani nan gaba "cewar amma tana kallon fattu cikin tausayawa. Share hawayen kuwa fattu tayi tare da kafe nanny da ido,zuciyarta na bugawa kamar ana. Kada ganga. Ahankali nanny ta fara magana"ammi ba itace asalin wacce ta haifi Adeeb ba,amma itace wacce ta rike shi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararararmmmm gaban fattu ya bada sautin karar da saida ta kusan faduwa tana daga zaune. Ai Ni kaina saida na tsorata na jefar da wayar nan dan tsoron jin abinda nanny zata faɗa . Muje zuwa masoyan fattu da Adeeb . Sai mun haɗe anjima in Sha Allahu. Anty mammy ce Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 65/66 ________________"Ki sanar dani dalilin da yasa baki son zuwana gurin yarinyar nan? Me alaƙarki da ita ?ko ince me ta tsaremiki uktee? Sarauniya suhaimat ta fada cikin haɗe fuska ,dan tasan kadan daga aikin ammi ta hanata zuwa gurin fattu. Zaro ido ammi tayi tana mai kallon suhaimat ,dan sai lokacin ta fahimci tana kokarin bada kanta,cikin in-ina ta fara magana "su...hai..mat,wane dalilin ne zaisa kuwa in hanaki zuwa gurinta?kawai ina gudun ace ko wata munaƙisar muka ƙulla yasa kike ta zarya,kinsan tunda wannan abun ya faru to komai ma laifi zai zama , amma bayan wannan bani da wani dalili"ammi ta fada tana kafe suhaimat da idanu. Murmushi suhaimat tayi ,kafin tace "Indai dan wannan ne karki damu ,ai kowa yasan Ni likitar matace,kuma ba laifi bane idan naje duba marar lafiya,kuma ma mace"suhaimat ta fada cikin yanayi na rashin damuwa.kafin ta juya ta bar ɗakin. Harara ammi ta biya da ita ,kamar idanunta zasu fado ,haushin suhaimat takeji fiye da tunanin mai tunani,wllh badan tana tsoron faruwar wani abu ba ,data gama da suhaimat ,dan itace silar shigar ta ko wace irin damuwa.amma ba komai muje zuwa sannu sannu bata hana zuwa,saidai dade ba'ajeba. koda sarauniya suhaimat ta koma bangaren Adeeb, kwance ta tarar da fattu adaki, idanunta alumshe kamar mai barci,yayinda Adeeb ke falo yana amsa waya. Bayan sun gaisa yake sanar da ita fattun tana cikin daki, dan sosai yake jin dadin yadda take kula masa da fattu. Tana shiga fattu ta buɗe idonta,da sauri sakamakon jin muryarta,dan dama tana kwancen nan, tunaninta Sarauniya suhaimat kawai take. Da murna ta tashi zaune tana murmushi,tare da kallon suhaimat, Itama cikin farin ciki ta karasa gareta ta zauna. Ahankali fattu tace "inna nayi tunanin bazaki dawoba,ina ta tunaninki araina"ta fada fuskarta ɗauke da annuri. Shafa fuskar fattu tayi kafin tace "ƴata kenan ,tunda nace zan dawo ,ai dole na na dawo naga kaykykyawar fuskar nan taki,ya jikin naki"suhaimat ta fada cikin murmushi. "Da sauki "cewar fattu. "Masha Allah,haka ake so ki kula da shan magungunanki kinji"cewar sarauniya suhaimat. Jinjina kai fattu tayi kafin tace "ina yan biyu " Murmushi suhaimat tayi kafin tace "suna can suna shiryawa ,Basu san nazo nan ba da kin gansu sun biyoni, dan sun damu dake sosai" ta fada cikin murmushi. Fattuna murmushin tayi, tana wasa da ƴan yatsunta. Sun jima suna hira da fattu,duk da tana ɗan jin kunyar sarauniya suhaimat din,amma zakayi mamakin yadda ya sake suke ta hira ,harda dariya . Anan ne take sanar da ita cewar yau zasu tafi garinsu. Lokaci guda fattu ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka, "Ayya inna meyasa zaki tafi?dan Allah ki zauna anan,bana son ki tafi "fattu ta faɗa tana mai kallon sarauniya suhaimat. Ahankali suhaimat ta kamo hannun fattu ta rike cikin nata tana ɗan murmushi,duk da itama sam batason rabuwa da Fattun,amma dan ta kwantar mata da hankali sai tayi murmushi tace"karki damu my princess ai zan rinka zuwa ina ganinki,kuma wataran zance yarima ya kawomin ke muyi hutu,ko bazaki zoba"?ta fada tana kallon fattu. "Zanzo mana inna dama bana son zama agidan nan tsoron wannan mai kama da hamman nawa nake"ta fada cikin yanayi na damuwa, idanunta har ya kawo kwalla. Cikin damuwa itama suhaimat ta tallafi kumatun fattu,tana mai cewa"ki kwantar da hankalinki ƴata, ba abinda zai miki kinji,ki daina tsoronsa,yanzu haka yana can akwance cikin halin mutuwa da rayuwa,kuma hammanki yana tare da ke"ta fada cikin salon kwantar da hankali. Jinjina kai fattu tayi tana mai kallon suhaimat ɗin. Murmushi suhaimat tayi tana mai kallon wayarta dake ringing ,lokaci ta duba taga harta kara minti biyar akan time ɗin da zasu tafi,dan ma private jet ne.kuma mijinta bai sami halartar gurin ba saboda wani meeting da suke mai muhimmanci. "To ƴata zan tafi saina ƙara dawowa zan dawo mutafi tare dake ,kinji"suhaimat ta fada tana jin ba dadi cikin ranta,ji take kamar zata rabu da abu mafi muhimmanci arayuwarta. Ahankali fattu ta daga mata kai, idanunta na zubda kwalla,sam bata son suhaimat ta tafi,"Allah ya tsareku,ya kaiku lafiya inna ,saikin dawo"fattu ta faɗa tana ɗan kwantar da kanta jikin suhaimat. Rungumeta suhaimat tayi cikin alhinin rabuwa da ita .Adeeb ne ya shigo dakin da sallamarsa,da alama wanka yayi dan ya cire kayan dazu ya sanya riga da wando blue and white yayi matuƙar kyau sosai,sai ƙamshinsa yake kamar kullum. Kallonsu yayi yadda ko wanne ke zubda kwalla ,lallai lamarin Allah abin kallone,dubi yadda lokaci ɗaya shakuwa ta shiga tsakanin bayin Allahn nan?kamar sunsan juna.murmushi yayi yana kallon suhaimat kafin yace "anty suhaimat har yanzu kina nan da tausayi da kuma saurin kuka " ya faɗa yana kallonta.shikam tun sanin da yayi mata haka bakinta yake ,akwai tausayi da son mutane bata da kyamar dan adam. Share hawayen idanunta tayi kafin tace "prince wllh da zaka bani yarinyar nan dana tafi da ita can Ghana munyi zaman mu ,dan Allah ya doramin kaunarta cikin raina sosai" ta fada tana shafa kan fattu. "In baki ita ku tafi?Ni kuma inyi yaya,haka kawai ,ki tafimin da mata?inaaa"Adeeb ya faɗa cikin zuciyarsa.amma zahiri saiyace "karki damu watarana zata zo " "Allah yasa da gaske kake,yanzu dai kayi mana hoto dan tarihi"sarauniya suhaimat ta fada tana mai janyo fattu jikinta. Luuuf!! fattu tayi ajikin suhaimat tana mai jin wani irin sanyi acikin zuciyarta.hotuna Adeeb yayi musu kusan kala biyar awayarsa, hakama yayi musu awayar Sarauniya suhaimat ɗin. Da gyar suka rabu da juna cikin kewa da kaunar juna, fattu sai kuka take ta rungume Adeeb lokacin da suhaimat ta tafi rarrashinta yayi tayi da gyar ya samu tayi barci. Ammi kuwa sosai taji dadin tafiyar suhaimat,dan hankalinta sam bai kwanta ba ,gani take kamar zata iya gano wani abu game da fattu Yanzu damuwarta daya shine yadda ,zata bullowa lamarin Adeeb. Rashad ya farfaɗo ,saidai gaba ɗaya ankasa gane kansa ,dan kullum haka zaka ganshi shiru baya magana saidai kallo,abin yana matukar damun amma,haka zatayi ta kuka tana kallonsa,saidai kawai kaga hawaye yana bin fuskar Rashad din,ya rame sosai,dan baya wani cin abinci,ga karaya ajikinsa ta ko ina likitoci suna ta binciken kwakwalwarsa dan suna tunanin tanan ya sami matsala.saidai muce Allah ya bashi lafiya. Sam yanzu Adeeb baya kula tareeƙ ,haka zai zo yayi ta bashi haƙuri amma Adeeb bazai ce masa ko ci kankaba.duk da yadda yayi kewar tareeƙ ɗin cikin zuciyarsa. Abin yana yiwa tareek ciwo ,haka zai je gurin nanny yayi ta kuka ,saidai tabashi hakuri. Alhamdullah jikin fattu ya warke sosai,dan duk tabon ciwukanta ma babu,sosai shakuwa ta kara shiga tsakaninta da Adeeb,dan kuwa ya dawo da ita bangaren sa gaba ɗaya ,ya siyo mata sabbin kayan sawa ,da duk wani abu datake bukata. Yayin da gefe guda yake ci gaba da bincikensa akan al'amarin su Nazli da kuma sarƙar nan ta fattu,akan ammi ,saidai har yanzu ya kasa samun wata kwakwkwarar hujja da zai kama ammi da ita .dan haka ya kara yarda cewar hadin bakine na amma da nanny ,suke son hadashi da ammi. Bangaren rashad kuwa ,abin ba'acewa komai,dan har yanzu yana nan jiya iyau, baya uhhhm bare uhm -uhm .magani ta ko ina yi masa ake ,mai martaba da kansa abin yana damunsa,. Haka ma Adeeb yana jin ciwon abinda yayiwa ɗan uwan nashi,saidai koma menene shiyajawa kansa.kuma hakan bai hana shi neman masa magani ba . Shaikh lateef ya bawa Adeeb magungunan da zai rinka amfani dashi,kuma yana amfani dasu yadda ya kamata.zamu iya cewa yanzu abubuwa sun dan lafa agidan. Yanzu haka fattu ana mata lesson kullum ,zakuyi mamakin yadda fattu ta iya Yaren larabci sosai,tana ji kuma tana iya mayarwa, dan fattu akwai ƙwaƙwalwa,shikansa mai mata lesson yana mamakin hazaka irin ta fattu. Adeeb kullum yana kara nuna mata abubuwan da bata game ba.tayi kyau sosai ta goge idan ka ganta bazaka taba cewa itace ba. Kullum saisunyi waya da sarauniya suhaimat,sun shaku da juna sosai. Gimbiya Zulaihat ma tana nan tana nata shirin,dan yanzu kam tana ganin fattu na neman zama wata abar alfahari agidan,dan ta kereta ta ko ina,Shegiyar yarinya kyau kamar yar aljanu. Wannan kenan. Ammice zaune ƙaton falonta tana waya,dawowarta kenan daga gurin mai martaba,tana masa maganar ya dace ace zuwa yanzu Adeeb yayi aure ,dan shekaru na tafi kuma shine magajin fada. Dan haka abie yace ta zaba masa matar da zai aura ,tunda itace amminsa ,kuma yasan Adeeb bazaiki zabin ammin nashi ba.tun da dai shi ba kula yan mata yake ba. Cikin farin ciki kuwa ammi ta dawo ɗakinta ta kira kawarta. "Ƙawata ,albishirinki? Ammi ta fada cikin ɗoki. Bansan me akace mata ba ta dayan bangaren naji dai taci gaba da cewa"ai mai martaba ya bani damar zabawa Adeeb matar da zai aura,kuma ba kowa na zaba masaba face yar wajenki,maryam.kinga mun sami hanya cikin ruwan sanyi,da zamu cika burinmu akansa" ta fada cikin doki tana murmushi. Shiru na ɗan wani lokaci kafin taci gaba"ki rabu dashi, kawai ,nasan barazana ce yake min,amma kinsan bazan taɓa yarda Zulaihat ta auri Adeeb ba,dan kuwa ubanta zatayi wa aiki ba muba, Batun yarinyar da yazo da ita kuwa,na boye duk wata hanya danasan zai gane suwaye iyayenta na asali,kuma nasanya boka ya hana uwarta zuwa gasar nan ma gaba daya , Kinga har abada bazasu taba haduwa da junaba. Abu na gaba da zamuyi shine ,da zarar anyi auren nan,zamu sa ta kashe dan banza kowa ma ya huta, zan san yadda zanyi in shawo kan wancan mugun ya yarda ayi auren saimu kashe Adeeb din" Shiru ammi tayi tare da sauraron abinda ake fadi aɗaya bangaren. Kafin taci gaba"wllh ƙawata Ni kaina yarinyar nan na tsaneta ,bana don ganinta,Aduk lokacin dana ganta fuskar uwarta nake gani ,kuma ina tunano abinda ya faru abaya,dan haka itama kawar da ita zanyi kowa ya huta ,duk dana ɗauke sarƙar nan Tata,amma na nemeta na rasa ,kuma banganta awuyan yarinyar ba,dan haka ina tunanin bata koma gareta ba,ƙila dai nice na sauya mata gurin ajiya na manta" Shiru ammi ta sake yi ,kafin tace shikenan sai kinzo ma karasa maganar. Jikin fattu banda rawa da bari ba abinda yake ,zuciyarta sai neman tarwatsewa take , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!!wanann wace irin masifa ce haka,yanzu ammi tasan su waye iyayena dama ?kenan kashe Hamma zasuyi?me hakan ke nufi? kenan ammi ba itace mahaifiyar Adeeb ba?dan kuwa tasan ba ta yadda za'ayi uwa tayi yunkurin kashe ɗan ta, wai meke faruwa ne?wannan ɗin wane irin badakala ce kuma? Tsabar rawar da jikinta yakeyi bata san lokacin data buge wani flower vase dake ajiye agefenta ba ,ya fadi kasa ,jikake toshshs!! Ya fashe . Cikin tsoro da tazana fattu ,tayi sauri buya ajikin ƙofa tare da runtse idanunta. Ammi kuwa da sauri ta taso Dan ganin waye yayi mata labe ,har yaji sirri ta. Da mugun ƙarfi aka fizgi fattu akayi waje da ita ,buɗe baki fattu tayi da nufin kurma ihu,taji an toshe mata bakinta..... Waye ya dauke fattu? Me zai faru nan gaba? Muje zuwa anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 63/64 _______________Jikin nanny ne yayi sanyi sosai,ganin Adeeb atsaye,kuma ya gansu tare da amma,tasan yanzu kam kome zata faɗa masa ,bazai taba yarda da ita ba.ahankali take takawa zuwa gareshi,gaba ɗaya jikinta ba kwari, Shikuwa Adeeb yana tsaye ya kafeta da Mayun idanunsa ,masu sanya mutum yaji shi cikin tsoro da fargaba. Nanny Tana karasowa tace "magajin fada ,fushi kake dani ko"? Ta fada cikin sanyi murya da mutuwar jiki. Lumshe ido Adeeb yayi ,zuciyarsa na masa zafi yana mamakin abinda nanny tayi masa,ace wai nanny ta hada kai da maƙiyarsa tana tayata ƙoƙarin cutar dashi,matar daya ɗauka matsayin uwa ?mutum kenan. "Ko kaɗan nanny bana fushi dake,kawai ina godiya ga Allah ne ,daya nunamin gaskiya ,na gane irin mutanen da nake tare dasu,na daukeki tamkar mahaifiyata nanny,Amma bansan nayi babban kuskuren yin hakan ba,dan Allah kiyi haƙuri"ya faɗa yana mai haɗe hannayensa guri ɗaya alamun neman afuwa. Sosai nanny kejin ciwo cikin ranta ,damuwa da taraddadi sun cika mata zuciya,dama tayi wannan tunanin,tasan idan har Adeeb ya gansu tare da amma ,to shikenan,kuma kome zata faɗa masa bazai yarda da ita ba,amma Allah shine shaida bata da nufin cutar da Adeeb ko kaɗan. "Magajin fada wllh abinda kake zargi ba haka bane ,kada ganina tare da amma yasa maka kokwanto akaina, wllh nima Ina jinka tamkar tareeƙ bazan taɓa cutar dakaiba magajin fada. Nanny ta faɗa cike da damuwa aranta. Girgiza kai kawai Adeeb yayi tare da barin gurin,zuciyarsa kamar zata fashe tsabar damuwa . Kallonsa kawai nanny keyi,tana fatan Allah yasa ya gane gaskiya cikin sauri kafin komai ya daɗa lalacewa. Ba kowa cikin falon ammi,sai ƙamshi dake tashi ta ko'ina ,dan ammi akwai son kamshi,kai tsaye ya nufi dakin kwananta, nocking yayi amma shiru,hakan yasa shi shiga cikin dakin kai tsaye.saidai nan ma ba kowa cikin dakin. Harya juya zai fice ,sai kuma zuciyarsa ta raya masa ya duba wanann akwatin da yaji ammi na magana akanta. Dan haka juyowa yayi yana karewa dakin kallo. Ahankali yake duba dakin dan neman wannan akwatin,amma yayi iyakar dubansa bai ganta ba. Harya hakura sai kuma ya hango wata akwati mai kyau da ɗaukar ido,yasan akwatin Dan acikinta ammi ke ajiye kwalakwalanta ,dan haka sai yayi tunanin ba komai cikinta, har ya juya da nufin barin dakin,sai kuma zuciyarsa ta kwadaitu da son duba akwatin . Dan haka ahankali ya zauna tare da ɗauko akwatin, danna lanbobin bude akwatin yayi,dan kuwa tuni yasansu, aikuwa saiga akwati ta bude,gwalagwalai ne acikinta iya ganin ka ,masu kyau da ɗaukar hankali,kallo ɗaya zaka musu kasan an zubar da maƙudan kudade wajen mallakar sarkokin. Dubawa yayi tayi amma baiga komai aciki ba,sai wani dan karamin akwati mai kyau da ya gani,kallon akwatin yake da mamakin meye acikinsa aka wareshi ?lallai yana son ganin abinda ke ciki.dan haka hannu Ya mika tare da ɗauko akwatin ya bude. Mamaki ,al'ajabi ruɗu da kuma faduwar gaba sune suka ziyarci zuciyar Adeeb,sakamakon ganin sarƙar nan ta Hulwa data bace ,cikin wannan akwatin, Me yakawo sarkar Hulwa cikin kayan ammi?har akayi mata adana ta musamman?me hakan ke nufi,shidai yasan ammi tana da sarkokin da suka ninka kudin wannan bare yayi tunanin ta daukene dan bata da mai tsada kamar wannan ,to me hakan ke nufi kenan?innalillahi meke faruwa ne acikin gidan nan?kodai akwai Abinda ammin nashi ke kullawa da gaske ? Wayyo ina zaisa kansa ?dawa ya kamata ya yarda ne cikin fadar nan? Dauko sarƙar yayi cikin sauri ya maida komai inda yake sannan yayi saurin barin dakin na ammi ya koma part dinsa. Zuciyarsa na zafi kamar zata kama da wuta . Lokacin daya koma part din nasa fattu ta farka,tana zaune tana kuka,tsoro takeji,har lokacin barin ma dataga ita kadaice cikin dakin,ina Hamma ya tafi ya barta?karfa wannan Rashad din ya dawo mata? Gashi wannan innar ma bata dawo ba,wannan tunanin yasata ƙanƙame jikinta tana kuka. Adeeb kuwa cikin wani irin yanayi na sarewar zuciya ya shigo cikin dakin,abubuwa sunyi masa yawa cikin zuciyarsa,jinsa yake kamar bashiba, kansa banda ciwo ba abinda yake ,wai meke shirin faruwa da rayuwarsa ne ?me hakan ke nufi ?me amminsa ke nufi da ɗauke sarƙar Hulwa? Kukan hulwar da yaji Yone yasani saurin ƙarasawa cikin dakin. Tana jin motsi sa ta zabura atsorace tana mai kallon ƙofar dakin.ganin Adeeb ne ya shigo yasata saurin yunkurawa ta mike da gyar tana kuka tare da kallonsa. Da saurinsa ya ƙaraso inda take ,yana zuwa ya kamo hannunta tare da shafa gefen fuskarta yace "menene kike kuka?inane yake miki ciwo ?ya faɗa cikin mugun sanyin murya ,wanda har saida fattu ta ɗago kanta ta kalleshi, Idanunsa sunyi jajur sosai jijiyoyin kansa sun fito rudurudu,fuskarsa tayi jajur ,kana gani kasan yana cikin damuwa da tashin hankali. Cikin kuka fattu ta faɗa ƙirjinsa ta rungumeshi, tana faɗin "tsoro nakeji Hamma ,ko ina ganin ƙaninka nake yana min gizo Hamma" ta fada cikin kuka tana ƙanƙame Adeeb. Cike da tarin damuwar da baisan menene mafitarta ba shima ya ƙanƙame fattun ajikinsa yana mai lumshe ido da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi, Ahankali yake faɗin"kiyi haƙuri Hulwa , dagani harke muna cikin damuwa, Hulwa komai bayamin dadi na kasa gane dawa ya kamata in amince cikin fadar nan,Hulwa kowa na fadar nan so yake yaga bayana bansan me na tsare musu ba" Adeeb ya faɗa cikin murya mai tattare da karaya da sarewa. Shiru fattu tayi tana sauraron abinda yake fadi,ita fa sam bata fahimci inda zancen sa ya nufa ba,ahankali tace "Hamma ,su waye ke son kamin bayanka"? "Shiru yayi yana mai kara rungume fattu ajikinsa,dan sosai yake jin nutsuwa na samunsa sakamakon rungumeta da yayi,zuciyarsa tana yi masa sanyi .shafa gashin kanta kawai yake bai ce komai ba. Kusan minti biyar suna rungume da juna ,kafin Adeeb yayi karfin halin zareta daga jikinsa ya zaunar da ita abakin gado,kallonta yake ,har zuwa lokacin idanunta basu koma yadda suke ba,akwai kumburi da kuma dan jaa kadan acikinsu. Hannunta ya kamo cikin nashi ya rike gam-gam yana kallonta.ji yake kamar ita kadai ta rage masa wacce zai fadawa damuwarsa,saidai fattu yarinyace,idan ma ya faɗa mata damuwarsa bazata fahimci me yake nufiba. Kallonsa fattu tayi itama,tabbas akwai Abinda ke damun hamman nata,ko menene oho."Hamma meke danunka?baka da lafiya ne ?ta fada cikin muryar marasa lafiya ,wadanda suka sha kuka. Ahankali ya koma kusa da ita ya zauna ,kallonta yayi yace "Hulwa abinda ke damuna yana da yawa,ina cikin wata sarkakiya wacce Allah ne kawai zai fitar dani,bani da wanda zan fadawa damuwata ahalin yanzu,bana son sanar da abie na komai,dan gudun ɓacin ransa,saboda tsoron kar ciwonsa ya tashi,kiyi ta min addu'a kinji hulwatee" Adeeb ya faɗa yana mai riƙe habar fattu tare da zuba mata gajiyayyun idanunsa. Cike da tausayawa fattu ke kallon Adeeb,kafin itama ta sanya hannunta akan fuskarsa tana shafa gefen fuskar tashi, kamar yadda yake mata .sannan tace "Hamma zanyi ta maka addu'a Allah ya yaye maka damuwarka, kuma kaima kayi ta addu'a Allah maji rokon bawansa ne ,Allah ya bawa abie lafiya Hamma,amma me zai hana ka sanar da innarka itama ta tayaka addu'a" fattu ta faɗa bayan ta cire hannunta daga kan fuskar Adeeb. Wata sassanyar ajiyar zuciya Adeeb ya sauke lokacin da fattu ke shafa gefen fuskarsa ,ahankali ya lumshe idanunsa yana jin wani irin sanyi yana Ratsa zuciyarsa. Ahankali ya bude idonsa lokacin da yaji ta cire hannunta daga kan fuskarsa.kafin yace "Hulwa ammina tana daga cikin mutanen da nake son boyewa damuwata ,ahalin yanzu bazan iya sanar da ita komai daya danganci lamarinaba,ke dai kiyi ta min addu'a kinji"ya faɗa cikin murya mai cike da ban tausayi. Sosai fattu kejin tausayin hamman nata yana Ratsa zuciyarta.ahankali ta ɗora kanta gafen kafadunsa tare da rungumoshi ta gefe.tayi shiru cike da tunanin meke damun hamman nata. Ahankali shima ya dora kansa akan nata kan yana jinsa tamkar marayan da bai da kowa. "Hamma wannan innar bazata dawo ba ko?" Ta fada ahankali idanunta alumshe. Shima idonsa alumshe yake yana shafa kan fattu ,yace "kina so ganinta ne? "Daga kai tayi alamun eh sannan tace " eh Hamma ina son ganinta ,ina kaunar ta har cikin raina ,kuma tace daga yau itace inna ta" Ajiyar zuciya Adeeb yayi kafin yace " Hulwa ita kadai kike kauna ? Ni baki kaunata?ya faɗa ba tare da yasan ya fadi hakan ba .saida ya faɗa sannan ya fahimce me yace . "A'a Hamma ina ƙaunarka sosai mana,ina sonka,kaidin kamar baffana kake ,bani da kowa saikai, Hamma bana son wani abu ya tab aka ma" ta fada tana ɗago kai tare da kallon Adeeb. Cikin wani irin farin ciki da jin dadi Adeeb ke kallon fattu,zuciyarsa cike da jin dadi yace "da gaske kike Hulwa?" Ya faɗa cikin murmushi yana kallonta. Jinjina kai tayi itama cikin murmushi tana kallonsa. Ahankali ya janyota jikinsa ya rungumeta gamm yana mai lumshe ido , sosai yake jin wani irin. Daɗi da Nutsuwa cikin zuciyarsa. "Kina son ɓata min shiri ko ?,kisani wllh idan kikayi wani kuskuren dana rasa damata,kema zaki karbi naki hukuncin ,kin sanni kinsan halina,kuma kinsan abinda zan iya aikatawa ,dan haka ki kula da kanki,komai yana ƙoƙarin lalacewa saboda sakacinki,to bazan laminci wannan abinda kike yiba.wllh zan aikaki gurin da duk wanda zai zamenin matsala nake aikawa.akan wannan karagar zan iya batar da kowa" Wani mutum ne daya lulluɓe ilahirin fuskarsa ke fadin wannan maganar cikin ɓacin rai yana kallon ammi,wacce ke tsaye cikin tsantsar tsoro ,jikinta sai rawa yake cikin tashin hankali tace "dan Allah kayi hakuri ,wllh ina yin iyakar ƙoƙarina akan wannan abun ,kuma aKwai shirin da nake yi ,karka damu ka kara hakuri "ta fada cikin rawar murya,tana kallon mutumin da baka ganin komai bace kwayar idanunsa. Cikin fushi mutumin ya damƙi wuyan ammi ya hadata da jikin bango yana faɗin"bana son jin komai daga bakin ki kawai ki aikata abinda nace miki ,ki tabbatar ya bar duniyar nan nanda lokaci kankani,zan kawo miki abinda zaki saka mishi acikin abinci,zai mutu kuma ba wanda zai zargi wani abu,idan kuma aka samu kuskure .yayi shiru tare da sakin wuyan ammi wacce ke kakari tana kokarin shekawa. Tari sosai ammi keyi,lokacin da mutumin ya saki wuyanta sannan yayi tafiyarsa cikin sauri yana ƙara gyara rufin fuskarsa. Saida ammi ta samu nutsuwa kafin ta bar gurin ,kai tsaye dakinta ta nufa ,gaba ɗaya awahale take, Bakin gado ta zauna cike da damuwa tana tunani,can dai ta dauko akwatin sarkokinta,abin yayi matuƙar tsorata ta lokacin datayi arba da akwatin sarƙar fattu ba komai acikinta. Wani dan gajeren ihu ta kwalla cikin tashin hankali,tana dube dube cikin akwatin ,waye ya daukemin sarƙar nan?na shiga ukuna wayyo ni ammi .da sauri suhaimat ta shigo dakin ammi ,dan kuwa taji ihun da ammin ta kwalla."uktee lafiya ?naji kina ihu?suhaimat ta fada cikin damuwa tana rike ammi. "Ba komai suhaimat na Dan bugene "ammi ta fada cikin tashin hankali. Kallonta suhaimat keyi cikin rashin yarda da abinda ya fada,amma koma dai menene tunda taki faɗa shikenan . "To mukam muna ta shiri anjima jirginmu zai tashi .zanje in Kara duba yarinyar can "suhaimat ta fada tana kallon ammi. "Karkije suhaimat ,karkije,na roƙeki,ki rufamin asiri karkije "ammi ta fada cikin tashin hankali tana kama hannun suhaimat.dan tana tsoron kar ace sarƙar ta koma gurin fattu ne kuma suhaimat ta gani ta gane yarta. Cike da mamaki suhaimat ke kallon ammi,anya kuwa kalau take?ji yadda ta wani rikice daga cewa zani ganin yarinyar can. Kai gaskiya akwai wani abu aƙasa. Cikin hade fuska suhaimat tace "uktee ki fadamin menene dalilinki da baki son na haɗu da yarinyar can?me kike kullawa akanta ?menene hajjarki ? suhaimat ta fada cikin haɗe rai tana kure ammi da ido. Zato ido ammi tayi tana kallon suhaimat ,kafin cikin in Ina ta fara magana "su...haim..at ...... Hmmmmm muje zuwa masu karatu. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free book Page 67/68 _______________Da sauri ammi ta taso cikin tashin hankali da fargaba,dan kuwa tabbas tasan wani yaji me take cewa. Fattu kuwa tsabar ruɗewa da shiga tashin hankali tama rasa ina zata dosa,tsoro ya cika mata zuciya ganin ammi ta nufo inda take ,saidai cikin wannan yanayin ne taji an fizgeta da mugun ƙarfi anyi waje da ita.nan take tsoronta ya kara rubanya.buda baki tayi da nufin kurma ihu ,dan atunaninta masu kashe tan ne suka kamata.saidai gam!aka rufe mata baki,bata yadda zatayi ihu.kuma cikin wani irin sauri mai kama da gudu akayi waje da ita,ta wata hanya da bata nan ta shigo ba. Ammi kuwa tayi iyakar dubanta ,amma bata ga kowa ba,kuma tabbas tasan anshigo cikin dakin nan,to waye?dan duk ta kora yan aiki can farfajiyar gidan dan tasami damar yin wayarta. Ko dai Adeeb ne?kai bashi bane ,dan kuwa Adeeb baya zuwa gareta ba tare da yayi sallama ba.toko nanny ce ?kai idan nanny ce zan iya cimma ta kafin ta gudu,wai waye wannan yake son shiga rayuwata ne?waye yake son bakuntar lahira kwana kusa?na rantse da Allah idan na gano ko waye saina hukuntashi, hukunci mai tsanani.yanzu dole mu sake sabon tsari dan wannan kam ya rika ya lalace"ammi ta fada cikin zafin zuciya da kunar rai. Tana nan tsaye Zulaihat ta shigo dakin ba ko sallama,kawai ammi sai ganin mutum tayi bukut ya shigo cikin falon.guri ta nema ta zauna tare da ƙurawa ammi ido. Harara ammi ta Banka mata tana tunanin koma dai Zulaihat ɗin ce ta shigo dazu da tasan Zulaihat ba hankali gareta ba? "Ke Zulaihat kece kika shigomin daki dazu kina Min labe?"ammi ta fada cikin haɗe fuska. Wani shegen kallon Zulaihat ke jifan ammi dashi,kafin ta fara magana "lallai ma ammi har kina tunanin akwai wanda zan zauna inayiwa labe?to me zan labe naji,bayan duk wani tuggun da ake ƙullawa ina sane dashi,me kuma za'a boyemin ?kinsan Ni bana munafurci kai tsaye nake Abunda naga dama "Zulaihat ta faɗa cikin rashin kunya tana wani juya ido. Kallonta ammi tayi cikin tsantsar ɓacin rai da tsanar halayen ta na rashin kunya kafin tace " yanzu kina Min wannan gatsalin kike son na aura miki Dana?to wllh gara ki nutsu Dan bazan yarda ki auri Adeeb da wannan shegen halin naki ba,domin shirme zakiyi tayi mana,idan mun saki aiki"ammi ta fada cikin faɗa -fada. Wata irin dariya Zulaihat tayi tana kallon ammi kafin tace "Kinga ammi ki daina min tsawa keba uwata bace,ko iyayena lallaɓani suke ,kuma da kike cewa zan bata muku aiki,ku atunaninku idan anyi auren biye muku zanyi in cutar da abin sona,?wllh garama ku nutsu daga ke har daddy na Dan kuwa rungumar mijina zanyi musha soyayya ,kuma duk wanda yayi yunkurin cutar da shi ,wllh saina kashe mutum,kinsan nima na iya dabancin"Zulaihat ta faɗa cikin gadara tana kallon ammi ido cikin ido. Baki buɗe ammi ke kallon Zulaihat,lallai yarinyar nan ta wuce yadda suke tunani,Gara ta lallabata,karta jika mata aiki,dan haka cikin dan murmushin yake ammi tace "kai ƴata dadina dake baki san wasa ba,yanzu saiki maida abu gaske,ki kwantar da hankalinki,kinsan nima bazan taɓa bari a cutar min da Adeeb ba, dama nayi tunanin bakinsu ɗaya da mahaifi ki,shiyasa na fadi hakan"ammi ta fada cikin murmushin yaƙe tana hararar Zulaihat ƙasa ƙasa. "Ato Gara dai mutum ya kula wllh ,dan zan iya komai akan abinda nake so"Zulaihat ta faɗa tana mai gyara zamanta zuwa kwanciya,tare da lumshe idonta kamar zatayi barci. "Zanyi makaganinki daga ke har uban Maki shegiya"ammi ta fada cikin zuciyarta,tana shigewa daki,cike da tunanin mafita. Ba'a dire fattu a ko ina ba, sai cikin wani daki mai dan duhu, wanda kana iya ganin mutum ,amma bazakaga fuskarsa kai tsaye ba. Koda aka direta sam ba'asakar mata baki ba. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,sai ƙoƙarin cire hannun mutumin take daga bakinta, ammata kasa . Cikin nutsuwa da kwantar da hankali ya fara magana "ki nutsu ,niba cutar dake zanyi ba,koda na bude miki baki to karkayi ihu " Cikin hanzari fattu ke jinjina kanta idonta yayi zuru zuru ,burinta kawai tajita free. Ahankali ya dannan makunnar dake gefensa,nan take dakin yayi haske ta yadda kana iya ganin komai. Da sauri fattu ta daga idanunta tana kallon mutumin, "Hamma tareeƙ"ta fada cikin rawar murya,"ka bani tsoro Hamma tareeƙ,meke faruwa cikin gidan nan,wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana?fattu ta faɗa cikin muryar kuka tana kallon tareeƙ. Shima kallonta yake zuciyarsa na masa zafi ,yayi fatan ace Adeeb da kansa yaji wannan maganar ba wani ne yaji ba. "Ki kwantar da hankali ki fateema,da sannu zaki fahimci komai " Ya fada tare da ɗauko wayarsa yayi kira. "Ummee kuzo ina nan cikin dakin baya"haka kawai ya faɗa ya kashe wayar. Kallonsa fattu keyi jikinta har lokacin rawa yake ,tana cikin shock da zallar mamaki,kujera tareeƙ ya nuna mata tare da cewa"ki zauna anan fateema " jiki ba kwari fattu tabi bango ta zauna aƙasa ba tare da ta hau kan kujerar da tareeƙ ke nuna mata ba.zallar mamakin ammi da al'ajabi ta ke ɗawainiya da fattu,yanzu duk zaman da sukayi dama ammi tasan asalin iyayenta?kuma ita ta sace sarƙarta wacce take matsayin shaidar da zata sadata da iyayenta na asali?amma menene ribar ammi nayin hakan?wane amfani zata samu?lallai dole ta sanar da Hamma wannan maganar . Bude kofar da akayi ke ya katsar mata da tunaninta ,da sauri cikin tsoro ta kalli bakin ƙofar,nanny ce ta shigo ita da amma. Da sauri fattu ta mike cikin rawar jiki ta ƙanƙame nanny tare da sakin kuka mai ciwo da radadi," nanny wai zasu kashe min hammana ,kuma nima zata kasheni ,sannan tace tasan asalin iyayena ,amma bazata bari muhadu dasuba.nanny wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana,anya kuwa itace ta haifeshi ?fattu ta faɗa tana mai dago kanta tare da kallon nanny. Cike da tausayin fattu nanny ta riketa ajikinta Tana mai shafa bayanta ,alamun rarrashi,kafin tace "ki kwantar da hankalinki ɗiyata,ba abinda zai sameku da yardar Allah,kuma yau zan sanar dake alakar dake tsakanin Adeeb da amminsa" cewar nanny Tana me zaunar da fattu akan kujera. Amma kuwa tana tsaye ta kafe fattu da idanu,tabbas hasashenta ya tabbata ,dan kuwa ba tun yau take zargin cewa fattu yar sarauniya suhaimat bace,dan kuwa tasha ganin irin sarƙar wuyan Fattu atare da iyalin suhaimat,bayan nan sai kayi duba na tsanake zaka gano tsantsar kamar dake tsakanin fattu da suhaimat ɗin.aikuwa insha Allahu yau ba sai gobe ba zata sanar da fattu wacece ammi. Cikin kuka fattu ke kallon nanny kafin tace "Dan Allah nanny ki sanar dani ala'akar dake tsakanin hammana da kuma ammi,ko zuciyarta zata sami salama,ji nake kamar zan mutu,banson wani abu ya sami hammana nanny Ina kaunar hammana fiye da yadda nake son kaina idan wani abu ya sameshi wllh mutuwa zanyi"fattu ta faɗa cikin kuka mai ban tausayi. Hawaye nanny ta goge tana mai kallon fattu kafin tace "In Sha Allahu ba abinda zai sami magajin fada ki kwantar da hankalinki ɗiyata. Hannun fattu amma ta kamo cikin sanyin murya tace "kiyi shiru ,ki kuma kwantar da hankalinki,dan yau zaki san abubuwan da baki sani ba abaya,dan haka ki adana hawaye ki zai miki amfani nan gaba "cewar amma tana kallon fattu cikin tausayawa. Share hawayen kuwa fattu tayi tare da kafe nanny da ido,zuciyarta na bugawa kamar ana. Kada ganga. Ahankali nanny ta fara magana"ammi ba itace asalin wacce ta haifi Adeeb ba,amma itace wacce ta rike shi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararararmmmm gaban fattu ya bada sautin karar da saida ta kusan faduwa tana daga zaune. Ai Ni kaina saida na tsorata na jefar da wayar nan dan tsoron jin abinda nanny zata faɗa . Muje zuwa masoyan fattu da Adeeb . Sai mun haɗe anjima in Sha Allahu. Anty mammy ce Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 51/53 _________________Abakin ƙofar hall ɗin Zulaihat ta tarar da Rashad ,yana tsaye da waya ahannunsa ,da alama kira yake ƙoƙarin yi,saidai yana ganinta ya maida wayar cikin aljihunsa yana mai faɗin,"yawwa dama ke nake ƙoƙarin kira,sai gaki kin fito. Ƙarasowa Zulaihat tayi kusa dashi ta tsaya" ya ake ciki ne ?" Ta faɗa tana ɗan waigen bayanta. "Yau burina zai cika ,zan sami abinda ke hanani barci,kuma zanyiwa Adeeb illah,saina rama dukan da yayi min akan yarinyar da yake iƙirarin yar amanar da ce,bayan kuma Ni nasan dadironsa ce ,kawai kishine da mugunta sukayi masa yawa,shine ya hanani Nima in ɗana"cewar Rashad yana mai kallon Zulaihat. "Kaga Rashad karka ƙara cewa dadiron my Prince ce,karkayi masa sharri,dan kuwa nasan halinsa nasan koshi waye,wllh bazai taba ajiye yarinyar nan dan biyan buƙatarsa ba,mutumin da har maganin sha'awa nake saka masa alemo,dan kawai yayi tarayya dani,amma duk yadda ya galabaita bazai koda rungumeni ba. Dama dai kaine akace ka ajiye ta dan biyan buƙatarka,to wannan kam na yarda dan nasan kai din namamajo ne " Zulaihat ta faɗa tana mai galla masa harara,dan taji haushin sharrin da yayiwa adeeb,ita da take burin ace itace zata fara bude Adeeb aledarsa ina zataso jin wannan batu. Wani shegen kallo Rashad ya watsa mata kafin yace " banza yar tasha ,ke har Ni zaki cewa na mamajo? Ai duk iskancina ban kaki ba,kefa ƴar maye ce sannan jarababbiya, Ni kaina sau nawa ina taimaka miki ?ina ce wataran har guduwa nake saboda jarabarki ?zaki raina min hankali wawiya kawai" Rashad ya faɗa cikin faɗa. Haushi sosai ya kama Zulaihat ,ranta ya ɓaci da kalaman Rashad gareta ,wato har gori zaiyi mata ,dan ta neme shi kusan sau uku ?ba komai zai gane kurensa wllh. "Ni kakeyiwa gori Rashad ?to wllh kasani bazan taimaka maka akan ƙudirinka na yauba ,saidai kayi kai kadai ,banza marar mutunci" Zulaihat ta faɗa cikin ɓaci rai tana mai barin gurin cikin sauri. Tsaki Rashad yayi yana mai faɗin"aikin banza ,da me zaki iyamin agurin banda kema kice kina so intaimaka miki ,Ni kuwa ranata ta yau duka ta fine baby ce,yar ƙwaya kawai " ya faɗa yana mai nufar part ɗin ammi. Ammi kuwa tana zuwa part ɗinta cikin ɗakinta ta nufa ,ƙullewa tayi tare da zama bakin gado,tana tunani iri iri cikin ranta, wata akwati ta ɗauko dake can ƙasan gadon ta tare da budewa, Tana buɗewa wani hayaƙi yayo sama baƙiƙirin dashi,banda wari ba abinda ke tashi cikin hayaƙin nan,da sauri ammi ta toshe hancinta, tana mai zaro ido waje,abayyane ta furta " na shiga ukuna ba dai kwalbar nan ta fashe ba? Shikenan ta faru ta ƙare ,dama nasan hakan zata faru wayyo Allah na" ammi ta faɗa tana mai bin wata kwalba yar gajeriya da ta tarwatseda ido,wani farin abu mai kauri yana ta motsi kamar tsutsa. Bugun ƙofar da ammi tajine yasata saurin rufe akwatin ta tura can kasan gado,saita kanta tayi cikin ɗauriya ta nufi ƙofar . Rashad ta gani tsaye abakin ƙofar ,"ammi ya ake ciki ne ?ta yaya zan ɗauki yarinyar ne ?kinsan ba aɗakin ta zan aiwatar da ƙudirina ba,dan wancan mayen zai iya zuwa ya cin mini" ya faɗa yana kallon fuskar ammi . "Ka tafi can ɗayan part ɗina ka jira zan kawo maka ita da kaina ,ina son kayi mata abinda nan da wata guda ma bazata san inda kanta yake ba,bana son ka tausaya mata ko kaɗan"ammi ta fada fuskarta ahaɗe. "Kada ku damu ammi bazan taɓa baki kunya ba,nayi alƙawarin saina yi mata abinda Bama ki tsammata ba"Rashad ya faɗa yana wani irin killer smile. Ficewa ammi tayi tare da nufar part ɗin su fattu.ba kowa afalon,dan kuwa nanny ta ɗan leƙe gurin taron ,ganin fattu kwance tana barci. Cikin ɗakin ammi ta shiga ,tsaye tayi agaban gadon da fattu ke kwance ,idanunta arufe kamar mai barci,amma idanunta biyu,hammanta kawai take tunani. Kusan minti uku ammi tayi tana kallon fattu dake kwance ,tabbas ko tantama batayi ,wannan yarinyar gimbiya suhaimat ce ,dan kuwa sai yanzu take ganin tsantsar kamannin dake tsakaninsu,amma ta yaya suka haɗu da Adeeb?har ya taho da ita nan?wannan shine abinda take son sani. Ganin fattu ta ɗan motsa ne yasa ammi ta ɗan kira sunanta " fateema tashi" Ammi ta faɗa tana ɗan shafa kan fattu. Ahankali cikin nutsuwa fattu ta tashi zaune tana ɗan mika ,dan ta jima akwance. Murmushi tayiwa ammi tare da sunkuyar da kanta ƙasa cikin kunya . "Fateema Sarkin kunya,ke kadaice aɗakin ne"ammi ta faɗa cikin Hausa ,dan kuwa ta iya Hausa sosai itama. Jinjina kai fattu tayi tana wasa da ƴan yatsunta. Murmushi ammi tayi tana shafa kan fattu kafin tace " to ya jikin naki,?" " Da sauƙi inna"fattu ta faɗa cikin yar karamar muryarsa mai dadi. "Kinga bai kamata ki zauna ke kaɗai anan ba kowa ba,dan haka maza ki tashi ki koma can ɗaya part ɗin sauki kwanta kiyi barcinki kinji?kafin tashi daga taron" ammi ta faɗa tana mai kamo hannun fattu cikin nata ,suka fice daga ɗakin. Binta fattu tayi ba tare da ta musaba, dan tana tsananin jin kunyar ammi,saidai haka kawai taji gabanta na faɗuwa,gashi hammanta yace karta fita ko ina ,karya dawo bai ganta ba ransa ya ɓaci. Haka dai tabi ammi har zuwa wancan part ɗin da Rashad take ciki. Wani ɗaki ammi ta kaita tare da zaunar da ita akan kado,tace cikin murmushi"ki zamanki anan kinji,idan kina jin barci saiki kwanta,akwai abubuwan ci ,acikin fridge idan kinji bukatar ci" ammi ta faɗa tana mai kallon fattu ,fuskarta ɗauke da murmushi. Jinjina kai fattu tayi kafin tace "inna !Hamma yace karbaje ko ina ,karya dawo kuma bai ganni ba"ta faɗa kanta aƙasa. Wata uwar harara ammi ta bankawa fattu,kuji yar iyayi shegiya mai kama da aljanu,zaki gane kurenki, ne yau zaki yabawa aya zaƙinta,dagake har Adeeb ɗin. Da sauri ta saki fuska tana murmushi,ganin fattu ta ɗago kai tana kallonta,"karki damu habeebtee zan sanar da Adeeb nina kawoki nan kinji?"ammi ta faɗa tana sumbatar goshin fattu .kafin ta fice daga ɗakin. Rashad ta ci karo dashi abakin ƙofar ,daga shi sai wando iya gwuiwa da singlet,kallonsa ammi tayi cike da murmushi,tana mai faɗin"Rashad kenan,wannan zumuɗin haka?,nidai ka kula da maganata banson asami matsala" ammi ta faɗa tana mai kamo kunnensa. Murmushi yayi yace "baki da matsala ammina,ke dai kawai kijira sakamako"ya faɗa yana mai murmushin mugunta. "Amma ka jira sai an jima kadan,zan kulle ƙofar ta baya,inka gama sauka fice ta ɗayan ƙofar" jinjina kai Rashad yayi cikin zaƙuwa da son ammi tayi ta fice daga ɗakin. Adeeb yana zaune kusa da abie ,saidai haka kawai yakejin gabansa na faɗuwa ,sosai yake jin faduwar gaban.fattu kawai yake tunani yana ji cikin ransa yana buƙatar ganinta ahalin yanzu. Kallonsa ya kai inda Rashad ke zaune,saidai ba alamunsa agurin.gabansa ne ya ƙara mugun faɗuwa,ina Rashad ya nufa?yaushe ya bar gurin? Da sauri ya yunƙura zai mike,dan zuwa ya duba fattu,saidai gurin taron ne ya kara de da kiran sunansa Adeeb,ana buƙatar yayi jawabin godiya ga baki . Kallon abie yayi cikin yanayi na marairaita ,amma abin ya jinjina masa kai alamun yaje yayi jawabin. Haka Adeeb ya karbi lasifikar nan badan ransa yaso ba,burinsa kawai yaje gurin fattu. Adaidai wannan lokacin kuma Rashad ya kulle ƙofofin ɗakin daga falon har zuwa toilet duka,ɗakin da fattu ke ciki kawai ya bari abuɗe .kai tsaye ya kunna kansa cikin ɗakin. Fattu na zaune abakin gadon inda ammi ta zaunar da ita,zuciyarta sam bata aminta da zaman ɗakin nan ba, sai kalle kalle take, Da sauri ta juyo atsorace jin kamar mutum atsaye akanta. Ido huɗu sukayi da Rashad tsaye abakin ƙofa yana kallonta ,fuskarsa ɗauke da murmushi irin na yan duniya, Da sauri fattu ta miƙe tsaye jikinta na rawa,me wannan mutum yake yi anan kuma?ba innar Hamma tace nan ma ɗalibta bane?innalillahi,wayyo hammana kana ina?fattu ta faɗa cikin ranta jikinta na rawa matuƙa. Murmushi Rashad keta famanyi,yana takowa cikin ɗakin bayan ya kulle ƙofar,cikin harshen larabci yake faɗin"yan mata meye na tsorata haka?nimafa nazone nayi miki abinda wancan wawan yayan nawa ke miki,ki nutsu yarinya musha daɗinmu tare ,dan kuwa yau wllh ko mutuwa zakiyi saina kwashi daɗi" ya faɗa yana mai karasowa bakin gadon. Kuka fattu ta fara tana mai yarfe hannu, dan kuwa sosai take fahimtar yaren yanzu,dan haka ta fahimci da dama abubuwan daya faɗa, "Wayyo Allah na kayi hakuri dan Allah ,wllh niba yar iska bace ,kuma Hamma baya min komai,kayi min rai dan Allah"fattu ta faɗa cikin kuka sosai tana ja da baya. Zagaye suka fara ita da Rashad,yana ƙoƙarin kamota,ita kuma tana zillewa cikin kuka tana masa magiya,akan ya barta karya mata komai. Ganin zata ɓata masa lokaci ne kawai yayi wani tsalle tare da damko gashin kanta cikin fushi ya wanka mata mari tare da hankaɗata kan gadon. "Dan ubanki ki nutsu wllh idan kika ɓatamin lokaci,saina yi miki fata-fata anan gurin,kina abu kamar baki san me nake sanyi ba ,ko irin baki taba yi ɗin nan ba,shi wancan wawan idan yazo haka kike masa?Rashad ya faɗa cikin tsawa yana mai haurowa kan gadon. Cikin azama fattu ta mirgina can karshen gadon tana kuka,tare da kiran "wayyo hammana kazo ,Hamma kazo ka taimakeni" Ran Rashad ne ya ƙara ɓaci ganin zata ɓata masa lokaci,da sauri shima ya bita ya damko gashin kanta,ya ƙara wanke ta da mari, nan da nan gefen bakinta ya fashe jini ya fara zuba. Ihu fattu ta kwalla cikin azaba tana kuka tare da riƙe hannunsa daya damko gashin kanta . Ƙoƙarin Rashad yake ya haɗe bakinsa dana fattu ,amma sai kauda kai take tana kuka tare da juya kai. Bakinta Rashad ta matse da karfin gaske ,gaba ɗaya kamaninsa sun sauya ,ba abinda yake so da buri illa yabiya buƙatarsa da fattu.gashi sai neman bashi matsala take. Hannunsa ɗayan ya ɗora akan ƙirjin fattu ,zaro ido fattu tayi cikin tsantsar razana da jin hannunsa inda ba wanda ya taba ɗorawa,da karfi ta dunkule hannunta tare da buga masa aciki. Ihu Rashad ya kwalla Dan kuwa ta bugeshi sosai acikinsa. Hankaɗata yayi jikin bango ,aikuwa ta buga kanta ajikin bangon ,ji kake gummm!!ta gwara kanta. Ihu ta kwalla cikin azaba tana mai dafe goshinta da jini ya wanke ,tsabar azaba numfashinta har ɗauke wa yake. Ko tashi ta kasayi,da rarrafe ta nufi bakin ƙofa jini na zuba agoshinta. Cikin mugun bacin rai Rashad ya nufota, rigarta ya kamo ta baya ya fizgota baya. Mari yayi ta sauƙe mata har guda hudu,sannan ya cilla ta kan gadon, Gaba ɗaya fattu ta fita daga hayyacinta ,ko hannunta bata iya dagawa,numfashinta sai kaiwa da kawowa yake, Rashad kuwa cikin rashin imani ya zare wando sa tare da singlet yayi kan fattu gadan -gadan ,yana zuwa ya janye gadon tare da kama rigar fattu ya yagatadaga sama har ƙasa ,sannan ya........... Wayyo fattu ,Hamma kana ina kazo ka ceci fattunka,shikenan Rashad zai cutar da fattunka . Da gudu na fice dan nemo inda Adeeb yake .saiki biyoni muje nemansa tare. Taku ce anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 53/54 ________________Gaba ɗaya Rashad ya zama kamar wani mahaukaci,ba abinda ke gabansa face biyan buƙatarsa. Gaban rigar fattu ya kama da karfin tsiya ya tsargeta ,tun daga sama har ƙasa. Nan da nan farar best ɗin fattu da baƙin skin tite ɗin ta suka bayya, Allah ma yasa wandon har ƙasa yake. " Wllh yau ko da zaki mutu ,saina ida nufina akanki,banga wanda zai iya karbarki daga hannuna ba" Rashad ya faɗa cikin wata irin murya ta azzalumai,waɗanda suka manta da cewar Allah yana kallonsu duk abinda suke aikatawa. Da gyar fattu ta iya buɗe rinannun idanunta ,wanda tsabar mari da kuka suka sanya idanun kumbura sosai. Ahankali take daga lips ɗin ta magana take amma saiƙa kura mata ido zaka fahimci me take cewa."wallahu galibun ala amrina" shine abinda take ta maimaitawa abakinta. Ƙoƙarin zare skin tite ɗin Rashad keyi amma sam ya kasa,jikinsa sai rawa yake,yana jin kamar wanda ake jona masa shocking,Amma tsabar masifa da jaraba ,yaki fasa abinda yakeyi, Cikin haushi,ya ƙara kaiwa kumatun fattu mari mai zafi da shiga jiki."Dan ubanki me kikasa ajikinki?idan na taɓaki nakejin kamar ana zuƙemin jini?"Rashad ya faɗa yana mai kai fuskarsa saitin Tata,bakinsa ya ɗora akan na fattu,aikuwa ba wata wata fattu ta gartsa masa cizo alips ɗinsa.kara ya kwalla yana mai komawa gefe dafe da lips ɗin sa na ƙasa "kai -kai -kai Ni kika ciza Dan uwarki?zaki gane kurenki ,wllh yau saina kusan kasheki Shegiyar yarinya mai taurin kai"Rashad ya faɗa yana mai danƙo gashin fattu ,wanda yayi buju-buju. Fattu fa ko motsin kirki bata iyayi,gaba ɗaya jikinta ya saki,tunda take a rayuwarta,bata taɓa shiga tashin hankali da azaba irin na yauba. Sunan Allah kawai take ambata cikin ranta. Adeeb kuwa cikin gaggawa yayi jawabinsa tare da godiya ga baƙin da suka zo dan tayashi murnar dawowa gida cikin ƙoshin lafiya.sosai ƙirjinsa ke mugun bugawa zuciyarsa kamar zata fito waje,idanunsa sunyi jajur dasu,wani irin ɗaci yakeji cikin zuciyarsa,sannan ko dana second ɗaya ne fattu taƙi barin tunaninsa. Gefen da Rashad ke zaune Adeeb ya ƙara kai dubansa, baya gurin har zuwa yanzu,kai gaskiya akwai Abinda ke faruwa ,dole yaje ya duba Hulwa. Dan haka cikin hanzari ya mike tsaye ,kallonsa abie yayi tare da tambayar ina zashi haka ?ya mike cikin hanzari,sanar da abie yayi cewar kansa ke ciwo yana son yaje ya kwanta. Sanin da abie yayi cewar ,sam Adeeb yana son hayaniyane,yasa shi cewa yaje ya kwanta sannan yasha magani,akwai maganar da zasu yi zuwa dare. Cikin sauri da sassarfa Adeeb ya nufi ƙofar barin hall ɗin,yana ɗan kallon gefen da tareeƙ ke zaune,saidai baiga tareeƙ agurin ba.dan haka ficewa yayi daga hall ɗin yana mai takawa da sauri sosai. Bangaren nanny ya nufa kai tsaye,yana shiga ya tarar da tareeƙ da nanny atsaye cirko -cirko,gabansa ne ya ƙara faɗuwa ,da sauri ya karasa gurin nanny yana kallonta,"nanny Ina Hulwa?"ya faɗa cikin muryar damuwa. Kallonsa nanny tayi itama da alamun damuwa akan fuskarta tace " to magajin fada,nan da ka ganmu wllh ita muke nema,naje gurin taron can kenan,na barta tana barci,kuma ina dawowa naga bata ɗakin,na duba ko ina cikin bangaren nan banganta ba,saiga tareeƙ kuma yana tambayar ko Rashad ya shigo nan" Da sauri Adeeb ya nufi ɗakin da fattu ke zaune gabansa naci gaba da bugawa da ƙarfi. Ko ina ya duba amma bata nan,to ina taje?yasan dai ba yawo takeyi ba ,ba inda ta sani cikin fadar nan,ko part ɗin sa ma sau ɗaya ya kaita,da sauri ya juyo yana kallon tareeƙ," Ina Rashad yayi?"ya tambayi tareeƙ cikin wata irin murya mai kama da ta basawa. "Yallaɓai ina zaune naga lokacin da Rashad ke waya,kuma saiya fito waje,hankalina bai kwanta da fitowar sa ba,dan haka saina biyoshi,ina fitowa na hangesu shida Zulaihat,dan haka na buya ina sauraron me zasuce,yallaɓai amma banji me suke tattaunawa ba,saidai ga dukkan alamu akwai abunda suka ƙulla tare, sai dai kuma basu sami jituwa ba,dan kuwa cikin fushi suka rabu. Nayi ƙoƙarin bin Rashad Dan ganin inda ya nufa amma ban ganshi ba" tareeƙ ya faɗa yana kallon Adeeb cikin damuwa. Dafe kai Adeeb yayi zuciyarsa na masa zafi,lallai idan har wani abu Rashad ke ƙoƙarin aikatawa akan Hulwa ,to zai gane kurensa wllh azeem,saiya ɗanɗani kudarsa. Cikin sauri Adeeb ya nufi ƙofar fita daga part ɗin,tareeƙ ya na biye dashi,ganin zasu fice yasa nanny tayi saurin bin bayansu dan bazata iya zama ba. Suna fita daga part din, kai tsaye Adeeb part din ammi ya nufa,ko fattu can ta tafi,saidai suna gab da shiga ya tsinkayi Muryar ammi na kiran sa,tsayawa yayi harta ƙaraso,"lafiya na ganku haka afujajan?gashi ka bar gurin taro ba'atashi ba?"ammi ta faɗa tana karantar yanayin Adeeb. Ahankali Adeeb ya sauke wata ajiyar zuciya mai zafi,tare da lumshe idanu kana yace "ammi mun rasa inda yarinyar nan tayi ne ,shine zamu duba ko tana party ɗinki" Adeeb ya faɗa cikin yamutsar fuska kamar zaiyi kuka. "Hmmmmm ji dan Allah wai akan wannan Shegiyar yarinyar suka tada hankalinsu haka,dan kawai basu ganta ba. Tukunnama wllh sai kunga yadda rayuwarta ta koma yanzu,dan nasan Rashad ya kammala aikinsa"ammi ta faɗa cikin zuciyarta,amma azahiri, Cikin hanzari ta riƙo hannun Adeeb tana mai zaro ido." Ikon Allah ina kuma ta nufa?dan gaskiya bata part ɗina, sai dai kuma ɗazu naga Rashad yana shawagi tsakanin part ɗina Dana nanny,Allah yasa bashine yayi mata wani abu ba" cewar ammi tana mai dafe kai cikin nuna tsantsar tashin hankali. Gaban Adeeb ne ya fadi ,shikenan dama yasan hakan zata iya kasancewa, dan kuwa sam yau bai yarda da Rashad ba dama ,"innalillahi "Adeeb ya faɗa cikin ruɗu da tashin hankali. Da sauri ya kunna kansa cikin part ɗin na ammi,suka rufa masa baya. Saidai nan ma sunyi iya bincike su amma bata nan,wasa -wasa fa sune har part ɗin Rashad Amma bashi ba Hulwa,zuwa wannan lokacin Adeeb ya shiga tsantsar tashin hankalin da bazai misaltuba,gaba ɗaya fuskarsa tayi jaaa kamar manja, idanunsa sun koma kala kalan nan,idan ya buɗe baki har wani turiri zakaga yana fitowa daga bakin nasa. Hankali kowa ya tashi,tsakanin ammi ,tareeƙ ,nanny dakuma amma ,wacce ta tsincesu abangaren Rashad,Dan itama nemansa tayi ta rasa agurin taron,shine tazo dubawa ko part ɗin sa ya dawo. Sai kuma ta riskesu suna dubansa.sosai tashiga tashin hankali,karfa Rashad ya janyo mata wata sabuwar matsalar,amma tasan ma bai zama lallai abinda suke zargi ya kasance ba. Cikin wani irin voice Adeeb ya juyo yana kallon amma tare da fara magana " wllh !wllh!!wllh!!! idan wani abu ya sami hulwa ta silar ɗank,i nayi alƙawarin saina illatashi,ta yadda ke kanki bazaki so ganinsa ba" Adeeb ya faɗa yana mai nuna amma da ɗan yatsanshi, tsabar masifa da bala'i kumatunsa har rawa suke. Cikin tsoro amma ta ja baya tana mai dafe ƙirjinta ,dan kuwa ta tsorata da yanayin na Adeeb,tana kuma fatan Allah yasa ba hannun Rashad aɓatan fattu. Can kuwa wajen taro ,anyi addu'oi,kuma anci ansha taro ya tashi lafita,abie yana ta tunanin ina iyalin nashi suka nufa ,dan baiga kowa agurin taron ba,zuciyarsa na raya masa akwai Abinda ke faruwa ,dan haka kai tsaye bayan ya sallami baƙinsa ya nufi bangaren sa ,jakadiyarsa ya tura cikin gida dan ta gano masa ko lafiya. Adeeb yana gama korawa ammi warning yayi waje cikin zazzafar zuciya da jin jikinsa yana masa wani irin rawa,idanunsa gaba ɗaya ya rine zuwa kalar na macizai.tsoro sosai ya kama su ammi da nanny,hatta tareeƙ atsorace yake,dan bai taba ganin yallaɓan nashi cikin wannan yanayin ba. Part ɗin sa ya nufa kai tsaye,saidai yana zuwa saitin ɗaya part ɗin na ,ammi yaji zuciyarsa ta tsananta da bugawa ,cak yaja ya tsaya tare da ƙure ƙofar part ɗin da idanunsa.zuciyarsa na raya masa ya shiga ya duba,saidai yana tunanin ammi bata fiye amfani da bangaren nan ba ,kuma me zai kawo Rashad nan ma ? Idan kuma yazo nan ɗin da Hulwa dan kawar da tunaninka fa ?ɗayar zuciyar ta bashi amsa.dan haka ba bata lokaci ya kama handle ɗin kofar ya murza da zummar shiga,saidai kuma akulle yaji ƙofar ,hakan ya matukar bashi mamaki,dan kuwa kullum part din nan abuɗe yake ,koda ammi bata ciki akwai hadimai acikinsa.amma how comes yau zai kasance akulle haka.nan take zuciyarsa ta bashi lallai Hulwa na cikin part ɗin nan.daidai lokacin su ammi suka ƙara so gurin.kallon tareeƙ yayi cikin wata irin murya yace " na tabbata Hulwa na cikin nan,saidai ina mamakin yadda part ɗin ya kasance akulle karon farko" ya faɗa yana kallon ammi,wacce tayi wiƙi -wiƙi tsoro ya ɗan bayyana akan fuskarta. Dan kuwa Adeeb ya kafeta da mayun idanunsa.sam ba zargin ta yake ba,kawai yana tunanin yadda aka yaudareta ne itama har akayi amfani da part ɗinta.dan baya raba ɗaya biyu cewar Rashad na cikin part ɗin. Cikin in-ina ammi tace "habeebe a.a.a...k.wai spy ..kk...eyy " ta faɗa cikin jan numfashi. Kallonta tareeƙ yayi cike da zargi,dan shikam harga Allah tun farko ita ya zarga dan yasan bakin nufin ta akan abun daya shafi Adeeb sarai. Amma ma kallon ammi take cike da tuhuma,karfa tuggu ta haɗawa Rashad Dan kawai tana son ganin bayanta? " Wai wannan wane irin wandone kika sa ?kusan minti nawa ina ƙoƙarin cirewa amma na kasa?wllh idan ma wani siddabarun kikayiwa wandon nan yaƙi fita,to zanyi abuna ahaka, dan ubanki yau ɗin nan nayi alƙawarin ,sai Adeeb yayi kwanan baƙin ciki "Rashad ya faɗa yana hankaɗa fattu kan wani ƙaton tebur dake ajiye gefen gado ,da alama an ajiyeshine ɗan ɗora kofuna ko abinci idan bukatar hakan ta taso. Aikuwa tana fadawa ta fada kan wani glass cup, nan da nan ya tarwatse gaba ɗaya ya sossoketa aƙirjinta da wuyanta.wani marayan ƙara fattu ta sanya ,wanda koshi Rashad baiji sautin ƙaranba, dan kuwa muryarta tayi mugun dashewa.ahankali idanunta ke lumshewa yana budewa,gaba ɗaya jini ya bata farar best ɗin dake jikinta.amma bako imani bare tausayi haka Rashad yake ƙoƙarin keta mata haddi, ba tare da ya cire koda wannan skin tite ɗin ba. Wata irin zabura Rashad yayi sakamakon ƙaran da fattu ta kwalla,wanda yayi daidai da ƙarar faduwar kofar dakin . ”RASHAD!!!!!!............" Aka kwallah kiran sunan Rashad Wanda saida Rashad ɗin ya buge kansa ajikin tebur ɗin nan tsabar razana da yayi da wannan kiran sunan nashi da akayi...... Hmmmmm masu karatu,nima tsabar tsoro bansan sanda wayar hannuna ta fadi kasa ba,mutara zuwa gobe idan na ɗauki wayar .fatana dai wayata bata fashe ba. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 55/56 _________________"RASHAAADDDD" Aka kwallah kiran sunan Rashad,Wanda saida ɗakin ya amsa.gaba dayan mutanen da suka shigo ɗakin saida suka tsorata ,saboda yadda amon Muryar ya fito da mugun ƙarfi da sauti mai firgitarwa. Ahankali fattu da ke neman macewa ta buɗe kunburarrun idanunta da gyar,ta saukesu akan fuskar hammanta, wata shashshekar kukace ta zo mata ,numfashinta na hawa da sauƙa ,da gyar ta daga hannunta tana mikawa Adeeb , Da wani irin mugun sauri Adeeb yayi kanta yana mika mata nashi hannu,saidai kafin ya ƙara so tuni hannun nata ya koma ƙasa sharaff!! Ahankali kuma idanunta suka kulle ,duk wata jijiya dake jikinta tasaki,ataƙaice dai fattu ta sume. Wani irin ƙara Adeeb ya kwalla mai matukar firgitarwa ,hayaƙi na fita ta bakinsa da hancinsa, hannun fattu ya kama ya riƙe cikin nashi tare da damkewa kamar zai balla hannun nata. Jikinsa gaba ɗaya rawa yake kamar ana kaɗa masa gangi,ɗago da kansa yayi afusace ya sauke idanunsa akan Rashad,Wanda tsabar tsoro ya kasa koda matsawa daga kan table ɗin gashi tsirara haihuwar uwarsa. Da sauri Rashad ya runtse idanunsa,numfashinsa na wani irin hawa da sauka kamar shima zai shide tsabar tsoron ganin yadda idanun Adeeb ya koma,ga wani irin bakin hayaƙi daya fara cika ɗakin, Wani ƙaran Adeeb ya sake kwalla,wanda yafi na farko sanya tsoro da razani,gaba ɗaya dakin yayi wani irin bakiƙirin ,baka ko ganin hannunka bare na kusa dakai. Su ammi da amma,nanny tareeƙ ,jakadiya,da Zulaihat wacce zuwan ta kenan,bangaren dan ta sami labari gurin yan s.i.d ɗinta.gaba daya tsoro ,firgici da tsantsar mamakin abinda ke faruwa yasa sun kasa koda motsine agurin ,bare suyi wani abu. Sun ƙanƙame juna jikinsu yana wani irin bari,nanny Banda sunan Allah ba abinda take ambata"innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, meye wannan ke shirin faruwa haka,tareeƙ kana ina bana ganin komai fa " nanny ta faɗa tana ƙanƙame tareek dake kusa da ita. Shi kansa tareeƙ jikinsa rawa yake ,sam ya kasa magana sai rungume mahaifiyarsa da yayi sosai ajikinsa. Ƙaran rashad ne ya karaɗe dakin ,cikin wani irin sauti na azaba,wanda kana jinsa kasan wanda ke wannan karan yana cikin azaba da halin ƙunci. Kuka kawai amma ta sanya ,dan tasan yau kam ɗan ta sai abinda hali yayi,shikenan yau abinda ake shukawa agidan ya dawo kansu. Ahankali ɗakin ya fara washewa daga tsantsar duhun da yayi ,kusan minti uku suna cikin halin tsoro da razani kafin ,suka fara ganin komai tar-tar . "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shine abinda Dukansu suka haɗa baki wajen faɗa,sakamakon ganin wani narkeken maciji mai girman gaske nannade da Rashad ,Wanda kallo ɗaya zakayiwa Rashad kasan cewa ba alamun numfashi atare dashi. Kallon kallo ake tsakanin mutanen dake cikin dakin,wanda suka shiga tashin hankali fiye dana farko,dan kuwa ba Adeeb aɗakin sai wannan narkeken macijin,wato dai Adeeb shine ya zama wannan macijin. Jikin nanny Banda rawa ba abinda yake ,haka ammi da amma,jakadiya da Zulaihat wacce tuni ta jiƙa jikinta da fitsari,tana tsaye ƙanƙame da amma wacce itama ta ƙanƙame Zulaihat ɗin. Sun kasa magana sai kallon ikon Allah suke. Macijin nan yana tsaye nannade da Rashad ya fasa kai yana wani irin huci da fesar da wani irin bakin abu daga bakinsa.juyi ya farayi da ƙarfi kafin ya maka rashad ajikin bango,ji kake timmmm!!Rashad ya baje akasan tyles,tuni jini ya fara zubowa daga kansa.hakan bai ishi macijin nan ba ya kara zuwa ya nannade Rashad tare da kara makashi jikin bango. Ihu suka farayi ganin macijin nan na ƙoƙarin tarwatsa kasusuwan Rashad. Da gudu jakadiya ta juya tayi waje tana ihu ,ta nufi part ɗin mai martaba,tana faɗuwa tana mikewa,gaba ɗaya bata cikin hayyacinta. Zulaihat ma silalewa tayi agun ba alamun numfashi atare da ita. "Wayyo jama'a ku taimaka min ,zai kashemin yarona,wayyo Allah na na shiga uku ku taimaka min"amma ta faɗa cikin ficewar hayyaci,dan tsabar tsoro gadan gadan take nufar cikin dakin gurin da Rashad ke kwance ayashe, aikuwa kafin ta ƙarasa kaiwa inda Rashad ke kwance, saijin wani abu tayi mai kama da bulala ya fyadeta a gadon bayanta,wani ihu amma ta kurma tare da faduwa sakamakon azabar raɗaɗin da taji gadon bayanta ya ɗauka.da rarrafe ta koma inda take tsaye. Jikinta na rawa . Ammi fa tsoro ya gama kasheta,dan ko tsayuwar kirki ta kasayi, sam batayi tsammanin haka abin yake ba,ashe dai da gaske mutum yana iya komawa wata halittar ta hanyar asiri?lallai yau taga abinda ya fi ƙarfinta , sam bata tsammaci abun haka yake ba, amma dole tayi wani abu dan gudun zargi.dan haka cikin bugawar zuciya da tsananin tsoro ta fara takawa zuwa gurin da Adeeb ke tsaye yana zagaya Rashad yana huci. "A...a.ddd..ee.e.bbb."ammi ta kira sunansa cikin tsinkewar numfashi, shikuwa baiko kalli inda take ba ,burinsa kawai yaga Rashad yayi motsi ya kara karairaya masa inda bai gama lalacewa ba. "Ka nutsu Adeeb ɗana,.n...i.cce ammin ...ka, ka ...ka...ji."ta faɗa tana matsawa cikin tsoro da firgici. Ai kuwa jin takunta da adeeb yayi ,afusace ya juyo tare da kai mata tsafka, cikin sa'a kuwa ya damketa,ihu ta farayi tana neman taimako,"wayyo Allah na taimako jama'a taimako"ammi ta faɗa lokacin da Adeeb ke nannaɗeta kamar buhun goro.saida yagama naɗeta sannan ya fasa kansa saitin fuskar ammi yana huci.tsabar firgici tuni ammi ta sume ,kura mata ido Adeeb yayi kafin ya fara dakinta ahankali ,ta faɗa kan gado. Gurin fattu ya koma tare da hawa gadon bayanta, nade ta yayi tare da mirgina ta ta juyo rigingine,kallon fuskarta yake wani irin farin Ruwa na zubowa daga idanunsa ,kwanciya yayi akan cikinta yayi lamo yana mai juya kansa ,tare da yin wani irin ƙara yana bude bakinsa. Al'amarin yayi matuƙar tsorata dukkan wadanda ke cikin dakin,dan nanny ma tuni ta sume ,amma ce kawai mai ƙarfin hali ,dan tana zaune riƙe da bayanta da tasha bulala. Tareeƙ kuwa hawayene ke zuba daga idanunsa.yana matukar tausayawa yallabai ɗin nasa. Ana cikin wannan halin ne,abie ya shigo dakin tare da waziri da manyan faɗa ,sai Shaikh lateef ,babban malamine dake koyar da ilimin addini sannan masani akan abinda ya shafi jinya da maganinta, ya ƙware sosai wajen magance abun daya shafi sihiri. Lokacin da jakadiya ta kaiwa abie labarin,shikuma suna tare da su waziri suna ɗan tattauna wata magana mai muhimmanci,shine suka garzayo gaba ɗayansu, ɗan ganin abinda ke faruwa. Ba ƙaramin kaɗuwa abie yayi ba,lokacin da ya wannan kumurcin macijin amatsayin Adeeb ɗinsa,hawaye ne kawai ke zuba cikin idanunsa, ya ƙurawa Adeeb ɗin ido.tunanni kawai yake ,waye wanda yayiwa adeeb wannan aika -aikar?me yatsarewa wanda yayi masa haka?ace yaro mai gata dan sarauta kamar Adeeb yana zama maciji?duk yadda Adeeb ya kasance mai tausayi da taimakon al'umma ,amma ashe wasu suna can suna shirya masa mugunta.lallai dole ya tsaya tsayin daka ,wajen bawa yaronsa abin sonsa kariya ta ko wacce siga.yasan ammi na ƙoƙarin wajen yiwa adeeb addu'a ,kuma tana sawa ayi masa kamar yadda take faɗa amma dole shima ya dage ta bangarensa. Abie ne ya kalli Shaikh lateef,cikin damuwa da zubar hawaye yace "Shaikh kaga Adeeb ga ,kaga halin da yake ciki,menene abinyi ?abie ya faɗa yana mai share kwalla. Shaikh lateef kuwa wanda tun shigowar su yake kallon Adeeb,kallo na tsinake,sai lokacin yayi ajiyar zuciya kana ya kalli abie,yace" ranka shi daɗe lallai Adeeb yana cikin tsaka mai wuya ,da tuggun maƙiya ,amma In Sha Allah komai yazo ƙarshe,yanzu dai ayi ƙoƙarin diban bayin Allah dake kwance dan akaisu ga likita,sannan sai musan abinda ya kamata muyi"Shaikh lateef ya faɗa yana mai kallon abie. Nan da nan kuwa aka kwashe su ammi da nanny,Zulaihat ,sai dai ko yaya akayi yunƙirin zuwa inda Rashad ke wance kamar gawa,take macijin nan zaiyo kan mutum afusace. Ganin haka ya sanya abie cikin ƙarfin hali ya tunkari Adeeb dake fagen fattu yana fasa kai,ya kasa ya tsare, Ahankali abie ke kallon Adeeb da idanuwansa masu fidda hawaye kafin yace"habeebee kayi hakuri adauke dan uwanda,dan asuba lafiyarsa, koma me yayi maka nine nan,zan ɗaukar maka mataki,bazan taɓa yarda da zalunci ba"Abie ya faɗa cikin sanyin murya yana kallon Adeeb. Huci kawai Adeeb keyi yana kallon Abie kafin ya maida kansa ga fattu yana kallonta,sannna ya ɗago kai ya kalli abie, Jinjina kai abie yayi cike da fahimtar Adeeb ɗin yace "na fahimta habeebee,dole zan ramawa yarinyar nan abinda rashad yayi mata,dan kasan ba'a zalumci amasarautata" abie ya faɗa yana mai ƙara sawa kusa da Adeeb ɗin ahankali ya sanya hannunsa yana shafa bayan Adeeb. Shikuwa Adeeb sai huci yake yana guri da wata iska mai matukar zafi.haka aka samu aka lulluɓawa Rashad Abu ajikinsa kafin kayi waje dashi, amma duk yadda akayi ƙoƙarin ɗauke fattu Adeeb ya hana ,dan hatta mai martaba ,da yayi yunƙurin daukar ta saida Adeeb ya kai masa tsafka.haka suna ji suna gani ba yadda suka iya,sai lulluɓe mata jiki da sukayi itama ,dan kuwa yaƙi barin jikinta ma. Shaikh lateef ne zaune gaban Adeeb yana karanto wasu addu'oi yana tofa masa,lokaci guda jikin Adeeb yayi laushi, gaba ɗaya baya ko kwakwkwaran motsi,sai huci da yake fiddawa ,ya dora kansa akan ruwan cikin fattu dake lulluɓe,jikinsa sai wani bakin hayaƙi ke fita. Ci gaba Shaikh lateef yayi da addu'ar sa yana tofawa Adeeb,yayin da su abie ke gefe guda suna kallon ikon , Allah,dan zuwa lokacin murƙususu kawai macijin nan keyi,kafin wannan hayaƙin ya turnuke dakin,baka iya ganin komai tsabar duhu. Su abie suma addu'a suka fara,lokacin da suka ga wanan hayaƙin,dan Shaikh lateef yace karsuji tsoron komai ,duk abinda zasu gani kawai suyi addu'a. Can kusan wucewar mintuna biyar suna ta addu'oi ,dakin ya fara haske yana washewa har ya gama washewa tar, kamar ba shine yayi wannan duhun ba. Adeeb ne durƙushe agaban wannan table ɗin da fattu ke kwance,kansa har lokacin yana kan cikin fattu. Hamdala Abie da su waziri sukayi,ganin Adeeb ya dawo asalin halittarsa, dan abie yayi matuƙar tsorata, kar ace ahaka Adeeb ɗin zai zauna. Ahankali Adeeb ke buɗe idanunsa ,da har zuwa lokacin basu gama komawa normal ba. Kanshi ya daga da gyar yana ɗan yatsine fuska tare da dafe kan,dan ciwo yake masa sosai. Sai kuma yayi saurin zabura ya mike tsaye "Hulwa" shine abinda ya faɗa cikin daga murya yana waige waige, " Habeebee ka nutsu kaji ga hulwar taka nan kusa da kai "abie ya faɗa yana mai mikewa shima tare da riko kafadun Adeeb. Sai lokacin Adeeb ya ga su abie aɗakin,kallon abie yayi kafin ya kalli inda abie ke nuna masa,zaro ido yayi ganin hulwarsa kwance kamar gawa,"Hulwa " Adeeb ya faɗa yana mai girgiza fattu,amma ina Hulwa tayi nisan zango. Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungumeta tare da fashewa da wani irin kuka mai tsanani ciwo da zafi.irin kukan da Adeeb keyi kaɗai zai fahimtar da kai yadda yake jin Hulwa da kuma ciwo acikin ransa. "Rashad ! Rashad !! Rashadddd!!!ka tabka babban kurkuren ƙoƙarin tabamin mata,kayi kurkure,idan Hulwa ta mutu"yayi shiru yana mai goge hawayen dake kwatanta cikin idanunsa,kafin ya ɗago idanunsa da suka yi wani irin mugun jaaa,ya kalli Abie sannan yaci gaba"wllh billahi,saina kashe Rashad ,idan har matata ma mutu sanadin sa"Adeeb ya faɗa cikin karfafa murya da nuna gaskiyar abinda yake fadi har cikin ransa. Kallonsa kowa keyi acikin ɗakin,dan kuwa sun zama speechless,matarsa yake ta kira,kodai yarinyar nan amatsayin matarsa take?ko kuma yana nufin ita zai aura? Shine abinda yake ta yawo cikin zukatan su Abie. "Ya kamata akai yarinyar asibiti yanzu,nikuma zanje gida domin yin bincike akan larurar prince ranka shi dade"cewar Shaikh lateef yana mai mikewa tare da shafa kan Adeeb,dan yana tausayawa yaron sosai. " Haka ne Shaikh bari akaita asibiti yanzun nan " cewar abie yana mai kallon Adeeb dake ƙankame da Hulwa kamar zai maidata cikinsa. Kafin su ankara tuni Adeeb ya sungumi fattu yayi hanyar barin dakin da ita." Habeebee kayi hakuri akai yarinyar asibiti,kaima fa ba cikakkiyar lafiya gareka ba" cewar abie kenan ,ganin Adeeb na ƙoƙarin ficewa daga ɗakin. " Ba wanda zai kara tabamin mata abie ,domin itaɗin mallakina ce mata tace ta Sunnah,hakkin kula da ita yana kaina,dan haka bana bukatar taimakon kowa,karka manta ,likitanci bangarenane" yana faɗin haka yayi waje da fattu rungume aƙirjinsa. Kai tsaye fart ɗinsa ya nufa da fattu ,yana zuwa ya shimfiɗeta akan lafiyayyen gadonsa, kallo yabi jikinta dashi,cikin wani irin zafi da ƙunar zuciya,gaba ɗaya glasses sun maƙale ajikinta ,jini duk ya bata mata jiki.hatta fuskarta baka ganewa. Gimbiya suhaimat ce tsaye tana bin Adeeb da kallon sabe da yarinya akafadunsa,haka kawai gabanta ke tsananin bugawa,so kawai take taga yarinyar, Ko menene ya sameta oho?ahankali ta juya taci gaba da tafi zuwa dakin ammi,dan su basu san abinda ke faruwa ba. Zuciyarta gaba ɗaya taki samun nutsuwa ,ba abinda take son gani sama da wannan yarinyar,gaskiya bazata iya jurewa ba dole taje taga yarinyar,sannan ta san meke damunta?me yasame haka gaba ɗaya jikinta jini... Masu karatu ku biyoni dan jin gimbiya suhaimat zata je ganin fattu ne ko yaya? Taku anty mammy Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment more typing [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 57/58 ________________Gimbiya suhaimat ta gama tsara cewa data huta zataje part ɗin Adeeb dan ganin yarinyar nan, Saidai shigarta part ɗin ammi da yanayin da taga ammin yasa ta saurin,ƙarasawa cikin dakin ,cikin damuwa take faɗin"ukktee meke damunki? Yana ganki akwance?gimbiya suhaimat ta faɗa tana kamo hannun ammi ,wanda ba'a daura mata ruwa ajikinsa ba. Ahankali ammi wacce tayi nisa cikin tunani ta buɗe idonta tana kallon gimbiya suhaimat,kafin ta sauke ajiyar zuciya tare da lumshe ido ta buɗe" ke dai bari suhaimat,yau naga abinda ban taba gani ba arayuwata,nan ta bata labarin abinda ya faru,saidai ta boye mata asalin labarin fattu,sai cewa tayi wata baiwa ce Rashad ɗin yayiwa fyade,dan ita atunanninta Rashad yayiwa fattu fyaɗen. Sosai gimbiya suhaimat ta tausayawa yarinyar,sannan tayi Allah wadai da halin Rashad,zuciyarta na tsananin bugawa ,har cikin ranta take jin tausayin yarinya.kuma tayi alwashin ,saitaje taga yarinyar nan kafin ta bar ƙasar. Rashad kuwa kai tsaye aka wuce dashi,lafiyayyen asibitin dake masarautar,emergency akayi dashi,cikin gaggawa likitoci suka duƙufa akansa dan ceto rayuwarsa. Dan da dama cikin likitocin , sunyi tunanin hatsari ya samu mai muni. Karon farko ruwa suka fara ɗauka masa,kafin suka fara bincikarsa,karayama kusan biyar ce ajikinsa, bayan munanan raunuka dake jikin sa,sannan since kansa ya bugu ,dole sai sunyi bincike akwakwalwarsa, dan tabbatar da lafiyarta. Amma kuka take sosai cike da tarin damuwa da baƙin ciki ,meyasa Rashad zaiyi mata haka?me yasa gaba ɗaya halayyar Rashad ta sauya ne?da ɗan ta mai hankaline da nutsuwa ,sannan yana bin maganarta,amma daga baya ya fandare ya zama gagararre,yanzu ga irin abinda ya jama kansa.karaya har biyar ajikin mutum.Nan dai taci kukanta ta ƙoshi,tana zaune gefen ɗan ta. Nanny ma ta farfaɗo ,hankalinta amatukar tashe ,tana zaune hawaye na zuba cikin idanunta,yayin da tareeƙ ke rarrashinta cikin kwantar da murya. "Kayya tareeƙ abinnan na magajin faɗa,ya isheni yaron nan tun yana ƙuruciya yake haɗuwa da tuggun maƙiya,har zuwa girmansa,yaushe ne zai sami salama shima,kadufa wai Adeeb ne ya zama wannan ƙaton macijin,wanda idan awani gurin ka ganshi,sai inda ƙarfi ka ya ƙare wajen ceto rayuwarka. Yanzu idan haka ta faru dashi awani gurin yunkurin kasheshi fa zasu yi"nanny ta ƙarasa cikin kuka tana fyace majina. Hannunta tareeƙ ya kara damƙewa cikin nashi,kafin yace " wai ummeee yaushe zasu sanar da gaskiyar da muka jima da sanine?yaushe zamu taimakawa yallaɓai mu haska masa hanya danya gane irin haɗari dake bibiyarsa arayuwa?na gaji da boye gaskiya ummeee kiyi wani abu"tareeƙ ya faɗa cikin damuwa. "Tareeƙ baka san masarautar ya take ba,idan baka iya kama ɓarawoba ,to shi zai kama ka,dole mubi komai asannu,akwai lokacin bayyana gaskiya kaji?kayi hakuri"nanny ta faɗa tana mai shafa kan ɗan nata. Yanzu ya jikin ɗiyata yake ?shikenan yanzu yaron nan ya lalata nata rayuwa?ya karbi budurcinta awulaƙance sannan tana cikin al'ada ?kai ban taba ganin fajiri irin Rashad ba,Allah ya saka miki ɗiyata"nanny ta faɗa cikin kuka sosai,tana tausayawa fattu. Tareeƙ ma runtse ido yayi zuciyarsa na masa zafi,dan kuwa yasan ahalin yanzu Adeeb yana can cikin bakin ciki da damuwa,saidai shikam yana ganin kamar Rashad ɗin bai sami damar yiwa fattu fyaɗen ba suka karaso, yana kuma fatan Allah yasa hasashensa yazama gaskiya. Akan gado Adeeb ya shimfida fattu,wacce ke kwance kamar gawa,bata ko motsi,gaba ɗaya jini ya wanke mata fuska,jikinta ko ina raunine ,dan kuwa ba ƙaramin azaba Rashad ya gana mata ba,lips ɗin ta sun bushe idanunta ya kumbura sosai. Runtse ido Adeeb yayi lokacin da idanunsa suka sauka kan wuyanta zuwa ƙirjinta ,fasassun kwalabe duk sun soketa, zama yayi abakin gadon,cikin wata irin karaya da zafin zuciya.ji yake kamar yaje ya kama Rashad yayi gutsin-gutsin dashi, Hannunta ya kama na dama ,ya riƙe cikin nashi,gam-gam .jikinsa sai rawa yake ,yama kasa aikata komai akanta.wai hulwarsace kwance agabansa kamar gawa. "Why Rashad ?why ?duk matan dake cikin fadar nan sai matata?me yasa zaka aikata haka agareni?Adeeb ya faɗa afili yana mai kaiwa bango naushi, ji yake kamar zuciyarsa zata kama da wuta. Da sauri ya mike tare da ɗauko first aid box ɗinsa, dan Adeeb cikakken likitane akan fannin lafiya yayi karatunsa . Farar vest ɗin fattu data yage kaɗan daga sama ya kama,wacce ta rine da jini, ya cire mata ahankali,nan da nan albarkatun ƙirjinta suka bayyana,cikin faduwar gaba Adeeb ya kawar da kansa ga barin kallonsu,zuciyarsa na ci gaba da bugawa. haka ma ya zare wannan dogon wando dake jikinta ya ajiye gefe,ya rage daga ita sai pant Wanda shima gaba ɗaya yayi stairs saboda yadda jini ya ɓalle mata ,tsabar yadda ta shiga ruɗu da razani. Hannun Adeeb karkarwa yake ya kasa aikata komai,dan haka cikin sauri ya janyo ƙaton bargonsa ya lulluɓe fattu dashi,iya saman ƙirjinta zuwa kanta ya bari abuɗe. Sosai ya tausayawa fattu lokacin da yake cire mata kwalaben nan,dan kuwa taji ciwo da yawa,ko yaya ya taba gurin da kwalbar take saita zabura kamar zata farfaɗo. Haka dai ya gama cire mata kwalaben nan,tas yayi mata dressing ɗin duk inda ya kamata, ya sami ruwan zafi da towel ya goge mata jikinta .sai dai kuma ba wani kayan da pant da kuma pad ɗin dazai canja mata. Dan haka rigarsa ya ɗauko fara ƙal ,doguwar ya zura mata, kafin ya dauko mata kayanta,dan kuwa yana tunanin ta dawo nan part ɗinsa da zama kenan. Ƙarin Ruwa ya sanya mata ,kafin ya nufi ƙofa, kai tsaye ya kulle ƙofar ya fita zuciyarsa kamar wuta haka yake jinsa,ya nufi part ɗin nanny. "Tareeƙ na roƙeka kada kace zaka sanar da magajin faɗa komai ahalin yanzu,dan kuwa bamu da kwararan hujjoji akan hakan ,ka bari nan da lokaci kankanin shida kansa zai gano komai,zamu nuna masa hanya ta yadda zai fahimci abubuwa da dama" nanny ta faɗa tana rike da hannun tareeeƙ. Umme wllh zuciyata zafi take,Aduk lokacin dana ga yallaɓai cikin wani halin,yana zagaye da maƙiya ,amma bai sani ba,shi yana zaune dasu zuciya ɗaya .... "Su waye maƙiyan nawa?sannan wace gaskiyar ce ake boyemin?" Suka tsinkayo Muryar Adeeb yana faɗin haka cikin sautin da ba wasa acikinsa. Da sauri suka juyo gaba ɗayansu, dan basu tsammanci ganin Adeeb ɗin awannan lokacin ba. "Magajin faɗa yaushe ka shigo?ya jikin naka?ina ɗiyata take ?"nanny ta faɗa cikin inda-inda da son n kawar da zancen. Ƙura mata ido Adeeb yayi cike da tuhuma ,gaba ɗaya ta daburce.da alama akwai abunda take boyewa ita da tareeƙ .kallonsa ya dawo dashi kan tareeƙ wanda kansa ke ƙasa ,shi yaji dadin jinsu da Adeeb yayi,fatansa ɗaya ayi komai yau akare. "Tareeƙ, what wrong me kuke ɓoyemin? Dama akwai Abinda zaka iya boyemin tareeƙ ?na dauke tamkar kanina da muka fito ciki daya,why tareeƙ?" Adeeb ya faɗa yana kallon tareeƙ. Kallon nanny tareeƙ yayi,yana jin ba dadi cikin ransa,dama yasan watarana hakan zata iya faruwa,shi baiga amfanin biye boyen ba , amma suna haɗa ido da nanny tayi saurin girgiza masa kai,alamun karya ce komai. "Tareeeƙ,am tolking to you me kuke hidden mini?kada kusa na fara zarginku fa,Please nanny,bayan ammina da abie, ku kadaine mutanen dana yarda dasu arayuwata,ku kaɗai ne waɗanda nake ganin bazasu taba cutar dani ba,karki karyamin zuciya nanny, Please me kuke ɓoyemin?" Adeeb ya faɗa cikin wata kalar murya mai cike da tsoron kar ace nanny da tareeƙ suma suna daga cikin maƙiyansa . "Ka kwantar da hankalinka magajin faɗa,wllh har abada bazamu taba cutar da rayuwarka ba,saidai mu bata kariya, amma kasani akwai mutanen da kake kallo matsayin maƙiyanka,saidai sam,ba haka abin yake ba. azahiri kake ganinsu matsayin maƙiya,amma abaɗini sune masoyanka na haƙika. Su kuma wadanda kake kallo matsayin masoya,suke son ganin bayanka, sune waɗanda suke cin dunduniyarka,Adeeb ka kula kazamo mai lura da mutanen da kake tare dasu " nanny ta faɗa tana mai riƙe da hannun Adeeb,fuskarta ɗauke da damuwa. Kallonta kawai Adeeb keyi,tunda ta fara maganarta ,me take nufi kenan?su waye ya yarda dasu ,kuma suke cin dunduniyarsa? Sannan suwaye yake wa kallon maƙiya ,alhalin sune masoyansa na asali?kallon nanny yayi cike da tarin tambayoyi zuciyarsa na harbawa da gudu. "Nanny ban fahimceki ba,me kike nufi da kalamanki? Please kiyimin bayanin da zan gane"Adeeb ya faɗa yana kallon nanny,idanunsa sun kada sunyi jajur dasu. Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe mai ƙarfin gaske,sannan tace magajin faɗa ,idan baka manta ba,shekaru kusan sha takwas mijina da kuma gimbiya nazli sunyi haɗari suka mutu,sanadiyyar wuta data kama motar da suke ciki,harda yaranta mata su biyu,nanny ta faɗa tana kallon Adeeb, Runtse ido Adeeb yayi da mugun ƙarfi,har abada bazai taba mantawa da wannan baƙar rana ba ,ranar data zamo mafi muni arayuwarsa. Bude idonsa yayi wanda suka cika da kwalla yana kallon nanny kafin cikin rawar murya yace " tabbas nanny bazan taɓa mantawa da wannan rana ba,domin itace rana mafi muni arayuwata" ya faɗa yana mai lumshe idanunsa hawaye suka ziraro sharrrt. "To kasani wannan haɗarin ba afkuwa yayi ba ,shiryashi akayi" nanny ta faɗa tana mai kallon Adeeb , Azabure Adeeb ya bude idanunsa,da suka gama zama jajur dasu,kallon nanny yake cikin kiɗima da ruɗewa" nanny kamar ya ban gane ba,me kike nufi da shiryashi akayi?waye ya shirya?kuma meye dalilin shiryawa?"Adeeb ya faɗa aruɗe. Kamo hannunsa nanny tayi ta zaunar dashi akan kujera dan kuwa gaba ɗaya jikin sa rawa yake. "Tareeƙ maza jeka kulle mana ƙofar nan"nanny ta faɗa cikin damuwa. Ahankali tareeƙ ya nufi ƙofar tare da kullewa, yana jin sanyi aransa,koba komai yau zasu sauke nauyin da yayi musu bake bake acikin zuciya. " Nanny kiyi saurin sanar dani, domin zuciyata gab,take da tarwatsewa,dan kaɗuwa" Adeeb ya faɗa cikin tsantsar zaƙuwa . Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace " ina son ka saurari maganata da kunnen basira ,sannan kayi min kyakykyawan fahimta,kasani bazan taɓa cutar da kaiba, kuma duk abinda nayi nayine don tsiratar da rayuwarka" nanny ta faɗa hannunta riƙe dana Adeeb. "Please nanny go street to the point kina kara sani cikin wasi-wasi" Adeeb ya faɗa cikin muryar damuwa ,jikinsa na rawa ,ba abinda yake son ji sai wanda ya shirya wanann haɗarin. Mikewa nanny tayi tare da zuwa jikin window ta tsaya ,kallon Adeeb take tare da karantar yanayinsa, kamar yadda shima yake kallonta cike da ƙosawa. Ahankali ta buɗe baki tace"ba kowa bane ya shirya wannan hadarin face .......... Wayyo masu karatu cajina ya kare ,amma karku damu mu tara anjima, Nice dai anty mammynku. Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 59/60 ________________Ahankali nanny ta ke kallon Adeeb,kafin ta sauke ajiyar zuciya,tunani take ta yadda Adeeb zai karbi wannan magana,ta yaya zata sanar dashi cewar,amminsa itace silar faruwar komai?shin zai amince da abinda zata faɗa masa ko yaya? Wane irin kallo zai musu idan yasan cewa amminsa ce ta kashe sarauniya Nazli da yaranta tare da baban tareeƙ,kuma abakinsu?anya kuwa basu barowa kansu aiki ba? "Nanny kiyi magana mana kinyi shiru, ki sanar dani wake da hannu akan hadarin nan?" Da sauri nanny ta dawo daga dogon tunanin data tafi,kallon tareeƙ tayi cike da karayar zuciya ,amma cikin ƙarfafa gwuiwa tareeƙ ya kalli nanny yana mai jinjina kai da nuna alamun ,kwantar da hankali. Ajiyar zuciya nanny ta sauƙe Tana mai kallon fuskar Adeeb,kafin ta fara magana. "Magajin fada kamar yadda na faɗa maka,wasu abubuwan muna kallonsu ne ba a yadda suke ba,ka sani abinda zan faɗa maka ba ƙarya ,ba kuma cutarwa.shiru ta ɗanyi tana jinjina maganar kafin taci gaba"ba kowa ya shirya wannan hadarin ba, face Amminka"nanny ta faɗa tana mai kure Adeeb da ido. Da wani irin slow Adeeb ya mike tsaye bakinsa bude,zuciyarsa na wani irin bugawa kamar guduma, ji yayi kunnensa ya ɗauki wani ƙara ƙuuuuuuuu!!! Sai yake jin maganar ta nanny Tana rarrabewa,kamar baiji me take faɗi daidai ba,jikinsa rawa ya kama,ta yadda yana mikewa tsayen yaji kamar zai fadi dan haka da sauri ya koma ya zauna,idanunsa ƙuri,akan fuskar nanny, Cikin in-ina ya ke cewa"na...nan.,...y mek....Ike ..son....f..a...ɗ..I n..ee." ya faɗa numfashinsa na rarrabewa,ji yake kamar zuciyarsa zata fito tsabar yadda take bugawa. Da sauri nanny ta ƙaraso kusa da Adeeb ta zauna ,cikin nutsuwa take shafa bayansa tare da kallon fuskarsa cikin tausayawa,dole yaji maganar tazo masa kamar saukar aradu."ka nutsu Adeeb domin Abinda nake faɗa maka yana buƙatar nutsuwa,tabbas Amminka itace ta shirya wannan hadari,tare da taimakon wani ma aikaci dake cikin gidan nan,mai kula da harkokin motocin gidan"nanny ta faɗa cikin sanyin murya tana jin zafin rashin mijinta da uwar dakinta kamar yau abin ya faru. Kallonta Adeeb yake cikin wani irin yanayi na mamaki ,al'ajabi,tsoro,ruɗu dakuma firgici,ji yake kamar zuciyarsa zata iya fashewa ako wane lokaci,wannan wane irin magana nanny keyi?anya kuwa tana cikin hayyacinta?yaushe nanny ta koma maƙiyarsa ta hanyar hade kai da amma?dan su shiga tsakaninsa da amminsa? Dan kuwa yana tabbatar da cewa wannan shirin amma ne,lallai duniya ba tabbas .cikin zuciyarsa yake wannan maganar,kafin a fili ya kalli nanny ,sannan ya kalli tareeƙ,sai kuma yayi murmushi wanda yafi kuka ciwo ,sannan ya miƙe tsaye yana mai sanya hannunsa cikin aljihu,sannan ya fara magana bayan ya juya bayansa yana kallon bango" ban taba tsammanin cewa matar data raineni tun ƙuruciya zata iya hade kai da makiyana,ɗan ganin sun shiga tsakanina da ammina ba ,yau na kara tabbatar da cewa lallai wanda kake kallonsa matsayin masoyi ,to shine makiyinka aboye, amma bantaba tsammanin haka daga gareki ba nanny;Adeeb ya faɗa cikin zazzafar murya yana mai juyowa ,idanunsa sun kada sunyi mugun jaa, kallo ɗaya zaka masa kasan cewa zuciyarsa akaraye take.ci gaba yayi da cewa"nanny why ?why nanny me yasa zaki canja daga yadda na sanki?me yasa zaki so ganina cikin damuwa?na dauke ki tamkar mahaifiyata,duk wani abinda ya dameni ina zuwa gareki dan samun mafita,ammina tana kula dake da duk wani bukatun ki,amma meyasa kika hada kai da maƙiyanta?me yasa kika saida kanki dan bata alaka tsakanin da da mahaifiya?nanny why?tareeƙ me yasa nanny zatayi min haka?Adeeb ya faɗa yana mai riƙe kafadun tareeƙ idanunsa na zubda kwalla ,gaba ɗaya jinsa yake kamar ba shiba, wani sashen na zuciyarsa yana son karbar maganar nanny,saidai sashe mafi rinjaye na zuciyarsa na tunatar dashi wacece ammi agareshi,dan me zai yarda da batun nanny?. Cikin damuwa da alhini tareeƙ ya kama hannun Adeeb ,cikin murya mai nuna tabbatarwa ,tareeƙ ke fadin, "yallaɓai ka kwantar da hankalinka,kuma kayiwa maganar nanny kyakykyawar fahimta,da sannu zaka gano gaskiyar dake cikin batunta, yallaɓai munsan abubuwa da dama wanda kai baka sansuba,amma da sannu zaka gane da kanka"tareeƙ ya faɗa cikin marairaita yana kallon Adeeb. Fizge hannunsa Adeeb yayi tare da dafe kansa da yake jinsa kamar zai tarwatse,kafin ya kalli tareeƙ yana mai jinjina kai"well na gane ,na gane tareeƙ kaima kana bin bayan mahaifiyarka ko?da kai aka hada baki,am disappointed tareeƙ" Adeeb ya faɗa yana girgiza kai cikin karayar zuciya,idanunsa na fitar da hawaye mai tsananin zafi da ƙuna.ahankali ya juya ya nufi ƙofa yana dafe kansa . Cikin damuwa da zubda kwalla nanny ta miƙe da sauri tana kiran Adeeb" magajin fada karkayi saurin yanke hukunci akan maganata kana bukatar nutsuwa da bincike dan Allah ka yarda dani ɗana, bazan taɓa cutar da kaiba."nanny ta fada cikin zubda hawaye . Ko waiwayowa Adeeb baiyi ba ya fice daga ɗakin ,cikin sauri, dan ko ganin fuskar nanny baya sonyi ahalin yanzu.zuciyarsa na tafarfasa ,ji yake kansa kamar zai kama da wuta.kai tsaye part ɗin ammi ya nufa ko zai sami salama cikin zuciyarsa. "Tareeƙ ka gani ko?kaga Abinda nake faɗa maka,Adeeb ya riga ya makance,baya ganin laifin ammi ko kaɗan,yanzu bansan wane kallo zai rinƙa yi mana ba"nanny ta fada cikin kuka. Kamata tareeƙ yayi ya zaunar da ita akan kujera ,hannunsa ya sanya yana share mata hawayen dake zuba daga idonta,kafin yace " ummee na,ki kwantar da hankalinki,dama shi aikin alheri haka yake,dole saika fuskanci ƙalubale,nasan yallaɓai zaiyi fushinsa na wani lokacin kafin ya sauko,kuma nasan daga yau zai fara bincike akan abinda kika sanar dashi,In Sha Allah muke da nasara ,tunda akan gaskiya muke"tareek ya faɗa cikin yanayin ƙarfafawa mahaifiyar sa gwuiwa. "In sha Allah tareeƙ ,Allah ya datar damu"nanny ta fada tana share hawayenta. Ameen yace ,kafin suka ci gaba da tattaunawa akan matsalar. Kai tsaye ya shiga part din na ammi,ko kula gaisauwar da hadimanta keyi baiyi ba,dan zuciyarsa ba abinda take sai tafarfasa,bai taɓa tsammanin haka daga su nanny ba,lallai mutum bashi da tabbas. Afalo ya ci karo da sarauniya suhaimat,tana zaune da yaranta,suna cin apple da ya'yan itaceya ,gefe guda kuma suna kallo. Da gudu su zayyad suka taso suka rungume Adeeb suna murnar ganinsa,kansu kawai ya shafa tare da rungumarsu,shima. Kallonsa sarauniya suhaimat keyi,dan kuwa taga tarin damuwa cikin idanunsa. "Sannu yarima ,ya jikin naka?dana yarinyar ?"sarauniya suhaimat ta fada cikin yanayi na nuna damuwa . Lumshe ido Adeeb yayi cikin damuwa da yanayinsa na rashin son magana yace "da sauƙi" atakaice . "Allah ya bata lafiya " ta fada da yanayi na damuwa. "Ameen" Adeeb ya faɗa ahankali. "Ammin naka tana ciki"sarauniya suhaimat ta fada cikin kulawa. Kai kawai Adeeb ya jinjina mata kafin ya wuce zuwa cikin dakin. " Bangane ba ?kamar ya nayi sakacin da kwalbar ta fashe,bayan irin kulawa da ita da nake?kasan irin kuɗin dana kashe akan akwatin da aka ƙera na sanya kwalbar ciki? Shiru tayi ,da alama tana sauraron abinda ake faɗane daga can bangaren. "Shikenan ,yanzu muna cikin alhini ne na wannan abun daya faru,dan haka kajira nan da kwana biyu,zan nemeka,dan awannan karon aiki nakeso ayimin na ban mamaki,bana kuma son asami matsala " ammi ta faɗa cikin wani yanayi mai nuna ta shirya mugunta mai zafi cikin ranta. Gaban Adeeb ne yayi wata irin faɗuwa da har saida ya dafe ƙirjinsa,wane akwati ammi ke magana akai?wace kwalbar ce ta fashe?da wa ammi ke waya?waɗan nan sune tambayoyin da Adeeb ke yiwa kansa,saidai bashi da amsar ko daya daga ciki. Ganin ammin ta gama wayar kuma tana ƙoƙarin juyowa ne ,dan ta ba ƙofa baya,yasa Adeeb saurin saita kansa yayi sallama tare da shiga. Da sauri aɗan razane ammi ta juyo tana kallon Adeeb ɗin,dan batayi tsammanin ganinsa yanzu ba, saidai da alama baiji me take faɗi ba,itafa wllh tsoronsa ma ta fara ji yanzu,amma saita maze ta saki murmushi,tare da miƙa masa hannu,alamun ya ƙaraso gareta. Ahankali Adeeb ke takawa har yaje bakin gadon ya zauna,dan jikinsa sam ba kwari,murmushin ƙarfin hali yayiwa ammi yana kallon fuskarta, "Habeebee ya jikinka? na tsorata sosai da yanayin dana ganka ɗazu"ammi ta faɗa tana mai janyo Adeeb zuwa jikinta. Sam yau Adeeb ji yayi baya wani jin dadin kwanciya akan cinyarta,Dan saiyajisa kamar akan ƙaya, dan haka da sauri ya tashi daga kwanciyar da yayi,kafin ya dan saki murmushi,yana mai cewa"ƙalau nake ammi,kada ki damu,ya naki jikin?"ya faɗa sam fuskarsa ba walwala. "Shafa kansa tayi kafin tace naji sauki dana karka damu"ta faɗa tana kallon fuskarsa ,dan kuwa sam ba haka yake mataba,yau kam ba wannan shaukin da yake nuna mata idan suna tare. Mikewa yayi yana mai faɗin ammi zanje in duba yarinyar can zan dawo anjima" yana faɗin haka yayi waje abinsa. "Yawwa yarima ,ina son in duba yarinyar nan "sarauniya suhaimat ta fada tana mikewa lokacin da Adeeb ya zo zai wuce. Shiru yayi yana ɗan nazari,akwai bukatar ta duba ta ,tunda likita ce itama ,kuma fannin mata ta karanta. Dan haka yace "ok muje ,tana part ɗina" Ficewa sukayi tare suka nufi part din Adeeb. Toh masu karatu ,mubi su Adeeb dan duba Hulwa. Sai mun hade next page. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing.m [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book page 61/62 ________________Ficewa sukayi daga part ɗin ammi zuwa na Adeeb, haka kawai gaban sarauniya Nazli ke faduwa,sam ta kasa gane kan wannan faɗuwar gaban nata,saidai kawai ta alaƙa ta hakan da tunanin halin da zata ga yarinyar data sanya tausayi ta cikin zuciyarta. Su zayyad ma biyo ta sukayi,dan sunce suma son gannin marar lafiyar ,kuma zasuyi wasa agurin uncle Adeeb ɗin. Suna zuwa Adeeb ya dannan lambobin securityn daya sanya lokacin da zai fice,nan take ƙofar ta bude suka shiga. "Tana cikin daki" Adeeb ya faɗa yana kallon sarauniya suhaimat wacce ke tsaye cikin faduwar gaba. Kallonsa tayi cikin tausayawa, tare da jinjina kai . sam zuciyarsa Adeeb da jikinsa basa masa daɗi, yana cikin matsananciyar damuwa ,abubuwa sunyi masa yawan da har yana rasa me Yakamata yayi. " Ku zauna anan maza kafin na fito kunji" ta faɗa tana shafa kan yaran nata,kafin tabi bayan Adeeb zuwa cikin dakin. Tana kwance kamar yadda ya barta,ruwan daya ɗaura mata ya kusan karewa. Jiki asanyaye sarauniya suhaimat ta karasa bakin gadon da fattu ke kwance .sosai bugun zuciyar sarauniya suhaimat ya tsananta. Zama tayi tare da ƙurawa fattu idanu,lokaci guda taji wata masifaffiyar kaunar yarinyar tana ratsa dukkan sannan jikinta,ji take kamar bata taɓa son abu makamancin yadda take jin son yarinyar na shiga lungu da sako na jikinta ba. Hannun fattu ta kamo tare da riƙewa gam-gam cikin nata,wani sanyi taji yana ratsata lokacin data kama hannun fattun,batare da saninta ba kawai ta rungume hannun fattu aƙirjinta ,tare da runtse idonta.wani irin shauƙi takeji yana shiga jikinta irin na ƙaunar dake tsakanin ɗa da uwa.haƙika takamu da matsananciyar kaunar yarinyar lokaci guda. Kallon fuskar fattu take bata ko ƙifta idanunta,Adeeb na tsaye agefe guda yana kallonta ,mamakin yadda yaga fuskarta ta nuna so da kaunar fattu yake,koda yake haka Allah ke al'amarinsa.ganin ta kasa cewa komai kawai tana rungume da hannun fattu ta kura mata ido yasa shi sauke ajiyar zuciya yana mai faɗin"anty lafiya kuwa naga kinyi shiru "ya faɗa yana mai kallon fuskar sarauniya suhaimat. Sai lokacin tadanyi firgigit ta ɗago kai tana kallon Adeeb,ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi kafin tace "wllh Prince haka kawai naji ina kaunar yarinyar har cikin raina ,sosai nake jin tausayinta, yanzu ka dan bamu guri inason na dubawa"ta fada ta na mai shafa kan fattu. Kallon fattu Adeeb yayi cike da tausayawa,zuciyarsa na masa wani irin ɗaci ,kafin ya sauke ajiyar zuciya kana yayi falo gurin su zayyad da yazeed. Sosai sarauniya suhaimat taji mugun daɗi lokacin data gane fattu period ma take,kuma babu alamun Rashad yayi mata wani abu,hamdala tayi ga Allah tana jin zuciyarta wasai, murmushi kwance kan fuskarta take kallon fattu,wacce ta fara dan motsi tana yamutsa fuska. Hannunta sarauniya suhaimat ta kara riƙewa da kyau tana mai faɗin"princess buɗe idonki ki ,kalleni kinji" tana faɗin haka tana ɗan buga kumatun fattu. Ahankali fattu ke buɗe idanunta da suka yi wani irin jaaaa kamar jini ya taru a cikinsu,har ta bude idon fess,tare da kafe silin da ido,bata ko ƙiftawa.da alama tana son tuno wani abune, shiru sarauniya suhaimat tayi tana bin idanun fattu da kallo. Kusan minti ɗaya fattu tana kallon silin ,kafin ta zabura tare da kwalla kara tana kokarin tashi,da sauri sarauniya suhaimat ta cire mata karin ruwan dan dama ya kare . "Wayyo Allah na ,wayyo hammana kazo ka ceceni,zai lalamin rayuwa,wayyo baffana,wayyo innata kizo ,dan Allah ka bari wllh niba yar iska bace karkamin bana so banaso wayyoooooo!!!" Abinda fattu ke faɗa kenan tana fizge -fizge ,dan gani take kamar lokacin Rashad ke ƙoƙarin yi mata fyade,janyota sarauniya suhaimat tayi da sauri ta rungumeta tsam-tsam ajikinta ,cikin mugun tausayinta,tana faɗin"ki nutsu princess ba kowa buɗe idonki ki gani,nice ba Rashad bane ya tafi kiyi shiru ya isa"abinda take faɗi kenan tana shafa kan fattu ,wacce ilahirin jikinta ke rawa ,ta rufe idanunta ƙam -ƙam taƙi budewa. Da hanzari Adeeb ya ƙaraso cikin dakinz su zayyad ma bishi sukayi da gudu ,jin ihu da fattu ta kwalla,har neman faduwa Adeeb yake tsabar sauri,yana zuwa ya zauna abakin gadon tare da kamo hannun fattu ,da sauri ta fizge hannunta tana mai sakin ƙara ,"ahhhhhh,wayyo ni kasakeni banaso ,wayyo hammana kana ina? wayyo Hamma kazo ka taimakeni" fattu ta faɗa tana kokarin zamewa daga jikin sarauniya suhaimat. Cike da damuwa Adeeb ya ƙara kamo hannunta ya rike cikin nashi ,duk yadda take ta ƙoƙarin kwace hannun nata,amma yaƙi saki, "Hulwa ki nutsu kinji ,nine hammanki,buɗe ido ki kalleni ,ba Rashad bane nine Hamma" Adeeb ya faɗa cikin sanyin murya yana mai shafa kan fattu. Jin muryarsa da fattu tayi yasata saurin buɗe kunburarrrun idantuna ,ta sauke akan fuskar Adeeb,ɗan kafeshi tayi da ido,gabanta na faɗuwa kamar zai fado kasa. "Nine ,hammanki ne Hulwa kalleni ki gani ,nine Hamma Adeeb " ya faɗa yana ɗan matso da fuskarsa saitin Tata. Ahankali tace "hammana" "Na'am Hulwa is me "Adeeb ya faɗa yana mika mata hannu. Da sauri ta fada ƙirjinsa tare da fashewa da wani irin kuka,mai matukar ban tausayi,kukane irin na wanda ke cikin tashin hankali kuma ya sami mai taimakonsa. "Hamma ina kaje ka barni?wannan mai kama da kai ɗinne yazo zaiyi min fyade,Hamma dan baki yarda shine yayi ta dukana,ya fasamin baki,ya bugamin kaina ajikin katanga,Hamma bana sonshi,bana son ganinsa ,dan Allah Hamma ka fitar dani daga gidan nan bana so"fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka muryarta har wani yankewa take kamar numfashinta zai dauke. Ƙamm ƙamm,Adeeb ya rungumeta ajikinsa,yana jin wani irin zafi akirjinsa, mugun tausayinta ne yake zaga dukkan wata kofa dake jikinsa,haushin kansa ma yake ji,wai me yasa ma ya tafi gurin taron ya barta anan?me yasa bai tafi tare da itaba? Ahankali yake shafa kanta,yana mai faɗin"am sorry Hulwa,kiyi haƙuri laifinane,dana tafi na barki,na miki alkawarin ba wanda zai sake ƙoda miki kallon banza ne bare hakan ta kara kasancewa,ki yafemin hulwata ,an sorry "ya faɗa yana kara ruƙunkumeta ajikinsa,wasu hawaye Masu zafi suna zirarowa daga idanunsa. Zuru su zayyad sukayi suna kallon fattu,dan yazeed ma tuni ya fara kuka ,dan shi yana da mugun tausayi. Sarauniya suhaimat na zaune ta kura musu ido,cikin tausayi take zubda kwalla itama,ji take kamar yarta akayiwa wannan zalumcin ,Allah Sarki Adeeb ya cika dan halak dan ga dukkan alamu yana kula da yarinyar nan,duk da kasancewarta ma aikaciya agidansu,kuma tabbas taga zallar kaunar yarinyar cikin idanun Adeeb. Sun jima cikin wannan yanayin,har saida Adeeb ya tabbatar Hulwa ta sami nutsuwa ta hanyar daidaiton da yaji bugun zuciyarta yayi,sannan ya rabata da jikinsa. "Sannu princess hulwar Adeeb"sarauniya suhaimat ta fada ,fuskarta ɗauke da murmushi. Sai lokacin fattu ta juya tana kallonta .rassa!rassa!!rassa!!! gaban fattu ya yanke ya fadi,ƙurrr ,ta kure sarauniya suhaimat da ido,lokaci guda taji ƙaunar matar na ratsata fiye da yadda tayi tunani,duk kunya irin ta fattu,da bata yarda kuyi ta haɗa ido da ita,amma yau kam ta kafe sarauniya suhaimat da ido bata ko ƙiftawa. Murmushi sarauniya suhaimat take sakarwa fattu,kafin tace" baki sanni ba ko? Ta fada cikin yanayi na murmushi. Kamar wata doluwa haka fattu ta daga kai idonta akan fuskar sarauniya suhaimat. "Daga yau nice innarki ,danaji kina faɗi kinji "ta faɗa tana mai shafa kan fattu. Ahankali fattu ta matsa kusa da ita tare da ɗora kanta akan cinyar sarauniya suhaimat tana mai faɗin "innata"ahankali tare da lumshe idonta. Kallonsu kawai Adeeb keyi,zuciyarsa na darsa masa abubuwa da dama,wannan wane irin shakuwace ta lokaci ɗaya?gaba ɗayansu sun kamu da kaunar juna daga haduwar farko,anya ba wani al'amarine mai ƙarfi atsakinsu ba ?. Hammmmm mudaije zuwa. "Sannu anty "zayyad ya faɗa cikin tausayawa. Ahankali fattu ta ɗago kai tana kallon yaran masu tsananin kama, Lokaci guda yaran suka shiga ranta. Masha Allah kyawawa dasu. Jinjina kai tayi tana kallonsu cike da kauna. "Maza kuje falo ko anty zatayi wanka" cewar suhaimat. Kama hannunsu Adeeb yayi suka fice zuwa falon. Saida Sarauniya suhaimat ta taimakawa fattu tayi wanka ta gyara mata jikinta sosai,ta bata abinci taci ta sha magunguna sannan ta kwanta barci .kafin ta bar ɗakin akan zata kara dawowa ta duba ta.har ta kai bakin ƙofa fattu ta ce"innata" da sauri sarauniya suhaimat ta juyo ,dan har cikin ranta taji sunan ya shigeta. "Zaki dawo "fattu ta faɗa tana kallonta . Jinjina kai tayi tana mai yiwa fattu murmushi tace "tabbas zan dawo ƴata"murmushi fattu tayi cikin karfin hali tare da rufe idanunta.ba ɓata lokaci barci yayi gaba da ita.dan kuwa harda maganin barci acikin wanda ta sha. Koda sarauniya suhaimat ta koma bangaren ammi,zaune ta tarar da ammin ta buga uban tagumi,duk sallamar da take sam ammin bata jiba,dan tayi nisa cikin duniyar tunani,saida ta tabata kafin ta san da zuwanta gurin. "Suhaimat ina kikaje ?na duba baki afalon? Ammi ta faɗa da kokarin kawar da samuwar dake kan fuskarta. Zama suhaimat tayi susa da ammi tace ,wllh yarinyar nan da abin nan ya faru da ita naje na gani,dan kuwa sosai lamarinta ya tsayamin araina ji nake kamar inada wata alaƙa da yarinyar" suhaimat ta fada tana mai lumshe idonta. Azabure ammi ta kalli sarauniya suhaimat tana mai dafe ƙirji"na shiga ukuna ,suhaimat gurin yarinyar kikaje?me kika gani?da wa kikaga tana miki kama?ammi ta faɗa cikin rudewa da tashin hankali,dan bata taba tsammanin suhaimat zataje gurin fattu ba. Kallon mamaki suhaimat ɗin ke bin ammi dashi ,kafin tace "uktee ,yanaga kin rude haka?daga jin cewar naje gurinta?kuma dawa kike tsammanin zanga tana kamar?ta fada cikin mamaki tana kallon ammi,da sai lokacin ta fahimci tayi baran -barama kuma tana son bada kanta. Cikin sauri ta saita kanta,kafin tace "ai nayi mamakin yadda kika damu da baiwane,har kikaje dan ganinta"ammi ta faɗa cikin basarwa. Murmushin suhaimat tayi kafin tace "wllh yadda nake jin yarinyar nan cikin raina ,ko su zayyad bana jinsu haka"ta faɗa cike da shauki akan fuskarta. Wani shegen kallon ammi ta jefa mata ,tana mai faɗin ,aikuwa saidai kiyi ta jin wannan shaukin cikin ranki,amma keda ƴarki har abada,bazan ƙara bari ki ganta ba,dan kuwa kashe shegiya zanyi kowa ya huta.ammi ta fada cikin ranta. Amma afili saitayi murmushi tana faɗin,"ke dai suhaimat kina nan da son jama'a har yanzu,sukuwa mutane ba abin yarda bane ,Gara ki kula" Jinjina kai suhaimat tayi kafin tace "ai idan har kana abu tsakaninka da Allah ,to tabbas Allah zai zama gatanka, kuma bazai taba ba maƙiya Sa'a akanka ba,kuma kinsan shi sharri dan aikene,idan ka cutar da wani to kana zaune zakaga sakayyar Allah"cewar sarauniya suhaimat kenan cikin murmushi take bayaninta. Kallonta ammi keyi,cike da sanyin jiki,sai take ganin kamar magana suhaimat ke faɗa mata afakaice,amma ai tasan suhaimat bata san komai game da halayyar ta ba ,bare tayi mata shagube.dan haka ta Badar da maganar sukaci gaba da hira. "Ranka ya dade ,hakika al'amarin Adeeb babban abune,wanda Allah shine kadai zai iya kareshi,domin kuwa sihirin da akaiwa yaron nan,badan ƙarfin addu'ar dake tare dashiba, to tabbas mutuwa zaiyi,domin kuwa sihirin anyi shine badan ya rayu ba,saidai akasheshi. Dan haka ba abinda zamuyi face addu'a domin Allah ya kareshi da duk wani mai nemansa da sharri" Shaikh lateef ya faɗa ,yana mai kallon mai martaba , Shiru abie yayi cike da tsantsar mamakin waye yayiwa ɗansa wannan aika aikar,kallon ƙaninsa waziri yayi cikin damuwa yace "ɗan uwana kanaji? Kana jin abinda Shaikh ke faɗi, me Adeeb ya tsarewa jama'a ?yaro mai hakuri,hankali da hangen nesa,ba ruwansa da kowa bai tsarewa kowa komai ba,amma ana neman ganin bayansa,Allah ka karemin ɗana ,ka raba shi da sharrin makiya,yanzu Shaikh menene abinyi. ?"abie ya faɗa cikin damuwa yana jin kamar ya zubda hawaye. Jinjina kai Shaikh lateef yayi yana Jan carbinsa dake maƙale adan yatsansa. "Ranka ya dade ba abinda zamuyi masa daya wuce addu'oi,sannan zan hada masa maganin karya sihiri wanda zai sha yayi wanka dashi,amma fa kasancewar samutum akoda yaushe abune mai matukar wahala,dan kuwa Aduk lokacin da ya shiga yanayi na ɓacin rai mai tsanani to tabbas akwai yuwuwar komawarsa macijin " Shaikh ya faɗa yana mai kallon abie. Wazirine ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Shaikh cikin damuwa kafin yace "yanzu ba wata hanya da Ya kamata abi,Dan arabashi da wannan iftila'in?ta yaya za'ace mutum yana komawa wata halittar? Shaikh aduba dai "waziri ya faɗa yana kallon Shaikh. Murmushi Shaikh yayi yana mai girgiza kai,kafin yace ,tabbas da 'ace akwai hanyar da zanbi dan ganin na raba yaron nan da wannan al'amarin ,to danabi ,kamar yadda na faɗa muku, anyi amfani da mugayen aljanu waɗanda suka samo macizan da ba irinsu afadin duniyar nan,kafin aka hada lakanin da akayi masa sihirin dashi, dan haka addu'a itace kadai mafitarmu" Ajiyar zuciya abie ya sauke ,zuciyarsa kamar zata fashe tsabar damuwa da ɓacin rai,sosai yake jin tausayin Adeeb,waye wanda ke son ganin bayan Adeeb? Me ya tsarewa mutane haka? Dole ya tsaya sosai ya kula da rayuwar dansa ,ta hanyar bashi kariya ta kowace sigar. "Shikenan Shaikh Allah ya shige mana gaba ,ya bamu Sa'a akan abinda muke nema"cewar abie yana mai lumshe idonsa lokaci guda damuwarsa ta baya ta dawo masa ,yana tuna abinda ya faru shekarun baya,sam baya son abu makamancin abinda ya faru a baya ya sake faruwa. "Yanzu ranka shi dade,ina son aturomin yarima zuwa anjima dan akwai abubuwan da zamu tattauna dashi"Shaikh lateef ya faɗa yana mai mikewa dan barin dakin. Bayan fitarsa waziri ya kalli abie wanda yayi shiru fuskarsa gaba ɗaya ta sauya ,ta koma kalar damuwa sosai, "Ranka ya dade ka kwantar da hankalinka,In Sha Allahu komai yazo ƙarshe,ba abinda zai sake samun yarima"waziri ya faɗa cikin kwantar da murya aƙokarinsa na kwantarwa da abie hankali. "Allah yasa waziri,amma abin yana damuna ,kasan yadda nake son Adeeb ,bana son abinda zai tabashi komai ƙanƙantarsa,domin shine magajina" "Ba komai ranka ya dade mubar komai hannun allah."cewar waziri. Jinjina kai abie yayi kafin yace ,sai kuma wannan matsalar ta Rashad,Dole in ɗauki mataki mai ƙarfi akansa,jira nake kawai ya sami lafiya" "Haka ne yaya dole ahukunta Rashad ,Dan yana don bata mana suna" cewar waziri cikin damuwa.nan dai sukaci gaba da tattaunawa akan matsalar. Rashad yana nan har yanzu kwance kamar gawa ,ko motsi bayayi, gaba ɗaya kamanninsa sun sauya ,abin tausayi,kullum amma cikin kuka take tana tausayawa halin da ɗan nata ke ciki, Gimbiya Zulaihat ma tun daga wannan ranar bata kuma ganin Adeeb ba,dan tsoronsa take ji sosai,amma har lokacin tana nan akan bakanta na son aurensa. Adeeb kuwa yana dakin da fattu ke kwance tana barci,kallonta yake cike da tausayi,gefe guda kuma wayar da ammi tayi gaba ɗaya ta tsaye masa arai,ga maganar da nanny ta fada masa,shi gaba ɗaya ma ya shiga ruɗu baisan me Yakamata yayi ba,yanzu gurin wa zai je neman shawara?waye zai sanarwa da damuwarsa?yanzu tsoron mutanen fadar nan yake ,dan kuwa cike take da mutane marasa amana da gaskiya. Ahankali ya shafa gefen fuskar fattu tare da sumbatar goshin ta kafin ya mike tare da ficewa daga ɗakin. Kai tsaye amma ta fito daga part ɗin Rashad bayan ta gama kukanta ta koshi,tunani tayi kan cewar ya kamata akawo karshen wannan al'amarin dake dukunkune cikin fadar nan,dan haka tana da bukatar magana da nanny Dole taje tayi magana da ita yanzu . Dan haka can ta nufa ,cikin sa'a ta tarar da nanny zaune afalo, kallo ɗaya zakayi mata kasan tana cikin damuwa da alhini.tana ganin amma ta mike tana mata maraba cikin girmamawa. Zama amma tayi tare da kallon nanny tace"zauna nanny inason muyi magana dake . "ta fada tana mai kallon nanny ,wacce itama kallonta take.zama nanny tayi jikinta asanyaye kafin tace "wace magana kike son yi dani ranki ya dade?inaga da kin aiko ankirani nazo gurinki dan gudun zargi ,idan aka ganki anan"nanny ta fada cikin damuwa. "Ajiyar zuciya amma tayi kafin tace ,ya kamata mu daina boye-boye nanny akan abinda muka san menene gaskiyarsa,ki duba halin da ɗana yake ciki ?kuma duk akan wannan makirar matar ,nasan cewa kome ya faru shirinta ne,meyasa zamu zauna mu zuba mata ido tana aikata abinda taga dama?dan haka dole mu kawo ƙarshen zalunci ta"amma ta faɗa cikin ɓacin rai da damuwa. Ajiyar zuciya nanny ta sauke mai ƙarfi kafin tace "ranki ya dade wannan abun fa abune mai matukar hadari ,dakuma tarin ƙalubale,domin nayiwa magajin fada maganar hadarin sarauniya Nazli, na sanar dashi wanda ke da hannu akan hadarin, amma sam bai yarda dani ba yayi fushi mai tsanani.tunda ya fita bai sake dawowa ba.dan haka ina ganin mudan jinkirta zuwa wani lokaci,har wannan abinda ya faru yayi sanyi" Jinjina kai amma tayi cike da gamsu,tace "wannan gaskiya ne ,dan kuwa nasan mai martaba ma jira yake Rashad ya farfaɗo ,kafin ya yanke hukunci akan abinda ya aikata .Allah shine kawai zai fitar damu " ta fada kwalla na cika idonta. "Kiyi haƙuri ranki ya dade ,komai yayi farko, yana da karshe ina sha Allah muke da nasara"cewar nanny cike da damuwa akan fuskarta. "Shikenan nanny Bari na koma can gurin Rashad din"Amma ta faɗa tana mikewa. Biyota nanny tayi tana mata sallama ,har farfajiyar gidan suka fito nanny na kara kwantarwa da amma hankali. Daidai lokacin kuma Adeeb ya fito daga part ɗinsa ,idonsa ne ya sauka akan nanny tsaye tare da amma. Kallonsu yayi cike da tsantsar mamaki,da kara tabbatar da zarginsa akansu. Suma kallonsa suke cikin yanayi na damuwa da rashin jin dadin ganinsu da yayi . Tafiya amma tayi daga gurin ,ganin irin kallon da Adeeb ke mata. Nanny kuwa jikinta ne yayi sanyi sosai.da hanzari ta nufi gurin da Adeeb ke tsaye........ Hmmmmm masu karatu muhaɗe next page . Takuce anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 63/64 _______________Jikin nanny ne yayi sanyi sosai,ganin Adeeb atsaye,kuma ya gansu tare da amma,tasan yanzu kam kome zata faɗa masa ,bazai taba yarda da ita ba.ahankali take takawa zuwa gareshi,gaba ɗaya jikinta ba kwari, Shikuwa Adeeb yana tsaye ya kafeta da Mayun idanunsa ,masu sanya mutum yaji shi cikin tsoro da fargaba. Nanny Tana karasowa tace "magajin fada ,fushi kake dani ko"? Ta fada cikin sanyi murya da mutuwar jiki. Lumshe ido Adeeb yayi ,zuciyarsa na masa zafi yana mamakin abinda nanny tayi masa,ace wai nanny ta hada kai da maƙiyarsa tana tayata ƙoƙarin cutar dashi,matar daya ɗauka matsayin uwa ?mutum kenan. "Ko kaɗan nanny bana fushi dake,kawai ina godiya ga Allah ne ,daya nunamin gaskiya ,na gane irin mutanen da nake tare dasu,na daukeki tamkar mahaifiyata nanny,Amma bansan nayi babban kuskuren yin hakan ba,dan Allah kiyi haƙuri"ya faɗa yana mai haɗe hannayensa guri ɗaya alamun neman afuwa. Sosai nanny kejin ciwo cikin ranta ,damuwa da taraddadi sun cika mata zuciya,dama tayi wannan tunanin,tasan idan har Adeeb ya gansu tare da amma ,to shikenan,kuma kome zata faɗa masa bazai yarda da ita ba,amma Allah shine shaida bata da nufin cutar da Adeeb ko kaɗan. "Magajin fada wllh abinda kake zargi ba haka bane ,kada ganina tare da amma yasa maka kokwanto akaina, wllh nima Ina jinka tamkar tareeƙ bazan taɓa cutar dakaiba magajin fada. Nanny ta faɗa cike da damuwa aranta. Girgiza kai kawai Adeeb yayi tare da barin gurin,zuciyarsa kamar zata fashe tsabar damuwa . Kallonsa kawai nanny keyi,tana fatan Allah yasa ya gane gaskiya cikin sauri kafin komai ya daɗa lalacewa. Ba kowa cikin falon ammi,sai ƙamshi dake tashi ta ko'ina ,dan ammi akwai son kamshi,kai tsaye ya nufi dakin kwananta, nocking yayi amma shiru,hakan yasa shi shiga cikin dakin kai tsaye.saidai nan ma ba kowa cikin dakin. Harya juya zai fice ,sai kuma zuciyarsa ta raya masa ya duba wanann akwatin da yaji ammi na magana akanta. Dan haka juyowa yayi yana karewa dakin kallo. Ahankali yake duba dakin dan neman wannan akwatin,amma yayi iyakar dubansa bai ganta ba. Harya hakura sai kuma ya hango wata akwati mai kyau da ɗaukar ido,yasan akwatin Dan acikinta ammi ke ajiye kwalakwalanta ,dan haka sai yayi tunanin ba komai cikinta, har ya juya da nufin barin dakin,sai kuma zuciyarsa ta kwadaitu da son duba akwatin . Dan haka ahankali ya zauna tare da ɗauko akwatin, danna lanbobin bude akwatin yayi,dan kuwa tuni yasansu, aikuwa saiga akwati ta bude,gwalagwalai ne acikinta iya ganin ka ,masu kyau da ɗaukar hankali,kallo ɗaya zaka musu kasan an zubar da maƙudan kudade wajen mallakar sarkokin. Dubawa yayi tayi amma baiga komai aciki ba,sai wani dan karamin akwati mai kyau da ya gani,kallon akwatin yake da mamakin meye acikinsa aka wareshi ?lallai yana son ganin abinda ke ciki.dan haka hannu Ya mika tare da ɗauko akwatin ya bude. Mamaki ,al'ajabi ruɗu da kuma faduwar gaba sune suka ziyarci zuciyar Adeeb,sakamakon ganin sarƙar nan ta Hulwa data bace ,cikin wannan akwatin, Me yakawo sarkar Hulwa cikin kayan ammi?har akayi mata adana ta musamman?me hakan ke nufi,shidai yasan ammi tana da sarkokin da suka ninka kudin wannan bare yayi tunanin ta daukene dan bata da mai tsada kamar wannan ,to me hakan ke nufi kenan?innalillahi meke faruwa ne acikin gidan nan?kodai akwai Abinda ammin nashi ke kullawa da gaske ? Wayyo ina zaisa kansa ?dawa ya kamata ya yarda ne cikin fadar nan? Dauko sarƙar yayi cikin sauri ya maida komai inda yake sannan yayi saurin barin dakin na ammi ya koma part dinsa. Zuciyarsa na zafi kamar zata kama da wuta . Lokacin daya koma part din nasa fattu ta farka,tana zaune tana kuka,tsoro takeji,har lokacin barin ma dataga ita kadaice cikin dakin,ina Hamma ya tafi ya barta?karfa wannan Rashad din ya dawo mata? Gashi wannan innar ma bata dawo ba,wannan tunanin yasata ƙanƙame jikinta tana kuka. Adeeb kuwa cikin wani irin yanayi na sarewar zuciya ya shigo cikin dakin,abubuwa sunyi masa yawa cikin zuciyarsa,jinsa yake kamar bashiba, kansa banda ciwo ba abinda yake ,wai meke shirin faruwa da rayuwarsa ne ?me hakan ke nufi ?me amminsa ke nufi da ɗauke sarƙar Hulwa? Kukan hulwar da yaji Yone yasani saurin ƙarasawa cikin dakin. Tana jin motsi sa ta zabura atsorace tana mai kallon ƙofar dakin.ganin Adeeb ne ya shigo yasata saurin yunkurawa ta mike da gyar tana kuka tare da kallonsa. Da saurinsa ya ƙaraso inda take ,yana zuwa ya kamo hannunta tare da shafa gefen fuskarta yace "menene kike kuka?inane yake miki ciwo ?ya faɗa cikin mugun sanyin murya ,wanda har saida fattu ta ɗago kanta ta kalleshi, Idanunsa sunyi jajur sosai jijiyoyin kansa sun fito rudurudu,fuskarsa tayi jajur ,kana gani kasan yana cikin damuwa da tashin hankali. Cikin kuka fattu ta faɗa ƙirjinsa ta rungumeshi, tana faɗin "tsoro nakeji Hamma ,ko ina ganin ƙaninka nake yana min gizo Hamma" ta fada cikin kuka tana ƙanƙame Adeeb. Cike da tarin damuwar da baisan menene mafitarta ba shima ya ƙanƙame fattun ajikinsa yana mai lumshe ido da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi, Ahankali yake faɗin"kiyi haƙuri Hulwa , dagani harke muna cikin damuwa, Hulwa komai bayamin dadi na kasa gane dawa ya kamata in amince cikin fadar nan,Hulwa kowa na fadar nan so yake yaga bayana bansan me na tsare musu ba" Adeeb ya faɗa cikin murya mai tattare da karaya da sarewa. Shiru fattu tayi tana sauraron abinda yake fadi,ita fa sam bata fahimci inda zancen sa ya nufa ba,ahankali tace "Hamma ,su waye ke son kamin bayanka"? "Shiru yayi yana mai kara rungume fattu ajikinsa,dan sosai yake jin nutsuwa na samunsa sakamakon rungumeta da yayi,zuciyarsa tana yi masa sanyi .shafa gashin kanta kawai yake bai ce komai ba. Kusan minti biyar suna rungume da juna ,kafin Adeeb yayi karfin halin zareta daga jikinsa ya zaunar da ita abakin gado,kallonta yake ,har zuwa lokacin idanunta basu koma yadda suke ba,akwai kumburi da kuma dan jaa kadan acikinsu. Hannunta ya kamo cikin nashi ya rike gam-gam yana kallonta.ji yake kamar ita kadai ta rage masa wacce zai fadawa damuwarsa,saidai fattu yarinyace,idan ma ya faɗa mata damuwarsa bazata fahimci me yake nufiba. Kallonsa fattu tayi itama,tabbas akwai Abinda ke damun hamman nata,ko menene oho."Hamma meke danunka?baka da lafiya ne ?ta fada cikin muryar marasa lafiya ,wadanda suka sha kuka. Ahankali ya koma kusa da ita ya zauna ,kallonta yayi yace "Hulwa abinda ke damuna yana da yawa,ina cikin wata sarkakiya wacce Allah ne kawai zai fitar dani,bani da wanda zan fadawa damuwata ahalin yanzu,bana son sanar da abie na komai,dan gudun ɓacin ransa,saboda tsoron kar ciwonsa ya tashi,kiyi ta min addu'a kinji hulwatee" Adeeb ya faɗa yana mai riƙe habar fattu tare da zuba mata gajiyayyun idanunsa. Cike da tausayawa fattu ke kallon Adeeb,kafin itama ta sanya hannunta akan fuskarsa tana shafa gefen fuskar tashi, kamar yadda yake mata .sannan tace "Hamma zanyi ta maka addu'a Allah ya yaye maka damuwarka, kuma kaima kayi ta addu'a Allah maji rokon bawansa ne ,Allah ya bawa abie lafiya Hamma,amma me zai hana ka sanar da innarka itama ta tayaka addu'a" fattu ta faɗa bayan ta cire hannunta daga kan fuskar Adeeb. Wata sassanyar ajiyar zuciya Adeeb ya sauke lokacin da fattu ke shafa gefen fuskarsa ,ahankali ya lumshe idanunsa yana jin wani irin sanyi yana Ratsa zuciyarsa. Ahankali ya bude idonsa lokacin da yaji ta cire hannunta daga kan fuskarsa.kafin yace "Hulwa ammina tana daga cikin mutanen da nake son boyewa damuwata ,ahalin yanzu bazan iya sanar da ita komai daya danganci lamarinaba,ke dai kiyi ta min addu'a kinji"ya faɗa cikin murya mai cike da ban tausayi. Sosai fattu kejin tausayin hamman nata yana Ratsa zuciyarta.ahankali ta ɗora kanta gafen kafadunsa tare da rungumoshi ta gefe.tayi shiru cike da tunanin meke damun hamman nata. Ahankali shima ya dora kansa akan nata kan yana jinsa tamkar marayan da bai da kowa. "Hamma wannan innar bazata dawo ba ko?" Ta fada ahankali idanunta alumshe. Shima idonsa alumshe yake yana shafa kan fattu ,yace "kina so ganinta ne? "Daga kai tayi alamun eh sannan tace " eh Hamma ina son ganinta ,ina kaunar ta har cikin raina ,kuma tace daga yau itace inna ta" Ajiyar zuciya Adeeb yayi kafin yace " Hulwa ita kadai kike kauna ? Ni baki kaunata?ya faɗa ba tare da yasan ya fadi hakan ba .saida ya faɗa sannan ya fahimce me yace . "A'a Hamma ina ƙaunarka sosai mana,ina sonka,kaidin kamar baffana kake ,bani da kowa saikai, Hamma bana son wani abu ya tab aka ma" ta fada tana ɗago kai tare da kallon Adeeb. Cikin wani irin farin ciki da jin dadi Adeeb ke kallon fattu,zuciyarsa cike da jin dadi yace "da gaske kike Hulwa?" Ya faɗa cikin murmushi yana kallonta. Jinjina kai tayi itama cikin murmushi tana kallonsa. Ahankali ya janyota jikinsa ya rungumeta gamm yana mai lumshe ido , sosai yake jin wani irin. Daɗi da Nutsuwa cikin zuciyarsa. "Kina son ɓata min shiri ko ?,kisani wllh idan kikayi wani kuskuren dana rasa damata,kema zaki karbi naki hukuncin ,kin sanni kinsan halina,kuma kinsan abinda zan iya aikatawa ,dan haka ki kula da kanki,komai yana ƙoƙarin lalacewa saboda sakacinki,to bazan laminci wannan abinda kike yiba.wllh zan aikaki gurin da duk wanda zai zamenin matsala nake aikawa.akan wannan karagar zan iya batar da kowa" Wani mutum ne daya lulluɓe ilahirin fuskarsa ke fadin wannan maganar cikin ɓacin rai yana kallon ammi,wacce ke tsaye cikin tsantsar tsoro ,jikinta sai rawa yake cikin tashin hankali tace "dan Allah kayi hakuri ,wllh ina yin iyakar ƙoƙarina akan wannan abun ,kuma aKwai shirin da nake yi ,karka damu ka kara hakuri "ta fada cikin rawar murya,tana kallon mutumin da baka ganin komai bace kwayar idanunsa. Cikin fushi mutumin ya damƙi wuyan ammi ya hadata da jikin bango yana faɗin"bana son jin komai daga bakin ki kawai ki aikata abinda nace miki ,ki tabbatar ya bar duniyar nan nanda lokaci kankani,zan kawo miki abinda zaki saka mishi acikin abinci,zai mutu kuma ba wanda zai zargi wani abu,idan kuma aka samu kuskure .yayi shiru tare da sakin wuyan ammi wacce ke kakari tana kokarin shekawa. Tari sosai ammi keyi,lokacin da mutumin ya saki wuyanta sannan yayi tafiyarsa cikin sauri yana ƙara gyara rufin fuskarsa. Saida ammi ta samu nutsuwa kafin ta bar gurin ,kai tsaye dakinta ta nufa ,gaba ɗaya awahale take, Bakin gado ta zauna cike da damuwa tana tunani,can dai ta dauko akwatin sarkokinta,abin yayi matuƙar tsorata ta lokacin datayi arba da akwatin sarƙar fattu ba komai acikinta. Wani dan gajeren ihu ta kwalla cikin tashin hankali,tana dube dube cikin akwatin ,waye ya daukemin sarƙar nan?na shiga ukuna wayyo ni ammi .da sauri suhaimat ta shigo dakin ammi ,dan kuwa taji ihun da ammin ta kwalla."uktee lafiya ?naji kina ihu?suhaimat ta fada cikin damuwa tana rike ammi. "Ba komai suhaimat na Dan bugene "ammi ta fada cikin tashin hankali. Kallonta suhaimat keyi cikin rashin yarda da abinda ya fada,amma koma dai menene tunda taki faɗa shikenan . "To mukam muna ta shiri anjima jirginmu zai tashi .zanje in Kara duba yarinyar can "suhaimat ta fada tana kallon ammi. "Karkije suhaimat ,karkije,na roƙeki,ki rufamin asiri karkije "ammi ta fada cikin tashin hankali tana kama hannun suhaimat.dan tana tsoron kar ace sarƙar ta koma gurin fattu ne kuma suhaimat ta gani ta gane yarta. Cike da mamaki suhaimat ke kallon ammi,anya kuwa kalau take?ji yadda ta wani rikice daga cewa zani ganin yarinyar can. Kai gaskiya akwai wani abu aƙasa. Cikin hade fuska suhaimat tace "uktee ki fadamin menene dalilinki da baki son na haɗu da yarinyar can?me kike kullawa akanta ?menene hajjarki ? suhaimat ta fada cikin haɗe rai tana kure ammi da ido. Zato ido ammi tayi tana kallon suhaimat ,kafin cikin in Ina ta fara magana "su...haim..at ...... Hmmmmm muje zuwa masu karatu. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 65/66 ________________"Ki sanar dani dalilin da yasa baki son zuwana gurin yarinyar nan? Me alaƙarki da ita ?ko ince me ta tsaremiki uktee? Sarauniya suhaimat ta fada cikin haɗe fuska ,dan tasan kadan daga aikin ammi ta hanata zuwa gurin fattu. Zaro ido ammi tayi tana mai kallon suhaimat ,dan sai lokacin ta fahimci tana kokarin bada kanta,cikin in-ina ta fara magana "su...hai..mat,wane dalilin ne zaisa kuwa in hanaki zuwa gurinta?kawai ina gudun ace ko wata munaƙisar muka ƙulla yasa kike ta zarya,kinsan tunda wannan abun ya faru to komai ma laifi zai zama , amma bayan wannan bani da wani dalili"ammi ta fada tana kafe suhaimat da idanu. Murmushi suhaimat tayi ,kafin tace "Indai dan wannan ne karki damu ,ai kowa yasan Ni likitar matace,kuma ba laifi bane idan naje duba marar lafiya,kuma ma mace"suhaimat ta fada cikin yanayi na rashin damuwa.kafin ta juya ta bar ɗakin. Harara ammi ta biya da ita ,kamar idanunta zasu fado ,haushin suhaimat takeji fiye da tunanin mai tunani,wllh badan tana tsoron faruwar wani abu ba ,data gama da suhaimat ,dan itace silar shigar ta ko wace irin damuwa.amma ba komai muje zuwa sannu sannu bata hana zuwa,saidai dade ba'ajeba. koda sarauniya suhaimat ta koma bangaren Adeeb, kwance ta tarar da fattu adaki, idanunta alumshe kamar mai barci,yayinda Adeeb ke falo yana amsa waya. Bayan sun gaisa yake sanar da ita fattun tana cikin daki, dan sosai yake jin dadin yadda take kula masa da fattu. Tana shiga fattu ta buɗe idonta,da sauri sakamakon jin muryarta,dan dama tana kwancen nan, tunaninta Sarauniya suhaimat kawai take. Da murna ta tashi zaune tana murmushi,tare da kallon suhaimat, Itama cikin farin ciki ta karasa gareta ta zauna. Ahankali fattu tace "inna nayi tunanin bazaki dawoba,ina ta tunaninki araina"ta fada fuskarta ɗauke da annuri. Shafa fuskar fattu tayi kafin tace "ƴata kenan ,tunda nace zan dawo ,ai dole na na dawo naga kaykykyawar fuskar nan taki,ya jikin naki"suhaimat ta fada cikin murmushi. "Da sauki "cewar fattu. "Masha Allah,haka ake so ki kula da shan magungunanki kinji"cewar sarauniya suhaimat. Jinjina kai fattu tayi kafin tace "ina yan biyu " Murmushi suhaimat tayi kafin tace "suna can suna shiryawa ,Basu san nazo nan ba da kin gansu sun biyoni, dan sun damu dake sosai" ta fada cikin murmushi. Fattuna murmushin tayi, tana wasa da ƴan yatsunta. Sun jima suna hira da fattu,duk da tana ɗan jin kunyar sarauniya suhaimat din,amma zakayi mamakin yadda ya sake suke ta hira ,harda dariya . Anan ne take sanar da ita cewar yau zasu tafi garinsu. Lokaci guda fattu ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka, "Ayya inna meyasa zaki tafi?dan Allah ki zauna anan,bana son ki tafi "fattu ta faɗa tana mai kallon sarauniya suhaimat. Ahankali suhaimat ta kamo hannun fattu ta rike cikin nata tana ɗan murmushi,duk da itama sam batason rabuwa da Fattun,amma dan ta kwantar mata da hankali sai tayi murmushi tace"karki damu my princess ai zan rinka zuwa ina ganinki,kuma wataran zance yarima ya kawomin ke muyi hutu,ko bazaki zoba"?ta fada tana kallon fattu. "Zanzo mana inna dama bana son zama agidan nan tsoron wannan mai kama da hamman nawa nake"ta fada cikin yanayi na damuwa, idanunta har ya kawo kwalla. Cikin damuwa itama suhaimat ta tallafi kumatun fattu,tana mai cewa"ki kwantar da hankalinki ƴata, ba abinda zai miki kinji,ki daina tsoronsa,yanzu haka yana can akwance cikin halin mutuwa da rayuwa,kuma hammanki yana tare da ke"ta fada cikin salon kwantar da hankali. Jinjina kai fattu tayi tana mai kallon suhaimat ɗin. Murmushi suhaimat tayi tana mai kallon wayarta dake ringing ,lokaci ta duba taga harta kara minti biyar akan time ɗin da zasu tafi,dan ma private jet ne.kuma mijinta bai sami halartar gurin ba saboda wani meeting da suke mai muhimmanci. "To ƴata zan tafi saina ƙara dawowa zan dawo mutafi tare dake ,kinji"suhaimat ta fada tana jin ba dadi cikin ranta,ji take kamar zata rabu da abu mafi muhimmanci arayuwarta. Ahankali fattu ta daga mata kai, idanunta na zubda kwalla,sam bata son suhaimat ta tafi,"Allah ya tsareku,ya kaiku lafiya inna ,saikin dawo"fattu ta faɗa tana ɗan kwantar da kanta jikin suhaimat. Rungumeta suhaimat tayi cikin alhinin rabuwa da ita .Adeeb ne ya shigo dakin da sallamarsa,da alama wanka yayi dan ya cire kayan dazu ya sanya riga da wando blue and white yayi matuƙar kyau sosai,sai ƙamshinsa yake kamar kullum. Kallonsu yayi yadda ko wanne ke zubda kwalla ,lallai lamarin Allah abin kallone,dubi yadda lokaci ɗaya shakuwa ta shiga tsakanin bayin Allahn nan?kamar sunsan juna.murmushi yayi yana kallon suhaimat kafin yace "anty suhaimat har yanzu kina nan da tausayi da kuma saurin kuka " ya faɗa yana kallonta.shikam tun sanin da yayi mata haka bakinta yake ,akwai tausayi da son mutane bata da kyamar dan adam. Share hawayen idanunta tayi kafin tace "prince wllh da zaka bani yarinyar nan dana tafi da ita can Ghana munyi zaman mu ,dan Allah ya doramin kaunarta cikin raina sosai" ta fada tana shafa kan fattu. "In baki ita ku tafi?Ni kuma inyi yaya,haka kawai ,ki tafimin da mata?inaaa"Adeeb ya faɗa cikin zuciyarsa.amma zahiri saiyace "karki damu watarana zata zo " "Allah yasa da gaske kake,yanzu dai kayi mana hoto dan tarihi"sarauniya suhaimat ta fada tana mai janyo fattu jikinta. Luuuf!! fattu tayi ajikin suhaimat tana mai jin wani irin sanyi acikin zuciyarta.hotuna Adeeb yayi musu kusan kala biyar awayarsa, hakama yayi musu awayar Sarauniya suhaimat ɗin. Da gyar suka rabu da juna cikin kewa da kaunar juna, fattu sai kuka take ta rungume Adeeb lokacin da suhaimat ta tafi rarrashinta yayi tayi da gyar ya samu tayi barci. Ammi kuwa sosai taji dadin tafiyar suhaimat,dan hankalinta sam bai kwanta ba ,gani take kamar zata iya gano wani abu game da fattu Yanzu damuwarta daya shine yadda ,zata bullowa lamarin Adeeb. Rashad ya farfaɗo ,saidai gaba ɗaya ankasa gane kansa ,dan kullum haka zaka ganshi shiru baya magana saidai kallo,abin yana matukar damun amma,haka zatayi ta kuka tana kallonsa,saidai kawai kaga hawaye yana bin fuskar Rashad din,ya rame sosai,dan baya wani cin abinci,ga karaya ajikinsa ta ko ina likitoci suna ta binciken kwakwalwarsa dan suna tunanin tanan ya sami matsala.saidai muce Allah ya bashi lafiya. Sam yanzu Adeeb baya kula tareeƙ ,haka zai zo yayi ta bashi haƙuri amma Adeeb bazai ce masa ko ci kankaba.duk da yadda yayi kewar tareeƙ ɗin cikin zuciyarsa. Abin yana yiwa tareek ciwo ,haka zai je gurin nanny yayi ta kuka ,saidai tabashi hakuri. Alhamdullah jikin fattu ya warke sosai,dan duk tabon ciwukanta ma babu,sosai shakuwa ta kara shiga tsakaninta da Adeeb,dan kuwa ya dawo da ita bangaren sa gaba ɗaya ,ya siyo mata sabbin kayan sawa ,da duk wani abu datake bukata. Yayin da gefe guda yake ci gaba da bincikensa akan al'amarin su Nazli da kuma sarƙar nan ta fattu,akan ammi ,saidai har yanzu ya kasa samun wata kwakwkwarar hujja da zai kama ammi da ita .dan haka ya kara yarda cewar hadin bakine na amma da nanny ,suke son hadashi da ammi. Bangaren rashad kuwa ,abin ba'acewa komai,dan har yanzu yana nan jiya iyau, baya uhhhm bare uhm -uhm .magani ta ko ina yi masa ake ,mai martaba da kansa abin yana damunsa,. Haka ma Adeeb yana jin ciwon abinda yayiwa ɗan uwan nashi,saidai koma menene shiyajawa kansa.kuma hakan bai hana shi neman masa magani ba . Shaikh lateef ya bawa Adeeb magungunan da zai rinka amfani dashi,kuma yana amfani dasu yadda ya kamata.zamu iya cewa yanzu abubuwa sun dan lafa agidan. Yanzu haka fattu ana mata lesson kullum ,zakuyi mamakin yadda fattu ta iya Yaren larabci sosai,tana ji kuma tana iya mayarwa, dan fattu akwai ƙwaƙwalwa,shikansa mai mata lesson yana mamakin hazaka irin ta fattu. Adeeb kullum yana kara nuna mata abubuwan da bata game ba.tayi kyau sosai ta goge idan ka ganta bazaka taba cewa itace ba. Kullum saisunyi waya da sarauniya suhaimat,sun shaku da juna sosai. Gimbiya Zulaihat ma tana nan tana nata shirin,dan yanzu kam tana ganin fattu na neman zama wata abar alfahari agidan,dan ta kereta ta ko ina,Shegiyar yarinya kyau kamar yar aljanu. Wannan kenan. Ammice zaune ƙaton falonta tana waya,dawowarta kenan daga gurin mai martaba,tana masa maganar ya dace ace zuwa yanzu Adeeb yayi aure ,dan shekaru na tafi kuma shine magajin fada. Dan haka abie yace ta zaba masa matar da zai aura ,tunda itace amminsa ,kuma yasan Adeeb bazaiki zabin ammin nashi ba.tun da dai shi ba kula yan mata yake ba. Cikin farin ciki kuwa ammi ta dawo ɗakinta ta kira kawarta. "Ƙawata ,albishirinki? Ammi ta fada cikin ɗoki. Bansan me akace mata ba ta dayan bangaren naji dai taci gaba da cewa"ai mai martaba ya bani damar zabawa Adeeb matar da zai aura,kuma ba kowa na zaba masaba face yar wajenki,maryam.kinga mun sami hanya cikin ruwan sanyi,da zamu cika burinmu akansa" ta fada cikin doki tana murmushi. Shiru na ɗan wani lokaci kafin taci gaba"ki rabu dashi, kawai ,nasan barazana ce yake min,amma kinsan bazan taɓa yarda Zulaihat ta auri Adeeb ba,dan kuwa ubanta zatayi wa aiki ba muba, Batun yarinyar da yazo da ita kuwa,na boye duk wata hanya danasan zai gane suwaye iyayenta na asali,kuma nasanya boka ya hana uwarta zuwa gasar nan ma gaba daya , Kinga har abada bazasu taba haduwa da junaba. Abu na gaba da zamuyi shine ,da zarar anyi auren nan,zamu sa ta kashe dan banza kowa ma ya huta, zan san yadda zanyi in shawo kan wancan mugun ya yarda ayi auren saimu kashe Adeeb din" Shiru ammi tayi tare da sauraron abinda ake fadi aɗaya bangaren. Kafin taci gaba"wllh ƙawata Ni kaina yarinyar nan na tsaneta ,bana don ganinta,Aduk lokacin dana ganta fuskar uwarta nake gani ,kuma ina tunano abinda ya faru abaya,dan haka itama kawar da ita zanyi kowa ya huta ,duk dana ɗauke sarƙar nan Tata,amma na nemeta na rasa ,kuma banganta awuyan yarinyar ba,dan haka ina tunanin bata koma gareta ba,ƙila dai nice na sauya mata gurin ajiya na manta" Shiru ammi ta sake yi ,kafin tace shikenan sai kinzo ma karasa maganar. Jikin fattu banda rawa da bari ba abinda yake ,zuciyarta sai neman tarwatsewa take , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!!wanann wace irin masifa ce haka,yanzu ammi tasan su waye iyayena dama ?kenan kashe Hamma zasuyi?me hakan ke nufi? kenan ammi ba itace mahaifiyar Adeeb ba?dan kuwa tasan ba ta yadda za'ayi uwa tayi yunkurin kashe ɗan ta, wai meke faruwa ne?wannan ɗin wane irin badakala ce kuma? Tsabar rawar da jikinta yakeyi bata san lokacin data buge wani flower vase dake ajiye agefenta ba ,ya fadi kasa ,jikake toshshs!! Ya fashe . Cikin tsoro da tazana fattu ,tayi sauri buya ajikin ƙofa tare da runtse idanunta. Ammi kuwa da sauri ta taso Dan ganin waye yayi mata labe ,har yaji sirri ta. Da mugun ƙarfi aka fizgi fattu akayi waje da ita ,buɗe baki fattu tayi da nufin kurma ihu,taji an toshe mata bakinta..... Waye ya dauke fattu? Me zai faru nan gaba? Muje zuwa anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 67/68 _______________Da sauri ammi ta taso cikin tashin hankali da fargaba,dan kuwa tabbas tasan wani yaji me take cewa. Fattu kuwa tsabar ruɗewa da shiga tashin hankali tama rasa ina zata dosa,tsoro ya cika mata zuciya ganin ammi ta nufo inda take ,saidai cikin wannan yanayin ne taji an fizgeta da mugun ƙarfi anyi waje da ita.nan take tsoronta ya kara rubanya.buda baki tayi da nufin kurma ihu ,dan atunaninta masu kashe tan ne suka kamata.saidai gam!aka rufe mata baki,bata yadda zatayi ihu.kuma cikin wani irin sauri mai kama da gudu akayi waje da ita,ta wata hanya da bata nan ta shigo ba. Ammi kuwa tayi iyakar dubanta ,amma bata ga kowa ba,kuma tabbas tasan anshigo cikin dakin nan,to waye?dan duk ta kora yan aiki can farfajiyar gidan dan tasami damar yin wayarta. Ko dai Adeeb ne?kai bashi bane ,dan kuwa Adeeb baya zuwa gareta ba tare da yayi sallama ba.toko nanny ce ?kai idan nanny ce zan iya cimma ta kafin ta gudu,wai waye wannan yake son shiga rayuwata ne?waye yake son bakuntar lahira kwana kusa?na rantse da Allah idan na gano ko waye saina hukuntashi, hukunci mai tsanani.yanzu dole mu sake sabon tsari dan wannan kam ya rika ya lalace"ammi ta fada cikin zafin zuciya da kunar rai. Tana nan tsaye Zulaihat ta shigo dakin ba ko sallama,kawai ammi sai ganin mutum tayi bukut ya shigo cikin falon.guri ta nema ta zauna tare da ƙurawa ammi ido. Harara ammi ta Banka mata tana tunanin koma dai Zulaihat ɗin ce ta shigo dazu da tasan Zulaihat ba hankali gareta ba? "Ke Zulaihat kece kika shigomin daki dazu kina Min labe?"ammi ta fada cikin haɗe fuska. Wani shegen kallon Zulaihat ke jifan ammi dashi,kafin ta fara magana "lallai ma ammi har kina tunanin akwai wanda zan zauna inayiwa labe?to me zan labe naji,bayan duk wani tuggun da ake ƙullawa ina sane dashi,me kuma za'a boyemin ?kinsan Ni bana munafurci kai tsaye nake Abunda naga dama "Zulaihat ta faɗa cikin rashin kunya tana wani juya ido. Kallonta ammi tayi cikin tsantsar ɓacin rai da tsanar halayen ta na rashin kunya kafin tace " yanzu kina Min wannan gatsalin kike son na aura miki Dana?to wllh gara ki nutsu Dan bazan yarda ki auri Adeeb da wannan shegen halin naki ba,domin shirme zakiyi tayi mana,idan mun saki aiki"ammi ta fada cikin faɗa -fada. Wata irin dariya Zulaihat tayi tana kallon ammi kafin tace "Kinga ammi ki daina min tsawa keba uwata bace,ko iyayena lallaɓani suke ,kuma da kike cewa zan bata muku aiki,ku atunaninku idan anyi auren biye muku zanyi in cutar da abin sona,?wllh garama ku nutsu daga ke har daddy na Dan kuwa rungumar mijina zanyi musha soyayya ,kuma duk wanda yayi yunkurin cutar da shi ,wllh saina kashe mutum,kinsan nima na iya dabancin"Zulaihat ta faɗa cikin gadara tana kallon ammi ido cikin ido. Baki buɗe ammi ke kallon Zulaihat,lallai yarinyar nan ta wuce yadda suke tunani,Gara ta lallabata,karta jika mata aiki,dan haka cikin dan murmushin yake ammi tace "kai ƴata dadina dake baki san wasa ba,yanzu saiki maida abu gaske,ki kwantar da hankalinki,kinsan nima bazan taɓa bari a cutar min da Adeeb ba, dama nayi tunanin bakinsu ɗaya da mahaifi ki,shiyasa na fadi hakan"ammi ta fada cikin murmushin yaƙe tana hararar Zulaihat ƙasa ƙasa. "Ato Gara dai mutum ya kula wllh ,dan zan iya komai akan abinda nake so"Zulaihat ta faɗa tana mai gyara zamanta zuwa kwanciya,tare da lumshe idonta kamar zatayi barci. "Zanyi makaganinki daga ke har uban Maki shegiya"ammi ta fada cikin zuciyarta,tana shigewa daki,cike da tunanin mafita. Ba'a dire fattu a ko ina ba, sai cikin wani daki mai dan duhu, wanda kana iya ganin mutum ,amma bazakaga fuskarsa kai tsaye ba. Koda aka direta sam ba'asakar mata baki ba. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,sai ƙoƙarin cire hannun mutumin take daga bakinta, ammata kasa . Cikin nutsuwa da kwantar da hankali ya fara magana "ki nutsu ,niba cutar dake zanyi ba,koda na bude miki baki to karkayi ihu " Cikin hanzari fattu ke jinjina kanta idonta yayi zuru zuru ,burinta kawai tajita free. Ahankali ya dannan makunnar dake gefensa,nan take dakin yayi haske ta yadda kana iya ganin komai. Da sauri fattu ta daga idanunta tana kallon mutumin, "Hamma tareeƙ"ta fada cikin rawar murya,"ka bani tsoro Hamma tareeƙ,meke faruwa cikin gidan nan,wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana?fattu ta faɗa cikin muryar kuka tana kallon tareeƙ. Shima kallonta yake zuciyarsa na masa zafi ,yayi fatan ace Adeeb da kansa yaji wannan maganar ba wani ne yaji ba. "Ki kwantar da hankali ki fateema,da sannu zaki fahimci komai " Ya fada tare da ɗauko wayarsa yayi kira. "Ummee kuzo ina nan cikin dakin baya"haka kawai ya faɗa ya kashe wayar. Kallonsa fattu keyi jikinta har lokacin rawa yake ,tana cikin shock da zallar mamaki,kujera tareeƙ ya nuna mata tare da cewa"ki zauna anan fateema " jiki ba kwari fattu tabi bango ta zauna aƙasa ba tare da ta hau kan kujerar da tareeƙ ke nuna mata ba.zallar mamakin ammi da al'ajabi ta ke ɗawainiya da fattu,yanzu duk zaman da sukayi dama ammi tasan asalin iyayenta?kuma ita ta sace sarƙarta wacce take matsayin shaidar da zata sadata da iyayenta na asali?amma menene ribar ammi nayin hakan?wane amfani zata samu?lallai dole ta sanar da Hamma wannan maganar . Bude kofar da akayi ke ya katsar mata da tunaninta ,da sauri cikin tsoro ta kalli bakin ƙofar,nanny ce ta shigo ita da amma. Da sauri fattu ta mike cikin rawar jiki ta ƙanƙame nanny tare da sakin kuka mai ciwo da radadi," nanny wai zasu kashe min hammana ,kuma nima zata kasheni ,sannan tace tasan asalin iyayena ,amma bazata bari muhadu dasuba.nanny wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana,anya kuwa itace ta haifeshi ?fattu ta faɗa tana mai dago kanta tare da kallon nanny. Cike da tausayin fattu nanny ta riketa ajikinta Tana mai shafa bayanta ,alamun rarrashi,kafin tace "ki kwantar da hankalinki ɗiyata,ba abinda zai sameku da yardar Allah,kuma yau zan sanar dake alakar dake tsakanin Adeeb da amminsa" cewar nanny Tana me zaunar da fattu akan kujera. Amma kuwa tana tsaye ta kafe fattu da idanu,tabbas hasashenta ya tabbata ,dan kuwa ba tun yau take zargin cewa fattu yar sarauniya suhaimat bace,dan kuwa tasha ganin irin sarƙar wuyan Fattu atare da iyalin suhaimat,bayan nan sai kayi duba na tsanake zaka gano tsantsar kamar dake tsakanin fattu da suhaimat ɗin.aikuwa insha Allahu yau ba sai gobe ba zata sanar da fattu wacece ammi. Cikin kuka fattu ke kallon nanny kafin tace "Dan Allah nanny ki sanar dani ala'akar dake tsakanin hammana da kuma ammi,ko zuciyarta zata sami salama,ji nake kamar zan mutu,banson wani abu ya sami hammana nanny Ina kaunar hammana fiye da yadda nake son kaina idan wani abu ya sameshi wllh mutuwa zanyi"fattu ta faɗa cikin kuka mai ban tausayi. Hawaye nanny ta goge tana mai kallon fattu kafin tace "In Sha Allahu ba abinda zai sami magajin fada ki kwantar da hankalinki ɗiyata. Hannun fattu amma ta kamo cikin sanyin murya tace "kiyi shiru ,ki kuma kwantar da hankalinki,dan yau zaki san abubuwan da baki sani ba abaya,dan haka ki adana hawaye ki zai miki amfani nan gaba "cewar amma tana kallon fattu cikin tausayawa. Share hawayen kuwa fattu tayi tare da kafe nanny da ido,zuciyarta na bugawa kamar ana. Kada ganga. Ahankali nanny ta fara magana"ammi ba itace asalin wacce ta haifi Adeeb ba,amma itace wacce ta rike shi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararararmmmm gaban fattu ya bada sautin karar da saida ta kusan faduwa tana daga zaune. Ai Ni kaina saida na tsorata na jefar da wayar nan dan tsoron jin abinda nanny zata faɗa . Muje zuwa masoyan fattu da Adeeb . Sai mun haɗe anjima in Sha Allahu. Anty mammy ce Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 69/70 ___________Ahankali nanny ta fara magana ,tana cewa"Ammi ba ita bace asalin mahaifiyar Adeeb,amma itace wacce ta rikeshi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararrararaammm!!!gaban fattu ya bada ƙara, sakamakon jin maganar nanny datayi kamar saukar aradu, Da sauri ta dafe gefen kujerar da take kai,dan ji tayi kamar zata faɗi. Baki buɗe take kallon nanny cike da tsantsar mamaki,cikin rawar murya tace "nanny kina nufin ammi itace ta kashewa Hamma mahaifiyarsa?to amma me yasa Hamma yake mata kallon uwa?me yasa bai dauki mataki akanta ba?"fattu ta faɗa cikin rudani. Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace "saboda bashi da masaniya akan abinda ya faru,kuma ya yarda da ammi fiye da kowa,dan yana mata kallon uwa mahaifiyane,baya tunanin zata taba cutar dashi.ki saurare Ni da kunnen basira ,zaki ji abinda ya faru yanzun nan. "Sarauniya Nazli,ƴace agurin ƙarin baban mai martaba uwa daya uba daya,wato kenan ita da mai martaba ,yan uwan juna ne ,dan kuwa auren zumunci akayi musu. Suna kaunar juna matuka bayan anyi auren,suna zamansu lafiya cikin so da aminci, lokacin da akayi auren nasu,iyayen sarauniya Nazli duk sun rasu,hakan yasa take zaune a hannun mahaifiyar mai martaba ,dalilin hankali da nutsuwarta yasa mahaifiyar mai martaba ta zaba masa ita matsayin matar da zai aura inda ranar da aka daura musu aure aka naɗa shi matsayin sarkin misra. Shekara guda dayin aurensu Allah ya azurtata da zamu yaro , kyakykyawa abin so ga kowa, ranar suna aka rada masa suna adeeb. Adeeb ya taso cikin so da kauna, agurin iyayensa, da ma duk wani wanda yake fadar nan,yana da matukar hakuri ,hazaka ,ladabi da kuma biyayya. Nice wacce ke rainon Adeeb ,kasancewar mijina yana aiki acikin fadar nan,shine drivern dake tuka sarki da iyalinsa. Lokacin ina goyon dana tareeƙ ,dan haka na hadasu duka ina rainonsu,saidai ko da wasa ban taba hada tareeƙ da Adeeb matsayi daya ba,duk lokacin da zanyi musu wani abu saina farayiwa Adeeb,sannan nake yiwa tareek,ko wasa suke yi nakan sanya Adeeb matsayin shugaba ne tareeƙ kuma bafadensa.hakan yasa suka taso cikin kaunar juna da girmamawa,dan kullum nakan nusar da tareeƙ cewar Adeeb ɗan sarkine kai kuma dan bafaden sarkine,dan haka kada ka haɗa kanka da Adeeb . Sosai shakuwa ta shiga tsakanin Adeeb da tareeƙ,dan kuwa ko gurin sarki Adeeb zaije to dole saida tareeƙ ,kuma tun lokacin ƙuruciya tareeƙ ke kiran Adeeb da yallaɓai. Muna jin dadin zama da sarauniya Nazli,dan kuwa macece mai matukar girmama dan adam,ba ruwanta da nuna isa ko iko,akan kowa ,tana janmu ajikinta sosai ,hakan yasa kowa ke kaunarta cikin masarautar nan. Kwatsam batun karin auren mai martaba ya taso,kuma auren zaiyi shine da mata biyu a lokaci daya, dayar ƙánwar abokinsa ce wato amma,dayar kuma yar abokin babansa wato ammi. ko kaɗan sarauniya nazli bata tada hankalinta ba,koda mai martaba ya nuna tayi hakuri,shima bada son ranshi zaiyi auren ba ,nuna masa tayi ma tafi shi farin ciki tayi masu fatan alkairi ,duk da kuwa can ƙasar zuciyarta tana jin kishi da zafin abin aranta,amma haka ta daure ta nuna ba komai. Bayan anyi bikin mai martaba da matansa guda biyu,da farko ana zaune lafiya kowa na ba kowa girmansa,sai kuma abubuwa suka zo suka fara lalacewa,yau kaji wannan maganar gobe kaji waccan.ammi itace wacce ke haddasa komai,sam bata son zaman lafiya ta cika gutsiri tsoma,amma sarauniya Nazli bata kulata ,dan kuwa lokacin tana fama da laulayin cikinta na biyu. Amma ce ma ke dan maida mata martani, Kullum amma na zuwa gurin sarauniya Nazli tana kula da ita, sosai suke zaman lafiya a tsakaninsu ba gutsiri tsoma ko kaɗan,hakan kuwa ba ƙaramin bata ran ammi yake ba ,dan ita burinta kawai ta farraka su. Lokacin da sarauniya Nazli ta zo haihuwa kuwa ,cikin nasara ta haifi yaranta tagwaye duka mata, Masha Allah,karkuzo kuga kyau garin yaran nan,sosai kowa ke murna da samun yan yaran nan, Adeeb yana bala'in kaunar ya'yan nan,kullum yana kusa dasu yana musu wasa,shida tareeƙ ,wani lokacin hana daukar yaran ma suke,idan za'a daukesu suyi ta kuka kar'a taba musu kannai.kuma daidai lokacin ne amma ta fara laulayi itama. Sosai mai martaba yake jin dadin zama da matansa ,dan kowa na kokarin kyautata masa.koda labarin cikin amma ya sameshi yayi murna sosai . Wayyo ai tunda ammi ta kyalla ido ta gano ciki jikin amma,hankalinta yayi magun tashi,ya za'ayi haka ?an aurosu tare amma ita har yanzu ko batan wata bata taba yi ba?ina da sake wllh saita zubar da cikin Nan.shikenan saisuyi ta haihuwa ,su gaje masarautar ita ko oho? Ba irin abunda ammi batayi ba akan cikin rashad ya zube,amma hakarta bata cimma ruwa ba. Haka aka haifi Rashad , kyakykyawa dashi ,suna matuƙar kama da Adeeb,Adeeb yana son Rashad fiye da yadda yake san twince husna da haseena,kullum yana tare da Rashad shida tareeƙ ,barci ne kawai ke rabasu. Hakan yana dagawa ammi hankali,tun daga nan saita fito da sabon salo, wato ta fara jan yaran ajikinta,da farko sam Adeeb bai saki jiki da ammi ba ,dan shi irin yaran nan ne miskilai,idan Kinga dariyarsa to shida tareeƙ ne ko mai martaba da mommansa ,ko kuma ni,sai kuma Rashad da amma . Saidai yana da yawan kyauta ,yanzun nan zai baka abu yace na kyauta na baka,hakan yasa kowa ke kauanarsa sosai, Kusan tunda ga lokacin wasu da yawa ke kiransa da magajin fada,ciki kuwa hardanki.ciki kuwa harda Ni. Amma kasancewar ammi makirar mace ,ta san ta yadda zata ja hankalin mutum ,sai Adeeb ya fara yarda da ita,harta kai ta kawo yana kwana anan bangarenta.daga wannan lokacin ne kuma Adeeb ya fara tsiro da wata halayyar sam baya son Rashad yazo inda yake ,lokacin Rashad yana rarrafe,wai zai bata masa jiki,saidai idan shi yaga dama yayi masa wasa . Wata rana mijina ya dawo gida hankalinsa atashe,koda na tambayesa lafiya ?meke faruwa?nagansa cikin tashin hankali .nan yake sanar dani cewar ,yau ya kai ammi anguwa ,yana zaune yana jiranta, bata fitina, kawai saiya dan zagaya dan ya ware ƙafarsa ,yana zuwa saitin window yaji tana magana da wani mutum, kuma suna tattaunawa ne akan yadda zasu kawar da Adeeb harda tareeƙ,sannan yaji tana sanar da mutumin cewar aiki yayi kyau,dan yanzu sam Adeeb baya kaunar Rashad,baya son Rashad yazo koda inda yake ne.yanzu abinda take so shine a cire musa mahaifiyarsu daga ransu,ta yadda sai abinda tace suyi zasuyi, Tana son saita lalata musu tarbiyyar sun zama abin kwatance ,sun haddasawa iyayen su ciwon zuciya sun mutu,kafin ta kawar dasu,inya so ta gaji dukiyar mai martaba ita kadai. Hankalina yayi matuƙar tashi lokacin dana ji wannan maganar ,nan take na fara kuka ,ya zama dole na sanar da iyayen yaran nan,su kula da ƴaƴansu, Amma nasan sarauniya Nazli,koda na faɗa mata ,ita macece mai hakuri da tawakkali ba abinda zatayi akan hakan,zata iya cemin ma indaina kawo mata zancen wani,kowa yayi dai dai kansa. Dan haka gurin amma na nufa,ina kuka nake sanar da ita komai da mijina ya faɗa min,hankalinta yayi mugun tashi sosai,nan take ta tashi ta nufi gurin nazli cikin ɓacin rai, tana zuwa ta labarta mata komai ,sannan ta kara da cewa idan muka zuba ido fa zata lalata mana yara ,tayi musu asiri su rabu damu, dan haka ya zama dole mu taka mata burki"alokacin hankalin Nazli ya tashi,dan tasan amma bazata mata karya ba,kuma itama ta fuskanci sauyi daga gurin Adeeb ɗin,dan haka saitace zata dauki mataki akan abin muyi hakuri abi komai ahankali. Aikuwa Nazli da kanta ta je gurin ammi dan suyi magana akan yaran ,kuma tajene akan zata yi mata magana cikin hikima ta yadda tsoron Allah zai shigeta,abinda bata sani ba ,tuni ammi tayi nisan da bata jin kira. Tana zuwa dakin zata shiga ,tajiyo Muryar ammi tana waya , "Kun tabbata dai kun dauke yarinyar nan?kuma kun fitar da ita can wata kasar daban?bana son asami matsala ,so nake tayi nisa,nisa na har abada ,ta yadda bazata ƙara ganin yar ba,ai wllh dama na faɗa duk wanda yaci tuwo dani miya yasha. Shikenan ,zakaji alart. Tana gama faɗin haka ta ajiye wayar tana murmushi. "Suhaimat ,kinyi kuskuren auren wanda nake da burin aure,wllh nayi ta sanya rayuwarki cikin bakin ciki da tashin hankali,nasa an dauke ƴarki,an jefar da ita ,can wata kasar,ta yadda ko gawarta bazaki gani ba,na Tsaneki suhaimat,na tsani ganinki,kin auremin wanda nake so ,sannan kin haihu Ni ban haihuba, wllh sainayi ta shuka miki bakin cikin da zaiyi silar mutuwarki,bana ƙaunarki sam cikin raina.kuma keda ƴarki har abada"ammi ta fada cikin muryar azzalumai tana wani murmushi na mugunta. Jikin Nazli banda rawa ba abinda yake ,tashin hankali ya baibaye dukkan ilahirin jikinta. Yanzu zalumcin ammi harya kai kan yar uwarta?yar uwarta take cutarwa haka,ta sanya an sace Mata yarta an jefar,wannan wane irin rashin imani ne,? innalillahi. Cikin mugun ɓacin rai sarauniya Nazli ta buga kofar falon ammi da karfi ta shigo ciki,idanunta na zubda hawaye, Azabure ammi ta mike tsaye tana kallon momma,koba'a faɗa mata ba ,tasan cewar amma taji duk abinda take faɗi,dan haka kura mata ido tayi cikin yanayi na rashin gaskiya . Momma kuwa wato Nazli,cikin muryar kuka take magana da cewa"wllh ammi kiji tsoron Allah,ki sani zaki mutu ,kuma ,zaki koma gareshi,duk abinda kikeyi yana kallon ki,wacce irin zuciya gareki?da har yar uwarki ma bata tsallake sharri ki ba?to kisani tabbas sai naje na sanar da iyayenku abinda kika aikata azzaluma marar imani,sannan kisani,duk abinda kike aikatawa akan yayanmu to yazo kunnenmu ,kuma in sha Allah asirinki bazaiyi tasiri akan yaran mu ba,baki isa ki rabamu da suba.turrr da hali irin naki makira"momma na gama faɗin haka ta fice daga ɗakin cikin tashin hankali,har bata san inda take sanya ƙafartaba. Ammi kuwa tuni zuciyarta ta tsinke tsoro da fargaba sun gama baibaye zuciyarta,yanzu idan Nazli ta tona mata asirifa?me yakama tayi ,dole ta dauki mataki tun kafin maganar taje kunnen wanda bataso suji,wayyo Allah me Yakamata nayi"ammi ta fada cikin tashin hankali tana mai Safa da marwa. Kuka sosai Nazli keyi cikin dakinta tana mamakin zalunci irin na ammi,yanzu ashe mutum zai iya cutar da ɗan uwansa akan abin duniya?wannan wane irin rayuwane?turrrr da halin ammi Allah ya shiga tsakaninsu da ita . Tana cikin wannan halin ne, na isketa,dan haka cikin damuwa na tambayeta meke faruwa.nan take sanar dani abinda kunnenta yaji,hankalina yayi matuƙar tashi lokacin dan banyi tunanin rashin imaninta yayi nisa har haka ba. Nan sarauniya Nazli ke sanar dani gobe gobe zata je har gidansu ammi ta fadi abinda ammin tayi .naso in hanata Amma tace sam bazata iya zama da wannan abin cikin ranta ba ,dan kuwa har ta sanar da mai martaba tana son zuwa anguwa. Washe gari kuwa mijina ya dauki ammi da yaranta ,suka tafi,amma banda Adeeb ɗan lokacin ma suna makaranta .ko minti goma ba'ayin da fitarsu ba aka aiko cewar motar su ta kama da wuta sun kone kurmus... Kuka ne yaci karfin nanny ta kasa magana sai kuka da takeyi,haka ma amma banda kuka ba abinda takeyi, tareeƙ kuwa idanunsa sunyi jajur dasu,fuskarsa har wani karkarwa take. Fattu kuwa tsabar kuka har neman shiɗewa take,abubuwa sun taru sunyi mata yawa,ga tsantsar tausayin Adeeb ,ga kuma mamaki da al'ajabi cewar ammi yar uwar mahaifiyarta ce .sannan itace silar rabata da iyayenta...sosai take kuka ta ƙanƙame jikinta akan kujera,wani irin zafi take ji cikin zuciyarta ,duniya ba tabbas,yanzu dan uwa shine zai cutar da ɗan uwansa,ashe shiyasa ta dauke sarƙar nan yawa?dan bata yi tsammanin ina raye ba ,kuma saigashi Allah ya kawoni har mazaunin ta,shin wacece mahaifiyar tawa? Acikin yan uwan ammi.wayyo Allah na gode maka ya Allah ka sadani da ahalinsa cikin aminci.allah sarki baffana. Duk fattu ke wannan zancen cikin zuciyarta,tana jin kamar ba ita bace. Cikin kuka da muryarta wacce ke rarrabewa tace"wa...c..e..cc...ee ma...ha...I...fiya .....ta Kuma .....ina....za.....n...ga..nta." Muje zuwa ɗan jin ya zata kaya. Sorry jiya kuna ta jirana na ƙunƙuni shiru, bankin daɗi ne wllh. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 69/70 ___________Ahankali nanny ta fara magana ,tana cewa"Ammi ba ita bace asalin mahaifiyar Adeeb,amma itace wacce ta rikeshi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararrararaammm!!!gaban fattu ya bada ƙara, sakamakon jin maganar nanny datayi kamar saukar aradu, Da sauri ta dafe gefen kujerar da take kai,dan ji tayi kamar zata faɗi. Baki buɗe take kallon nanny cike da tsantsar mamaki,cikin rawar murya tace "nanny kina nufin ammi itace ta kashewa Hamma mahaifiyarsa?to amma me yasa Hamma yake mata kallon uwa?me yasa bai dauki mataki akanta ba?"fattu ta faɗa cikin rudani. Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace "saboda bashi da masaniya akan abinda ya faru,kuma ya yarda da ammi fiye da kowa,dan yana mata kallon uwa mahaifiyane,baya tunanin zata taba cutar dashi.ki saurare Ni da kunnen basira ,zaki ji abinda ya faru yanzun nan. "Sarauniya Nazli,ƴace agurin ƙarin baban mai martaba uwa daya uba daya,wato kenan ita da mai martaba ,yan uwan juna ne ,dan kuwa auren zumunci akayi musu. Suna kaunar juna matuka bayan anyi auren,suna zamansu lafiya cikin so da aminci, lokacin da akayi auren nasu,iyayen sarauniya Nazli duk sun rasu,hakan yasa take zaune a hannun mahaifiyar mai martaba ,dalilin hankali da nutsuwarta yasa mahaifiyar mai martaba ta zaba masa ita matsayin matar da zai aura inda ranar da aka daura musu aure aka naɗa shi matsayin sarkin misra. Shekara guda dayin aurensu Allah ya azurtata da zamu yaro , kyakykyawa abin so ga kowa, ranar suna aka rada masa suna adeeb. Adeeb ya taso cikin so da kauna, agurin iyayensa, da ma duk wani wanda yake fadar nan,yana da matukar hakuri ,hazaka ,ladabi da kuma biyayya. Nice wacce ke rainon Adeeb ,kasancewar mijina yana aiki acikin fadar nan,shine drivern dake tuka sarki da iyalinsa. Lokacin ina goyon dana tareeƙ ,dan haka na hadasu duka ina rainonsu,saidai ko da wasa ban taba hada tareeƙ da Adeeb matsayi daya ba,duk lokacin da zanyi musu wani abu saina farayiwa Adeeb,sannan nake yiwa tareek,ko wasa suke yi nakan sanya Adeeb matsayin shugaba ne tareeƙ kuma bafadensa.hakan yasa suka taso cikin kaunar juna da girmamawa,dan kullum nakan nusar da tareeƙ cewar Adeeb ɗan sarkine kai kuma dan bafaden sarkine,dan haka kada ka haɗa kanka da Adeeb . Sosai shakuwa ta shiga tsakanin Adeeb da tareeƙ,dan kuwa ko gurin sarki Adeeb zaije to dole saida tareeƙ ,kuma tun lokacin ƙuruciya tareeƙ ke kiran Adeeb da yallaɓai. Muna jin dadin zama da sarauniya Nazli,dan kuwa macece mai matukar girmama dan adam,ba ruwanta da nuna isa ko iko,akan kowa ,tana janmu ajikinta sosai ,hakan yasa kowa ke kaunarta cikin masarautar nan. Kwatsam batun karin auren mai martaba ya taso,kuma auren zaiyi shine da mata biyu a lokaci daya, dayar ƙánwar abokinsa ce wato amma,dayar kuma yar abokin babansa wato ammi. ko kaɗan sarauniya nazli bata tada hankalinta ba,koda mai martaba ya nuna tayi hakuri,shima bada son ranshi zaiyi auren ba ,nuna masa tayi ma tafi shi farin ciki tayi masu fatan alkairi ,duk da kuwa can ƙasar zuciyarta tana jin kishi da zafin abin aranta,amma haka ta daure ta nuna ba komai. Bayan anyi bikin mai martaba da matansa guda biyu,da farko ana zaune lafiya kowa na ba kowa girmansa,sai kuma abubuwa suka zo suka fara lalacewa,yau kaji wannan maganar gobe kaji waccan.ammi itace wacce ke haddasa komai,sam bata son zaman lafiya ta cika gutsiri tsoma,amma sarauniya Nazli bata kulata ,dan kuwa lokacin tana fama da laulayin cikinta na biyu. Amma ce ma ke dan maida mata martani, Kullum amma na zuwa gurin sarauniya Nazli tana kula da ita, sosai suke zaman lafiya a tsakaninsu ba gutsiri tsoma ko kaɗan,hakan kuwa ba ƙaramin bata ran ammi yake ba ,dan ita burinta kawai ta farraka su. Lokacin da sarauniya Nazli ta zo haihuwa kuwa ,cikin nasara ta haifi yaranta tagwaye duka mata, Masha Allah,karkuzo kuga kyau garin yaran nan,sosai kowa ke murna da samun yan yaran nan, Adeeb yana bala'in kaunar ya'yan nan,kullum yana kusa dasu yana musu wasa,shida tareeƙ ,wani lokacin hana daukar yaran ma suke,idan za'a daukesu suyi ta kuka kar'a taba musu kannai.kuma daidai lokacin ne amma ta fara laulayi itama. Sosai mai martaba yake jin dadin zama da matansa ,dan kowa na kokarin kyautata masa.koda labarin cikin amma ya sameshi yayi murna sosai . Wayyo ai tunda ammi ta kyalla ido ta gano ciki jikin amma,hankalinta yayi magun tashi,ya za'ayi haka ?an aurosu tare amma ita har yanzu ko batan wata bata taba yi ba?ina da sake wllh saita zubar da cikin Nan.shikenan saisuyi ta haihuwa ,su gaje masarautar ita ko oho? Ba irin abunda ammi batayi ba akan cikin rashad ya zube,amma hakarta bata cimma ruwa ba. Haka aka haifi Rashad , kyakykyawa dashi ,suna matuƙar kama da Adeeb,Adeeb yana son Rashad fiye da yadda yake san twince husna da haseena,kullum yana tare da Rashad shida tareeƙ ,barci ne kawai ke rabasu. Hakan yana dagawa ammi hankali,tun daga nan saita fito da sabon salo, wato ta fara jan yaran ajikinta,da farko sam Adeeb bai saki jiki da ammi ba ,dan shi irin yaran nan ne miskilai,idan Kinga dariyarsa to shida tareeƙ ne ko mai martaba da mommansa ,ko kuma ni,sai kuma Rashad da amma . Saidai yana da yawan kyauta ,yanzun nan zai baka abu yace na kyauta na baka,hakan yasa kowa ke kauanarsa sosai, Kusan tunda ga lokacin wasu da yawa ke kiransa da magajin fada,ciki kuwa hardanki.ciki kuwa harda Ni. Amma kasancewar ammi makirar mace ,ta san ta yadda zata ja hankalin mutum ,sai Adeeb ya fara yarda da ita,harta kai ta kawo yana kwana anan bangarenta.daga wannan lokacin ne kuma Adeeb ya fara tsiro da wata halayyar sam baya son Rashad yazo inda yake ,lokacin Rashad yana rarrafe,wai zai bata masa jiki,saidai idan shi yaga dama yayi masa wasa . Wata rana mijina ya dawo gida hankalinsa atashe,koda na tambayesa lafiya ?meke faruwa?nagansa cikin tashin hankali .nan yake sanar dani cewar ,yau ya kai ammi anguwa ,yana zaune yana jiranta, bata fitina, kawai saiya dan zagaya dan ya ware ƙafarsa ,yana zuwa saitin window yaji tana magana da wani mutum, kuma suna tattaunawa ne akan yadda zasu kawar da Adeeb harda tareeƙ,sannan yaji tana sanar da mutumin cewar aiki yayi kyau,dan yanzu sam Adeeb baya kaunar Rashad,baya son Rashad yazo koda inda yake ne.yanzu abinda take so shine a cire musa mahaifiyarsu daga ransu,ta yadda sai abinda tace suyi zasuyi, Tana son saita lalata musu tarbiyyar sun zama abin kwatance ,sun haddasawa iyayen su ciwon zuciya sun mutu,kafin ta kawar dasu,inya so ta gaji dukiyar mai martaba ita kadai. Hankalina yayi matuƙar tashi lokacin dana ji wannan maganar ,nan take na fara kuka ,ya zama dole na sanar da iyayen yaran nan,su kula da ƴaƴansu, Amma nasan sarauniya Nazli,koda na faɗa mata ,ita macece mai hakuri da tawakkali ba abinda zatayi akan hakan,zata iya cemin ma indaina kawo mata zancen wani,kowa yayi dai dai kansa. Dan haka gurin amma na nufa,ina kuka nake sanar da ita komai da mijina ya faɗa min,hankalinta yayi mugun tashi sosai,nan take ta tashi ta nufi gurin nazli cikin ɓacin rai, tana zuwa ta labarta mata komai ,sannan ta kara da cewa idan muka zuba ido fa zata lalata mana yara ,tayi musu asiri su rabu damu, dan haka ya zama dole mu taka mata burki"alokacin hankalin Nazli ya tashi,dan tasan amma bazata mata karya ba,kuma itama ta fuskanci sauyi daga gurin Adeeb ɗin,dan haka saitace zata dauki mataki akan abin muyi hakuri abi komai ahankali. Aikuwa Nazli da kanta ta je gurin ammi dan suyi magana akan yaran ,kuma tajene akan zata yi mata magana cikin hikima ta yadda tsoron Allah zai shigeta,abinda bata sani ba ,tuni ammi tayi nisan da bata jin kira. Tana zuwa dakin zata shiga ,tajiyo Muryar ammi tana waya , "Kun tabbata dai kun dauke yarinyar nan?kuma kun fitar da ita can wata kasar daban?bana son asami matsala ,so nake tayi nisa,nisa na har abada ,ta yadda bazata ƙara ganin yar ba,ai wllh dama na faɗa duk wanda yaci tuwo dani miya yasha. Shikenan ,zakaji alart. Tana gama faɗin haka ta ajiye wayar tana murmushi. "Suhaimat ,kinyi kuskuren auren wanda nake da burin aure,wllh nayi ta sanya rayuwarki cikin bakin ciki da tashin hankali,nasa an dauke ƴarki,an jefar da ita ,can wata kasar,ta yadda ko gawarta bazaki gani ba,na Tsaneki suhaimat,na tsani ganinki,kin auremin wanda nake so ,sannan kin haihu Ni ban haihuba, wllh sainayi ta shuka miki bakin cikin da zaiyi silar mutuwarki,bana ƙaunarki sam cikin raina.kuma keda ƴarki har abada"ammi ta fada cikin muryar azzalumai tana wani murmushi na mugunta. Jikin Nazli banda rawa ba abinda yake ,tashin hankali ya baibaye dukkan ilahirin jikinta. Yanzu zalumcin ammi harya kai kan yar uwarta?yar uwarta take cutarwa haka,ta sanya an sace Mata yarta an jefar,wannan wane irin rashin imani ne,? innalillahi. Cikin mugun ɓacin rai sarauniya Nazli ta buga kofar falon ammi da karfi ta shigo ciki,idanunta na zubda hawaye, Azabure ammi ta mike tsaye tana kallon momma,koba'a faɗa mata ba ,tasan cewar amma taji duk abinda take faɗi,dan haka kura mata ido tayi cikin yanayi na rashin gaskiya . Momma kuwa wato Nazli,cikin muryar kuka take magana da cewa"wllh ammi kiji tsoron Allah,ki sani zaki mutu ,kuma ,zaki koma gareshi,duk abinda kikeyi yana kallon ki,wacce irin zuciya gareki?da har yar uwarki ma bata tsallake sharri ki ba?to kisani tabbas sai naje na sanar da iyayenku abinda kika aikata azzaluma marar imani,sannan kisani,duk abinda kike aikatawa akan yayanmu to yazo kunnenmu ,kuma in sha Allah asirinki bazaiyi tasiri akan yaran mu ba,baki isa ki rabamu da suba.turrr da hali irin naki makira"momma na gama faɗin haka ta fice daga ɗakin cikin tashin hankali,har bata san inda take sanya ƙafartaba. Ammi kuwa tuni zuciyarta ta tsinke tsoro da fargaba sun gama baibaye zuciyarta,yanzu idan Nazli ta tona mata asirifa?me yakama tayi ,dole ta dauki mataki tun kafin maganar taje kunnen wanda bataso suji,wayyo Allah me Yakamata nayi"ammi ta fada cikin tashin hankali tana mai Safa da marwa. Kuka sosai Nazli keyi cikin dakinta tana mamakin zalunci irin na ammi,yanzu ashe mutum zai iya cutar da ɗan uwansa akan abin duniya?wannan wane irin rayuwane?turrrr da halin ammi Allah ya shiga tsakaninsu da ita . Tana cikin wannan halin ne, na isketa,dan haka cikin damuwa na tambayeta meke faruwa.nan take sanar dani abinda kunnenta yaji,hankalina yayi matuƙar tashi lokacin dan banyi tunanin rashin imaninta yayi nisa har haka ba. Nan sarauniya Nazli ke sanar dani gobe gobe zata je har gidansu ammi ta fadi abinda ammin tayi .naso in hanata Amma tace sam bazata iya zama da wannan abin cikin ranta ba ,dan kuwa har ta sanar da mai martaba tana son zuwa anguwa. Washe gari kuwa mijina ya dauki ammi da yaranta ,suka tafi,amma banda Adeeb ɗan lokacin ma suna makaranta .ko minti goma ba'ayin da fitarsu ba aka aiko cewar motar su ta kama da wuta sun kone kurmus... Kuka ne yaci karfin nanny ta kasa magana sai kuka da takeyi,haka ma amma banda kuka ba abinda takeyi, tareeƙ kuwa idanunsa sunyi jajur dasu,fuskarsa har wani karkarwa take. Fattu kuwa tsabar kuka har neman shiɗewa take,abubuwa sun taru sunyi mata yawa,ga tsantsar tausayin Adeeb ,ga kuma mamaki da al'ajabi cewar ammi yar uwar mahaifiyarta ce .sannan itace silar rabata da iyayenta...sosai take kuka ta ƙanƙame jikinta akan kujera,wani irin zafi take ji cikin zuciyarta ,duniya ba tabbas,yanzu dan uwa shine zai cutar da ɗan uwansa,ashe shiyasa ta dauke sarƙar nan yawa?dan bata yi tsammanin ina raye ba ,kuma saigashi Allah ya kawoni har mazaunin ta,shin wacece mahaifiyar tawa? Acikin yan uwan ammi.wayyo Allah na gode maka ya Allah ka sadani da ahalinsa cikin aminci.allah sarki baffana. Duk fattu ke wannan zancen cikin zuciyarta,tana jin kamar ba ita bace. Cikin kuka da muryarta wacce ke rarrabewa tace"wa...c..e..cc...ee ma...ha...I...fiya .....ta Kuma .....ina....za.....n...ga..nta." Muje zuwa ɗan jin ya zata kaya. Sorry jiya kuna ta jirana na ƙunƙuni shiru, bankin daɗi ne wllh. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 65/66 ________________"Ki sanar dani dalilin da yasa baki son zuwana gurin yarinyar nan? Me alaƙarki da ita ?ko ince me ta tsaremiki uktee? Sarauniya suhaimat ta fada cikin haɗe fuska ,dan tasan kadan daga aikin ammi ta hanata zuwa gurin fattu. Zaro ido ammi tayi tana mai kallon suhaimat ,dan sai lokacin ta fahimci tana kokarin bada kanta,cikin in-ina ta fara magana "su...hai..mat,wane dalilin ne zaisa kuwa in hanaki zuwa gurinta?kawai ina gudun ace ko wata munaƙisar muka ƙulla yasa kike ta zarya,kinsan tunda wannan abun ya faru to komai ma laifi zai zama , amma bayan wannan bani da wani dalili"ammi ta fada tana kafe suhaimat da idanu. Murmushi suhaimat tayi ,kafin tace "Indai dan wannan ne karki damu ,ai kowa yasan Ni likitar matace,kuma ba laifi bane idan naje duba marar lafiya,kuma ma mace"suhaimat ta fada cikin yanayi na rashin damuwa.kafin ta juya ta bar ɗakin. Harara ammi ta biya da ita ,kamar idanunta zasu fado ,haushin suhaimat takeji fiye da tunanin mai tunani,wllh badan tana tsoron faruwar wani abu ba ,data gama da suhaimat ,dan itace silar shigar ta ko wace irin damuwa.amma ba komai muje zuwa sannu sannu bata hana zuwa,saidai dade ba'ajeba. koda sarauniya suhaimat ta koma bangaren Adeeb, kwance ta tarar da fattu adaki, idanunta alumshe kamar mai barci,yayinda Adeeb ke falo yana amsa waya. Bayan sun gaisa yake sanar da ita fattun tana cikin daki, dan sosai yake jin dadin yadda take kula masa da fattu. Tana shiga fattu ta buɗe idonta,da sauri sakamakon jin muryarta,dan dama tana kwancen nan, tunaninta Sarauniya suhaimat kawai take. Da murna ta tashi zaune tana murmushi,tare da kallon suhaimat, Itama cikin farin ciki ta karasa gareta ta zauna. Ahankali fattu tace "inna nayi tunanin bazaki dawoba,ina ta tunaninki araina"ta fada fuskarta ɗauke da annuri. Shafa fuskar fattu tayi kafin tace "ƴata kenan ,tunda nace zan dawo ,ai dole na na dawo naga kaykykyawar fuskar nan taki,ya jikin naki"suhaimat ta fada cikin murmushi. "Da sauki "cewar fattu. "Masha Allah,haka ake so ki kula da shan magungunanki kinji"cewar sarauniya suhaimat. Jinjina kai fattu tayi kafin tace "ina yan biyu " Murmushi suhaimat tayi kafin tace "suna can suna shiryawa ,Basu san nazo nan ba da kin gansu sun biyoni, dan sun damu dake sosai" ta fada cikin murmushi. Fattuna murmushin tayi, tana wasa da ƴan yatsunta. Sun jima suna hira da fattu,duk da tana ɗan jin kunyar sarauniya suhaimat din,amma zakayi mamakin yadda ya sake suke ta hira ,harda dariya . Anan ne take sanar da ita cewar yau zasu tafi garinsu. Lokaci guda fattu ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka, "Ayya inna meyasa zaki tafi?dan Allah ki zauna anan,bana son ki tafi "fattu ta faɗa tana mai kallon sarauniya suhaimat. Ahankali suhaimat ta kamo hannun fattu ta rike cikin nata tana ɗan murmushi,duk da itama sam batason rabuwa da Fattun,amma dan ta kwantar mata da hankali sai tayi murmushi tace"karki damu my princess ai zan rinka zuwa ina ganinki,kuma wataran zance yarima ya kawomin ke muyi hutu,ko bazaki zoba"?ta fada tana kallon fattu. "Zanzo mana inna dama bana son zama agidan nan tsoron wannan mai kama da hamman nawa nake"ta fada cikin yanayi na damuwa, idanunta har ya kawo kwalla. Cikin damuwa itama suhaimat ta tallafi kumatun fattu,tana mai cewa"ki kwantar da hankalinki ƴata, ba abinda zai miki kinji,ki daina tsoronsa,yanzu haka yana can akwance cikin halin mutuwa da rayuwa,kuma hammanki yana tare da ke"ta fada cikin salon kwantar da hankali. Jinjina kai fattu tayi tana mai kallon suhaimat ɗin. Murmushi suhaimat tayi tana mai kallon wayarta dake ringing ,lokaci ta duba taga harta kara minti biyar akan time ɗin da zasu tafi,dan ma private jet ne.kuma mijinta bai sami halartar gurin ba saboda wani meeting da suke mai muhimmanci. "To ƴata zan tafi saina ƙara dawowa zan dawo mutafi tare dake ,kinji"suhaimat ta fada tana jin ba dadi cikin ranta,ji take kamar zata rabu da abu mafi muhimmanci arayuwarta. Ahankali fattu ta daga mata kai, idanunta na zubda kwalla,sam bata son suhaimat ta tafi,"Allah ya tsareku,ya kaiku lafiya inna ,saikin dawo"fattu ta faɗa tana ɗan kwantar da kanta jikin suhaimat. Rungumeta suhaimat tayi cikin alhinin rabuwa da ita .Adeeb ne ya shigo dakin da sallamarsa,da alama wanka yayi dan ya cire kayan dazu ya sanya riga da wando blue and white yayi matuƙar kyau sosai,sai ƙamshinsa yake kamar kullum. Kallonsu yayi yadda ko wanne ke zubda kwalla ,lallai lamarin Allah abin kallone,dubi yadda lokaci ɗaya shakuwa ta shiga tsakanin bayin Allahn nan?kamar sunsan juna.murmushi yayi yana kallon suhaimat kafin yace "anty suhaimat har yanzu kina nan da tausayi da kuma saurin kuka " ya faɗa yana kallonta.shikam tun sanin da yayi mata haka bakinta yake ,akwai tausayi da son mutane bata da kyamar dan adam. Share hawayen idanunta tayi kafin tace "prince wllh da zaka bani yarinyar nan dana tafi da ita can Ghana munyi zaman mu ,dan Allah ya doramin kaunarta cikin raina sosai" ta fada tana shafa kan fattu. "In baki ita ku tafi?Ni kuma inyi yaya,haka kawai ,ki tafimin da mata?inaaa"Adeeb ya faɗa cikin zuciyarsa.amma zahiri saiyace "karki damu watarana zata zo " "Allah yasa da gaske kake,yanzu dai kayi mana hoto dan tarihi"sarauniya suhaimat ta fada tana mai janyo fattu jikinta. Luuuf!! fattu tayi ajikin suhaimat tana mai jin wani irin sanyi acikin zuciyarta.hotuna Adeeb yayi musu kusan kala biyar awayarsa, hakama yayi musu awayar Sarauniya suhaimat ɗin. Da gyar suka rabu da juna cikin kewa da kaunar juna, fattu sai kuka take ta rungume Adeeb lokacin da suhaimat ta tafi rarrashinta yayi tayi da gyar ya samu tayi barci. Ammi kuwa sosai taji dadin tafiyar suhaimat,dan hankalinta sam bai kwanta ba ,gani take kamar zata iya gano wani abu game da fattu Yanzu damuwarta daya shine yadda ,zata bullowa lamarin Adeeb. Rashad ya farfaɗo ,saidai gaba ɗaya ankasa gane kansa ,dan kullum haka zaka ganshi shiru baya magana saidai kallo,abin yana matukar damun amma,haka zatayi ta kuka tana kallonsa,saidai kawai kaga hawaye yana bin fuskar Rashad din,ya rame sosai,dan baya wani cin abinci,ga karaya ajikinsa ta ko ina likitoci suna ta binciken kwakwalwarsa dan suna tunanin tanan ya sami matsala.saidai muce Allah ya bashi lafiya. Sam yanzu Adeeb baya kula tareeƙ ,haka zai zo yayi ta bashi haƙuri amma Adeeb bazai ce masa ko ci kankaba.duk da yadda yayi kewar tareeƙ ɗin cikin zuciyarsa. Abin yana yiwa tareek ciwo ,haka zai je gurin nanny yayi ta kuka ,saidai tabashi hakuri. Alhamdullah jikin fattu ya warke sosai,dan duk tabon ciwukanta ma babu,sosai shakuwa ta kara shiga tsakaninta da Adeeb,dan kuwa ya dawo da ita bangaren sa gaba ɗaya ,ya siyo mata sabbin kayan sawa ,da duk wani abu datake bukata. Yayin da gefe guda yake ci gaba da bincikensa akan al'amarin su Nazli da kuma sarƙar nan ta fattu,akan ammi ,saidai har yanzu ya kasa samun wata kwakwkwarar hujja da zai kama ammi da ita .dan haka ya kara yarda cewar hadin bakine na amma da nanny ,suke son hadashi da ammi. Bangaren rashad kuwa ,abin ba'acewa komai,dan har yanzu yana nan jiya iyau, baya uhhhm bare uhm -uhm .magani ta ko ina yi masa ake ,mai martaba da kansa abin yana damunsa,. Haka ma Adeeb yana jin ciwon abinda yayiwa ɗan uwan nashi,saidai koma menene shiyajawa kansa.kuma hakan bai hana shi neman masa magani ba . Shaikh lateef ya bawa Adeeb magungunan da zai rinka amfani dashi,kuma yana amfani dasu yadda ya kamata.zamu iya cewa yanzu abubuwa sun dan lafa agidan. Yanzu haka fattu ana mata lesson kullum ,zakuyi mamakin yadda fattu ta iya Yaren larabci sosai,tana ji kuma tana iya mayarwa, dan fattu akwai ƙwaƙwalwa,shikansa mai mata lesson yana mamakin hazaka irin ta fattu. Adeeb kullum yana kara nuna mata abubuwan da bata game ba.tayi kyau sosai ta goge idan ka ganta bazaka taba cewa itace ba. Kullum saisunyi waya da sarauniya suhaimat,sun shaku da juna sosai. Gimbiya Zulaihat ma tana nan tana nata shirin,dan yanzu kam tana ganin fattu na neman zama wata abar alfahari agidan,dan ta kereta ta ko ina,Shegiyar yarinya kyau kamar yar aljanu. Wannan kenan. Ammice zaune ƙaton falonta tana waya,dawowarta kenan daga gurin mai martaba,tana masa maganar ya dace ace zuwa yanzu Adeeb yayi aure ,dan shekaru na tafi kuma shine magajin fada. Dan haka abie yace ta zaba masa matar da zai aura ,tunda itace amminsa ,kuma yasan Adeeb bazaiki zabin ammin nashi ba.tun da dai shi ba kula yan mata yake ba. Cikin farin ciki kuwa ammi ta dawo ɗakinta ta kira kawarta. "Ƙawata ,albishirinki? Ammi ta fada cikin ɗoki. Bansan me akace mata ba ta dayan bangaren naji dai taci gaba da cewa"ai mai martaba ya bani damar zabawa Adeeb matar da zai aura,kuma ba kowa na zaba masaba face yar wajenki,maryam.kinga mun sami hanya cikin ruwan sanyi,da zamu cika burinmu akansa" ta fada cikin doki tana murmushi. Shiru na ɗan wani lokaci kafin taci gaba"ki rabu dashi, kawai ,nasan barazana ce yake min,amma kinsan bazan taɓa yarda Zulaihat ta auri Adeeb ba,dan kuwa ubanta zatayi wa aiki ba muba, Batun yarinyar da yazo da ita kuwa,na boye duk wata hanya danasan zai gane suwaye iyayenta na asali,kuma nasanya boka ya hana uwarta zuwa gasar nan ma gaba daya , Kinga har abada bazasu taba haduwa da junaba. Abu na gaba da zamuyi shine ,da zarar anyi auren nan,zamu sa ta kashe dan banza kowa ma ya huta, zan san yadda zanyi in shawo kan wancan mugun ya yarda ayi auren saimu kashe Adeeb din" Shiru ammi tayi tare da sauraron abinda ake fadi aɗaya bangaren. Kafin taci gaba"wllh ƙawata Ni kaina yarinyar nan na tsaneta ,bana don ganinta,Aduk lokacin dana ganta fuskar uwarta nake gani ,kuma ina tunano abinda ya faru abaya,dan haka itama kawar da ita zanyi kowa ya huta ,duk dana ɗauke sarƙar nan Tata,amma na nemeta na rasa ,kuma banganta awuyan yarinyar ba,dan haka ina tunanin bata koma gareta ba,ƙila dai nice na sauya mata gurin ajiya na manta" Shiru ammi ta sake yi ,kafin tace shikenan sai kinzo ma karasa maganar. Jikin fattu banda rawa da bari ba abinda yake ,zuciyarta sai neman tarwatsewa take , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!!wanann wace irin masifa ce haka,yanzu ammi tasan su waye iyayena dama ?kenan kashe Hamma zasuyi?me hakan ke nufi? kenan ammi ba itace mahaifiyar Adeeb ba?dan kuwa tasan ba ta yadda za'ayi uwa tayi yunkurin kashe ɗan ta, wai meke faruwa ne?wannan ɗin wane irin badakala ce kuma? Tsabar rawar da jikinta yakeyi bata san lokacin data buge wani flower vase dake ajiye agefenta ba ,ya fadi kasa ,jikake toshshs!! Ya fashe . Cikin tsoro da tazana fattu ,tayi sauri buya ajikin ƙofa tare da runtse idanunta. Ammi kuwa da sauri ta taso Dan ganin waye yayi mata labe ,har yaji sirri ta. Da mugun ƙarfi aka fizgi fattu akayi waje da ita ,buɗe baki fattu tayi da nufin kurma ihu,taji an toshe mata bakinta..... Waye ya dauke fattu? Me zai faru nan gaba? Muje zuwa anty mammy ce Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 67/68 _______________Da sauri ammi ta taso cikin tashin hankali da fargaba,dan kuwa tabbas tasan wani yaji me take cewa. Fattu kuwa tsabar ruɗewa da shiga tashin hankali tama rasa ina zata dosa,tsoro ya cika mata zuciya ganin ammi ta nufo inda take ,saidai cikin wannan yanayin ne taji an fizgeta da mugun ƙarfi anyi waje da ita.nan take tsoronta ya kara rubanya.buda baki tayi da nufin kurma ihu ,dan atunaninta masu kashe tan ne suka kamata.saidai gam!aka rufe mata baki,bata yadda zatayi ihu.kuma cikin wani irin sauri mai kama da gudu akayi waje da ita,ta wata hanya da bata nan ta shigo ba. Ammi kuwa tayi iyakar dubanta ,amma bata ga kowa ba,kuma tabbas tasan anshigo cikin dakin nan,to waye?dan duk ta kora yan aiki can farfajiyar gidan dan tasami damar yin wayarta. Ko dai Adeeb ne?kai bashi bane ,dan kuwa Adeeb baya zuwa gareta ba tare da yayi sallama ba.toko nanny ce ?kai idan nanny ce zan iya cimma ta kafin ta gudu,wai waye wannan yake son shiga rayuwata ne?waye yake son bakuntar lahira kwana kusa?na rantse da Allah idan na gano ko waye saina hukuntashi, hukunci mai tsanani.yanzu dole mu sake sabon tsari dan wannan kam ya rika ya lalace"ammi ta fada cikin zafin zuciya da kunar rai. Tana nan tsaye Zulaihat ta shigo dakin ba ko sallama,kawai ammi sai ganin mutum tayi bukut ya shigo cikin falon.guri ta nema ta zauna tare da ƙurawa ammi ido. Harara ammi ta Banka mata tana tunanin koma dai Zulaihat ɗin ce ta shigo dazu da tasan Zulaihat ba hankali gareta ba? "Ke Zulaihat kece kika shigomin daki dazu kina Min labe?"ammi ta fada cikin haɗe fuska. Wani shegen kallon Zulaihat ke jifan ammi dashi,kafin ta fara magana "lallai ma ammi har kina tunanin akwai wanda zan zauna inayiwa labe?to me zan labe naji,bayan duk wani tuggun da ake ƙullawa ina sane dashi,me kuma za'a boyemin ?kinsan Ni bana munafurci kai tsaye nake Abunda naga dama "Zulaihat ta faɗa cikin rashin kunya tana wani juya ido. Kallonta ammi tayi cikin tsantsar ɓacin rai da tsanar halayen ta na rashin kunya kafin tace " yanzu kina Min wannan gatsalin kike son na aura miki Dana?to wllh gara ki nutsu Dan bazan yarda ki auri Adeeb da wannan shegen halin naki ba,domin shirme zakiyi tayi mana,idan mun saki aiki"ammi ta fada cikin faɗa -fada. Wata irin dariya Zulaihat tayi tana kallon ammi kafin tace "Kinga ammi ki daina min tsawa keba uwata bace,ko iyayena lallaɓani suke ,kuma da kike cewa zan bata muku aiki,ku atunaninku idan anyi auren biye muku zanyi in cutar da abin sona,?wllh garama ku nutsu daga ke har daddy na Dan kuwa rungumar mijina zanyi musha soyayya ,kuma duk wanda yayi yunkurin cutar da shi ,wllh saina kashe mutum,kinsan nima na iya dabancin"Zulaihat ta faɗa cikin gadara tana kallon ammi ido cikin ido. Baki buɗe ammi ke kallon Zulaihat,lallai yarinyar nan ta wuce yadda suke tunani,Gara ta lallabata,karta jika mata aiki,dan haka cikin dan murmushin yake ammi tace "kai ƴata dadina dake baki san wasa ba,yanzu saiki maida abu gaske,ki kwantar da hankalinki,kinsan nima bazan taɓa bari a cutar min da Adeeb ba, dama nayi tunanin bakinsu ɗaya da mahaifi ki,shiyasa na fadi hakan"ammi ta fada cikin murmushin yaƙe tana hararar Zulaihat ƙasa ƙasa. "Ato Gara dai mutum ya kula wllh ,dan zan iya komai akan abinda nake so"Zulaihat ta faɗa tana mai gyara zamanta zuwa kwanciya,tare da lumshe idonta kamar zatayi barci. "Zanyi makaganinki daga ke har uban Maki shegiya"ammi ta fada cikin zuciyarta,tana shigewa daki,cike da tunanin mafita. Ba'a dire fattu a ko ina ba, sai cikin wani daki mai dan duhu, wanda kana iya ganin mutum ,amma bazakaga fuskarsa kai tsaye ba. Koda aka direta sam ba'asakar mata baki ba. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,sai ƙoƙarin cire hannun mutumin take daga bakinta, ammata kasa . Cikin nutsuwa da kwantar da hankali ya fara magana "ki nutsu ,niba cutar dake zanyi ba,koda na bude miki baki to karkayi ihu " Cikin hanzari fattu ke jinjina kanta idonta yayi zuru zuru ,burinta kawai tajita free. Ahankali ya dannan makunnar dake gefensa,nan take dakin yayi haske ta yadda kana iya ganin komai. Da sauri fattu ta daga idanunta tana kallon mutumin, "Hamma tareeƙ"ta fada cikin rawar murya,"ka bani tsoro Hamma tareeƙ,meke faruwa cikin gidan nan,wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana?fattu ta faɗa cikin muryar kuka tana kallon tareeƙ. Shima kallonta yake zuciyarsa na masa zafi ,yayi fatan ace Adeeb da kansa yaji wannan maganar ba wani ne yaji ba. "Ki kwantar da hankali ki fateema,da sannu zaki fahimci komai " Ya fada tare da ɗauko wayarsa yayi kira. "Ummee kuzo ina nan cikin dakin baya"haka kawai ya faɗa ya kashe wayar. Kallonsa fattu keyi jikinta har lokacin rawa yake ,tana cikin shock da zallar mamaki,kujera tareeƙ ya nuna mata tare da cewa"ki zauna anan fateema " jiki ba kwari fattu tabi bango ta zauna aƙasa ba tare da ta hau kan kujerar da tareeƙ ke nuna mata ba.zallar mamakin ammi da al'ajabi ta ke ɗawainiya da fattu,yanzu duk zaman da sukayi dama ammi tasan asalin iyayenta?kuma ita ta sace sarƙarta wacce take matsayin shaidar da zata sadata da iyayenta na asali?amma menene ribar ammi nayin hakan?wane amfani zata samu?lallai dole ta sanar da Hamma wannan maganar . Bude kofar da akayi ke ya katsar mata da tunaninta ,da sauri cikin tsoro ta kalli bakin ƙofar,nanny ce ta shigo ita da amma. Da sauri fattu ta mike cikin rawar jiki ta ƙanƙame nanny tare da sakin kuka mai ciwo da radadi," nanny wai zasu kashe min hammana ,kuma nima zata kasheni ,sannan tace tasan asalin iyayena ,amma bazata bari muhadu dasuba.nanny wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana,anya kuwa itace ta haifeshi ?fattu ta faɗa tana mai dago kanta tare da kallon nanny. Cike da tausayin fattu nanny ta riketa ajikinta Tana mai shafa bayanta ,alamun rarrashi,kafin tace "ki kwantar da hankalinki ɗiyata,ba abinda zai sameku da yardar Allah,kuma yau zan sanar dake alakar dake tsakanin Adeeb da amminsa" cewar nanny Tana me zaunar da fattu akan kujera. Amma kuwa tana tsaye ta kafe fattu da idanu,tabbas hasashenta ya tabbata ,dan kuwa ba tun yau take zargin cewa fattu yar sarauniya suhaimat bace,dan kuwa tasha ganin irin sarƙar wuyan Fattu atare da iyalin suhaimat,bayan nan sai kayi duba na tsanake zaka gano tsantsar kamar dake tsakanin fattu da suhaimat ɗin.aikuwa insha Allahu yau ba sai gobe ba zata sanar da fattu wacece ammi. Cikin kuka fattu ke kallon nanny kafin tace "Dan Allah nanny ki sanar dani ala'akar dake tsakanin hammana da kuma ammi,ko zuciyarta zata sami salama,ji nake kamar zan mutu,banson wani abu ya sami hammana nanny Ina kaunar hammana fiye da yadda nake son kaina idan wani abu ya sameshi wllh mutuwa zanyi"fattu ta faɗa cikin kuka mai ban tausayi. Hawaye nanny ta goge tana mai kallon fattu kafin tace "In Sha Allahu ba abinda zai sami magajin fada ki kwantar da hankalinki ɗiyata. Hannun fattu amma ta kamo cikin sanyin murya tace "kiyi shiru ,ki kuma kwantar da hankalinki,dan yau zaki san abubuwan da baki sani ba abaya,dan haka ki adana hawaye ki zai miki amfani nan gaba "cewar amma tana kallon fattu cikin tausayawa. Share hawayen kuwa fattu tayi tare da kafe nanny da ido,zuciyarta na bugawa kamar ana. Kada ganga. Ahankali nanny ta fara magana"ammi ba itace asalin wacce ta haifi Adeeb ba,amma itace wacce ta rike shi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararararmmmm gaban fattu ya bada sautin karar da saida ta kusan faduwa tana daga zaune. Ai Ni kaina saida na tsorata na jefar da wayar nan dan tsoron jin abinda nanny zata faɗa . Muje zuwa masoyan fattu da Adeeb . Sai mun haɗe anjima in Sha Allahu. Anty mammy ce Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 69/70 ___________Ahankali nanny ta fara magana ,tana cewa"Ammi ba ita bace asalin mahaifiyar Adeeb,amma itace wacce ta rikeshi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararrararaammm!!!gaban fattu ya bada ƙara, sakamakon jin maganar nanny datayi kamar saukar aradu, Da sauri ta dafe gefen kujerar da take kai,dan ji tayi kamar zata faɗi. Baki buɗe take kallon nanny cike da tsantsar mamaki,cikin rawar murya tace "nanny kina nufin ammi itace ta kashewa Hamma mahaifiyarsa?to amma me yasa Hamma yake mata kallon uwa?me yasa bai dauki mataki akanta ba?"fattu ta faɗa cikin rudani. Ajiyar zuciya nanny tayi kafin tace "saboda bashi da masaniya akan abinda ya faru,kuma ya yarda da ammi fiye da kowa,dan yana mata kallon uwa mahaifiyane,baya tunanin zata taba cutar dashi.ki saurare Ni da kunnen basira ,zaki ji abinda ya faru yanzun nan. "Sarauniya Nazli,ƴace agurin ƙarin baban mai martaba uwa daya uba daya,wato kenan ita da mai martaba ,yan uwan juna ne ,dan kuwa auren zumunci akayi musu. Suna kaunar juna matuka bayan anyi auren,suna zamansu lafiya cikin so da aminci, lokacin da akayi auren nasu,iyayen sarauniya Nazli duk sun rasu,hakan yasa take zaune a hannun mahaifiyar mai martaba ,dalilin hankali da nutsuwarta yasa mahaifiyar mai martaba ta zaba masa ita matsayin matar da zai aura inda ranar da aka daura musu aure aka naɗa shi matsayin sarkin misra. Shekara guda dayin aurensu Allah ya azurtata da zamu yaro , kyakykyawa abin so ga kowa, ranar suna aka rada masa suna adeeb. Adeeb ya taso cikin so da kauna, agurin iyayensa, da ma duk wani wanda yake fadar nan,yana da matukar hakuri ,hazaka ,ladabi da kuma biyayya. Nice wacce ke rainon Adeeb ,kasancewar mijina yana aiki acikin fadar nan,shine drivern dake tuka sarki da iyalinsa. Lokacin ina goyon dana tareeƙ ,dan haka na hadasu duka ina rainonsu,saidai ko da wasa ban taba hada tareeƙ da Adeeb matsayi daya ba,duk lokacin da zanyi musu wani abu saina farayiwa Adeeb,sannan nake yiwa tareek,ko wasa suke yi nakan sanya Adeeb matsayin shugaba ne tareeƙ kuma bafadensa.hakan yasa suka taso cikin kaunar juna da girmamawa,dan kullum nakan nusar da tareeƙ cewar Adeeb ɗan sarkine kai kuma dan bafaden sarkine,dan haka kada ka haɗa kanka da Adeeb . Sosai shakuwa ta shiga tsakanin Adeeb da tareeƙ,dan kuwa ko gurin sarki Adeeb zaije to dole saida tareeƙ ,kuma tun lokacin ƙuruciya tareeƙ ke kiran Adeeb da yallaɓai. Muna jin dadin zama da sarauniya Nazli,dan kuwa macece mai matukar girmama dan adam,ba ruwanta da nuna isa ko iko,akan kowa ,tana janmu ajikinta sosai ,hakan yasa kowa ke kaunarta cikin masarautar nan. Kwatsam batun karin auren mai martaba ya taso,kuma auren zaiyi shine da mata biyu a lokaci daya, dayar ƙánwar abokinsa ce wato amma,dayar kuma yar abokin babansa wato ammi. ko kaɗan sarauniya nazli bata tada hankalinta ba,koda mai martaba ya nuna tayi hakuri,shima bada son ranshi zaiyi auren ba ,nuna masa tayi ma tafi shi farin ciki tayi masu fatan alkairi ,duk da kuwa can ƙasar zuciyarta tana jin kishi da zafin abin aranta,amma haka ta daure ta nuna ba komai. Bayan anyi bikin mai martaba da matansa guda biyu,da farko ana zaune lafiya kowa na ba kowa girmansa,sai kuma abubuwa suka zo suka fara lalacewa,yau kaji wannan maganar gobe kaji waccan.ammi itace wacce ke haddasa komai,sam bata son zaman lafiya ta cika gutsiri tsoma,amma sarauniya Nazli bata kulata ,dan kuwa lokacin tana fama da laulayin cikinta na biyu. Amma ce ma ke dan maida mata martani, Kullum amma na zuwa gurin sarauniya Nazli tana kula da ita, sosai suke zaman lafiya a tsakaninsu ba gutsiri tsoma ko kaɗan,hakan kuwa ba ƙaramin bata ran ammi yake ba ,dan ita burinta kawai ta farraka su. Lokacin da sarauniya Nazli ta zo haihuwa kuwa ,cikin nasara ta haifi yaranta tagwaye duka mata, Masha Allah,karkuzo kuga kyau garin yaran nan,sosai kowa ke murna da samun yan yaran nan, Adeeb yana bala'in kaunar ya'yan nan,kullum yana kusa dasu yana musu wasa,shida tareeƙ ,wani lokacin hana daukar yaran ma suke,idan za'a daukesu suyi ta kuka kar'a taba musu kannai.kuma daidai lokacin ne amma ta fara laulayi itama. Sosai mai martaba yake jin dadin zama da matansa ,dan kowa na kokarin kyautata masa.koda labarin cikin amma ya sameshi yayi murna sosai . Wayyo ai tunda ammi ta kyalla ido ta gano ciki jikin amma,hankalinta yayi magun tashi,ya za'ayi haka ?an aurosu tare amma ita har yanzu ko batan wata bata taba yi ba?ina da sake wllh saita zubar da cikin Nan.shikenan saisuyi ta haihuwa ,su gaje masarautar ita ko oho? Ba irin abunda ammi batayi ba akan cikin rashad ya zube,amma hakarta bata cimma ruwa ba. Haka aka haifi Rashad , kyakykyawa dashi ,suna matuƙar kama da Adeeb,Adeeb yana son Rashad fiye da yadda yake san twince husna da haseena,kullum yana tare da Rashad shida tareeƙ ,barci ne kawai ke rabasu. Hakan yana dagawa ammi hankali,tun daga nan saita fito da sabon salo, wato ta fara jan yaran ajikinta,da farko sam Adeeb bai saki jiki da ammi ba ,dan shi irin yaran nan ne miskilai,idan Kinga dariyarsa to shida tareeƙ ne ko mai martaba da mommansa ,ko kuma ni,sai kuma Rashad da amma . Saidai yana da yawan kyauta ,yanzun nan zai baka abu yace na kyauta na baka,hakan yasa kowa ke kauanarsa sosai, Kusan tunda ga lokacin wasu da yawa ke kiransa da magajin fada,ciki kuwa hardanki.ciki kuwa harda Ni. Amma kasancewar ammi makirar mace ,ta san ta yadda zata ja hankalin mutum ,sai Adeeb ya fara yarda da ita,harta kai ta kawo yana kwana anan bangarenta.daga wannan lokacin ne kuma Adeeb ya fara tsiro da wata halayyar sam baya son Rashad yazo inda yake ,lokacin Rashad yana rarrafe,wai zai bata masa jiki,saidai idan shi yaga dama yayi masa wasa . Wata rana mijina ya dawo gida hankalinsa atashe,koda na tambayesa lafiya ?meke faruwa?nagansa cikin tashin hankali .nan yake sanar dani cewar ,yau ya kai ammi anguwa ,yana zaune yana jiranta, bata fitina, kawai saiya dan zagaya dan ya ware ƙafarsa ,yana zuwa saitin window yaji tana magana da wani mutum, kuma suna tattaunawa ne akan yadda zasu kawar da Adeeb harda tareeƙ,sannan yaji tana sanar da mutumin cewar aiki yayi kyau,dan yanzu sam Adeeb baya kaunar Rashad,baya son Rashad yazo koda inda yake ne.yanzu abinda take so shine a cire musa mahaifiyarsu daga ransu,ta yadda sai abinda tace suyi zasuyi, Tana son saita lalata musu tarbiyyar sun zama abin kwatance ,sun haddasawa iyayen su ciwon zuciya sun mutu,kafin ta kawar dasu,inya so ta gaji dukiyar mai martaba ita kadai. Hankalina yayi matuƙar tashi lokacin dana ji wannan maganar ,nan take na fara kuka ,ya zama dole na sanar da iyayen yaran nan,su kula da ƴaƴansu, Amma nasan sarauniya Nazli,koda na faɗa mata ,ita macece mai hakuri da tawakkali ba abinda zatayi akan hakan,zata iya cemin ma indaina kawo mata zancen wani,kowa yayi dai dai kansa. Dan haka gurin amma na nufa,ina kuka nake sanar da ita komai da mijina ya faɗa min,hankalinta yayi mugun tashi sosai,nan take ta tashi ta nufi gurin nazli cikin ɓacin rai, tana zuwa ta labarta mata komai ,sannan ta kara da cewa idan muka zuba ido fa zata lalata mana yara ,tayi musu asiri su rabu damu, dan haka ya zama dole mu taka mata burki"alokacin hankalin Nazli ya tashi,dan tasan amma bazata mata karya ba,kuma itama ta fuskanci sauyi daga gurin Adeeb ɗin,dan haka saitace zata dauki mataki akan abin muyi hakuri abi komai ahankali. Aikuwa Nazli da kanta ta je gurin ammi dan suyi magana akan yaran ,kuma tajene akan zata yi mata magana cikin hikima ta yadda tsoron Allah zai shigeta,abinda bata sani ba ,tuni ammi tayi nisan da bata jin kira. Tana zuwa dakin zata shiga ,tajiyo Muryar ammi tana waya , "Kun tabbata dai kun dauke yarinyar nan?kuma kun fitar da ita can wata kasar daban?bana son asami matsala ,so nake tayi nisa,nisa na har abada ,ta yadda bazata ƙara ganin yar ba,ai wllh dama na faɗa duk wanda yaci tuwo dani miya yasha. Shikenan ,zakaji alart. Tana gama faɗin haka ta ajiye wayar tana murmushi. "Suhaimat ,kinyi kuskuren auren wanda nake da burin aure,wllh nayi ta sanya rayuwarki cikin bakin ciki da tashin hankali,nasa an dauke ƴarki,an jefar da ita ,can wata kasar,ta yadda ko gawarta bazaki gani ba,na Tsaneki suhaimat,na tsani ganinki,kin auremin wanda nake so ,sannan kin haihu Ni ban haihuba, wllh sainayi ta shuka miki bakin cikin da zaiyi silar mutuwarki,bana ƙaunarki sam cikin raina.kuma keda ƴarki har abada"ammi ta fada cikin muryar azzalumai tana wani murmushi na mugunta. Jikin Nazli banda rawa ba abinda yake ,tashin hankali ya baibaye dukkan ilahirin jikinta. Yanzu zalumcin ammi harya kai kan yar uwarta?yar uwarta take cutarwa haka,ta sanya an sace Mata yarta an jefar,wannan wane irin rashin imani ne,? innalillahi. Cikin mugun ɓacin rai sarauniya Nazli ta buga kofar falon ammi da karfi ta shigo ciki,idanunta na zubda hawaye, Azabure ammi ta mike tsaye tana kallon momma,koba'a faɗa mata ba ,tasan cewar amma taji duk abinda take faɗi,dan haka kura mata ido tayi cikin yanayi na rashin gaskiya . Momma kuwa wato Nazli,cikin muryar kuka take magana da cewa"wllh ammi kiji tsoron Allah,ki sani zaki mutu ,kuma ,zaki koma gareshi,duk abinda kikeyi yana kallon ki,wacce irin zuciya gareki?da har yar uwarki ma bata tsallake sharri ki ba?to kisani tabbas sai naje na sanar da iyayenku abinda kika aikata azzaluma marar imani,sannan kisani,duk abinda kike aikatawa akan yayanmu to yazo kunnenmu ,kuma in sha Allah asirinki bazaiyi tasiri akan yaran mu ba,baki isa ki rabamu da suba.turrr da hali irin naki makira"momma na gama faɗin haka ta fice daga ɗakin cikin tashin hankali,har bata san inda take sanya ƙafartaba. Ammi kuwa tuni zuciyarta ta tsinke tsoro da fargaba sun gama baibaye zuciyarta,yanzu idan Nazli ta tona mata asirifa?me yakama tayi ,dole ta dauki mataki tun kafin maganar taje kunnen wanda bataso suji,wayyo Allah me Yakamata nayi"ammi ta fada cikin tashin hankali tana mai Safa da marwa. Kuka sosai Nazli keyi cikin dakinta tana mamakin zalunci irin na ammi,yanzu ashe mutum zai iya cutar da ɗan uwansa akan abin duniya?wannan wane irin rayuwane?turrrr da halin ammi Allah ya shiga tsakaninsu da ita . Tana cikin wannan halin ne, na isketa,dan haka cikin damuwa na tambayeta meke faruwa.nan take sanar dani abinda kunnenta yaji,hankalina yayi matuƙar tashi lokacin dan banyi tunanin rashin imaninta yayi nisa har haka ba. Nan sarauniya Nazli ke sanar dani gobe gobe zata je har gidansu ammi ta fadi abinda ammin tayi .naso in hanata Amma tace sam bazata iya zama da wannan abin cikin ranta ba ,dan kuwa har ta sanar da mai martaba tana son zuwa anguwa. Washe gari kuwa mijina ya dauki ammi da yaranta ,suka tafi,amma banda Adeeb ɗan lokacin ma suna makaranta .ko minti goma ba'ayin da fitarsu ba aka aiko cewar motar su ta kama da wuta sun kone kurmus... Kuka ne yaci karfin nanny ta kasa magana sai kuka da takeyi,haka ma amma banda kuka ba abinda takeyi, tareeƙ kuwa idanunsa sunyi jajur dasu,fuskarsa har wani karkarwa take. Fattu kuwa tsabar kuka har neman shiɗewa take,abubuwa sun taru sunyi mata yawa,ga tsantsar tausayin Adeeb ,ga kuma mamaki da al'ajabi cewar ammi yar uwar mahaifiyarta ce .sannan itace silar rabata da iyayenta...sosai take kuka ta ƙanƙame jikinta akan kujera,wani irin zafi take ji cikin zuciyarta ,duniya ba tabbas,yanzu dan uwa shine zai cutar da ɗan uwansa,ashe shiyasa ta dauke sarƙar nan yawa?dan bata yi tsammanin ina raye ba ,kuma saigashi Allah ya kawoni har mazaunin ta,shin wacece mahaifiyar tawa? Acikin yan uwan ammi.wayyo Allah na gode maka ya Allah ka sadani da ahalinsa cikin aminci.allah sarki baffana. Duk fattu ke wannan zancen cikin zuciyarta,tana jin kamar ba ita bace. Cikin kuka da muryarta wacce ke rarrabewa tace"wa...c..e..cc...ee ma...ha...I...fiya .....ta Kuma .....ina....za.....n...ga..nta." Muje zuwa ɗan jin ya zata kaya. Sorry jiya kuna ta jirana na ƙunƙuni shiru, bankin daɗi ne wllh. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 67/68 _______________Da sauri ammi ta taso cikin tashin hankali da fargaba,dan kuwa tabbas tasan wani yaji me take cewa. Fattu kuwa tsabar ruɗewa da shiga tashin hankali tama rasa ina zata dosa,tsoro ya cika mata zuciya ganin ammi ta nufo inda take ,saidai cikin wannan yanayin ne taji an fizgeta da mugun ƙarfi anyi waje da ita.nan take tsoronta ya kara rubanya.buda baki tayi da nufin kurma ihu ,dan atunaninta masu kashe tan ne suka kamata.saidai gam!aka rufe mata baki,bata yadda zatayi ihu.kuma cikin wani irin sauri mai kama da gudu akayi waje da ita,ta wata hanya da bata nan ta shigo ba. Ammi kuwa tayi iyakar dubanta ,amma bata ga kowa ba,kuma tabbas tasan anshigo cikin dakin nan,to waye?dan duk ta kora yan aiki can farfajiyar gidan dan tasami damar yin wayarta. Ko dai Adeeb ne?kai bashi bane ,dan kuwa Adeeb baya zuwa gareta ba tare da yayi sallama ba.toko nanny ce ?kai idan nanny ce zan iya cimma ta kafin ta gudu,wai waye wannan yake son shiga rayuwata ne?waye yake son bakuntar lahira kwana kusa?na rantse da Allah idan na gano ko waye saina hukuntashi, hukunci mai tsanani.yanzu dole mu sake sabon tsari dan wannan kam ya rika ya lalace"ammi ta fada cikin zafin zuciya da kunar rai. Tana nan tsaye Zulaihat ta shigo dakin ba ko sallama,kawai ammi sai ganin mutum tayi bukut ya shigo cikin falon.guri ta nema ta zauna tare da ƙurawa ammi ido. Harara ammi ta Banka mata tana tunanin koma dai Zulaihat ɗin ce ta shigo dazu da tasan Zulaihat ba hankali gareta ba? "Ke Zulaihat kece kika shigomin daki dazu kina Min labe?"ammi ta fada cikin haɗe fuska. Wani shegen kallon Zulaihat ke jifan ammi dashi,kafin ta fara magana "lallai ma ammi har kina tunanin akwai wanda zan zauna inayiwa labe?to me zan labe naji,bayan duk wani tuggun da ake ƙullawa ina sane dashi,me kuma za'a boyemin ?kinsan Ni bana munafurci kai tsaye nake Abunda naga dama "Zulaihat ta faɗa cikin rashin kunya tana wani juya ido. Kallonta ammi tayi cikin tsantsar ɓacin rai da tsanar halayen ta na rashin kunya kafin tace " yanzu kina Min wannan gatsalin kike son na aura miki Dana?to wllh gara ki nutsu Dan bazan yarda ki auri Adeeb da wannan shegen halin naki ba,domin shirme zakiyi tayi mana,idan mun saki aiki"ammi ta fada cikin faɗa -fada. Wata irin dariya Zulaihat tayi tana kallon ammi kafin tace "Kinga ammi ki daina min tsawa keba uwata bace,ko iyayena lallaɓani suke ,kuma da kike cewa zan bata muku aiki,ku atunaninku idan anyi auren biye muku zanyi in cutar da abin sona,?wllh garama ku nutsu daga ke har daddy na Dan kuwa rungumar mijina zanyi musha soyayya ,kuma duk wanda yayi yunkurin cutar da shi ,wllh saina kashe mutum,kinsan nima na iya dabancin"Zulaihat ta faɗa cikin gadara tana kallon ammi ido cikin ido. Baki buɗe ammi ke kallon Zulaihat,lallai yarinyar nan ta wuce yadda suke tunani,Gara ta lallabata,karta jika mata aiki,dan haka cikin dan murmushin yake ammi tace "kai ƴata dadina dake baki san wasa ba,yanzu saiki maida abu gaske,ki kwantar da hankalinki,kinsan nima bazan taɓa bari a cutar min da Adeeb ba, dama nayi tunanin bakinsu ɗaya da mahaifi ki,shiyasa na fadi hakan"ammi ta fada cikin murmushin yaƙe tana hararar Zulaihat ƙasa ƙasa. "Ato Gara dai mutum ya kula wllh ,dan zan iya komai akan abinda nake so"Zulaihat ta faɗa tana mai gyara zamanta zuwa kwanciya,tare da lumshe idonta kamar zatayi barci. "Zanyi makaganinki daga ke har uban Maki shegiya"ammi ta fada cikin zuciyarta,tana shigewa daki,cike da tunanin mafita. Ba'a dire fattu a ko ina ba, sai cikin wani daki mai dan duhu, wanda kana iya ganin mutum ,amma bazakaga fuskarsa kai tsaye ba. Koda aka direta sam ba'asakar mata baki ba. Fattu kuwa banda rawa ba abinda jikinta keyi,sai ƙoƙarin cire hannun mutumin take daga bakinta, ammata kasa . Cikin nutsuwa da kwantar da hankali ya fara magana "ki nutsu ,niba cutar dake zanyi ba,koda na bude miki baki to karkayi ihu " Cikin hanzari fattu ke jinjina kanta idonta yayi zuru zuru ,burinta kawai tajita free. Ahankali ya dannan makunnar dake gefensa,nan take dakin yayi haske ta yadda kana iya ganin komai. Da sauri fattu ta daga idanunta tana kallon mutumin, "Hamma tareeƙ"ta fada cikin rawar murya,"ka bani tsoro Hamma tareeƙ,meke faruwa cikin gidan nan,wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana?fattu ta faɗa cikin muryar kuka tana kallon tareeƙ. Shima kallonta yake zuciyarsa na masa zafi ,yayi fatan ace Adeeb da kansa yaji wannan maganar ba wani ne yaji ba. "Ki kwantar da hankali ki fateema,da sannu zaki fahimci komai " Ya fada tare da ɗauko wayarsa yayi kira. "Ummee kuzo ina nan cikin dakin baya"haka kawai ya faɗa ya kashe wayar. Kallonsa fattu keyi jikinta har lokacin rawa yake ,tana cikin shock da zallar mamaki,kujera tareeƙ ya nuna mata tare da cewa"ki zauna anan fateema " jiki ba kwari fattu tabi bango ta zauna aƙasa ba tare da ta hau kan kujerar da tareeƙ ke nuna mata ba.zallar mamakin ammi da al'ajabi ta ke ɗawainiya da fattu,yanzu duk zaman da sukayi dama ammi tasan asalin iyayenta?kuma ita ta sace sarƙarta wacce take matsayin shaidar da zata sadata da iyayenta na asali?amma menene ribar ammi nayin hakan?wane amfani zata samu?lallai dole ta sanar da Hamma wannan maganar . Bude kofar da akayi ke ya katsar mata da tunaninta ,da sauri cikin tsoro ta kalli bakin ƙofar,nanny ce ta shigo ita da amma. Da sauri fattu ta mike cikin rawar jiki ta ƙanƙame nanny tare da sakin kuka mai ciwo da radadi," nanny wai zasu kashe min hammana ,kuma nima zata kasheni ,sannan tace tasan asalin iyayena ,amma bazata bari muhadu dasuba.nanny wacece ammi ?meye alaƙarta da hammana,anya kuwa itace ta haifeshi ?fattu ta faɗa tana mai dago kanta tare da kallon nanny. Cike da tausayin fattu nanny ta riketa ajikinta Tana mai shafa bayanta ,alamun rarrashi,kafin tace "ki kwantar da hankalinki ɗiyata,ba abinda zai sameku da yardar Allah,kuma yau zan sanar dake alakar dake tsakanin Adeeb da amminsa" cewar nanny Tana me zaunar da fattu akan kujera. Amma kuwa tana tsaye ta kafe fattu da idanu,tabbas hasashenta ya tabbata ,dan kuwa ba tun yau take zargin cewa fattu yar sarauniya suhaimat bace,dan kuwa tasha ganin irin sarƙar wuyan Fattu atare da iyalin suhaimat,bayan nan sai kayi duba na tsanake zaka gano tsantsar kamar dake tsakanin fattu da suhaimat ɗin.aikuwa insha Allahu yau ba sai gobe ba zata sanar da fattu wacece ammi. Cikin kuka fattu ke kallon nanny kafin tace "Dan Allah nanny ki sanar dani ala'akar dake tsakanin hammana da kuma ammi,ko zuciyarta zata sami salama,ji nake kamar zan mutu,banson wani abu ya sami hammana nanny Ina kaunar hammana fiye da yadda nake son kaina idan wani abu ya sameshi wllh mutuwa zanyi"fattu ta faɗa cikin kuka mai ban tausayi. Hawaye nanny ta goge tana mai kallon fattu kafin tace "In Sha Allahu ba abinda zai sami magajin fada ki kwantar da hankalinki ɗiyata. Hannun fattu amma ta kamo cikin sanyin murya tace "kiyi shiru ,ki kuma kwantar da hankalinki,dan yau zaki san abubuwan da baki sani ba abaya,dan haka ki adana hawaye ki zai miki amfani nan gaba "cewar amma tana kallon fattu cikin tausayawa. Share hawayen kuwa fattu tayi tare da kafe nanny da ido,zuciyarta na bugawa kamar ana. Kada ganga. Ahankali nanny ta fara magana"ammi ba itace asalin wacce ta haifi Adeeb ba,amma itace wacce ta rike shi bayan ta kashe mahaifiyarsa." Dararararmmmm gaban fattu ya bada sautin karar da saida ta kusan faduwa tana daga zaune. Ai Ni kaina saida na tsorata na jefar da wayar nan dan tsoron jin abinda nanny zata faɗa . Muje zuwa masoyan fattu da Adeeb . Sai mun haɗe anjima in Sha Allahu. Anty mammy ce Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 71/72 _______________Cikin kuka da rawar murya ,fattu ta fara magana "wa...ce...ce .ma...haifi.......yata?kuma ina ne take ?sannna me ya faru da Hamma na bayan rasuwar momma?"ta fada cikin kuka mai ban tausayi. Saida Nanny ta share hawayen idanunta kafin taci gaba da fadin" lokacin da labarin hadarin nan ya iske mu,mun shiga tashin hankali bana wasa ba,dan kuwa nan take mai martaba ya yanke jiki ya fadi asume,gaba ɗaya faɗa ta rikice da kuka da alhinin rashin mutuniyar kirki kamar Momma, wacce ke son talakawa da taimakonsu. Lokacin da Adeeb suka dawo daga makaranta,ya ji labarin mutuwar Mommansa da kannansa,shima sumansa uku,saida gyar aka samo kansa,tun daga wannan lokacin Adeeb ya kara komawa shiru shiru,bashi da aiki sai tunani haka zaki ganshi zaune shi kadai yayi tagumi yana zubda hawaye,saida aka tashi tsaye akansa da addu'oi kafin ya dan warware. Mai martaba kuwa,ciwon zuciya ne ya kamashi, saboda tsabar damuwa da tunani. Yana matukar kaunar Momma,Dan macece mai hakuri da shiga rai. Tana faranta masa rai,duk abinda yace tayi bata ko musu akan umarninsa. Bayan sadakar bakwai ne ,aka fara bincike akan abinda ya sami motar tunda kai tsaye motar ta kama da wuta, kai tsaye aka gano bomb aka sanyawa motar.dan haka wannan hadimin mai kula da harkar motoci shi aka fara kamawa. Anyi -anyi ya fadi abinda yayiwa motar amma yaƙi,shidai yace tabbas bomb ɗin ne ajikin motar,saidai idan ya fadi wadanda suka sashi,to zasu kasheshi ne. Dukan tsiya akayi masa tare da kulleshi akurkuku. Cikin dare muka shirya zuwa gareshi,dan ya faɗa mana wadanda suka sa sashi,akan idan ya faɗa zamu sakeshi ya gudu. Amma saidai me?lokacin da mukaje, tuni Ammi ta riga mu zuwa,tana tsaye ita da wani mutum wanda ya nannaɗe fuskarsa da bakin gyalle.ta yadda ba wanda zai gane fuskarsa. "Wato so kake ka tona mana asiri ko?lallai kayi babban kuskure,dama ko kafada ko karka faɗa dole ne ka baƙunci lahira, tunda har kashigo hannu, kuma kasanar dasu da gaske bomb ɗinne ajikin motar,to watarana idan kaji azaba zaka sanar dasu mune muka saka ka sanya bomb din Dan haka yau zaka bi su Nazli kaima"Ammi ta fada tana mai dagowa daga sunkuyon da tayi tana yiwa mutumin magana. "Kuyi min rai, ranki ya dade,wllh bazan ce kune kuka sani na aikata wannan aikin ba,dan Allah karki kasheni" mutumin ya faɗa galabaice dan yaci duka dazu. "Kai!!! sakaran bawa, rufe mana baki, mu zakayiwa magiya mu gyaleka?wllh baka isaba,dole ka mutu dama baka da wani amfani agaremu, tunda kasan sirrinmu dole ka mutu"yana gama faɗin haka ya shaƙe bawan nan ,tun yana turje turje har ya daina alamun rai yayi halinsa. Gaba dayanmu dagani har Amma kuka muke jikinsu na rawa,tsabar tsoro da razani.wanene wannan wanda ke taimakawa Ammi wajen aikata ta addancinta?ta yaya zamu gane shi ?shine abinda ke ta yawo cikin kwakwalwarmu.amma bamu da amsa. Ganin yadda amma ke kuka kamar ranta zai fice ,gashi jikinta sai rawa yake,yasa nayi saurin janyeta dan barin gurin. Saidai agarin guduwa muka bigi wani bokiti ya fadi kasa yayi kara sosai.wanda ya jawo hankali su Ammi. Gudu muka farayi tun karfinmu, dan kuwa akwai tazara sosai tsakanin cikin faɗa da kuma sijin ɗin. Suma basu fasa ba kuwa suka biyo mu. Ganin zasu cimmana yasa Amma ta ce in buya,karsu ganni, ita zata tsaya ayi wacce za'a . Dan Ni zasu iya kasheni nan take ,amma ita tasan yadda zatayi. Haka na buya jikin wasu bishiyu.ta yadda bazasu ganni ba,amma Ni ina hango su dajin duk abinda suke fadi. Koda suka cimma Amma tana zaune tana numfarfashi, tsayawa sukayi akanta suna kare mata kallo. Ammi ce cikin ɓaci rai tace "dama nayi tsammanin kece,dan kuwa nasan ba wani dan kasadar da zaiyi yunkurin bin bayana ɗan ji da ganin sirrina.to kingani, kuma kinji,hankalinki ya kwanta,amma wllh idan naji wata magana akan abinda kika gani na rantse da Allah saina kashe danki da adeeb,kisa mafi muni,kuma na lakamiki kisan, nace ke kika kashesu, kuma kinsan zan iya. abinda yasa bazan kashe kiba yanzu, ina son kiga yadda zan lalata rayuwar yaranku ,insanya kiyayya atsakaninsu,ta yadda wataran daya shi zai zamo ajalin daya. Kuma kinsan menene ke nake so kizabi wanda zai zamo ajalin wani acikinsu"Amma ta kare maganarta tana dariya da kallon Amma. Kuka kawai Amma keyi, tana jinjina rashin imani irin na Ammi,mace kamar kafura?sam ba Allah cikin ranta.Amma na kuka take rokon Ammi akan ta gyale musu yara ,taji tsoron Allah,duk abinda take yana kallonta.Amma cikin rashin imani Ammi ke cewa "shikenan Ni zan zaba da kaina,nasan kina son danki,dan haka zan miki adalci yazamo shine zai kashe Adeeb "ta fada tana wani ware hannu da daga gira. Cikin sauri Amma tace "a'a karki kashe Adeeb,gara Rashad ya mutu amma dan Allah karki cutar da Adeeb Maraya ne,zuciyarsa akarye take karki illatashi na roƙeki"Amma ta faɗa cikin kuka. "Wow zabi mai kyau,kin zabi dan kishiya akan danƙi ko?lallai kin ciki shashasha,shikenan duk abinda zanyi akan su, naki idone ,daidai da rana daya kika yi min wata magana saina kashe Adeeb kinsan banda asara,bansan ciwon makida ba"tana gama faɗin haka ta karasa kusa da wannan mutum da suke tare,wanda dama yana tsaye dan nesa dasu yana kallon hanya. Saida suka bacewa ganinmu sannan na ƙaraso gurin amma,wacce ke kuka sosai.haka na kamata muka koma cikin fada,zuciyoyinmu sam ba dadi. Tun daga wannan lokacin Adeeb ya daina yiwa amma magana ,sai harara da bakaken maganganu,masu nuni da cewar yana zargin tana da hannu wajen kashe Momma.kuma nasan duk sharrin Ammi ne.kuma Daidai da rana daya Amma bata taɓa kula Adeeb ba saidai tayi ta kuka. Adaidai lokacin ne kuma suka tafi Singapore karatu.inda Adeeb yayi karatu bangaren likitanci,tareeƙ yayi karatun sa na koyon aikin jirgi,shikuma Rashad injiniya ne. Bayan dawowarsa daga karatune kuma babban tashin hankali ya samemu, na rasa Adeeb da akayi sama ko kasa, kwanansu uku da dawowa daga Singapore akawayi gari ba Adeeb ba labarinsa.duk inda ya kamata aje nemansa anje amma babushi,lokacin kuma da ya dawo daga Singapore,yana da tarin dukiya wacce shi kansa baisan adadinta.dan dan kasuwane mai neman na kasan,bai damu da matsayi ko mulkin gidansu ba ,yana da kamfanoni da dama akasashe da yawa,ciki harda nigeria.hakan yasa Adeeb ya iya Yaren Hausa sosai,dan darasi yake dauka na musamman akan bangaren. Dan haka lokacin da aka rasa Adeeb,tareeƙ shine yaci gaba da kula da duk wasu al'amura na dukiyar Adeeb .har Allah yayi dawowarsa ta silarki, Ashe kema rabon ki sadu danaki iyayen ne,kuma ba kowa bace mahaifiyarki, face sarauniya suhaimat" Baki buɗe fattu ke kallon Nanny ,Tana jinjina kai cike da jinjinawa ƙudirar Ubangiji,yanzu dama innar yan biyu itace mahaifiyarta? ashe shakuwar da sukayi ta lokaci ɗaya ba banza ba?waɗan kyawawan yaran kannantane?wayyo Allah na gode maka Allah mai yadda yaso ga bawansa. Allah Sarki hammana yaga rayuwa,ya hadu da ƙaidin matar uba.wacce yakewa kallon muguwa itace masoyiyarsa. Ita kuma wacce ya dauka uwa itace ke son ganin bayansa.lallai yazama dole In fahimtar da hammana. Cikin kuka da sarkewar murya fattu tace "amma waye yayiwa Hamma asiri ya zama maciji? Ajiyar zuciya Amma tayi ta fara magana akaron farko,tun zamansu aɗakin, tace "wannan ne har yanzu muke son sani,dan bamu da tabbacin Ammi ita tayi masa asirin, saidai muna zargin wannan mutumin da muka kasa sanin ko waye yana da hannu akan al'amarin"Amma ta faɗa tana share hawaye. Hannunta fattu ta kama cikin kuka,tace "lallai Amma kincika mutum mai halacci, kin sadaukar da rayuwar danki,dan ki ceci dan kishiya,nayi miki alkawarin in Sha Allah komai zai dai daita. Hamma zai dawo gareki matsayin uwa da data,sannan rashad zai zamo abin alfahari gareki. Sai yanzu na gane wannan abinda ya faru dani itace ta shirya komai,dan kuwa ita ta kaini bangaren da kanta,kuma ta kulle ƙofofin, sannan ita ta dauke sarkata wacce baffana yace itace shaidar da iyayena zasu gane Ni da ita." "Na sani ƴata,nasan itace ta shirya komai, sannan tun ganin farko da nayi miki nake ayyana ke yar sarauniya suhaimat ce ,dan kuwa akwai kamar ta atare dake .ina fatan Allah ya bamu sa'a akan abinda muke shirin aikatawa na alkairi "cewar amma. "Nanny kema kiyi haƙuri komai zai daidaita in Sha Allah"fattu ta faɗa tana rungume nanny cikin kuka. Kukan nanny ma keyi,tace "Allah ya amince ƴata. Kallon tareeƙ tayi tace" Hamma tareeƙ kayi hakuri in Sha Allah abokinka ,kuma dan uwanka,zai dawo gareka"jinjina kai yayi tare da saurin share hawayen daya gangaro masa,yana murmushi. "Amma kibi komai ahankali yata,hammanki ya aminta da Ammi sosai ,ta yadda baya ganin laifin ta ko kaɗan"amma ta faɗa tana shafa kan fattu. Jinjina kai fattu tayi tace "In Sha Allah Amma zan kula" Adeeb kuwa,gaba ɗaya ya duba ko ina baiga fattu ba ,hankalinsa ya tashi sosai,ina kuma taje?ko wani abune ya faru da ita?"ya Salam"ya faɗa yana mai fitowa daga part ɗin nashi cikin sauri. Kicibis sukayi da fattu tana shirin komawa bangaren nashi,dan Nanny ce tace ta koma kar Adeeb ya ganta anan yayi wani tunanin, Kallonta Adeeb yayi idanunta sunyi mugun jaaa, cikin hanzari ya kamo kafaɗunta yana girgiza kai,gabanshi na faduwa"me yasameki? Wani ne yayi miki wani abu? Ko Rashad ne ?"ya faɗa cikin ruɗu yana duba jikinta. Ita kuwa fattu kallonsa kawai take cikin tausayawa,yana cikin matsala babba,amma shi Sam baigani,zuciyarsa da idanunsa sun rufe,ya rike azzulamar uwa matsayin mai kaunarsa.jikinsa ta fada tare da sakin wani sabon kukan mai tsuma zuciya. Hankalin Adeeb gaba ɗaya ya tashi,jikinsa har rawa yake ,tana rungume ajikinsa ya bude part dinsa suka shige ciki,sai kuka fattu keyi harda shashsheka. Kai tsaye cikin daki ya wuce da fattu,bakin gado ya samu ya zauna tare da rungumeta ajikinsa ,yana jin damuwarsa na kara yawaita,zuciyarsa kamar zata fashe . "Am sorry Hulwa ki sanar dani abinda ke damunki zuciyata na min zafi,bazan iya jurar ganinki cikin damuwa hakaba "Adeeb ya faɗa kamar zaiyi kukan shima. Fattu dai taki cewa komai sai kuka take tare da kara kankameshi.ganin irin kukan da takeyi ne ,kuma baisan me zai mata tayi shiru ba ,ya sanya Adeeb ɗago kanta,ba tare da bata lokaciba kawai ya haɗe bakinsu guri ɗaya.ɗiff kukan fattu ya dauke,sai ajiyar zuciyarsu kake ji,cikin ƙankanin lokaci suka lula wata duniyar ,kasancewar Adeeb yana cikin damuwa da rashin nutsuwa,hakan ya kara ingiza shi cikin tsantsar bukatuwa da son kasancewa da fattu. Ita kuwa fattu,tsabar tausayinsa da tashin hankali,yasa ta sakarmasa jikinta yake sarrafa ta yadda yaso. Gaba ɗaya sun fice daga hayyacinsu,tun abu yana karami harya girmama, dan takai ga Adeeb ya raba su da kayan jikinsu banda rawa ba abinda jikinsa keyi,ita kuwa sai wani ƙara rukunkumeshi take tare da kiran sunansa cikin wata irin murya. "Hamma ka bari ,Hamma! hammana!!kawai take iya fadi tana kara shigewa jikinsa. Cikin murya mai cike da tsantsar bukatuwa da ficewar hankali Adeeb yace"h....uul...wa ki....n.amin..ce...dani.....matsayin ....... Abo...kin rayuwa? Kin amince na kusanceki........ Danƙari!!! masu karatu ya kenan?Hulwa kuwa zata amince ? Me zai biyo baya ? Muje zuwa Mrs babi ce 💘💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 75/76 💥🔥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 🔥💥🔥💥🔥💥🔥🔥💥 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji💃🏻💃🏻💃🏻🔥 Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji 🔥💥 Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan💥🔥💃🏻 Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa😉😉 Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki👍🏼💃🏻💃🏻 Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc 💥🔥 Kalolin tsumi👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono raƙumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar HQ💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida🥰🥰🥰🥰🥰👍🏼👍🏼👍🏼👍🏼 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah🤝🏼🤝🏼 Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera sokoto state💥🔥💥🔥💃🏻 ________________Kasa ƙarasa maganar tareeƙ yayi,kawai ya durƙushe agurin,tare da sakin kuka kamar wata mace. Da ƙarfi Adeeb ya runtse idanunsa,sakamakon jin kukan tareeƙ da yayi,yasan tareeƙ jarumin namijine,lallai abinda zai sanya shi kuka babban abune,nan take shima zuciyarsa tayi rauni idanunsa ya cika da kwalla,bazai iya yin fushi da tareeƙ na tsawon lokaciba, dan yana kaunar tareeƙ har cikin ransa.dan haka ahankali ya juyo tare da karasowa inda tareeƙ ke durƙushe yana kuka. Kafadun tareeƙ ya kama,tare da miƙar dashi tsaye. Kallon juna suke cike da kewa,ahankali tareeƙ yace"yallaɓai, am sorry"kawai ya faɗa ƙirjin Adeeb suka rungume juna. "Am sorry yallaɓai,ka sani ba zamu taba cutar da kaiba,munyi haka ne dan fitar dakai daga cikin duhun da kake ciki,amma ka yafemana,nanny Tana cikin damuwar rashinka agareta"tareeƙ ta faɗa cikin muryar kuka. Ahankali Adeeb ya sanya bayan hannunsa ya share hawayen daya zubo daga idanunsa na dama,zuciyarsa na masa zafi,yana jin dama ba nanny ce ta bashi wannan labarinba, da saiya horata,ta yadda zata faɗa masa gaskiyar al'amari. Ahalin yanzu he was compused,ya rasa me yakamata yayi. Ɗago da tareeƙ yayi daga jikinsa,ya sanya hannu yana share masa hawayen idanunsa,kafin ya fara magana cikin nutsuwarsa ta ko yaushe"tareeƙ na yarda daku,nasan bazaku taba cutar daniba,saidai abinda kuka zo min dashi,ba abune da hankali zaiyi saurin dauka ba,nayi bincike kuma ina kanyi,amma har yanzu Banga wani abu da zai nuna min ammi itace da hannu wajen hadarin mommana ba, me ma zaisa tayi hakan?dan haka ina son mu bar maganar nan Please" Adeeb ya fada yana kallon tareeƙ. Jinjina kai tareeƙ yayi cikin rashin jin dadin yardar da Adeeb ya bawa Ammi,azzalumar mace,amma In Sha Allahu yasan zasuyi nasara wataran,tunda yanzu fattu ma tasan komai. Murmushi Adeeb yayi tare da ɗan marin kumatun tareek,kamar yadda yake masa idan yayi abin da ya burge Adeeb ɗin. "Good boy,ka ce ina gaida nanny"Adeeb ya faɗa tare da nufar cikin part din nashi. Cikin ɗoki da farin ciki,tareeƙ yace"yallaɓai Madam fa?fatan tana lafiya?" Juyowa Adeeb yayi fuskarsa ɗauke da murmushi kafin yacewa tareeƙ "she's fine"tare da shigewa ciki. Koda ya shiga tuni fattu ta farka daga barcin,tana kwance kan gado tana kuka. Da sauri ya karasa gareta ya zauna tare da kamo hannunta,cike da kulawa yake tambayar ta"sannu Hulwa,meke damunki yanzu?ina ke miki ciwo?me zaki ci"ya jero mata waɗan nan tambayoyin ajere. Fattu kuwa jin muryarsa yasata saurin runtse ido,tare da turo baki tana kukanta,taki yi masa magana. "Sorry hulwatee ƙurratu ainun, me kike so?"ya faɗa yana kai mata kissing a lips dinta da sukayi jajur dasu,sai sheƙi suke. Cikin Muryar shagwaba da fattu ta koya yanzu tare da tarin ƙuruciya tace "Ni ka kyaleni Hamma,ba ruwana da kai bazan sake kulaka ba"ta fada cikin Muryar kuka tana ɗan murza ido. "Ayya hulwata idan kika daina kukani kuma, waye zai bani nishadi da farin cikin da kika bani yau?kinga shikenan kina ji kina gani hammanki zai shiga gararin rayuwa"ya faɗa cikin marairaita murya kamar zaiyi kuka. Ahankali fattu ta ɗan buɗe idanunta daya,dan ganin da gaske kukan yake,aikuwa tana budewasuka haɗa ido,da sauri ta mayar da idonta ta kulle gabanta na faɗuwa,wllh kunyar Hamma takeji,Bama idan ta tuna cewa ya gama ganin jikinta,sai taji kunyarsa ta lunku akan wacce takeji ɗin. Murmushi Adeeb yayi yana mai shafa kwantaccen gashin gaban goshin ta yace"Please Hulwa ki faɗa min ina ne yake miki ciwo kinji"ya faɗa cikin muryar rarrashi,asaitin kunnenta. "Ni bayana ne yake min ciwo,da ƙasana,kuma fitsari nake sonyi amma na kasa tashi"fattu ta faɗa tare da sanya kuka . Rungumeta yayi zuwa jikinsa,yana mai jin tausayinta sosai cikin ransa."ayya Hulwa ki daina kuka zai daina miki zafin kinji?amma sai kin daina wannan kukan,In kuma ba haka ba saidai asakeyin irin na dazun,shine zaki daina jin zafi"Adeeb ya faɗa cike da zolaya fuskarsa ɗauke da murmushi. Da sauri fattu ta ɗan zabura tare da buɗe idanunta ,da suka ɗan yi jaaa, tace "a'a wllh baza'a ƙarayi ba har abada,bana so "ta fada tana turo masa baki.dariya yayi har fararen haƙoransa suka bayyana reras kwanin sha'awa.kafin yace "shikenan Hulwa yanzu bari na taimaka miki kiyi fitsari sai kiyi alwala ko?In yaso saikici abinci da magani ki kwanta,shikenan zakiji ki garas kin warke "ya fada yana ƙoƙarin kamata dan ta mike tsaye. "Ni da kaina zan tashi,karka rakani ko ina,ba nace mun bata ba"fattu ta faɗa tana turo baki. Kallonta Adeeb yayi tare da sakin murmushi,ashe Hulwa ma ta iya rigima haka?ji yadda take turo masa wannan dan karamin bakin nata,kamar ba ita bace Sarkin tsoron nan da kunya,lallai yau Hamma yayi laifi.adeeb ya faɗa cikin ransa yana murmushi,sosai take burgeshi idan tana masa wannan shagwbar, yakanji kaso casa'in na damuwarsa ya goge. Fattu kuwa cikin karfin hali ta sake yunkurawa zata mike,amma ina,wani sautin ƙara da bayanta ya bada shine yasa ta komawa da sauri tare da riƙe ƙugunta"wayyo Allah ƙuguna,wllh Hamma ka karyamin ƙugu bazan yarda ba saika biyamin"ta fada tana ɗan kukan shagwaba. Da sauri Adeeb ya tarota yana faɗin"yi ahankali hulwa,bazaki iya tashi bafa, ki barni da hamman nan tunda ya karya miki ƙugu ko,saina hukuntashi,dan yayi babban laifi wa hulwata"ya faɗa yana janyota jikinsa.da gyar take takawa suka nufi toilet,ko wajen fitsarin ma da gyar ya samu tayi,dan tace idan tayi gurin zafi zai mata . Ruwan zafi ya bata tayi tsarki ,sannan tayi alwala suka fito. Bayan ta isar da salla ne ya bata abincin da aka shirya musu akan daining,farfesun kayan ciki ya bata,mai zafi da dan yaji.kuma ta ɗan ci sosai .sallar ishsha tayi ya bata magani ta sha da gyar,sannan ya kwantar da ita akan gado tare da lullubeta. Zama yayi bakin gadon yana shafa kanta tare da rarrashinta cikin malamai masu dadi har tayi barci. Murmushi yayi tare da sumbatar kumatunta sannan ya fita zuwa gurin ammi,bayan ya kulle part din nasa da security. Ammi kuwa tana can garden ɗinta,inda suka saba haduwa da mai nannaɗaɗɗiyar fuska,to yauma dai shine yazo,dan haka suna zaune acan cikin garden ɗin. Magana yake wa ammi fuskarsa arufe kamar kullum"ki tabbata kin aikata kamar yadda na faɗa miki,dan kuwa wannan gubar idan har yaci abinci da ita,to saidai wani ba shiba,kuma ba wanda zai zargi wani abu,dan kuwa zata lalata masa kayan cikinsa ne ahankali, ta yadda badaga cin abincin gubar zatayi aiki ajikinsa ba,kinga da zarar ya mutu,zuciyar ubansa zata buga,bugawar da na tabbata zata zamo ajalinsa ne,shikenan mun jefi tsuntsu biyu da tarko daya"mutumin nan ya fada cikin salo na kwarewa a mugunta, yana mai jingina bayansa jikin kujerar da yake kai. Ajiyar zuciya ammi ta sauke,tana jin wani irin farin ciki aranta."lallai kayi tunani mai kyau,shikenan idan akayi haka ,burin kowa zai cika,daga Ni har kai.shikuwa wancan ya riga ya zama marar amfani,ahaka zaiyi ta zama cikin ƙunci da tashin hankali,dan haka bana jin ta tashi"ammi ta fada tana mai kallon kwalbar da mutumin ya bata mai dauke da guba. Adeeb kuwa koda yaje part din ammi bata nan,kai tsaye ya wuce garden,Dan yasan bata wuce can,tunda bata bangaren abie,amma kuma me takeyi a garden da wannan daren?kasancewar garden ɗin akwai wadataccen haske,kana iya ganin komai tar tar kamar rana.can Adeeb ya hango ammi zaune da wani mutum,cike da mamaki yake kallonsu ,yana yawan ganin wannan mutumin mai fuska arufe,waye shidin?me yake kawoshi gurin ammi?kuma duk zuwa sai da daddare? Ƙara sauri yayi dan yaje ya cimma mutumin nan yau kam saiga ko waye shi. Da sauri yaga mutumin ya mike tare da bin wata hanyar yayi waje yana gyara rufin fuskarsa. Ammi kuma tana boye abu cikin rigarta.dan mutumin shine ya hango Adeeb yana tahowa,shine ya sanar da ammi ya mike da sauri ya tafi. Cike da tuhuma Adeeb ya karasa gurin da ammi ke zaune tana wani muzurai,zama yayi shima tare da kafe ta da Mayun idanunsa,waɗanda ke cike da tuhuma. Murmushin karfin hali ammi tayi tana mai faɗin"Prince kaine da daren nan?aida kayi zamanka ma zuwa gobe saikazo,bana son kana wahalar da kanka"ta fada cikin basarwa tana kallon gefe guda. Adeeb kam kallonta kawai yake,dan duk wasu alamu na rashin gaskiya ya bayyana akan fuskarta.cikin dakakkiyar murya yace "ammi waye wancan mutumin daya bar gurin nan yanzu?meye alaƙarki dashi?meyasa Aduk lokacin dana ganku tare yake saurin barin gurin kafin na iso?Adeeb ya jerowa ammi waɗan nan tambayoyin ,da suka matukar firgitata.tunda suke dashi bai taba mata tambaya makamancin haka ba,duk lokacin da zai ganta tare da wannan mutumin baya taɓa tambayar ta waye wannan mutumin,amma yau tambayar ta yake,hakan yana nuni da cewar kiri-ƙiri Adeeb ya fara zarginta kenan. Cikin dakiya da son basarwa ammi tace "wannan wace irin tambayace Prince?wannan mutumin yana zuwa karbar tallafi ne na gidauniya,bayan wannan ba wata alaƙa tsakanina dashi "ta faɗa cike da bugawar zuciya tana kallon Adeeb. "Amma me yasa kullum sai dare yake zuwa?ammi Please karkisa zuciyata ta fara aminta da abinda ke kai kawo cikinta akanki,Please ammi don't disappointed me "Adeeb ya fada kamar zaiyi kuka,dan kuwa zuwa yanzu sosai yake jin zargin ammi cikin zuciyarsa. Kallonsa ammi tayi cike da tsoro da fargaba,me zuciyar tasa ke raya masa akaina?kodai yasan wani abu ne game dani?ko yaji me muke fadine yanzu?kai bai iiba ,dan kuwa da yaji hakika da bazai tsaya yana min wannan maganar ba,na tabbata wani abune dai da ban. Cikin salo da iya kissa ammin ta sanya kuka tare da kamo hannun Adeeb ta rike gam cikin nata,kallonsa take idanunta na zubda kwalla "yanzu ashe akwai ranar da zata zo ace kana zargin amminka?akwai ranar da maƙiya zasu sanya maka kokwanto akaina?nice fa amminka ,nice wacce na kula da rayuwarka fiye da yadda na kula da tawa,me yasa kake son sanya kokwanto akaina ?bazan taɓa cutar da kaiba Adeeb kasan da haka, dan Allah kadaina sanya komai cikin ranka, yin hakan zai zame mana damuwa "ammi ta karasa cikin kuka tana ɗora kanta agefen kafadun Adeeb. Shiru Adeeb yayi yana sauraronta, wani sashen na zuciyarsa na tausayinta,wani sashen kuma ya kasa gasgatata,abubuwa da dama suna masa yawo akwakwalwarsa. Ahankali ya sanya hannunsa yana mai ɗago ammi ,kallonta yayi cikin tausayawa yace "kiyi haƙuri ammi I don't mean that,kawai bana son kina hulda da irin wadan nan mutanen ne,amma bana zargi ki da aikata komai"ya faɗa yana share mata hawaye. "Shikenan dana,ka tashi ka shiga ciki dan akwai sanyi awajen da safe zamuyi magana,sannan ya kamata ka dawo da fattu gurin nanny,Dan gudun zargi ko"ammi ta fada tana share hawayenta. Jinjina kai Adeeb yayi kafin ya mike yace "saida safe ammi"ya fada yana barin gurin ba tare da ya su ɓaci hannunta ba,kamar yadda ya saba. Binsa ammi tayi da wani shegen kallo cike da tsana ,kafin ta furta"kayi kuskure daka fara zargina Adeeb,dan kuwa zaka tafi lahira da damuwar rashin samun gamsashshiyar amsa akaina." Koda Adeeb ya dawo part dinsa ,wanka yayi tare da dauro alwala,sannan ya fito,kayan barci da ya sanya ,bayan ya feshe jikinsa da turaren barcinsa. Sannan ya kwanta kusa da hulwarsa ya rungumeta tsam! Ajikinsa. Wata ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi yana jinsa cikin wani irin nutsuwa,kaso da yawa na damuwarsa ya kau. Kissing din wuyanta yayi sannan yayi musu addu'a tare da ja musu bargo ya kunshe idonsa. Ya jima yana nazari akan abubuwa da dama kafin barci ya dauke shi. Tunda yayi sallar asuba,bai kona barci ba,karatun Alqur'ani mai girma yai tayi,har zuwa lokacin da gari ya fara haske. Cak ya dauki fattu yayi toilet da ita,sai jinta tayi cikin bahon wanka,kukan shagwaba ta fara masa,shikuma yana lallabata, tare yayi musu wanka.tunda fattu ta rufe idonta bata budeba tsabar kunya,dan bazata iya ganin hammanta ahakaba,shikuwa ko ajikinsa,sai tsokanarta ma yake. Bayan sun shirya ne kuma ya kamo hannunta zuwa falo,dan yasan zuwa wannan lokacin,an gama shirya breakfast. Zaunarta yayi sannan shima ya zauna.abincine gasu nan kala kala na larabawa dana turawa.tea ya fara hadawa sannan ya matso kusa da fattu yace" Bismillah amaryar Hamma Adeeb "ya faɗa yana nufar bakinta da tea ɗin...... Masu karatu me zai faru? Shin fattu zata sha tara ɗin na ko yaya? Muje zuwa anty mammynku ce Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 71/72 _______________Cikin kuka da rawar murya ,fattu ta fara magana "wa...ce...ce .ma...haifi.......yata?kuma ina ne take ?sannna me ya faru da Hamma na bayan rasuwar momma?"ta fada cikin kuka mai ban tausayi. Saida Nanny ta share hawayen idanunta kafin taci gaba da fadin" lokacin da labarin hadarin nan ya iske mu,mun shiga tashin hankali bana wasa ba,dan kuwa nan take mai martaba ya yanke jiki ya fadi asume,gaba ɗaya faɗa ta rikice da kuka da alhinin rashin mutuniyar kirki kamar Momma, wacce ke son talakawa da taimakonsu. Lokacin da Adeeb suka dawo daga makaranta,ya ji labarin mutuwar Mommansa da kannansa,shima sumansa uku,saida gyar aka samo kansa,tun daga wannan lokacin Adeeb ya kara komawa shiru shiru,bashi da aiki sai tunani haka zaki ganshi zaune shi kadai yayi tagumi yana zubda hawaye,saida aka tashi tsaye akansa da addu'oi kafin ya dan warware. Mai martaba kuwa,ciwon zuciya ne ya kamashi, saboda tsabar damuwa da tunani. Yana matukar kaunar Momma,Dan macece mai hakuri da shiga rai. Tana faranta masa rai,duk abinda yace tayi bata ko musu akan umarninsa. Bayan sadakar bakwai ne ,aka fara bincike akan abinda ya sami motar tunda kai tsaye motar ta kama da wuta, kai tsaye aka gano bomb aka sanyawa motar.dan haka wannan hadimin mai kula da harkar motoci shi aka fara kamawa. Anyi -anyi ya fadi abinda yayiwa motar amma yaƙi,shidai yace tabbas bomb ɗin ne ajikin motar,saidai idan ya fadi wadanda suka sashi,to zasu kasheshi ne. Dukan tsiya akayi masa tare da kulleshi akurkuku. Cikin dare muka shirya zuwa gareshi,dan ya faɗa mana wadanda suka sa sashi,akan idan ya faɗa zamu sakeshi ya gudu. Amma saidai me?lokacin da mukaje, tuni Ammi ta riga mu zuwa,tana tsaye ita da wani mutum wanda ya nannaɗe fuskarsa da bakin gyalle.ta yadda ba wanda zai gane fuskarsa. "Wato so kake ka tona mana asiri ko?lallai kayi babban kuskure,dama ko kafada ko karka faɗa dole ne ka baƙunci lahira, tunda har kashigo hannu, kuma kasanar dasu da gaske bomb ɗinne ajikin motar,to watarana idan kaji azaba zaka sanar dasu mune muka saka ka sanya bomb din Dan haka yau zaka bi su Nazli kaima"Ammi ta fada tana mai dagowa daga sunkuyon da tayi tana yiwa mutumin magana. "Kuyi min rai, ranki ya dade,wllh bazan ce kune kuka sani na aikata wannan aikin ba,dan Allah karki kasheni" mutumin ya faɗa galabaice dan yaci duka dazu. "Kai!!! sakaran bawa, rufe mana baki, mu zakayiwa magiya mu gyaleka?wllh baka isaba,dole ka mutu dama baka da wani amfani agaremu, tunda kasan sirrinmu dole ka mutu"yana gama faɗin haka ya shaƙe bawan nan ,tun yana turje turje har ya daina alamun rai yayi halinsa. Gaba dayanmu dagani har Amma kuka muke jikinsu na rawa,tsabar tsoro da razani.wanene wannan wanda ke taimakawa Ammi wajen aikata ta addancinta?ta yaya zamu gane shi ?shine abinda ke ta yawo cikin kwakwalwarmu.amma bamu da amsa. Ganin yadda amma ke kuka kamar ranta zai fice ,gashi jikinta sai rawa yake,yasa nayi saurin janyeta dan barin gurin. Saidai agarin guduwa muka bigi wani bokiti ya fadi kasa yayi kara sosai.wanda ya jawo hankali su Ammi. Gudu muka farayi tun karfinmu, dan kuwa akwai tazara sosai tsakanin cikin faɗa da kuma sijin ɗin. Suma basu fasa ba kuwa suka biyo mu. Ganin zasu cimmana yasa Amma ta ce in buya,karsu ganni, ita zata tsaya ayi wacce za'a . Dan Ni zasu iya kasheni nan take ,amma ita tasan yadda zatayi. Haka na buya jikin wasu bishiyu.ta yadda bazasu ganni ba,amma Ni ina hango su dajin duk abinda suke fadi. Koda suka cimma Amma tana zaune tana numfarfashi, tsayawa sukayi akanta suna kare mata kallo. Ammi ce cikin ɓaci rai tace "dama nayi tsammanin kece,dan kuwa nasan ba wani dan kasadar da zaiyi yunkurin bin bayana ɗan ji da ganin sirrina.to kingani, kuma kinji,hankalinki ya kwanta,amma wllh idan naji wata magana akan abinda kika gani na rantse da Allah saina kashe danki da adeeb,kisa mafi muni,kuma na lakamiki kisan, nace ke kika kashesu, kuma kinsan zan iya. abinda yasa bazan kashe kiba yanzu, ina son kiga yadda zan lalata rayuwar yaranku ,insanya kiyayya atsakaninsu,ta yadda wataran daya shi zai zamo ajalin daya. Kuma kinsan menene ke nake so kizabi wanda zai zamo ajalin wani acikinsu"Amma ta kare maganarta tana dariya da kallon Amma. Kuka kawai Amma keyi, tana jinjina rashin imani irin na Ammi,mace kamar kafura?sam ba Allah cikin ranta.Amma na kuka take rokon Ammi akan ta gyale musu yara ,taji tsoron Allah,duk abinda take yana kallonta.Amma cikin rashin imani Ammi ke cewa "shikenan Ni zan zaba da kaina,nasan kina son danki,dan haka zan miki adalci yazamo shine zai kashe Adeeb "ta fada tana wani ware hannu da daga gira. Cikin sauri Amma tace "a'a karki kashe Adeeb,gara Rashad ya mutu amma dan Allah karki cutar da Adeeb Maraya ne,zuciyarsa akarye take karki illatashi na roƙeki"Amma ta faɗa cikin kuka. "Wow zabi mai kyau,kin zabi dan kishiya akan danƙi ko?lallai kin ciki shashasha,shikenan duk abinda zanyi akan su, naki idone ,daidai da rana daya kika yi min wata magana saina kashe Adeeb kinsan banda asara,bansan ciwon makida ba"tana gama faɗin haka ta karasa kusa da wannan mutum da suke tare,wanda dama yana tsaye dan nesa dasu yana kallon hanya. Saida suka bacewa ganinmu sannan na ƙaraso gurin amma,wacce ke kuka sosai.haka na kamata muka koma cikin fada,zuciyoyinmu sam ba dadi. Tun daga wannan lokacin Adeeb ya daina yiwa amma magana ,sai harara da bakaken maganganu,masu nuni da cewar yana zargin tana da hannu wajen kashe Momma.kuma nasan duk sharrin Ammi ne.kuma Daidai da rana daya Amma bata taɓa kula Adeeb ba saidai tayi ta kuka. Adaidai lokacin ne kuma suka tafi Singapore karatu.inda Adeeb yayi karatu bangaren likitanci,tareeƙ yayi karatun sa na koyon aikin jirgi,shikuma Rashad injiniya ne. Bayan dawowarsa daga karatune kuma babban tashin hankali ya samemu, na rasa Adeeb da akayi sama ko kasa, kwanansu uku da dawowa daga Singapore akawayi gari ba Adeeb ba labarinsa.duk inda ya kamata aje nemansa anje amma babushi,lokacin kuma da ya dawo daga Singapore,yana da tarin dukiya wacce shi kansa baisan adadinta.dan dan kasuwane mai neman na kasan,bai damu da matsayi ko mulkin gidansu ba ,yana da kamfanoni da dama akasashe da yawa,ciki harda nigeria.hakan yasa Adeeb ya iya Yaren Hausa sosai,dan darasi yake dauka na musamman akan bangaren. Dan haka lokacin da aka rasa Adeeb,tareeƙ shine yaci gaba da kula da duk wasu al'amura na dukiyar Adeeb .har Allah yayi dawowarsa ta silarki, Ashe kema rabon ki sadu danaki iyayen ne,kuma ba kowa bace mahaifiyarki, face sarauniya suhaimat" Baki buɗe fattu ke kallon Nanny ,Tana jinjina kai cike da jinjinawa ƙudirar Ubangiji,yanzu dama innar yan biyu itace mahaifiyarta? ashe shakuwar da sukayi ta lokaci ɗaya ba banza ba?waɗan kyawawan yaran kannantane?wayyo Allah na gode maka Allah mai yadda yaso ga bawansa. Allah Sarki hammana yaga rayuwa,ya hadu da ƙaidin matar uba.wacce yakewa kallon muguwa itace masoyiyarsa. Ita kuma wacce ya dauka uwa itace ke son ganin bayansa.lallai yazama dole In fahimtar da hammana. Cikin kuka da sarkewar murya fattu tace "amma waye yayiwa Hamma asiri ya zama maciji? Ajiyar zuciya Amma tayi ta fara magana akaron farko,tun zamansu aɗakin, tace "wannan ne har yanzu muke son sani,dan bamu da tabbacin Ammi ita tayi masa asirin, saidai muna zargin wannan mutumin da muka kasa sanin ko waye yana da hannu akan al'amarin"Amma ta faɗa tana share hawaye. Hannunta fattu ta kama cikin kuka,tace "lallai Amma kincika mutum mai halacci, kin sadaukar da rayuwar danki,dan ki ceci dan kishiya,nayi miki alkawarin in Sha Allah komai zai dai daita. Hamma zai dawo gareki matsayin uwa da data,sannan rashad zai zamo abin alfahari gareki. Sai yanzu na gane wannan abinda ya faru dani itace ta shirya komai,dan kuwa ita ta kaini bangaren da kanta,kuma ta kulle ƙofofin, sannan ita ta dauke sarkata wacce baffana yace itace shaidar da iyayena zasu gane Ni da ita." "Na sani ƴata,nasan itace ta shirya komai, sannan tun ganin farko da nayi miki nake ayyana ke yar sarauniya suhaimat ce ,dan kuwa akwai kamar ta atare dake .ina fatan Allah ya bamu sa'a akan abinda muke shirin aikatawa na alkairi "cewar amma. "Nanny kema kiyi haƙuri komai zai daidaita in Sha Allah"fattu ta faɗa tana rungume nanny cikin kuka. Kukan nanny ma keyi,tace "Allah ya amince ƴata. Kallon tareeƙ tayi tace" Hamma tareeƙ kayi hakuri in Sha Allah abokinka ,kuma dan uwanka,zai dawo gareka"jinjina kai yayi tare da saurin share hawayen daya gangaro masa,yana murmushi. "Amma kibi komai ahankali yata,hammanki ya aminta da Ammi sosai ,ta yadda baya ganin laifin ta ko kaɗan"amma ta faɗa tana shafa kan fattu. Jinjina kai fattu tayi tace "In Sha Allah Amma zan kula" Adeeb kuwa,gaba ɗaya ya duba ko ina baiga fattu ba ,hankalinsa ya tashi sosai,ina kuma taje?ko wani abune ya faru da ita?"ya Salam"ya faɗa yana mai fitowa daga part ɗin nashi cikin sauri. Kicibis sukayi da fattu tana shirin komawa bangaren nashi,dan Nanny ce tace ta koma kar Adeeb ya ganta anan yayi wani tunanin, Kallonta Adeeb yayi idanunta sunyi mugun jaaa, cikin hanzari ya kamo kafaɗunta yana girgiza kai,gabanshi na faduwa"me yasameki? Wani ne yayi miki wani abu? Ko Rashad ne ?"ya faɗa cikin ruɗu yana duba jikinta. Ita kuwa fattu kallonsa kawai take cikin tausayawa,yana cikin matsala babba,amma shi Sam baigani,zuciyarsa da idanunsa sun rufe,ya rike azzulamar uwa matsayin mai kaunarsa.jikinsa ta fada tare da sakin wani sabon kukan mai tsuma zuciya. Hankalin Adeeb gaba ɗaya ya tashi,jikinsa har rawa yake ,tana rungume ajikinsa ya bude part dinsa suka shige ciki,sai kuka fattu keyi harda shashsheka. Kai tsaye cikin daki ya wuce da fattu,bakin gado ya samu ya zauna tare da rungumeta ajikinsa ,yana jin damuwarsa na kara yawaita,zuciyarsa kamar zata fashe . "Am sorry Hulwa ki sanar dani abinda ke damunki zuciyata na min zafi,bazan iya jurar ganinki cikin damuwa hakaba "Adeeb ya faɗa kamar zaiyi kukan shima. Fattu dai taki cewa komai sai kuka take tare da kara kankameshi.ganin irin kukan da takeyi ne ,kuma baisan me zai mata tayi shiru ba ,ya sanya Adeeb ɗago kanta,ba tare da bata lokaciba kawai ya haɗe bakinsu guri ɗaya.ɗiff kukan fattu ya dauke,sai ajiyar zuciyarsu kake ji,cikin ƙankanin lokaci suka lula wata duniyar ,kasancewar Adeeb yana cikin damuwa da rashin nutsuwa,hakan ya kara ingiza shi cikin tsantsar bukatuwa da son kasancewa da fattu. Ita kuwa fattu,tsabar tausayinsa da tashin hankali,yasa ta sakarmasa jikinta yake sarrafa ta yadda yaso. Gaba ɗaya sun fice daga hayyacinsu,tun abu yana karami harya girmama, dan takai ga Adeeb ya raba su da kayan jikinsu banda rawa ba abinda jikinsa keyi,ita kuwa sai wani ƙara rukunkumeshi take tare da kiran sunansa cikin wata irin murya. "Hamma ka bari ,Hamma! hammana!!kawai take iya fadi tana kara shigewa jikinsa. Cikin murya mai cike da tsantsar bukatuwa da ficewar hankali Adeeb yace"h....uul...wa ki....n.amin..ce...dani.....matsayin ....... Abo...kin rayuwa? Kin amince na kusanceki........ Danƙari!!! masu karatu ya kenan?Hulwa kuwa zata amince ? Me zai biyo baya ? Muje zuwa Mrs babi ce 💘💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 73/74 _______________Cikin wata irin murya,mai kama da wanda yake cikin mayen barci,Adeeb ke fadin" Hul...wa....k.i...n...amin...cce dani..ma..tsayin...abokin....ray..uwa?kin aminci na kusa.....nc.c.eki?"ya karasa da gyar numfashinsa na hawa da sauka. Fattu kuwa gaba ɗaya ta rude sai wani juye-juye take kamar tarwada,cikin kasalalliyar murya tace "Hamma ba kyau,baffa yace yin hakan haramunne Hamma,ina jin tsoro ka bari"abinda bakinta ke faɗi kenan,amma kuma sam ba hakan bane cikin zuciya da gangar jikinta,tana faɗin ya bari kuma tana kara rikeshi ajikinta sosai,dan bata fata da son ya daina yi mata abinda yake mata,yanzu. Cikin rawar murya shima yake faɗin"Hulwa abinda ke shirin shiga tsakaninmu ba haramun bane,ke ɗin mallakina ce, na biya sadakinki,bazan taɓa cutar dake ba Hulwa,Please ki bani damar samun nutsuwa atare dake,i promise not to hurt you"Adeeb ya fada,cikin yanayinsa na bukatuwa, yana mai tura kansa gefen wuyanta. "Hulwa kin amince?kin bani damar zama mallakinki?"Adeeb ya faɗa yana rawar jiki. Ahankali cikin rashin sanin abinyi fattu tace "na amince hammana,nasan bazaka taba cutar dani ba,amma Hamma ina jin tsoro Ni yarinya ce Hamma bana son na mutu"fattu ta faɗa cikin wani irin salo idanunta arufe. "Bazaki mutu ba hulwatee zan biki ahankali nasan da karancin shekarunki, amma ba yadda zamuyi Hulwa,wannan itace kaddararmu"Adeeb ya faɗa cikin sanyin murya asaitin kunnen fattu. Cikin nutsuwa Adeeb ke yin komai,yana ƙoƙarin bin fattu cikin lumana dan sosai yake jin tausayinta kasancewar tana da ƙarancin shekaru,sam baiyi niyyar wani abu ya shiga tsakaninsu ahalin yanzu ba,saidai yadda yake jinsa halin yanzu bazai iya dakatar da zuciya da gangar jikinsa akan abinda suke bukataba. Addu'ar saduwa da iyali Adeeb ya fara karantowa afili,kafin ya danna wata yar na'ura dake maƙale jikin gadon,nan da nan dakin yayi wata kalar duhu mai burgewa, labulaye masu hudu suka sauko suka rufe ko ina nacikin dakin. Sannan dakin yayi duhu baka iya ganin fuskarsu. Ni dai ina daga gefe bana iya ganin komai dan duhu,saidai cikin lokaci ƙanƙani na fara jiyo ihun fattu ,da karfi ta kwalla ƙara,karon farko,sai kuma naji shiru nadan lokaci, kafin wani ƙaran ya kara biyo baya. Da sauri na bar ɗakin zuciyarta cike da tausayin fattu.dan kuwa gaba ɗaya Adeeb ya rasa gane inda yake,hankali da tunaninsa gaba ɗaya sun bar jikinsa,hakan yasa ya manta da wa yake tare,ya zage iyakar karfinsa yana making love da fattu. Bayan kusan awanni biyar ina nan zaune na buga tagumi,ina son komawa dan dauko muku rahoto,amma har zuwa lokacin dakin duhu gareshi ,saidai ina iya jiyo sautin kuka, kuma Muryar Adeeb nake jiyowa,dan haka cike da alhini na ɗan leƙa dakin. Adeeb na hango kwance gefen fattu,hawaye na tsiyaya daga idanunsa,yayin da yake rike da fattu ajikinsa,ya rungumeta kam ƙam.idanunsa alumshe suke,yayi luf akan gadon riƙe da fattunsa,wacce kallo daya nayi mata cikin dan haske. Da Adeeb ya kunna bayan komai ya wakana,gabana yayi mugun faɗuwa ,domin kuwa ko motsi fattu batayi ,sannan gaba ɗaya zanin gadon da suke kai ya ɓaci kaca-kaca da jini.lallai fattu taga aikin manya. Adeeb kuwa yana daga kwancen nan,tunani yake tunda yake arayuwarsa bai taba tsintar kansa cikin nishadi da kwanciyar hankali tare da jin dadi irin na yau ba.gaba ɗaya fattu ta rikita masa lissafi,wannan shine karonsa na farko daya taɓa sanin ya mace,bai taba tsammanin haka abin yake ba domin jinsa yayi kamar ba a duniya yake ba,wani irin masifaffen so da kaunar fattu ke ratsa dukkan wani kashi da bargonsa ,ji yake ahalin yanzu zai iya sadaukar da rayuwarsa akan fattu,lallai fattu ta cika yar baiwa domin yaji abinda bai taba tsammanin ji ba atare da ita.kuma yayi alƙawarin saidai mutuwa ce zata tabashi da fattu,dan bayajin zai iya koda cikken awa daya ba tare da Fattun ba. Ahankali ya daga hannunsa daga ƙugun fattu zuwa kanta,shafa kan nata yake slowly tare da ƙara lumshe idanunsa,kissing ɗin wuyanta yayi akaro na ba adadi kafin ya dan ɗago kansa dake masa ciwo sosai,leka fuskar fattu yayi dan yaji kamar bata motsi. Aikuwa da sauri ya zabura tare da zama akan gadon ya birkito da fattu yana kallonta. Kunnensa ya kai saitin hancinta,amma yaji shiru,nan ya gane da ta suma.cikin sauri ya janyo boxern sa ya sanya,sannan ya kunna hasken dakin.da sauri ya runtse idanunsa yana dafe ƙirjinsa,dan yadda yaga gadon ya mugun ɓaci da jini face-face.dafe kansa yayi yana mai jin mugun tausayin fattu cikin ransa,garin yaya yayi mata wannan aika-aikar?shidai yasan yayi iyakar ƙoƙarinsa Dan bida ita ahankali,amma baisan ya akayi ya rasa nutsuwa da tunaninsa ba.kallonta ya karayi akaro na biyu,yayi saurin kawar da kansa,dan kuwa ko tantama bayayi cewar fattu ta karu,"ya salam" ya furta ahankali,kafin yayi saurin shigewa toilet,ruwa ya haɗa mai matukar zafi,ya sanya abubuwan da zasu rage mata radadi cikin ruwan,kafin ya dawo dakin,tana nan kamar yadda ya barta,da sauri ya sureta yayi toilet da ita,bai zame da ita ko ina ba sai cikin kwamin wankan daya cika da ruwa. Yana zuwa ya sanyata cikin ruwan ahankali tare da zama abakin kwamin yana riƙe da kafaɗunta. Fattu kuwa lokacin da zafin ruwan nan ya fara ratsata yana shiga jikinta,ta farfaɗo tare da kwallah ƙara mai ƙarfi,jikinta yana rawa kamar dan mazari tana kokarin tashi daga cikin ruwan. Da sauri Adeeb ya riketa tare da danne kafaɗunta ta yarda bazata ita tashi ba."sorry Hulwa kiyi haƙuri kinji,ki zauna cikin ruwan zakiji daɗin jikinki AM sorry " Adeeb ya faɗa cikin sanyin murya kamar zaiyi kuka. "Wayyo allahna Hamma ka bari bana so ,wayyo zafi nakeji dan Allah kayi hakuri Hamma na fasa ban yarda ba wllh ,zaka kasheni wayyo baffana wayyo Allah Hamma ,dan Allah kaji tausayina,nice fa fattunka,kace bazaka cutar daniba wallahi idan ka ci gaba mutuwa zanyi wayyo Allah zafi"abinda fattu ke faɗi kenan cikin dasasshiyar muryarta,dan da alama saida ta sha kukanta kafin ta sume, Jikinta sai rawa yake kamar dan mazari. Cike da mugun tausayinta Adeeb ya rungumeta bayan shima ya shige cikin ruwan,bai damu da zafin da ruwan ke da shiba,tsabar tausayin fattu ke azalzalar zuciya da ruhinsa."am sorry Hulwa,ba abinda zan sake miki,buɗe idonki ki gani ba komai nake miki ba ,ina gasa miki jikinki ne dan ki daina jin zafin,kiyi haƙuri Hulwa I don't mean to hurt you am sorry"Adeeb ya faɗa yana rungumeta ajikinsa,ji yake kamar yayi kuka. "Dan Allah Hamma ka fitar dani daga nan zafi nakeji akasana Hamma zafi"fattu ta faɗa lokacin data buɗe idonta ta kalli inda suke. "Kiyi shiru to zan cireki daga ruwan amma ki daina kukan nan Please"ya faɗa yana riƙe kumatunta. Kuka kawai fattu keyi tana kiran zafi,wayyo Allah baffanta,ita gurin baffa zata je.da gyar Adeeb ya samu ta dan bari ruwan ya sane ya cire ta daga ciki,wankan tsarkin ma shi yayi mata tana ta kuka tare da yarfe hannu,wankan yayi shima kafin ya nannaɗeta cikin ƙaton towel ya daukota zuwa cikin dakin. Akan kujera ya ajiye ta tana ta kuka kamar ba gobe,gaba ɗaya hankalinsa ya tashi matuka,haka ya cire zanin gadon ya shinfida wani,sannan ya daukota ya dora kan gadon.zama yayi kusa da ita tare da riko hannunta cike da damuwa yake faɗin"dan Allah Hulwa kiyi shiru kanki zaiyi ciwo fa,an sorry bazan sakeba kinji"ya faɗa yana kissing din hannunta. Kam-kam fattu ta rufe idonta,tama ki budewa bare ta kalleshi,kukanta kawai take,tana tunanin abinda hamman nata yayi mata,shikenan yanzu sunyi zina kenan?Allah zai ƙonasu awutar jahannama? innalillahi ta ci amanar baffanta?kuka ta sake sanyawa cikin dasasshiyar muryarta tana faɗin"saida nace maka karkayi -karkayi ba kyau ,baffa yace duk wanda yayi wannan abun Allah konashi zaiyi,amma kaki yarda,saida kayi,yanzu gashi gurin sai zafi yakemin,kilama ka ciremin shi wayyo allahna shikenan Ni fattu na shiga ukuna,wllh gurin baffana zan koma bani bakai Hamma ,bazan ƙara kulaka ba ,tunda baka da tausayi"fattu ta faɗa cikin kuka tana mai fizge hannunta da gyar,dan gaba ɗaya jikinta ba kwari. Adeeb kuwa shiru yayi saida ta gama banbaminta kafin yace "Hulwa ba mu aikata haramunba,kuma Allah bazai ƙonamu ba,domin ke ɗin matata ce ,ban shigo dake cikin kasar nan ba saida aka daura mana aure,domin nasan haramcin yin tafiya da mace alhalin ba muharramarka bace,dan haka ki daina tunanin mun aikata kuskure,ke ɗin mallaki Adeeb Muhammad ashraf ce,ko tareeƙ yasan da hakan domin shine wanda na bawa sadakinki,Hulwa na aurekine domin rama alkairin da kukayimin,amma a wancan lokacin ban sani ba ko ina sonki ko bana sonki,amma ahalin yanzu ,na gane kedin kece rayuwata ,kece haskena, kuma farin cikina, bazan iya rayuwa ba tare dakeba,ina sonki,ina kaunarki, bazan taɓa rabuwa dakeba Hulwa ana ahubbikteeer Hulwa anti sururi abadan" Adeeb ya faɗa cikin wani irin. Shauƙi yana kara kamo hannun fattu cikin nashi,kallo ɗaya zaka masa kasan maganganunsa daga can kasan zuciyarsa suke fitowa,sune iyakar gaskiyarsa. Kallonsa fattu keyi,cike da mamakin jin abinda yake fadi,kenan shidin mijinta ne?ya aureta?amma me yasa bai sanar da ita ba tun da wuri?wayyo Allah yanzu Hamma mijina ne ? Kuma yana soma?fattu ta faɗa cikin zuciyarta tana jin wani irin sanyin daɗi yana ratsa zuciyarta.hawayene kawai ke saukowa daga kan fuskarta.kamar yadda shima Adeeb hawayen ke sulmiyowa daga cikin fareren idanuwansa masu matuƙar kyau da haske.kallon juna suke cike da wani irin shauƙi daya bayyana cikin idanunsu. "Hulwa kina so na ?zaki zauna dani matsayin mijinki?"Adeeb ya faɗa yana kallon cikin idanun fattu. Cikin zubda hawayen daɗi fattu ta jinjina masa kai tana kuka,saikuma tayi saurin turo baki tare da girgiza masa kai tace "ba kai bane kayimin wannan abun mai zafi,ba ruwana da kai,kuma Ni ba matarka bace, Ni gurin baffana zan koma"fattu ta faɗa cikin kuka tana turo baki,amma kana kallon fuskarta zaka fahimci zallar farin cikin da yake ciki,domin Allah ya sani tana matukar kaunar hamman nata,saidai bata san cewar sonshi take ba,sai wannan lokacin data san cewar shiɗin mijinta ne. Murmushi Adeeb yayi ganin yadda ta sauya amsarta lokaci ɗaya,wato fushi take dashi,amma ba tun yauba yasan fattunsa tana kaunarsa, dan haka cikin yanayin shagwaba da baisan yana da itaba ya wani langabe kai tare da shagwabe fuska yace "Please hulwata kiyi haƙuri,bazan ƙara ba fa,idan baki sona zanyi kuka"ya faɗa cikin irin Muryar datayi masa magana. Harara ta balla masa tare da kara turo baki tana mai lumshe ido,kafin ta maƙale kafada alamun taki. "Shikenan to kirama Abunda nayi miki,nima sai inji zafin inyi kuka,kinga shikenan ko"Adeeb ya faɗa cikin wata murya mai cike da nishadi da farin ciki.jinsa yake kamar wani sarki,yau gashi ga fattunsa ,sun zama abu daya,kuma harya sanar da ita matsayinta agurinsa,sannan ya bayyana soyayarsa agareta.wannan kaɗai ya isheshi farin cikin rayuwa. Hawayene ke silalowa daga idanun fattu zuwa kuncinta,kuka biyu take ,na farko zafin da takeji akasanta,na biyu farin cikin sanin Hamma mijinta ne ,ba haramci ya aikata da itaba ,wannan kadai ya isheta jin dadi.tasan ta sami miji mai kaunarta,wanda zai kare mata mutuncinta,sannan jarumi cikin jaruman maza. Ahankali Adeeb ya kai hannunsa kan wuyan fattu,zafi yaji sosai alamun zazzaɓi ya rufeta.cikin hanzari ya haɗa allura yazo yayi mata.kawai saijin tsininn allura tayi ajikinta.kuka ta sanya cike da shagwaba tana turo baki, Kwanciya yayi tare da rungumeta ajikinsa yana rarrashinta,dan har data barci ya hada mata,dan yana son ya dubata idan akwai yiwuwar yayi mata ɗinki saiyayi mata. Aikuwa tana cikin kukan barci yayi gaba da ita. Jin alamun tayi barcine yasashi tashi ya leka fuskata,aikuwa barcin take,ga hawayenan kwance akan fuskarta,ta turo baki cike da shagwaba,murmushi yayi tare da sumbatar kumatunta ,kafin ya buɗe bargon daya rufe ta dashi. Sosai Adeeb ya tausayawa fattu dan kuwa yaji mata ciwo sosai,dole sai yayi mata ɗinki,gurin ya kumbura sosai abin tausayi.haka yayi mata dinkin nan,yana tausaya mata,duk da allurar barcin da yayi mata,idan ya tsira allurar nan saita yamutse fuska kamar zatayi kuka.haka dai har suka gama .jikinta zafi sosai na zazzaɓi. Ammice zaune acikin dakinta,waya take kuma da alama wayar mai muhimmanci ce ,dan kuwa tayi shiru tana sauraron abinda ake faɗa mata acan daya bangaren. Ajiyar zuciya tayi kafin tace "shikenan,zan saka masa maganin,amma dai sai zuwa gobe,kamar yadda ka bukata,kasan yanzu akwai riski bana son abinda zai zo ayi zargina cikin mutuwarsa"ammi ta fada murya ƙasa -ƙasa. Ta jima tana sauraron me ake fadi mata kafin tace "karka damu da wannan matar ai na gama da ita ,bazata iya faɗin komai ba,kuma yanzu ta danta take,tun lokacin da boka yace min asirin jikinsa ya karya,na sanya aka rufe masa baki,shiyasa ma sam baya iya yin magana,bare ya fadi wani abu akai na" Shikenan sai kaji labari zuwa goben.ammi ta fada tare da ajiye wayar hannunta,tana sakin murmushi cike da farin ciki"Adeeb ka shirya bin mahaifiyarka, dan kuwa gobe iwar haka ana zaman makokinka, tunda na fahimci ka fara zargina,ka daina fadamin abubuwan da suka shafi rayuwarka,dole kabar duniyar nan,kafin dan uwansa ya biyo bayanka, saikuma wancan tsohon mahaifin naka"ta fada tana jingina bayanta jikin kujera ,feeling so happy. Su Amma kuwa ɗakin Rashad suka nufa bayan barin fattu daga dakin,yana kwance idanunsa buɗe ,ya kurawa saman dakin idanu,hawayene ke zuba daga idanunsa. Zuciyarsa tana mai zafi sosai,yana son yayi magana amma sam ya kasa,duk lokacin da yayi yunkurin yin magana sai yaji wani irin azababben abu ya tokare masa maƙoshi,kamar zai mutu. Zama Amma tayi kusa dashi tare da sanya hannu ta share masa hawayen dake zubowa daga idanunsa,itama hawayen yana zuba daga nata idanun,sosai take jin tausayin ɗan nata,kallonta yayi da idanunsa da sukayi jajur,ya fashe da kuka harda shashsheka. Ficewa amma tayi daga dakin cikin sauri,dan bazata iya jurar wannan kukan na Rashad ba.nanny ma Binta tayi da sauri tana hawayen tausayin bayin allahn na. Tareeƙ ne yazo kusa dashi ya zauna tare da riƙe hannunsa yace "haba Rashad kayi hakuri mana ,ka ɗaurewa koma me kakeji cikin zuciyarka, domin karfafawa mahaifiyarka gwuiwa,In Sha Allah komai ya kusan zuwa karshe"tareeƙ ya faɗa cike da ƙarfafawa Rashad gwuiwa. Jinjina kai Rashad yayi tare da juya kansa can bangaren,shi kadai yasan irin zafin da yake ji cikin zuciyarsa,yana son ganin dan uwansa ,dan sosai yake jin kewar Adeeb cikin ransa. Bayan Adeeb ya gama yiwa fattu ɗinki,wanka yaje ya karayi,ya sanya riga da wando kanana,bakin wando da milk din riga,turare ya feshe jikinsa dashi,kamar ko yaushe ,sannan ya taje kansa ,fuskar nan tayi fayau yayi wani irin mugun kyau,sai sheƙi yake,kallo ɗaya zakayi masa kasan yana cikin tsantsar farin ciki.zama yayi bakin gadon da fattu ke kwance tana barci,hannunta ya kama ya riƙe cikin nashi,tare da kura mata ido. Sosai yake jin kaunar fattu na ratsa jikinsa,gaskiya fattu alherice agareshi,shikam bai taba tsammanin akwai wani nishadi da farin ciki irin wanda ya samu yau ɗin na ba,yarinya karama amma ta sanyashi cikin nishadi da jin dadi,lallai zai kula da fattu kamar yar tsabar zinare,zai bata dukkan farin cikin da take nema,sannan zai sadata da mahaifanta in Sha Allah,koda zai karar da dukkan abinda ya mallaka. Shiru yayi tare da lumshe ido,sosai yake jin kewar tareeƙ ,yana son ganinsa,amma so yake ya nuna musu kuskurensu, duk da sosai maganarsu tatsaye masa cikin ransa,yana jin kamar suna da gaskiya,amma idan yayiwa Ammi wannan kallon kamar yaci amanar ta, ne,itace wacce ta maye masa gurbin mahaifiyarsa,ta kula dashi, ta bashi duk wani gata da kulawa kamar ita ta haifeshi.amma yana nan yana ci gaba da bincike cikin tsinake. Kiran sallar magrib shine ya sanya Adeeb tashi ahankali ya nufi toilet ,alwala yayi ya fito,kallon fattu yayi wacce ke barcinta cikin nutsuwa,har zuwa lokacin bakinta ature yake lips dinta yayi jaa sai sheƙi yake,murmushi yayi tare da matsawa gareta,jikinta ya taba yaji ba zafi alamun zazzabin ya sauka kenan. Saida ya gyara mata rufuwarta kafin yayi kissing lips dinta sannan ya fice zuwa masallaci,bayan ya sanya security Ako ina na part din nashi. Ana fitowa daga masallaci yaje gurin abie kamar yadda ya saba ,bayan sun dan tattauna ne ya miƙe tare da yiwa abie sallama ya fito. Part dinsa ya nufa kai tsaye.abakin part din nashi yaci karo da tareeƙ yana zaune ya buga tagumi kamar wani Maraya. Ta gefen ido Adeeb ke kallon tareeƙ ɗin,har cikin ransa yake jin kaunar tareek,kuma yana kewarsa sosai.amma haka ya fuske yayi kamar bai ganshiba. Da sauri tareeƙ ya mike yayi gurin Adeeb din."yallaɓai Please ka yi hakuri dan Allah ka saurareni,na kasa jure fushin nan naka akaina kayimin duk hukuncin da zakayi min amma dan Allah ka daina shareni,bani da kowa daga kai sai ummeena"tareeƙ ya faɗa cikin rawar murya alamun kuka ke son kwace masa. Runtse ido Adeeb yayi yana jin wani irin tausayin tareeƙ ɗin cikin ransa,amma sai yayi kamar bai ji saba ,yaci gaba da tafiya harya ƙaraso kofar shiga part din nashi. "Dan Allah yallaɓai karka tafi kabarni,kasan Ni masoyinka ne daga Ni har mahaifiyata bazamu taba cutar dakai ba ,wllh zan iya bada raina fansa akanka,idan har zakaci gaba da fushi damu,tabbas zamu bar garin nan gaba ɗaya,domin saboda kai muke cikin masarautar nan kuma......."tareeƙ ya kasa ƙarasa maganarsa sakamakon kukan daya kufce masa.durƙusawa yayi agurin ya fashe da kuka kamar mace...... Muje zuwa masu karatu,anty mammyn kuce. Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 14:58] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page77/78 🌾💐🌾💐🌾💐🌾💐🌾💐🌾 *INA MATAN DA SUKE DA BURIN GANIN SUN MALLAKI MAZAJENSU CIKIN SAUKI BATARE DA SUN KAUCE HANYA BA , ZAKI SAMU DAMAR JUYA MIJINKI YADDA KK SO DA SIRRIN DANDANONKI* *Shin kinada labari shahararrar Mai Saida kayan matan nan Yar mutan sokoto wadda kukafi sani da mmn zarah sokoto to uwar gida da amarya Kusha kuruminku ta shirya tsaf ta sake kawo maku zafafa Kuma kayatattun kayan Mata masu kyau da inganci Wanda Basu da wata illa ajiki sayen dai dai ko sari Ina sokoto Ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah ,kisani Yar uwa Babu kalan kayan matan da bamudashi Kuma akan farashi Mai sauki ga Mai bukatar ganin kalolin kayan zai iya nemana ta wannan number 07034251528 call or WhatsApp Ina maraba daku*🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗 Ga kadan daga cikin abunda muke dashi👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin tsumi Kalolin sabulan wanka dana tsarki Dahuwar kaza Dahuwar zuciya Dahuwar yan shila Dahuwar zabo Mai sirrin mallaka Dahuwar yan ciki Dahuwar ciccibi ko soyayyen ciccibi Dahuwar kwai ukku Dahuwar tsoka Tara Maganin sanyi Maganin nono Mai sa cikowar nono da tsayuwarshi Maganin hips Mai sa hips dinki ya ciko sosai gwanin sha'awa Maganin kiba Wanda zaisa kiyi kiba Yar dai dai ba Mai Muni ba Dilkar amare sabulun amare sabulun dilka sabulun oray White da sauransu , Akwai maltinar Mata Hadin karya gado Sahihin hadin mallaka Hadin Mai jego Hadin sabon budurci Butar tsarki Dan goshi da mahadinshi Dan goshi sabon salo Sirrin tafin kafa Kalolin humra Hatsabibin turare Dai dai sauransu ga Mai bukatar ganin kalolin kayan da muke dashi zai iya nemana ta wannan number 07034251528 call or WhatsApp karku manta da sunan *Mmn zarah sokoto.ina sokoto Ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah* 07034251528 _______________Shayi Adeeb ya tsiyayo cikin wani kofi mai kyau,saida ya firfita shayin dan ya dan rage zafi,sannan ya tunkaro bakin fattu dashi yana faɗin""Bismillah amaryar hammata Adeeb"ya faɗa cikin murmushi da tsantsar kaunar fattu. Kallonsa tayi tare da kallon shayin,ta turo baki"nifa Hamma akwai Abinda ke damuna,wanda nake son faɗa maka jiya,shine kaikuma kayimin wannan abu mai zafin tsiya"fattu ta faɗa tana kawar da kanta daga kusa da kofin da Adeeb ya miko mata . Murmushi Adeeb yayi kafin yace " kinga yanzu dai kiyi haƙuri Kisha tea ɗin nan,inyaso daga baya saiki fadamin abinda kike son sanar dani raguwata"ya faɗa yana kara mika mata tea ɗin bayan ya debo cikin tea spon. Buɗe baki fattu tayi da nufin karbar tea din,sai kuma tayi saurin kawar da kanta tana mai zaro ido"Hamma daga ina aka kawo maka wannan abincin?ta fada cikin rawar jiki tana nuna tulin abincin dake gabansu. Kallonta yayi ganin yadda gaba ɗaya ta sauya, lokaci guda tsoro ya bayyana akan kyakykyawar fuskarta. Kafin yace "Duk abincin da kikaga ana kawomin,to daga ɓangaren Ammi ne,dan ita ke kula da abincina,saboda tsoron sharrin makiya"Adeeb ya faɗa yana ƙoƙarin kai te ɗin nan bakinsa. Da mugun hanzari fattu ta buge spoon din tare da kofin dake hannun Adeeb na tea din.nan take kofin ya fadi kasa ya tarwatse.cike da tsoro da fargaba take bin kofin da kallo,gabanta na ci gaba da mugun bugawa. Cikin mamaki shima Adeeb ke kallon fattu, ganin abinda tayi ,kafin ya ce "Hulwa lafiyarki kuwa?menene yasa kika zubar da tea din?"ya faɗa yana kallonta. Cikin rawar jiki da rashin kwarin jiki fattu ta yunƙura ahankali ta mike tsaye sannan ta kama hannun Adeeb tare da janye shi daga jikin daining table."Hamma karkaci komai dake gurin nan,wllh akwai guba aciki"fattu ta faɗa cikin tsoro tana kara matsar da Adeeb daga gurinn. Cike da mamaki Adeeb ke kallon fattu,yace "guba kuma Hulwa?waye yasa gubar ?kuma ta yaya kika san akwai guba aciki. Sosai jikin fattu ke rawa tana kallon Adeeb sannan tace "Hamma da kunne na naji za'a sanya guba acikin abincin da zakaci, kuma na tabbata an saka ɗin,dan yau aka shirya sanya maka gubar, shine abinda najiyo jiya nazo zan sanar da kai ina kuka"fattu ta faɗa tana rike hannun Adeeb cikin rawar jiki. Gaban Adeeb ne yayi mugun faɗuwa,tabbas yasan tunda fattu ta fadi haka,to tajidin ne,dan bata taba masa ƙarya ba,sannan bata san meke faruwa acikin gidan ba,bare yayi tunanin wani abu,amma waye wanda yana batun sanya masa guba cikin abinci?cikin fargaba Adeeb ya rike kafadun fattu,wacce ke neman fita daga hayyacinta tsabar tsoro da fargaba. "Hulwa a ina kikaji ana batun sanya min guba?waye kikaji yana maganar"Adeeb ya faɗa cikin tashin hankali. Ɗago kai fattu tayi ta zuba masa idanu hawaye na zuba daga cikin idanunta kafin tace "Hamma bata kaunarka, bata son ganinka cikin doron duniyar nan, da kunne na naji tana faɗin haka,sannan itace silar rabani da mahaifana na asali,sannan ta sanya akayi min katanga tsakanina da mahifiyata,Hamma itace ta kashe maka momma da ƙannanka,wllh Hamma bata sonka naji tana faɗa cikin waya, nan fattu ta bashi gaba dayan labarin abinda nanny ta sanar da ita , tana kallon Adeeb tana kuka."haka fattu ta kai ƙarshen zancen ta tare da fashewa da wani irin kuka mai tsananin ciwo da zafi,tana fadawa jikin Adeeb,tare da rungumeshi ƙam-ƙam tana kukanta. Jikin Adeeb banda rawa ba abinda yake,ji yayi kamar bazai iya tsayuwar ba,dan haka cikin karfin hali ya jingina da jikin bango,tare da riƙe fattu ajikinsa sosai,gabansa na mugun bugawa kamar zuciyarsa zata tsaga ƙirjinsa ta fito. Shiru yayi yana sauraron irin kukan da fattu keyi,so yake ya tambayeta waye wanda taji yana faɗin hakan,amma zuciyarsa na tsananin tsoron jin wanda fattun zata ce taji yana faɗin hakan. Cikin dauriya da fizgo kalmar yace "Hulwa waye kikaji yana faɗin hakan"Adeeb ya faɗa sounding so scared. Ɗago da kai fattu tayi cikin kuka tace "AMMI ce,Hamma ammi naji tana faɗin hakan da kunne kuma na ganta da idona"fattu ta faɗa cikin kuka tana kallon idanun Adeeb. Wata zabura da Adeeb yayi saida suka fadi kasa dagashi har fattu," innalillahi wa'inna ilaihir raji'un shikenan ta tabbata ammi ke cin dunduniyarsa,kuma itace ta kashe masa mommansa,sannan itace ta raba Hulwa da iyayenta,tabbas biri yayi kama da mutum,saboda boye ta shaida yasa ta dauke sarƙar fattu,kuma ta gane fattun tun farko,amma tayi shiru,"why ammi why? Me nayi miki?me yasa kika rabani da farin cikina?me yasa kika kashemin mommana da ƙannaina?harda bawan Allahn da baiji ba bai gani ba?why ammi whyyyyyy" adeeb ya faɗa cikin karaji da wata irin murya,mai matukar ban tsoro,da sauri fattu ta maƙale jikinta tana kuka.wata irin rawa jikin Adeeb yake kamar zai karkarye,idanunsa sunyi mugun sauya kala,daga fari zuwa kaloli daban daban,jikinsa sai wani irin. Hayaƙi yake fitarwa. Jijiyoyin kansa sunyi ruɗu -rudu kamar zasu fito waje. Wani irin ƙara Adeeb ya sanya tare da fizge ƙatuwar plaxma dake nanne jikin bangon dakin ya dokartada kasa nan take ta tarwatse agurin.yana faɗin" why ammi,whyyyy you killed my family ,you ruined my life,ammi "Adeeb ya faɗa yana jifa da duk abinda yazo hannunsa. Gaba ɗaya fattu a tsorace yake,firgici da tashin hankali,ya sanyata jin kamar zata mutu.banda kuka ba abinda takeyi.gashi Adeeb duk yajiwa kansa ciwo,hannunsa ya yanke sai jini ke zuba amma bai fasa fashe -fashen da yakeba. Ganin da gaske neman illata kansa yake yasa Fattu ta mike da gyar ta nufi inda yake yana fasa wasu haɗaɗɗun flowers dake gefen daining ɗin.kai tsaye ta fada ƙirjinsa tana kuka kamar ranta zai fita"Hamma ka daina,ka daina dan Allah, hannunka yana jini,Hamma kana bani tsoro "ta fada cikin muryar kuka mai tsanani. Jin fattu ajikinsa ya sanya shi kankameta kamar zai maidata cikinsa.wani irin numfashi yake saukewa kamar mai shirin suma. Cikin ƙarfin hali fattu ke karanato addu'oi saitin kunne Adeeb tana tofa masa. Kusan minti goma suka dauka cikin wanna halin,kafin taji Adeeb ya fashe da kuka jikinsa yana rawa , zamewa yayi ya zube a kasa.da sauri ta bishi tare da kamo shi zuwa jikinta,itama tana kuka. Zama tayi tare da ɗora kan Adeeb ɗin kan cinyarta tare da rungume kan nashi tana kuka. Mugun tausayin Adeeb takeji yana ratsata,tunda take bata taba ganin Adeeb yana hawayeba sai yau,kuma yau ɗin kuka yake mai fidda sauti cike da karayar zuciya,ya dugungune jikinsa tare da rungume cikin fattu yana kuka sosai. Haka suka dauki tsawon lokaci suna kuka, abin gwanin ban tausayi,shi dai Adeeb ji yake kamar zuciyarsa zata kama da wuta,bai taba tsammanin wannan abun daga amminsa ba,matar daya ɗauka matsayin uwa,ashe itace ta kashe masa mahaifiyarsa,kuma ta ɗorawa wata,wacce sam bata da hannu cikin abinda ya faru sannan ta tabashi da ɗan uwansa wanda shi kadai yake dashi, ta sanya kiyayyar matar dake mai soyayya tsakani da allah cikin zuciyarsa. Tabbas komai zaiyiwa ammi bazai tama abinda tayi masa ba,kuma bazai taba mantawa da ammi ba cikin rayuwarsa,ta cutar dashi shida hulwarsa Allah shine kawai zai saka musu. Nan da nan zazzaɓi mai shegen zafi ya rufe Adeeb ruff. Jikinsa sai rawa yake haƙoransa na sama na dukan na kasa. Da gyar ya iya buɗe baki yace "Hulwa ki rungumeni,karki sakeni,karki barni Hulwa,sanyi nakeji Hulwa zuciyarsa zafi take min ,kiyimin addu'a jinake kamar zan mutu "ya faɗa cikin zafin zazzaɓi ya na juya kansa acinyar fattu. Rungumeshi sosai fattu tayi tana kuka"har abada bazan taɓa sakinka ba Hamma,ina tare da kai duk wuya duk runtse, kuma ba abinda zai sameka"fattu ta faɗa cikin kuka.wanda ita kanta zazzabin ke neman rufeta. Ammi kuwa tana can part dinta cike da farin ciki,birninta ya gama cika,dan tasan dole fattu ma zata ci wannan abincin,shikenan itama zata mutu.wayyo yau tana cikin farin ciki sosai. Zulaihat ce ta shigo dakin ammi kamar an jehota, kallo ɗaya zaka mata kasan bata cikin hayyacinta, tana zuwa ta tsaya kan ammi cike da masifa da karaji take magana"me yasa kukayi haka?me yasa zaki kashe min adeeb,me yasa lukaci amanata keda abbana? Wllh na rantse da Allah idan wani abu ya sami Adeeb saina kasheku dake da abbana"Zulaihat ta faɗa cikin karaji kamar zata rufe ammi da duka. Mikewa ammi tayi cikin haɗe fuska tana nuna Zulaihat da dan yatsa. Tace ke kishiga hankalinki dan ubanki,niba sa'arki bace wawiya marar hankali,kafin kiga bayana Ni zanga bayanki,dakarar yarinya kawai"ammi ta fada cikin tsawa tana hararar Zulaihat. "Wllh kisa wannan aranki, saina tona muku asiri,daga ke har abbana ,azzalumai mugaye, masu kashe mutane.kuma yanzu daga nan gurin Adeeb zan tafi in sanar dashi ko kedin wacece"tana kaiwa nan ta juya zata bar ɗakin. Cikin hanzari ammi ta rarumo wani ƙaton kofin tangaran ta rafkawa Zulaihat akanta. Ƙara Zulaihat ta kwalla tare da zubewa agurin jini na zuba akanta. Muje zuwa masu karatu, Abin yazo fa. Ina fara tallata muku sabon book dina da zai biyo bayan wannan ,mai suna , RAINON DAWO.daga jin suna kunsan ba magana, Dan haka ku shirya ,dan zai sauka da zafinsa, Sannan ga mai bukatarsa zaku iya min magana tun yanzu dan biyan kuɗinku akan lokaci. Normal 300 Special 500 Hmmm karku bari baku labari mu fan. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment more typing. [30/08 14:59] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page77/78 🌾💐🌾💐🌾💐🌾💐🌾💐🌾 *INA MATAN DA SUKE DA BURIN GANIN SUN MALLAKI MAZAJENSU CIKIN SAUKI BATARE DA SUN KAUCE HANYA BA , ZAKI SAMU DAMAR JUYA MIJINKI YADDA KK SO DA SIRRIN DANDANONKI* *Shin kinada labari shahararrar Mai Saida kayan matan nan Yar mutan sokoto wadda kukafi sani da mmn zarah sokoto to uwar gida da amarya Kusha kuruminku ta shirya tsaf ta sake kawo maku zafafa Kuma kayatattun kayan Mata masu kyau da inganci Wanda Basu da wata illa ajiki sayen dai dai ko sari Ina sokoto Ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah ,kisani Yar uwa Babu kalan kayan matan da bamudashi Kuma akan farashi Mai sauki ga Mai bukatar ganin kalolin kayan zai iya nemana ta wannan number 07034251528 call or WhatsApp Ina maraba daku*🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗 Ga kadan daga cikin abunda muke dashi👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin tsumi Kalolin sabulan wanka dana tsarki Dahuwar kaza Dahuwar zuciya Dahuwar yan shila Dahuwar zabo Mai sirrin mallaka Dahuwar yan ciki Dahuwar ciccibi ko soyayyen ciccibi Dahuwar kwai ukku Dahuwar tsoka Tara Maganin sanyi Maganin nono Mai sa cikowar nono da tsayuwarshi Maganin hips Mai sa hips dinki ya ciko sosai gwanin sha'awa Maganin kiba Wanda zaisa kiyi kiba Yar dai dai ba Mai Muni ba Dilkar amare sabulun amare sabulun dilka sabulun oray White da sauransu , Akwai maltinar Mata Hadin karya gado Sahihin hadin mallaka Hadin Mai jego Hadin sabon budurci Butar tsarki Dan goshi da mahadinshi Dan goshi sabon salo Sirrin tafin kafa Kalolin humra Hatsabibin turare Dai dai sauransu ga Mai bukatar ganin kalolin kayan da muke dashi zai iya nemana ta wannan number 07034251528 call or WhatsApp karku manta da sunan *Mmn zarah sokoto.ina sokoto Ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah* 07034251528 _______________Shayi Adeeb ya tsiyayo cikin wani kofi mai kyau,saida ya firfita shayin dan ya dan rage zafi,sannan ya tunkaro bakin fattu dashi yana faɗin""Bismillah amaryar hammata Adeeb"ya faɗa cikin murmushi da tsantsar kaunar fattu. Kallonsa tayi tare da kallon shayin,ta turo baki"nifa Hamma akwai Abinda ke damuna,wanda nake son faɗa maka jiya,shine kaikuma kayimin wannan abu mai zafin tsiya"fattu ta faɗa tana kawar da kanta daga kusa da kofin da Adeeb ya miko mata . Murmushi Adeeb yayi kafin yace " kinga yanzu dai kiyi haƙuri Kisha tea ɗin nan,inyaso daga baya saiki fadamin abinda kike son sanar dani raguwata"ya faɗa yana kara mika mata tea ɗin bayan ya debo cikin tea spon. Buɗe baki fattu tayi da nufin karbar tea din,sai kuma tayi saurin kawar da kanta tana mai zaro ido"Hamma daga ina aka kawo maka wannan abincin?ta fada cikin rawar jiki tana nuna tulin abincin dake gabansu. Kallonta yayi ganin yadda gaba ɗaya ta sauya, lokaci guda tsoro ya bayyana akan kyakykyawar fuskarta. Kafin yace "Duk abincin da kikaga ana kawomin,to daga ɓangaren Ammi ne,dan ita ke kula da abincina,saboda tsoron sharrin makiya"Adeeb ya faɗa yana ƙoƙarin kai te ɗin nan bakinsa. Da mugun hanzari fattu ta buge spoon din tare da kofin dake hannun Adeeb na tea din.nan take kofin ya fadi kasa ya tarwatse.cike da tsoro da fargaba take bin kofin da kallo,gabanta na ci gaba da mugun bugawa. Cikin mamaki shima Adeeb ke kallon fattu, ganin abinda tayi ,kafin ya ce "Hulwa lafiyarki kuwa?menene yasa kika zubar da tea din?"ya faɗa yana kallonta. Cikin rawar jiki da rashin kwarin jiki fattu ta yunƙura ahankali ta mike tsaye sannan ta kama hannun Adeeb tare da janye shi daga jikin daining table."Hamma karkaci komai dake gurin nan,wllh akwai guba aciki"fattu ta faɗa cikin tsoro tana kara matsar da Adeeb daga gurinn. Cike da mamaki Adeeb ke kallon fattu,yace "guba kuma Hulwa?waye yasa gubar ?kuma ta yaya kika san akwai guba aciki. Sosai jikin fattu ke rawa tana kallon Adeeb sannan tace "Hamma da kunne na naji za'a sanya guba acikin abincin da zakaci, kuma na tabbata an saka ɗin,dan yau aka shirya sanya maka gubar, shine abinda najiyo jiya nazo zan sanar da kai ina kuka"fattu ta faɗa tana rike hannun Adeeb cikin rawar jiki. Gaban Adeeb ne yayi mugun faɗuwa,tabbas yasan tunda fattu ta fadi haka,to tajidin ne,dan bata taba masa ƙarya ba,sannan bata san meke faruwa acikin gidan ba,bare yayi tunanin wani abu,amma waye wanda yana batun sanya masa guba cikin abinci?cikin fargaba Adeeb ya rike kafadun fattu,wacce ke neman fita daga hayyacinta tsabar tsoro da fargaba. "Hulwa a ina kikaji ana batun sanya min guba?waye kikaji yana maganar"Adeeb ya faɗa cikin tashin hankali. Ɗago kai fattu tayi ta zuba masa idanu hawaye na zuba daga cikin idanunta kafin tace "Hamma bata kaunarka, bata son ganinka cikin doron duniyar nan, da kunne na naji tana faɗin haka,sannan itace silar rabani da mahaifana na asali,sannan ta sanya akayi min katanga tsakanina da mahifiyata,Hamma itace ta kashe maka momma da ƙannanka,wllh Hamma bata sonka naji tana faɗa cikin waya, nan fattu ta bashi gaba dayan labarin abinda nanny ta sanar da ita , tana kallon Adeeb tana kuka."haka fattu ta kai ƙarshen zancen ta tare da fashewa da wani irin kuka mai tsananin ciwo da zafi,tana fadawa jikin Adeeb,tare da rungumeshi ƙam-ƙam tana kukanta. Jikin Adeeb banda rawa ba abinda yake,ji yayi kamar bazai iya tsayuwar ba,dan haka cikin karfin hali ya jingina da jikin bango,tare da riƙe fattu ajikinsa sosai,gabansa na mugun bugawa kamar zuciyarsa zata tsaga ƙirjinsa ta fito. Shiru yayi yana sauraron irin kukan da fattu keyi,so yake ya tambayeta waye wanda taji yana faɗin hakan,amma zuciyarsa na tsananin tsoron jin wanda fattun zata ce taji yana faɗin hakan. Cikin dauriya da fizgo kalmar yace "Hulwa waye kikaji yana faɗin hakan"Adeeb ya faɗa sounding so scared. Ɗago da kai fattu tayi cikin kuka tace "AMMI ce,Hamma ammi naji tana faɗin hakan da kunne kuma na ganta da idona"fattu ta faɗa cikin kuka tana kallon idanun Adeeb. Wata zabura da Adeeb yayi saida suka fadi kasa dagashi har fattu," innalillahi wa'inna ilaihir raji'un shikenan ta tabbata ammi ke cin dunduniyarsa,kuma itace ta kashe masa mommansa,sannan itace ta raba Hulwa da iyayenta,tabbas biri yayi kama da mutum,saboda boye ta shaida yasa ta dauke sarƙar fattu,kuma ta gane fattun tun farko,amma tayi shiru,"why ammi why? Me nayi miki?me yasa kika rabani da farin cikina?me yasa kika kashemin mommana da ƙannaina?harda bawan Allahn da baiji ba bai gani ba?why ammi whyyyyyy" adeeb ya faɗa cikin karaji da wata irin murya,mai matukar ban tsoro,da sauri fattu ta maƙale jikinta tana kuka.wata irin rawa jikin Adeeb yake kamar zai karkarye,idanunsa sunyi mugun sauya kala,daga fari zuwa kaloli daban daban,jikinsa sai wani irin. Hayaƙi yake fitarwa. Jijiyoyin kansa sunyi ruɗu -rudu kamar zasu fito waje. Wani irin ƙara Adeeb ya sanya tare da fizge ƙatuwar plaxma dake nanne jikin bangon dakin ya dokartada kasa nan take ta tarwatse agurin.yana faɗin" why ammi,whyyyy you killed my family ,you ruined my life,ammi "Adeeb ya faɗa yana jifa da duk abinda yazo hannunsa. Gaba ɗaya fattu a tsorace yake,firgici da tashin hankali,ya sanyata jin kamar zata mutu.banda kuka ba abinda takeyi.gashi Adeeb duk yajiwa kansa ciwo,hannunsa ya yanke sai jini ke zuba amma bai fasa fashe -fashen da yakeba. Ganin da gaske neman illata kansa yake yasa Fattu ta mike da gyar ta nufi inda yake yana fasa wasu haɗaɗɗun flowers dake gefen daining ɗin.kai tsaye ta fada ƙirjinsa tana kuka kamar ranta zai fita"Hamma ka daina,ka daina dan Allah, hannunka yana jini,Hamma kana bani tsoro "ta fada cikin muryar kuka mai tsanani. Jin fattu ajikinsa ya sanya shi kankameta kamar zai maidata cikinsa.wani irin numfashi yake saukewa kamar mai shirin suma. Cikin ƙarfin hali fattu ke karanato addu'oi saitin kunne Adeeb tana tofa masa. Kusan minti goma suka dauka cikin wanna halin,kafin taji Adeeb ya fashe da kuka jikinsa yana rawa , zamewa yayi ya zube a kasa.da sauri ta bishi tare da kamo shi zuwa jikinta,itama tana kuka. Zama tayi tare da ɗora kan Adeeb ɗin kan cinyarta tare da rungume kan nashi tana kuka. Mugun tausayin Adeeb takeji yana ratsata,tunda take bata taba ganin Adeeb yana hawayeba sai yau,kuma yau ɗin kuka yake mai fidda sauti cike da karayar zuciya,ya dugungune jikinsa tare da rungume cikin fattu yana kuka sosai. Haka suka dauki tsawon lokaci suna kuka, abin gwanin ban tausayi,shi dai Adeeb ji yake kamar zuciyarsa zata kama da wuta,bai taba tsammanin wannan abun daga amminsa ba,matar daya ɗauka matsayin uwa,ashe itace ta kashe masa mahaifiyarsa,kuma ta ɗorawa wata,wacce sam bata da hannu cikin abinda ya faru sannan ta tabashi da ɗan uwansa wanda shi kadai yake dashi, ta sanya kiyayyar matar dake mai soyayya tsakani da allah cikin zuciyarsa. Tabbas komai zaiyiwa ammi bazai tama abinda tayi masa ba,kuma bazai taba mantawa da ammi ba cikin rayuwarsa,ta cutar dashi shida hulwarsa Allah shine kawai zai saka musu. Nan da nan zazzaɓi mai shegen zafi ya rufe Adeeb ruff. Jikinsa sai rawa yake haƙoransa na sama na dukan na kasa. Da gyar ya iya buɗe baki yace "Hulwa ki rungumeni,karki sakeni,karki barni Hulwa,sanyi nakeji Hulwa zuciyarsa zafi take min ,kiyimin addu'a jinake kamar zan mutu "ya faɗa cikin zafin zazzaɓi ya na juya kansa acinyar fattu. Rungumeshi sosai fattu tayi tana kuka"har abada bazan taɓa sakinka ba Hamma,ina tare da kai duk wuya duk runtse, kuma ba abinda zai sameka"fattu ta faɗa cikin kuka.wanda ita kanta zazzabin ke neman rufeta. Ammi kuwa tana can part dinta cike da farin ciki,birninta ya gama cika,dan tasan dole fattu ma zata ci wannan abincin,shikenan itama zata mutu.wayyo yau tana cikin farin ciki sosai. Zulaihat ce ta shigo dakin ammi kamar an jehota, kallo ɗaya zaka mata kasan bata cikin hayyacinta, tana zuwa ta tsaya kan ammi cike da masifa da karaji take magana"me yasa kukayi haka?me yasa zaki kashe min adeeb,me yasa lukaci amanata keda abbana? Wllh na rantse da Allah idan wani abu ya sami Adeeb saina kasheku dake da abbana"Zulaihat ta faɗa cikin karaji kamar zata rufe ammi da duka. Mikewa ammi tayi cikin haɗe fuska tana nuna Zulaihat da dan yatsa. Tace ke kishiga hankalinki dan ubanki,niba sa'arki bace wawiya marar hankali,kafin kiga bayana Ni zanga bayanki,dakarar yarinya kawai"ammi ta fada cikin tsawa tana hararar Zulaihat. "Wllh kisa wannan aranki, saina tona muku asiri,daga ke har abbana ,azzalumai mugaye, masu kashe mutane.kuma yanzu daga nan gurin Adeeb zan tafi in sanar dashi ko kedin wacece"tana kaiwa nan ta juya zata bar ɗakin. Cikin hanzari ammi ta rarumo wani ƙaton kofin tangaran ta rafkawa Zulaihat akanta. Ƙara Zulaihat ta kwalla tare da zubewa agurin jini na zuba akanta. Muje zuwa masu karatu, Abin yazo fa. Ina fara tallata muku sabon book dina da zai biyo bayan wannan ,mai suna , RAINON DAWO.daga jin suna kunsan ba magana, Dan haka ku shirya ,dan zai sauka da zafinsa, Sannan ga mai bukatarsa zaku iya min magana tun yanzu dan biyan kuɗinku akan lokaci. Normal 300 Special 500 Hmmm karku bari baku labari mu fan. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment more typing. [30/08 14:59] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 79/80 💥🔥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 🔥💥🔥💥🔥💥🔥🔥💥 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji💃🏻💃🏻💃🏻🔥 Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji 🔥💥 Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan💥🔥💃🏻 Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa😉😉 Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki👍🏼💃🏻💃🏻 Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc 💥🔥 Kalolin tsumi👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono raƙumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar HQ💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida🥰🥰🥰🥰🥰👍🏼👍🏼👍🏼👍🏼 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah🤝🏼🤝🏼 Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera sokoto state💥🔥💥🔥💃🏻 ________________Ƙara zuhailat ta kwalla mai ƙarfi,tare da zubewa agurin asume jini na zuba akanta. "Ni zaki kawowa iskanci Zulaihat?wllh baki isa ki tona min asiriba, shashashar yarinya,daga yau zaki gane nafi ƙarfin Sakarcin ki" ammi ta fada tana kallon Zulaihat dake kwance cikin jini. Kasancewar ba kowa cikin falon nata, sai tayi saurin jan Zulaihat zuwa wani daki dake can gefe,dakin akulle yake sam ba'a amfani dashi,dan haka nan ta bude ta sanya Zulaihat ciki,bayan ta daddaureta,hatta bakinta taba bari abuɗe ba. Dawowa falon tayi tare da goge inda jinin ya bata,sannan ta zauna tana sakin murmushi,yanzu kam bata da wata damuwa,tasan zuwa wannan lokacin guba ta fara aiki jikinsu Adeeb da fattu,ita kuma wannan tsagerar,zatayi tunanin hukuncin da zata yanke akanta. Allah Sarki Adeeb yana kwance kan cinyar fattu,idanunsa arufe,kamar mai barci saidai ba barcin yake ba,tunanine kala kala cikin ransa,damuwa tayi masa yawa,ji yake kamar zai bar duniyar Ammi ta cutar dashi,dole ya hukuntata, saidai yana bukatar yin komai cikin sirri,ta yadda zai kamata dumu-dumu ya hukuntata a daidai,sosai jikinsa yayi zafi,sai rawar sanyi yake, Ƙara rungume fattu yayi sosai ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya. Kansa fattu ke shafawa cike da zallar tausayi,ji take dama tana da yadda zatayi da ta dawo da damuwar Adeeb zuwa kanta.amma duk da haka,zata tayashi yakar Ammi koda kuwa zata rasa ranta ne. Ahankali Adeeb ya yunkura ya tashi zaune,idanunsa sunyi jaa sosai, kallon fattu yayi yaga yadda har lokacin hawaye take zubarwa,janyota yayi zuwa jikinsa ya rungumeta ba tare da yace mata komai ba.itama fattu kawai kwantar da kanta tayi tana zubda kwalla. "Hulwa kiyi shiru Please,kukan ki yana kara dagamin hankali, ina buƙatar nutsuwar zuciya,amma idan har zan ganki cikin damuwa,bazan taɓa samun nutsuwaba"Adeeb ya faɗa yana shafa kan fattu. Ahankali fattu ta sanya hannunta ta share hawayenta kafin tace" bazan iya daina kuka ba Hamma,domin kaima kana cikin damuwa, bana son ganinka cikin tashin hankali,dole kayi wani abu domin kawo karshen wannan badakalar, Hamma kana bukatar su nanny awannan lokacin,domin nasan suna da masaniya akan abubuwan da kai baka sani ba"ta fada tana kallon idonsa bayan da ɗago daga kan ƙirjinsa. Jinjina kai Adeeb yayi,tabbas maganar Hulwa gaskiya ne,yana buƙatar ganin nanny,Allah Sarki nanny ashe duk abinda ta fada masa gaskiyane? Ashe itama ammi ta cutar da ita ta hanyar kashe mata miji?dan haka dole ya ga nanny da amma,wacce ta sadaukar da danta,dan kawai ta tsiratar da rayuwarsa, sannan ta jure duk wata tsana da tsangwama da yake nuna mata,lallai Amma ta cika kishiya ta gari,abar alfahari ga duk wanda ta kasance uwa agareshi. "Hulwa ina buƙatar ganin ƙanina, ina son ganin Rashad habebe"Adeeb ya faɗa yana mikewa cikin sauri . "Hamma baka da lafiya,sannan hannunka yana jini,ka bari sai anjima tukunna"fattu ta faɗa tana kamo hannunsa. "Hulwa wannan ciwon dake jikinsa ba komai bane idan aka danganta shi da wanda ke cikin zuciyata,bazan iya zama anan ba ina buƙatar haduwa da nanny,Amma,tareeƙ da kuma Rashad,Ina buƙatar in rungumeshi ajikina Hulwa,Ina kewar Dan uwana"Adeeb ya faɗa cike da wani irin shaukin son ganin Rashad. "Shikenan Hamma muje kagansu"fattu ta faɗa tana rike da hannun adeeb.kallonta yayi cike da tausayi da kuma ƙauna kafin yace "Hulwa baki da lafiya,zaki iya zuwa?kodai ki jirani inje in dawo?"ya faɗa yana shafa gefen fuskarta. "Zan je hamma,zan iya zuwa Daga yau har zuwa lokacin da komai zai dai daita zan kasance kusa da kai zan taimaka maka ta inda nake da karfin yin hakan"ta fada cikin karfin hali,dan dauriya kawai takeyi. Rungumeta Adeeb yayi cikin ƙauna da yaba hankali da basirar fattu,yace "na gode hulwata Allah ya faranta miki kema" Haka suka fice hannunsu riƙe da juna,kallo ɗaya zakayi musu kasan Dukansu suna cikin damuwa. Kai tsaye suka wuce part din Amma,lokacin amma na zaune kusa da Rashad Wanda ke sana'ar tashi ta kuka,kansa yana kallon sama,Amma na zaune gefensa tayi tagumi cike da tausayin ɗan nata,idanunta na zubda kwallah. Da sallama suka shiga cikin dakin,fattu da adeeb,tsabar nisan da amma tayi cikin tunani batama san sun shigo ba,shikuwa Rashad dama kullum cikin tunani yake ,wani lokacin sai ka tabashi yake sanin akwai mutum kusa dashi .saida fattu ta ɗan taba amma sannan tadawo hayyacinta.dan zabura amma tayi tana kallon fattu,sai kuma tayi saurin juyawa ta kalli gefen fattun,zaro ido tayi tare da goge idon ta dan tabbatar da abinda idonta ya gani,tabbas Adeeb ne,Adeeb ne yau a part dinta,idan zata iya tunawa ,yau yakai kusan tsawon shekara goma sha,rabon da Adeeb yazo inda take.cikin rawar murya tace "a'a..de.ee.bb"idanunta naci gaba da zubda kwalla. Shima Adeeb kallonta yake cike da tausayi,yace "Amma "cikin wata irin murya mai cike da kewa. Hannunsa amma ta kama tana kallonsa ,cikin hawaye ta kasa cewa komai. Jin amma ta ambaci sunan Adeeb yasanya Rashad saurin juyo da kansa,aikuwa akan kyakykyawar fuskar yayan nashi idonsa ya sauka.wani irin yunkuri yayi da hanzari,aikuwa cikin ikon Allah saigashi ya tashi zaune,wanda rabon daya tashi zaune da kansa tun lokacin da abin ya faru. "A.de..eb Akh ee"rashad ya faɗa cikin rarrabewar murya. Da sauri dukansu suka juyo suna kallon Rashad,cike da mamaki amma ke kallonsa ,tana son gasgata shidin ne yayi magana ko kunnenta ne yayi mata gizo. Ahankali ya kara furta"Adeeb akhee" Wani farin ciki ne ya lulluɓe amma,wanda ya sanyata kara sanya kuka tana dafe bakinta. cikin hanzari Adeeb ya ƙaraso jikin gadon da Rashad yake zaune,hannun Rashad ya kama Wanda Rashad din ke miko masa. Rungume Adeeb Rashad yayi tare da fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi. Adeeb ma rungume Rashad yayi sosai ajikinsa,yana jin wani irin sanyi na ratsa zuciyarsa,hakika ammi ta shiga haƙƙinsu,ta cutar dasu,Allah ne kadai zai saka musu. Ahankali yake shafa kan Rashad Wanda Sam ya kasa hana kansa kuka,sai ƙanƙame Adeeb yake ajikinsa. Amma ma kuka take cikin farin ciki,jin Rashad yana magana,lallai wannan alamace ta nasara,ta tabbata zuwa wannan lokacin Adeeb yasan gaskiya ,shiyasa ma yazo inda suke,cikin kuka amma ta kamo hannun fattu tare da rungumeta. Fattu ma cikin hawaye ta rungume amma tana mai jin dadi cikin ranta,koba komai ta zamo silar da yan uwan suka fahimci juna,yanzu burin ta kawai ace amma ta girbi abinda ta shuka ,sannan itama ta sadu da nata iyayen. "Fattu kin gama mana komai,kin zama silar da Adeeb ya fahimci gaskiya,ba abinda zan ce miki sai Allah yayi miki albarka,ya sadaki da iyayenki lafiya,kalli sanadin ki Rashad yayi magana alhamdullah"amma ta fada,tana kara rungume fattu. Murmushi fattu tayi tare da cewa"amma bani na cancanci yabo ba,face ke,domin ke ɗin jarumace kinyi abinda ba kowa zai iya yinsa ba,Allah ne kadai zai biya ki"ta fada cikin murmushi tana kallon amma. Ɗago da Rashad Adeeb yai tare da sanya hannunsa yana sharewa Rashad din idanu,Amma wani hawayen na ƙara zubowa,kallon Adeeb yake shima cike da son dan uwan nashi,yace "akhee nayi kewarka,Please kayi hakuri da abubuwan da suka faru,wllh bansan yadda akayi hakan ke faruwa dani ba,na cutar da kai ta gurare da dama,kuma ina jin zafin hakan ahalin yanzu"Rashad ya faɗa cikin hawaye. Girgiza kai Adeeb yayi tare da cewa"kai lil bana son ragwanta fa,kuka kake kamar wani mace?kazamo jarumi mana,kada ka kara sanya damuwa cikin ranka,akhee ɗin ka na tare da kai humm?"Adeeb ya faɗa yana daga girarsa ta dama yana kallon rashad. Jinjina kai Rashad yayi tare da sakin murmushi,yana jinsa cikin farin ciki marar iyaka. Amma ma murmushin take cike da godiya ga Allah,daya karkato da hankalin Adeeb, ya gane gaskiya. Kallon Agogon hannunsa adeeb yayi,tare da latsa wani guri,naji ya fara magana"tareeƙ kazo part din Amma tare da nanny yanzu"yana faɗin haka ya latsa wani guri tare da mikewa ya karasa gurin da Amma ke tsaye tana kallonsu cike da farin ciki. Hannun Amma ya kama cikin nashi,yana kallonta.kamar yadda itama take kallonsa."Amma an sorry for everything,ki yafemin Amma,nasan nayi maki ba daidai ba,amma hakan ya faru ne cikin rashin sani,lokacin da kaina yake cikin duhu,but now, Allah ya fahimtar dani gaskiya,na san komai amma,na gode da sadaukarwar da kikayi agareni, bani da abinda zan saka miki dashi face addu'a thank you Amma, thank you for everything"Adeeb ya faɗa cikin jimami da jin ciwon abubuwan da yayi ta yiwa amma abaya. Cike da farin ciki amma ke kallon Adeeb tana murmushi,gefen fuskarsa amma ta shafa cike da ƙauna tace "ban taba kullatarka ba dana,domin nasan duk abinda ke faruwa ba yin kanka bane,dan haka karka damu kanka"Amma ta faɗa cikin murmushi. Sumbatar hannunta Adeeb yayi cike da jin dadi,hannun nashi ta kalla taga ciwo adan rude tace "habeebee me yasami hannunka ?kaji ciwo ne?sannu"ta fada adan rude. Murmushi yayi tare da cewa"karki damu amma dan karamin ciwo ne kuma bayamin zafi" Ya faɗa yana kallon fattu dake gefe tana kallonsu cike da nishadi. Murmushi ya sakar mata,itama da maida masa martanin murmushi tana wasa da hannunta. Nanny ce ta shigo tare da tareeƙ, Allah Sarki tana shigowa ta kafe Adeeb da ido,cike da fargabar jin abinda zaice mata,daga can gefe ta tsaya tana kallonsa.ciki dan salon shagwaba Adeeb ya ƙaraso kusa da nanny,hannunta ya kama yana faɗin "ayya nanny bazakimin magana ba?fushi kike dani ?am sorry nanny yanzu na san gaskiyar komai nanny,na San wacece ammi,kuma ina neman tallafinku,wajen aiwatar da abinda nake son aiwatarwa, dan na tabbata akwai mai taimakawa Ammi akan duk abinda take aikatawa,ina son gano wadanda ke taimaka mata" Kuka kawai nanny ta sanya,tsabar dadin da maganar Adeeb tayi mata,wannan itace ranar da tajima tana son gani,yau gashi Allah ya kawo mata ita. Cikin damuwa Adeeb ke sharewa nanny hawayenta yana faɗin "am sorry nanny na" "Allah yayi maka albarka magajin fada,naji dadin fahimtar gaskiya da kayi" Kama hannunta yayi suka nufi kan kujera, Zama sukayi gaba ɗaya aɗakin suna jajantawa juna irin makircin da Ammi ta kulla akansu. Inda nanny ke kara bawa Adeeb labarin irin kalubale da suka fuskanta agurin Ammi,da irin barazanar da tayiwa amma. Sosai Adeeb yayi mamakin irin halin Ammi,yanzu abinda yake fata da buri shine sanin wanda yayi masa asirin da ya zama maciji,ba zai kyale hatta bokan da yayi wannan aikin ba. Nan nanny ke sanar da shi, sarauniya suhaimat itace mahaifiyar fattu,sosai Adeeb yayi mamaki,dan dazu ko sanin mahaifiyar fattu bai nemi yiba da take bashi labari,tsabar tashin hankali. Sai yanzu ya fahimci dalilin da yasanya suke kaunar juna lokaci guda,ashe alaƙa ce ta jini. To meye dalilin ammi na raba yar uwarta da diyarta? Wannan shine abinda ya tsaye masa arai, so yake gobe ya sanya rayuwar ammi cikin tashin hankali, zai sanyata cikin kunya tsoro da fargaba,dan haka nan take yayi kiran sarauniya suhaimat,ya sanar da ita lallai ta taho gobe,ita da ahalinta, dan ya sami labari akan yarsu data bata shekarun baya.amma baya son Ammi tasan zasu zo,dan yana so yayi mata bazata,sannan karsu sauka agidan nasu,su sauka awani gurin daban.zai turo adaukosu. Ai cikin rudewa da tsantsar al'ajabi sarauniya suhaimat ta sanar da mijinta ,dan lokacin dama suna tare,Adeeb ya kirata. Ai ba bata lokaci aka shirya jirgi suka nufi hanya cike da fatan Allah ya sa ƙarshen damuwarsu ne yazo. Tooooohhhh Masu karatu bari mu bisu ɗan ganin irin wainar da za'a toya. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More tyipng. [30/08 15:00] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 81/82 🌾💐🌾💐🌾💐🌾💐🌾💐🌾 *INA MATAN DA SUKE DA BURIN GANIN SUN MALLAKI MAZAJENSU CIKIN SAUKI BATARE DA SUN KAUCE HANYA BA , ZAKI SAMU DAMAR JUYA MIJINKI YADDA KK SO DA SIRRIN DANDANONKI* *Shin kinada labari shahararrar Mai Saida kayan matan nan Yar mutan sokoto wadda kukafi sani da mmn zarah sokoto to uwar gida da amarya Kusha kuruminku ta shirya tsaf ta sake kawo maku zafafa Kuma kayatattun kayan Mata masu kyau da inganci Wanda Basu da wata illa ajiki sayen dai dai ko sari Ina sokoto Ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah ,kisani Yar uwa Babu kalan kayan matan da bamudashi Kuma akan farashi Mai sauki ga Mai bukatar ganin kalolin kayan zai iya nemana ta wannan number 07034251528 call or WhatsApp Ina maraba daku*🤗🤗🤗🤗🤗🤗🤗 Ga kadan daga cikin abunda muke dashi👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Kalolin gumba Kalolin matsi Kalolin tsumi Kalolin sabulan wanka dana tsarki Dahuwar kaza Dahuwar zuciya Dahuwar yan shila Dahuwar zabo Mai sirrin mallaka Dahuwar yan ciki Dahuwar ciccibi ko soyayyen ciccibi Dahuwar kwai ukku Dahuwar tsoka Tara Maganin sanyi Maganin nono Mai sa cikowar nono da tsayuwarshi Maganin hips Mai sa hips dinki ya ciko sosai gwanin sha'awa Maganin kiba Wanda zaisa kiyi kiba Yar dai dai ba Mai Muni ba Dilkar amare sabulun amare sabulun dilka sabulun oray White da sauransu , Akwai maltinar Mata Hadin karya gado Sahihin hadin mallaka Hadin Mai jego Hadin sabon budurci Butar tsarki Dan goshi da mahadinshi Dan goshi sabon salo Sirrin tafin kafa Kalolin humra Hatsabibin turare Dai dai sauransu ga Mai bukatar ganin kalolin kayan da muke dashi zai iya nemana ta wannan number 07034251528 call or WhatsApp karku manta da sunan *Mmn zarah sokoto.ina sokoto Ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah* 07034251528 _______________Nan take sarauniya suhaimat da mahaifin fattu,suka shirya tahowa Misra,hankalinsu gaba ɗaya atashe yake ,barinma sarauniya suhaimat,burinta daya taji a inda aka sami labarin yarta,tayi alkawarin ko awace duniyar take zataje nemanta, fatan ta daya Allah ya nuna mata yarta,yasa ace Adeeb ɗin yasan inda take zaune. Haka aka shirya musu jet,cikin lokaci kankani, su zayyad suna school dan haka ba'a taho dasu ba,Basu san da tafiyar Bama. Ko acikin jirgin gaba ɗaya suhaimat ta kasa samun nutsuwa,fargaba da tunanin wane labari zata samu akan diyarta, ya cika mata ciki. Ahankali mijinta ya kamo hannunta ya rike cikin nashi,kallonsa tayi cike da karaya,murmushi yayi mata tare da cewa"ki kwantar da hankalinki Fulani na In Sha Allahu alkairine yake kiranmu" sarki ya faɗa cike da kokarin kwantarwa da matar tasa hankali. Jinjina kai tayi tare da faɗin "Allah yasa hakan mijina" Cikin hikima da tsari Adeeb ya tsara musu yadda zasuyi su kama ammi,sannan yana son abie yaji komai da kunnensa,kuma duji wanda ke taimakawa ammi akan waɗan nan abubuwa da tayi ta aikatawa. Dan haka sun tsara akan amma zata tunkari ammi akan cewar me yasa ta karya alkawarinsu? Tasan cewar itace ta sanyawa Adeeb wani abu yaci,dan gashican yana fama da ciwon ciki yana ƙoƙarin mutuwa. Sukuma zasu tsaya a waje ɗan jin duk abinda ammi zata faɗa da kanta. Haka dai suka shirya abinda zasuyiwa ammi domin tona mata asiri. Adeeb ne ya kalli tareeƙ yace idan jirginsu ya sauka kaje ka daukosu,ka kai su can guest house ɗina,idan lokacin shigowar su yayi,zan kiraka saika kawosu. Amsawa tareeƙ yai da to, Gaban fattu sai bugawa yake,tana jin wani irin tsoro da fargaba,wani sashen kuma na zuciyarta tana jin wani irin farin ciki,wai yau itace zata sadu da iyayenta?yau zataga ahalinta, hakika bazata taba mancewa da wannan ranar ba,ranace wacce zata sanyata cikin ranaku mafi muhimmanci arayuwarta. Kallonta Adeeb yayi cike da ƙarfafa gwuiwa,ya riko hannunta,da sauri ta kalleshi tana ɗan marairaice fuska,lumshe ido yayi tare da sakar mata murmushi yana ɗan murza hannunta. Ahankali ta sauke ajiye zuciya tana mai kallon hamman nata,tana jin sanyi cikin zuciyarta. Cikin nutsuwa da dauriyar zuciya Adeeb ya mike,duk da zafin da jikinsa ke dashi na zazzaɓi,dan har yanzu akwai zazzaɓi sosai ajikinsa,amma sam baya jin zai iya kwanciya ahalin da ake ciki yanzu,faɗa musu yayi kan cewar zaije ya kira mai martaba,dan yajiyewa kunnensa,sannan yace amma yaje gurin ammi,tayi magana da ita,tabi duk wata hanyar datasan zata bi dan ammi tayi magana yadda mai martaba zaiji da kunnensa.sannan yace idan ya kira mai martaba ,,zai sanar da ita ta hanyar yi mata flashing awaya,Dan haka wayarta ya karba ya kira number ta kafin ya yayi saving din number nata. Cikin sanyin murya da gajiyawar zuciya Adeeb ya kalli tareeƙ yace "tareeƙ ina buƙatar rashad ya kasance agurin shima"ya faɗa yana shafa kan Rashad,Wanda yake kallon dan uwan nashi,cike da tausayawa,dan yasan Adeeb jarumi ne na gaske,yaga rayuwa kala kala,wanda badan Allah yana kareshi ba,da tuni wani zancen ake ba wannan ba. Bayan sun gama tsara yadda komai zai tafi yadda suke bukata,kai tsaye Adeeb ya wuce bangaren martaba,lokacin da yaje mai martaba yana shirin fita fada,gaida shi yayi cikin girmamawa sannan yayi shiru kansa aƙasa.cike da kulawa abie ya zauna kusa da adeeb,kansa ya shafa cikin ƙauna kafin yace "habeebee meke tafe da kai?me kake so ?dan naga akwai Magana cikin bakinka"abie ya faɗa yana mai ci gaba da shafa kan Adeeb . Ahankali Adeeb ya sauke ajiyar zuciya tare da ɗago da kansa,hannun abie ya kama ya sumbata,sannan yace "abie akwai tarin damuwa atare dani, amma In Sha Allah yau komai zai zo karshe,ina son ka biyoni bangaren ammi,domin jin komai da kanka,amma inason dan Allah abie duk abinda zakaji,kada ka sanya damuwa aranka, kada ka bari abun yayi tasirin da zai tada maka ciwonka Please"Adeeb ya faɗa yana mai kara damke hannun abie cikin nashi. Cike da tausayawa abie ke kallo Adeeb,hakika Adeeb yana cikin damuwa,dan kuwa kallo ɗaya zakayi masa kasan akwai gagarumin abinda ke samun zuciyarsa.dan haka cikin tattasan lafazin abie yake faɗin"In Sha Allah habeebee zan zama mai sanya juriya da tawakkali akan duk abinda kunnena zaiji,fatana daya ne ,Allah ya yaye maka duk wata damuwa dake damunka. "Ameen abiena,na gode sosai"Adeeb ya faɗa yana ɗan ɗora kansa akafadun abie. Wazirine ya shigo cikin ƙaton falon da sallamarsa,amsawa abie yayi kafin ya shigo ya kwashi gaisuwa.nan abie ke sanar dashi yana da uzurin da zaiyi yanzu dan haka ya kula da faɗa kafin ya fito. Da to waziri ya amsa kafin kafin ya nufi ƙofa,bayan Adeeb ya gaidashi.har zai fice Adeeb yayi tunanin waziri ma familynsa ne,kuma zai iya taimakawa agurin idan bukatar hakan ta taso,dan haka yace abie ya kamata uncle ya biyomu koba komai shima jininkane" Jinjina kai abie yayi cike da kokarin don faranta wa Adeeb ɗin kafin yace "shikenan habeebee,ba damuwa idan hakan kake so" Nan abie ya sanar da waziri akwai bukatar ya biyoshi bangaren ammi dan akwai muhimmin abu da suke son aikatawa acan. Da to kawai waziri ya amsa sannan suka tashi gaba ɗaya suka nufi bangaren ammi. Suna fitowa Adeeb yace yana son suje su duba rashad kafin su wuce can ɗin. Dama kuma yau abie bai shiga duba rashad ɗin ba,dan kullum yana zuwa ya ga ya jikin nashi.dan haka sai suka wuce can. Daidai lokacin da sukaje tuni rashad yana kan keken guragu azaune. Sosai abie yaji dadin ganin cewar rashad sauki ya fara damuwa,tunda har sunan shi ya kira. Adeeb me yace ya kamata su tafi part din na ammi yanzu,dan kammala komai cikin lokaci.shidai abie baisan me ke faruwab a,amma haka nan ya tsinci kansa cikin faduwar gaba. Haka suka fito gaba dayansu suka nufi part din ammi. Daidai wannan lokacin kuma,tuni amma tana part din ammi, Zaune ta tarar da ammi kan kujera,tayi shiru da alama tunani yake,abin duniya ya isheta,tana tunanin idan aka san abinda tayiwa zulaihat,tabbas komai yana iya faruwa,tasan mahaifin Zulaihat ya fita iya shege,kuma bazai gyaleta ba in yasan abinda tayiwa yarsa. Dan haka kawai ta yanke shawarar ta sanya afitar da Zulaihat can jeji akashe ta ayarda gawarta ajejin. Tana cikin wanna tunanin taji shigowar amma,kai tsaye ba tare da ko sallama ba,kuma da karfi ta buga kofar. Juyowa tayi da hanzari dan ganin wanda ya shigo mata daki haka,ya ɓuga kofa da karfi. Ido hudu sukayi da amma,cike da mamaki da kallon ƙasƙanci ammi tace "ke mahaukaciyar inace zaki shigo min daki bako sallama?ta fada tana kallon amma cike da raini da tsana. "Baki da wannan matsayin da zanyi miki sallama,domin ke ɗin mushrika ce,azzalumai,maha'inciya kuma maci amana"amma ta faɗa cikin zafin murya tana nuna ammi da hannunta. Daidai lokacin su Adeeb da mai martaba suka iso babban falon ammi,suna ƙoƙarin buɗe kofar da zata sadaka da falon da su ammin ke magana da amma.kuma duk abinda amma ta faɗa akan kunnensu. Alamu abie yayi musu na su dakata anan gurin,ɗan jin abinda ammi ta fara faɗa. Cikin dariya irin ta mugaye ammi tace"banda abinki menene na maimaita abinda kin riga kin sani?kuma nima na sani,ina mai gargadinki daki gaggauta fita daga dakin nan,kokuma yanzu ina aikata miki abinda zaki jima baki manta da wannan ranar ba"ammi ta fada cikin haɗe rai . "Menene kuma ya rage ammi?duk irin zalumcin da kika aikata mana abaya, kina nufin akwai wanda zakiyi mana shi yanzu ya girgizamu? Kin kashe rayuka masu yawan da kema bakisan me suka aikata miki ba,dan haka karki damu barazanar ki ta daina tsoratani,nazo in sanar dake cewar ina sane da gubar da kika sanyawa Adeeb yau cikin abincinsa. Darammm gaban mai martaba ya fadi da sauri ya nemi gurin zama sakamakon ji da yayi yana neman faduwa.... Manage plessa yau Ina busy ne Mrs babi 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 15:01] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 85/86 _______________Ƙarar faɗuwar abu da sukaji,itace tayi sanadiyyar juyowarsu gaba ɗaya,ba komai bane ya fadi face tanfatsestiyar wayar queen suhaimat,Wanda shigowar su kenan ita da mijinta,dan tuni tareeƙ yayi musu iso zuwa dakin ammi,kuma gaba daya kalaman ammi akunnensu suka sauka, Cikin rawar jiki queen suhaimat ta ƙaraso cikin dakin,zuciyarta kamar ta kamar ta tsaga ƙirjinta tafito, dan yadda take bugawa da ƙarfi,zaka iya juyo sautin bugun nata. Gaban ammi tazo ta durgushe tana kallonta baki buɗe,kafin tace "uktee me kike cewa?me kunne na keji kina faɗa?Please kada kisa zuciyata ta buga,akan abinda kunne na yaji"queen suhaimat ta fada cikin rawar murya tana kamo hannun Ammi. Cikin azaba ammi take kallon suhaimat,tana jin wani irin bakin ciki da ɓacin rai,yanzu shikenan, suhaimat tayi galaba akanta?shikenan suhaimat zata san wacece yarta,kuma ta ganta araye? Ina idan hakan ta faru shikenan ta zama marar nasara arayuwarta.dan haka cike sa tsana ta fizge hannunta daga cikin na Queen suhaimat,kafin ta yunkura da gyar ta tashi zaune,jingina tayi da jikin bango tana maida numfashi kafin ta fara magana"tabbas abinda kunnenki yaji suhaimat,to haka yake,nice nan narabaki da ƴarki,tun tana karama,Ni nasanya baiwarki ta satomin ita,kuma nasa aka jefar da ita acan wata ƙasar,ta yadda har abada bazaki ganta ba,domin ajeji nasa aka yardata, wanda nasan,ba wani mahaluki da zai ganta agurin,kuma ko namun dawa basu cinyeta ba,yunwa zata kasheta, sannan na kashe baiwarki da hannuna dan rufuwar asirina"ammi ta faɗa cike da rashin imani tana wani zazzaro kunburarrun idanunta. Da baya Queen suhaimat ta koma ta zauna dabass.kunnenta yana amsa kuwwar maganar ammi,ko amafarki bata taba tsammanin jin wanan bayanin daga bakin ammi ba,she can't believe ace ƴar uwarta ita ce silar batan yarta,amma me tayiwa ammi haka da zafi?me ta tsare mata da har take burin ganin bayanta? Cikin muryar kuka queen suhaimat tace"uktee,me nayi miki?wane laifin na aikata agareki, da har na cancanci wannan aika aikar agareki?nifa yar uwarkice ta jini,amma kika zabi ki cutar da Ni da abinda nafiso fiye da duniyata" Cikin zafin rai ammi tace "saboda bana kaunar ki,bana sonki,na Tsaneki,ban taba sonki matsayin yar uwa ba,domin kedin mai nasarace,akan komai, ke kekiyin nasara akaina,an fifita sonki akaina,bayan haka kikazo kika auri mutumin da na ƙwallafa rai akansa,wanda nake fatan aura,amma aka aura mikishi,Ni kuma aka aura min wanda bashine cikin raina ba.suhaimat na Tsaneki,kuma nayi alƙawarin ganin bayanki, keda zuri'arki,dan kuwa ko su zayyad Allah ne ya tseratar dasu daga kaidina, da tuni na hallakasu sun bar duniyar nan"ammi ta fada tana jan numfashi da gyar,tsabar yadda take jin jiki. Kuka sosai queen suhaimat keyi,tana jin wani irin ciwo da radadi cikin zuciyarta,yanzu yar uwar ta itace ta cutar da rayuwarta haka?wannan wane irin son zuciya ne, Cikin kuka ta kalli ammi,yadda take fidda numfashi da gyar,ga ƙafarta ta dama sai jini take. Tace "amma me yasa baki sanar dani kina son habib ba? Wllh Dana bar miki shi kin aura ,meyasa kika yi haka yar uwata?ina yata take ?ina kika kaita?na rokeki ki sanar dani inda kika kaita,zan tafi neman ta, koda zan rasa raina akan hanyata ta zuwa neman ta ne,hakan shine kadai zai sanya Ni farin ciki"queen suhaimat ta fada cikin matsanancin kuka, Shi kuwa Sultan Habib tsabar kaduwa ya kasa koda matsawa daga inda yake,kallon ammi kawai yake yana jin kamar yaje ya shaketa ta mutu tabar duniyar ma kowa ya huta. Ahankali Adeeb ya riko hannun fattu,wacce take bin iyayen nata da kallo,tun shigowar su,wani irin shauƙi da farin ciki ke dibarta, ji take ko ahalin yanzu ta koma ga mahaliccinta,tabbas tayi nasara tunda har ta ga iyayenta,wayyo Allah baffa ko kana ina ?dagaka wannan ranar da kake burin zuwanta. Da sauri ta kalli Adeeb hawaye na zuba cikin idanunta,lumshe ido yayi tare da girgiza kai alamun kar tayi kuka,sannan ya sanya hannu yana share mata hawayen idonta,kafin yayi mata nuni da taje gurin queen suhaimat.kallonsa tayi gabanta na tsananta faduwa,amma ya jinjina mata kai tare da sakin murmushin da zai kwantar mata da hankali. AHankali ta fara takawa,cikin hikima da fargaba,kasancewar ba wata cikakkiyar lafiya gareta ba, hakan ya kara bata damar tafiya ahankali,kallo su amma da nanny suka bita dashi,cike da tausayawa,saidai nanny tana son gano kamar wani abu ya faru da fattu,duba da yadda take takawa ahankali,kuma tana ɗan dingisawa.amma tunani da sanin da wa fattun ke tare dashi,yasa ta kawar da tunanin da takeyi,ta dauki hakan amatsayin fargaba ce kawai. Queen suhaimat na kuka gaban,ammi tana faɗin "na roƙeki,ki sanar dani inda kika kaimin yata dan Allah "kawai saiji tayi andafa kafaɗunta . Da sauri ta juyo tare da kamo hannun wanda ya dafata, Fattu ta gani tsaye kusa da ita tana hawaye. Kallon fattu tayi cikin kuka itama tace"dan Allah ƴata ko kinsan in da zan hadu da gudan jinina?wallahi itace rayuwata,bani da wani abinso sama da ita,ki taimaka min idan kina da masaniya akan ƴata"ta kai karshen zancen ta tana Dora goshinta cikin rafin hannun fattu. Kuka fattu keyi sosai ,ganin yadda mahaifiyarta ke tsananin kaunarta,amma saboda zalunci aka rabata da ita,yanzu gashi suna tsaye tare da juna amma bata san ko wacece agabanta ba. Ahankali Adeeb ya taka zuwa garesu,hannunsa ya sanya cikin aljihunsa ya ɗauko wannan sarƙar,domin tana tare da shi dama. Kallonsa kowa keyi,harda queen suhaimat,ta bayan fattu ya tsaya tare da daura mata sarƙar nan.nan da nan sarƙar ta dauki walwali da haske ,tuni tambarin hoton zuciya mai dauke da harafin s&h ya bayyana jikin sarƙa. Cikin kasalalliyar murya ammi tace "a'a Adeeb , a'a karka daura mata sarkar nan, nayi alƙawarin suhaimat harta mutu bazata ga yarta ba,me yasa ka je kasato min sarkarnan?ashe kaine ka ɗauke sarƙar Adeeb,ka cuceni,kai amanata wayyo ni ammi na shiga uku komai ya kare"Ammi ta fada cikin yanayi na fitar hankali,wanda zamu iya cewa kwakwalwarta ta tabu. Wani shegen kallon tsana Adeeb ya jefo ammi dashi,kafin yace"kaicona rayuwarki ammi,kin cuci kanki,kuma tun yanzu kin fara ganin sakayyar Ubangiji akanki,Allah ya isa tsaninmu dake" Adeeb ya fadi hakan cikin zafin rai da kumar zuciya. Tareeƙ ne ya matso ahankali yana mai bubbuga bayan Adeeb,alamun rarrashi. Cikin tsantsar ruɗu da wani irin farin ciki queen suhaimat ke bin sarƙar da ido,kafin ta kamo sarƙar tana kalla, da sauri ta fizgi sarƙar dake wuyanta,ta kara da sarka wuyan fattu,sak!!irinsu ɗaya komai da komai, Hakan na nuna cewar fattu itace yarta?fattu itace gudan jininta wacce ta dauki tsawon shekaru tana nema?ya salam yanzu dama soyayyar da takeji azuciyarta ta fattu,tana da nasaba da kasantuwar fattu diyarta ta cikinta?wani irin kuka ne mai tsananin karfi ya kwacewa queen suhaimat,Tana mai kamo fuskar fattu,tana girgiza kai,cikin wata irin murya mai fidda amo tace "FATIMA ZARA, da gaske kece ?kece zarana diyata abin sona?"queen suhaimat ta fada cikin yanayi na rudewa. Cikin kuka sosai fattu ta jinjina kai tana kallon mahaifiyarta,da wata irin kalar soyayya mai narkar da zuciya. Kankameta queen suhaimat tayi tare da kara sakin wani irin kuka mai rikitar da mai sauraro,tana faɗin"Alhamdullah ya Allah,Nagode maka ubangiji, kaine mai juya farin ciki ya koma bakin ciki,bakin ciki ya koma farin ciki,yau kukana ya ƙare ka nuna min yata farin cikina abin sona,ya Allah ka kara karemin yata karka ba azzalumai dama akanta,Fatima zata diyata,abin sona "irin kalaman da queen suhaimat keyi kenan,tana ƙanƙame fattu,kamar za'a kwace mata ita,wanda saida ta sanya kowa kuka agurin, Cikin sassarfa Sultan Habib ya ƙaraso gurin tare da rungumesu gaba ɗaya shima yana kuka. Duk mai imani idan yaga wannan bayin Allah ,dole ya tausaya musu,dan kuka suke bilhakki da gaskiya.fattu har neman shiɗewa take tsabar kuka. Su sukuwa sai sum batar fattu suke tare da godewa Allah,daya bayyana musu ita cikin aminci. Kusan minti biyar suna cikin wannan yanayi kafin abie yayi gyaran murya cike da alhini,yana jin zuciyarsa nayi masa zafi sosai,yace "Alhmdllh ba Abinda zamucewa Allah sai godiya,yanzu kam komai yazo ƙarshe,azzamar matar nan zata girbi abinda ta shuka,tsawon shekaru.dan haka akwai bukatar kowa yaje ya hutawa zuciya da jikinsa.Rashad kuyi hakuri,akan abubuwan da nayi ta nuna muka abaya kaida mahaifiyarka,sam hakan ba yin kaina bane,sharrin wanann makirar ne"abie ya faɗa yana nuna Ammi,wacce take kwance sharaf kamar gawa. Girgiza kai Rashad yayi kafin yace "abie nima ka yafemin,domin nayi ta sanya ka cikin damuwa da tashin hankali,kuma duk sharrin ammi ne azzaluma"ya fada yana hararar gurin da ammi ke kwance sharkaf. Matsowa gareshi Adeeb yayi tare da shafa kansa yace "Allah ya baka lafiya lilna, sannan ya kara tsaremi daga sharrin masu hali irin na ammi" da Amin suka amsa gaba dayansu. Ko kallon inda ammi take Adeeb baisonyi,dan sosai yakejin haushin kansa ,na kasa fahimtar gaskiya da yayi tun dadewa,har ammi tayi wannan gagarumar nasara akansa. Abie ne ya sanya wasu dakaru suka shigo dan fitar da ammi daga dakin,yace su kaita can kurkuku mafi tsanani da duhu su ƙullewa aciki.kafin ayanke mata hukunci. Haka suka kinkimi ammi batama san inda kanta yake ba sukayi waje da ita. Juyawa sukayi gaba ɗaya,Suna shirin barin dakin sukaji kamar motsi cikin dakin da aka kulle Zulaihat,dan haka cikin azama tareeƙ da Adeeb suka nufi ƙofar,da gyar suka balle kofar,dan sun rasa makullin. Aikuwa suna budewa suka hangi Zulaihat kwance abakin ƙofar adaddaure, gaba ɗaya jikinta jini kaca -kaca.cikin azama suka fara kunceta,ta galabaita sosai kuma har lokacin kanta na zubda jini, Da gyar ta buɗe idonta ta kalli Adeeb tace "my prince,karkaci abincin nan akwai guba aciki, kuma tare suka hada baki zasu kasheka"ta karasa da gyar,jini na zuba daga bakinta. Abie ne ya ƙaraso gurin da sauri yana faɗin"Zulaihat Meya sameki haka?waye yayi miki wannan abun,kuma ammi ita da wa suka hada bakin"abie ya faɗa yana jin bugun zuciyarsa na kara tsananta,dan baisan kuma wa Zulaihat zata ce ba. "Cikin mawuyacin hali,Zulaihat tace"Abba.....na,abba na ne,tare suke kulla komai shida ammi,karku barshi"tana faɗin haka idanunta suka kakkafe jikinta ya saki. Cikin wani irin bugawar zuciya abie yace "w...a....z..... Sai kuma ya kasa karasawa kawai ya zube agun asume. Hmmmmm masu karatu wannan wace irin rayuwace ?wacce amana tayi karanci?dan uwa shine zai cutar da dan uwansa. Allah kasa nufi karfin zuciyarmu ammen. Mu hade next page. Mrs babi ce 💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 15:01] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free book Page 83/84 💥🔥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 🔥💥🔥💥🔥💥🔥🔥💥 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji💃🏻💃🏻💃🏻🔥 Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu 👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji 🔥💥 Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan💥🔥💃🏻 Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa😉😉 Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki👍🏼💃🏻💃🏻 Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc 💥🔥 Kalolin tsumi👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻 Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono raƙumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar HQ💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida🥰🥰🥰🥰🥰👍🏼👍🏼👍🏼👍🏼 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah🤝🏼🤝🏼 Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera sokoto state💥🔥💥🔥💃🏻 ________________Nazo in sanar dake cewa,na sami labarin gubar da kika sanyawa Adeeb cikin abincinsa yau,kuma ina mai tabbatar miki awannan lokacin bazan gyalekiba,zanyi duk wacce zanyi wajen ganin bayanki"amma ta faɗa cikin fushi tana hararar ammi. Dararaam!!! gaban abie ya fadi,cikin hanzari ya nemi gurin zama,dan ji yayi jiri na neman kayar dashi, innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,guba kuma Ammi ta sanyawa gidan jininsa,?dan da ta raina da hannunta?meye ribarta idan ta kashe adeeb?me take nema. Da sauri Adeeb ya matso kusa da mai martaba tare da kama hannunsa ya rike gam cikin nashi,ɗago kai mai martaba yayi idanunsa sunyi jaa,yana kallon Adeeb ,lumshe ido Adeeb yayi yana ɗan karyar da kansa ,alamun abie ya kwantar da hankalinsa.jinjin kai mai martaba yayi tare da lumshe ido yana ambaton sunan Allah,dan tuni zuciyarsa ta fara masa zafi.sai dai cikin hanzari ya bude idonsa sakamakon jin abinda ammi ke faɗi. Hahhhhhh,ammi ta gyalgyale da dariya,kafin ta fara magana"wai kekam meye naki ne aciki idan na kashe adeeb?shin ke kika haifi Adeeb ko yaya?burina ne in kashe adeeb, kamar yadda na kashe uwarsa da yan uwansa,domin basu da wani amfani agareni,baki sani ba,wani ƙarin bayanin ma,zan kashe wancan tsohon mijin naki, bayan na gama da ɗan gaban goshin nashi,ke ko kishin yadda sarki ke ƙaunar Adeeb bakyayi?saboda ke shashashar uwace,har sadaukar da ɗan cikin ki kikayi akan wani banzan ɗan kishiya,to ki sani wllh idan kikace zaki zama Tsaiko,akan abinda nake shiryawa, tayi shiru tana sakin wani irin murmushi mai cike da zalumci,kafin taci gaba"zan kashe ki kema,dan bana barin duk wanda ya shigo hanyata.dan haka ya fi miki kiyi gum da bakinki, ko kya samu damar kula da wancan masakin dannaki,wanda na gama da rayuwarsa,ko yanzu nasan naci riba akanku,na lalata alakar dake tsakanin Adeeb da Rashad,na sanya musu tsanar juna,ta yadda har abada zasu so junansu ba.sannan na sanyawa Adeeb tsanarki cikin zuciyarsa,dan kuwa na sanar dashi kece kika sanya mai kula da motoci ya sawa uwarsa bomb amota,Dan kawai baki sonta,kuma shima baki sonshi. Naso ace Adeeb yana da zafin zuciyar da zai iya kashe ki,dan nayi ta yunkurin sanyashi aikata hakan, amma ban samu dama ya kashekin ba.kinyi sa'a.saidai kina don jefe rayuwarki cikin matsala,da don shiga sabgar da baruwanki cikinta,ki kula domin Ni da kaina tsoron kaina nake"ammi ta fada tana wa amma kallon gargadi. Cikin dakiya da nuna jarumta amma tace "kinyi kuskure ammi,domin kin manta cewa rana daya ta barawo,rana daya ta mai kaya.in sha Allahu asirinki ya kusan tonuwa,za'ayi walkiya kowa ya ganki,yanzu kin zalunci yaro ,kunsa yana mako kallon uwa,ashe ke ba kallon da kike masaba, to ki sani wllh haƙƙinmu kadai ya isheki bakin cikin rayuwa"amma ta faɗa idanunta cike da kwalla. "Hakki ?hakki kike magana?wayace miki ina tsoron hakki ?kada ki damu kanki domin wannan abun da nayi maku,nayi shine cikin tausasawa da nuna sanayya,amma bayan haka da tuni na gama daku"ta fada cikin murmushi tana lumshe ido da budewa. Gaba daya jikin abie banda rawa ba abinda yake ,tashin hankali ya bayyana ƙarara cikin idonsa,kai duniya,yanzu ammi itace ta kashe masa matarsa abin sonsa?itace ta kashe masa yayansa ?tare da amintaccen drivernsa?kai ammi ta cutar dashi,ta lalata masa farin cikinsa,ta karya masa zuciya bazai taba yafe mata ba har abada. Nan take hawaye ya fara wanke masa fuska ba abinda yake tunani sai yadda ya dauki amana ya mikawa ammi,ita ke kula da komai nashi,bayan irin maganganun da take faɗa masa akan amma,shiyasa sam yana wani damuwa da amma da ɗanta, ashe duk makircin ammine,kai wannan mata ta cika azzaluma. Cike da tausayawa da tarin damuwa Adeeb ya ƙara damke hannun abie,cikin tashin murya yace "abie kayi hakuri nasan dole hankalinka ya tashi,nima kwatankwacin irin hakan naji,lokacin da nasan gaskiyar komai,abie akwai sauran abubuwan da baka saniba game da ammi,dan Allah ka kwantar da hankalinka mu shiga domin tuhumarta gaba da gaba,abie ammi ta jima ta cutar da al'umma,harda yan uwanta ma bata bari ba,kasan kuwa itake da hannu wajen batan ɗiyar sarauniya suhaimat?"Adeeb ya faɗa cikin ƙasa ƙasa da murya ta yadda ammi bazata kiyo suba. Cike da wani karin mamakin abie ke kallon Adeeb kafin yace "duk muguntar ta Adeeb bana tunanin zata cutar da yar uwarta,amma kai ina ka sami wannan labarin?"abie ya faɗa muryarsa na rawa numfashinsa na cikowa. Ajiyar zuciya Adeeb yayi kafin ya kalli gurin da fattu ke rakube jikin nanny,kuka kawai suke cike da nuna godiyarsu ga Allah,domin yau ƙarshen zaluncin ammi yazo. "Abie wannan yarinyar da na taho da ita from Nigeria,itace yar gidan anty suhaimat da Sarkin Ghana Sultan Habib nawar"ya faɗa yana kallon fattu wacce kanta ke duke zuwa wannan lokacin. Cike da zallar mamaki abie ke kallon fattu,lallai ammi tayi nisan da bazata taba jin kira ba,to menene dalilinta na cutar da yar uwarta?me yasa ta zabi batar da yarinyar ƙanwarta?"sannu kinji yarinya Allah ya baku hakurin jure wannan jarabawar,sannu kinji "abinda abie ke iya fadi kenan cike da tausayawa. Mikewa sukayi gaba ɗayansu suka nufi cikin falon da su ammi ke ciki.dai dai lokacin tana fadin" wllh nayi alƙawarin ganin bayan wannan ahalin,saina karbe masarautar nan daga hannunku, bazan bar daya daga cikin ku ya rayuba,zan gama daku dukkan ku,tunda har ina da goyon baya na daya daga cikin masarautar nan, kuma...... Kalama ammi suka katse,sakamakon ganin mutane suna ta shigowa cikin falon, Da mugun hanzari ammi ta mike tsaye jikinta yana rawa,baki buɗe take kallon su abie,Adeeb ,fattu da kuma nanny,meya kawosu awannan lokacin?me sukazoyi mata haka gaba dayansu?ko dai wani abu suka ji?ko suma sunsan cewar ta zubawa adeeb gubar ne?wayyo allah,me Yakamata tayi ne?ya zama dole ta kwace kanta fa.dan haka cike da tsabar makirci da iya kissa tayi saurin zuwa gurin mai marta,jikinta na rawa . "Naji dadin zuwanku mijina,Allah ne ya cecini daga sharrin wannan makirar,domin tazone ta sanar dani,wai zata kasheni,kamar yadda ta kashe Nazli,mijina wannan matar azzalumace, Ta zubawa adeeb guma shima cikin abincinsa sannan ita ta lalata rayuwar sanya da kanta,yanzu take fadamin hakan kuma shigo,dana ku taimaka min ku fitar da ita daga ɗakin nan kasheni zatayi"ammi ta fada cikin kuka da nuna tana cikin tsoro,tare da ƙanƙame hannun Sultan wato abie. Cikin mamaki gaba dayansu suke kallon ammi,lallai ammi ta cika ta batse, sharri,makirci,kissa da kisisina,tabbas ajikinta suke,yanzu badan sunji duk abinda take faɗi ba,ba yadda za'ayi kace zancen ta ba gaskiya bane,duba da yadda lokaci ɗaya ta rikice tayi wuji wuji da ita tana kuka. Cikin zafin zuciya da tsantsar tsana ,abie ya sanya dukan hannayensa biyu ya hankade ammi daga jikinsa,ji kake timmmm!ta fada kan wani table dake gefen kujera. Wani azababben ƙara ta kwalla tare da kallon abie,jikinta na mugun rawa,lallai tasan yau kam komai yazo ƙarshe,wato alamu sun nuna abie yaji duk abinda take faɗi,kenan makirci amma ta kulla mata? Amma tsabar kokari irin nata,yunkurawa tayi cikin dauriya ta mike,tana kallon abie da Adeeb, tace "dan Allah ku yarda da abinda da na wllh wannan matar makirace zata kashe Ni kuma ita ce... Maganar ta maƙale sakamakon wasu gigitattun maruka da abie ya saukewa ammi akumatun ta har guda hudu. Faduwa tayi can gefe cikin azabar raɗaɗin da kumatunta keyi,ji tayi ma kamar gurin ya sale. Ihu ta kara kwallawa cikin azaba tana faɗin , "Wayyo mai martaba na tuna kayimin rai ka daina dukana wayyo Allah kumatuna" Kafin ta gama rufe baki kawai taji duka ta ko ina,fuskanta abie keyi kamar ya sami kayan wanki,tun tana ihu tana neman taimako harta kasa daga koda Dan yatsantane,jini ta baki ta hanci.da gyar Adeeb ya janye abie,kuka sosai abie keyi,tanadin"kin cuceni,kin zalunceni,Allah ya isa tsakanina dake,kuma na sakeki saki daidai har uku,sannan saikin girbi abinda kika shuka,muguwa makirar mace,kuma maza maza ki sanar dani dalilin ki na batar da wannan yarinyar daga ahalinta" Abie ya faɗa cikin rawar murya yana kamo hannun fattu ya matso da ita kusa da ammi ,wacce ke kwance cikin mugun yanayi,ko motsin kirki batayi,gaba ɗaya jikinta ya saki,da gyar take fidda numfashi, Idonta daya ya kumbura suntum,bakinta ma ya aune, kamamaninta duk sun sauya. Banda kuka ba abinda fattu keyi,gana daya atsorace take jikinta rawa kawai yake tana kallon ammi. Cikin tsawa abie yace "bazakiyi magana ba,saina karasaki"ya fada yana kai mata kafa, Wani wahalallen ƙara ammi ta sanya,cikin azaba tana ɗan bude idon ta daya"zanyi bayani, zanyi bayani dan Allah kuyi min rai,tabbas wannan yar gidan suhaimat ce,kuma nice na batar da ita tun tana karama" Ƙarar faduwar abu da sukaji ne yasashi saurin juyawa ɗan ganin ko menene,ba kowa bace face suhaimat da mijinta,wanda tareeƙ ya shigo dasu yanzun,kuma maganar ammi ta sauka akan kunnensu..... Masu karatu muje zuwa, Gada ammi kwance cikin mugun yanayi,wane fata ,zakuyi mata. Ina mai nannadaddiyar fuska ne? Muje zuwa, takuce anty mammy Mrs babi💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 15:01] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 87/88 _______________Cikin wani irin mugun bugawar zuciya, abie ya bude bakinsa dake rawa yace "wa.....z..ii..rr"sai kuma ya kasa ƙarasawa, sakamakon numfashinsa daya dauke.nan ya zube gurin asume. Cikin hanzari Adeeb da su Sultan Habeeb,sukayo kansa. "Abie !abie!!Adeeb ya kira sunan Sultan yana jijjigashi.amma ko motsi bayayi,da hanzari suka zareshi suka nufi part dinsa dashi,suna zuwa likitocinsa suka rufu akansa. Zulaihat ma asibitin cikin masarautar aka nufa da ita kai tsaye,sosai ta galabaita,dan jini sai zuba yake ta bakinta,kamar ma aman jinin take, Queen Suhaimat,na riƙe da hannun ɗiyarta gam, dan bazata ƙara bari,fattu tayi nisa da itaba in Sha Allah. Amma ma tabi su Adeeb dan ganin ya jikin Sultan ɗin. Dan haka nanny ke tura keken Rashad suka fice daga ɓangaren Ammi,kai tsaye bangaren Sultan suka nufa suma,dan hankalinsu yaki kwanciya,suna buƙatar ganin ya jikin nashi. Cikin ikon Allah kuwa aka samu Sultan ya farfaɗo,saidai banda hawaye ba abinda idanunsa keyi. Damuwarsa ta ninka ta farko,wannan cin amana da me yayi kama?ace dan uwanka ma baka wuce ya cutar da kaiba,yanzu dama za'a iya hada baki da waziri acutar da rayuwarsa,dashi ake ƙoƙarin kashe masa gudan jininsa?lallai yau da iyayensu suna raye tabbas ba abinda zai hana zuciyoyinsu bugawa. Duk irin so da ƙaunar daya nunawa waziri,amma ƙarshen halaccin da zaiyi masa kenan?yana tare dashi, komai nashi waziri,ko wace shawara dashi yake,ashe shikuma yana amfani da wannan damar ne yana cin dunduniyarsa?kai rayuwa Allah ya shige mana gaba. Adeeb ne ya,zauna kusa da mahaifin nashi, tare da riko hannunsa yana kallon idonsa,cikin tattasan lafazi yake rarrashin Sultan"abie dan Allah ka kwantar da hankalinka,Ni dama najima ina zargin uncle,kuma koda muka shiga part din Ammi,Ina kallon lokacin daya zare jiki ya bar part din,Dan haka nayi saurin bada umarnin akamoshi dan dama tuni na shirya komai,yanzu haka yana hannu"Adeeb ya faɗa cikin sanyin murya yana murza hannun abie cikin nutsuwa. Ajiyar zuciya Sultan ya sauke tare da lumshe ido,kafin ya buɗe su. "Habeebee mutanen dana yarda dasu,su suka cutar dani,nayi dana sanin kasancewarsu makusantana,kuma na gode Allah dayasa bani da zuri'a da Ammi,da ta gurbatamin zuri'a da mugun iri,Allah Sarki matata Nazli,Allah ya jiƙanki yayi miki rahama,tare da yarana da kuma amintaccen driverna"abie ya faɗa cikin zubda hawaye yana jin zafi cikin zuciyarsa. Haka su Adeeb da baban fattu sukayi ta rarrashinsa akan ya kwantar da hankalinsa,karya sanya damuwa cikin ranshi har yazo ya samu matsala babba. Barcine ya dauke Sultan,dan haka suka fito zuwa babban falo,suka zauna dan tattauna yadda za'ayi. Fattu na zaune kusa da mahaifiyarta,ta ɗora kansa akan cinyar innarta,wani irin nishaɗi da jin dadi takeji cikin ranta,wai yau itace tare da mahaifanta, lallai duk wanda ya mika lamuransa ga Allah,to tabbas zai ga daidai arayuwarsa. Queen Suhaimat ma cike take da farin ciki,zuciyarta fess,ahankali take shafa kan fattu cike da tsantsar ƙauna,itakam tayiwa Allah godiya da wannan ni'ima da yayi mata,yau gata ga zaranta bayan shuɗewar shekaru masu yawa,ita dama bata taɓa cire rai da tsammani ba. Suna nan zaune saiga su Adeeb sun fito daga cikin dakin,yana tura keken da Rashad ke kai,dan suna zuwa falon shima ya shiga gurin mahaifin nasu. Tunda suka fito idon Adeeb yana kan fattu,kamar yadda itama take kallonsa,tana jin wata irin kaunarsa na ratsa dukkan sassan jiki da jininta,haƙiƙa Adeeb ya zame mata alkairi,haduwa dashi nasarace,kuma in sha Allah zata kula dashi,zata nuna masa soyayya ta gaskiya cikin amana da girmamawa. Murmushi Adeeb ya sakar mata tare da dan shagwabe fuska,irin na nayi kewarki ɗin nan,itama murmushin ta sakar masa tare da lumshe ido alamun rarrashi,kamar yadda yake mata. Zama yayi kan kujerar dake saitin wacce Queen suhaimat ke zaune,ta yadda zai rinƙa kallon fattunsa. Duk abinda sukeyi nanny na kallonsu,murmushi kawai tayi tare da girgiza kai. Queen Suhaimat ce tace "ya jikin Sultan ɗin?" "da sauki jikinsa kam,yanzu haka yayi barci ma"Adeeb ya bata amsa cikin girmamawa. Wayar Adeeb ce tayi ƙara, ta jikin agogonsa, dagawa yayi tare da cewa ku "shigo dashi ciki" Ya kashe wayar. Ko minti biyar ba'ayiba saiga wasu dakarun fadar sun shigo da waziri yana gaba suna binsa abaya,yayi tsilli tsilli da ido,kunyar duniya ta gama lalata masa zuciya, Durkushewa yayi atsakiyar falon kansa aduƙe,yana jin kamar ƙasa ta tsage ya shige ciki. Kallonsa kawai suke cike da alhini da jinjina rashin amana irin na waziri. Adeeb ne ya miƙe cikin nutsuwa ya nufi gaban waziri,tsayawa yayi tare da sanya hannu cikin aljihun wandonsa, ya kafe waziri da ido,na tsawon lokaci kafin ya nisa ya fara magana"uncle ka bani mamaki,ka sanya zuciyata tunanin cewar lallai mutane ba abin yarda bane,uncle me muka tsare maka arayuwa?me nayi maka kake son ganin bayana tare da mahaifina?uncle me ka nema agurin mahaifina bai maka ba?uncle yanzu da kai za'a hada baki ɗan ganin bayan dan uwanka? Uncle why ?yaushe kazama haka?yaushe ka bari shaidan yayi nasara akanka?har idanunka suka rufe kake cutar da wanda ya aminta dakai sama da kowa?"Adeeb ya faɗa cikin salon sa mai sanya mutum shiga taitayinsu. Kuka kawai waziri ya sanya tare da kamo ƙafar Adeeb"kayi hakuri dana,ka yafemin wllh sharrin zuciya dana shaidan ne suka sanyani aikata wannan abubuwan,da kuma kwadaituwa da son hawa karagar mulki,dan Allah ku gafarceni"ya faɗa cikin kuka sosai yana riƙe da kafar Adeeb. Lumshe ido Adeeb yayi zuciyarsa na masa zafi sosai haƙiƙa abubuwan da su uncle suka aikata shida Ammi,sun cancanci hukunci,dan haka dole ahukuntasu. Cikin salon sa na haɗe rai yake kallon uncle kafin yace "menene gaskiyar al'amari akan asirin zama maciji da akayi min ?"cewar Adeeb kenan yana kallon waziri. Ɗago kai waziri yayi cikin zubda hawaye,yace "tabbas bazan boye maka ba,nine nan nasa akayi maka asiri ka zama maciji,domin farko nayi niyar ka auri yata Zulaihat,inyaso inbata guba ta sanya maka cikin abinci kaci ka mutu,sai kuma ka nuna rashin amincewa da auren Zulaihat,wannan shine ya kara tunzurani,naje gurin boka aka hada maka zazzafan asiri da kalolin macizai na duniyoyin aljanu da ban daban,wanda idan ka bar fadar nan,shikenan ka barta har abada,kuma nine da kaina na daukeka na kaika can yankin Nigeria,dan ko ganin ka bana sonyi kusa da fadar nan"waziri ya faɗa yana hawaye. Salati gaba ɗayansu suka dauka,kowa yana Allah wadai da waziri,saboda son zuciya da abin duniya,yake kokarin hallaka dan dan uwansa. Runtse ido Adeeb yayi cike da kumar zuciya,yama rasa me ya kamata yayi. Daga bakin ƙofar dakin abie sukaji magana yana faɗin"waziri ka cuceni ka ci amanata ka yaudari soyayya irin ta yan uwan taka,me nayi maka haka da zafi ?kake son ganin bayana?duk irin kulawa da soyayya irin ta yaya da ƙani dana nuna maka,amma yau kaine ke son ganin bayana?kaje dan kanka,duniya zata koya maka hankali,kuma ko yanzu kasan Allah shine ke da iko akan kowa,dan gaka a ƙasa Ni kuma da iyalina muna samanka"abie ya faɗa cikin zubda hawaye yana dafa bango. Da sauri Adeeb yayi gurinsa tare kamo hannunsa ya zaunar dashi akan kujera. Cikin kuka waziri ya rarrafo gurin mai martaba yana bashi hakuri, Suna cikin haka Tareeƙ ya shigo cikin dakin da sauri . Duk waigawa sukayi suna kallonsa, Cikin girmamawa yayiwa Sultan sannu da jiki,kafin ya isar musu da saƙon mutuwar Zulaihat . Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,shine abinda Dukansu suka haɗa baki gurin faɗa. Shikenan Zulaihat ta riga mu gidan gaskiya,Allah ya yafe mata kurakuranta. Waziri kuwa daskarewa yayi azaune jin labarin mutuwar ɗiyar tasa guda ɗaya tilo, Ihu ya sanya tare da faduwa agurin yana birgima... Mu hade anjima. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 15:01] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE 🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 89/90 _______________Waziri kuwa,daskarewa yayi agurin,tsabar shiga ruɗu da yayi,sakamakon jin abinda tareeƙ ke faɗa. Ihu ya sanya tare da faduwa agurin yana birgima da kuka.shikenan ya rasa yarsa, Zulaihat ta tafi ta barshi,ita kadaice ƴar da ya mallaka a duniya,yanzu gashi sakamakon mugun nufinsa ya rasata.kuka yake sosai cike da tarin nadama da dana sani. Gaba daya sun ji mutuwar Zulaihat,cike da alhini suka dunguma har waziri,saidai yana karkashin kulawar dakaru,saboda karyayi yunkurin aikata wani abu. Haka akayiwa Zulaihat wanka,tare da sallar gawarta aka kaita gidanta na gaskiya.sai muce Allah ya yafe mata kurakuranta. ,Kai tsaye daga gurin makoki,kurkuku aka wuce da waziri. Sukuma suka dawo falon Sultan suka zauna.anan Adeeb ke sanar dasu Queen Suhaimat cewar akwai wanda ya rike fattu,ma'ana wanda ya tsinceta tun tana karama,kuma shine ya raineta harta girma. Sannan shine mutumin da suka taimakeshi tare da Fattun.dan haka idan ansami nutsuwa yana son zasu tafi da fattu domin dubo halin da yake ciki. Sultan Habeeb ne yayi gyaran murya kafin yace "ai wannan tafiya damu ya kamata ayi ta,dolene muje musaka masa da abinda yayi mana,dan kuwa ya cancanci yabo da kyautatawa agaremu" Sultan ya faɗa cike da jinjinawa bawan Allah daya kula masa da ɗiyarsa. Shiru falon yayi nadan lokaci kafin Adeeb yayi gyaran murya,yana mai kallon kowa cike jinjina maganar da yake son fadi. Baisan ya zasu dauki maganar ba.ko zasu yarda da batun aurensa dake kan fattu?duba da yanayin shekarunta. Dan haka cikin nutsuwa ya fara magana"Abie,uncle da sauran mutanen dake cikin dakin nan,akwai Abinda nake son sanar daku,amma bansan ta yaya zaku fahimci maganar tawaba, saidai nayi hakan ne bada wata manufa ba,saidan kare hakkin addinina.yayi shiru yana da kallon yanayin fuskokinsu,kafin ya maida kallonsa ga fattu,wacce ke jikin mahaifiyarta,ta ɗora kanta akafadun innarta,jikinta yayi mugun sanyi,dan sosai taji mutuwar Zulaihat,dan adam ba abakin komai yake ba,yanzu duba fa dazun nan Zulaihat tana raye,amma yanzu har an kaita makwancinta.Allah kasa mudace. Haɗa ido sukayi da Adeeb wanda yake kallonta cike da kauna,yana fatan Allah yasa iyayensu su yarda da batun auren dake tsakaninsa da fattu,dan bazai iya rayuwa ahalin yanzu batare da fattu ba. Fattu ta zama jinin jikinsa,ta zame masa,mahadin rayuwa,kuma farin cikinsa. "Muna jinka dana, ka fadi abinda ke cikin ranka karka damu,zamu zama masu fahimtar ka"Sultan Habeeb ya faɗa yana mai dafa kafadun Adeeb,dan yana kusa dashi ne. Jinjina kai Adeeb yayi kafin yaci gaba da faɗin"lokacin da zamu taho kasar nan da Fatima,nayi tunanin haramcin yin tafiya da yarinya mace,wacce ba muharramarka ba,dan haka,nayi shawara da tareeƙ akan cewar,zan auri Fatima in taho da ita amatsayin matata,kuma zata ci gaba da zama matsayin matar tawa,har zuwa lokacin da iyayen ta zasu bayyana.sai In sawwake mata ta koma garesu,lokacin da aka daura auren itama kanta bata sani ba,sannan tareeƙ shine wanda ya zama waliyyinta,shina bawa sadakinta,kafin aka daura mana aure.yayi dan shiru kansa akasa kafin yaci gaba"awancan lokacin nayi aurenne da nufin idan iyayen Fatima suka bayyana zan sawwake mata,saidai kuma ahalin da ake ciki yanzu,bazan iya rabuwa da Fatima ba,ina rokon alfarmar ku barmu, mu rayu tare muci gaba da zama matsayin ma'aurata,domin ina sonta"Adeeb ya kai karshen zancen sa cike da faduwar gaba,yana fatan Allah yasa su amince da batunsa. Ajiyar zuciya suka sauke dukansu, hakika wannan batun yayi matuƙar daɗaɗa musu rai,domin Adeeb mutum ne wanda duk wasu iyaye zasuyi fatan ya kasance mijin ga yarsu,dan haka ta bangaren su Queen Suhaimat kam,ba wata matsala,dan kallon juna sukayi ita da mijinta cike da jin dadi,suna murmushi. Abie ma abun yayi masa daɗi,saidai dole abawa yarinyar da iyayenta dama,idan sun amince da batun auren shikenan,sannan itama yarinyar sai sunji ta bakinta idan ta amince shikenan. Amma ma taji daɗin maganar Adeeb sosai,domin ta jima tana fatan ace,inama Adeeb zai auri fattu,dan ta yaba da hankali da kuma nutsuwar fattu,saidai awancan lokacin ba damar fadin abinda ke cikin ranta. Abie ne yayi murmushi cike da jin daɗi,kafin ya kalli Sultan Habeeb,ya fara magana"Sultan kaji abinda ɗan nata ya faɗa ko,ina fatan dai zuciyarka tana irin tunani da fatan da nakeyi, dan haka ina jiran jin ta bakinka,kaida mai dakinka" Murmushi uncle Habeeb yayi kafin yace "ai ranka shi dade,wannan abun yayi min daɗi fiye da yadda kake tsammani,dan haka mudai ba abinda zamuce, sai Allah ya haɗa kansu,ya basu zaman lafiya, sannan ya karesu daga dukkan sharrin abin ki"ya kai zancen sa fuskarsa ɗauke da murmushi. Wani irin sanyin daɗi ne ya ratsa zuciyar Adeeb, Alhamdullah shikenan iyayen fattu ma sun amince da aurensu, shikenan bashi da wata matsala. Kallonshi ya kai ga fattu,amma bai sami damar hada ido da itaba,dan kanta na duke,murmushi yayi wato fattu irin matan nan ne masu,kunyar ,hmmm zama ta ware ne ,dan shikam wllh zagewa zaiyi ya koyar da ita salon soyayya kala -kala,dan shi mutum ne mai son soyayya daga matarsa. Hamdala abie yayi kafin yace "tunda yanzu mu Dukansu mun amince da wannan auren,yana da kyau muji ta bakin yarinyar,dan kar'ashiga hakkinta,tunda bada saninta akayi auren ba.dan haka Ƴata karki cuci kanki,ki sanar dani shin kin amince da wannan auren ko kuwa?"abie ya faɗa yana mai kallon fattu,da fatan Allah yasa itama tace ta amince. Fattu kuwa kunyar duniya ta gama cika mata ciki,ji take kamar ƙasa ta tsage ta shige ciki,yanzu ta yaya zata amsa muce cewar tana son Hamma?tab !wllh bazata iyaba. Gaba ɗaya dakin yayi shiru,amsar fattu kawai ake jira,saidai ba alamun fattu zatace wani abu. Ƙuri !!Adeeb ya kure fattu da ido,karfa Hulwa ta ki amincewa da aurensa?kai baya wannan tunanin, domin yasan Hulwa na sonsa sosai bazata taba kin zama dashi ba.dan haka kallonta yake danjin mezatace. Ganin fattu ta kasa magana sai kara sunkuyar da kanta take,yasa ammi dafa kafadunta cikin murmushi tace "karki ji tsoro yata,ba wanda zaiyi miki dole,amsarki kawai ake bukata"nan ma dai shiru fattu tayi bata ce komai ba.kunya take ji sosai. Ajiyar zuciya abie yayi kafin yace "to alamu dai sun nuna Fatima bata amince da wannan auren ba,dan haka habeebee dole kayi hakuri ka sawwake mata"abie ya faɗa yana kallon fattu dan ganin yanayinta. Aikuwa da sauri ta ɗago kai tana zaro ido waje,cikin muryarta mai kama da shagwaba tace "a'a Abie nifa bance bana sonshi ba,dan Allah karkasa ya sakeni,na amince Nima Ina sonshi"fattu ta faɗa cike da kuruciyarta, idonta akan Adeeb. Gaba daya saida ta basu dariya,dan dai kawai suna cikin alhinin rashin Zulaihat ne, ya hana su darawa.amma saida suka murmusa. Ajiyar zuciya Adeeb yayi yana mai kafeta da ido,sosai yake jin tana kara shiga cikin zuciyarsa. Koda su Sultan zasu koma Ghana,sun bukaci tafiya da fattu, domin ta gana da yan uwanta,sannan ta dan saba dasu,amma ba jimawa zatayi ba tunda da aurenta. Adeeb ji yayi kamar ya kwalla ihu, dan yasan zai sha wahala zama ba tare da fattu ba,amma ba yadda ya iya dole ya amince,akan idan komai yayi daidai, zaizo sai su wuce Nigeria wajen baffa. Queen suhaimat kuwa tayi hakanne,dan tana son ta gyara yarta sosai,yadda zata kara martaba agurin Adeeb. Cikin yanayi na gajiyar jiki da zuciya,ga tarin kewar fattu da Adeeb ya fara tun yanzu,ya mike tare da cewa"Anty bari muje dan ta shirya kayanta"ya faɗa yana kallon fattu,fuska amarairaice. Kallonsa fattu ma keyi,cike da tausayinsa,dakuma kewarsa,amma dole tabi iyayenta,dan kuwa tana bukatar jin duminsu ajikinta,sannan tana son ta san yan uwanta. Queen suhaimat ce ta kalli fattu tace "Zara kije ki shirya kayanki maza "ta fada tana shafa kan diyar Tata cike da so da ƙauna. Mikewa fattu tayi,cike da kunya,tabi bayan Adeeb dan tuni yayi gaba. Tana fita ta ganshi ya jingina bayansa da jikin bango,idanunsa alumshe.tana zuwa ta tsaya akusa dashi,tare da sanya hannu ta rike hannunsa.ahanakli ya buɗe idonsa tare da saukewa akan kyakykyawar fuskarta.baice komai ba ya rike hannun nata suka nufi part dinsa. Suna shiga ya janyota jikinsa ya rungume tsam.ahankali yake sauke ajiyar zuciya,idanunsa alumshe.fattu ma lumshe ido tayi cike da jin tsananin so da kaunar Adeeb cikin zuciyarta. Ahankali ya fara magana"Hulwa komai yazo ƙarshe,Allah ya bayyana mana azzalumai,mun ganesu, yanzu lokacine da nake bukatar kulawar ki da soyayya,saidai kuma gashi zakiyi nisa dani, alokacin da nake tsananin bukatarki kusa dani,Hulwa zanyi kewarki sosai"Adeeb ya faɗa cike da jin kewar fattu sosai yana kara kankameta ajikinsa. Cike da tausayi fattu tace"Hamma nima fa zanyi kewarka, amma ai ba dadewa zanyi ba,ina son zama tare da iyayena,dan inji dadin da ake ji idan ana tare da su.amma Hamma zanyi kewarka sosai"itama ta faɗa ahankali tana mai ƙara kwantar da kanta cikin faffadan kirjinsa. Sun jima ahaka,rungume da juna,Adeeb yana ta saukewa fattuhadda, wanda har bata san lokacin da ta biye masa ba itama,duk abinda yayi mata, itama shi take masa.basu rabu da juna ba har saida Adeeb ya samu nutsuwa sosai.kafin suka daure suka rabu da jikin juna,sai lokacin fattu ta fahimci ko kaya babu ajikinsu.kunya ce ta kamata,da sauri ta janyo bargo ta rufe jikinta tare da lumshe idonta. Murmushi Adeeb yayi yana mai gyara mata gashin kanta daya barbaje,kafin yace "Hulwa meye kuma na rufe ido?nifa bana son wanna kunyar taki,Please ki buɗe ido ki kalleni,kinji?"ya faɗa yana hura mata iska akan idanunta. Cikin wani irin salon murya mai cike da nishadin soyayya tace "Hamma Ni wllh kunya nakeji,kayi ta gane min jiki"ta faɗa ahankali tana rungumeshi. Rungumeta shima yayi cike da soyayya kafin yace "hulwata idan ban kalli jikin ba,jikin wa zan kalla?jikinki mallakina ne,shine abinda zan kalla ya debemin kewa dan Allah karki hanani kallon abinda ke sani nutsuwa" ya faɗa cikin salon sa na shagwaba yana ɗan turo baki. Murmushi fattu tayi tana mai kara cusa kanta akirjinsa,cike da kaunarsa. Gaba daya sun shagala da nunawa juna soyayya,sun manta da su, Sultan Habib dake jiran fattu,saida wayar Adeeb tayi kara sannan suka farga,kiran Abie ne dan haka cike da kasala ya mika hannu ya daga wayar, "To Abie gamunan "kawai ya faɗa tare da kallon fattu yace "Hulwa su anty na jiranmu"ya fada kamar zaiyi kuka. Da sauri fattu ta mike tana zaro ido,wllh sam ta ma manta da batun tafiya Ghana,gaba ɗaya Hamma ya mantar da ita komai da soyayyarsa. Shagwabe fuska tayi tana mai faɗin"Hamma kaga kasa na manta da su inna suna jirana ko?"ta fada tana nufar toilet da sauri tana tafe tana bubbuga kafa,ciki da tabara. Lumshe ido Adeeb yayi yana mai faɗin "wayyo hulwata,zaki kasheni da salonki"kafin ya bita toilet din,wanka sukayi tare sannan suka fito,da kansa ya shirya fattu,kafin ya haɗa mata kayan da yasan zata bukata,sannan suka fito. Haka Adeeb da Hulwa suka rabu cike da kewar juna,Adeeb ji yake kamar yayi kuka. Tunda fattu ta tafi Ghana,kullum sai su wuni suna waya da Adeeb,sosai yake nuna mata yadda yayi kewarta,ita kuwa tausayinsa duk ya gama kamata,ba abinda yake son ji da gani sama dashi.saidai tayi tararrashinsa,tun tana kunyar fada masa kalamai harta zo ta daina,take zagewa tana nuna masa soyayya. Ba irin gatan da fattu bata ganiba,agurin iyaye da danginta,kowa sonta yake,yana riritata,gyara kuwa tunda suka zo innarta ke fama,an tsuma fattu sosai,ta yadda da kanta wataran take jin tana bukatar Adeeb akusa da ita. Tayi kyau jikinta ya kara gogewa,kallo ɗaya zaka mata kasan tana cikin jin dadi da annashuwa,komai yaji ajikinta. Satinta biyu a ghana Adeeb ya kasa daurewa ya shirya kayansa yace ya tafi Ghana. Amagarkama kuwa,lamarin ammi ya gwabe sosai,dan kuwa zuwa yanzu bai zama lallai ka gane ta ba,wasu abubuwa take tamkar na mahaukata,tayi ta ihu kenan tana faɗin irin abubuwan da ta aikata,ƙafarta ɗaya ta lalace sakamakon ciwon da taji,banda wasu irin kuraje da suke fito mata masu tsananin karni da doyi.haka zatayi ta ihu tana yagunin jikinta.duk wanda yazo inda take,da gyar yake iya tserewa dan kuwa hauka take sosai,tana dukan mutane.hakan yasa aka kulle gurinta,saidai atura mata abinci ta kasan kofa. Waziri kuwa,an yanke masa hukumcin daurin shekaru arba'in agidan yari, yayi nadama sosai kullum cikin kuka yake da neman gafara. Rashad kuwa zuwa yanzu jiki alhamdullah,dan sosai yaji sauki walwalarsa ta dawo, Amma ma hankalinta ya kwanta sosai take kula da abie,abin sai godiyar Allah. Ranar da Adeeb ya sanar da zuwansa Ghana,ba ƙaramin farin ciki fattu tayi ba,murna sosai takeyi har saida innarta ta fahimta,shiri akayi mata na musamman,cikin shiga irin ta ya'yan sarakuna, tayi matukar kyau kamar kasace ta ka gudu,sai ƙamshi take zubawa,gashi tadanyi kina kwanin sha'awa. Wani kayataccen daki aka sauki Adeeb,ko ina yayi fes sai ƙamshi ke tashi,an jere masa kayan ciye- ciye,amma ko ruwa ya kasa sha,burinsa kawai yayi tozali da hulwarsa. Wani sihirtaccen kamshine ya bugi hancinsa,wanda ya sanya shi saurin ɗago kai,cikin hanzari ya mike tsaye tare da kafe fattu da lumsassun idanunsa,wadanda ke cike da tarin gajiya da bukatar fattun tare da kewarta. Murmushi take sakar masa cike da shaukin ganinsa.tana takawa kamar wata tarwada. Cikin wani irin salo da zaƙuwa Adeeb ya bude mata hannayensa,alamun ta taho gareshi,da sauri ta ƙaraso tare da fadawa jikinsa,shikuma ya mayar da hannunsa ya rungumeta tsammm. Muje zuwa masu karatu. Mrs babi ce💘💘 Share and comment fisabilillah. More comment More typing. [30/08 15:01] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 Free book Page 91/92 _____________Cikin wani irin salo wanda ke nuna tsantsar farin ciki da zaƙuwa,Adeeb ya bude hannayensa,alamun fattu ta taho gareshi. Da sauri fattu ta ƙaraso gareshi,cikin takunta mai jan hankali,tare da fadawa jikinsa tana murmushi. Maida hannunsa yayi ya kulle tare da rungume fattu tsamm,ajikinsa. Atare suka sauke ajiyar zuciya,wacce ke nuna tsantsar kewar juna da sukayi. Banda ajiyar zuciya ba abinda Adeeb ke saukewa,kamar wanda yayi wasan tsere. Ahankali cikin murya mai tattare da shauki yace "I miss You so much Hulwa"ya faɗa yana kare matseta akirjinsa,kamar zai maidata cikinsa. Kusan minti biyar suka dauka ahaka,kafin Adeeb yayi karfin halin ɗago da fattu daga jikinsa yana kallon kyakykyawar fuskarta.gani yake kamar ba fattunsa ba,kamar wanda aka sauya masa ita,tayi kyau matuka,ta kara gogewa kai kace acikin ƙanƙara tare rayuwa. Fattu ma kallonsa take cike da jin zazzafar kaunarsa na ratsa jini da tsokarta,dan gani tayi yayi mata kyau sosai,ya ɗanyi kiba kaɗan ya kara fari,ga sajen da ya kara ajiye wa yayi matuƙar ƙawata fuskarsa. Ahankali ta kai hannunta tare da shafa gefen fuskarsa,lumshe ido yayi yana mai jin sanyi cikin ransa.cike da son nunawa Adeeb yadda tayi kewarsa ta kai bakinta kan nashi,ta fara kissing dinsa,kawai sai jin bakin fattu yayi cikin nashi. Ai kamar mayen karfe haka Adeeb ya karbe lips din fattu ya fara sha kamar ya sami lollipop. Tun abun yana karami har yazama babba,dan sun kasa rabuwa da juna,ganin suna neman faduwa ne yasa su zubewa akan lafiyayyar kujerar dake kusa dasu.adeeb bai bar wannan dama ba ,saida ya kara angoncewa, sosai ya shiga ruɗu da gigita,ɗan jin fattu yayi kamar bai taba ma saninta matsayin ya mace ba,sosai ya nishadantu da ni'imarta,ya rikice mata sosai haka yayi ta sunbatu yana hawaye.albarka kuwa fattu ta shata ba adadi da kyaututtuka kala kala. Saida suka sami nutsuwa kafin Adeeb ya samu yaci abinci.anan dakin sukayi wanka tare,gaba ɗaya Adeeb ya kara kwarewa fattu,ko yaya tayi motsi hankalinsa na kanta,wani irin so yake mata marar misaltuwa.fattu duk da taji zafi amma haka ta daure bata nunawa Adeeb raki ba.nan suka shantake suna nunawa juna so da kauna,dama tuni Adeeb ya mika gaisuwa ga Sultan Habib da innar fattu. Dan haka salla ma acikin dakin nan yakeyinta. Fattu kuwa ranar ta yabawa aya zaƙinta,dan ta tabbatar da cewar Adeeb yayi kewarta,kuma shidin jarumi ne na gaske. Washe gari suka tashi daga Ghana zuwa Nigeria,da tareeƙ akayi tafiyar,dan dama tare suka zo da Adeeb,shiya sauka a masauki na daban. Kai tsaye a Jos suka sauka,kafin suka nufi kauyen su fattu cikin dalla dallan motocinsu. fattu da Adeeb cikin mota daya suke,yana rungume da ita ajikinsa,motar su ce agaba,ko kaɗan fattu bata manta hanyar kauyen nasu ba,dan haka tana lura da inda suke nufa. Sai motar Sultan Habib shida innar fattu dasu zayyad. Kauyen yana nan inda fattu ta sanshi, ba abinda ya sauya.gidansu ta fara hangowa,cike da doki take nunawa Adeeb gidan"Hamma ga gidanmu can,yanzu zanga baffana,Hamma bazan iya kwatanta irin farin cikin da nake ciki ba"fattu ta faɗa tana rike hannun Adeeb cike da murna idanunta ya cika da kwalla. Murmushi yayi,dan shima saiya tsinci kansa cikin farin ciki, ganin yadda Hulwarsa ke farin ciki. "Nima ina farin ciki Hulwa zataga baffanta,saidai anya kuwa zai gane ki?Adeeb ya faɗa yana kallonta da murmushi. Cikin doki da dariya fattu tace "wllh zai ganeni,ko me nazama na tabbata baffana zai ganeni kuma zaka gani"ta fada daidai lokacin da sukayi facking akofar gidansu fattu. Da hanzari fattu ta buɗe kofar motar ta fito,bata ko tsaya sauraron Adeeb ba,burinta kawai tayi tozali da baffa.da sallama ta shiga cikin gidan tana rarraba ido dan ganin ta inda zataga baffanta. Ba kowa cikin tsakar gidan,gaba ɗaya gidan yayi datti,ko ina kazantace cikinsa.jin sallama yasa gwogwgo hansai fitowa daga cikin dakinta,tana ta soshe soshen kwarkwata. "Waye yau agidan nan nawa?rabon da naji wani yazo gidan nan,harna manta,kodai Hau......maganar gwogwgo hansai ta makale sakamakon ganin wata balarabiyar yarinya da tayi tsaye fuskarta ɗauke da murmushi. Cikin rawar jiki gwogwgo hansai ta fara fadin"maraba lalle baiwar Allah,daga ina?wa kike nema kodai gidan mai gari kike nema?"gwogwgo hansai ta fada cikin rawar jiki tana kallon fattu. Dariya fattu tayi tana kallon gwogwgo Hansai,duk ta rame tayi baki sosai gashi ta tsufa,kallo ɗaya zakayi mata kasan tana cikin wahalar rayuwa. "Gwogwgo,baki ganeni ba ?nice fa,nice fattun baffa"fattu ta faɗa tana kama hannun gwogwgo Hansai ba tare da gyama ba. Galala gwogwgo tayi tana kallon fattu,cike da ƙaryata abinda fattun ta fada,saidai kuma wa yasan fattun awani guri?bare yazo yayi mata wasa.cikin rawar murya tace "fa....t.t.tu,kece haka ?kece kika zama kamar balarabi?ina kika je kika zama mai kudi haka?ta fada tana shashshafa fattu. Dariya fattu tayi kafin tace" nice gwogwgo tare muke da iyayena fa da hammana,suna waje bari nace su shigo,wai ina baffana ne tunda na shigo nake nemansa"fattu ta faɗa cike da doki tana nufar waje. Lokacin da ta fita atsaye ta tarar da itayenta da Adeeb,mutanen garin sun zagayesu suna kallonsu da shafa motar da suka fito daga ciki. Bata damu da mutanen gurinba tacewa su Adeeb su shigo. Murna take sosai kamar wacce akayiwa bushara da gidan aljanna. Gwogwgo Hansai jiki na rawa ta shimfida musu wata rubabbiyar tabarmar kaba.ko kaɗan basu nuna mata gyamaba suka zauna. Bayan gaishe gaishene, gwogwgo tayi ta kuka tana bawa fattu hakuri,itadai fattu burinta daya taji ina baffanta yake. Nan gwogwgo Hansai ta sanar da ita duk abinda ya faru da baffa,ranar da suka bar garin. Kuka sosai fattu ta sanya,tana jin wani irin kunci cikin zuciyarta,ina zata ga baffa?mutumin daya tallafi rayuwarta ,ya bata kulawa,wayyo Allah.haka fattu tayi ta kuka,ajikin Adeeb yana rarrashinta. Gwogwgo Hansai cikin nadama take faɗin"bayan tafiyar malam,gaba ɗaya lamari ya lalace garin nan,kowa abinda yake so shi yakeyi,haka inaji ina gani,yarana mata sukayi cikin shege,yanzu haka bansan duniyar da suka shiga ba,shima namijin tuni ya zama rikakken barawo,yayiwa yar mutane fyade shine ya gudu,ya bar rugar nan.mai gari yana nan ya zama gurgu,jauro kuwa abarsa ta lalace har yanzu bata da amfani,haka haroji yana na da fuska kamar ta dodo,saidai yaje Bara cikin gari,dan Allah fattu ki yafe mana ,nasan hakkinkine ke bibiyarmu"gwogwgo Hansai ta fada cikin kuka. Haushin ta sosai Adeeb yakeji,dan yasan kadan daga cikin mugayen halayenta. Tashi sukayi domin barin rugar,dan bawani amfanin zamansu,tunda wanda suka zo gurinsa baya nan. Kudi mai yawa sultan habib ya bawa gwogwgo hansai,sai murna take tana godiya,haka ya tabawa mutanen kauyen ma kafin suka bar garin. Kuka sosai fattu keyi ajikin Adeeb,ta shiga damuwa mai tarin yawa,haka yayi ta rarrashinta,har suka iso cikin garin jos. Wata babbar motace tayi faci akan tsakiyar kwalta,hakan ya haddasa go slow agurin,suna tsaye cikin mota,masu bara sai zuwa suke suna Bara. Wani dattijone cikin shiga ta almajirai,kallo ɗaya zakayi masa kasan yana shan wahala yazo jikin motar su fattu yana Bara,kasancewar gilas din motar irin mai duhun nan ne,yasa na waje baya ganin na ciki. Fattu ce tayi firgigit tatashi daga jikin Adeeb tana kallon tsohon dake barar. Wani dan ihu ta sanya tana mai ƙoƙarin buɗe kofar motar.kira take "Hamma baffana,baffana"tana faɗa cikin rawar jiki tana kokarin buɗe motar. Da sauri shima Adeeb ya kai kallonsa inda fattun ke nuna masa. Tabbas baffa ne kuwa.gana ɗaya fattu ta rikice tana kici kici buɗe kofar Amma tsabar farin ciki tama kasa,budewar sai kira take"baffana,baffana" Hannunta Adeeb ya riko yace "ki nutsu hulwa,karkije kiki ciwo kinji bari muje gurin baffan"ya faɗa yana bude kofar motar. Da sauri fattu ta fito daga cikin motar ta nufi gurin mutumin da yayi dan gaba dan zuwa wajen wata motar ya sami sadaka. Da sauri ta kamo hannunsa tana faɗin "baffana kaine,haka ?"cikin azama baffa ya juyo sakamakon jin Muryar da akullum saiyayi kukan rashin ta,kuma duk kuɗin da yake samu na bara tarawa yake,dan yayi ta zaga garuruwa yana neman fattu,yasan watarana zasu hadu. Jifa yayi da dan buhun dake hannunsa,wanda yake tara kudin barartasa ciki. "Fattu,kece"baffa ya faɗa cike da shauki. Kuka fattu keyi tana kallon baffa,kafin ta rungumeshi ajikinta tana kuka.shima baffa kuka yake cike da godewa Allah,yau gashi ga fattunsa,shikenan burinsa ya cika. Sultan habib,da innar fatyu ma,fitowa sukayi,dan kobasu tambaya ba,sunsan wanna shine baffan fattunsu. Adeeb kansa saida yaji kwalla ta cika masa ido,dan tausayin tsohon da yadda ya koma. Horn din da motoci ke musu ne ya dawo dasu cikin hayyacinsu,dan tuni an janye motar data haddasa go slow ɗin,dan haka cikin hanzari suka shige mota dan ba mutane hanya. Motar su fattu baffa ya shiga,su Sultan ma suka koma cikin tasu ,sannan suka bar gurin. Kai tsaye gidan da suka sauka suka koma,dan yau suke don komawa Ghana, Fattu sai murna take daga ga baffanta. Wanka kawai suka bari baffa yayi,aka bashi wasu kayan ya sanya,kafin suka daga sai Ghana.... Masu karatu bari muyi musu rakiya zuwa ghanar muma. Ina kuke Masoya anty mammy? Albishirinku,ina mai farin cikin sanar daku,sabon littafina mai suna RAINON DAWA,yana nan akan hanya,da zarar mun kammala MACIJINE,hmmmm Daga jin sunan kinsan ba magana. Karku bari abaku labari. Ga mai bukata ,zai iya biyan kudinsa tun yanzu,domin nan da kwana uku zaku fara samun wannan kayataccen labarin na RAINON DAWA. akan fashi mai sauki, Normal group 300 Special group 500 Sannan akwai manyan mata dake son atura musu private to kuma ga naku farashi,1000 Dan haka saina jiku, Acc. No. Saratu kabir A.u.b 2215749011 Saiku nuna shadar biya ta wannan no. 08148360851 Saina jiku,masoya. Show ne your love akan novel ɗi Nan, 😍😍😍🥰🥰🥰🥰 Mrs babi ce💘💘 [30/08 15:01] %Faiza%: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄 MACIJI NE🪱🪱🪱 Na mammy kabeer (Anty mammy) Elegant online writers📚📚 https://facebook.com/groups/943534712916776/ Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din👆🏽 Free book Page 93/94 _______________Ko a cikin jirgi fattu na kusa da baffanta,wanda yayi tsuru cike da tsoron jirgin,dan kuwa wannan shine karon farko daya hau jirgi.amma haka fattu ke kwantar masa da hankali har suka ƙarasa Ghana. Part guda aka warewa baffa wanda ke dauke da duk wani kayan more rayuwa.baffa ya cika da farin cikin ganin irin rayuwar jin dadin da fattunsa keyi.abinci kala kala aka ajiye masa,har yama rasa wanda zaici.haka fattu keta zuba masa abincin tana tura masa. Saida ya huta sosai nutsuwarta ta dawo jikinsa, sannan aka taru apart din da aka saukeshi, har Sultan Habib.godiya suka farayiwa baffa,bisa irin taimakon da yayiwa rayuwar yarsu,sannan suka ce suna bukatar yayi zamansa anan gurinsu,tunda bashi da kowa acan Nigeria. Kuka kawai baffa keyi na gani yadda bayin Allah nan ke karramashi, suna son ya kasance tare dasu,amma wadanda ya taso cikinsu,haka suka koreshi korar kare bayan sun karbe masa dukiya. Fattu ce ta dan turo baki tana kallon innarta da mahaifinta,kafin tace "Ni gaskiya ban yarda baffana ya zauna anan ba,tare zamu tafi dashi can gida,bana son yayi nesa dani,kuma shima yafi son zama kusa da fattunsa ko baffa"fattu ta faɗa cikin salon shagwabarta. Murmushi baffa yayi,yace kwarai kuwa fattun baffa,duk inda kike to Nima Ina can koda kuwa cikin dokar dajine"baffa ya faɗa cikin murmushi. Dariya sukayi suma,kafin mahaifin fattu yace "wato dai zara kin kwace mana baffanki ko?"ya faɗa da murmushi akan fuskarsa. Dariya fattu tayi kafin tace "Allah ba haka bane daddy nayi kewar baffana,kuma nima inason in kula dashi,kamar yadda ya kula da rayuwata abaya" Jinjina kai sukayi gaba ɗaya,suna ayyana irin kaunar dake tsakanin fattu da baffanta. Kafin su bar kasar Ghana saida mahaifin fattu ya mallaka wa baffa kanfaninsa na ƙera takalma da jakunkuna,ya maida sunan sa akan takardun kamfanin,sannan ya bashi gida,wanda idan yazo zai rinka sauka aciki sannan ya damkawa fattu takardun gida dana kamfanin,harda mukullin sabuwar mota yar yayi. Kuka sosai baffa yayi yana godiya,fattu ma tayi matukar murna sosai.adeeb kam godiya yayiwa Sultan habeeb,haka innar fattuma ba'a barta abaya ba,dinkuna ta sanya aka yiwa baffa,na gani na faɗa, masu kyau da tsada.sosai baffa ke yaba karamcin iyayen fattu,ba abinda zaice saidai Allah ya saka musu da aljanna. Washe gari kuwa jirginsu ya daga zuwa Misra,fattu harda kukan rabuwa da yan uwanta,haka innarta ta cika ta da kayan gyara kala kala. Wani ƙayataccen bangare su fattu suka sauka,wanda bayan tafiyarta Ghana ,Adeeb sanya aka kera musu.tsyawa fadar irin tsaruwar da bangaren yayi abune mai matukar wahala.kallo daya zakayiwa gurin kasan an kashe kudade makudai. Baffama bangare guda aka ware masa inda zai zauna.haka yasha kyaututtukan gurin iyalan Adeeb,sannan shima Adeeb ya ba baffa kanfaninsa na motoci,baffa neman zaucewa yayi da irin wannan kyautukan da ake ta bashi. Sosai ake girmama baffa cikin fadar,dan kowa yasan shidin waye. Cikin lokaci kalilan baffa ya wanke yayi fes dashi,masha Allah kyakykyawan bafillatani,yayi kiba ya koma Alhaji sosai.ba jimawa suka shirya shida Adeeb da fattu dasu nanny sukaje suka sauke farali. Sun dawo da kwana uku aka shirya gagarumin taron nadin Adeeb matsayin sarki.sannan ranar za'a gudanar da bikinsu shida fattu. Anyi taro na ban mamaki wanda saida ya girgiza duniya,taron daya hada sarakunan hasashe daban daban,daga turawa,larabawa zuwa hausawa,ba kalar mutanen da babu agurin. Taro yayi taro,an nada Adeeb matsayin sarkin misra,SULTAN ADEEB MUHAMMAD ASHRAF. haka aka kammala taro ya tashi lafiya,kuma ranar Adeeb ya mallaka fattu dankareriyar mota mai shegen tsada da kyau,sannan ya mallaka mata kamfaninsa wanda ake hada mayukan shafawa na mata da kayan kwalliya. Murna dai agurin fattu ba'a cewa komai. Sati biyu da nada Adeeb matsayin Sarki,fattu ta kama laulayi, wayyo kuzo kuga murna gurin bayin Allah nan,haka nanny ta zage tana kula da fattu,ita da amma,suna bata gata da kulawa sosai,haka uban gayya,dan har kuka yayi lokacin da labarin cikin fattu ya sameshi.kuma yayi mata alƙawarin idan ta haihu ta zabi inda take son zuwa yin karatu. Cikin fattu nada wata biyar aka yi auren tareeƙ da wata yar uwarsa,rana daya aka daura auren dana Rashad,anyi biki na kece raini,su fattu sune akan komai na biki, zakuyi mamaki yadda fattu ta zama babbar mace,tayi mugun kyau har ta gaji,suna nunawa juna soyayya mai tsafta ita da Adeeb,yayin da suke rainon cikinsu cike da so da kauna.saidai fattu tana da girman ciki,dan yanzu haka inka ganta zaki tunanin cikin yakai wajen watanni bakwai, dan girmansa. Komai yana tafiya daidai arayuwarsu fattu,basu da wata matsala yanzu,domin suna cikin aminci da kulawar yan uwa,sarauniya suhaimat da Sultan habeeb,sunyi matukar murna da samun cikin fattu,addu'oi kuwa,ba irin wanda fattu bata samu,domin takanas ake biyawamutane makka,dan suke suyi mata addu'a. Lokacin da cikin fattu ya cika wata tara,ko tashi bata iyayi da kanta,saidai idan Adeeb ya tasheta idan tana zaune ko kwance,amma kasancewarta mai hakuri da kawaici,haka take daurewa tana nuna bata jin wahalar ciki,shikuwa Adeeb tausaya mata yake sosai. Wata rana da safe suna barci nakuda ta kama fattu,aikuwa,nan da nan likitoci kwarraru,wadanda ke mata awo suka rufu akanta,cikin hikimar ubangiji,fattu ta haifi yaranta takwaye, mace dana miji masu matuƙar kama da Adeeb, kyakykyawa na ban mamaki. Irin murnar da ahalin nan suka nuna abin ba'a cewa komai,ta ko ina zuwa ake ganin jarirai,ranar suna aka sanya musu sunan baffa dana Nazli,Abubakar,amma ana kiransu da Ameer da ameera. Fattu ta sami alkairi sosai haihuwar yaran nan.dan motoci ma sun sami sama da guda sha biyar,banda gidaje da tsabar kudi.sai muce Allah ya raya twince. Bayan suna da sati biyu aka daura auren baffa da nanny,bisa ga amincewarsu,bayan fattu tayi shawara dasu,ba nuna ja suka amince,dan dama sun kamu da son juna. Ammi kullum abu sai kara lalacewa yake,hauka take tun ƙarfi,gaba ɗaya ta gama kwarzane jikinta,tananan kamar wata horuwa, tayi ta ihu tana yakushun jikinta.(ai dama ammi hausawa sunce idan zaka gina ramin mugunta ka gina daidai da kai,hakkin rayukan da kika kashema kadai sun isheki) Waziri ma yana gidan yari,saidai shikam yayi ladama,ya koma ga Allah,kullum yana istugfari. Yaran fattu sun taso cikin kulawa da soyayya,idan kun gansu gurin fattu,to nono kawai zata basu,dan tuni ta fara karatunta ,tace anan gida zatayi karatu,bazata je ko ina ta bar mijinta ba. Abin sai son barka,rayuwa tayi musu daɗi,suna zaune cikin kwanciyar hankali,fattu ta buɗe gidajen marayu ajahohin Nigeria sosai,ta taimakawa yan kauyen su,tayi musu makaranta, ga ruwa ya wadata,ta tallafawa mabukata, gaba ɗaya sunyi nadama abinda suka yiwa fattu da baffanta,dan lokacin da baffa yaje basu ganeshi ba,haka gwogwgo hansai tayi ta kuwa wai ya maidata dakinta,dariya kawai yayi tare da bata makudan kudade kafin ya bar kasar. Amare da angwanye ma suna zaune cikin aminck da soyayya,yayinda ko waccensu ke dauke da yaron ciki,saidai muce Allah ya raba lafiya. Fattu ce zaune akan kujera tana bawa ameer nono,yayinda Adeeb ke gefenta riƙe da ameera,kallonta yeke cike da ƙauna da sha'awa,yadda take shayar da yaron cikin nutsuwa. Ajiyar zuciya yayi tare da faɗin "Alhamdullah ,Allah na gode maka kacikani da ni'imarka ta ko ina ,ka bani mace mai hankali da nutsuwa,sannan ka hadamin kan ahalina,ka bani yara kyakykyawa har biyu a lokaci daya,Allah Nagode maka"Adeeb ya faɗa cike da kushu'i yana mai jin dadi cikin ransa. Murmushi fattu tayi tare da kamo hannunsa tayi kissing, sannan ta Dora kanta akan kafadunsa, tace "Ina sonka mijina kaine farin cikina,kuma rayuwata,Allah ya raya mana yaranmu bisa hanya madaidaiciya" "Ameen Hulwa ana ahubbikteeer Hulwa anti sururi"ya faɗa yana mai kara rungumeta ita da yaran ajikinsa. Tammat bi hamdillah.anan na kawo karshen wanna littafi Mai suna MACIJI NE. Jinjina gareka mijina,na gode da gudunmawarka gareni,Allah ya bamu zaman lafiya,ya raya mana zuri'a. Much love. Godiya ta musamman gareki,maman nafi,na gode sosai da gudun mawarki akan wannan littafi. Gaisuwa gareku macijine fans inq kaunarku. Jinjina ga elegant online writers,Allah ya hade kanmu. Ina godiya gareku yan uwana,da addu'ar ku gareni 🫠🫠🫠 Allah ya sa mu amfana da darasin dake cikinsa,muyi watsi da sharrin dake cikinsa. Allah ka yafe mana kuraruranmu,kasanya imaninmu ya nunku fiye da nada. Godiya agareku masoyansa ,da kukayi ta bibiyar wannan littafi,tun daga farko har karshe,Allah ya hadamu gidan aljanna. Sai mun haɗe daku cikin sabon littafina RAINON DAWA. Ga mai bukata,zai fita kudinsa kamar haka. Normal group 300₦ Special group 500₦ Manyan mata masu bukata ta private,kuma ga naku1000₦ Zaku biya ta wannan acc. Din. Saratu Kabir U.b.a 2215749011. Evidence of payment 08148360851 Saina jiku masoya. Show me You love, Kuyi payment na wannan littafin.💘💘💘 Kada kusake baku labari. Saina jikiku. Takuce har kullum anty mammy. Mrs babi💘💘