馃摑馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌 *亘爻賲 丕 賱賱賴 丕賱乇 丨賲賳 丕賱乇 丨賷賲貙* 06/09/2017.10:24 PM *A TRUE LIFE STORY* 馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 1鈨� *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌馃崌 *Gargad'i! Gargad'i! Gargad'i! dan Allah kar a juya mi wannan labarin tako wacce siga har sai an nemi izinina dan Allah ko harafin (A) kar a canza min bana so* *Ina mik'a sak'on Barka da sallah na ga d'aukacin al'ummar musulmai baki d'aya Allahu rabbi ya amshi ibad'un da muka aikata Allah ya maimaita mana shekaru masu yawa da al'bakar wad'anda ke k'asa mai tsarki Allah ya dawo daku cikin lafiya* *Alhamdulillah lillahi ala kulli halin na godewa Allah da ya bani rai da lafiya da nitsuba da konciyar hankali har na samu damar fara rubuta wannan littafi cikin k'oshin lafiya ya Allah ka bani iko da damar gama shi lafiya kamar yadda na fara lafiya Ameeen ya rabbil izzati* Suna iso kan layin uguwar tasu Usman ya dafa kafad'un abokin shi Nura dake jan motar tasu cikin dan fidda ido yace. "Kai Nuru tsaya a nan ba sai ka shiga cikin gidaba zan sauk'a a nan!." Kai Nuru ya juyo tare da k'are mishi kallon sai kuma yayi murmushi ganin yadda Usman sarkin surutu ya wani zaro ido cikin murmushin yace. "Kai Usman ni wallahi Hamma Umar mamaki yake bani ji yadda yake wani tsareka a gida kamar mace! ji yadda kake wani zaro ido dan kasan yanzu yana harabar gidan yana duba marasa lafiyan dake zuwa gunshi." Shi dai Usman balle marfin motar yayi ya fita yana hararan Nuru tare da cewa. "Ban za kawai lailamajanun duk ka zama majanuni akan mace sai dare yayi kazo kace in raka ka kakuwa sani sarai Hamma Farouq zai nemeni dan zai bani magani na." Shi dai Nuru dariya yayi tare da jan motarsa ya tafi. Shi kuwa Usman cikin sand'a da d'an d'aga k'afa da lek'e-lek'e ya shiga cikin gidan, gaba d'aya hankalin shi na can gefen wasu yan bukkoki da akayi da ginin zamani sai samansu kuwa da akayiwa rufi da ciyawa suka fita kamar bukkokin rigar Fulani sai fulawowi masu kyau da suka zagaye harabar gidan da haske tako ina cikin bukkokin da sukafi kama dana shak'atawa wani farin matashi ne mai cikar haiba da tsurawa wanda yafi kama da laraba Dr Umar Faruoq kenan shine yake zaune kan kujerun dake zagaye a bukkokin sai mutane kusan 8 dake zaune daga dukkan alamu sunzo ya duba lafiyar sune gaba d'aya hankalin shi na kansu. Shiko Usman ganin haka yasa cikin sauri da d'an d'aga k'afa ya zille yayi cikin gidan, kai tsaye Parlour Nenne ya nufa cikin yana yinsa na fara'a yayi sallama, tare da shiga cikin Parlour yana ta haki da d'an zare ido. Nenne ce ta fito daga cikin bedroom cikin sakin fuska tace. "Usman daga ina haka kaketa zare ido?." Dariya ya d'an yi tare da zamewa ya zauna gefen Ummul dake ta binshi da ido sai ya Adam da ya Sadik dake zaune a gafe duk sun zubawa Usman ido cikin murmushi Ummul tace. "Mugun ne ya koroka ko ya Usman?." Kai ya d'an juya cikin sauk'e ajiyan zuciya yace. "Tab Nenne Hamma Umar yazo ya nemeni ko.?" Cikin sauri da salon tsokana ya Adam yace. "Ehh yazo k'afa 3 yana neman ka." Ido ya kuma d'an zarowa yace. "Toh ni fa ba wani wuri naje ba! kawai na d'an raka abokina Nuru zance gun budurwar sane, kuma yanzu nasan Hamma Umar zaice yawo natafi ban sha maganina ba." Dariya Nenne tayi cikin kula tace. "A a baizo bafa Usman." Shima dariya yayi cikin sauk'e ajiyan zuciya yace. "Ummul me kika dafa mana me? Dan wallahi yunwa nikeji." Ya Sadik ne yace. "A a saidai ta tashi ta dafa maka ko indomi ne dan miyar ganye tayi kai kuma kasan an hanaka ci." Fuska ya d'an tsuke cikin badda zancen yace. "Ummul kawomin zanci na yau kawai bazai min komai ba." Nenne ce ta kalleshi cikin kula tace. "A a fa Usman ka kiyaye dokokin Doctors ko dan samun lafiyar ka." Baki ya kuma turawa yace. "Wallani ni nagaji da wannan dokokin ace duk wani abu green bazan ciba, dan Allah Nenne yau kawai kinji ko?." Ita kam Nenne gaba d'aya take jin tausan Usman a ranta sabida ciwon dake tare dashi gashi yaro matashi . Shi kuwa Usman cikin dariya ya kalli Ya Adam yace. "Ya Adam kasan me Nuru yakeyi in munje gun babynshi?." Murmushi ya Adam yayi tare da cewa. "Inako zan sani sai ka fad'a min dai." Ummul ce tayi carab tace. "Ya Usman me yake yi?." Hannu yasa ya kamo na Ummul d'in cikin yanayin shi na abin dariya yace. "Jeki kawo min abinci zan baku labari." "Toh" tace tare da haura saman d'an steps d'in da zai sadata da kitchen d'in sauri-sauri tasa mishi abincin a pilet sannan ta dawo parlour stol tajawo gaban shi ta ajiye mishi abincin cikin son jin zancen tace. "Toh ga abin cin bamu labarin." Murmushi yayi cikin raha ya mik'e tsaye tare da cewa. "Nenne kina jiko kullum Nuru zaizo yace na rakashi zance amman sam in munje ba abinda yake sai shirme." Ido ya Adam ya tsura mai cikin gimtse dariyar shi yace. "Kamar yayafa?." Dariya ya kuma tare da cewa. "kuna jiko Nenne kullum in munje muna zuwa k'ofar gidan su budurwar tashi sai Nuru ya kalle ni cikin in inarsan nan yace min k.. k.. kai Bosho k.. katsaya a cikin motar nan karka fito, ni kuma sai nayi dariya nace toh , in an aika ta fito sai yace ta zauna kan motar , ita kuma sai ta wani d'ale saman motar ta zauna tana kallon shi." Ajiyan zuciya tayi tare da cewa. "Hmmmm Nenne kin san me Ruk'ayyan take ce masa?." Su ya Adam kam da ya Sadik tuni sun fara dariya itama Ummul sai dariya take . Ita ma Nenne murmushi take yi tare da girgiza kai alamar a,a. Shi kuwa Usman cikin nuna musu abin a zahiri ya jawo hannun Ummul ya ajiyeta kan hannun kujera shi kuma ya matso gaban ta gab da ita ya d'an sa k'afarsa d'aya a gaba d'aya kuma ya maidata baya sannan ya rink'a d'an sunkuyawa yana d'an d'agowa kamar maiyin wazifa sai kuma ya kalli ya Sadik yace. "Ya Sadik Kunga haka ko?, wallahi haka Nuru yake tsayuwa a gaban ta kamar mai jin bacci yayi ta layi ita kuma sai tayi ta wani mishi murmushi kamar sokuwa." Sai ya kuma kalli Nenne yace. "Nenne kin san me take ce mata kuwa.?" Cikin dariya tace. "Me yake ce mata?." Dariya yayi tare da koikoyar muryar Ruk'ayya budurwar Nurun yace. "sai tace ,Nuru ina sonka." Sai kuma yayi dariya yace. "Nenne ba tace masa Nuru ina sonka ba?." Cikin dariya Ummul tace. "Ehh". Shima dariya ya kumayi tare da cewa. " shi kuma soko sai ya kalleta murya can k'asa yace. "Allah ya d'aiyiba." Sai kuma suka rink'a dariya cikin dariya Usman yace. "Kijifa Nenne wai Allah d'aiyiba sai kace wad'anda akayiwa haihuwa Allah ko Nuru yana bani dariya shi yasa nake son rakashi zance, kumafa kullum haka suke hirar tasu ,tace Nuru ina sonka shiko gogan yace, Allah d'aiyiba." Gaba d'aya dariya suke shiko Usman yaja pilet d'in abincin ya fara ci kamar bashi ya basu dariyar ba. Autan gidan ne Aliyu ya kalleshi cikin sanyi yace. "Ya Usman ba doctor ya hanaka cin duk wani abu green ba kuma kake cin miyar ganye kasan fa Hamma Umar zaiyi fad'a." Harara ya cillawa Aliyu tare da cewa. "Toh sai dai in kaine zaka gaya mishi naci miyar dan nasan ka ka iya gulma." Haka yaci gaba da cin abincin suna ta dariya da hira da raha. Yana cikin cin abincin ya d'ago kanshi da sauri jin k'amshin turaren Hamma Umar na ratso hancin sa, da sauri ya ture pilet d'in kasan kujara sai kuma yayi zuru-zuru da ido yana sauraron ta ina Dr Umar d'in zai shigo. Shi kuwa Doctor Umar dama sarai yasan Usman baya cikin gidan kuma ya ganshi lokacin da ya shigo cikin gidan haka yasa yana gama sallaman marasa lafiyan kai tsaye part d'in su ya nufa wonka yake sonyi amman bazai iya zama har yayi wonka baije ya bawa Usman maganin shi ba hakan yasa ya d'auko magungunan tare da goran FARO a hannushi ya nufi cikin gidan. Sallama yayi tare da tsayuwa a bak'in k'ofar yana jin suna ta hira da dariya bai shiga ba har sai da ya kuma sallama Nenne ta amsa mishi tare da bashi izinin shiga. Shi kuwa Usman tuni ya tonk'oshi kai yayi kalan tausayi . Ummul kuwa mik'ewa tayi ta koma gefen Nenne dan jin muryar Hamma Umar d'in dan ta sanshi sarai yanzu zai samo laifin da zai turama . Ya Adam da Ya Sadik kuwa Usman suka tsurawa ido. Shi kuwa Dr Umar kan shi a sunkuye ya shiga cikin parlon cikin girmamawa ya gaida Nenne amsawa tayi fuska a sake tare da cewa. "Umar bak'in naka duk sun tafi kenan?." Murya can k'asa yace. "Ehh" dan shi baida rakad'i irin na Usman kuma baya da yawan surutu bashi kuma da shiga sabgar wani baya kuma wasa da yara kasan cewarshi shine babba a family nasu baki d'aya gashi da iya horon marasa jin magana. Usman ya kafe da ido cikin tsuke fuska da yanayin tuhuma. Shi kuwa Usman a hankali ya tashi ya matso gaban yayan nashi cikin ladabi da tsantsar k'aunar juna yace. "Afwan Hamma Umar bazan sake ba." Ido Hamma Umar ya kawar sannan yasa hannushi ya rok'k'oshi kan Usman tare da kamo kunnen shi ya d'an matse cikin yanayin hukun tawa. Hannu Usman ya rink'a d'an yarfawa yana d'an k'ara tare da cewa. "Hamma na natuba kayi hakuri bazan kuma zuwa yawo ba." Sake mishi kunnen yayi sannan ya ajiyeshi kan kujera yana kallon fuskar sa, Magungunan ya b'abb'allo sannan ya mik'a mishi, hannu Usman yasa ya karb'a tare da afasu a bak'in sa yana mai yamutsa fuska, shi kuwa Dr Umar goran ruwan FARON ya b'alle cikin kula yasawa Usman bak'in goran a bak'in shi, shiko Usman ido ya rumtse sannan ya had'iye magungunan nashi. Murya can k'asa Umar yace. "Kaci abinci?." cikin sauri Usman yace. "Eh Hamma naci." Kai ya gyad'a sannan ya tattara magungunan tare da rufe goran ruwan ya juya ya kalli Nenne da ta zuba musu ido cikin tausayin su da mamakin irin kauna da kulawan da Umar yake bawa k'aninshi Usman. A hankali Doctor Umar yace. "Nenne sai da safe." cikin kula Nenne tace "Allah ya bamu al'heri Faruoq, Allah ya biya ka hidiman da kakeyi da d'an uwanka, Allah ya bashi lafiya." "Amin ya rabbil izzati." Yace tare da ficewa . Kai tsaye Bedroom d'in su ya wuce wonka yayi tsab sai k'amshi yake zubawa yana fitowa yasa wonddon shi 3 qtr sai rigarshi Mara hannu turare ya d'an fesa sannan ya jawo woyarshi da laptop d'in shi, Usman ya kira, Shi kuwa Usman tuni ya biyo bayan Hamman nashi ganin ya shi ga wonka ne ya dawo parlour ya zauna yana kallo, ganin kiran Hamma Umar d'in nashi yasa ya mik'e da sauri ya nufi cikin bedroom d'in, yana shiga gefen shi ya zauna cikin son juna suka kalli juna, a hankali Dr Umar Faruoq yace. "Na had'ama ruwan zafi kaje kayi wonka." "Toh" yace tare da mik'ewa ya dawo gaban Hamma Umar d'in ya tsuguna yana mai kallon shi da yana yin shi yake jira. Shi kuwa Dr Umar laptop d'in nashi ya d'an ture gefe sannan yasa hannu ya b'abb'ale boturan jikin rigar Usman d'in, yana gama bud'e mishi boturan Usman d'in ya mik'e ya cire rigarsa, sai kuma ya matso gaban Hamma Umar d'in ya tsaya , kai Hamma Umar ya girgiza tare da b'allewa Usman d'in beld'in dake k'ugunshi sannan ya d'an sunkuyo ya fara kuncewa Usman d'in igiyoyin takalman shi. Shi kuwa Usman sai kallon hannun d'an uwan nashi yake yi. Yana gama kunce mishi ya kalleshi a hankali fuska a d'an tsuke yace. "Wai kai Usman yaushe zaka koyi kula da kanka ne? , ace kana namiji baka iya d'aure igiyan takalmin ka da kuncewa ba bel d'in jikin kama baka iya. mannashi ba hatta botur bazaka iya sawa da cirewa ba komai sai nayi maka randa bana kusa da kai kuma toh ya za kayi?." Dariya yayi tare da shigewa toilet yana cewa. "Hamma Umar ai ko Aure kayi tare zamu tare a gidan bazan bari kayi nesa da niba." Shi dai Hamma Umar kai kawai ya jinjina tare da bin d'an uwanshi da kallo. Bayan ya fito wonkan ne, Umar ya had'a mishi tea sannan ya bashi ya sha, yana gamawa ya konta gefen Hamma Umar d'in nashi dake ta lallatsa laptop d'in shi. A haka har zuwa d'an wani lokacin sanna Hamma Umar ya rufe laptop d'in tare da jawo blanket ya rufe Usman d'in cikin kula yace. "B'iyaye na Usman kayi Addu'a kayi bacci kasan gobe ma akwai zuwa office ko?." Fuska ya d'an tab'e tare da d'ago hannushi zai fara Addu'ar yace. "aikin bankin ko aikin jaraba ni wallahi na gaji da aikin ma fa Hamma." Ido ya d'an tsura mishi tare da tsuke fuska yace. "Bacci fa nace muyi ba surutu ba , dan na lura kai kafi son zaman banza." Addu'a sukayi sannan suka konta baccin su. 2:00 Am Doctor Umar ya tashi yayi ta nafilfili tare da karatu k'ura'ani yana mai nemawa d'an uwanshi lafiya a gun mai bada lafiyar. Haka yayi ta karatu sai da aka kira assalatu sannan ya tashi Usman suka tafi masallaci.. Bayan sun dawo masalla cin ne Doctor Umar ya d'an koma bacci bayan ya fitarwa Usman kayan aikin shi tare da had'a mishi ruwan wonka, yana konciya lokacin d'aya bacci ya saceshi , shi kuwa Usman bai tasheshi ba dan sanin yau sai azahar zai tafi hospital d'in su. wonka yaje yayi sannan yazo ya kimtsa ya saka kayan shi, shiru yayi tare da kallon Hamma nashi sai kuma ya matso gaban Dr Umar Faruoq d'in cikin kallon fuskarsa yasa yatsunsa biyu ya matse hanc......... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBATACCEN AL'AMARI* Page 2⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ya d'an matse saman hancin shi kad'an tare da tsura mashi ido, cikin bacci Hamma Umar Faruoq ya d'an bud'e ido jin an rik'e mishi hanci yasan ba maiyi mishi haka sai B'iyayen shi, idon ya tsurawa Usman yana kallon fuskarsa da hannushi dake rik'e da net d'inshi, a hankali ya mirgino bakin gadon yayi rufda ciki tare da zuro hannayen shi k'asa, shi kuwa Usman k'afarshi ya turo kusa da hannayen Hamma Umar d'in. A hankali Dr Umar Faruoq yasa hannu ya d'aurewa Usman igiyoyin takal man nashi sannan ya d'an d'ago hannushi ya manna mishi bel d'in shi, shi kuwa Usman duk abinda Hamman nashi ke mishi binshi da ido yake yana jin k'aunar B'iyayen nashi har cikin ranshi, yana gama manna mai bel d'in ya mik'e tsaye tare da kamo net d'in wuyan Usman d'in ya gyara mai zaman shi sannan ya kalleshi cikin muryar bacci yace. "zo kasha tea." Kai ya gyad'a cikin sauri yabi bayan shi a parlour suka tsaya shi Dr Umar Faruoq ya had'awa Usman d'in tea tare da mik'a mishi cup d'in, karb'a yayi yana d'an kurb'a yace. "Hamma zan shiga cikin gida." Kai ya gyad'a mishi ba tare da yayi magana ba, shi kuwa Usman murmushi yayi ya fita ya nufu cikin gidan, Usman d'in na fita shi kuwa ya mik'a a hankali yayi mik'a tare da yin salati cikin takun bacci ya nufi cikin d'akin da nufin ya koma baccin har ya konta idonshi ya haggo mishi magungunan Usman dake kan mirror daga duk kan alamu Usman baisha maganin ba hakan yasa Faruoq d'in mik'ewa da sauri ya d'auki magungunan tare da fitowa parlour goran Faro ya d'auka ya fito ya nufi cikin gidan. Shi kuwa Usman a part d'in kakarsu Hajjajo ya samesu suna zaune a parlorn ta suna ta hira, cikin yana yinsa na sakin fuska ya shiga hannun shi rik'e da cup d'in tea yana sha yana d'an lumshe ido, yana shiga Hajjajo ta kalleshi cikin k'aunar jikan nata fuska dauke da murmushi tace. "Usumanu ka fito ne." har yakai cup d'in bakin shi ya cire tare da yi mata kallon kinafa bata min suna fuska ya d'an tsuke yace. "Allah ko Hajjajo kina b'ata min suna wai Usumanu kice min Usman na kawai inbaza ki iyaba kibar kirana." Murmushi tayi tare da cewa. "Zo ka zauna kaci abinci." "Toh" yace sannan ya matso kusa da Ya Adam hannu ya mik'a mishi suka gaisa sannan ya gaida ya Sadiq, sannan ya juya zai k'arisa gaban Inna yazo dai-dai gaban Ummul khairi dake zaune kan hannun kujera sai ya tsaya ganin yadda ta karya wuya ta tsura mishi ido tana murmushi gaban ta ya matso dai-dai lokacin Nenne da Aliyu kuma suka shigo parlour, ita kuwa Ummul kai ta k'ara d'agowa cikin koikoiyar muryar Ruk'ayya budurwar Nuru tace. "Ya Usman ina son ka." Murmushi yayi tare da k'ara matso ta ya tura k'afa d'aya gaba d'aya kuma ya maida shi baya ya d'an rink'a sonkuyowa kanta sannan ya koikoiyi muryar abokinshi Nuru yace. "Allah d'aiyiba ." Gaba d'aya su Nenne da ya Adam da ya Sadiq kam sai dariya suke Aliyu harda rik'e ciki Hajjajo kuwa sai binsu tayi da ido tana murmushi dan tasan shek'iyan cin Usman yawa ne dashi. Shi kuwa Usman ko a jikin sa sai tea d'in shi yaci gaba da sha, Itama Ummul sai murmushi takeyi ta zauna gefen shi tana sa mishi abinci. dai-dai lokacin Dr Umar Faruoq kuma yayi sallama duk da yana jin yadda suke ta dariya, yana shiga ya gaida Nenne ya Adam da Sadiq kuwa suka gaida shi, gefen Hajjajo yaje ya zauna tare da tonk'oshe k'afafun shi kanshi a sunkuye yace. "Hajjajo an tashi lfy." Juyowa tayi tana fuskan tarshi tare da zubawa kekkyawar fuskar sa ido, shi kuwa bai bita kan ta amsa mishi gaisuwar ba ya sunkuyar da kai yana b'allo magungunan Usman d'in. Ido Hajjajo ta lumshe cikin k'aunar jikan nata da takeji tamkar ranta donko ya kasan ce shine jikanta na forko da ta fara mallaka uwa uba ga tsananin kamar da ya keyi da mahaifin shi gashi takwaran mijin tane hakan yasa take masa wani irin so mai tarin yawa gashi da halaiyar girma Doctor Umar Ibrahim Umar shuwa kenan. Cikin kula tace. "Umaru sanda kafi mata yanga Umaru kafi k'arfin kab'i mace sai dai ta bik'a Ummaru sanda mai k'amshin al'miski sanda babuga mai taimakon na gida da woje , Ummaru tsiyar ka rigima da mishkilanci ko maganar ka tsada gareta." Kanshi a k'asa ya d'an lumshe ido har ga Allah shi wannan halin nashi halittar sa ce haka Allah yayishi bai san ya zaiyi ya canza kanshi ba haka yake, a ranshi yace. "Ya zanyi da Rubutaccen al'amari haka Allah ya halicceni bazan iya canza kaina ba". Ita kuwa Ummul tuni ta tsuke fuska dan sam bata jin Hamma Umar Faruoq d'in nasu kamar jinin ta haka kuma ya samo asali ne da yanayin halin Faruoq baida shiga harkar da ba tasaba bayi da yawan magana baya kuma son raini da hayaniya yana da girmama na sama dashi har ranshi kuma yake jin son y'an uwanshi a ranshi yana kuma kula da yanayin tarbiyar k'annen shi a matsayin shi na babban yaya, suma kuma suna son d'an uwansu sai Ummul ce da sam bata ko son su had'a inuwa d'aya da shi. Tsuke fuska Ummul ta kuma yi jin yadda Hajjajo ke wani bashi kula ta musamman shiko ya wani shareta. Su Adam da Sadiq da Aliyu da Usman sai murmushi sukeyi. Shi kuwa yana gama b'allo maganin ya mik'awa Usman tare da bud'e mishi ruwan ya bashi yasha sannan ya had'a maganin wuri d'aya tare da mik'ewa ya fita a hankali yana zuwa bakin kofar woyarshi ta fara tsuwa cikin wani sautin wak'ar India kaal hoh nan hoh sautin ne da ya kasan ce ko ba,a ga Umar Faruoq a wurin ba matukar akaji sautin toh tabbas yana kusa da wurin sauti mai cike da sanyi da tausayi. A hankali ya fito a barandar Hajjajo ya koma gefen baya kad'an tare da zauna wa kan kujerun dake jere a wurin. Woyarshi ya zaro a hankali yayi picking ya fara magana a hankali. Su kuwa a parlour Usman ne ya mik'e tare da cewa. "Nenne bari in tafi gwadago." Murmushi ya Sadiq yayi tare da cewa. "Tab ai kai kam aikin wuya kam baka cikin kai da zuciyar ka take rabi ai sai dai kaje back kana shan rab'a." Hannun shi yasa ya d'an dafe k'irjin shi cikin lumshe ido yace. "Da kenan ya Sadiq yanzu nayi lafiya zuciya ta kamar taka take ko buhu zan iya d'agawa." Adam ne ya d'an kalleshi yace. "Sai dai buhun kam amman damuwa da firgicin da zuk'atan mu zasu iya jurewa taka zuciyar bazata iya d'auka ba." Murmushi sukayi baki d'aya ita kuwa Ummul maya finta ta gyara cikin fara'a tace. "Yauwa ya Usman dama zanje gidan Anty Sadiya dan tunda akayi sallah ban jeba." Hannu ya mik'a mata tare da cewa. "Zomu tafi yar k'anwata zan kaiki." Aliyu ne ya kalli Nenne da sauri yace. "Nenne kina ji wai zata tafi gidan Anty Sadiya kuma batayi girkin ranaba." Da sauri Nenne tace. "Ehh haka nefa Autana kaga har na manta, kai kam Usman tafi kawai abinka kar ka makara, Ita Ummul sai tayi girkin rana." Lokacin d'aya idanun Ummul suka ciko da k'ollah tib hannu ta rink'a yarfawa a hankali tana d'an buga k'afafun ta tare da yin kan Aliyu tana cewa. "Ma gulmacin yaro dan munafurci Aliyu duk k'asa min ido a rayuwa ta shi yasa wallahi na gomma ce ina school ba mai takura wa rayuwa ta." Sai ta kuma juyowa gun Nenne cikin muryar lallashi tace. "Ayyah Nenne na kiyi hak'uri ki barni naje wallahi zan dawo da wuri inyi aikin dare." Kai Nenne ta girgiza alamun bazata jeba. Sai hawaye car-car a fuskarta. Shi kuwa Aliyu dariya ya fara yi cikin jin dad'in ya d'ana mata tarko. Kanshi tayi a fusace tana. "Munafuki wallahi sai na dokeka." Cikin dariya ya zille ya fara gudu ita kuma tana binshi a baya ta kasa kamashi. Shiko Aliyu gudu yake tare da cewa. "Yoh ai laifin ba nawa bane tunda bani nace duk randa kika dawo Hutu ko weekend kece zakina yin girki ba, Hamma Umar Faruoq ne ya fad'a, kuma kice ni zaki daka, kije ki ce mishi bazakiyi girkin ba mana, ni me nawa a ciki?." Kuka ta farayi tana binshi tana cewa. "Ai shima mugun tace kawai ya hanani hutawa a rayuwa ta, ga masu aikin Amman don mugunta yace ni zanke yin girki mugu kawai mai bak'in hali." Dariya Aliyu ya kuma yi harda yi mata gwalo yace. "Shifa Hamma Umar yana tausayawa mijin da zaki aurane shi yasa yace ke zakina aikin , don karkije baki iya girkiba, a ga laifin iyayenmu." Binshi tayi da sauri shi kuma ya nufi woje da gudu yayi gefen da ya hoggo Hamma Umar d'in nasu yana gudu yana juyowa yana kallon ko ta kusa kamoshi. Shi kuwa Dr Umar Faruoq tun da ya katse kiran woyan da yake yin, yake jiyo hayani yarsu shi Aliyu a hankali yake tsokanar ita kuwa Ummul sai mita da kuka take yana jin tana ta cewa Aliyu munafuki, Kalmar da baya k'aunar yaji an suffanta mutun da ita. Ita kuwa sam bata lura da Hamma Umar d'in a wurin ba. Shi kuwa Aliyu ya zo dai-dai gaban Hamma Umar d'in ya sule yayi wani irin mugun fad'uwa a k'asan tayis, gum ya buge bak'in shi a take sai ga jini, cikin wahala ya saki kuka mai k'arfi, wanda yasa su Nenne fitowa a guje. Shi kuwa Hamma Umar da sauri ya mik'e ya d'ago Aliyu ranshi a b'ace ya kalli yadda bak'in yaron keta zubda jini, ita kuma tsayuwa tayi jikinta nata rawa ganin yadda jini yake zuba a bak'in k'anin nata ga wani irin mugun kallo da Hamma Umar ke watsa mata. Ganin su Nenne sun fito tayi maza tayi bayan ya Usman dan shi kad'ai ne mai kareta su ya Adam ma kullum fad'a suke mata da biyewa Aliyu da takeyi tayi ta jibagarsa. Ita kam Nenne da sauri ta k'arisa gaban Dr Umar Faruoq da ya tallab'e hab'ar Aliyu cikin fad'a tace. "Ummul zaki kashe min yaro a banza ga yadda kika fasa mishi baki akan zuwa uguwa." Ita dai Ummul sai hawaye hannun Usman ta rik'e da k'arfi ganin Dr Umar Faruoq ya kirata da hannunshi cikin rawan murya tace. "Ya Usman dan Allah ka bashi hak'uri wallahi bazan sake ba Allah ban san zai fad'iba." A hankali Usman yace. "Hamma tace kayi hak'uri." Fuska ya tsuke murya a fad'ace yace. "Zo nan." K'ara k'ak'k'ame hannun Usman tayi tana zubda k'olloh, shi kuwa Usman hannushi yasa a hankali ya b'amb'areta a jikin shi cikin rad'a yace. "In baki jeba zai k'ara hatsala kije ki k'arb'i hukun cinki." Cikin zubda k'olloh tayi gaban shi a hankali take taku har zuwa gaban shi tana zuwa ta durk'usa a gaban shi. A hatsele yasa k'afa ya tureta tare da cewa, " taso." Da sauri ta mik'e ta tsaya a gaban shi. Mari ya watsa mata cikin fad'a ya nunata da yatsa yace. "Kika kuskura kika k'ara cewa wani munafuki wallahi sai na fasa miki baki, ke kullum bakya jin magana, kiyi ta munafurta mutane kuma kece mai halin muna fukan, kalli yadda kike kuka tun ba'a tab'aki ba, ko shi da kika fasawa bak'in baiyi wannan kukan ba, kuma kiji daga baki na ba inda zaki je sai shegen son yawo." Sai ya kuma watsa mata mari tare da cewa. "Ki wuce kiyi cikin gida ki fara akin ki tun wuri." Baki na rawa tace. "Toh" Ta fice ta tafi tana kuka Usman ne yabi bayan ta da sauri yana lallashin ta har saida ta d'an huce ya kalleta cikin kulawa yace. "Allah ya d'aiyiba." Murmushi tayi tare da cewa. "Ya Usman Ina sonka." fuskarta ya shafa tare da koikoiyan muryar Nuru yace. "Allah ya d'aiyiba Dariya sukayi baki d'aya sannan ya fice ya tafi. Hajjajo kuma da Nenne da su ya Adam parlour Nenne suka bita, Nenne da su ya Adam fad'a suke mata, ita kuwa hajjajo lallashinta take yi. Shi kuwa Dr Umar Faruoq yana rik'e da hannun Aliyu har suka shiga parlour su, kan kujera ya kontar da Aliyu dressing na wurin yayi mishi tare da bashi maganin ya sha, sannan ya kunna mishi A,C da TV. a hankali Aliyu ya rink'a sauk'e ajiyan zuciya tare da lumshe ido, lokacin d'aya yayi bacci, shi kuwa Dr Umar Faruoq wonka yayi tare da kimtsawa ciki shigarsu irin ta manyan doctors sai k'amshi yake zubawa ya fito ya nufi katafaren chemist d'inshi mai suna Baba aura chemist dayake kusa dasu, yana zuwa dai-dai bakin wurin yayi wani irin....... By *GARKUWAR FULANI* [6:47AM, 9/20/2017] ‪+234 706 196 7803‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 3⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wannan shafi d'ugguruggum dinshi naki ne ke kad'ai Mamyn Najmah ina al'fahari dake ina sonki har cikin raina Allah ya bar zumunci ngd da k'aunar ki gareni 😘😍🤝* *A*jiyan zuciya tare da lumshe ido, ganin mutane da suke cike a harabar bakin chemist d'in mata da maza manya da yara, cikin ranshi yake fad'in, "Allah ya bashi ikion dubasu baki d'aya". Fitowa yayi cikin nutsuwa ya nufi wurin da ya kasance wurin zaman shi a ko wacce rana matuk'ar dai ya shigo potiskum toh shi baya samun hutun weekend d'in. Yana isa yaranshi da ke aiki chemist d'in suka yi mishi barka da safiya, sannan ya zauna ya fara duba marasa lafiyan d'aya bayan d'aya yana mai basu kulawa yadda ya kamata duk da ba sakin fuska yake yiba amman a fili za'a gane fuskarsa mai ciki da tausayi ne da jink'an marasa lafiyan, dan bashi da surutu maganar sa a k'aiyade take . Haka ya yayi ta dubasu har zuwa azahar daga nanne ya tashi tare da sa yaran nashi suka rufe chemists d'in sannan sukayi alwala suka nufi masallaci dan yin sallan a jam'i. Bayan an idar da sallah su suka koma bakin aikin su shi kuma kai tsaye gida ya nufa dan gaba d'aya ya gaji ga yunwa ga baccin da yake ji. Ita kuwa Ummul bayan ta shiga kitchen ta fara aiki kenan , woyarta ta fara suwa tun kafin ta d'aga tasan waye ne dan sautin kiran kawai ke shaida mata Mustapha ne ke kiran ta haka yasa cikin shauk'i da k'aunar juna suka fara magana a woyar, gas d'in ta kashe sannan ta fita cikin takunta mai cike da nitsuwa, kai tsaye ta nufi part d'in kakarsu Hajjajo bedroom ta wuce tana zuwa ta d'ale kan gadon ta mai rumfa cikin sanyin muryar da ko kana gefen ta a kan gadon bazaka ji abin da take fad'i ba, Ido ta lumshe cikin sauk'e ajiyar zuciya tace. "Habeebi" "Na'am." Yace mata tare da cewa. "Ummul kina sani d'imuwa soyayyarki tana cazamin kai da jinin jikina k'ok'olwata na cushe in banji muryar ki na awa 3 ba Ummul ki daure ki soni ko rabin yadda nake sonki." Ido ta kuma lumshe wa cikin hura mishi iska a kunne murya can k'asa tace. "Ya Habeebi ka kontar da hankalin ka Ummul taka ce jiki da jini da duk wani motsina kana cikin raina ko bacci nake fuskar ka itace k'awan yata." Mustapha kam k'ara sakewa yayi kan kujerar da yake konce gaba d'aya tsikar jikin shi yana mik'ewa lokaci d'aya kalaman ta suka sakar mai wani kasala da shauk'i k'aunar ta yakeji na ratsashi har cikin k'ahon zuciyarshi, yayin da ita kuwa Ummul take jin duk duniya ba yanayin da take so da jin dad'in shi kamar kasan cewa a haka suna musayan zantukan so masu sanyi, ji take matuk'ar babu Mustapha a rayuwarta toh gani take kamar ba nunfashi tare da ita. Haka sukaci gaba da soyewa kamar su shiga jikin juna, ita kuwa Ummul gaba d'aya ta manta da wani batun girkin da aka sata, haka yasa tayi ta woyarta sune basu katse hirar ba sai 12:23 pm tana katse kiran kuma bacci ya kwashe ta, bata farka ba sai yanzu da taji muryar Hamma Umar a parlour HaJajjo. Ita kuwa Nenne dama ta shiga mak'o tansu duba mara lafiya so batasan me Ummul tayi ba. *Asalin dengar takan su, Zuriya d'aya ce duk su jikokin Alhaji Umaru shuwa'arab ne* Alhaji Umaru Shuwa'arab asalin sa shi da matarsa Rabi'atu Hajjajo kenan su Shuwa'arab ne asalin ma zauna garin patiskum cikin unguwar tudun wada yamma da fce, kowa yasan shuwa'arab kyewawane kuma masu jin larabci ne, Alhaji Umaru da Hajjajo suna da yaran su 3 duk mazane babban d'ansu Alhaji Ibrahim Umar shuwa sai k'anneshi biyu tagwaye ne Hassan da Husaini sun tashi cikin gata da tsantsanr k'aunar juna, Alhaji Ibrahim shine babba kuma ya kasan ce mutun mai tausayi da k'aunar k'annenshi yana musu so mai tsanani, iyayensu kuwa sun basu tarbiya mai inganci tare da ilimin addini da na zamani sun tashi cikin tsabtacecciyar rayuwa, da kulawar iyayen su bayan sun girma ne Alhaji Ibrahim yayi aure ya auri matarsa Amina ba fullatanar potiskum d'in, mace mai mutunci da kara da sanin ya ka mata, bayan anyi auren bada jimawa ba Allah yayiwa Alhaji Umaru Shuwa rasuwa, daga nan ragamar gidan ya zama a hannun Alhaji Ibrahim yake ya rik'e k'anneshi da amana ya basu dukkan abinda uba zai bawa ya ranshi sunci gaba da karatu su . Yana zaune da matarsa da mahaifiyar shi a gidan shi da k'annenshi baki d'aya, Ranar da Alhaji Umaru Shuwa ya cika shekara d'aya da rasuwa a ranar Amina matar Alhaji Ibrahim ta haifi d'anta fari tas kekyawa dashi mai kama da babanshi, ran suna yaro yaci sunan kakanshi Umar Faruoq kenan. Yaro ya tashi cikin gata da kulawan mahaifiyar shi da kakarshi da k'annen mahaifinshi Hassan da Husaini, yaro mai farin jini da kwarjini. bayan shekara 4 Alhaji Ibrahim, yayiwa k'annenshi Aure rana d'aya, suka tare a gida jen da ya gina musu a gefen nashi. Bayan watannni 5 da auren Khadija matar Hassan ta fara laulayin cikinta na fari a lokacin kuma Amina matar Alhaji Ibrahim itama tana da cikin d'anta na biyu, matar Hussani kuma bata da ciki tukun , Bayan wani lokacin Amina matar Alhaji Ibrahim ta haifi d'anta na biyu mai suna Usman a lokacin Umar Faruoq kuwa ya cika shekara 5 da y'an watanni, Khadija matar Hassan kuma ta haifi d'anta na fari mai suna Adam wanda tsaka ninshi da Usman kwana 12 ne Usman d'in ya girmi Adam da kwana 12 haka yaran suka tashi cikin shak'u da juna ko mai tare akeyi musu, Umar Faruoq ya tashi da k'aunar k'annenshi. Usman da Adam suna da shekara d'aya a duniya Allah yayiwa Alhaji Ibrahim maifin Umar da Usman rasuwa. Rashuwa da ta shiga jikin Hassan da Hussain da Hajjajo sunyi kukan rashin d'an uwansu wanda shine madadin mahaifinsu a garesu. Amina matar Alhaji Ibrahim mahaifiyar su Umar wacce yaran ke karanta da Ammi tayi kukan rashin mijinta da rabuwa da yaranta dan tana gama ta kaba ta koma gidan iyayen ta, Alhaji Hassan wanda suke kira da Abba ya karb'i Umar da Usman ya dank'asu a hannun matarsa Khadija wacce yaran ke kira da Nenne sannan kakarsu Hajjajo itama tana gidan suka taru suka raini yaran cikin kulawa da tsantsar gata ta yadda su Umar basu san zafin maraici ba. Nenne kuma bayan ta haifi Adam ta kuma haihuwa yaran 4 Sadiq sai Sadiya sai Rabi'atu wacce take takwarar Hajjajo ce amman suna kiranta da Ummul khairi sai kuma d'an autanta Aliyu. Yaran sun tashi cikin k'aunar juna baka gane cewa Nenne ba ita ta haifi su Umar ba, Sai dai kowa da halinsa dan shi Umar mishkili ne baya wasa da yara kuma kasan cewarsa shine babba a family d'in su yasa k'annenshi suna girmamashi shi kanshi Umar yana jin haushin yadda yake halinshi, yayinda hakan ya jamishi kiyeyyah a uzuciyar Ummul ita kuma gani take yana takura rayuwarta a, zahiri Umar yana jin zafin yadda wasu lokutan ake gaza gane cewa wannan halin fa ba yin kanshi bane Allah ne ya halicce shi a hakan. Sun tashi cikin gata da kulawa inda Umar a yanzu haka shi babban doctor ne yana d'aya daga cikin yerdeddun governor damaturu shine doctor dake duba lafiyar governor nasu kuma shine babban doctor dake aiki a general hospital damaturu, Usman kuwa shi accounter ne sai . Sai Adam Airforce ne yanzu haka a Kaduna yake sai in yazo ziyara. Sai Sadiq shi kuma yana aiki a ministry of justice. sai Halimatu Sadiya ita kuma nurse ce tana aiki anan cikin garin potiskum. Sai Ummul khairi ita kuma bayan ta gama primary school d'in ta aka jona mata secondary school GGC damaturu inda ta koma cikin damaturu da zama a cikin makaran ta, yayin da shi kuwa Alhaji Hassan Abban Ummul kenan shi yana aikine a offishin gwamna a damaturu hakan yasa Abba yana da gida a can inda yake zama yana aikin shi sai alhamis ya taho week end cikin garin patiskum d'in, hakan yasa idan anyi hutu Ummul takan zauna a gidan shi dake gidan jen maikata na ministry of works and housing dake gashua road damaturu dan jira ya gama aikin sa sai su tafi tare su koma cikin potiskum tare. A hakan ne wata rana Ummul ta fita ita da k'awayen ta suna d'an zagawa cikin uguwar, anan ta had'u da Mustapha saurayin da suke soyayya a yanzu haka, shima yazo gun abokan shine a unguwar, dan shi Mustapha gidan su na commissioners quarters dake Maiduguri road damaturu, haka sukayi ta soyeyya in sunyi hutu yana zuwa har gidan su Ummul d'in dake potiskum, Haka yasa ya saba da ita ya saba da y'an uwanta suna yiwa juna so mai tsabta. Shi kuwa Umar sosai ya zuba ido kan lamuran Ummul, gashi in Abba baya nan kusan shine uba a gidan, so yana tsanani sa mata ido dan kare tarbiyar ta ita kuwa hakan yasa ta k'ara tsanarsa da jin tsoronshi, dan baya mata da sauk'i. Usman kuwa mutun ne mai fara'a da sakin fuska yana watsa da kawo dan shi ko da Abba wasa yake mishi kamar kakanshi, haka yasa Usman ya kasance wani jigo na gidan in ya fita ko na awa d'aya ne sai anyita ceki yarshi, shi da Umar kuwa suna yiwa juna wani irin so mai tsanani Umar yana k'aunar Usman fiye da komai a rayuwarshi suna yawan kaiwa Amminsu ziyara a gidan kakannin su. Usman tun yana k'arami ya tashi da ciwon zuciya mai tsanani inda Abba da Daddy Hussain in Abban kenan sukayi ta jin yarshi, a haka abin tashi hankali da fari an gane cewa zuciyar Usman tana da d'an hujin dake sashi ciwon zuciya so anyi ta bashi kula, amman kuma Usman na girma abin na k'aruwa haka yasa zuciyarshi ta zama ta tsage , dole aka fitar dashi Egypt so acan akayi mishi aikin tare da kulawar d'an uwanshi Umar Faruoq aikin da akayiwa Usman a cikin zuciyar shi aiki ne da yasa an bar wasu na'urori a cikin k'irjinshi d'an zuciyar tashi tayi raunin da bazata iya harba jininshi ba sai da wannan na'uran haka kuwa aka k'inda ya mishi dokokin aka hanashi cin duk wani abu green dan abubuwa green suna sa jinin d'an adam kauri shi kuwa zuciyarshi nada raunin harba tsinkekken jinima bare mai kauri sai na'urar ke iya harba jinin , haka duk bayan shekara 5 yake zuwa a canza na'urar, ko kusa da kai Usman ya zauna zakaji yedde na'urarnan take aikin a jikin shi tana, *cak-cak* yana harba amman sai ka matso kusa dashi sosai zakaji sautin a hankali. Wannan larura da Usman yake da ita yasa gaba d'aya zuriyarsu suke tausayawa mishi duk wata kulawa suna bashi, yayinda Umar Faruoq kuwa a duniya baida wata matsala sai damuwar ciwon B'iyayen shi, shi yasa duk wata kulawa ta duniya wacce uwa da una zasu bawa d'an su ya had'eta yana bawa k'aninshi Usman. Ummul kuwa da Usman suna rayuwa tamkar abokai, Anty Halima kuwa tana gidan mijin ta amman duk wata kulawa tana yiwa Ya Usman d'in nasu. Ya Adam da Usman kuwa su tamkar tagwaye suke tunda dama kwana 12 Usman yake bawa Adam. Ya Sadiq kuwa mutumin Hamma Umar ne. Auta Aliyu kuwa abokin fad'an Ummul ce shima yanzu ya kusa gama secondary school d'in shi ita kuwa Ummul sune suka gama this year so yanzu tana gida ana sama mata admission a FCE (T) potiskum zatayi NCE d'in ta akan maths and computer. toh fa a d'an wannan zaman da takeyi a gidanne take k'ara fuskantar takura fad'a da Umar ke mata hakan yasa ta k'ara tsanarshi. Haka Ita kuwa Ummul take da wani irin ciwon mara a duk lokacin da zatayi al'adarta kasan cewar a makaran ta tafara ciwon cikin sai ba'a santa dashi sosai ba tana dai fad'a tana ciwon ciki amman Nenne bata san ciwon mai tsanani bane..... *Tak'aitaccen labarisu kenan* Mun dawo kan labarin yanzu. Nenne na dawowa ta lek'a kitchen tana kiran Ummul tana fad'in. "Ummul kin gama ne?." Ido ta d'an zaro ganin ba abin da tayi a kitchen d'in cikin sauri ta fito parlour kan dinning table d'in ma ba komai agogo ta kalla da sauri ta fita ganin har 2:00 pm tayi. Parlour Hajjajo ta nufa tana kiran Ummul d'in. tana shiga Parlour ta kalli Umar Faruoq d'in cikin b'acin rai da fushi tace........ [truncated by WhatsApp] [6:47AM, 9/20/2017] ‪+234 706 196 7803‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 4⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Fatan alkhairi a gareku masoya na da wannan littafi nawa ina godiya da k'aunarku gareni 🙈🙈 kuyi hak'uri nasan wasu zasuce ba zasu fara karatu yanzuba sai nayi nisa sabida basa son farawa suzo suna jira toh dan Allah kuyi hak'uri duk wacce tasan sai anyi nisa zata fara toh ta Tarawa kanta kar sai nakai 20 ko 30 azo ayita bina P/C a nace ana so ni banzan iya hanaku ba sabida ina son mai sona kuma bana iya fiffik'e ido nayi banza da d'an Adam sabida d'an Adam abin karramawa ne Amman wallahi ina takuruwa gashi inada eyes problem kuyi hak'uri Ku tarawa kanku ngd Allah bar zumunci da k'auna GARKUWAR Fulani tana al'fahari da masoyan ta* Rai a b'ace cikin yana yin kai k'ararta tace "Umar kaga Ummul tafiya tayi bata yi aikin komai ba ko, yanzu-yanzun nan kira min Halima kace maza ta turota gida." Kallon Nenne yayi yace. "Tafiya tayi gidan Haliman ne? kuma batayi aikin ba?." Cikin takaici Nenne tace. "Ehh tafiya tayi mana tunda bata gidan nan tun dazu nake kiranta ban jita ba, gacan kitchen d'in kuma ba abinda ta tsinana." Hajjajo ce tayi tsaki dan ko ita bata san Ummul na cikin d'akin nata ba, cikin mita irin ta tsofaffi tace. "Wannan yarin ya akwai lalaci da k'in aiki, fisabillahi yanzu a haka za aurar da ita a kaiwa wani yayi ta famar yi mata bauta." Wani dogon tsaki Hamma Umar d'in ya ja, sosai yakejin zafin rashin jin maganar ta. Ita kuwa Ummul tuni ta fara had'a zufa dan tun dazu take son fita jin Hamma Umar d'in a parlour Hajjajo ya hanata fita, gashi yanzu kuma tanaji Nenne ta kawo kararta gun shi dama ya lafiyar kura a dawa bare an tab'oshi, hannu ta yarfa cikin sanyi da rawan murya tace. "Nenne nifa gani nan ba inda naje fa, kuma wallahi zanyi girkin." A hatsale Nenne tace. "Toh me kikeyi a cikin d'akin da kika kasa fitowa?, me kike aika tawa? wato ke har kullum indai batun aiki ne sai kin b'ata min rai ko?." Taku ta farayi a hankali tana fitowa parlour murya a hankali tace. "Ayyah Nenne kiyi hak'uri wallahi zanyi aikin yanzu zan gama." Hajjajo kam salati ta rink'a yi tana tafa hannu cikin mamaki tace. "Ke takwarata yanzu yaushe kika shigo ban ganki ba? kuma uwar me kikeyi a d'akin?." Baki ta d'an tura cikin kallon kakar tasu tace. "Wani abu nake yi." Harara Nenne ta watsa mata cikin jin haushi tace. "Bar min aikina zanje nayi abina, ki zauna nan ki gayawa Hamman ku dalilin ki na k'in yin aikin." Tana kaiwa nan ta fice part d'inta ta koma kai tsaye kitchen ta wuce ta fara aikin ta cikin sauri da tsanaki. Shi kuwa Hamma Umar tunda Ummul ta fito bai kalli inda take ba har Nenne ta fice , yana komce kan 3 str sai y'ar k'aramar k'orya da ke gaban shi mai cike da kindirmo mai kyau fari tas, konce yake rigin gine sai laptop d'in shi dake kan ruwan cikin sa ya hard'e k'afafun shi. Ita kuwa Ummul cikin tsarguwa ta tsuguna gefen shi kad'an tayi k'asa da kanta tana d'an satan kallon shi, Hajjajo kuwa mik'ewa tayi ta kalli Hamma Umar d'in cikin kula tace. "In dama maka da furane? ko insa maka dakkere ne?." Baiyi magana ba sai lumshe ido yayi, ita kuwa ganin haka ta shige d'aya d'akin ta fara dama mishi da fura. Shiru parlour su duka biyu ba wanda yayi magana har zuwa wani lokacin ganin haka Ummul ta gyara durk'usuwan da tayi don guiwowin ta sun fara tsami, fuska ta marairaice ta lokk'oshe kanta a kafad'ar ta tai rau-rau da ido murya can k'asa tace. " Hamma kayi hak'uri wallahi bazan sake ba". Shiru bai kula taba, itama shirun tayi dan ta sani da ta k'ara magana toh ta k'ara laifine dan zaice ta cika mishi kunne da hayani yarta." Haka yasa kawai sai ta rink'a jujjuya guiwowinta dan sun tara jini, gashi ta fara jin ciwon marar da yake mata duk wata, haka yasa ta fara zubda k'ollah tana d'an gogewa da tafin hannun ta, murya na rawa tace. "Hamma kayi hak'uri." Sai yanzu ya bud'e idanun shi a hatsale yace. "Uban me ya hana ki yin aikin?, wacce tsiyar kike aika tawa a cikin d'akin tun da safe?." Baki na rawa ta d'an matsa baya a hankali tace. "Hamma har na fara aikin fa, sai Mustapha ya kirani shine na zo nan d'in." Daga koncen yasa bayan hannushi ya yarfa mata mari da bayan hannun nashi, sannan ya tashi zaune ido ya kafa mata tare da cewa. "Amsa kiran Mustapha yafi aikin da zaki yiwa mahaifiyar ki ko?." Kai ta rink'a juyawa cikin toshe bak'in ta dan karta saki kuka, tana juya kai tace. "Kayi hak'uri Hamma bazan k'ara ba." Tashi yayi ya mik'e fuska a murtuk'e ya watsa mata harara tare da cewa. "Mik'e kije kiyi aikin kar in b'ab'b'allaki fitinenniya kawai mara jin magana." Da sauri ta fice tana zubda k'ollah tare da k'uk'k'ini k'asa-k'asa kai tsaye kitchen d'in ta shiga. tana zuwa tace. "Ayyah Nenne kiyi hak'uri' ki kawo aikin zan k'arasa." Rai a d'an had'e tace. "Je kici gaba da baccin ki, nayi aiki na, in bakiyi na gidan kuba ai zakiyi na gidan miji inda ko godiya baza'ayi miki ba." Haka Nenne tayi ta mata fad'a har suka gama aikin, itako tana bata hak'uri, Shi kuwa Hamma Umar nonon ya karb'a sannan ya koma part d'insu. Nenne kuwa suna gama aikin rana taje tayi wonka ta kimtsa d'akin Abba dan yau zai shigo potiskum d'in, haka yasa ta barwa Ummul sauran aiyu kan girkin dere da kuma abincin Usman da ban. Su ya Adam kuwa da ya Sadiq da Aliyu duk suna tare a parlour Nenne suna kan dinning table suna cin abinci. Aikin take yi cikin k'arfin halin dan ciwon da mararta keyi ya fara yawa sai ta shiga kitchen d'in ta d'an yi aikin in matar ta murd'a sai ta dawo parlour ta konta kan kujera tayi ta murk'ususu sai tayi jigib da zufa dan azaba. Shi kuwa Aliyu duk abin da take yi hankalin shi na kanta, dan yana matukar son yar uwarshi haka yasa yana lura da yadda take zuwa ta kontan . 8:00 pm Abba ya iso gida cikin family d'in shi su ya Adam da ya sadik duk suka nufi part d'in Hajjajo suna zuwa suka tsame shi shida Hussain in shi wato Daddy suna ta hira da dariya Hajjajo na zaune a tsakiyar su Hamma Umar kuma yana gaban su Abban kanshi a sunkuye yana zaune tsakiyar k'annen mahaifin shi, Abba ne ya kalleshi cikin kula yace. "Farouq ya ina k'annen naka? ban gansu ba." Ya d'ago kanshi zaiyi magana kenan su Adam suka shigo cikin girmamawa suka gaidasu sannan suka zauna sukaci gaba da hira, kallon Hamma Umar Abba ya kumayi tare da cewa. "Usman da ummul fa ina suke?." Aliyu ne yayi carab yace. "Abba Anty Ummul bata da lafiya tun d'azu kuka takeyi, ya Usman kuma yanzu ya dawo bai shigo ba tukun." Daddy ne ya kalli Hamma Umar d'in cikin yana yin tabbaya yace. "Farouq meke damun Ummul d'in.?" Kai ya sunkuyar a hankali yace. "Daddy ni ban san bata da lafiya bama sai yanzu." Nenne ya kuma kalla a hankali yace. "Nenne meke damun ta.?" Fuska ta d'an tab'e cikin kula tace. "Hmmm Umar kafa san Ummul da raki tun bayan sallan magariba take kuka wai cikin da mararta ke ciwo ko tashi tak'i tayi wai bazata iya ba." Cikin mamaki Abba yace kai Khadija mamana bata da lafiya kice raki , duk rakin Ummul indai taji na dawo toh zata zo tamin sannu da zuwa , tunda kikaga har ta k'asa tashi toh gaskiya tana jin jiki." Hajjajo tace. "Gaskiya kam gwara a dubata." Daddy ne ya kalli Hamma Umar din cikin bada umurni yace. "A gaskiya bata da lafiyan ne, Farouq kaje ka dubata." "Toh" yace tare da mik'ewa ya fita a ranshi yana cewa. "Mara lafiya ke zuwa gun doctor ita kuma uwar sakalci da raki doctor ne zaije ya sameta dan tsabar samun sake." A tsakar gida ya had'u da Usman murmushi Usman d'in yayi tare da sosa k'eya yace. "Hamma tun d'azu fa na dawo, yanzu sai naci abinci zanzo insha maganin." Kafeshi yayi da ido cikin k'aunar k'anin nashi da tausaya mishi, hannu yasa ya d'an bugi k'eyarsa tare da matse kunnenshi yana. "Usman baka jin magana , baka kula da lafiyar ka, baka jin tsoron da nake ji akan ciwon nan naka." Shi kuwa Usman d'an kara ya saki tare da cewa. "Wayyo Abba na Daddy kuzo Hamma na zai tsinke min kunne." Abba ne yayi dariya jin muryar Usman yace. "Da ka iso wuri ko ido bai ganka ba kunne zai shaida zuwan ka Usmanu shehu sarkin barkwanci shi kowa kakan sa ne." Daddy ne yayi murmushi tare da cewa. "Usman kenan shi shiya d'auki halin Baban mu komu y'ay'anshi bamuyi irin yanayin shi ba kamar yadda Usman yayi. , shiko Farouq koman shi. na Yaya Ibrahim ne har tausayin shi da kulawan shi a kan k'annenshi." Usman kuwa dariya ya rink'a yi yana juyawa Hamma Umar na binshi da ido yana kallon yadda k'anin nashi ke harkokin sa tamkar baisan ciwon da ke jikin shiba. A haka ya wuce ya nufi parlour Nenne, shi kuma Usman ya tafi gunsu Abba yana zuwa. Ya gaida su sannan ya kalli Aliyu cikin murmushi yace. "Kai Auta ina Ummul ban ganta ba?." Hajjajo ce ta kalleshi tare da cewa. "Bata da lafiya mai baka duk abinci da kake so kaci d'in, yau anan zakaci abinci." Cikin zillewa zancen yace. "Ni duk abinda doctors suka hanani bana cin karki wani had'ani da su Abba, kuma ko Nenne ma shaida ce bana cin komai matuk'ar dai green ne, dan haka karma kiyiwa Ummul lak'el kice ita ke bani komai naci, kowa yasan ina bin doka." Aliyu ne yayi carab yace. "A a kam ya Usman wallahi ko jiya kaci miyar ganye." Kai ya sunkuyar yana murmushi ganin yadda Abba da Daddy suka tsareshi da ido cikin tsoro Daddy yace. "Usman meyasa baka kiyaye lafiyar ka Usman ka rufa mana asiri kake bin dokokin doctors ko zamu samu ka rabu da ciwon nan." Murmushi yayi cikin k'arfin guiwa ya kalli Abba da gaba d'aya ya karaya jikin shi yayi sanyi hannun Abban dana Daddy ya d'an rik'e a hankalin yace. "Cuta ba itace mutuwa ba , lafiya kuma bata hana mutuwa nasan abinda kuke tsoro, ba haushe yace, nisan kwana maganin annoba, karku damu yanzu nayi lafiya jin zuciya ta nake kamar ta k'arfe." Murmushi su duka sukayi tare da sauk'e ajiyan zuciya sannan sukaci gaba da hirar. Shi kuwa Hamma Umar a hankali yayi sallama, a bak'in k'ofar ya tsaya jin ba'a amsa sallama ba sai sheshek'an kukanta da yake ji, haka yasa ya kutsa kanshi cikin d'akin kan gado ya hoggota konce sai murk'ususu takeyi hanna yenta rik'e da mararta kuka takeyi sosai cikin wahala gaba d'aya ta birki ce, A hankali ya matso bak'in gadon murya can k'asa yace. "Ke me haka? shin baki iya Addu'a bane sai kuka? ki nitsu ki gaya min meke damun ki?." Ido ta k'ara rumtsewa cikin wahala ta d'an mirgino tayi rigingine tare da cewa. "Wayyo Allah na! cikana! marana!." Fuska a tsuke ya sunkuye kanta kanshi ya kawar tare da rumtse ido a hankali ya tura hannun shi cikin rigar ta kan mararta yasa yatsunshi ya matse tare da danne matar tata. Mik'a tayi tare da sakin wani irin kuka cike da azaba a gigice ta yunk'uro cikin rawan jiki ta sa hannu ta dam k'o.... By *GARKUWAR FULANI* [6:47AM, 9/20/2017] ‪+234 706 196 7803‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL'AMARI* Page 5⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Wannan shafi naki ne k'awata ta gari Ngd da k'aunar ki gareni Hauwa Halliru (Mmn khairat) Allah bar zumunci da k'aunar Ngd Ngd Ngd 🤝😘😍* Hannun shi cikin wahala da gala baita ta ture hannun taci gaba da murk'ususu tana yarfa hannu da juya kai, duk da sanyin a/c dake ratsa d'akin ita zuface keta tsatstsafo mata duk ta inda hudan gashin jikin ta yake, tsayuwa yayi tare da tsuke fuska kai ya jinjina ya fice abin shi, Parlour Hajjajo ya nufa, sallama yayi tare da shiga gefen Abba ya zauna kanshi a sunkuye yace. "Abba tak'i ta tsaya in dubata sai kuka take yi." Nenne ta kalli Abba tare da cewa "Toh ai kunji ko mara lafiya da gardama, yoh ba sai abarta da ciwon taba, ai bai dameta bane da ita zata nemi maganin". Daddy ne ya mik'e tare da Hajjajo Ya Usman da Ya Adam na biye da su a baya har sunje bak'in k'afar Daddy ya juyo ya kalli Dr Umar Farouq d'in cikin murmushi dan yasan Umar ya hatsala ne, murmushi yayi kumayi sannan yace. " Farouq zo muje ka dubata ko." Kai ya kuma sunkuyar wa cikin yana yinshi na girmamawa ya mik'e yabi bayan su, Nenne ma da Abba da Aliyu biyosu sukayi. Suna zuwa Parlour Nenne Daddy ya zauna tare da d'an d'aga murya yace. "Ummul kizo nan, taso kizo ko mamana, kizo Hamman ku ya dubaki." Jin muryar Daddy ne yasa ta k'ara sakin kuka dan tasan Daddy yana matuk'ar k'aunar ta da lallab'ata, Jin ta fashe da kukan ne Hamma Umar ya zauna kan carpet a gefen Daddy a hankali yayi tsaki, Usman kuwa da Hajjajo cikin bedroom d'in suka wuce suna zuwa, Hajjajo ta zauna gefen ta cikin sauri ganin yadda take kuka da juyi gaba d'aya fuskarta tayi jazazir sai zuba da ya mik'a jikinta kab sai numfashi take a wahalce, da sauri ta rik'o ta cikin kid'ima take kiranta. "Subahannalhai Ummul me yake damun ki haka? yaushe ya fara miki wannan ciwon ?." Kanta ta kuma kifewa kam pillow cikin cije lips d'in ta ta junk'ura ta zauna gaba d'aya jikinta rawa yakeyi hannu ta rink'a damk'e wa baki na rawa tace. "Marata zata b'alle jiri nakeji cikina k'uguna yana sarawa." A kid'ime Hajjajo ta kamota tsayar da ita tayi tare da talla beta cikin tattaro k'arfinta tace. "wannan wanne irin ciwone kamar maiyin nak'uda." A haka suka nufi parlour Usman kuwa na biye dasu a baya gaba d'aya tausayin ta ya cika shi ya kasa komai sai. sannu yake ce mata. Kan 3 str Hajjajo ta kontar da ita . Nenne kuwa gaba d'aya jikin ta sai ya kama rawa ganin yadda yartata ta birkice. gaba d'aya sai sannu suke ce mata, abu kamar nak'uda duk ta galabai ta, Abba ne ya kalli Hamma Umar d'in tare da cewa. "Farouq me haka kuma? meke damun ta.?" Juyawa yayi gaban ta ya d'an taso ya tirk'usa kan giiwarsa sannan ya kalleta cikin tsura mata ido yace. "Ki nitsu ki gaya min ina ke miki ciwo." Kai ta jinjina a wahalce. Shi kuwa kai ya d'an sunkuyar sannan yace. "Meke damun ki?." "Cikina da marata." "Yaushe ya fara miki ciwon?." "Tunda yamma." Kallon ta ya d'an yi sannan yace. "Cikin da matar kad'ai ne ke ciwon?." Dafe k'ugunta tayi murya na rawa tace. "Harda k'uguna yana sarawa kamar zai b'alle." Harararta yayi k'asa-k'asa tare da tsuke fuska yace. "Karki cika min kunne da kuka in zaki magana kimin yadda zan gane kin sani sarai bana son hayaniya." Usman ne ya d'an matso tare dasa d'an kwalinta ya goge mata zufan ya kuma d'an kalli Hamman nashi a hankali yace. "Hamma meke damun ta?." Ya fad'a shima kamar zaiyi kuka Shi kuwa fuska ya kuma tsukewa yace. "Dama kina irin wannan ciwon ne?." Kai ta gyad'a alamar ehh. Juyawa ya d'an yi kanta sannan yace. "Bak'in ki bazai iya magana bane? ko kuma kin zama kurma?." "Ehh dama yana min." Ta fad'a a hankali. "Sau nawa ya tab'a yi miki hakan?." Ido ta rumtse cikin jin kunya tace. "Ko wanne wata sai yamin haka." Baki ya tab'e dan gano matsalar ta, Hajjajo ma da Nenne sun gano abin da ke sata hakan shiyasa sukayi shiru suna kallon ta. Shi kuwa Hamma Umar kamar cikin mugunta yace. "Allurai 3 za ayi miki." Jin allurai har 3 yasa ta zaro ido woje cikin rawan murya tace. "Ni dai a barni da ciwona zuwa gobe zai bari, dan Allah Hamma kar kamin allura." Daddy kuwa da Abba Umar suka ni da ido cikin yana yin tabbaya suka tsareshi da tabbayarki me yake sata ciwon . Shi kuwa Hamma Umar mutun ne mai tsananin kunya hakan yasa gaba d'aya sai ya resa ya zaiyi musu baya min ciwon nata. Sai ya kalli Ummul d'in cikin lumshe ido yace. "Ke me yake saki ciwon? kinaji ana tabbaya kinyi shiru, ko kina jiran ni zan amsa miki ne?." Kai ta sunkuyar cikin tsananin kunya da wahala sai hawaye car-car a fuskarta. Shi kuwa Hamma Umar ganin su Abba sun maida hankalin su kanta, yasa yayi maza ya zille ya fita. Part d'in su ya nufa yana zuwa ya had'a alluran da zai mata sannan ya ajiye cikin firij woyarshi ya zaro tare da kiran Nenne tana d'agawa yace. "Nenne Ummul d'in tazo zan mata allurar, tazo da sauri dan akwai masu jirana a woje zan fita gunsu." toh Nenne tace. sannan tasa Ummul d'in ta mik'e ta fita badon ta soba. Shi kuwa zama yayi ya d'an jirata, ganin shiru bata shigoba ya mik'e ya shiga toilet wonka yayi sannan ya fito daure da towel a k'ugunshi, parlour ya fito da nufin ya d'aukam woyarshi ya sake kiran Nenne. Ita kuwa Ummul a daddafe ta shigo parlour tana shiga yana shigowa shima. Ganin ta a tsaye ya sashi juyawa da sauri ya koma cikin bedroom d'in, tsaki yaja sannan ya kimtsa tare da fesa turare a jikin shi. Parlour ya dawo yana watsa mata harara, ita kuwa Ummul batama ganshi ba lokacin da ya fito d'in haka yasa bayan san abinda yakewa harara da tsakin ba. Bayan ta ya zagaya rigar ta ya d'an nad'e sannan ya d'an yi k'asa da zanin ta, ba tare da ya ture farin ondawunyan ta da pan d'in tabaya dire bakin alluran a kansu, dan shi haka yake matukar zai yiwa mutun allura mace ko namiji ba tab'a yarfa ya kalli fatar jikin mutun dai-dai yayi alluran a kan gajeron wonddon mutun inko mave ce kan siket d da pan d'in yake d'aura allurar. Tana jin yana murza bak'in alluran sai kuma ya tsaya cikin fad'a yace. "Ke ki sake jikin ki uwar tsoro allurace ba mashi ba kike wani Kane jikin ki, kuma d'aga yau karki sake shigo min d'aki tunda baki iya sallama ba, ki bari sai randa kika koti sallama." Ita dai kai kawai take gyad'awa da rumtse tafin hannun ta. K'ara ta d'an saki tare dasa hannun ta ta baya ta kamo k'ugunshi ta rik'e da k'arfi ido ta rumtse jin yadda ya zirnik'a mata allurar, k'ara damk'e shi tayi dan yadda taji zafin yadda ruwan allurar ke shiga jikin ta. Shiko Hamma Umar da sauri ya zare allurar sannan ya janye hannun ta dake kan k'ugunshi kan mazaunanta ya dire mata hannayen nata sannan ya tura ta murya a fad'ace yace. "B'acemin da gani, sokuwa kawai ba abinda kika iya sai koke-koke banza kawai duk kin cika min kunne." Ita kam Ummul tuni ta koma gefen ta jingina da jikin kujera dan jiri take ji ga wani irin suka da taji k'ugunta nayi lokaci d'aya kuma taji d'umin jini na bin k'afafun ta. Ido Hamma Umar ya zaro mata tare da buga mata tsawa fuska a yatsine yace. "Fice min a d'aki kina tsaya har saidakika zubar min da k'azan tarki , ubanwa zai goge miki wannan abin." Ya fad'a yana nuna jinin dake bin k'afafun ta a take kuma rumtse ido yana yamutsa fuska cikin fad'a yayi kanta. Dai-dai lokacin Usman kuma ya shigo. Da sauri yaje gaban ta cikin kula ya kamo hannun ta kai ya lok'osa a kafad'an shi cikin sanyi yace. "Hamma kayi hak'uri ni zan gyara wurin." tsaki yaja sannan ya fice yana cewa. "Wallahi ka gyara wurin kafin na dawo ita kuma ta bar nan." Yana fita Usman ya kalleta a hankali yace . "Kije cikin gida." A kunyace ta fice ta nufi parlour Nenne . Shi kuwa Usman gyara wurin yayi tsab sannan ya feffesa turare. Yana gama wa Hamma Umar d'in ya shigo rik'e da magungunan shi, kan kujera ya zauna sannan ya bashi maganin, d'aga nan kuma suka yita hirarsu tare da Ya Adam da Sadik da suka shigo. Ita kuwa Ummul kai tsaye toilet ta shige wonka tayi ta kimtsa jikin ta sannan tazo ta konta kusa da Nenne ta, a hankali Nenne tace. "Ummul yanzu duk wata haka like gama da wannan ciwon cikin?." "Ehh " tace mata tare da lumshe ido dan kunya takeji. A khana a tashi haka rayuwa tayi ta juyawa shak'uwa tsakanin Usman da Ummul kullum k'aruwa yake yi zuroyarsu cike da farin ciki. Nasu da wata matsala Sai matsalar ciwon Usman da Ummul, wasa-wasa ko wanne wota Ummul sai ta galabai ta abin yaci tsura tasha magunguna da allurai har tagaji a banza. Abba kuwa ya matsala Nenne da tabbayarshin dama haka ko wacce mace take fuskantar wannan matsalar ne yayin yin al'adarta. Nenne takan ce mishi . "Insha Allah in tayi aure zai bari." A haka suka bar maganar. Sai yau kuwa tunda gari ya waye Ummul ta tashi da. ciwon ciki da matar ga sarawar da k'ugunta keyi. Kasan cewa Hamma Umar baya gida yana cikin Damaturu yasa Abba ya d'auketa shida Nenne suka kaita jama'a clinic kasan cewa doctor abokin Hamma Umar ne. Gwajin forko da doctor yayi ya gane matsalar ta, cikin girmamawa doctor yayiwa Abba baya nin ciwon nata ya kuma k'ara da cewa. "Abba dama akan samu wasu matan da irin wannan larurar, maganar gaskiya duk magungunan da za'a bata ko allurai duk aikin banza ne mafita d'ayace wacce zata rabata da ciwon nan da izinin Allah muddin akayi mata aure ta mu'amalantu da zaman takewar aure toh insha Allah zata rabu da ciwon nan." Cikin kad'uwa Abba yace toh, "Doctor menene mafita?." Ajiyan zuciya ya sauk'e tare da cewa . "Mafitar dai itace ayi mata aure kawai." Da wannan shawarar Abba ya koma gida tare da Nenne Ita kuwa Ummul bata san abinda ke wakana ba. Sai fama da takeyi da ciwon ta. Bayan kwana biyu Abba ya kira Hussain shi suka zauna a d'akin Hajjajo suka tattauna kan maganar Ummul su yasu suka gama maganarsu ba and a yasan abinda suka zantar. Yau jumma'a tun safe Ummul keta gyare-gyare da girkr-girke dan yau Habeebin ta Mustapha yana kan hanyarshi ta zuwa, 4:15 pm Mustapha ya iso, yana isowa Abba da Hamma Umar suka shigowa, da sauri Mustapha yayi parking ya fito ya nufi su Abba yana zuwa kusa dasu,yayi sauri ya.... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 6⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ya tsugana gaban Abba cikin girmamawa irin ta tsurkai ya yace. "Barka da dawo Abba." "Barka dai Mustapha ya hanya?." "Alhamudulallah Abba." "Masha Allah , taso ka isa daga ciki ko." Mik'ewa yayi cikin kunya tare da d'an murmushi a fuskar sa, gaban Hama Umar ya matso cikin sakin fuska ya mik'a mishi hannu. Shima Hamma Umar d'in d'an gajeren murmushi yayi tare da mik'o hannunshi suka gaisa. Abbanne ya kalli Hamma Umar d'in tare da cewa. "Farouq isar dashi parlour ciki." "Toh" yace sannan yayi gaba Mustapha na biye dashi a baya. Shi kuwa Abba part d'in shi ya nufa. Suna zuwa Umar ya kalli Mustapha a fakaice yace. "Ka isa ni zanyi cikin gida." "Toh nagode Hamma Umar Allah bar girma." "Amin" yace a tak'aice sannan ya fita , cikin gida ya wuce parlour Hajjajo ya nufa, yana zuwa yayi sallama jin shiru ba wanda ya amsa yasashi shigowa a hankali, parlour ba kowa, kan 2. str ya zauna tare da dan jingina jikin kujarar ido ya lumshe yana mai fidda numfashi a hankali, Hajjajo ce ta fito parlour hannun ta rik'e da carbi ido ta d'an zare tare da cewa. "Kai Umaru yashe ka shigo?." "Yanzu." ya bata amsa a gajarce, gefen shi taje ta zauna ta d'an kalleshi tare da tab'e baki tace. "Hmmm yau kuma halin ya motsone?." bai kulata ba sai zamewa yayi ya konta kan kujeran, ganin haka itama ta koma gefe ta zauna tana murmushi tana mamakin hali irin na Umar mutun ba'a gane inda ya dosa. A parlour Nenne kuwa Usman ne zaune yana kallon yadda Ummul ke zuba shek'i tayi kolliya mai kyau tayi shigarsu na shuwa'arab ta tubke gashinta tayi ras da ita riga da siket ne a jikin ta sunyi d'as gwanin shawa sai laffaya da ta yane jikin ta dashi har zuwa sama tayi irin yanawar da y'an mata sukeyi, ga wani irin k'amsi da take zubawa na turarukan humrarsu na shuwa, fuska ya d'an tab'e ya kalleta a d'an gyatsine yace. "Wai gasar kyau zaki je kike ta wannan kolliyar akan wannan Mustapha naki." Murmushi tayi tare da d'an juya ido ta d'an tsuke bakinta lips d'inta tad'an had'e tayi taku d'aya zuwa biyu tace. "Kai Ya Usman kaima da kanka kasan Mustapha da banne dole kuma komai nashi da banne." Fuska ya kuma tsukewa ya kalli Anty Halima dake ta nad'a mata laffayar yace. "Waike Halima me naki na zak'ewa kina shiryata kamar wata amarya." Murmushi tayi sannan ta kalli Usman cikin fara'a tace. "Ya Usman ai mace 'yar gyara ce." Ya Adam ne ya kalli Ummul d'in da Halima cikin harara yace. "Aiki ya same ku ai, ni wallahi sam Mustapha nan ba wani burgeni yake yiba kuma wallahi zan zuga su Abba a hanashi ma zuwa kawai ." Lokaci d'aya fuskar Ummul ta canza gaba d'aya annurin ta ya gimtse. Aliyu ne ya kalleta cikin tsokana yace. "Ummul in an hanaki shi zaki mutu ko? dan wallahi na lura jinshi kike kamar sarki." Harara ta cillawa Aliyu fuska a tsuke tace. "Mustapha yafi sarki a gareni shi shugaba zai zame min kuma shi tamkar jinina ne, shine bugun zuciya ta duk randa na ratsashi na rasa farin cikina." Ido Usman ya zuba mata yana mamakin yadda take son Mustapha, Halima ko murmushi kawai tayi , Ya Sadik ne ya kalleta a tsokone yace. "Kuma wallahi inaji a jikina bazaki auri Mustapha ba." Juyawa tayi tana fita tare da cewa. "Ashe ko duk wanda aka hanani Mustapha a dalilinshi toh tabbas yayi ban kwana da farin ciki a rayuwar sa zai fuskanci k'iyeyyar iya k'iyayya zai samu bak'in ciki mai isarsa." Tana kaiwa nan ta fice, Usman ne ya bita da sauri gaban ta ya tsaya cikin yin murmushi yace. "Koda ko d'an uwanki ne?." "Sosai ma ya Usman ko d'an uwa nane." K'irjinshi ya dafe cikin lumshe ido yace. "Koda ko nine ya Usman d'in ki?." Dariya tayi cikin lumshe ido tace. "Kai ai kai d'an uwa nane mai tayani son abin da nake so kai nasan bazaka zama silar bak'in cikina ba." Tana fad'in haka ta wuce ta tafi, shi ko Usman d'akin Hajjajo ya shiga yana murmushi gafen Hamma Umar d'in shi yaje ya zauna cikin sauk'e ajiyan zuciya yace. "Hamma yau kuma k'irjina yana min nauyi." Da sauri Hamma Umar ya mik'e tare da bud'e ido yana kallon Usman cikin tuhuma yace. "Me kaci? kashe maganin ka ?." Ido ya lumshe sannan yace . "Allah ko Hamma na ba abin da naci, maganin nedai ban shaba." Hannu yasa ya d'an bugi k'eyarsa cikin mik'ewa tsaye ya fice . Jim kad'an ya shigo hannushi rik'e da magungunan shi, bashi yayi yasha sannan ya kalleshi a hankali yace. "Jeka shirya kazo muje jama'a clinic na d'an dubaka sai mu biya, baba aura chemist na d'auko ma magungunan ka d'an sun kusa k'arewa." "Toh" yace sannan suka fito suka nufi part d'insu Usman ne ya fara wonka sannan yana fita Umar ya fitomai da kayan da zai saka, shima ya shiga yayi wonkan yana fitowa ya shirya tsab, shiga irin d'aya sukayi shigar shuwa'arab shigar da tafi kama da ta larabawa, sun fito ras tamkar tagwaye komai nasu irin d'aya hatta tafiyar su farar fatarsu sajen fuskarsu kamace ta sak da sak suke sun fito ras tamkar taurari sai shek'i da k'amshi suke zubawa, Suna fitowa Motar Umar suka shiga shi yake jan motar kai tsaye al'ameen restaurant suka nufa, suna zuwa suka shiga can ciki, lokaci d'aya aka had'a musu abinci dan sun saba zuwa wurin su maikatan har sunsan iya abincin da Usman ke iyaci so dama suna zuwa za'a kawo musu komai yadda ya kamata, kamar yaro Umar ya tasa Usman a gaba saida yaci yayi tik sannan ya biya komai suka fito, daga nan kuma clinic d'in suka wuce anan ya k'ara duba lafiyar d'an uwan nashi suna fitowa nan, kai tasaye katafaren chemist d'inshi suka wuce, ya had'a komai na maganin Usman d'in sannan, suna fita Umar ya sake jansu sai dicency super market , suna zuwa Umar ya had'e musu duk wani abin buk'atan su sannan aka loda musu a mota suka fito suka nufi gida. Ummul kuwa da Mustapha hirarsu sukayi sosai gaba d'aya sun susucewa juna hak'ik'a Mustapha yana son Ummul so na hak'ik'a haka itama take mishi so da iya gaskiyarta hirarsu suke basuma san maggariba tayiba saida suka ji kiran sallah, Mustaphanne ya kalleta cikin tarin so ido ya lumshe tare da sauk'e ajiyan zuciya murya can k'asa yace. "Ummul idanuna basa gajiya da ganin kekyawar fuskar ki! kunnuwana basa k'osawa da jin sautin ki mai zak'i ! hancina bayi da wani b'uri daya wuce shak'ar k'amshin ki, Ummul ina sonki son da bana yiwa kaina." Tafin hannun ta tasa ta rufe fuskar ta cikin jin dad'i da kunya tace. "Habeebi dani da murya ta da fuskarta da k'amshi na duk naka ne." Ido ya tsura mata tare da tasowa yazo gaban ta durk'usawa yayi a guiwowin shi a k'asa ido ya lumshe sannan ya bud'e su a hankali yace. "Ina jin tsoro Ummul inajin tsoron karna rasaki Ummul har yanzu baki zama tawaba gashi ban san yaushe Allah zai mallaka min keba ina sonki inason mu kasance ma'aurata Ummul kimin al'k'awarin duk rinsi kina tare dani ki min tattalin kanki kada idon wani namiji ya dira a kanki." Kallon shi tayi cikin murmushi tace. "Ako da yaushe ina shaida maka kai Habeebi da'iman ne a gareni zuciya ta ba inda wani zai samu ma tsuguni." Ajiyan zuciya ya sauk'e sannan ya mik'e yana kallon ta, itama mik'ewa tayi ta d'an matsa gefen shi, cikin sanyi tace. "Sai yaushe zaka kuma zuwa?." "Ko gobe in kina so zanzo, ina damaturu ina potiskum garin masoyi baya nida." "Gobe kam ai baka huta bama tukun." "Hutu kuma Ummul aini bani da wani hutu har sai na ganki cikin gida na." Murmushi tayi sannan tace, " toh muje kayi sallan maggariba sai ka tafi kar dare ya maka." "Kin gaji da ganina ne?." "Inko zangaji da kallon fuskar ka toh zan gaji da kallon tawa fuskar kenan." Murmushi yayi ya mik'a mata hannu wai suyi musabaha, kai ta sunkuyar a hankali tace. "Da saura." kai ya juya sannan ya had'e hannu a k'irjin yayi muryar tausayin yace. "Haka ne toh da wacce Kalmar za'a sallameni?." Juyawa tayi ta fara fita yana biye da ita a baya sunzo dai-dai inda zatayi cikin gida shiko zaiyi woje tace. "Laisa Lee misluka abadan ya habeebi. gareni bakada damka masoyina, ina sonka so mai tsananin Habeebi zanyi maka tattalin kaina dan cika zuciyar ka da farin ciki." Mustapha kam tamkar ya had'iye ta yakeji da tsabar k'aunar da da hali zai nuna mata sonta a fili amman ba dama, sai murmushi yayi tare da cewa. "Anti sururi, kece cikon farin cikina." Ya matsota zaiyi magana kenan yaga Hamma Umar dake zaune can gefen yana al'wala, haka yasa ya sallama ta, tayi cikin gida shiko yaje kusa da Hamma Umar d'in shima al'awalan yayi sannan suka tafi masallaci, ana idar da sallan suka nufi gida a bak'in gate Mustapha ya tsayai da Aliyu ya fito da manyan lododi guda biyu ya bawa Aliyun yace, ya kaiwa Ummul . Shi kuwa ya kama hanyar komawa damaturu A parlour suka baje tarkacen daya kawo mata kayan k'amshi ne sai atampopi guda 2 da les 2 sai shadda 2 sai yadukan laffaya masu kyau da taushi guda 3 , Anty Halima sai kallon Ummul take tana . "Iyeeh manyan masoya." Nenne kuma cewa tayi. "Maza Ummul had'e kayayya kin nan ki adana ko turaren bazaki fesaba." Fuska a marairaice tace. "Ayyah Nenne am kullum Mustapha ya kawo min abu sai ki hanani amfani dashi ban san me yasa ba ko kema bakya sonshi ne Nenne?." Murmushi Nenne tayi sannan tace. "Me yasa ina son Mustapha ai yaron kirki ne kawai dai wannan Al',adarmu ce budurwa bata amfani da kayan saurayi sai in sunyi aure, mu a gunmu in kiyi amfani da kayan saurayi kamar kasawa ce, toh kinga ke kuma ba abinda muka regeki dashi." Murmushi tayi ta tattara kayan, sannan suka ci gaba da hira, Abba da Umar da Usman dasu ya Adam kuma saida sukayi sallan ishah sannan suka dawo, suna shigowa su Usman sukayi parlour Nenne Hamma Umar kuma Abba ya kirashi suka tafi parlour Hajjajo, suna shiga suka samu Daddy ma yazo gun Hajjajon. Su Usman ko suna shiga, cikin halin girma Usman ya kalli Halima fuska a tsare yace. "Ke Sadiya har yanzu baki tafi ba?." Cikin girmamawa tace. "Ya Usman yanzu zan tafi." Mik'ewa yayi tare da cewa. "Muje in maida ki kinzo kin wuni bai kamata ki kai dare ba." Maza Ummul ta mik'e tare da cewa. "Yauwa ya Usman muje in rakaku." Kai ya gyad'a yace. "Oga Mustapha ya barki ne?." "Mustapha kuma ji ya Usman fa dama Mustapha ne ke hanani zuwa unguwa?." Juyawa yayi ya fita Sadiya na biye dashi a baya ita kuma Ummul tana gefen shi, kallon ta ya d'an yi sannan yace. "Keda ki kace Mustapha ya fimu matsayi." Murmushi tayi tare da rufe idon ta, shi kuma Sadiya ya kalla cikin murmushi yace. "Shiga baya kinsan Ummal da son zaman gaban mota kamar ba fullatana." Dariya sukayi sannan suka tafi. A parlour Hajjajo kuwa bayan su Abba sun d'anyi hira Abba yayi gyaran murya cikin kula ya kalli Daddy sannan ya kalli mahaifiyar su Hajjajo sai ya kuma kalli Hamma Umar cikin wani irin yanayi yace. "Farouq ina maganar aure da mukayi da kai?." Kai ya sunkuyar yayi shiru, ido Daddy ya tsura mishi tare da cewa. "Farouq shi fa aure dolene a gareka tunda Allah bai hanaka yadda zakayi ba, shin a zatonka munajin dad'in zaman ka hakan ne, Farouq ka sani duk girman mutun da darajarsa da matsayinsa matukar baiyi aure ba toh bai cika mutun ba." har lau dai baiyi magana ba sai sunkuyar da kai ya k'ara yi, a hankali Daddy yace. "Farouq me kake jira ne? da har yanzu baka fara maganar aure ba." Kanshi a sunkuye murya can k'asa a hankali yace. "Daddy ina jiran...... By *GARKUWAR FULANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 7⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *"Abba* ina jiran Usman ne." ido Abba da Daddy suka zuba mishi Hajjajo ko kai ta jinjina cikin mamaki tace. "Usman kana jiran Usman kuma? toh ka jirashi a kan me? me zakayi mishi da kake jiran shi?." shiru bai amsa mata ba bai kuma kalleta ba sai zaman shi da ya d'an gyara, juyowa gaban shi Abba yayi cikin son fahimtar sa yace. "Farouq! Usman kake jira? meyasa kake jiran shi d'in? ko so kake kuyi aure rana d'aya?." kanshi ya d'an d'ago cikin tok'k'oshi wuyanshi kan kafad'arsa cikin sanyi ya kalli Abba da Daddy murya a raunane yace. "Abba ina jiran Usman ne ! Abba inaso inga Usman ya samu mai kula dashi kafin nayi nesa dashi ! Abba in nayi aure yanzu wazai kula da Usman kaga baya son shan maganin shi kuma baya son bin dokokin doctors kuma kaga inba ana samishi idoba komai ya samu zaici, gashi ko yau saida yace min k'irjin shi na mishi nauyi." Sai kuma yayi shiru dan muryarsa da ta fara rawa, dan har cikin ranshi yake jin tausayin d'an uwanshi da yana da damar karb'awa Usman ciwon daya karb'a mishi. Abban ma shiru yayi tausayin 'yay'an d'an uwan nashi na ratsashi yana son Usman da Umar a ranshi fiye da yaran shi. Daddy ne ya d'an gyara zama cikin kallon Hajjajo da ta fara zubda k'ollah cikin k'arfin haki yace. "Farouq aure rahama ne meyasa kake ganin aure zai nesan taka da d'an uwanka Allah shike kula da Usman ba wayon mu ko dabararmu ba." Kai ya sunkuyar a hankali yace. "Daddy inajin tsoron barin Usman shi kad'ai dan baya son shan magani gashi dole dai in nayi aure zan koma cikin Damaturu da zama, Abba gashi bansan matar da zan auraba, gashi matan yanzu basa son dangin miji sai k'alilan ake samun masu son dangin mijin su, tayiwu nayi aure matar ta nuna bata son Usman yana rab'ata ko taga na fifita Usman a kanta har azo ta fara tunanin shiga tsaka nina da d'an uwana." Gaba d'aya parlour shiru sukayi cikin nazartan kalaman Hamma Umar tabbas matan yanzu k'alilan ke son dangin miji, kuma kamar yadda ya fad'a Usman tamkar yaro yake a gaban Umar, a hankali Abba yace. "Toh kai Farouq yanzu haka zakayi ta zama kenan?, ko dai auren ne baka so Farouq?." Kai ya jinjina cikin sanyin murya da tausayawa kanshi a hankali yace. "A,a Abba bawai auren ne bana soba! Abba ni bansan matar da zan aura bane , Abba ban san ya zanyi in samo matar da zata tayini kula da Usman ba." Sai ya kuma juyawa ya kalli Daddy da Hajjajo da take ta zubda k'ollah a hankali yace. "Ni da zan samu sai Usman yayi aure ya samu matar da zata kula dashi, in yaso daga nan sai na nemi auren, amman yanzu ina tsoron nayi aure nabar Usman gashi ni bansan ya zan fara neman auren bama bare na nemi wacce zata tayani kula da Usman." Gaba d'ayan su shiru suka yi kowa da tunanin dake ranshi. Cikin sanyi Abba yace. "Umar ba dai so kake ka auri matar da zata taya ka kula da Usman ba.?" Kai ya jinjina tare da murza yatsun hannun shi. Shiko Abba sai juyawa yayi ya fiskan ci d'an uwanshi Daddy kenan, Hajjajo kuwa shiru tayi cikin zurfin tunani... Su Ya Usman kuwa suna zuwa k'ofar gidan Anty Halima suka had'u da mijin ta zaije d'auko ta, ganin ya Usman ya dawo da ita suka gaisa, da mijin k'anwar tashi sannan suka juya shida Ummul suka nufi gida. Suna juyawa Ummul ta kalleshi cikin murmushi tace. "Yauwa ya Usman ya batun koyamin tuk'in ne? tun da muka fita sau 2 bamu kuma fitaba." Juyawa yayi ya d'an kalleta a fakaice yace. "Ke da kike da Mustapha ai shi zai koya miki." Baki ta d'an tura tare da cewa. "Wai ya Usman kaima ka tsani Mustapha ne kam? wai me yasa bakwa son bawan Allah nanne kam?." Baki ya d'an tab'e yace. "A,a Hajia ni bance ba, bance miki bana sonshi ba." "Toh ka koya min kaji ko Ya Usman na, Habeebi Katir katir." dariya yayi tare da cewa. "Allah ko Ummul kin rainani watoma Mustapha shine Habeebi da'iman ni kuwa Habeebi katir-katir na zama.?" murmushi tayi tare da cewa. "Ina sonka ya Usman dinnan." Murmushi yayi yace. "Allah d'aiyi ba." sai kuma sukaci gaba da dariya, suna cikin dariyar phone d'in Usman ya fara suwa a hankali yana d'agawa yaga Nuru ne, juyawa yayi ya kalli Ummul dake ta kiciniyar murza siterin motar tare da taima konshi, a hankali yace. "Ga lailamajanun yana kirana." Murmushi tayi tace . "Toh yauma zaku je zancen kenan?." Kai ya gyad'a mata tare da amsa kiran yana d'agawa Nuru yace. "Kai Gwanja ina kake ne? gani nazo gida Aliyu yace ka fita." Dariya yayi tare da cewa "Toh d'an anace naga jiya mafa kaje shine yauma zaka wani takura ni, toh yau nima na fara zuwa zance gani ga Baby na tana ta cemin, Ina sonka niko nace Allah d'ai yiba." Shiko Nuru tsaki yaja yace. "Kai da Allah ka same ni a k'ofar gidan su." "Toh" yace sannan ya katse kiran, hannu yasa ya d'an ture hannun Ummul dake kan nashi yana kallon titin yace. "Bari sai gobe zamu fita da rana zan koya miki yanzu muje in maida ke gida dan zanje gun Nuru inban jeba zaita damuna." "Toh tace sannan tace. " Ya Usman ina son fruits." Kai ya gyad'a sannan ya tsaya a gefen titin yaje ya saya mata sannan ya dawo suka tafi, a bak'in gate ya sauk'e ta da nufin zai juya, da sauri tace. "A a ya Usman zomuje na yanka maka fruits d'in kasha kafin ka tafi." "Ki bari sai na dawo." "A a wallahi ni dai kazo mu shiga inya so na gyara maka ka tafi dashi ko a cikin mota zaka ci." Binta yayi suka shiga cikin gida kai tsaye kitchen d'in Nenne suka shiga , gaban sink ta tsaya tare da wonke su tsab sannan ta jawo wata yar roba mai kyau ta zuba mishi, suna fitowa Aliyu ya kalli Ummul yace. "In anga kina kiciniya dai toh kinga kayan zak'ine, nanne za'aga k'wazon ki." "Eh d'in me ruwan ka da ni d'an sa ido kawai." Kitchen d'in ya shige yana cewa. "Uhum shazumami kawai kin iya shan zak'i kin iya yi mana kuka in cikin ki ya fara ciwo, kita b'are mana baki." Kanshi tayi da sauri zata kai mishi duka, shi ko zillewa yayi ya koma bayan Ya Adam dake harararta yace. "Ai gaskiya ce Aliyu ya fad'a kike wani fiffik'ewa ke zakiyi duka." Shi dai Ya Usman dariya yayi ya jawo hannun ta ya nufi parlour Hajjajo da ita yana cewa. "Ko Hamma Umar mai son kalota miki laifi bazaice fruits zai saki ciwon ciki ba, k'anwata sha abinki." ba tare da tunanin su Abba na cikan d'akin ba suka shiga tare da sallama. Suna shiga Hamma Umar ya d'ago kanshi fuska a tsuke ya d'an harari Ummul dake rik'e da Apple a hannun ta tana ci, baki ta tura tare da kauda kanta da sauri a ranta tana. "Mugu ko yaushe fuska a tsuke." Shi ko Usman cikin dariya yace. "Abba yau mitin kukeyi da Hajjajo da d'an jikinta a gefe ne." Kallon shi kawai su Abba sukayi zuk'atan su cike da alhinin irin son da Umar keyi mishi, shiko Usman ganin yadda suke zaune daga dukan alama magana mai mahimmanci sukeyi sai ya d'an zauna tare da gaida su, itako Ummul dama tuni ta fita ta tsaya a barandar ganin bai fito bane tace. "Ya Usman bari in kai maka robar cikin motar ko." "Toh muje nima gani nan zuwa." Juyawa tayi ta nufi harabar gidan nasu, shima yana gaida su ya fito yabi bayan ta, robar ta ajiye mishi sannan ta koma cikin gida, tana shiga Mustapha ya kira dan shaida mata ya isa lafiya, daga nan kuma sukaci gaba da hira, shi kuwa ya Usman wurin abokin shi Nuru ya nufa, A parlour hajjajo kuwa cikin zurfin tunani Abba yabi bayan Usman da kallo a hankali ya sauk'e ajiyan zuciya sannan ya kalli Hamma Umar cikin nitsuwa, shiko Hamma Umar kanshi ya sunkuyar, kai Abba ya juya ya fuskanci Daddy da Hajjajo ajiyar zuciya ya kumayi sannan cikin yanke hukunci yace. "D'an uwana Hussani da maifiyata Ku zama shaida a gareni na bada auren Ummul khairi ga d'an d'an uwana , na bada auren ta ga shi..... By *GARKUWAR FULANI* 棣冩憫棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 8閳拷 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳 *Fans na fatan alkhairi a gareni baki d'aya ina mai Baku hak'uri kwana biyu zaku jini shiru sakama kon tafiyar da zanyi gobe zanyi tafiya YOLA 2 KANO kuma biki zani ba damar yin typing sai Allah ya dawo dani lafiya ina barar addu'arku gareni* *INA kuke masoyan yan gaskiya Firdausi Sodaggi tare da Hassana d'an larabawa Wannan shafi nakune INA al'fahari daku* *TABITAL FULAKU group GARKUWAR FULANI group AYSHA ALI GARKUWA fans GARKUWA AYSHA&UMMEE novels tare da BANDIRAWO fans kun zamoni na zamo Ku Kusani kab groups na inajin daku kamar yadda kuke ji dani bani da kamarku a duniyar gizo-gizo棣冾檪棣冩棣冩* *"N*a bawa Umar auren Ummul khairi, ku sani na bashi auren ta na kuma yanke hukuncin za,ayi bikin nanda wani d'an lokoci domin aurar dasu ga juna shine mafita da zamu sama musu ." Daddy kam da Hajjajo kallon Abba sukeyi cikin jin dad'i Daddy sai murmushi yake yi ita kuwa Hajjajo kai take ta jinjina wa, gaba d'aya sai farin ciki ya cika zuk'atan su, Shi kuwa Hamma Umar tunda yaji furucin da Abba yayi, gaba d'aya yaji jikin shi na rawa gabb'an jikin shi kab kamar an sassare su, sai zufa yaji yana ketomai tako ina ido ya d'ago ya kalli iyayen nashi sai kuma atake yaji wata iriyar kunya mai tarin yawa ta rufeshi nauyin Abba yaji gaba d'aya ya kama shi, cikin tsananin kunya ya sunkuyar da kanshi k'asa yatsun hannushi ya rink'a murzawa tare da yin shiru sai bugun zuciyar shi da ya tsanan ta, Daddy ne ya kalli shi cikin kula yace. "Farouq kaji ta inda Allah ya kawo mana mafita ko?, tunda dama kai tunanin ka matar da zaka aura ta kasan ce mai tausayawa Usman ta taya ka kula dashi kar tazo ta rabaka da d'an uwanka, kaga a sauk'ak'e ita Ummul yar uwarsa ce kuma ko yanzu tana kula dashi." Shiru yayi bai d'ago ya kalli Daddy ba sai gyad'a mishi kai yakeyi, haka yasa Abba ya zuba mishi ido cikin kula yace. "Farouq." Shiru bai amsa ba sai gyad'a kai ya kumayi alamar amsawa, shima Abba kai ya jinjina tare da k'ara kiran shi a karo na uku yace. "Farouq." Jin Abban nata jerama mishi kiran yasa ya d'ago kanshi kad'an cikin raunin murya yace. "Na'am Abba." a hankali Abba yace. "Farouq d'ago kanka ka kalleni." Kai ya jinjina a hankali ya d'an kalli k'anin mahaifin nashi, sai ya kuma yin k'asa da idanun shi, kafad'an shi Abba ya dafa murya a tausashe yace. "Farouq kai da banne a cikin yaran mu kowa da halinsa kowa ana fahimtar ina ya dosa amman kai haka Allah ya halicce ka kana da zurfin ciki ba'a gane abin da kake so da abinda baka so kuma bakin ka baya furtawa, toh ka sani duk da haka bazan cutar da kaiba, dan kafin ka zama maraya mu muka zama marayu kuma d'an uwanmu Abbanka shi ya zame mana uwa da una bai regemu da komai ba yakan hak'ura da farin cikinsa dan ya sama mana farin ciki, haka zaisa Farouq bazan k'untata rayuwar kaba, yadda Ummul take y'ata haka kaima d'anane jininane ni da maifinka uwa d'aya uba d'aya Farouq ina sonka son da bana yiwa y'ay'an cikina, Farouq ni ubane a gareka kuma aboki kuma amini kuma mashawarci, Farouq bazan yimaka doleba sai da son ranka karkaji kunyar shaida min baka son Ummul in har baka sonta ka gaya min ,dan bazan yimaka auren cusheba bare na dole, ka furta min kana son Ummul? ko baka sonta?." Kai ya rink'a jujjuyawa yana sauk'e numfashi a ranshi yake juya kalaman Abba a fili kuwa cikin raunin murya yace. "A,a A,a Abba a,a ba kaina nake tunawa ba , Abba Ummul bata sona, ko cikin yayunta ni da ban ta d'aukeni kuma gashi tana da wanda take so, Abba me za'a cewa Mustapha? Ummul da Mustapha nake tunawa kar sanadi na a cutar dasu hakan zaisa Ummul ta k'ara tsanata bana son na zama bak'in jakada a Rayuwar Ummul da Mustapha." Sai kuma yayi shiru yana murza yatsun sa tare da kamo lips d'in shi na k'asa yana d'an ciza. Abba da Daddy kuwa ido suka zuba mishi yayin da Hajjajo kuwa gaba d'aya take kallon shi da suffar maihaifinshi , Umar Faruoq shi haka Allah yayi shi baya son shiga hakk'in kowa . Kai Abba ya jinjina sannan yace. "Farouq amsa min tabbaya ta, shin kana son Ummul ? ko baka sonta?." Kai ya k'ara sunkuyar wa cikin cushewar tunani a ranshi yake tuna. "Abba ya zanyi in kalli tsabar idanun ka nace bana son y'arka ta cikin ka?." A zahiri kuwa kai ya girgiza murya a raunane a hankali yace. "A,a Abba ya zanyi ink'i y'ar uwata." Nannauyan ajiyan zuciya Abba ya dire sannan ya kalli Daddy cikin jin k'arfin guiwa da kara yace. "Hussaini ina nemawa d'ana Umar Faruoq auren d'iyar mu Ummul." Murmushi Daddy yayi tare da yin hamdala yace. "Na bada auren Ummul ga d'ana Umar Faruoq." Hajjajo ko murmushi tayi da hamdala sannan ta sanya alkhairi a acikin abin, shi kuwa Hamma Umar kai ya d'ago a hankali yace. "Abba nagode Daddy Allah ya biyaku." Da sauri Abba yace . "A a Farouq godiya kuma a tsakanin mu ai nauyin mu ne mike sauk'e wa." Kai ya kuma sunkuyar wa murya a raunane yace . "Abba ya za'ayi da Mustapha? Abba me za'acewa Mustapha? Abba ya Ummul zata d'auke ni?." Gyara zama Daddy yayi sannan a nitse yace. "Farouq wannan magana bamu gaya maka itaba har saida mukaje muka samu iyayen Mustapha mu kayi misu bayanin Ummul zamu bada ita ga d'an uwanta, Alhamdulillah iyayen Mustapha masu mutun cine sun fahim cemu inda anan take suka kira Mustapha a gaban mu akayi mishi baya ni, tabbas Mustapha yana son Ummul kuma ita tana sonshi d'an Mustapha ya san haka d'an tunda mahaifinshi ya mishi bayani Mustapha kuka yake tamkar yaro, Amman kuma hakan bai hanashi ya fahimci abinda mik'e nufi ba, d'an haka yace , yaji kuma ya yarda amman don Allah kar a hanashi zuwa gun Ummul tunda ba'asan Rubutaccen AL'AMARI da zai wakana ba yace zaici gaba da neman ta in ita rebonshi ne zaka bar mishi ita, haka yasa yake zuwa gunta har yanzu kuma munce karya gaya mata yakuma yarda munkuma ce ya rege kiranta da zuwa duk ya yarda." Allah sarki Umar Faruoq mai sadaukar da farin cikin sa ga wani gaba d'aya sai yaji ya tsani kanshi dan yanaga ya shiga hurumin wasu ya tsaga soyeyyarsu, gaba d'aya jikin shi ya mutun a haka suka tashi taron su, Daddy ya tashi ya koma gidan sa shi kuwa Abba yayi part d'in sa a parlour shi ya samu Nenne tana zaune rik'e da carbi hankalin ta na kan tv tana kallon tashar sunnah tv, zama yayi gefen ta cikin sakin fuska da halin girma ya kalleta tare da cewa. "Khadija rege sautin tv nan akwai maganar da zamuyi." cikin girmamawa ta rege sautin sannan ta juyo gareshi cikin nitsuwa tace. "Fatan alkhairi." kai ya jinjina cikin girma da isa da gidan shi ya shaida mata yadda sukayi da y'an uwanshi kab. sannan ya d'ora da cewa. "Kinji hukuncin da muka yanke." shiru Nenne tayi cikin zulumin abinda zai biyo baya a hankali kamar cikin rashin fahimta tace. "Umar ko Usman?." cikin zuba mata ido yace "Umar dai ba Usman ba ko kina da magana ne?." Kai ta juya yayin da idanun ta sukayi tab da k'olloh cikin sanyi tace. "A a me zance ba komai sai fatan Allah ya sanya alkhairi Allah yasa sanadin haka zumunci ya k'ara k'arko." sai kuma tayi shiru sannan tace. "Lallai Mustapha yayi halin kirki, sai kuma ita Ummul." Cikin kula Abba yace. "Ummul kam ai dole tabi umurni na." Kai Nenne ta gyad'a tare da tarin zulumi. Daga nan sukaci gaba da hirar yadda bikin zai kasan ce. Shi kuwa Hamma Umar su Abba na fita ya koma kan 3 str ya konta yayi shiru tafin hannushi yasa ya rufe fuskar sa, gaba d'aya zuciyarshi ta cushe ta cika da tausayin Mustapha da Ummul shi kam gani yake tabbas ba'ayi musu adalci ba, d'aya rumtse idonshi sai ya rink'a ganin yadda Mustapha ke kallon Ummul zuwanshi na k'arshe, Hajjajo ce ta matso shi gefen shi ta zauna a hankali tace. "Umaruh Farouqu farin cikin ka iyayen ka ke bid'a shi yasa suka yanke wannan hukuncin da su sama maka dad'in rayuwa, ba k'inka sukeyi ba." ido ya d'an bud'e sannan yace . "Na sani basa nufin cutar dani." daga nan kuma ya mik'e jikin a mace yace. "sai da safe." "Allah bamu alkhairi." Part d'in su ya nufa yana zuwa ya samu Usman yana konce sanyi da 3qtr shi a jikin shi matso shi yayi a hankali ya kalli B'iyayen nashi ganin yayi bacci ne yajawo blanket ya rufeshi, sannan yayi addu'a ya shafa mishi sannan yaje yayi wonka yayi al'wala yazo suka konta.. A hankali Abba ya kammala shirye-shiryen auren Ummul da Umar hatta kayan d'akin Ummul Abba ya had'o mata a saudia ba abin daya rege, abin mamaki shi kam Hamma Umar daga ranan basu kuma maganar dasu Abban ba, Abin da ke bashi mamaki kuwa hatta kayan d'akin an kaishi gidan da yake zama a damaturu cikin gida jen ma'aikatan an shirya komai tsab ba abin da ya rege da bobu a gidan hatta kitchen d'in an shirya komai tsab. Ita ko Ummul duk abinda akeyi bata da labari, shak'uwa tsakanin Hamma Umar da Usman kuwa kullum k'aruwa yake Hamma Umar sam baya yarda ya kwana a damaturu yana tashi daga office nashi zai kama hanyar potiskum, Ummul da Mustapha kuwa suna soyewa son ransu shima Mustapha har manta maganar su Abba yakeyi wasu lokutan. Yau jumma tun da safe Ummul ta tashi da ciwon cikin da mararta kad'an-kad'an, haka yasa bata samu tayi aikin da Hamma Umar ya k'indaya mata ba, shi kuwa Umar Faruoq tun da sassafe ya shirya tsab shida Usman tea kawai suka d'an sha sannan suka fita a tare Usman ya nufi wurin aikin shi shima Hamma Umar ya nufi cikin damaturu, kasan cewar ya jumma'ace aikin ba yawa sosai. 11:00 Am kiran Adam ya shiga woyar Hamma Umar d'in, yana d'agowa yace. "Adam ya akayi ne?." "Yauwa Hamma Umar dama Abba ne ya aikoni da masu gyaran labulaye yace a canza labulayen toh munzo kuma baka gida gashi gidan a rufe." "OK gani nan zuwa yanzu ku jirani kad'an bari in k'arisa aikin dan tare zamu koma cikin potiskum d'in." "Toh" yace sannan suka koma cikin mota suka zauna. Jimawa k'adan Hamma Umar d'in ya iso ya bud'e musu gidan nashi suka shiga , a take su Abdul suka canza labulayen gidan kab sannan suka kimatsa komai suka shimfid'e carpet masu lau shi da taushi gaba d'aya gidan ya d'auki k'amshin da shek'i ga k'amshin sabon penti ga k'amshin sabbin kayan d'akin ga k'amshin kasan cewar Hamma Umar ma abocin tsabta da k'amshin ne komai yayi ras sai shek'i da k'amshin yake zubawa, shi kam Hamma Umar yana tunanin me Abba yake shirin yi tunda yasan har yau Ummul bata san da zancen ba haka dai ya bar abin a ranshi tunda shi bashi da yawan magana, su Abdul na gamawa suka d'auki hanya tare da Hmma Umar.. Suna zuwa gida sallan jumma'a suka tafi, Bayan an taso masallacin ne Dr Umar ya wuce chemist d'in shi, Abba kuwa da sauran gida suka dawo, Itako Ummul zuwa yanzu ciwon cikin ta ya fara tsananta, tana zaune a parlour Nenne tana d'an juya kai Aliyu ya shigo parlour kallon ta yayi cikin kula yace. "Sannu Anty Ummul ko inje in kira Hamma Umar ne?." a d'an wahalce ta harareshi tace. "Barni in mutun." Dariyan tsokana yayi sannan yace. "Kije Abba na kiran ki." Da sauri ta d'an zaro ido gami da dafe k'irji cikin tsoro tace. "Ni? da gaske Abba na kirana?." "Ehh wallahi da gaske ne, toh menene dan Abba ya kiraki ji yadda kike zaro ido." "A a wallahi Aliyu Abba baya kirana ko batun makaran ta ne Nenne yake gayawa ta gaya min, ni dai naji tsoron kiran nan nashi." "Toh koma dai menene kije maji daga baya." cewar Aliyu kenan. A bak'in kofar parlour Abban ta tsaya tare da yin sallama , Daddy ne ya amsa tare da cewa . "Ummul na shigo." Kai ta sunkuyar cikin jin tsoro ta shiga a hankali can gefen Daddy ta zauna yayin da zuciyarta ke luguje, a hankali ta gaida su, sannan tace. "Abba Aliyu yace kana kirana." Kallon ta yayi cikin k'aunar y'ar tashi a hankali yace. '"Ehh ina kiran ki." Sai kuma duk sukayi shiru, can dai Abba yayi gyaran murya tare da cewa. "Ummul ni wayene a gareki?." Kai ta d'ago cikin k'arin firgici a hankali tace. "Mahaifina." Kallon ta ya kumayi sannan yace. "A duniya bayan mahaifi yarki akwai wanda ya fini sonki?." Baki na rawa tace. "A,a babu." "Na tabbatar kina da sanin cewa shariya ta bani damar zab'a mik'a majin aure ko." "Ehh." ta bashi amsa hawaye na bin fuskarta. Shi kuwa gyaran murya yayi sannan yace . "Abin da ban saniba ko zaki iya min biyeyya kan zab'in da nayi miki." Zuwa yanzu kam ta k'asa magana sai kai take gyad'a wa tana wasa da yatsun ta. Cikin bada umurni Abba yace. " toh nayi miki miji, kiyi biyeyya a kanshi ko bana raye shine mijin ki, mahaifiyata da d'an uwana sune shaida, na bada auren ki ga d'an uwanki Umar Faruoq." Kalaman Abba sun maida Ummul kurma sun sata wani irin razani da firgici gaba d'aya jikin ta rawa yakeyi bugun zuciyar ta kuma kamar zai b'allo ya fito woje kunya yayi mata wani irin nauyi cikin rawan baki tace. "Hamma Umar Faruoq?." Kai Abba ya gyad'a mata tare da cewa. "Ehh shi d'in dai." Hannu tasa cikin tsoro ta kama kanta ta bud'e baki zatayi magana Abba ya dakatar da ita cikin tsuke fuska yace. "Tashi ki tafi bana buk'atar jin komai daga gareni ba shawara bace umurni nane wannan." Tanaji Abba na cewa tashi Amman ta k'asa ko d'aga yatsarta, sai da taji ya zuba mata tsawa, cikin firgici ta mik'e ta fita , tana fita kai tsaye part d'in Nenne ta ta nufa , tana zuwa a parlour ta samu su Ya Usman su ya Adam ya Sadik da Aliyu kai tsaye cikin bedroom ta shige, Usman na binta da kallon ganin yadda take a firgice. Tana zuwa ta zauna gefen Nenne dake kan sallaya cikin wani irin yanayin ta kifa kanta kan k'afafun Nenne cikin cushewar sauti ta saki wani irin galabaicen kuka mai cike da tausayi kuka takeyi mai tsuma zuciyar mai sauraro kukan take da sauti, Nenne kam tana ganin haka tasan me yasa ta kukan gaba d'aya sai zuciyarta ta cika da tausayawa y'ar tata, su Ya Usman kuma suna jin kukan da takeyi cikin sauri suka shigo d'akin , cikin tarin tausayawa Usman ya zauna gefen ta baki na rawa yace. "Ummul meke faruwa? meya sameki? meke miki ciwon?." Ba amsa sai kukan da takeyi, Nenne kuwa tsuke fuska tayi cikin fad'a tace. "Ke ni tashi a kaina tunda abin naki iskanci ne ana miki magana kina kukan banza bazan kiyi magana ba." Cikin kuka mai cushe zuciya ta d'ago kanta baki na rawa tace. "Wayyo Allah wayyo Nenne kiji abin da Abba yace min Nenne wallahi ina son Mustapha ina sonshi yana sona dan Allah Nenne ki bawa Abba hak'uri wallahi ina son Mustapha." Wani irin dogon tsaki ya Adam yaja cikin buga mata tsawa yace. "Ai Mustapha yafi miki kowa a duniya tunda har kike kuka da umurnin Abban mu, ni wallahi kin saman na k'ara tsanar sa." Juyowa tayi cikin kuka tace. "Ya Adam kasan da waye Abba zai had'a ni?". A hatsala yace. " Na sani mana kuma yafi Mustapha da komai." Cikin kad'uwa da bugawar zuciya Ya Usman ya kalleta tare da cewa. "Waye za'a had'a ki dashi?." Kuka ta saki tare da cewa. "Ya Usman waifa Abba da Hamma Umar zai had'a ni aure." Ido Usman ya zaro cikin wani irin yanayin yayi wani irin..... By *GARKUWAR FULANI* 妫e啯鎲#鍐ㄧ3妫e啫纾虫#鍐ㄧ3妫e啫纾虫#鍐ㄧ3妫e啫纾虫#鍐ㄧ3妫e啫纾� *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 9闁愁煉鎷� *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 妫e啫纾虫#鍐ㄧ3妫e啫纾虫#鍐ㄧ3妫e啫纾虫#鍐ㄧ3妫e啫纾虫#鍐ㄧ3妫e啫纾� *Alhamdulillah ala kulli halin nayi tafiya lfy na dawo lfy yanzu zanci gaba da typing insha Allah har k'arshe* ```NI na jinjina muku y'an KADUNA bamai rabani daku jama'ar KANO kui hak'uri ga shafinku ya iso mun jinjina muku reedars damu writers daku d'ayane bamai rabu daku sai Allah kui hak'uri ga pagenku ya fito kanawa sunce mini GARKUWAR a baya kinyi wani kuskure duk novels da kinkayi a social media dad'in su yayi ta kewaya nahiya sun shiga sak'ok'in Nigeria shin meyasa kika ware hausawa bakya yin novels da su sai FULANI? Hausawa ne sukayi min wannan tabbayar shaidar suna k'aunata gaba d'aya, NIKO NACE MUSU , dole naje duk inda rebo yake dan bani Rena masoya na kuma ban raina ranar da novel yayi mini ta sanadi an sannu garuruwa INA alfahari da Gombe Taraba ADAMAWA YOLA gida nake tun fari su sukayi mini GARKUWA妫e啯顫� tunda nazo a cikin y'ay'an Adam duk ajizi an sanshi da kuskure kuyi hak'uri novelna na gaba da hausawa yana nan tafe, dan ni garin mosoya nisa bai mini da na fad'a kuma yanzu ina tuni Allah ya kaddara in zamto Zuma dana fito ai tayi mini sansani, yau hak'uri zan bawa hausawa dan sunfi so na tsaya tamkar gini, RABBI nufeni silar novel da zanyi mutan k'asarmu su zauna lfy, Forko mutan KANO zanai kira wanda fagen nema basa jira maza da mata Manya da k'ank'ana a gsky na sansu da Hattara sunce nazo naga yadda abin yake sannan na tabbaya ni sukayi jira na mori so da k'aunar da suke mini sannan sunce na dage fannin k'irk'ira妫e喚妾#鍐╊潰Kanawa wannan shafi naku ne``` *Y*ayi mata wani irin kallo cikin tarin mamaki da jin zafi a ranshi murya can k'asa yace. "Ummul duk wannan kukan kina yinshi ne dan an had'a auren ki da Hamma Umar? Ummul duk wannan zafi da tarin bak'in ciki dan an shigar da Hamma na cikin rayuwar ki ne kike haka?." Sai kuma yayi shiru tare da dafe k'ahon zuciyarshi a hankali cikin jin jiri ya koma baya kad'an ya zauna ido ya rumtse da k'arfi sannan ya jingina da jikin gini, numfashi ya rink'a furzarwa da sauri-sauri yana mai cushewar tunani. Ita kuwa Ummul cikin kuka tace. "Na tsaneshi na tsani Hamma Umar bana sonshi duniya da lahira ko fuskar sa bana k'aunar gani, Hamma Umar ba abinda yake jazamin a rayuwa sai bak'in ciki ya zame min bak'in jakada a rayuwa ta." K'ara ta saki da k'arfi tare da dafe fuskar ta jin wani irin zazzafan mari da ya Sadik ya zuba mata cikin huci da zafin rai ya nunata da yatsa murya a hargitse yace. "Ki kula kisan furucin da zakiyi ki san waye Hamma Umar wallahi a kanshi zamu iya miki komai, shi Mustapha ko tare kuka fito duniya bake ba shi." Kife kai Ummul tayi a bakin gado ta saki wani irin kuka mai cike da zafi a zuciya kuka mai cushe zuciya gaba d'aya jikin ta sai b'ari yake lokaci d'aya ciwon mararta da ciki da k'ugunta suka taso a tare, kuka take cikin tausayawa kanta da Mustapha. Gaba d'aya sukuwa shiru su kayi cikin jin sautin kukan ta, ya Usman ne yake tunani a ranshi tabbas Ummul akwai kuna a ranta akwai zafi da ciwon rabuwa da masoyi, sannan ga cushen mak'iyi da akayi mata, har cikin ranshi yake tausayawa mata, a sashin zuciyar shi kuwa, yana jin zafi da bak'in ciki da takaici yadda Ummul ta tsani d'an uwanshi mafi soyuwa a gareshi. Nenne kuwa itama shiru tayi tana jin sautin kukan y'ar tata har cikin ranta take tausayawa mata, amman a zahiri tafi jin dad'in auren Ummul da Umar akan ace da Mustapha dan ita Nenne tana son Umar da Usman tamkar yayanta na cikinta bata son abinda zai b'atawa Usman rai da yanayin ciwon sa bata k'aunar taga damuwa a fuskar Umar dan shi jigone mai burin samawa kowa farin ciki shi baya shiga sabgar daba tasaba, shi ba a gane matsalar sa dan ba fad'a zaiyi ba duk halin da yake ciki dan shi mutun ne mai kunya da zurfin ciki da kara da kawaici shiyasa bata son abinda zai cutar da Hamma Umar d'in, haka yasa take ji a ranta dole zata iya juya d'iyarta tayi mishi biyeyya. Ya Adam kuwa wata iriyar kunyace ta rufeshi ganin yadda a gaban Usman Ummul ke kuka kamar ranta zai fita dan an hada ta Aure da Hamma Umar, kunya yake ji ya Ummul zata nuna bata son d'an uwan shi alhalin shi a koda yaushe cikin nuna mata kulawa da gata yake. Ya Sadik har cikin ranshi yake jin tsanar Mustapha tunda a kan Mustapha ne Ummul take furta kalaman k'iyeyyar Hamma Umar d'in nasu haka kuma yake jin zai iya yiwa Ummul ko wanne hukuncin matuk'ar zatayi wa Hamma Umar d'in rashin da'a. Auta Aliyu kuwa abokin fad'in Ummul kuma kaninta mai tausayawa mata ganin yadda take kuka ba wanda yake lallashin ta gashi dama ya Usman ne mai kareta kuma yau shima fad'an ya shafeshi, kawai shima Aliyu sai hawaye yake zubda wa a hankali ya matso kusa da Ummul d'in murya na rawa yace. "Ayyah Anty Ummul kiyi hak'uri kibar yin kukan haka." Cikin tausayawa kanta da kanta ta fad'a jikin Aliyu kanta ta kife kan cinyar shi ta saki kuka mai cushewar sauti, shima Aliyu sai hawaye car-car yana jin tausayin ta a ranshi, cikin kuka tace. "Aliyu yau kowa baya sona duk an tsanani sabida Hamma Umar ! sannan an rabani da Mustapha sabida Hamma Umar ! Auta kalli yau ya Usman ma fushi yake yi dani sabida Hamma Umar! kalli ya Adam da ya Sadik ji suke kamar su kashe ni sabida Hamma Umar! Abban mu da Nenne duk basa sona a yau sabida Hamma Umar! Aliyu ba wanda ya tausayawa min sai kai." sai kuma ta saki wani sabon kuka. Ya Adam ne yayi kanta cikin nunata da yatsa murya a fad'ace yace. "Kifa dena cika mana kunne da kuka wallahi in ba hakaba zan tattakaki." Ya Sadik kuwa tsaki yaja cikin zuciya yace. "Kiyi duk yadda kika ga dama ya rege naki tunda bakya ganin alkhairi zab'in da iyayen mu suka yi miki, Mustapha ne dai bazamu bashi auren kiba." Daga nan suka fice ita kuwa Nenne tsaki taja ta fice ta shiga kitchen ta kama aikin ta, Aliyu kuwa tafin hannushi yasa yana gogewa Ummul d'in k'olloh dake bin fuskar ta, shi kuwa ya Usman zama yayi kusa da Ummul d'in daketa murk'ususu tana ta cike lips d'in ta zufa na keto mata tako ina sai kukan da takeyi cikin raunin da wahala. A hankali ya kalleta cikin sanyi ya d'an yi murmushi yace. "Ummul khairi banyi fushi da keba , ki sani ke tawace kamar yadda Hamma Umar yake nawa ni Usman Ku duk nawa ne ba Wanda zank'i a cikin Ku kiyi hak'uri k'anwata kiyiwa kanki da Hamma na addu'a Allah ya muku zab'in abinda yafi zamewa alkhairi a gare Ku." Kai kawai ta juya tana mai azabtuwa da ciwon cikin da tarin damuwa. Shi kuwa Usman haka yayi ta bata baki , Amman ina Ummul bata ma san yana yiba, ganin haka yasa. Usman ya fita kai tsaye parlour Hajjajo yaje, cikin sanyi yayi mata maganar abinda ke faruwa, kai ta d'an jinjina cikin k'arfin guiwa ta kalli Usman tace. "Ku kanta na d'an wani lokacin ne zatayi ta bari ta saduda ta zauna da Umaru cikin aminci, aini naji kukan nata zuwa ne bazan yiba, dan inta ga ana damuwa da kukan nata dayin lallashin ta toh bazata bariba ku fita sha'anin ta." Ido ya tsurawa Hajjajo cikin sanyi yace. "Hajjajo indai Hamma Umar na son wannan had'in toh ina farin ciki da auren nan domain farin ciki B'iyayen na shine nawa." Haka suka d'an tattauna kan zancen. Itako Ummul tunda suka waste suka barta take kuka kamar zata had'iyi zuciya ta mutu, Aliyu yayi ta lallashin ta amman ina dan abin ya had'e mata ga ciwon ga bak'in ciki, haka Aliyu sai ya fito yaje kitchen ya dawo gunta yana ta sintiri ya kasa zama. Haka har dere yayi Nenne kam ko ta kanta bata kuma biba dan inta tsaya kusa da ita tana jin tausayin d'iyar tata, ta dai sa abinci Aliyu ya kawo mata, ita kuwa Ummul yau abincin bazai ciwuba. 9:00 pm har yanzu Ummul tana kuka ne hannun ta dafe da mararta da k'ugunta akaro na biyu Aliyu ya shigo cikin tausayawa yace. "Ummul naje na gayawa Nenne baki da lafiya Abba kuma yace kije gun Hamma Umar ya duba ki." Kai ta kuma kifewa kan kago ta ci gaba da kukan da sautin shi baya fita dan muryar ta ta dashe, Ya Adam ne dake zaune a parlour Nenne jin Abinda Aliyu ya fad'a yasa shi mik'e wa ya shigo bedroom d'in cikin tsuke fuska da bada umurni yace. "Ke mike kije Hamma Umar d'in ya duba baki, kin zauna kin wuni kuka shin kukan zai miki magani ne? ki mik'e ko nace." Cikin kuka dabin umurnin mahaifin nata da Yayan nata da tsoron ya Adam d'in ta mik'e cikin wahala hannun ta damk'e da mararta ta fice tana kuka, kuma Ita da kanta ta san in Hamman ya mata Allurar tana jin sauk'i, cikin kukan ta nufi part d'in su Hamma Umar d'in. Shi kuwa Hamma Umar duk kukan da Ummul keyi yana ji dan lokacin da tafara kukan yana parlour Hajjajo jin kukan yayi yawane gashi yaji bala'in da su Adam ke mata yasa ya zame jikin shi ya dawo parlournsu cikin sanyi jiki ya konta kan kujera yasa tafin hannushi ya rufe fuskar sa, zuciyar shi cike da tausayin Ummul , yana koncen yaji sautin kukanta a hankali yana ratsa parlour cikin rawan murya yaji tana sallama, ido ya lumshe cikin jin zafin kukan da takeyi ga kunyar da ta rufeshi, a hankali ya amsa mata sallamar, Ita ko da zuwa yanzu ko tsawonta bata iya mik'ewa, a sunkuye ta shigo parlour hawaye cike a fuskar ta da tayi jazir da kuka ida nunta duk sun kumbura, a hankali ta durk'usa gaban kujerar da yake konce cikin kuka da rawan murya tace. "Abba yace inzo kamin al..! alluran da kake min." Shiru yayi zuciyar shi cike da tausayin ta gaba d'aya yake jin haushin kanshi tunda sana dinshi take irin wannan kukan. Ita kuwa ganin bai kulatan ba ta saki kuka mai cike da raunin gaba d'aya jikin ta rawa yakeyi, jin yadda take kukan ne ya mik'e cikin sanyi bedroom ya shige yana zuwa ya had'a allurar, sannan ya dawo parlour yana zuwa gabanta ya k'afa guiwowin shi a k'asa kan carpet suna fuskan tar juna, kanshi a sunkuye yasa hannushi ta bayan ta a hankali ya murza siket d'in atampa dake jikin ta, ita kam Ummul ido ta rumtse da k'arfi zuciyar ta cike da tsanarsa a ranta, fuskarta ya d'an kallah sannan ya zira bakin allurar a cikin jikin ta, k'ara ta saki cikin kuka da zafi ta fad'a jikin shi. Ido ya rumtse da k'arfi sannan yasa hannushi d'aya ya matso ta cikin sanyi da raunin murya yace. "Kar kiyi inji miki ciwon ki nitsuba ba zafi." kuka ta kuma fara cikin dashewar muryar, shi kuwa idoya lumshe sannan ya k'ara saita allura a hankali ya rink'a cusa ruwan a jikin ta, yanayi a hankali yana ce mata . "Sorry." Ita kuwa jin zafin yadda ruwan ke ratsata yasa ta ya matso shi ta rik'eshi gam, yana gamawa ya zare allurar sannan a hankali ya tureta baya ya janye jikin shi, ya mik'e kenan ya kalli Usman dake dafe da bak'in k'ofa ya zuba musu ido sai kallon suyake cikin wani irin yanayi. Ita kuwa yana tureta ta mik'e cikin jin jiri ta ratsa gefen ya Usman d'in ta wuce. Tana fita Hamma Umar ya kawo hannun Usman d'in cikin tsantsar kulawa , kan kujera ya ajiye shi sannan ya d'auki maganin shi yazo ya bashi yasha, a hankali yace. "Usman gobe zamuje gun Ammin mu." murmushi Usman yayi sannan yace. "Toh Allah ya kaimu." "Amin" yace sannan suka she ga bedroom d'in a tare sukayi shirin baccin su. Washe gari da safe bayan sun gama shirin su tsab sannan suka shiga cikin gida a parlour Nenne suka zauna bayan sun gaida Nenne suka fito parlour Hajjajo suka wuce suna zuwa Hamma Umar d'in ya shiga kitchen d'inta da niyar zai d'auki cup, Sai kuma yayi baya a hankali ya tsaya a bakin kofar yana jin abinda Ummul ke fad'a, ya Adam da Hajjajo dake bayan kitchen d'in ma suna jin abinda take fad'in ta window ita kuwa cikin sanyi taci gaba da cewa. "Nayi alk'awarin har Abadan..... By *GARKUWAR FULANI* 棣冩憫棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 棣冩晸 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳棣冨磳 *'Yan KADUNA duk Nisan da nayi musu Amman dani sai al'fahari suke in sunga novel na ko a fushi suke farin ciki gurbi nasa zai shige da zana jeni mu zauna so suke basu da niyar tsigen fiffige,棣冩嫅棣冨編棣冾檪棣冩 da gaskiya nunan k'auna suke dan sun kirani sunai mini magiya, na jinjina muku mutan Kaduna domin kuna da karamci hakan yasa na sadaukar da wannan page a gareku* *C*ikin kuka murya na rawa tace. "Habibi Mustapha nayi ma al'kawarin ni taka ce har Abadan bazan bari wani yayi nasarar rabamu ba, nayima alk'awarin zan adana maka kaina zan killace maka jikina ba wani mahaluk'in da zai zama hijabi a tsaka nin mu." Sai kuma tayi shiru tare da sheshshek'an kuka murya na rawa tace. "Hamma Umar zai rayu cikin bak'in cikin rayuwa tunda har ya kasance a sanadin shi za,a rabamu , bazai sake samun farin ciki da konciyar hankali ba gidan shi zai zame mai tamkar kurkuku zai rayu cikin k'unci da bank'in ciki ta yadda shida kanshi zai sauwa k'amin ba tare da neman shawarar kowa ba, Mustapha tun jiya duk wani tsoron Hamma Umar ya fita a raina na tsaneshi ji nake kamar na kashe sa." Sai kuma ta saki kuka mai sanyin sauti, shi kuwa Mustapha lallashin ta yake cikin raunin murya yake cewa. "Kiyi hak'uri Ummul ki daina kuka ki sani har Abadan kina cikin raina bazan dena sonki ba, amman kuwa duk yadda nake sonki bazan so sanadi na ki sab'awa iyayenki ba, Ummul kiyi biyeyya ga mahaifan ki." Cikin raunin tace. "Mustapha zanyi biyayya ga iyayena amman bazan yi biyeyya ga Hamma Umar ba zan d'and'awa zuciyarshi bak'in ciki mai tarin yawa sai yaji irin d'acin da ya jiyar dani, tabbas sai zuciyar shi ta raunatu jinin shi sai ya hau hankalin shi bazai sake konciya ba." Haka ta rink'a fad'in irin uk'uba da cin fuskar da ta tana darwa Hamma Umar d'in yana jinta, Hajjajo kuwa da ya Adam bushewa sukayi suna kallon juna cikin jin tsoron furucin Ummul d'in da mamakin yadda take k'ok'ari da niyar cusawa bawan Allah bak'in ciki. Shi kuwa Hamma Umar a hankali ya juya cikin sanyi fuskar sa a raunane lips d'in shi ya kamo ya ciza cikin jinjina kai ya juya ya fita, a parlour suka had'u da su ya Adam da Hajjajo cikin mamaki ya Adam ya kalleshi ganin daga kitchen d'in ya fito ita Hajjajo kallon shi take, shiko ganin kamar zasu zargi wani abu yasa ya d'an yi murmushi cikin yanayin sanyi ya gaida Hajjajo sannan ya kalli Usman dake tsaye gefen Hajjajo yana mik'a mata hannun shi da alamar ta d'aure mai agagon hannushi , Ita ko sai kiciniya take ta kasa, matso su yayi cikin sanyi ya matso ta ya d'an bugi k'eyar Usman cikin kula yace. "Kai komai baka iyaba agogo ma bazaka iya mak'alawa ba sai da taima kon tsohuwa." Murmushi yayi yace. "Toh Hamma Umar ai kaine ka b'atani haka komai kace bazan iyaba banda lafiya kai zaka min." Dariya sukayi baki d'aya shiko Umar murmushi yayi daga nan suka sallami Hajjajo suka fita suka tafi kai tsaye dicency super market suka wuce suna shiga suka yiwa Ammin su shopping komai na buk'atan rayuwa suka had'a mata kamar yadda suka saba, daga nan gidan su Ammin su suka nufa. Suna isa bakin gate ko parking Hamma Umar bai k'arisa yiba, Usman ya b'alle marfin motar cikin jin dad'i da raha ya d'an d'aga murya yana. "Ammi ! Ammina ! Ammiiiiii ! Ina kike ne?." Shi kuwa Hamma Umar murmushi yayi ya juya gun mai gadin ya mik'a mishi key d'in motarsa cikin sanyi yace. "Isah shigo da kayan cikin gida." cikin mutuntawa Isah ya karb'a, sannan shi kuma yabi bayan Usman d'in. Ita kuwa Ammi tunda tajiyo muryar Usman tayi wani irin murmushi mai cike da jin dad'i da k'aunar y'ay'an nata, ido ta lumshe tare da shak'ar kanshi turaren da ta sani na Hamma Umar ne, dan shi kafin ya isa wuri turarenshi keyin sallama. Kai ta jinjina tare da ture y'ar roban da ta k'wab'a lallen gargaji da nufin zatasa a k'afafun ta, tana k'ok'ari tashi taga Usman har ya iso, kawai sai ta koma ta zauna cikin yin dariya, cikin happy tace. "Lale marhabin da yaran kirki yara na gari y'an albarka abin alfaharin Ammin su." Da sauri ya k'arisa gaban ta cikin k'aunar mahaifiyar tasu ya zauna gaban ta , hannu ya mik'a mata itama hannu ta mik'a mishi sukayi musabaha, sannan ya zame gefen ta cikin lumshe ido da yana yin shogoba ya konta a hankali ya d'aura kanshi kan cinyarta tare da sauk'e ajiyan zuciya murya a tausashe yace, "Ammina ina sonki' Ammina munyi kewar ki." Kanshi ta shafa cikin kula da k'aunar irin ta uwa da d'anta tace. "Allah ya muku albarka." "Ameeen ya rabbi Habibi Ammin mu." Inna dake cikin d'akin ne ta fito jin muryan jikan nata da kuma k'amshin turaren babban jikan nata, cikin sauri ta fito, tana zuwa ta kalli Usman yadda yake zuba yarinta a gaban mahaifiyar tashi , dariya tayi sosai tace. "Shin wai kaika kam Usmanu baka ganin ka girma ne gankafa tsoho da kai." Kallon ta yayi cikin dariya yace. "D'a baya girma a gaban iyayen shi, na rasa d'umin jikin Abba na tun ina da shekara d'aya kinga ko dukda haka Hamma Umar na ya zame min madadin Abba na." Murmushi sukayi dukan su, dai-dai lokacin kuwa Hamma Umar yayi sallama cikin sanyi, fuska a sake Inna ta amsa mai gami da cewa. "Umaru sanda kafi mata yanga Umaru kafi k'arfin kabi mace sai dai ta bika Umaru sanda mai k'amshin al'miski Umar mai yawan kyauta da tausayi." Murmushi yayi cikin sanyi yace. "Bakya gajiya da surutu ne ke kam?." "Ya zanyi in gani ance ma kowa irin Kane mai tsadan magana." Kallon ta ya d'an yi cikin sanyi yace. "Allah ko Ammin Inna ce ta b'ata miki yaro da surutu kinga Usman ko duk surutun ta ya d'auka." "Ehh d'in na b'atashin." Shi kuwa Usman dariya kawai yake dan yasan dama za'a rina, itako Ammi murmushi kawai takeyi tana kallon fuskar d'an nata, shi kuwa Hamma Umar a hankalin ya matso gaban Ammin nashi cikin girmamawa da tsananin k'aunarta ya durk'usa a gabanta guiwa bibbiyu cikin sunkuyar da kai ya cire hular kanshi, ya k'ara matsota tare da sunkuyar da kanshi. a hankali Ammi ta d'ago hannun ta cikin sanyi ta dafe tsakiyar kan nashi sannan ta kalleshi cikin kula tace. "Allah yayi muku albarka rabbi ya karemin ku aduk inda kuke Allah ya tsare min imanin ku." a hankali ya d'ago hannayen shi duka biyu ya dafe hannun ta dake tsakiyar kanshi cikin sanyi yace. "Amin Amin Ameeen ya rabbil izzati , Ammi Allah ya kare mana ke." "Amin Amin" tace sannan ya koma ya zauna gabanta ya tonk'oshe k'afafun shi yana fuskantar ta, shi kuwa Usman yana konce kanshi na kan cinyarta shima yana fuskantar d'an uwan nashi. Wannan shine d'abi'a ko once al'adarsu Hamma Umar muddin suka zo gunta. Ita kuwa Inna sai murmushi take tana kallon d'iyar tata da yaranta, itako Ammi ajiyan zuciya ta sauk'e cikin sanyi tace. "Farouq ya jikin d'an uwanka?." kai ya d'an d'ago ya kalleta a hankali yace. "Ammi da sauk'i sai dai Usman sam baya son bin dokan likita komai ya samu ci yakeyi yayita d'ure-d'ure kuma yasan zuciyar sa nada rauni Ammi kiyi mishi fad'a bana son abinda zai cutar dashi." ya karishe maganar cikin raunin murya Hannu Ammi tasa ta kamo kunne Usman d'in cikin hukuntawa tace. "Baka ji ko?." k'ara ya d'an saki cikin d'an yarfa hannu yace. "Kai Ammi ninefa banda lafiyar amman kuma wai sai Hamma Umar zaki tabbaya ya jikina d'in, shiko ya fiye tsare-tsare." Dariya Inna tayi tace. "Baka dai ji shiyasa." .dai-dai lokacin yayan Ammin nasu ya shigo shima dariya yakeyi d'an yana matukar k'aunar yaran k'anwar tasu. Bayan sun gaggaisa ne, sukaci gaba da hira, Usman yana zaune gefen Ammin su yana bare banana yana mik'a mata tanaci inya bata d'aya sai ya kuma bawa Inna sannan ya mik'a wa kawun nasu pilet d'in, shi kuwa Hamma Umar zaune yake kusa da Ammin nashi yana rik'e da hannun ta yana yanke mata farce, abinda tunda Umar ya girma shike yanke mata farce, yakan shirya sam musamman dan yaje ya yanke mata farce kuma hakan shike yankewa Usman ma fartatunshi. Suna cikin hiran kawun nasu ya d'an yi gyaran murya cikin sanyi yace. "Umar kwana ki su Abban ku sunzo sun min baya nin batun auren ka da d'iyar Abban naki, mun tattauna maganar kuma yadda sukayi yayi dai-dai, toh shekara jiya sunzo sun shaida min asabar mai zuwa za'a d'aura auren sun kuma cemin sun gama komai za'a fara bikin nanda kwana 3 , toh Amman duk da sunce sun gama komai mukuwa mun had'a kayan lefen , yanzu haka Antyn ku sun tafi kai lefen ne shiyasa kukaji gidan shiru." Kai ya d'an d'ago ya kalli kawun nasu da Ammin shi sannan ya kalli Inna da Usman a hankali yace. "Dama nazone in shaida muku batun, ashe Abba har yazo." sai ya juya gun Ammin shi murya can k'asa yace. "Ammi ban nemi auren nan ba su Abba bani kawai sukayi shiyasa baki tab'a jin na miki zancen ba ko Usman ban gaya mishi ba dan nima a satin daya wucene suka gaya min, amman Ammi ya kika gani kina son abin ko a barshi?." Murmushi tayi tare da shafa kanshi cikin kula tace. "INA so Farouq ina al'fahari da wannan had'in fatana Allah ya baka ikon rik'e amanar da suka baka ka kular musu da d'iyarsu fiye da yadda suka kula da kai da d'an uwanka." Cikin rauni yace. "Insha Allah Ammi yadda kikace haka za'ayi." Shi kuwa Usman murmushi ya rink'a yi cikin jin dad'i da wani yanayin da zuciyarsa keyi ya kalli Hamma Umar d'in yace. "Ko zakayi zurfin ciki ga kowa a duniya ni ban canccanci kayi zurfin ciki a gareni ba." Kan Usman d'in ya dafa cikin sanyi yace. "Ba wani abu nawa wanda zan boye maka a duniya, Abba ne ya hanani in gayawa kowa shiyasa B'iyaye na ka gafar ceni." Rik'e hannu Hamman nashi yayi cikin happy yace. "A duniya zanyi fushi da kowa amman banda kai da Ammin mu ina farin ciki in nagan ka cikin farin ciki." Murmushi yayi sannan ya kalli kawun nashi cikin sanyi yace. "Kawun in nayi Aure zan d'auki Ammi na da Usman su koma gidana nima na samu ladan mahaifiya ta da k'anina." Kai kawun ya juya mishi alamar a,a sannan yace. "Banzan hanaka ba Umar amman kaga auren naku kamar auren cushene akayiwa yarinyar nan dan haka sai kaga ya yana yin zaman naku zai kasan ce." cikin sauri Ammi tace. "A duk inda kake kana samun ladana ni kam d'an uwanka kuma ai kaine jigonsa, nima zan kula da tawa mahaifiyar." Shiru kawai yayi dan shi kam a ranshi ya kudurta yana son mahaifiyar shi ta kasance kusa dasu. Daga nan sukaci gaba da hirarsu, haka suka wuni cikin farin ciki, sai dare suka tafi. A gida kula Ummul tunda matan su Kawun suka kawo kayan auren, yayin da su Mama matar Daddy da Anty Halima da k'annen Nenne suka tarbi bak'in Ummul ta shige d'akin Hajjajo ta rink'a wani irin kuka , haka ta wuni kuka baci ba sha ta k'aura cewa kowa ta k'aura cewa komai gani take duk ba masoyan ta bane . Haka tayi ta kuka har dare, Anty Halima ce ta shigo tare da Ya Usman cikin takaici tace. "Ummul kiji tsoron Allah ki tausayawa kanki yanzu wannan kukan maganin me zai miki?." Kuka ta k'ara sakewa cikin dashewar murya tace. "Anty kiji yadda Hamma Umar yake harkokin sa shi ko a jikin sa ni aka cusawa bak'in ciki, na tsani Hamma Umar bana sonshi ko a matsayin d'an uwa bare abokin rayuwa." Tsaki Anty Halima taja sannan ta juya ta fice tana cewa. "Tunda bakya jin magana kiyi duk yadda kike so, Aure ne dai saura kwana 6 nima daga gobe zanzo su Anty Shuwa kuwa suma gobe zasu zo dan su fara shirya ki." Tana kaiwa nan ta fice abinta, ita kuwa Ummul sai hawaye, Ya Usman ne ya matsota cikin sanyi yace. "Kiyi hak'uri kibar kukan Ummul kina soyamin zuciya da kukan ki, Ummul ko so kike zuciyata ta fashe." Shiru tayi cikin tausaya mishi baki na rawa tace. "Ya Usman kasha maganin ka." Murya a raunane yace. " ko nasha maganin ba zaiyi aiki ba in har baki bar kukan nan ba." Cikin tsoron halin da zai iya kasan cewa, tasa hannun ta share hawaye ta, murya na tace. "Nayi shiru ya Usman." "Toh" yace sannan ya kamo hannun ta suka fito parlour abinci ya bata ta d'an ci . Haka abu yake tafiya ba mai iya lallashin Ummul sai Usman kuma ba wanda take saurarawa sai shi bata cin abinci Sai in ya Usman d'in nata ne matsamata bata shiri da kowa sai shi shiko Usman shi kad'ai yasan cikin halin da yake rayuwa yana boye sirrinshi a zuciyar shi, abinda bamu saniba shin zuciyar Usman zata iya jurewa kuwa? . Yau talata tun da sassafe gidan su yake cike tib da bak'in haka yasa Ummul ta takure kanta cikin d'akin Hajjajo akan gadon ta mai rumfa, ko k'awayen ta tak'i su ganta, tana konce a hankali taji k'amshin turaren Hamma Umar d'in a take taji wani irin tsanarsa na ratsata, shi kuwa kai tsaye bak'in gadon ya nufa yana zuwa ya tura hannu shi a k'asan..... By *GARKUWAR FULANI* 濡絽鍟幉顐o純閸愩劎锛撳Λ锝呭暙绾捐櫕锛冮崘銊э紦濡絽鍟壕铏純閸愩劎锛撳Λ锝呭暙绾捐櫕锛冮崘銊э紦濡絽鍟壕锟� *RUBUTACCEN AL,AMARI* page 1闂佹剚鐓夐幏锟�1闂佹剚鐓夐幏锟� *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 濡絽鍟壕铏純閸愩劎锛撳Λ锝呭暙绾捐櫕锛冮崘銊э紦濡絽鍟壕铏純閸愩劎锛撳Λ锝呭暙绾捐櫕锛冮崘銊э紦濡絽鍟壕锟� *Zan abbato mutanen sokkoto su y'an kwaraine basu da tsoggoma idan kaje ka sanya fad'a musu zasu rik'eka da kyau harda lallamah k'warai-k'warai na gane duniya mai sonka shike yi maka hiddima masoya na na sokkoto kun gaman gata gaisheku 濡絽鍠氬顏咃純閸愨晩娼濆Λ锝呭暞椤垺锛冮崘鈺佹殟濡絽鍟欢銊︼純閸愮偓顎塶akeyi domin kuke raba gardama濡絽鍟崯銏★純閸愩劎娉曞Λ锝呭枤濡撅拷 sokkotawa ina al'fahari daku domin baku da hassada a zuk'atan ku shiyasa na sadaukar da wannan shafi gareku sokkotawa濡絽鍠氬顏咃純閸愨晩娼板Λ锝呭暞閸熴垺锛冮崘銊ф硶* *Ha*nnushi ya tura kasan pillow dake gefen ta da niyar zai jawo laptop d'in shi daya bari a wurin, lalubawa yakeyi aman baiji inda laptop d'in yakeba dan d'akin yana da duhu gashi kan gadone mai rumfa duk yasha gyara da shimfid'a da labulaye sai ya k'ara duhun, Ita kuwa Ummul tana ganin shi dan ita ta dad'e a d'akin so duhun yabi idonta shi kuma yanzu ya shigo d'akin shiyasa yake ganin duhun sosai, tab'e fuska tayi cikin ko in kula tasa hannu ta turo laptop d'in nashi k'asa dai-dai sautin kan yatsunshi ta turo shi, shi ko da sauri ya sunkuya da nufin yasa hannu ya taro laptop d'in kar ya kai k'asa gudun karta lalace, amman ina cikin rashin sa'a ta fad'o kan yatsunshi tsinin aggil d'in jikin marfinta ya caki kan farcen babbar yatsarsa, cakar da a take farcen ya tsage lokaci d'aya jini ya fara zuba a take k'afar ta fara wani irin b'ari dan azabar daya ratsashi gaba d'aya yatsar kuma sai motsi take kamar zata fice a jikin shi, cikin wani irin azaba dayaji ya ziyarci k'ahon zuciyarshi ya dafe kanshi da k'arfi hannun shi sai rawa suke gaba d'aya jijiyoyin kanshi suka taso ida nunshi sukayi jazir ya kasa magana sai harshen shi ya d'an zaro ya rink'a d'an kad'awa yana furza numfashi tuni zufa ta keto mai ta sashoshin jikin sa, harshen yake d'an kad'awa yana fidda sautin. "Shihhhhhhhh ahhhhshhhhhh." Sai kuma k'afar tashi daya d'an d'ago yana yarfawa, Ita kuwa Ummul sai murmushi mugunta ta rink'a yi tanaji dariya nason kufce mata murmushin takeyi tuk'uru cikin jin dad'in azabtar dashi da tayi sai wani kad'a kai takeyi tana magana a ranta. "Kad'an ma kaji Hamma Umar wannan shine makullin wahalar da zakasha a hannun na, kaida azabtuwa kun kullah, Sai kayi kuka cur-cur da hawaye ka sai ka gommace kid'i da karatu sai ka sakeni saki mafi muni wanda zan haramta maka har sai inna nasake wani auren an sakeni." Kai ta jinjina taci gaba da maganar zuciyar da bata saniba na yanzun ya fito fili cewa take. "Tabbacin da nake dashi ko ince yak'ini na sani Mustapha bazai sakeni ba har Abadan zamu rayu tare." Da sauri Hamma Umar d'in ya bud'e idanun shi daya rumtse jin sautin Ummul d'in kan gadon ya tsurawa ido cikin wore idanun shi , fuskar ta ya tsare da ido cikin zafin nama ya mik'a hannushi kan gadon, ita kuwa ganin haka tayi wani irin dira daga kan gadon a guje tayi woje a parlour ta samu ya Usman da su Hajjajo da Inna tare da Anty Halima da Anty Shuwa k'anwar Nenne, cikin rawan jiki ta koma gefen ya Usman ta zauna cikin tura baki da tsuke fuska, Anty Halima ce ta kalleta cikin tuhuma tace. "Me kika aikata? kika fito a guje haka?." fuska ta k'ara tsukewa sannan ta kalli Anty Shuwa dake ta danna mata harara cikin son yin kuka tace. "Nayi ai ban sani bane." Hajjajo ta bud'e baki zatayi magana kenan sai kuma tayi shiru ganin Hamma Umar d'in d'aya fito cikin d'akin nata , tafiya yake yana d'ingisa k'afar tashi duk inda ya taka sai jini dake zuba gaba d'aya jijiyoyin kanshi sun taso kanshi a k'asa yake tafiya hannushi rik'e da laptop d'in nashi yayinda d'aya hannun kuma yake rik'e da iPhone d'in shi, Ya Usman ne da Anty Halima sukayi kanshi da sauri cikin rawan baki Ya Usman yace. "Hamma Umar me ya fasama yatsa yaushe ya fashe kalli yadda jiki ke zubafa." Anty Halima kuwa gaba d'aya jikin ta rawa yake ganin duk jini ya wonke mai k'afarsa cikin sanyi murya na rawa tace "Hamma Umar a tsaida jinin nan mana ya dena zuba." kai ya gyad'a musu cikin jarumta da dauriya ya nufi hanyar fita yana ce musu . "Ba komai fa." har yake bak'in k'ofar fita, Hajjajo da Inna sukayi kanshi da sauri cikin kula da tsananin k'aunar jikan nasu suka kalleshi, kusan a tare suke magana. "Kai Farouq me ya fasama k'afar? kayi magana kayi shiru ?." kai ya jinjina a hankali yace. "Tuntub'e nayi." fad'in haka da yayi ne yasa suka rink'a jeromai "sannu-sannu Amman kaji azaba kam ai abinda ya fasa farce ba k'ara min abu bane." Su tsoppin sun yarda Amman Anty Halima da Anty Shuwa kam sun gane sarai Ummul ce taji mai ciwon dan ganin yadda take zare ido da alamun rashin gaskiya Ita, kuwa Ummul har cikin ranta take jin dad'in ciwon da taji mishi, a wani sashin zuciyar ta kuwa tana mamakin yadda Hamma Umar d'in ya rufa mata asiri yak'i cewa Ita ta fasa mishi k'afar, dan ta tabbaya d'aya fad'a Ita kuwa da ta shiga 9 nema ba 3 ba. shi kuwa Hamma Umar ko inda take bai kallah ba ya fice yana d'ingisa k'afar, ya Usman kuwa karb'a laptop d'in Hamman nashi yayi ya rik'e cikin raunin fuskar sa kamar zaiyi kuka dan tausayawa d'an uwan nashi, har zasu fita ya juyo ya kalli Ummul d'in cikin raunin da yanayin tuhuma dan ya gane itace silar ciwon Hamman nashi, itama kallon shi takeyi cikin sanyi ta rumtse idonta, shi kuwa juyawa sukayi suka tafi. Suna zuwa part d'in su Hamm Umar d'in yayiwa yatsar tashi dressing sannan yawa kanshi allurar ya kuma sha magani. Ita kuwa Ummul suna fita Anty Shuwa da Anty Halima suka jata d'akin dake gefen na Hajjajo suka rink'a yi mata gyare-gyare tare da tsumata da irin tsumukansu na shuwa'arab , Anty Shuwa ce ta b'alle marfin wani roba sannan ta jijjiga tare da mik'ewa Ummul d'in cikin tsuke fuska tace. "Karb'a ki shanye yanzu ki bani robar." Kai Ummul d'in ta karya cikin kuka da gajiya da d'ure-d'uren da suke mata tace. "Ni dai amai nakeji dan Allah a barni hakanan." A fad'ace Anty Shuwa tace . "Sai kinsha muguwar banza yadda kike mishi mugunta haka zai rama kiji tsoron mutumin da baya magana inya tashi ramawa zaki yabbawa aya zakinta." kai Halima ta jinjina sannan tace . "Gaya mata dai Anty wallahi wata rana zakiyi nadama abinda kikewa Hamma Umar d'in." Haka suka rink'a yi mata fad'a da nasiha sunayi suna tsumata tare da dilketa da murjeta. Haka nan kullum Sai sun murjeta sun tsumata, ta fito tayi rasa sai wani shek'i take tamkar tarwad'a fatar jikinta kuma tamkar auduga komai nata yasha gyara sai wani k'amshin mai sanyi take fiddawa ko wucewa tayi k'amshin ta sai ya ratsa wurin gashin kanta kuwa ba'a maganar gyaran d'aya sha, an gyareshi gyara na mussamman k'afafun ta da hannayen ta kuwa an musu zanen Lalle na mu samman komai na Ummul ya fito rasa ta fito a shuwa'arab d'in sak. A gefen ago Hamma Umar kuwa , komai Ya Usman ne yake gudanarwa gaba d'aya ya gayyato abokon Hamma Umar d'in nashi ... Yau ta kama Jumma haji babbar rana Wanda ya kasance gobe asabar ne za'ayi d'aurin aure Ummul da Hamma Umar . Toh a rayuwar shuwa'arab akwai wata al'adar da sukeyi a duk lokacin da zasuyi bikin su , suna yin wannan al'adar tasune kamar gone za'a d'aura aure , kuma wannan al'adar tasu tana kunshe da wata al'adar kuwa Wanda a halin gaskiya a yanzu haka gaba d'aya shuwa'arab sunbar yin wannan al'adar ta biyun na farin dai sunyi Amman na biyun kam , a shuwa'arab d'in ma na zamanin yanzu da yawa basuma san al'adar ba dan tuni anbar yin al'adar duk da dai a zamanin da d'in ma a cikin aggwaye 100 da wuya a samu aggwaye 5 masu yin wannan al'adar domain al'adace mai nuni da d'auka alk'awari da kuma rik'o da amana suna kiran al'adar da sunan *Nad'in uwar gida* So shiyasa aggwayen yanzu basa wannan al'adar ta biyun kenan fa, Amman na farin kam har yanzu shuwa'arab sunyi kuma in an gama na farinne akeyin na biyun, so Yau jumma'a tun safe aketa shirin wannan al'adar tasu na. farin wanda dama asan dashi shi kuwa na biyu ba wanda yake da tabbacin za'ayishi a cikin shuwanma wasu basu san da wannan ba, tun safe aka k'afa tantuna a harabar gidan nasu aka shimfid'a kilisai na al'farma aka ajiye kujera na gani na fad'a kujera masu taushi gaba d'aya an zagaye wurin da kolliyoyin zamani tare dana al'adun shuwa'arab d'in, cikin kujerun kuwa a tsakiyar kujerun akwai na aggo da amarya wanda sunayen su ke rubuce a Kansu sai na k'awayen Amarya da abokin aggo suma duk sunayen su na rubuce akan kujerun nasu. Yadda ake al'adar tasu kuwa bayan an gama kimtsa wurin aggo zai fara zuwaya zauna da zugar abokan shi sai bayan ya zauna da mintuna kad'an sai a fito da amarya, fito da amaryarna kuma 'Yar uwar amaryar ce ta jini zata fito da amariyar rik'e da hannun ta , sai ta mik'a hannun amariyar ga hannun y'ar uwar aggo ko d'an uwan aggon, daga nan sai shiko d'an uwanshi ago yaja hannun Amarya ya kaita kusa da aggon ya ajiyeta, so y'an uwa da abokin arzik'i zasu tashi sunyi ta yiwa Amarya lik'in kud'i da gudumowowinsu, bayan duk an gama lik'inne sai shi kuwa aggo ya tashi yayi nashi lik'in, shike nan itace al'adar su ta farin . So haka aka tsaba wannan al'adar bayan an sauk'o sallan jumma'a Hamma Umar da abokanshi duk suka dawo gidan suka d'an huta sannan matayen su kuwa suna cikin gida , bayan anyi sallan la'asarne sannan aka fara shirin fita wurin taron, abokon Hamma Umar manyane masu cikar kamala abokai ne daku masu karatu kun sansu haka kuwa matayen su, haka sukayi shiga ta al'farma shiga irin ta shuwa'arab d'in sukayi baki d'ayan su suka fito rasa tamkar larabawa, Suma matayen su da k'awayen Amarya Ummul shiga sukayi ta shuwa'arab d'in gaba d'ayan su laffaya suka yane jikin su dashi suma dama gasu kyawawa. Haka yasa wurin taron ya zama tamkar a k'asar larabane , wani abin burgewa kuwa duk woni sak'o da luggu har cikin fulawowi na gidan an ajiye kaskon turaren wuta sai wani irin k'amshin ke tashi hakan yasa nishad'i a zuk'atan duk wani bani adam dake zaune a wurin. 5:00 pm zugar ago da abokanshi suka ido farfajiyar gidan Ya Usman ne a gaba yayinda sauran abokon ke binshi a baya , Hamma Umar kuwa yana tsakiyar su yasha sutura ta al'farma ya fito cikin haiba da cikar zati sajenshi sai wani irin shek'i yakeyi farar fatarshi ta fito ras tamkar balarabe sumar kanshi kuwa. yayi luf gwanin sha'awa ya murza hula a kan nashi yayinda gashin nashi yabi k'eyarshi da zagayen fuskar shi, idanun shi kuwa wani d'an siririn glass ne mai haske irin na Doctors ke manner a fuskar sa. dai-dai lokacin da suka fito a dai-dai lokacin kuma matayen abokan aggon suna suka fito , gaba d'aya wani taku suke a jere kamar yadda kujerun ke Jere kowa da matarsa a gefen Hamma Umar ne ya fara zama sai babban abokin shi , Hamma Yusuf da Ayshar sa sai Hamma Hassan da Fateemar shi sai kuma. Hamma Bashir da Ruk'ayyar shi Sai Hamma Mahmoud da Khadija shi sai kuma Hamma Aliyu Haydar tare da Minalin shi, A d'aya gefen kuwa wasu manyan abokan Hamma Umar d'in na gani da matayen su, Amadi da Nadiyar shi, sai Abuturrab da Batul d'in shi sai kuma Salim da Tawa Sai Abdullahi tare da Maryam d'in shi, daga gefen su kuwa Fauziyya ce da Al'ameen sai Aisar tare da Bintun shi sai kuma Abbah da Ruky pinkyn shi, ga kuma Ridwan da Zakiyya can kuma kusa dasu Ahmad Ana Muslim ne tare da khadijan shi sai kuma Assadiq da Safiyyar shi tare Hibbah da Faheem. Gaba d'aya sun zauna cikin nitsuwa da al'farma suna zaune cikin cikar haiba sun fito tamkar taurari sai shek'i sukeyi da wani irin k'amshin da suke zubawa zamane sukayi na masoyan gaske. Bayan sun zauna da kamar minti 5 Dangi da k'awayen Amarya da sauran mutane sukazo suka zauna, cikin nitsuwa da lumana, Jim kad'an, suka fara jiyo wani irin k'amshin na k'ara ratsa hancin su gaba d'aya sai wani irin shauk'i ya ziyar cesu ido suka lumshe tare da jin dad'in k'amshin dake k'ara bud'e su wanda Anty shuwace ke rik'e da kaskon turaren wuta, Anty Halima kuwa na biye da Ita a baya tana rik'e da hannun Ummul wacce tasha gyara iya gyara an yaneta cikin laffaya mai tsadar gaske ta fito a shuwa'arab d'in sak ta fito tamkar tauraruwar zarah dake kusa da wata, Anty Halima na rik'e da hannun ta suka iso farfajiyar gidan yayinda ita kuwa Ummul kanta ke sunkuye idanun ta na zubda wasu irin wahaye masu zafi da tafasa zuciya tafiya takeyi tamkar hawainiya, suna isowa Ya Usman ya mik'e cikin happy yaje gabansu ya tsaya cikin wani irin salon al'darsu ya d'an kife guiwarsa d'aya a k'asa sannan ya d'an d'ago hannunsh sama kad'an ya ware tafin hannushi cikin sanyi yace. "Halima samin hannun matar Hamma na cikin tafin hannuna ni zan kaiwa Hamman matarsa kusa dashi." murmushi Anty Halima tayi tare da kamo hannun Ummul d'in ta d'aura cikin tafin hannushi, wani irin nanauyan ajiyan zuciya ya sauk'e tare da rumtse idonshi da k'arfin, yatsun hannushi ya cusa cikin nata ya rik'o hannun ta sannan ya mik'e tsaye ya fara taku a hankali itama Ummul takun takeyi tamkar hawainiya a haka har suka isa gaban kujerar da zai zaunar da ita suna zuwa ya kamo kafad'unta ya juyota tana fuskantar shi yayinda ta bawa kujerar baya, cikin sanyi ya zaunar da Ita kan kujerar dake manne data Hamma Umar, a hankali ya fara tasowa daga sunkuye da yayi a kanta, Ita kuwa Ummul kanta ta kuma sunkuyarwa tare da sakin wani narkekken sautin kuka can k'asa, Sai kuma tayi shiru cikin sauri ta d'ago kanta tana kallon Ya Usman d'in nata jin kamar y'an watsa mata ruwa, abin mamaki da Ummul ta gani ba ruwan bane ya Usman ke watsa mata , Hawaye ne ke bin fuskar sa har yana diga cikin tafin hannun ta , ido ta zuba mai cikin yanayin tabbaya da tsantsar. mamaki a fuskar ta, shi kuwa cikin jarumta yasa tafin hannushi ya goge k'ollah dake zuba a idanun shi, murya na rawa yayi murmushin da yafi kuka k'una a zuciya murya can k'asa yace mata. "Allah ya d'aiyiba." itama murmushi tayi cikin zubda k'olloh murya a disashe tace. "Ya Usman ina son ka". ido ya lumshe da sauri cikin raunin murya yace. " Ummul nima ina sooonki." Ido Ummul kam ta kuma rumtsewa dan tasan ba haka suka saba cewa juna ba, Ita tasan in tace mai ya Usman ina sonka shiko sai yace Allah ya d'aiyiba Amman Yau kuma shima sai yace mata "Ummul nima ina sooonki " a madadin yace Allah ya d'aiyiba Sannan ga hawaye dake bin fuskarsa, tana cikin nazarin ne taji ya fara yi mata lik'in da Sabin kud'i na gudan dubu-dubu' gaba d'aya wuri aka fara tafi marok'a na . "Kaji k'anin aggo Usman d'an Maliki mai ruwan nare." lik'in sosai Ya Usman yayi mata yanayi yana zubda k'olloh cur-cur sai yasa tafin hannushi yana gogewa ganin haka yasa Ummul tayi murmushi cikin d'an d'aga murya kad'an yadda zai iya jinta tace. "Allah ya d'aiyiba min ya Usman dina." jin haka sai ya rink'a murmushi tare da kallon fuskar ta, a haka ya gama yi mata lik'in sannan Ya Adam da ya Sadik tare da Aliyu auta suma suka shigo sukayi mata lik'in , daga nan manyan abokan Aggo kuma jarumai suma suka fito sukayi lik'in ban girma, daga nan y'an uwa da abokan arzik'i sukayi nasu. lik'in, bayan duk an gama kowa ya koma mazaunin shi wuri yayi haske, cikin wani irin yanayi Hamma Umar d'in ya mik'e tare da juyowa gaban Ummul d'in sannan kanshi a sunkuye cikin sanyin muryar shi ya kalli marok'an yace. "Ku shaidawa Jama'a yanzu zanyiwa Ummul lik'in ne a matsayina, na babban Yayanta d'an uwanta." aiko a take marok'an nan suka rink'a shela suna fad'in. "Aggo yace a shaida muku yanzu zaiyi lik'in ga Amarya a matsayin shi na babban yayanta kuma d'an uwanta." gaba d'aya sai wuri ya ciki da shauk'i , abokan Hamma Umar da matan su sai murmushi suke, shi kuwa Hamma Umar lik'in kawai yake mata da rafa-rafa na dubu-dubu, haka ya rink'a zubawa Ummul kud'i tamkar ruwan sama, bayan ya gama ne sai ya kuma komawa kan kujera ya zauna, sannan k'awayen Amarya suka rink'a tattara kud'ad'en. Bayan sun gama ne Hamma Umar d'in ya sake tashi tsaye cikin cikar haiba da kamala gaban Ummul d'in ya kuma tsayawa cikin k'asaita yace. "Yanzu a matsayin aggo zanyi lik'in." marok'an ko tuni suka cika wurin da kirari suna. "Ummaru sand'a babuga mai nera Ummaru mai ado da zinari Ummaru Farouq mai K'amshin al'miski kunji Umaru Farouq babban adali doctor mai tausayi da jink'ai." Shi kuwa Hamma Umar Dolas ya zaro ya rink'a yiwa Ummul b'arinsu a kanta, Ya Usman kuma na tsaye a gefen shi rik'e da turaren mai suna *du'a'ul jannarh* mai tsananin k'amshin, bayan Hamma Umar ya gama lik'in sai ya kuma mik'a hannu ya karb'i turaren dake hannun Ya Usman, sannan ya d'an sunkuyo kan Ummul d'in ciki kallon fuskar ta ya fara fesa mata turaren yanayi yana k'ara matsota har ya isa gab da Ita sannan ya mik'ewa Usman turaren , a hankali ya rokk'fo gaban ta sannan ya sunkuye dai-dai kanta, mutanen wurin kuwa gaba dayasun maida hankalin su sukayi kan Hamma Umar d'in domin son ganin me zai aika ta, Hajjajo kuwa da Inna tuni sun fara mamakin abinda Umar d'in yake shirin aika tawa, sauran mutane kuma gaba d'aya kallon shi suke cikin tarin mamaki dan gano abinda yake shirin aika tawa, Ammin kuwa lokaci d'aya taji wasu siraran hawaye na bin fuskata tana kallon Abin da Babban d'an nata zaiyi, Abokan Hamma Umar kuwa ido suka zuba mai cikin mamaki su Hamma Yusuf duk an cika da mamaki sai k'ara rik'e hannun Ayshan sa yake. Itako Ummul gaba d'aya jikin ta sai kerma yake ido kawai ta zubawa Hamma Umar d'in fuskar ta cike da k'olloh, Nenne ma ido ta zuba mishi dan gano abinda zaiyi. Shi kuwa Hamma Umar cikin wani irin yanayi yasa hannushi ya cire hular kanshi sannan ya k'ara sunku yowa kan Ummul d'in tare da manna.... By *GARKUWAR FULANI* 婵☆偓绲介崯顖炲箟椤愶綇绱旈柛鎰╁妿閿涙挸螞閿濆懎鏆欑痪鎹愭珪閿涘啴宕橀妸褝绱︽俊顐到閸燁偆澹曢搹顐磾闁告劑鍔庨敍鎾澄涢敐鍛殭缁炬崘娅曢敍鍐礃閵娧嶇处婵☆偓绲介崯顐ゅ閿燂拷 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1闂備焦鍓氶悡澶愬箯閿燂拷2闂備焦鍓氶悡澶愬箯閿燂拷 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 婵☆偓绲介崯顐ゅ閾忣偓绱旈柛鎰╁妿閿涙挸螞閿濆懎鏆欑痪鎹愭珪閿涘啴宕橀妸褝绱︽俊顐到閸燁偆澹曢搹顐磾闁告劑鍔庨敍鎾澄涢敐鍛殭缁炬崘娅曢敍鍐礃閵娧嶇处婵☆偓绲介崯顐ゅ閿燂拷 *H*ularshi ya cire daga kanshi sannan ya kuma sunkuyowa kanta, yayin da gaba d'aya mutanen wurin kuwa suka zuba mai idanu, shi kuwa Hamma Umar kanshi a sunkuye cikin lumshe ido ya manna mata hular tashi a kanta sannan yasa hannu biyu ya dai-dai ta zaman hular a kan Ummul d'in hular tayi ras, ita ko Ummul ido ta zaro cikin tarin firgici gano cewa Hamma Umar al'adarsu ta biyun zaiyi a take zuciyarta ta rink'a buga wa a saba'in, Ammin shi kuwa sai murmushi take a ranta tana al'fahari da d'an nata, Abokan Hamma Umar kuwa kallon shi suke cikin sha'awa da burgewa, Ya Usman kuwa k'irjin shi ya dafe da k'arfi sannan yasa hannun shi d'aya ya damk'o hannun abokin shi Nuru dake zaune kusa dashi a sashin zuciyar sa kuwa yana al'fahari da hallaci irin na Hamma Umar d'in nashi yana jin dad'in yadda a gaban dubban al'ummah zaiyi al'k'awarin da d'aukar amana, Shi kuwa Hamma Umar bayan ya gyara zaman hulan nashi a kanta sai ya kuma sa yatsunsa biyu ya zaro siririn gilashin dake manne a fuskarsa cikin lumshe ido ya kuma mannawa Ummul gilashin tare da ajiyeshi ras a fuskarta , ita ko Ummul zuwa yanzu hawayen ta tuni suke d'iga kan tafin hannun ta tol-tol, ganin haka yasa cikin furza sassauk'an numfashi Hamma Umar d'in ya d'an rok'k'ofo ya zauna gabanta suna fuskantar juna zama yayi dirsham a gabanta ya tok'k'oshe k'afafun shi sannan ya had'e guiwowin sa, A hankali ya sunkuyo kanshi yana kallon k'afafun ta da su kasha zane , hannun shi yasa a hankali ya d'ago k'afafun nata sannan ya zare takal manta ya ajiye gefe cikin kula ya tallab'o k'afafun nata da tafin hannun shi cikin tabbacin abinda zaiyi ya d'ago k'afafun nata ya diresu kan guiwowin shi sannan ya had'a yatsun k'afafun ya rik'e yana d'an matsawa kamar mayi mata tausa sai kuma ya sunkuyar da kanshi cikin yanayin bugawar zuciya dan tabbas yasan hakan da yayi d'aukan babban al'k'awarine firgincin dake ranshi shin ko zai iya cika al'k'awarin da ya d'auka?, mutanen wurin kuwa gaba d'aya aka kaure da tafi maroka na gud'a cikin yin kirari ga aggo Umar Farouq, dan ba wanda yayi tunanin Hamma Umar zaiyi wannan abun, Hajjajo kuwa hamadala ta rinkayi cikin jin dad'i Inna kuwa sai k'ollah dake bin fuskata a fili tace. "Farouq na Allah Umar Farouq adon gari Farouq mai zuciyar taimako Allah ya baka ikon cika wannan al'k'awarin da ka daukarwa kanka." Anty Halima kuwa da Anty Shuwa farin cikin su baya fad'uwa ita kuwa Nenne kuka takeyi sosai a ranta tana ganin al'barkacin sune ita da Abba Ummul ta samu wannan karramawar a gun Hamma Umar d'in, Matar yayan Ammin Anty Nafeesat ce ta kalli Hajjajo dake gefen ta cikin mamaki tace. " Hajjajo me Wannan abinda Umar yayi yake nufi?." Murmushi Hajjajo tayi cikin al'fahari da jikan nata, ta kalli Anty Nafeesat tace. "Anty Nafeesat Wannan abin da Farouq yayi shi muke kira da nad'in uwar gida sannan mutu ka raba , Anty Nafeesat wannan abin da yayi d'aukar al'k'awarine mai k'arfin gaske na rik'e mace da amana da gaskiya." Numfa sawa Hajjajo tayi tare da ciga da cewa. "Anty Nafeesat idan namiji yayi wannan abin toh ya d'aukarwa kansa indan zai kashewa kansa dubu 50 toh zai kashewa matarsa dubu 100 ninkin ba nashi kenan kuma ba abinda zaici ba tare d'aya ciyar da matarsa ba kodako tsagin dabino ne sannan ya bata matsayin sarauniya shin ki kalli yadda yake zaune a gabanta mana kuma ya d'ora k'afafun ta a kashi tamkar itace sarauniyar shi." Kai Anty Nafeesat ta jinjina cikin jin dad'in abin tace. "Allah ya bashi ikon cika alkhairi." "Amin Amin." Hajjajo da Inna suka amsa. Tafi da sowan da mutane keyi da al'k'awarin da Hamma Umar ya d'auka su suka kara cushe zuciyar Ummul dan ganin duk Hamma Umar ya saye zuk'atan mutanen wurin ita kuwa zuciyar ta tamkar ta fashe dan tsabar tsanar Hamma Umar d'in sai wani irin kuka ta saki mai cin rai, shi kuwa Hamma Umar ba abin da ya fad'o mishi a ranshi sai tunanin mahaifinshi dan al'adarta su ana gamawa aggo zai wuce gun maihaifin shine dan ya samishi albarka da addu'ar Allah ya tayashi rik'o, tunanin shi a yanzu shi gashi yayi al'k'awarin Amman bayida mahaifi a duniya bare ya samishi albarka ya kuma tayashi Addu'ar Allah ya taya shi rik'o, tuno hakan ne yasa rauni a zuciyar Hamma Umar ta yadda lokaci d'aya hawaye ya b'allo a fuskarsa hawaye ne ke zuba cur-cur dan tuno mahaifinshi , zuba hawaye suke har kan k'afafun Ummul dake kan guiwowin sa, kuka yake cikin raunin sautin da ba wanda ke jinshi sai ita Ummul d'in da yake zaune a gabanta sai kuma Ya Usman da ya haggo hawaye na bin fuskar B'iyayen nashi, Ammi ma dake zaune gefen a lokacin tunanin mijinta ya dawo mata yau gashi ana bikin babban dansu amman ba mahaifin su Allah bai nuna mishi ba sai ita kad'ai, itama sai kuka, Ya Adam kuwa dake tsaye gefen Hamma Umar ya fara jin sheshshek'ar Hamman nasu tuni shima hawaye ya fara bin fuskarsa, Abokan Hamma Umar kuwa tasowa sukayi suka rink'a yi mishi liki, Ya Usman kuwa tuni zuciyar shi take harbawa hakan yasa ya sake hannun Nuru ya nufi gun Hamma Umar d'in nashi, shiko Nuru da sauri ya mik'e yabi bayan Usman din yana. "Usman anya kuwa yau kasha maganin ka kuwa? jikin ka ko? Usman kana wasa da lafiyar ka fa wato yau Hamma Umar yana cikin baki bai samu ya baka maganin kaba shine kai kuma bazaka iya shaba sai ya baka?." cikin rawan murya fuska cike da k'ollah Ya Usman yace. "A a Nuru a,a Hamma na ya bani maganin nasha , Hama Umar baya manta bani maganin duk hidamar da yake ciki, Nuru kalli Hamma Umar na yana kuka da hawaye Nuru sake ni naje kusa da B'iyaye na, Nuru Hamma Umar baya barin hawaye ya zuba a idanuna ,.Nuru ya za'ayi niko na k'asa tsaida nashi hawaye ?." cikin tausayin su Nuru ya sake mishi hannun shi, shi kuwa Usman kutsawa yayi cikin mutane yana zuwa ya durk'usa gefen Hamma Umar d'in daketa kuka hannun Usman yasa ya rik'o na Umar d'in cikin kuka yace. "Kai tona Hamma Umar kaito na tunda ina raye ban iya k'anwar da duk wani abu da zai saka kuka a rana mafi daraja a gare kaba." jin muryar d'an uwanshi yasa ya juyo ya rugume k'anin nashi, suka rugume juna cikin rauni Hamma Umar yace. "Usman Abban mu na tuna yau gashi ina bid'ar addu'arsa gashi kuma baya raye." ganin yadda suke kukan ne jikin kowa yayi sanyi haka yasa Ya Adam ya jagoranci abokan Hamma Umar din suka koma cikin gida a gefen baki Anty Shuwa kuwa taja k'awayen Amarya suka tafi, Anty Halima kuwa cikin kuka ta kamo hannun Ummul dake kuka kamar ranta zai fita sukayi cikin gida, haka aka watse taron, Ammi kuwa dama tuni tayi cikin gida kai tsaye d'akin Hajjajo ta wuce tana wani irin kuka mai karya zuciyar mutane, Hamma Umar kuwa shida Usman suna tashi suma suka wuce d'akin Hajjajo, suna zuwa suka zauna gaban Ammin su ita kuwa Ammin ta k'asa magana sai kuka, Hamma Umar ne ya matsota kanshi ya d'ora kan cinyarta cikin kuka da rauni ya jawo Usman kuma jikin shi ya rugume shi baki na rawa yace. "Am! Ammi! Ammeee! ki dena kuka Ammi ki samin al'barka kimin Addu'a Allah ya bani ikon cika al'k'awarin dana d'aukar wa kaina, bani da mai tayani Addu'a bayan ke da d'an uwana Ammi kibar kuka karki sa Usman a rud'ani." Hannunta ta dafe kanshi... *Kuyi hak'uri da Wannan Yau bak'in ciki kamar na d'aki kaina na gama typing 1 page mai Reed more 7 wlh garin gyara nayi delete nashi da ker nayi wannan* By *GARKUWA FULAni* 濠碘槅鍋撶徊浠嬪疮椤栫偛绠熸い鎰剁秶缁辨棃鏌涢幇鈺佸闁挎稒鎸歌灋闁挎繂鎳庨弳娆戠棯閹规劖鐝柨娑樺暣瀹曟﹢濡歌缁憋附淇婇顒傚埌闁哥噥鍋嗘竟鏇㈡惞椤愵剛纾鹃梺鍛婂姂閸斿酣鏁嶉幘婢勬盯鏁愰崨顓熸缂佺偓宕樺▍鏇㈡晬閸愵喖绀冮柕濞у秶澶勫┑鈽嗗亾缁蹭粙宕銈咁棜闁跨噦鎷� *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1闂傚倷鐒﹂崜姘舵偂婢舵劕绠柨鐕傛嫹3闂傚倷鐒﹂崜姘舵偂婢舵劕绠柨鐕傛嫹 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 濠碘槅鍋撶徊浠嬪疮椤愩倕顥氶柧蹇e亾缁辨棃鏌涢幇鈺佸闁挎稒鎸歌灋闁挎繂鎳庨弳娆戠棯閹规劖鐝柨娑樺暣瀹曟﹢濡歌缁憋附淇婇顒傚埌闁哥噥鍋嗘竟鏇㈡惞椤愵剛纾鹃梺鍛婂姂閸斿酣鏁嶉幘婢勬盯鏁愰崨顓熸缂佺偓宕樺▍鏇㈡晬閸愵喖绀冮柕濞у秶澶勫┑鈽嗗亾缁蹭粙宕銈咁棜闁跨噦鎷� *K*anshi ta dafe cikin muryar kuka tace. "Farouq Allah yayi muku albarka kai da d'an uwanka Allahu rabbi ya jibanci lamuran ka hak'ik'a yau ina al'fahari da kai, kuma na tabbatar yau da mahaifinku na raye zaiyi al'fahari da kai , domin ka cika d'a na gari d'a na hallas tabbas yau kasa farin ciki a zuk'atan iyayen rik'onku kai da d'an uwanka domin wannan abin da kayi zai sama musu nitsuwa a zuk'atan su ta yadda zasu samu k'arfin guiwar cewa ko bayan ransu zaka kula musu da y'ar su bisa amana da gaskiya, naji dad'i da samun yara nagari Umar Farouq da Usmanu shehu Allah ya muku al'barka ya k'ara muku k'aunar juna Allah ya sanya al'khairi a rayuwar Ku." Murmushi suka rink'a yi zuk'atan su cike da farin ciki da aminci jin irin addu'oin da mahaifi yarsu ke musu, Hamma Umar kuwa k'ara jawo Usman yayi jikin shi , shi kuma kanshi ya kara kontarwa kan cinyar Ammin sun, Hajjajo da Inna ma Addu'a sukayi tayi musu da sanya al'khairi da sa musu al'barka. Anty Halima kuwa tunda ta kamo hannun Ummul suka koma cikin gida kai tsaye d'akin Nenne ta wuce da ita, tana shiga ta saki hannun Ummul taje bak'in gado ta kifa guiwowin ta a k'asa kanta ta kife kan cinyar Nenne cikin kuka mai cike da tausayi murya a raunane baki na rawa tace. "Nenne Hamma Umar ya bani tausayi Nenne kiga irin al'k'awarin da Hamma Umar ya d'auka a kan Ummul Nenne sai kinga yadda Hamma Umar yake kuka cur-cur da hawayen shi ya rugume ya Usman suna ta kuka sun bani tausayi Nenne sun tuno Abban su." sai ta kuma d'ago kanta cikin zubda k'ollah ta kalli Ummul dake ta kuka tamkar zata amayo da ranta cikin sanyi tace. "Ummul ke kukan dad'i kikayi naki kukan najin dad'i ne iyayen ki na raye gaba da baya, bawan Allah Hamma Umar shiko kukan rashin uba yakeyi domin shi yasan zafin rashin Uba dan shi kam ya Usman Hamma Umar d'in ya meye mai gurbin mahaifin su, Hamma Umar bawan Allah maraya duk da tarin k'iyeyyar da kike nuna masa bai hanashi yin al'k'awarin zai rike da amana ba." Daga nan kuma sai ta mik'e ta fice ta nufi part d'in Abban ta, ita kuwa Ummul kuka take da bak'in ciki mai yawa a ranta a fili take gani duk an tsaneta tunda babu ko mai lallashin ta inba Ya Usman ba kowa harara ke had'a su ganin yadda su Anty Shuwa ke cilla mata harara yasa ta mik'e cikin kukan ta nufi part d'in Hajjajo, a parlour ta samu su Hamma Umar d'in da ya Usman dasu Hajjajon da Ammin su, har yanzu Hamma Umar kanshi na kife kan cinyar Ammin yana kuka k'asa-k'asa dan gaba d'aya jikin shi da zuciyar shi Abban shi kawai suke tuno mishi a yau d'in, shi kuwa Usman kukan Hamma Umar ne yake sashi kukan, itama Ammi ta kasa d'aure zuciyar ta sai k'ollah dake ta bin fuskar ta, itama Ummul nata kukan take ta wuce bedroom d'in Hajjajo kai tsaye kan gadon ta konta ta kife kanta cikin pillow taci gaba da kuka, ita kuwa Anty Halima a baki k'ofar parlour Abba tayi sallama cikin muryar kuka, cikin sanyi ta shiga bayan Abba ya amsa mata sallamar , Abban ta samu shida Daddy suna zaune sai fufun goro kusan guda 12 da katon-katon na sweet da k'oren dabino dake gaban su, gefen Abban nata taje ta zauna cikin sanyi ta gaida su sai kuma ta fara magana cikin raunin murya tace. "Abba Hamma Umar! Abba Hamma Umar da ya Usman sunata kuka sun tuno Abban su, Abba Hamma Umar ya bani tausayin Ammin suma sai kuka takeyi, Daddy kuje ku rarrashe su, Hamma Umar ya bani tausayin yanata kuka ya Usman ma yana kuka." kusan a tare Abba da Daddy suka mik'e suka fita kai tsaye parlour mahaifi yarsu Hajjajo suka nufa Anty Halima na biye dasu a baya, suna shiga parlour suka zauna gefen Ammi da yaranta Daddy ne ya jawo hannun Usman cikin kula yace. "Ya isa kukan ya isa haka habba Usman k'afa san zuciyar ka bata da cikekken lafiya." A hankali Usman ya kalli Daddy cikin sanyi yace. "Daddy kalli yadda Hamma Umar yake kuka , hawaye na bazasu bar zuba ba muddin idanun Hamma Umar na zubda k'ollah." Abba ne ya kalli Hamma Umar d'in cikin sanyi yace. "Farouq Kaine nake ganin kana da k'arfin zuciya sai gashi ka k'asa iya daurewa ga yadda kake kuka kalli yadda kukanka yasa d'an uwanka yin kuka kalli mahaifiyarku yadda kuka sata a rud'ani, shin ka manta zuciyar d'an uwanka ne? Farouq a yanzu ba abinda mahafinku keso daga gareku da mu da mahaifiyar mu sai Addu'armu." da sauri yasa hannu ya share hawaye shi cikin k'arfafa zuciyar shi yace. "Abba na bari, Usman kayi hak'uri ka koyi dauriya kajiko d'an uwana?." Kai Usman ya rink'a juyawa tare da goge k'ollah, daga nan su Abba sukayi ta musu nasiha sannan suka fita tare dasu dan jin an kira sallan maggariba, har sun fita gaba d'ayan su , sai kuma ya Usman ya juyo cikin sanyi ya shiga d'akin Hajjajo kai tsaye bak'in gadon da Ummul ke zaune yaje ya zauna cikin sanyi ya zaro hankicif d'in shi ya mik'a mata, bata karb'a ba sai d'ago kanta tayi ta zuba mishi ido cikin kuka tace. "ya Usman shike nan Hamma Umar zai rabani da Mustapha har *Abadan* shike nan nayi ban kwana da farin cikina, ya Usman kalli al'k'awarin da Hamma Umar yayi dan tsabar mugunta ya Usman shike nan Hamma Umar ya zame min k'arfen k'afa Ya Usman kasan ina son Mustapha gashi Hamma Umar ya rabamu gashi Abba na ya kwace woyata shike nan ya Usman ko muryar Mustapha baza a barni Mayo ba, ya Usman Hamma Umar ya binne min rayuwa ba Mustapha ba karatu na." sai kuma taci gaba da kuka, shi kuwa Usman ido ya tsura mata , sannan ya d'ago hannun shi ya dafe kahon zuciyar shi cikin tsura mata ido yace. "Ummul kece sanadin bugawar zuciyata zaki kasheni ki huta ki sani idan na mutu kece sila." cikin tsoro da mamaki ta zaro ido woje baki na rawa tace. "Ya Usman ni kuma? ni dai? in kasheka kuma? sabida me zan kasheka?." Kai ya jinjina mata cikin sanyi yace. "Ehh kasheni kike son yi tunda na lura bazaki bar koke-koken nan ba, na kuma gaya miki bana son inji kina kuka, Kukan ki nasa zuciya ta tayi nauyi bana son kina kira min sunan Mustapha in kina ki ranshi ji nake zuciya tana harbawa da k'arfi, kamar zata fashe." da sauri tasa hannu ta karb'i hankicif d'in sannan ta goge k'ollah cikin rawan murya tace. "Nayi shiru ya Usman na bar kukan , bana son ka mutu." Murmushi yayi sannan yace. "Allah ya d'aiyiba." itama murmushi tayi sannan tace. "Ina sonka ya Usman." cije lips d'in shi yayi da k'arfi sannan ya juya cikin sauri yayi hanyar fita har yaje bak'in k'ofar fita sai kuma ya tsaya cikin sanyi yace. "Allah ya d'aiyiba, nima ina sooon ki k'anwata Ummul." daga nan kuma sai ya fita, part d'in su ya nufa yana zuwa ya samu abokan Hamma Umar d'in duk sunyi al'wala shima al'walan yayi sannan suka nufi masallaci, bayan sunyi sallan maggariba basu dawo ba saida akayi sallan ishah sannan suka dawo gidan. 9:00 pm Hamma Umar ne da abo kanshi suke ta hira a parlour shi hira sukayi sosai cikin shak'uwa da sabo Abdallahn Maryam ne yayi murmushi cikin tsokana ya kalli Hamma Haiydar din Minali yace. "Kai General Aliyu wai ina Hamma Yusuf d'in Aysha ne ban ganshi ba?." Amadin Nadiya ne yayi murmushi tare da cewa. "You ai Hamma Mahmoud d'in Khadija ma ban ganshi ba." Salim d'in Tawa ne yayi murmushi tare da cewa. "Toh sa idawa." Abun batul kuwa murmushi yayi sannan yace. "Mutun da matar sa ai sai adena sa musu ido." Hamma Bashir d'in Rukayya ne yayi murmushi tare da nuna Hamma Hassan d'in Fateema yace. "Kaima ko zaka zillene kayi gaba da matar ka?." Hamma Haiydar d'in Meenarl ne ya d'an yi murmushi sannan yace. "Kai Aisar d'in Bintu sai dariya kawai kake kuma kaima anjima za'a nemeka a rasa zaka tafi gun matar ka." Al'ameen d'in Fauziyya ya mik'e cikin raha yace . "Nima nayi gaba." Ridwan d'in Zakiya kuwa shima sai murmushi yake yana woya da zakiyarsa Ahmad ana Muslim kuma shima dariya kawai yake. Suna cikin hira da dariyar su Hamma Yusuf ya shigo hannun shi rik'e da robobin inabi dasu Apple da reke sai kwakwa da dibino, ajiye su yayi a tsaki yarsu ya zauna gefen Abuturrab cikin murmushi ya kalli Aisar yace. "Ga inabi nan kusha , Aysha ce ta kirani tace in seyo mata shine kuma na kawo muku ku d'ana." dariya sosai Abban Rukky pinky yayi yace. "Aysha ta kiraka ko kai ka kirata." murmushi Hamma Umar d'in Ummul yayi tare da cewa, " Ku dai kuci kar kuyi tone -tone." dariya sukayi baki d'ayan su sannan sukaci gaba da hirarsu, suna hira suna cin lodin fruits din da Hamma Yusuf ya kawo musu, can sai kuma Hamma Umar d'in ya mike cikin sauri Key din motar Aisar ya zara sannan ya fice da sauri yana fita yaje ya lodowa Ummul fruits d'in da yacin gaba d'aya sannan ya dawo gida, Parlour nashi ya shiga inda ya samu su Abu har yanzu suna hira, Amadi ne ya kalleshi cikin tsokana yace. "Kaima Ummul tayi kira ne kaje ko?." murmushi kawai Hamma Umar d'in yayi tare da juya kai sannan ya zaro woyar shi auta Aliyu ya kira, Jim kad'an Aliyu ya shigo rik'e da hannun Hannah yarin yar Hamma Haiydar da Meenarl, robobin fruits d'in Hamma Umar ya mik'a wa Aliyu cikin yana yin aike yace. "Gashi ka kaiwa Ummul kace abokin nane ya seyo mana mukaci shiyasa itama na seyo mata nata." "Toh" Aliyu yace sannan ya karb'i robobin yayi cikin gida, kai tsaye parlour Hajjajo ya nufa, yana zuwa ko ya samu Ummul d'in tana zaune fuska duk a jeme , a hankali ya ajiye mata fruits d'in cikin kula yace. "Anty Ummul sarkin son zak'i gashi wai inji Hamma Umar wai abokin shi ne ya seyo sukaci shine kema ya seyo miki naki." ido ta d'ago cikin tsuke fuska ta buga mishi harara sannan tace . "Bana so ka meyar mai da abunshi." Kallon ta yayi cikin sanyi yace. "Kai Anty Ummul kinfa san ba kyau meda hannun kyauta." K'afa tasa ta ture robobin, Shi kuwa Aliyu hannu yasa ya d'auki robaa inabi guda d'aya ya fice tare da cewa. " ni dai zanci." Hajjajo kuwa tire ta d'auko ta tattara fruits d'in duka ta lodasu kan tiren cikin yin hamdala , ta rink'a nuna wa mutane tana cewa. "Ku gani Ku shida Farouq ya fara cika al'k'awarin d'aya d'aukar wa kanshi." suko sauran mata sai sunyi ta yabawa halin Hamma Umar d'in, ita kuwa Ummul ji take kamar taje ta shak'e shi ya mutu ta huta da bak'in cikin sa, kamar wasa Hajjajo ta dage tana bin d'aki-d'aki tana nuna musu abinda Umar ya aiko wa Ummul harsu abba sai da taje ta nuna musu, Ummul kuwa haka ta kwana cikin k'unci shiko Hamma Umar yana tare da abokan shi.. Washe gari misalin k'arfe 11:00 Am dai-dai dubban al'umma suka shaida daurin auren Umar Ibrahim Umar Shuwa tare da Rabi'atu Hassan Umar Shuwa Ummul kenan, d'aurin auren d'aya samu halartan manya-manyan bak'i kama daga gwamnan Yobe Ibrahim gaidam dan Hamma Umar shine doctor dake duba lafiyar gwamnan nasu na jihar Yobe tare da sarkin su, bayan an gama d'aurin auren ya Usman ne yazo ya rugume Hamma Umar d'in cikin happy yace. "Ina cin farin ciki Yau Allah ya nuna min auren d'an uwana Allah ya tayaka rik'o." murmushi Hamma Umar yayi tare da cewa. " Amin." daga nan abokan shi suka rink'a yi mishi musabaha suna tayashi murna, cikin zugar mutanen dake tayashi muryar ne yaga Mustapha ya mik'a mai hannu cikin sanyi sukayi musabaha sannan Mustapha yace. "Hamma Umar inayi maka fatan al'khairi a Rayuwar auren ka kaida Ummul ina taya ka farin ciki a matsayinna na d'an uwanka musulmi." sai kuma muryar shi ta fara rawa sai hawaye cur-cur a fuskar Mustapha, cikin tausayawa Hamma Umar ya rugume shi a hankali yace. "Mustapha ka gafar ceni na shiga rayuwar ka kai da Ummul Amman bayina bane Mustapha wannan rubutaccen al'amari ne bani da niyar rabaku, su Abba ne suka had'a aurena da Ummul, ku gafar ceni Mustapha domin na zame muku bak'in jakada a Rayuwar ku Mustapha ka gafar ceni." Cikin rawan murya Mustapha yace. "Hamma Umar na yarda da kaddar ta fatana ka rik'e min Ummul bisa amana." kara rugume shi yayi sannan ya sake shi cikin sanyi Mustapha ya juya ya tafi, shiko Hamma Umar haka yayi ta sallama da abokan shi dan duk yaune zasu tafi tunda biki ya kare gashi kuma abokan duk y'an nesane, Hamma Haiydar har Kaduna zai koma Hamma Yusuf kuwa Taraba Hamma Mahmoud Adamawa Yola Hamma Hassan Gombe yayin da Hamma bashin kuwa zai koma kano, haka Hamma Umar da ya Usman suka tsaya a harabar gidan nasu suna ta ban kwana da bak'on nasu, bayan duk sun tafi ne, saura baki matama dake cikin gida duk sun tattafi sai y'an kad'an da suka rege. Da daddare bayan Anyi Sallan maggariba da ishah Abba ya Tara family d'in shi harda Ammi da Inna da sauran mutanen gidan bayan sun zazzauna Daddy ya bud'e musu taron da Addu'a , sannan daga nan Abba kuma yayita musu nasiha mai ratsa jiki da zuciya, Ummul kuwa zuwa yanzu kuka ya zame mata jiki. Bayan Abba ya gama musu nasihar ne ya mik'e tsawon sa gaban Ummul yaje ya tsaya cikin bada umurni yace. "Ummul taso kizo." mik'ewa tayi cikin zubda k'ollah, shi kuwa Abba hannun ta ya kama yaja har gaman Hamma Umar d'in cikin kula ya kamo hannun Umar d'in ya tsaida shi sannan cikin girma da jagoranci yasa hannun Ummul cikin tafin hannun Umar d'in a hankali yace. "Farouq ga matar ka rik'e hannun ta ku tafi gidan Ku." kallon Abban yayi cikin sanyi sannan ya manner tafin hannun shi ya rumtse hannun Ummul d'in kamar yadda Abba ya umur ceshi, shi kuwa Abba Ummul ya kalla cikin tsuke fuska yace. "Kibi mijin ki ku tafi Allah ya baku zaman lafiya." "Amin Amin." sauran mutanen dake wurin suka amsa, shi kuwa Hamma Umar hannun Ummul d'in ya jawo cikin yin k'asa da guiwowin shi suka durk'usa gaban Abba a hankali yace. "Abba nagode Allah ya k'ara zumunci." "Amin Amin." Abba yace tare da shafa Kansu , sannan shi kuma Hamma Umar ya sake jan hannun Ummul gaban Daddy ya mishi godiya a haka ya rink'a jan Ummul suna zagaya wa har suka iso gaban Ammi da Nenne kamar kullum Hamma Umar hannun shi d'aya yasa ya ciro hularshi sannan ya jawo ummul suka durk'usa a gaban su cikin sanyi yace. "Ammi ! Nenne ! nagode Allah ya saka muku da al'khairi." dafa kanshi Ammi tayi kamar ko yaushe sannan tace. "Allah ya sanya haske a wannan Aure naku Allah ya taya ka rik'o Allah yayi muku al'barka." haka tayi ta musu Addu'a sannan tayiwa Abba ma godiya da kyautar y'ar shi d'aya bawa d'an ta. Shi kuwa Umar yana rik'e da hannun Ummul yaje ya rugume ya Usman cikin sanyi da k'aunar k'anin nashi murya na rawa yace. "Kamin al'k'awarin zaka kula da kanka, kasha maganin ka karkaci duk wani abu green kaji B'iyaye na, nanda kwana 5 Kaima zaka koma gidana inci gaba da kula da kai." murmushi Usman yayi cikin yanayin shi na abin dariya yace. "Nayi ma al'k'awarin zan kula da kaina kafin nima na auru matata taci gaba da kula dani, kaima ka kula da matarka Allah ya d'aiyiba." gaba d'ayansu dariya sukayi sannan Abba yace. "Farouq ku tafi dare yanayi." "toh" yace sannan suka rekosu harabar gidan Usman ne ya bud'e musu mota bayan sunyi saida safe sannan Hamma Umar yaja motar suka tafi. Tunda suka shiga motar ummul taci gaba da kukan ta, shi kuwa Hamma Umar tuk'in kawai yakeyi hankalin shi na kan titi haka sukayi tafiyar tasu Ummul daga Potiaskum har cikin Damaturu kuka take batayi shiru ba, suna isa k'ofar gidan ba tare d'aya shiga cikin gidan ba yayi parking sannan ba tare d'aya kalleta ba ya fito gefen da take ya zagayo marfin motar ya bud'e sannan ya jawo hannun ta, ita kuwa sai fizge hannun take tana k'ok'arin kwancewa, shiko sai matse hannun yayi da k'arfi cikin sanyi ya jata zuwa bak'in gate d'in juyawa yayi ya kalleta cikin bada umurni yace. "Ki nitsu kisan abinda kikeyi karki kuskura ki shigar min gida da k'afar hagu , sannan kiyi Addu'a kafin ki shigar min gida, dan na lura akwai shaid'anu a tsakiyar kanki, so ki watsar dasu anan kan titi karki kuskura ki shigar min gidana da su." kai ta sunkuyar cikin zubda k'ollah dan ta tuno Nenne tama ta horeta da tayi addu'ar kafin ta shiga gidan, k'ollah ta zubda sannan a hankali ta d'aga k'afar ta dama wanda kusan a tare suka d'aga k'afafun nasu, a hankali sukayi addu'ar shiga gida sannan suka shiga cikin gidan. A gida kuwa bayan Hamma Umar yaja motar sun tafi, Usman ne ya dafe k'ahon zuciyar shi da sauri jin yadda zuciyar shi ke bugawa da sauri-sauri idon shi ya rumtse da k'arfi lokaci d'aya yaga wani irin duhu cikin k'arfin hali ya juyo ya kalli Nenne sai yayi murmushi ya bud'e baki a hankali yace , "Shike nan yau kam ni kad'ai zan kwana ba Hamma Umar, da safe kuma ba Ummul wazan tsokana?." Dariya su Ammi sukayi mishi sannan suka juya zasuyi cikin gida kenan a dai-dai lokacin Usman yayi wani irin numfashi tare da dafe k'irjin shi yayi taggal-taggal ya fad'i kan kujerun jiki ba..... By *GARKUWAR FULANI* 婵犵妲呴崑鎾跺緤娴犲鐤い鏍仜缁犵喐銇勯幇鍓佺Ф缂佽鲸妫冮弻娑㈠箛閳轰礁顬嬮梺鎸庣⊕閹告瓕鐏嬮梺鎸庣箓閹冲酣寮冲▎鎴犳/闁硅鍔栭悵顏堟煥濞戞ê鏆g€规洘锕㈡俊姝岊檪缂佹唻闄勬穱濠囶敃椤掑倸鍩岄梺鍝ュ櫏閸嬪棙绔熼弴銏℃優妞ゆ劦鍓涚壕楣冩⒑閸涘﹤濮傞柛鏂块叄閺佸秹骞樺鍕洴閺佹劙宕ㄩ鐔割唲缂備胶鍋撳畷妯衡枍閺囥垺鏅柛鎰靛枛缁€鍐煏婵炑冪Ф婢跺嫬鈹戦埥鍡椾壕缂佽弓绮欏畷顖烆敃閵堝拋妫滈梺璺ㄥ櫐閹凤拷 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1闂傚倸鍊烽悞锕傚礈濮樿埖鍋傚鑸靛姇缁狀垶鏌ㄩ悤鍌涘4闂傚倸鍊烽悞锕傚礈濮樿埖鍋傚鑸靛姇缁狀垶鏌ㄩ悤鍌涘 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 婵犵妲呴崑鎾跺緤娴犲鐤い鎰╁€曢ˉ姘舵煣韫囷絽浜剧紒杈ㄦ閺屾盯骞囬埡浣割瀷闂佹寧绋掗幐姝岀亱闂佹寧绻傞幊搴ㄥ汲濞嗘垹妫柟瑙勫姈閻濐亪鏌ㄥ☉妯烘殻鐎规洘锕㈡俊姝岊檪缂佹唻闄勬穱濠囶敃椤掑倸鍩岄梺鍝ュ櫏閸嬪棙绔熼弴銏℃優妞ゆ劦鍓涚壕楣冩⒑閸涘﹤濮傞柛鏂块叄閺佸秹骞樺鍕洴閺佹劙宕ㄩ鐔割唲缂備胶鍋撳畷妯衡枍閺囥垺鏅柛鎰靛枛缁€鍐煏婵炑冪Ф婢跺嫬鈹戦埥鍡椾壕缂佽弓绮欏畷顖烆敃閵堝拋妫滈梺璺ㄥ櫐閹凤拷 *Y'an uwa abokai k'awaye yayu k'anne yara manya maza da mata masoya na da sab'anin haka writers da reedars dan Allah don soyeyyar mu da Annabi ina barar addu'arku ga mahaifiyata bata da lafiya dan Allah kusa min ita a addu'arku da bakunanku masu albarka Allah ya bata lafiya rabbi ya tashi kafad'an ta Allah yasa zakkan jiki ne a wanan gab'ar kuma zan shaida muku ba tabbas kuci gaba da samun posting nan kullum in nasamu nayi fani'imal in ban yiba la'basa nasan zaku min uzuri, DEDDE Am Allah ya baki lafiya 婵犵妲呴崑鎾跺緤娴犲鐤い鏍ㄧ箓閳ь剙鐡ㄦ穱濠囶敃椤掑倸鍩岄梺鍝ュ櫏閸ㄨ泛鐣烽鐐参╅柨鏃囧亹绾鹃箖姊洪崨濠傚闁告柨楠搁埢鏃堟晸閿燂拷* *A baya nace Usman Accounter ne so na batane Usman Lecturer ne a Yobe state university so daga yanzu a lecturer sa zamu tafi dan shine aikin sa na gaskiya* *B*a numfashi ya konta kan kujarar ba inda yake motsi a jikin shi, gaba d'aya su Nenne da Abba dasu Hajjajo a tare suka juyo kanshi ya Adam ne yayi sauri ya tallabo shi jikin shi cikin tsananin firgici ya rink'a juya kanshi yana d'an tab'a fuskar shi cikin d'imuwa yana . "Usman ! Usman ! Usmaaaaaaan! ka tashi ka tashi Usman , Abba Daddy ku gani Usman baya numfashi." Sai kuma ya k'ara rugumoshi jikin shi cikin rawan jiki, Abba ne yasa hannu ya jawo Usman d'in jikin shi cikin k'arfin hali irin na manya ya cewa Daddy. "Hussaini kawo wuruwa." jiki na rawa Daddy ya shiga cikin gidan, Ammi kuwa tunda Usman ya fad'i gaba d'aya sai jikin ta ya fara rawa kar-kar ko ina na jikin ta ya sake k'afafun ta suka k'asa d'aukar nauyin ta zuciyar ta sai bugawa take tara-tara cikin wani irin rashin kuzari ta zame a wurin ta zauna ta jingina da kujaran da Usman yake kai cikin sanyi baki na rawa take cewa. "Ya Allah ka rufa min asiri Allah ka dub'eni da idon rahama Allah ka hanani ganin mugun abu Allah ka jinkirtawa wannan bawa naka kabashi lafiya Usman Allah ya hanani ganin gawarka ganin na mahaifinku ma har yau bai bar idanuna ba." Inna ce ta dafa ta cikin sanyi tace. "Kiyi mishi Addu'a Amina addu'arki gare shi ba hijabi insha Allah karb'ebb'iya ce ." jin haka sai zuciyar Ammi ta kara karaya cikin sanyi ta kontar da kanta a cin yar Innarta ta kamo hannun Usman ta rink'a wani irin kuka mai cike da fargabar faruwar wani abu, Hajjajo ma sai kukan takeyi ya Sadip da Aliyu ma gaba d'aya sun k'asa saida hawaye su Anty Halima kuwa cikin gida ta shiga tana kuka cur-cur, Daddy kuwa yana zuwa ya d'auko goran ruwan mai sanyi ya dawo Abba ya mik'a wa, yana karb'a ya b'alle marfin gorar sannan ya tuttulo ruwan sanyin a tafin hannun shi da k'arfi ya watsa a fuskar Usman d'in, a take sai yayi wani irin ajiyan zuciya mai k'arfi sai kuma yayi shiru numfashi sa na harbaqa , cikin kuka Ammi ta rik'o hannun shi tana. "Usman ! Usman! Usmaaaan!." sai kuma ta fashe da kuka, Shi kuwa can sama-sama yake jin sautin kukan mahaifiyar shi da sauran yan uwa, cikin tsananin mutuwa jiki ya bud'e idanun shi kuma sai ya lumshe su ganin baya ganin su sosai , su kuwa ganin haka yasa Ya Adam ya zaro woyarshi da sauri yace. "Abba bari in kira Hamma Umar yazo ya duba shi." jin hakan yasa Usman d'in ya k'ara bud'e idanun shi cikin rawan. Murya yace. "Ah,Ah a a Adam kar ka gayawa Hamma Umar komai ka barshi , naji sauk'i." meda woyar Adama yayi cikin jin dad'i ya kamashi ya rugume murya na rawa yace. "Usman meyasa kake wasa da lafiyar ka me kake tunawa me damuwarka a duniyar nan Usman?." cikin k'arfin hali ya d'an ture Adam sannan ya d'an jingina da jikin kujerar ya kamo hannun Ammin shi ya kalli Hajjajo da inna dake ta zubda k'ollah yace. "Kai da Allah ni ku dena min kuka lafiyata lau ji tsoffin nan fa aini ras na ke sai namu rakiya kafin nima a min rakiya zuwa gidana na gaskiya, Abba kace su dena kuka ni na worke." Sai kuma ya kalli Ammin shi cikin sanyi yace. "Ammi shi komai da kika gani a duniyar nan toh Rubutaccen al'amari ne so karki damu ki sawa ranki dangana insha Allah ba zakiyi kuka ba matukar Hamma Umar na yana raye, karki damu shi d'aya ne tamkar da mu biyu kinji ko Ammi na." kanshi ta shafa cikin rawan murya tace. "Ku duk ina fatan ku rayu har bayan rayuwa ta." dariya ya d'an yi sannan ya kalli Abba da Daddy dake binshi da ido cikin fidda numfashi mai nauyi yace . "Dan Allah Abba kar a gayawa Hamma na kunga kar hankalin shi ya tashi." Nenne ce ta kalleshi a hankali tace, "Kasha maganin ka yau?." Kai ya gyad'a mata sannan yace. "Hamma Umar ya bani kafin ya tafi." so haka yayi ta basu k'arfin guiwa ya kuwa hanasu su gayawa Umar, a haka sukayi ta mishi nasiha kan shan maganin shi, sannan Abba yace daga yau shi da Adam zasuke kwana tare, haka kuwa akayi, shi kuwa Usman, suna shiga d'akin nasu ya zame ya shiga toilet k'ofar ya maida ya rufe cikin tarin takaici dajin haushin kanshi da zuciyar shi ya kife kanshi jikin gini ya rink'a wani irin kuka maicin rai kuka yake yana d'an dukan saitin kahon zuciyar shi cikin kukan yake cewa. "Kai tona da Wannan zuciya tawa mai zuwa hurumin daba nataba." haka yasha kuka har saida yaji kamar numfashi sa zai yanke sannan yayi al'wala ya fito ya shimfid'a sallaya ya fuskanci gabar, Adam ne ya kalleshi cikin kula yace. "Usman zaka iya tsayuwa ? ka konta mana ka d'an huta." Murmushi yayi cin juya fuskar sa dan baya son Adam yaga idanuwan shi da sukayi jazir suka kumbura, cikin yanayin wasa yace. "Kai nafa fika lafiya kuma zanyi wa Hamma na da Ummul addu'ar Allah ya basu zaman lafiya dakuma 'yan biyu." dariya Adam yayi tare da cewa. "A a yan ukune ba yan biyu ba." Toh hakafa rayuwa tayi ta juyawa Usman kullum yakan b'uya yasha kuka har sai yayi gyatsa ya kuma ji numfashi sa na carkewa sannan ya fito, ba kuma wanda yasan halin da yake ciki. *Gidan Hamma Umar da Ummul kuwa* Bayan sun shiga cikin gida Hamma Umar na rik'e da Hannun Ummul d'in a haka ya jata har bak'in k'ofar shiga cikin asalin gidan bak'in k'ofar parlour ya tsaya key ya zaro a haljihun shi sannan ya bud'e k'ofar cikin bada umurni yace. "Kiyi Addu'a ki kuma shiga da k'afar dama." bata kulashi ba sai k'ollah da take zubda wa sannan tayi yadda yacen, suna shiga cikin Parlour Ummul tayi fizge hannun ta cikin kallon yadda Abban ta ya binne mata dukiya a parlour fuska cike da k'ollah tayi cikin bedroom da gudu tana zuwa shiga ta maida kamar ta rufe kan gado ta fad'a cikin disashewar murya taci gaba da sana'arta, shi kuwa Hamma Umar shiru yayi a parlour ya tsurawa k'ofar d'akin ido yana jin sautin kukan can k'asa-k'asa kai ya juya ya fito kai tsaye motar shi ya shigar cikin gida ya ajiye ta a harabar gidan sannan ya bud'e bayan motar ya d'auko lodojin da ya ciko da abubuwan cin da sha, kai tsaye parlour ya shigo kan dinning table ya ajiye ledojin sannan ya bi d'an corridor dake gefen d'akin da Ummul ta shigan nan ma wani d'aki ne babba wanda yasha gyara da shimfid'u daga dukan alamu dama nanne d'akin da yake rayuwa in yazo Damaturun daga can d'aya b'arin kuma nan ma akwai wani bedroom d'in dan gidane mai yalwar d'akuna parlour ne guda d'aya babba wanda ke d'auke da dinning area mai girma da tsarina sai daga gefen shi wani d'an corridor ne da zai sadaka da kitchen sai sito dake manner a gefen shi, ta bayan kitchen din kuwa d'an k'aramin wurine mai cike da tsirrai masu kyau , cikin parlour kuwa yana d'auke da 3 bedroom, so yana shiga d'akin sa wonka yayi sannan ya fito yayi shirin baccin sa, parlour ya fito cikin nitsuwa yana taku mai cike da haiba a hankali ya jawo kujara ya zauna a dinning table d'in kanshi ya jingina jikin kujerar sannan ya d'ora k'afafun shi kan table d'in yana d'an kad'a su a hankali ida nunshi ya lumshe tare da kamo lips d'in shi ya matse yana jin yadda Ummul ke yin kuka cikin sauti mai cike da rauni da wahala da alamun gajiya daga kuma jin sautin kukan da alamun zazzab'i a jikin ta, ido ya k'ara rumtsewa dan yana jin kukan nata na ratsashi dan window d'akin ta yana ta saitin dinning area d'in, cikin sanyi ya mik'e a hankali yaje bak'in k'ofar, cikin murya mai cike da tausayawa yace. "Khairi kiyi hak'uri ki dena kukan nan ya isa kizo ki bud'e k'ofar kinji kibar kukan kar ya saki zazzab'i ki fito kici abinci kinji ko Khairi?." kukan Ummul ta kuma k'ara yi cikin dishewar muryar tace. "Bazan fito ba, ka barni nayi kukana in banyi kukaba me zanyi ? bazanci abincin ba inya so yunwar ta kasheni kowa ya huta tunda dama ba,a sona." Shiru yayi sannan ya d'an yi ajiyan zuciya tare da cewa. "Khairi baki da lafiya fa ki bud'e kizo kici abinci kisha maganin inyaso kyaci gaba da kukan tunda shi kikeso ." bata kuma kula shi ba haka tayi ta kukan ta yayi ta lallashin ta a banza, haka ya hakura ya barta ya koma bedroom d'in shi ba tare da yaci abincin ba, ita kuwa haka ta kwana kuka har Allah ya wayi gari. Bayan Hamma Umar d'in ya dawo masallaci ne ya zauna a parlour tare da kunna TV ya kama tashar manara idan ya samu sun saka sautin karatu k'ura'ani tare da muryar Ahmad Sulaiman volume ya k'ara ta yadda sautin ya rink'a ratsa cikin gidan baki d'aya kan kujera ya konta ya lumshe ido yana bin sautin karatu hannun shi kuma rik'e da carbi, itako Ummul tunda tayi salla ta konta kan sallayar cikin jin zazzab'i ga ciwon kai kuma ta k'asa barin kukan, a haka tana kukan har bacci ya saceta, shi kuwa bai bar parlour ba sai 9:00 am ya mik'e ya shige kitchen nasu gas ya kunna tare da d'an tafa musu ruwan tea sannan ya sake d'uma kajin daya seyo ajiyan ya had'a musu komai yazo ya ajiye kan dinning d'in , d'akin shi ya shige wonka yayi sannan ya shirya cikin kananan kayan ya fito ras sai k'amshi yake zubawa, kai tsaye k'ofar d'akin ta yazo ya tsaya cikin sanyi yace. "Khairi ! Khairi ! tashi kizo kiyi breakfast." tana jinshi tayi shiru kamar bata jinshi , sai mik'e wa tayi ta zauna ta jingina jikin gado tana jin yadda yake kiranta tayi cib kamar bata d'akin, shi kuwa sai komawa yayi ta jikin window ta ya bud'e glass d'in sannan yasa hannun ya bud'e labulen ido ya zuba bata, itama idon ta zuba mishi cikin nuna kiyayyarsa a fili, kai ya jinjina cikin jin tausayin ta yace. "Khairi taso kizo kinji ko." "Bazan zoba bazan cin abince ba, Na mutuwa mane me ruwan ka?." Kai ya juya tare da cewa. "Meyasa bazaki ciba." a kufule tace . "Sabida na tsane kaa! bana son ka! bana son ganin ka! bana son ko jin muryar ka!." ido ya zuba mata cikin tsananin mamaki da al'ajabi bai tab'a zaton k'iyayyar da Ummul take Mashi yakai matsayin da zata kalleshi ido da ido tace mishi bata sonshi bata k'aunar shiba, muryar tace ta kuma katsemai tunani tana cewa . "Na tsane ka tunda ko yaushe a sana dinka nake azabtuwa." Kallon ta ya kumayi sannan a hankali yace. "Kina son kanki ai?." "Sosai ma dama ina son kaina kam mana." murmushi ya d'an yi sannan yace. "Toh ki fito kici abinci dan ki kula da kanki ni kuma nagode da k'iyayyarki gareni." "Bazan ciba ! ba kuma zan fito ba!." Haka Hamma Umar yake ta fama da Ummul Amman sam tak'i fitowa , zuwa yanzu kuwa kukan har ya gaji da ita dan ba itace ta gaji da kukan ba kukanne ya gaji da ita sai dai tayi ta diri ba hawaye shi kuwa duk kula da tattali yana had'a mata Amman ko fitowa tak'i tayi bataci komai sai ruwan da take sha da fari bata jin yuwar Amman zuwa yau da tayi kwana biyu a hakan sai take jin yunwar kamar zata kasheta inta tsaya sai jiri , tayi wonka kuwa yafi sau 3 wai duk ko zataji k'arfi Amman abin yaci tura a deren kwana na 3 ne ta k'asa bacci dan yunwar dake kwak'ularta. Shi kuwa Hamma Umar gaba d'aya kewar d'an uwanshi ya cika mar jiki da zuciya haka yasa kullum sai sunyi magana a woya a kalla sau 5 zuwa sau 6 duk lokacin shan maganin Usman in yayi sai Umar ya kirashi yace mishi kasha maganin a b'aggaren Ummul kuwa yana damuwa da halin da take ciki. A al'adun shuwa'arab d'in kuwa suna yin wata al'adarsu duk lokacin da akayi Aure aka kai Amariya gidan ta washe gari y'an uwanta zasuje karb'ar tukuici a gun aggo kuma Wannan tukuici ba'a badashi sai aggo ya kusanci matarshi so haka yasa wasu basa zuwa washe garin randa aka kai Amariya sukan bari sai randa tayi kwana 3 ko 7 kuma Wannan tukuici ba'a ba dashi ga amariyar da bata kai budurcin ta gidan mijin taba, so Hamma Umar kuwa yasan da wannan al'dartasu, so yau ya tashi da wuri ya kimtsa ko ina na gidan dan yana tsammanin y'an uwan Ummul zasu zo yau d'in tunda yau kwanan ta uku da zuwa gidan, bayan ya gama komai yayi wonkan shi fes ya fito ya shirya cikin wagamri mai kalar sararin samaniya ya fito ras sai k'amshi yakeyi. kamar kullum yazo bak'in k'ofar d'akin nata cikin sanyi yace. "Khairi ki zo ki bud'e k'ofar nan zakiyi bak'i su Anty Shuwa na zuwa." A hankali cikin wahala da jiri ta mik'e tazo bak'in k'ofar ta bud'e sai kuma ta juya ta koma ta zauna gefen gado tana ta haki hannun ta rik'e da cikin ta, shi kuwa Hamma Umar yana ganin haka ya koma parlour dinning area ya nufa yana zuwa, ya d'auki cup tea ya had'a mata mai kauri sannan ya juyo ya dawo cikin d'akin yana shiga kiran Usman na shiga woyar shi gefen ta yaje ya zauna sannan ya mik'a mata cup d'in cikin kula yace. "Karb'i kisha tea zakiji k'arfi." kai ta juya tare da matse ido ta samu ta zubda k'ollah, shi kuwa woyarshi ya zaro ya amsa kiran yana kallon fuskar ta, gaisawa sukayi da Usman sannan yace . "Kashe maganin ko?." "Eh nasha tun d'azun ma." sai kuma yayi shiru... can kuma yace . "Hamma Umar Ummul fa?." "Gata nan tana ta kuka tak'i cin komai kuma bata da lafiya , gata bari in bata woyar." "Toh" yace sannan yayi shiru yana jin Hamma Umar d'in yana cewa. "Ga Usman yana magana." Karb'ar woyar tayi cikin rawan jiki murya na rawa tace. "Hello ya Usman." A hankali cikin sanyi yace. "Na'ammmm Ummul." Tana jin muryar shi sai kuma ta fashe da kuka cikin kukan tace. "Ya Usman cikina ciwo , kaina ciwo jiri nake ji duhu nake gani ya Usman ni dai zan dawo gida." sai kuwa ta fashe da kuka. shi kuwa Hamma Umar shiru yayi ya zuba mata ido yana sauraron magarda takeyi, shi kuwa Usman a hankali yace. "Ummul kinfi son zuciyata ta fashe ko? Ummul bazaki bar kukan nan ba ko? Ummul kina son inyi fushi da ke ko?." Kai ta rink'a juyawa kamar tana gaban shi sai kuma tasa tafin hannu ta share hawayen ta murya a sanyaye tace. "Ah ah ya Usman bana so kayi hak'uri nayi shiru." Ajiyar zuciya ya sauk'e sannan yace. "Ban yarda ba nasan yanzu haka idanun ki na zubda hawaye kuma ba zakici abinci ba." da sauri tace. "Wallahi nayi shiru kuma na share hawayen kuma wallahi zanci abincin." "Kin tabbata ?." "Ehh wallahi." "Na tabbayi Hamma Umar?." "Ehh gashi ka tabbaye shi." Sai kuma ta mik'awa Hamma Umar d'in woyar tana cewa. "Bani zansha shayin." Mik'a mata cup d'in yayi sannan ya karb'i woyar tashi, yana kallon fuskar ta, shi kuwa Usman dariya ya d'an yi cikin sanyi yace. "Hamma na tayi shiru ko? ta karb'i tea d'in ? ta fara sha ne?" Murmushi yayi tare da cewa. "Ehh ." Dariya Usman ya kumayi sannan yace. "Hamma na kai baka saba lallashin wani d'an adam bayan ni a duniya ba shiyasa ka k'asa sata tayi shiru Hamma dole ka koyi lallashi fa tunda Allah ya had'a ka da Ummul." murmushi kawai yayi sannan yace. "Toh." Bayan ya katse kiran ne ya juyo ya kalli Ummul da tuni ta shanye tea d'in sai zufa keta tsatstsafo mata tako ina sai damk'e cikin tayi tana murk'ususuwa, mik'ewa yayi ya tsaida ta sannan ya rink'a jijjigata har saida yaji tayi gyatsa sannan ya meda ita kan gadon ya kontar da ita, d'akin shi yaje jim kad'an ya dawo hannun shi rik'e da magani , shida kanshi ya bata tasha sannan ta koma ta konta, shi kuwa rafan kud'i ya ajiye mata a gefen ta wanda zasu kai dubu 100 sai kuma wata y'ar counter near yar k'arama sarkace da y'an kunne sai zobe, zoben ya zaro sannan ya kamo hannun ta ya zura zoben a yatsarta dake kusa da y'ar karamar yatsar ta sannan yace. "Gashi insu Anty Shuwa sunzo ki basu wannan kud'in da sark'ar." Harara tayi mishi k'asa-k'asa sannan ta zare zoben ta jefar gefe, shi kuwa parlour ya koma ya zauna, ya zauna kenan su Anty Shuwa suka iso bayan sun gaisa ne sai ya fita shida ya SADIK daya kawo su. Su Anty Shuwa kam tunda suka samu Ummul a konce ba lafiya sai sukayi zaton ta zama cikekkiyar matar aure, yayin da Usman ma tunda Hamma Umar yace mai Ummul bata da lafiya kuma tana ta kuka sai ya d'auka Hamman nashi ya zama oggone a daren jiyan, so haka suma su Anty Shuwa amman Anty Halima ita ta gane sarai ba abinda Hamma Umar yayiwa Ummul kawai ya bada tukuicin ne. haka suka wuni suka yi tayiwa Ummul nasiha ta kuma ci abinci so ta samu tayi k'arfi, sai yamma lis suka tafi. bayan sun tafi kuma ta wore ras ta fito parlour dan a cewarta yanzu lokaci yayi da zata fara gasa Hamma Umar d'in. Da dere yayi Hamma Umar yana d'akin shi bayan ya yayi wonka ya fito yayi shirin bacci har ya konta sai kuma ya mik'e ya nufi d'akin ta yana zuwa ya zauna gefen ta a hankali ya.... *Dedde na Allah ya baki lafiya* By *GARKUWAR FUlANI* 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1⃣5⃣ *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Alhamhadullih jikin Dedde na da sauk'i sosai ta samu lafiya nagode wa Allah daya bata lafiya kuma nagode muku masu kirana da masu turo min messages da yi mata addu'a a groups da masu bina pc, UWA uba wad'an da sukayi tattaki suka zo dubiya duk nagode da addu'oinku gareta ngd matuka Allah bar zumunci 🤝😘😍🤝* *K*allon ta yayi cikin mamaki ganin yadda take konce duk ta duk'unk'une wuri d'aya gaba d'aya ta takura kanta ga kayan jikin ta duk ta konta dasu hatta hijabin kanta bata cireba ta nad'e guiwowin ta har suna tab'a k'irjin ta sai hannun ta data sa ta kame kafad'un ta sannan ta cusa kanta cikin pillow da kaga ganta kasan bacci takeyi amman cikin tsoro duk ta takure hatta numfashi ta da kalan tsoro take fidda sautin shi, gyara zaman shi yayi yana fuskan tarta a hankali yasa hannu tare da kamo hijabin ya fara k'ok'arin zare mata shi a jikin ta, ita kuwa cikin baccin tsoron da tunda tazo gidan a haka take rayuwa cikin tsoro dan ita bata tab'a kwana ita kad'ai a d'aki ba a rayuwar ta gata da tsoro amman kuma k'iyeyyar Hamma Umar d'in ta hanata kusantan inda yake ta gommace ta rayu cikin tsoro, a hankali ta d'an motsa tare da k'ara jawo hijabin nata duk cikin bacci, shi kuwa ganin ta d'an motsa ne yasa ya d'an janye hannunshi yayi shiru yana kallon fuskar ta, can zuwa wani lokacin kuma ya d'an k'ara matsota sannan yasa hannun ya fara zaro hijabin har ya cire shi a kanta, dai-dai sanda ya cire ita kuwa ta bud'e idonta, gaba d'aya jikinta rawa yakeyi tamkar mazari sai wani irin zaro idanu tayi cikin tsoro ta mik'e tare da fizgewa tana tuttureshi, shi kuwa Hamma Umar kamota yayi da k'arfi ya maidata kan gadon pillow ya jawo sannan ya kontar da ita kan pillow sai kuma yasa hannu a hankali ya fara zuge zip d'in rigarta, ganin haka yasa ita kuwa tayi wani irin yunk'uri tare da sa hannu bibbiyu ta tureshi da k'arfi har saida kanshi ya bugi jikin gado da sauri ya dafe kanshi da hannun d'aya d'ayan kuma ya kamota ya rik'e gam, cikin sanyi yace. "Ina zaki je? ki nitsu mana zakiji wa kanki ciwo fa zoki konta ba abinda zai sameki gani a kusa da ke." hannu tasa tana ta kiciniyar b'amb'are yatsun hannu shi cikin tsiwa tace. "Bana so ka sake min hannun na ka fita harkata ba ruwan ka da ni ka barni inje duk inda naga dama kar woni zo ka mak'ale ni kace zaka min dad'in baki ni bana sonka bana son ganin ka." jawota yayi jikin shi cikin tsura mata ido yace. "Bakya sona fa kikace khairi nifa d'an uwan kine." "Eh bana sonka bana son ganin ka na tsanekaaa." lips d'in shi na k'asa ya kamo ya rink'a tsotsa a hankali yana jin zafin kala manta , sai kuma ya k'ara matsota tare da zare rigar sannan yasa hannun yana kunce d'aurin da tayiwa zanin ta, ita kuwa gaba d'aya sai wujijjigashi takeyi tana ta kici niyar kwace kanta amman ta kasa kawai sai ta sunkuyar da kanta tare da kafa bakinta a damtsen hannun shi ta datsa mishi cizo mai zafi dan gaba d'aya ta tsinke da Hamma Umar d'in, yana jin yadda ta dasa hak'oran ta a damtsen hannun shi zafin yana ratsashi madadin ya saketa sai ya k'ara matsota jikin shi ido ya rumtse da k'arfi cikin wani irin yanayi yace. "Zaki kasheni kike so? Ummu kiji tsoron Allah fa meyasa kika zab'i ki azabtar dani bayan kin san ni mijin kine." Ita kam ganin bata da k'arfin kwatar kanta yasa ta saki kuka mai cike da tsoro murya a birkice tace. "Ka sani wallahi ni bana sonka bana son ganin ka, ka fita hanya ta." Ido ya lumshe dan hak'ik'a yana jin ciwon yadda take cemai bata sonshi cikin sanyi yace. " Khairi bakya sona ko ?" "Ehh bana sonka." Kai ya jinjina sannan yace . "Kin dai san ni mijin kine ke kuma matata ce so kin san akwai hak'k'ina a kanki ko? kin kuwa san zaman aure mukeyi ni kuwa ba waliyi bane." tureshi ta k'ara yi cikin kuka tana Jan hijabinta tana k'ok'arin rufe jikin ta murya na rawa tace. "Ni bana sonka kuma ba zaman auren da zanyi dakai dan bazan karya al'k'awarin da nayiwa Mustapha ba ni ka sake ni." ajiyan zuciya ya rink'a sauk'e wa cikin yanayin cushewar tunani ga yanayin canji daya tsinci kanshi a ciki shi da kanshi bai san yana da wannan halittar ba dan a zaton shi da zai iya rayuwa ko ba mace amman gaba d'aya tunda akayi auren yake jin bak'in al'amura a jikin shi, saketa yayi cikin sanyi ya mik'e ya tsaya a bak'in gadon yana mai jin zafin kanshi data gwora da jikin gado da kuma cizon da tayi mishi, hannun yasa ya kamo hannun ta a hankali yace. "Ki dena kwana da bra a jikin ki yana haddasa ciwon k'irjin yana kuma iya jawo cancer ko ya sa miki toshewar numfashin, ki dena kwana da kayan masu nauyi a jikin ki, ki rink'a yin al'wala kafin ki kwanta ki kuma yi addu'ar bacci." Baki ta tab'e cikin jin haushin sa tace. "Nida jikina ba ruwan wani dani inyi yadda nike so kuma dole in kula da kaina tunda ina rayuwa da kai gida d'aya." Murmushi yayi gano wai danshi take kwana a hakan, hannun ta yaja har zuwa cikin bathroom a hankali yace. "kiyi al'wala." baki ta tura sannan tayi al'walar nan ma dan tasan hakan koyarwa ce ta annabi, bayan tayi al'walan suna fitowa ta zauna bak'in gadon cikin tsiwa tace. "Zanyi bacci fa." Kai ya gyad'a sannan yasa hannu ya kontar da ita blanket ya jawo ya d'an rufeta , hannun shi na cikin blanket d'in ya sunkuye kanta a hankali yace. "D'an d'ago bari in cire miki bra d'in." harara tayi mishi k'asa-k'asa cikin tura baki tace. "Ni ai ba karuwa bace." sai ta kuma ture hannun shi sannan ta juyo ta konta ta a kife, shi kuwa Addu'a yayi tare da shafe jikinta kamar yadda ya saba yiwa Usman , sannan ya kalleta ahankali ya juya ya fita, a parlour ya konta tare da son jin d'umin ta Amman yasan hakan bazai samu ba, haka ya kwana cikin halin takura. Haka rayuwa taci gaba da juya musu duk wata kulawa da gata Hamma Umar yanayiwa khairn shi yayin da ita kuwa take ta azabtar dashi , ta yadda baya samun ko magana mai dad'i ma bare ya samu hakkin shi dake kanta duk da yana yawan zuwa inda take amman haka ba abinda yake sama mishi sai azaba da bak'in ciki ko tafin hannun ta bai isa ya murzaba sai yasha bak'ar magana. Yau Monday kuma Yau kwanan su takwas da tarewa kenan, yau tunda sassafe Hamma Umar ya shirya komai tsab kamar yadda yasaba sannan ya shiga wonka sauri sauri ya shirya dan yau zai fita zaije gidan governor dan duba lafiyar shi duk da dai bai gama hutun auren nashi ba amman zaije dan duba lafiyar shi , bayan ya gama shirin shi tsab sannan ya fesa turaren shi mai tarin k'amshi laptop nashi da phone dinshi ya d'auko sannan ya fito parlour kan dinning table ya ajiye su , sannan ya jawo cups guda biyu tea ya had'a , sannan ya d'an juya rik'e da cups d'in ya nufi cikin parlour gaban Ummul d'in ya d'an tsaya cikin sanyi yace. "Khairi taso kisha tea sauri nake zan fita yanzu zan dawo." kallon shi tayi sannan ta kalli yadda tea d'in yake ta tiriri da alamun ruwan yana da zafi sosai ido ta lumshe cikin jin dad'in shawarar da shaid'an ya kawo mata fuskar shi ta kuma kalla cikin mugunta ta mik'e ta tsaya a gaban shi, hannu tasa ta karb'i cup d'in tare da tsura mishi ido, shi kuwa kanshi ya sunkuyar tare da d'an juya tea spoon d'in dake cikin cup d'in, itako murmushi mugunta tayi, cup d'in ta d'ago tare da watsa mishi ruwan zafin a fuskarsa , ba zato ba tsammani yaji ta watsa mishi tea d'in a fuskar da jikin wani irin zafi da rad'a d'i yaji yana ratsashi, jin zafin ruwan daya sauk'a a jikin shi yayi wani irin yunk'uri ya hankad'ata da k'arfi saida ta fad'i k'asa, sai kuma cup d'in hannun shima ya sub'uce yayi k'asa, hannun shi ya rink'a yarfawa yana d'an jujjuya kai yana jin zafin na ratsa fatarshi har cikin zuciyar shi yake jin zogin, a take fuskar shi tayi jazir sai zufa keta keto mishi tako ina, ita kuwa Ummul yana tureta tana fad'uwa ta kife kai tare da sakin kuka, kuka ta saki da k'arfi shi kuwa jin kukan yayi sauri yayi kanta yana zuwa ya d'ago ta ya sa hannu biyu ya rik'e kafad'un ta ido ya zuba mata cikin wani irin yanayi ya lumshe ido murya a sanyaye yace. "Kiyi hak'uri Ummulkhari bawai na tureki dan zafin ruwan da kika watsa min bane, a a wallahi na tureki ne dan kar ruwan ya fantsalu ya dawo jikinki ya k'onaki , kiyi hak'uri." Ido Ummul ta zuba mishi tare da k'ara sautin kukan nata tanayi tana mita, a cikin zuciyar ta kuwa tabbas ta cika da mamaki har cikin ranta taji mamakin yanayin da Hamma Umar keyi mata magana a yanzu bayan k'onashi tayi sannan kuma shike bata hak'uri har kuma yana cewa ya tureta ne dan kar itama ta k'one, kuma a zahiri da kaga fuskar shi kasan yana jin zafin k'unan amman bai bi ta kanshi ba ya tsaya bata hak'uri, shi kuwa Hamma Umar har cikin ranshi bawai ya tureta dan ta watsa mishi ruwan zafin bane kuma yaji zafin yadda ya ture harta fad'i har takai da tana kuka, a hankali ya kuma matsota yana kallon bakinta da take ta kuka da iya k'arfin ta ya lura so take ta tara mishi mak'otan su, kuka take tana. "Allah zai saka min ka rabani da kowa nawa kazo kana azabtar dani na tsane k...!" a hankali ya sunkuyar da kanshi cikin sauri ya manne bakin shi da nata lips d'in ta yayiwa rik'on taushi ida nunshi ya lumshi tare dasa hannun shi d'aya ya zagayo k'ugunta , ita kuwa ido ta zazzaro woje cikin tsantsar firgita da tsoro ga tarin mamaki Hamma Umar ne ke manne bak'in shi da nata , gaba d'aya ya rufe bak'in manata ya hanata kukan bare rakin da takeyi da son tara mishi mutanen, shi kuwa Hamma Umar idon shi a lumshe ya sab'ule lips d'in ta a bak'in shi cikin lumshe ido ya juya ya koma bedroom d'in shi , wonka ya sake yi sannan ya canza kaga , ya fito parlour kan dinning table yaje phone d'in shi ya d'auka kanshi a sunkuye yazo gefen ta ya tsaya yana jin yadda take yin kuka a hankali yace. "Ayyah Khairi kiyi hak'uri kibar kukan nan kinji bari inje in dawo ki gaya min me kike son in miki." mik'ewa tayi ta nufi bedroom d'in tana kukanta na rashin gaskiya, haka ya fita yana mai tuhumar kanshi daya gaza rik'e amanar daya d'auka. Tunda ya fita bai samu ya dawo ba sai 9:34 pm , yana shiga cikin gidan bedroom nashi ya shige wonka yayi sannan ya fito d'aure da towel a parlour ya d'an zauna jin gidan shiru kamar ba kowa a ciki, mik'a yayi tare da lumshe ido tabbas yana buk'atar kulawar Ummul amman haka ya faskara zuwa yanzu ya fara k'asa yin control d'in kanshi, a yanzu kuwa ya gane cewa shi mutunne mabuk'aci mai son kulawar matar sa, a hankali ya mik'e ya nufi d'akin nata cikin sa'a ya samu k'ofar a bud'e take a hankali ya murd'a hannun k'ofar tare da turawa , yana shiga ya haggota kwance kan gadon, k'ofar ya maida ya rufe cikin sanyi ya zauna gefen ta a hankali ya kwanta tare da sauk'e ajiyan zuciya jikin shi ya manna da nata a hankali yasa hannu ya jawota jikin shi , kan k'irjin shi ya kifeta a hankali ya fara shafa gadon bayan ta murya can k'asa cikin rad'a yace. "Ummul khairi ! Khairi ki tashi." ido ta bud'e cikin yunk'uri tare da yin mutsumutsu tana. "Wallahi bana so ni ka fita harkata." A hankali ya k'ara matsota bak'in shi ya saita cikin k'annen ta iska ya d'an hura mata cikin rauni da rawan murya yace. "Ki tausawa min Ummul khairi ki jik'aina ki tallafa min ki bani hak'k'ina Khairi karki zamto silar sani cikin wani hali." tureshi takeyi tana "Ni ba ruwana da halin da zaka shiga in saka cikin wani halin ko kasa kanka ka sakeni in auri wanda nake so kamai kaje can ka nemi wacce zata soka." cikin rawan murya kamar zaiyi kuka yace. "Khairi ki tausayawa mijinki Ummul nifa d'an uwanki ne zakiso na cutu plzz kiyi hak'uri ki amince dani Ummul bazan cutar da keba karki cutar dani ki barni na rab'i jikin ki , in ban rab'eki ba wa zanje in rab'a?." jin yadda yake magana yana cakud'ata da juyata yasa ta rink'a kuka tana birgima har saida ya saketa sannan ya zauna gefen ta yana mai karkarwa, ita kuwa ganin haka ta mik'e ta koma parlour. Daga wannan ranar haka suke rayuwa kullum da salon azabar da Ummul ke shirya wa Hamma Umar d'in shi kuwa gaba d'aya yana rayuwa ne cikin tarin bukarta yayinda hakan ya k'ara bawa Ummul damar juya shi haka kwana ki suna tafi mokonni sunja har sun fara irga watanni, Hamma Umar kuwa har yau baisan menene dad'in aure ba shi kuwa bai iya kai k'araba bare ya kai karanta, Anty Halima na yawan kiran Hamma Umar tace ya Ummul ta nitsu ko? sai yace mata ehh ba komai fa, ita kuwa Anty Halima bata gamsuwa hakan yasa tana yawan zuwa weekend toh hakan yasa kab ta lura da zaman da suke yi. ya Usman kuwa tunda akayi auren yak'i zuwa a cewarsa sai Ummul ta dena kuka, Hamma Umar kuwa rana d'add'aya ne baya zuwa cikin pataskum shida k'anin shi sunyi ta hira yana kula dashi kamar da sukan je gun Amminsu, su wuni. Yau Saturday tun safe Anty Halima da Hajjajo da inna da Aliyu suka shirya zasu je gidan su Hamma Umar d'in , Hajjajo kuwa ta dage sai dai Ya Usman ya kaisu , dolen shi a hakan badon yaso ba ya kalli Hajjajo tare da cewa. "Toh sai ku jirani na shirya ai Hajia Yawo." murmushi tayi tare da cewa. "Zamu jira jeka shirya, dan ni nafi yarfa da tuk'in ka kaida Umaru, Adam gudune dashi Abubakar ko motarsa kamar zai fire in mutun ya shiga." Murmushi kawai yayi ya tafi part d'in su, yana zuwa wonka ya shiga amman ya kasa sai kife kanshi da yayi a jikin gini ya rink'a wani irin kuka mai cin rai zuciyar shi na harbawa da k'arfi zuwa yanzu Ya Usman shi kad'ai yasan idan yayi tarin yakan ga jini amman yak'i gayawa kowa dan ya naga shi lokacin sane ya kusa. Haka yasha kukan shi sannan ya shirya ya fito suka tafi idanun shi na cike da begen ganin Ummul d'in. A gidan Hamma Umar kuwa yau kwana yayi cikin takura haka ya wayi gari a buk'ace bayan ya dawo masallaci d'akin shi ya wuce da niyar ko zai samu yayi bacci amman ina baccin yak'i zuwa, dole ya fito ya nufi d'akin nata yana shiga ya haggota tana zaune bakin gado cikin sanyi ya zauna gefen ta, shiru yayi yana kallon ta, ita kuwa tab'e baki tayi tare da harara shi k'asa k'asa dan ta rigada tasan damuwar shi ita kuwa ta naga ta nan zata cuzguna mishi, ajiyan zuciya ya sauk'e tare dasa hannun shi ya kamo nata cikin rawan murya yace. "Ina cikin matsala dan Allah ki taimaka min wallahi na fara cutuwa da rashin kulawar ki Ummul." cikin ko in kula ta mik'e taje gaban dressing Mirror ta tsaya tana gyara gashin kanta, mik'ewa yayi tare matsowa bayan ta suna kallon juna ta cikin madubin hannun shi yasa ya tattara gashin nata a hankali yace. "Ki tsammin aron lokacin ki da jikin na d'an wani lokacin ta haka zaki ceci lafiya ta." juyawa tayi a tsiwace zatayi magana kenan ya fizgota jikin shi, cikin rawan jiki ya had'e bakin su wuri d'aya, ido Ummul ta zare jin yadda Hamma Umar d'in yake mata wani irin hort kissi , cikin zafin nama ta tureshi ta koma jikin mirror ta tsaya tana rawan jiki tare da kallon yadda Hamma Umar d'in ya birkice gaba d'aya lips d'in shi sunyi jazir sai shek'i suke ida nunshi ma sai shek'i suke alamun sun ciko da k'ollah, ido ta kuma zarowa ganin ya zare jallabiyan jikin shi ya nufi kanta yana cewa. "Zan karb'i hak'k'ina Khairi tunda na lura baki da tausayi so kike ki kashe ni." kai ta rink'a juya mishi tana cewa. "Karka matsoni wallahi bana so." Bai kulata ba sai k'ara matsota yakeyi ganin haka yasa cikin sauri ta lalubo kolban turaren dake kan mirror, tana nuna mishi tana cewa. " karka isoni Hamma Umar ka fitan min a d'aki." bai kulata ba don shi a zaton shi ko buga mishi kolbar zatayi, ita kuwa yana iso ta cikin tsoro da mugunta ta saiti idanun shi ta dannan bak'in turaren feesssh sai cikin I.... By *GARKUWAR FULANI* 濠电姷顣藉Σ鍛村磻閹捐泛绶ゅù鐘差儏閻ゎ喗銇勯弽顐粶缂佺姷鍠愰妵鍕箛閸撲胶肖缂備浇椴稿Λ鍐蓟濞戙垹绠涢柍杞扮椤姊洪幐搴b姇闁瑰憡鐡曢悘瀣⒑閹稿海绠撻柟鍐查叄瀵啿鈻庨幋鐘筹紡闂佺顫夐崝鏍偟椤忓牊鐓ユ繛鎴灻弳锝団偓瑙勬礃閿曘垺淇婂宀婃缂備焦鍞婚梽鍕┍婵犲浂鏁冩い鎺戝€搁崺宀勬⒑閸濄儱娅忛柛瀣缁旂喖寮撮姀鈩冨劒濡炪倖鍔﹂崜娑氬妤e啯鈷戦柛娑橈工婵倿鏌涢弬鍧楀弰闁轰礁绉归獮妯侯熆閸曨剛娲撮柡浣瑰姍瀹曘劑顢橀悢鍓插敳缂傚倷鑳堕崑鎾崇暦濡 鏋嶉柡鍥ュ灪閺咁剟鏌涢幇闈涙灈缂佲偓閸愵喗鐓忓┑鐐戝啰肖濠㈣泛瀚埞鎴﹀煡閸℃ぞ澹曠紓浣藉紦缁瑥鐣烽鐑嗘晝闁靛牆鎷嬪Λ婊堟⒑鐠恒劌娅愰柟鍑ゆ嫹 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1闂傚倸鍊搁崐鐑芥倿閿曞倸绀堟慨妯垮煐閸嬪倸顭块懜闈涘缂佺媭鍨堕弻銊╂偆閸屾稑顏�6闂傚倸鍊搁崐鐑芥倿閿曞倸绀堟慨妯垮煐閸嬪倸顭块懜闈涘缂佺媭鍨堕弻銊╂偆閸屾稑顏� *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 濠电姷顣藉Σ鍛村磻閹捐泛绶ゅù鐘差儏閻ゎ喗銇勯幇鈺佲偓鏇⑺夊鑸电叄闊浄绲芥禍鍓х磼鏉堛劍顥堥柡灞剧洴楠炲洭鍩℃担鍓茬€烽梻浣瑰缁嬫帡骞愬宀€浜遍梻浣瑰缁诲倿骞婃惔銊ユ辈婵炲棙鍨瑰Λ顖炴煙鐟欏嫬濮堥柣婵愪邯閺屻劌鈽夊Ο鐑樻閻庤娲橀敃銏′繆濮濆矈妾紓浣瑰敾闂勫嫭绌辨繝鍥舵晝妞ゆ帒鍊搁崺宀勬⒑閸濄儱娅忛柛瀣缁旂喖寮撮姀鈩冨劒濡炪倖鍔﹂崜娑氬妤e啯鈷戦柛娑橈工婵倿鏌涢弬鍧楀弰闁轰礁绉归獮妯侯熆閸曨剛娲撮柡浣瑰姍瀹曘劑顢橀悢鍓插敳缂傚倷鑳堕崑鎾崇暦濡 鏋嶉柡鍥ュ灪閺咁剟鏌涢幇闈涙灈缂佲偓閸愵喗鐓忓┑鐐戝啰肖濠㈣泛瀚埞鎴﹀煡閸℃ぞ澹曠紓浣藉紦缁瑥鐣烽鐑嗘晝闁靛牆鎷嬪Λ婊堟⒑鐠恒劌娅愰柟鍑ゆ嫹 *S*ai cikin idanun shi, da k'arfi ya rumtse idanun tare dasa hannu ya damk'e kanshi da hannu. bibbiyu kai d'in ya rink'a juyawa tare da yin layi cikin wani irin azaban da bazai misal tuba gaba d'aya jikin shi b'ari yakeyi duk ta inda hudar gashin jikin sa yake zuface ke tsatstsafowa kwayar idanun shi tamkar zasu zazzago su fad'o k'asa ji yakeyi tamkar rushin wuta aka cusa mai a cikin idanun, ba abin da jikin shi keyi sai rawa daya bud'e bakinshi zaiyi magana sai ya kasa sai lips d'in shi suyi ta rawa tamkar maijin sanyi a haka ya rink'a juyu a cikin d'akin har yaje bak'in gado lokaci d'aya kuma ya rink'a murza kanshi a jikin gadon dan azabar da yakeji, Ita kuwa Ummul da fari murmushi tayi ganin yadda ya rumtse idanun shi jikin shi na rawa, amman zuwa yanzu tsoro ya rufeta ganin yadda Hamma Umar d'in yake cikin azaba da gigita gefe ta tsaya jikin ta na rawa cikin tsoro a hankali ta fara cewa. "Hamma! Hamma!." Yana jinta amman bashi da damar amsawa ba abinda yake yi sai murzan kan nashi da yakeyi, cikin dauriya da k'arfin hali ya d'an bud'e idon ihu Ummul tayi cikin firgicin ganin yadda kwayar idanun nashi sukayi jazir tamkar zasuyi aman wuta sun fiffito woje sun hargitse, shi kuwa Hamma Umar bud'e idon daya d'an yi sai da yaji k'ahon zuciyarshi tamkar zata dare dan iskar da ta d'an shiga cikin ido cikin sauri ya sake rumtse idanun ya k'ara danna kanshi a kan gadon, Ummul kuwa gaba d'aya ta tsinke sai kuka ta saki da iya k'arfin ta tana kiran shi tana, "Hamma Umar ka tashi! ka tashi mu tafi hospital. " Ganin yadda gaba d'aya ya fara sakewa ne yasa ta sake sakin wani k'ara mai k'arfi. Dai-dai lokacin Ya Usman kuwa yayi parking a harabar gidan jin yadda Ummul ke kuka da k'arfi yasa cikin zafin nama ya fito da sauri ya nufi cikin gidan yayin da Aliyu ke binshi da gudu, suna shiga parlour Ummul kuwa tana fitowa a nufin ta zata d'ebo mai ruwan sanyi ya woke idon, ganin ya Usman d'in ne tayi sauri taje gareshi cikin kuka da tsananin tsoro da firgici ta rik'e hannu Usman tana buga k'afafun ta da k'arfi tana kuka murya na rawa take cewa. "Ya Usman Hamma Umar! ya Usman Hamma Umar." shi Usman har ga Allah a zaton sa ko laifin tayiwa Umar d'in ya d'an razanata shiyasa take kuka, Aliyu kuwa tunda yaga yadda take kukan kawai sai ya nufi d'akin da take ta nunawan, ya shiga ya haggo Hamma Umar d'in yadda yakeyi da gudu ya juyo parlour cikin tsoro yace. "Ya Usman Hamma Umar baida lafiya fa zo kaga yadda yake." dai-dai lokacin kuma su Inna da Anty Halima da Hajjajo suka shigo jin abin da Aliyu ke fad'a yasa suka nufi cikin d'akin, suna shiga Usman ya tallabo d'an uwanshi a jikin shi cikin rawan murya da bugawan zuciya yace. "Hamma na! Hamma Umar ! d'an uwana ! me yake faruwa da kai Hamma Umar kayi min magana Hamma Umar meke faruwa?." Anty Halima ce cikin rawan jiki ta kira doctor Abbas abokin Hamma Umar d'in, sannan ta juya ta kalli Ummul dake ta zare ido jiki na rawa alamun rashin gaskiya cikin tuhuma Anty Halima ta buga mata tsawa tare da cewa. "Ki baryi mana kuka ki gaya mana meke damun shi me ya sameshi?." jikin Usman ta kuma matsowa ta kalli Hajjajo da inna da suke ta kuka, Aliyu kuwa gaba d'aya jikin shi rawa yake ganin yadda jikin Hamma Umar d'in ke rawa, tsawa Halima ta kuma buga mata cikin watsa mata harara, k'ara rik'e hannun Usman tayi, shi ma Usman da yake rugume da d'an uwanshi cikin rawan murya yace. "Ummul me ya samu Hamma Umar? meke matsa ciwon?." k'ara rik'e hannun Usman d'in tayi cikin rawan murya tace. "Ya Usman idonshi ne yake mai ciwo." cikin mamaki da k'arin tuhuma Anty Halima tace. "Me ya samu idanun nashi? yaushe ya fara mishi ciwo? me a cikin idanun ? nasan dai Hamma Umar baida ciwon ido, Amman ji yadda yakeyi kamar Wanda maciciji ya tsirta mishi dafi a cikin idon, me ya samu idon ina tabbayarki kinyi shiru." baki na rawa tace. "Turarene a cikin idon." gaba d'aya kusan a tare suka zare ido woje cikin tsoro sukace "turaren kuma?." "Ehh." ta basu amsa tana rawan murya. jin haka Usman ya rugumoshi cikin sauri yace . "Aliyu jeka bud'e min mota mu tafi asbitin su." Aliyu har ya mik'e Hajjajo ta kalesu cikin sauri tace. "Usman ajiye shi maza d'auki makullin motarka yanzu kaje laying FULANI ka seyo mana madarar shanu wanda ba'a tafasa ba daga nan ka biya Islamic kemis ka seyo zam-zam." cikin juya kai Usman yace. "Hajjajo wad'an nan abubuwan me zasuyi mu tafi asibiti kar turaren nan ya kashe mai ido." Inna ce ta kalleshi cikin k'arfin guiwa tace. "Ajiye shi ka gudu yanzu ka seyosu." toh yace tare da kontar da Hamma Umar d'in sannan suka fita da sauri shida Aliyu, kai tsaye layin filoli sukaje sukayi sa'a kuwa suka samu d'anyen madarar shanun daga nan suka seyo zam-zam sannan suka nufi gidan, a gidan kuwa doctor Abbas yazo tun bayan fitan su Usman amman Hajjajo ta hana a sa mishi komai, dole Dr ya hakura yana jiran dawowan su Usman , su Inna da Hajjajo kam gaba d'aya basuyi tunanin ya akayi turaren ya shiga idanun shi ba, Anty Halima kuwa tun tuni ta zargi k'anwarta bare da taga kolban turaren a tsakiyar d'akin. Su Usman na dawowa Hajja tace, a had'a zam-zam d'in da madarar shanu a bashi yasha , haka suka had'a suka bashi yasha, a hankali ya fara jin zogin da zuciyarshi keyi yana raguwa, sannan ta kamo hannun shi cikin sanyi tace. "Farouq." cikin rawan murya yace. "Na'am." "Alhamdulillah." Inna tace sannan cikin jin k'arfin guiwa tace. "Halima je kitchen nasu ki kawo roba mai d'an girma." "Toh" tace tare da ficewa da sauri , tana kawowa Hajjajo ta ajiye mai robar a gaban shi sannan ta matso da koryar madarar shanun, cikin kula tace. "Ga madarar shanu k'asa hannun ka a ciki ka rink'a d'iba kana wonke idanun ka bud'e idon." "Toh." yace sannan ya sunkuya kan robar ya ciki tafin hannushi da madarar sannan ya sunkuyo da kanshi idanun shi ya manna cikin ruwan madarar shanun sannan ya bud'e kwayar idanun a cikin ruwan madarar, wani irin zafi yaji ya ziyarci ruhinshi da zuciyarshi, gaba d'aya saida ya rink'a karkarwa hannushi d'aya yasa ya kamo hannun Ummul dake durk'ushe a gefen shi wanda shi baisan waya rik'e ba, sannu su Hajjajo suka rink'a jera mishi ya Usman kuma yana zuba mishi madarar shanun a haka duk wanda yasa idanun a ciki sai ruwan madarar yayi bak'i a hankali har ya fara yin ja har ya zamo inyasa idanun a cikin ruwan madarar baya canza launi haka kuwa a take idanun nashi sukayi fari tas, har kaman sunfi da d'in fari, sannan aka mik'a mishi goran zam-zam ya k'ara woke idanun sai gashi sun fito ras, Dr Abbas ne ya kalli doctor Umar Farouq cikin kula yace. "Kana ganina kuwa?." Murmushi Hamma Umar yayi tare da cewa. "Sosai ma kuwa ganina normal har kamar yafi na da." ajiyan zuciya dr Abbas yayi tare da cewa. "Tabbas muna da manyan likitoci a kusa ga magani mai sauk'i gaskiya nayi mamaki tsoffi sun zama likiticin babban doctor Umar." dariya sukayi baki d'aya sannan Hajjajo ta kallesu cikin yin k'arin bayani tace. "Ko maciciji in ya tsirtawa mutun yawunshi a idanun haka akeyi kuma da izinin Allah mutun zaiyi ras haka kuwa ko turaren ko wani abu mai Carmichael zakaga gubar zatabi jikin nonon." Dariya Usman yayi cikin jin dad'i yace. "Aiko munga zahiri." da haka Dr Abbas ya tafi, sukuwa parlour suka dawo suka zauna suna ta jira, Anty Halima kuwa gaba d'aya hankalin ta na kan UMMUL da Hamma Umar ta lura sarai da yadda Ummul ke yawan satan kallon Hamma Umar d'in shi kuwa kamar baima san da ita a wurin ba, hakan yasa ta k'ara zargin Ummul d'in. Anty Halima ce ta shiga kitchen ta fara yi musu girgi, Sai daga baya ta kira Ummul dake zaune kan dinning table ita da Aliyu suna lallatsa laptop d'in ya Usman, ta shiga kitchen d'in ta kalleta a fakaice tace. "Sarauniya kece da bak'in nice da shiga kitchen ko kunya babu kin zauna kina danne-danne, ga maggi ki b'are min, sannan ki wonke fruits dinnan ki kaiwa su Hamma Umar d'in da su Hajjajo." "Toh.' tace cikin sanyi sannan ta fara b'are margin dan ta lura Anty Halima tana tuhumarta gashi sai harara take watsa mata, kuma ta sani in Anty Halima ta gane itace ta fesawa Hamma Umar turaren a idanun shi tohfa ta shiga tara tasan ya Adam zaiji in kuma yaji Abban su zaiji inko sukaji shikenan sai buzunta. tana gama b'are margin ta mik'a mata sannan ta wonke fruits d'in ta shiryasu a pilet guda biyu sannan ta nufi parlour dasu, tana fita Anty Halima ta jawo robar da ta sa mata magin a ciki da niyar zata sa a girkin nata, sai taji robar tana k'amshin turare, k'ara shinshinar robar tayi aiko k'amshin kam rasa taji shi, kai ta jinjina tare da cewa. " ba shakka zargina ya tabbata Ummul ce ta fesawa Hamma Umar turaren a idanun shi." kai ta kuma juyawa tare da cewa. "Ummul banso had'a ki da ya Adam ba amman kin jawa kanki dole in gaya mishi." Ita kuwa Ummul a parlour tana shiga taji Hajjajo da Inna suna. "Wai ni abin mamaki Farouq ya akayi ka fesa turaren a idanun ka? kaiba yaroba." baiyi magana ba sai latsa woyar shi da yakeyi, Ita kuwa Ummul gaba d'aya jikin ta ya d'auki b'ari tana jin tsoron kar Hamma Umar ya fad'i abinda ke faruwa a tsakanin su, Inna ce ta kuma kallon shi cikin tausayawa dan ita tasan Umar da zurfin ciki koma menene ba fad'a zaiyi ba a hankali tace. "Ko garin fese-fesen turaren nan shine yaje ya fesa a idanun shi, tunda shi mutun ne ko yaushe ka jishi da turaren a jikin shi." Usman ne ya girgiza kai cikin kula yace. "A a kam ba yadda za'ayi ya fesawa kanshi turaren a cikin idanun shi ai ba yau ya fara mu'amalan tuwa da turaren ba ." ido Ummul ta kuma zarowa dan ganin kamar duk sun ganeta, sai kallon Hamma Umar d'in take cikin yanayin ya rufamata asiri, stool ta jawo gaban shi shida ya Usman ta ajiye musu pilet d'in fruits d'in sannan ta d'an dago cikin rawan ido da suka ciki da k'olloh alamar ka rufamin asiri, shi kuwa fuska ya tsuke cikin kauda idanun shi a kanta, gaban su Hajjajo taje ta ajiye musu nasu sannan ta zauna tana fuskantar Hamma Umar d'in da alamun neman al'farma, Hajjajo ta kalleshi tare da cewa. "Farouq ana maka magana kayi shiru ya akayi ka fesa turaren a idanun ka." Kai ya juyo cikin sanyi yace. "Ummul ce....!" ido Ummul ta zaro woje cikin rawan jiki sai hawaye car-car a idanun ta, Su Hajjajo kuwa suma ido suka zaro cikin kallon shi sukace Ummul ta fesema turaren?. " Fuska ya tsuke tare da cewa. "Ni kam bance ba kaji tsohuwa fa ki tsaya kiji me zance mana." Usman ne ya tsura mishi ido sannan ya kalli Ummul dake ta rawan jiki ya kuma kalli Hamma Umar d'in da yake kallon ta sai yace. "Toh Hamma Umar muna jinka." Tsuke fuska ya kumayi sannan yace. "Cewa zanyi Ummul ce zata gaya muku yadda akayi na fesa turaren a idanuna." Ummul d'in suka kallah cikin son jin zance sukace . "Ummul garin Yaya akayi ya fesa turaren a idanun shi?." Tsuru-tsuru tayi da ido shi kuwa kallon ta yake yana d'an murmushi yana jiran me zata ce musu, abin mamaki sai yaga Ummul ta gyara zama ta tokk'oshe k'afafun ta ta d'auki apply ta fara ci a hankali sannan tace. "Hajjajo waifa yaje yayi wonka ne ya fito ya zauna gaban mirror toh sai nazo ina taje mishi sumar kanshi ina d'an goge mishi sumar da towel, shine shi kuma yana ta kallona ta cikin madubin ya d'auki turaren wai zai fesa a sumar kan nashi , ya kuma zuba min ido ta cikin madubin a haka ya fesa turare kam cikin manyan idanun shi." Gaba d'aya su Hajjajo kam dariya sukeyi Aliyu ma sai dariya yakeyi, Usman kuwa anan take ya gano akwai wani abu a k'asa, shi kuwa Hamma Umar mamaki ne ya rufeshi sosai yake kallon fuskar Ummul yana mamakin yadda ta zame kanta a abin ta kuma maida abin da salon so lallai mace bata kad'an, Ita kuwa Ummul kallon shi tayi tare da d'aga mai girma d'aya sannan ta tab'e baki. Anty Halima kuwa baki ta cije tare da juyawa ta koma kitchen d'in ta kwaso abinci ta kawo sukayi suka sha sunata jira da dariya. Haka suka wuni har yamma sannan suka shirya suka fito, a harabar gidan Ummul ta kalli ya Usman d'in cikin zubda k'olloh tace. "Ayyah ya Usman nima zan koma gida." lumshe ido Usman yayi yana maijin wani irin yanayi a ranshi a hankali yace. "Toh ai bani zaki tabbaya ba ki tabbaya mijin ki." Aliyu ne yayi maza ya karb'e maganar cikin tsokana yace. "Ba inda zakije Hajia zauna a gidan ki haka kawai ki koma gida kiyi ta takurani, mu yanzu gidan mu ba wurin zaman ki ehe, Allah ko Hamma Umar karka barta." hararan shi tayi tare da kai mishi duka, shi kuwa sai zillewa yayi ya shiga mota, Ita kuwa cikin zubda k'olloh tace. "Hamma Umar inje ko?." murmushi yayi tare da cewa. "A,a kam in kin tafi wazai tayani zama a gidan?." murmushi Hajjajo tayi tace. "Toh kinji ko? kai Usman shiga mu tafi." haka suka tafi suna yiwa Ummul dariya shiko Usman tun a cikin motar ya k'asa tsaida hawaye shi abin ya had'e mishi ga ciwon zuciya ga k'aunar abinda bazai samuba ga tausayin halin da d'an uwanshi yake ciki dan ya gane Ummul na azabtar mishi da d'an uwanshi a hankali ya fara jin numfashi sa na toshewa, a haka suka isa gida, bayan sun sauk'e Inna a gidan ta suna shiga part d'in su ya wuce kai tsaye kan gado ya fad'a kife kanshi yayi ya rink'a wani irin kuka mai cushe numfashi gaba d'aya jikin shi sai rawa yakeyi lokaci d'aya zazzab'i mai zafi ya rufeshi ciwon kai mai tsanani ya rink'a sarawa zuciyarshi sai har bawa take a d'ari 200, haka ya rufe kanshi. Anty Halima Ku suna shiga cikin gidan cikin sa'a ta samu ya Adam yana zaune a parlour Nenne suna hira da ya Sadik da Nenne Aliyu kuwa bayan Hajjajo yabi, Nenne tana ganin su ta mik'e taje tayiwa hajjajo sannan da dawo ta kai mata abinci da ruwa sannan ta dawo parlour ta gun yaran nata shiko Aliyu tuni ya konta a parlour Hajjajo, Nenne na shiga suka zauna sukaci gaba da hira har zuwa d'an wani lokacin, a hankali Anty Halima ta gyara zama ta fuskanci ya Adam da Nenne a hankali tace. "Nenne! ya Adam Ummul zata kashe Hamma Umar watarana in dai ba'a d'auki mataki a kanta ba." cikin kad'uwa Nenne ta nemi k'arin bayani, itako Anty Halima cikin nitsuwa ta yimusu bayanin zaman Hamma Umar da keyi da Ummul da irin azabtar dashi da takeyi. ya Adam kam hatsala iya hatsala ya hatsala gaba d'aya ranshi ya b'aci ji yake kamar ya fire yaje ya tattaka Ummul d'in, Nenne kuwa tamkar tayi kuka dan takaici, ya Sadik ne ya yayi magana . "Nenne Ummul bata da tausayi in an barta da tunanin ta zata lahanta mana d'an uwa, kawai ya Adam ya gayawa Abba asan matakin da za'a d'auka a kanta." rai a b'ace Nenne tace. "Ni so nake Ku dakamin Ita sai ta dawo haiyacin ta." haka sukayi ta fad'a bayan anyi sallan ishah ya Adam ya samu Abban su a parlour shi cikin nitsuwa ya mishi bayani, sosai ran Abba ya b'aci cikin takaici yace. "Adam ka shirya gobe bayan sallan la'asar zamuje gidan Farouq d'in zanyi maganin abin." Haka suka yita tattaunawa kan lamarin. A gidan Hamma Umar kuwa bayan su ya Usman sun tafi, Ummul ta juya cikin kuka tayi cikin gida a parlour Hamma Umar ya same ta, gefen ta ya zauna cikin sanyi ya rik'o Hanna yenta ido ya tsura mata a hankali yace. "Ummul meyasa kike son sani cikin damuwa Ummul nifa d'an uwanki ne nijinin kine fa, ki tausayawa min ki bar kukan nan ki taimaka min na samu nitsuwa dake a matsayin ki na matata." kwace hannun ta tayi cikin kuka ta nufi d'akin ta tana cewa. "Bana sonka na tsaneka." tana shiga ta rufe k'ofar, Shi kuwa haka ya kwana cikin tsananin begen ta da buk'atuwa, koda gari ya waye haka ya wuni a matse gaba d'aya ya k'asa fita ko kofar parlour har zuwa yanzu karfe 3:30 pm, wonka yayi sannan ya kimtsa cikin k'ananan kaya sannan ya fito parlour, yana zama yaji ana buga k'afa cikin rashin kuzari yaje ya bud'e k'ofar, cikin fara'a ya kalli Abba yace. "Abba barka da zuwa ." Sai kuma ya d'an matsa cikin girmamawa yace. "Abba shigo." Sai ya kuma kalli ya Adam murmushi ya d'an yi sannan yace. "Nayi fushi da kai ai tunda kowa yazo kai kak'i zuwa." Murmushi yayi shima tare da cewa. "Gashi nazo ." "Ba kazo badai ka reko Abba dai." A parlour suka zauna cikin happy yaje kitchen ya kawo musu ruwan da juice sannan yaje bak'in kofar Ummul cikin d'an daga murya yace. "Ummul fito munyi bak'i." Tana jinshi rashin sani yasa tayi shiru tana ta shafa mai da murza jikin ta da turaruka dan yanzu ta fito wonka, shi kuwa Hamma Umar gunsu Abba ya koma yana cewa. "Abba tana zuwa." haka wasa-wasa sai da Hamma Umar ya buga mata k'ofa kusan sau 3 ganin haka Abba ya tabbatar da abinda Halima ta fad'a, cikin hikima Hamma Umar d'in ya zagaya ta dinning area d'in su glass d'in window ta ya bud'e cikin yin k'asa da murya yace. "Ummul Abba ne da Adam suka zo." ido ta zaro cikin tsoro jiki na rawa ta jawo katon hijabin ta nayin sallah ta d'aura kan d'aurin zaninta da ta d'aura a k'irji, sannan tayi bak'in kofar zuciyarta na har bawa tara-tara a parlour kuwa ya Adam ne ya mik'e a hatsale yazo bak'in k'ofar cikin d'aga murya yace. "Zaki fito ko sai na shiga na tattakaki?." jiki na rawa ta bud'e k'ofar, tana fitowa ya Adam ya rink'a zuba mata maruka a fuska, Hamma Umar d'in ne ya daka mishi tsawa cikin fad'a yace. "Adam kana da hankali kuwa? me kakeyi haka." Ita kuwa Ummul gaba d'aya jikin ta b'ari yake hannun ta Hamma Umar yaja suka nufi cikin parlour a gaban Abba suka zauna gaba d'ayan su a k'asa kan carpet, Ita kam Ummul ganin kallon da Abba yake mata ga marukan data sha gun ya Adam sai ta mak'ale hannun Hamma Umar d'in tana b'uya a jikin shi, shi kuwa gaba d'aya baiji dad'in dukan da Adam ya mata ba, cikin kaushin murya Abba ya fara magana rai a b'ace. "Ummul wato ni ban isa da keba ko? wato ban kai na baki umarni ki bi shiba ko? Ummul bansan cewa kinfi karfina ba ashe ban isa da keba bansan cewa kinfi k'arfin yimin biyayya ba Ummul ni mahaifinki ni kike tozarta wa ko? ni kike watsawa k'asa a ido?." kuka ta saki cikin rawan jiki tare da k'ara mik'ale hannun Hamma Umar d'in, cikin kuka. "ta rink'a juya kai baki na rawa kuka takeyi sosai cikin tsananin tsoro tace. " Abba na tuba ka gafarce ni wallahi bazan sakeba Abba wallahi zanbi umarnin ka Abba ka isa dani." Kai ya juya cikin yin mata tsawar da saida ta kife kanta a jikin Hamma Umar d'in cikin fad'a yace. "Da na isa dake da bazaki bijirewa umarnina ba dana isa dake da dole kiyi biyeyya ga mijin dana zab'a miki Ummul ina gab da cireki cikin jerin y'ay'ana matuk'ar ba zaki yi biyayya ga mijin kiba." cikin kuka ta k'ara rik'e hannun Hamma Umar d'in cikin rawan baki tace. "Abba ka gafarceni karka tsine min Abba na tuba zanyi biyayya ga umarnin ka." sai ta kuma kalli Hamma Umar d'in cikin tsananin kuka tace. "Ayyah Hamma Umar ka bawa Abba na hakuri na tuba." sai ta kuma kife kanta tana yin kuka mai cikeda tsoro, haka Abba yayita mata fad'a daga k'arshe ya dawo yi mata nasiha ita kuwa sai kuka takeyi, cikin lallashin Abba yace. "Ummul ki sani nayi miki zab'i na gari don son da nike miki, Ummul ki sani al'jannarki tana k'ark'ashin diga-digin mijin ki Ummul zanyi al'fahari da kene in kin yiwa mijin ki biyayya Ummul kiji tsoron Allah ki sauk'e nauyin mijin ki daya rataya a kanki." haka Abba yayi ta mata nasiha, Ita kam Ummul kuka takeyi mai cin rai tana ga dole tayiwa Abban ta biyeyya, haka Hamma Umar kuwa ya rink'a bawa Abba hak'uri, sannan suka tashi suka nufi hanyar fita, har sun fita Adam ya sake dawowa cikin zare ido ya nunata yana cewa. "Wallahi karki ga yau Abba lallashin ki yayi ni kuwa aka hanani dukan ki next time in na sake jin wani abu wallahi b'allaki zanyi kowa ya huta." ya fad'a yana nuna yadda zai b'allatan kuka ta saki da k'arfi, jin kukan ta ne Hamma Umar ya kalli Abba cikin raunin yace. "Abba Adam fa." Murmushi Abba yayi sannan yace koma ciki reki yar ta isa, ka turo min Adam d'in." "Toh Abba mun gode Allah ya kaiku lafiya." yace sannan ya koma cikin gida, yana shiga Ummul na ganin shi da gudu ta dawo gefen shi hannun shi ta rik'e cikin kuka, shi kuwa Hamma Umar k'eyar Adam ya d'an buga tare da cewa. "Fita ka tafi Abba na jiranka , kuma bama son ziyarar ka indai haka zakayi in kazo." murmushi yayi ya fita yana cewa. "Kin dai ji abin da nace." yana fita Hamma Umar ya maida k'ofar ya rufe, cikin yana yin lallashin da tsananin shauk'i da jin wani irin yanayi na ratsashi ya jawo Ummul ya rugume... [truncated by WhatsApp] 婵犵數濮烽。钘壩i崨鏉戠;闁规崘娉涚欢銈吤归悩宸剰闁汇値鍠楅妵鍕冀椤愵澀绮剁紓浣哄Х閸犳劙濡甸崟顖氱疀闁告挷鑳惰倴缂傚倷娴囨ご绋课涢崘顔艰摕婵炴垯鍨圭粻娑㈡煃鏉炴壆顦︽い顒€顑夊娲箰鎼达絺濮囬梺鐟版啞閻℃洟鎮樼€n喗鈷戦柟绋挎捣缁犳捇鏌熼崘鏌ュ弰鐎殿喖鍟块埢搴ㄥ箣閻樼绱¢梻浣侯攰椤宕濋弽顓熷仧妞ゅ繐鐗婇悡銉︾箾閹寸伝顏堝汲閿濆洠鍋撶憴鍕闁挎洏鍨烘穱濠傤潰瀹€濠冾€夌紓鍌欑劍閸炲姊介崟顒傗攳濠电姴娴傞弫鍐┿亜閹烘垵鈧悂宕哄畝鍕拺闁告縿鍎卞▍蹇涙煕鐎n亝顥炵紒鏃傚枛瀵挳濮€閳╁啫鍔掓俊鐐€栭崝锕傚礈濞戞艾顥氬Δ锝呭暞閳锋垿鏌涘☉姗堝伐濠殿喖鍊块弻娑㈠棘閸ф寮伴梺杞扮缁夊綊鐛Ο渚唵闁告洦鍓涘ú鎾煛娴g懓濮嶇€规洏鍔戦、姗€鎮㈤崜鎻掓暢缂傚倸鍊烽懗鍫曞磻閹惧磭鏆︽俊顖濄€€閺嬪秹鏌¢崶銉ョ仾闁哄拋鍓熼弻娑㈠箛闂堟稒鐏堢紓浣插亾闁告劦鍠楅悡蹇撯攽閻愭垵鍟拌倴婵犮垼娉涚€氼剟鍩為幋锕€鐓¢柛鈩冦仦婢规洜绱撴担钘夌处缂侇喗鐟ラ悾鐑筋敍閻戝棙鏅濋梺闈涚墕閹峰螞濠婂牊鈷戦悹鎭掑妼濞呮劙鏌熼崙銈嗗 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閻戣姤鍊块柨鏇炲€哥粈鍫熸叏濡灝鐓愰柛瀣€搁…鍧楁嚋闂堟稑顫岀紓浣哄閸ㄥ爼寮婚妸鈺傚亞闁稿本绋戦锟�7闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閻戣姤鍊块柨鏇炲€哥粈鍫熸叏濡灝鐓愰柛瀣€搁…鍧楁嚋闂堟稑顫岀紓浣哄閸ㄥ爼寮婚妸鈺傚亞闁稿本绋戦锟� *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 婵犵數濮烽。钘壩i崨鏉戠;闁规崘娉涚欢銈吤归悩宸剰闁汇値鍠楅妵鍕箛閳轰讲鍋撻弴鈶哄顫濋懜鐢靛弰闂婎偄娴勭徊鑺ョ閸撗呯<閺夊牄鍔嶉ˉ鍫ユ煛鐏炲墽娲存鐐叉喘閸┾剝鎷呴崜鑼偓鐑芥⒒娴g懓顕滅紒瀣浮楠炴劕顫㈠畝鈧禍閬嶆⒒娴g懓顕滅紒璇插€块獮濠冩償閵娿儲杈堝┑鐐叉閸ㄧ懓螞椤栫偞鐓欓悷娆忓婵牓鏌e┑鎰偗闁哄被鍔岄埥澶娢熼悜妯活啋闁诲氦顫夊ú姗€鏁冮姀鈥茬箚婵繂鐭堝顏嗙磽娴g懓鏁鹃梻鍕缁岃鲸绻濋崶鑸垫櫇濡炪倖甯掗崐鎼佸春瀹€鍕拺闁告縿鍎卞▍蹇涙煕鐎n亝顥炵紒鏃傚枛瀵挳濮€閳╁啫鍔掓俊鐐€栭崝锕傚礈濞戞艾顥氬Δ锝呭暞閳锋垿鏌涘☉姗堝伐濠殿喖鍊块弻娑㈠棘閸ф寮伴梺杞扮缁夊綊鐛Ο渚唵闁告洦鍓涘ú鎾煛娴g懓濮嶇€规洏鍔戦、姗€鎮㈤崜鎻掓暢缂傚倸鍊烽懗鍫曞磻閹惧磭鏆︽俊顖濄€€閺嬪秹鏌¢崶銉ョ仾闁哄拋鍓熼弻娑㈠箛闂堟稒鐏堢紓浣插亾闁告劦鍠楅悡蹇撯攽閻愭垵鍟拌倴婵犮垼娉涚€氼剟鍩為幋锕€鐓¢柛鈩冦仦婢规洜绱撴担钘夌处缂侇喗鐟ラ悾鐑筋敍閻戝棙鏅濋梺闈涚墕閹峰螞濠婂牊鈷戦悹鎭掑妼濞呮劙鏌熼崙銈嗗 *T*a tsam a jikin shi hannun shi yasa yana shafa gashin kanta d'aya hannun kuma ya zagoyo bayan ta yayinda ya manna kanta a wuyan shi ya d'an d'aga kanshi sama kad'an yana jin yadda take fidda sautin kukanta cikin tarin bak'in ciki, itama Ummul yau rashin ya Usman mai lallashin ta a kusa ga abin kuka an mata ga ba kowa hakan yasa ta lafe a jikin Hamma Umar d'in ta d'an sa hannu ta zagoyo k'ugunshi da bayan shi ta manna k'irjin ta da nashi tayi luf ta d'an d'aura hab'ar fuskar ta a damtsen hannun shi k'afafun ta kuwa kan nashi k'afafun ta taka ta tsaya ta yadda gaba d'aya a jikin shi take mak'ale gaba d'aya jikin ta tsuma yake tanayin wani irin kuka mai sanyin sauti, shi kuwa gaba d'aya tausayin ta ke ratsashi har cikin ranshi musamman yazu da yaga yadda ta lafe a jikin shi shid'in da ta tsana tana kuka, k'ara rugume ta yayi yana sauk'e ajin zuciya tare da lumshe ido, a hankali ya fara d'aga k'afafun shi wanda nata k'afafun suke a kan nashi a haka ya rink'a tafiya da ita a hankali tana manne a jikin shi tayi luf sai kuka takeyi tana k'ara mak'ale shi, a hankali ya shiga cikin bedroom da ita a hakan, yana shiga ya maida k'afar ya rufe kai tsaye bak'in gado ya nufa da ita cikin sanyi ya matso cikin fridge dake kusa da bak'in gadon yana rugume da itan, ita kuwa tana tsaye kan k'afafun shi ya d'an sunkuyo goran Faro ya d'auka a hankali ya bud'e cikin nitsuwa ya d'an sunkuyo kanta yasa mata bak'in goran murya can k'asa cikin yanayin lallashi yace. "Khairi." ido cike da k'ollah ta kalleshi sai hawaye car-car, shi kuwa ganin hakan yasa mata ruwan sanyin a bak'in ta, ido ta rumtse tare da d'an kurb'an ruwan, saida ta d'an sha kad'an sannan ya zame makin goran ya ajiye a kan fringe d'in a hankali ya zauna bak'in gadon sannan ya jawo pillows yasa a bayan shi a hankali ya konta kan pillows d'in sannan itama ya gyara mata konciyarta a kanshi, ita kuwa har zuwa yanzu kuka takeyi sosai, kai ya rink'a d'an juyawa tare da tsotsar lips d'in shi, idanun shi a lumshe, a hankali yasa hannun shi ya zare hijabin jikin nata ya tureshi gefe, ya rege daga ita sai zanin jikinta, a hankali ya ture d'aurin zanin nata ya d'an yi k'asa ta yadda gadon bayan ta ya bayyana, tattausan tafin hannun shi ya kife a kan k'afa d'unta ya rink'a shafawa tare da d'an bubbugata kad'an-kad'an har zuwa kan bayan ta yanayi cikin alamun lallashi, hakan yasa ita kuwa ta k'ara narkewa a jikin shi cikin tausayawa kanta, a kanshi aka doketa a kanshi aka zageta kuma dashi kawai aka barta a gidan ita kuma tana son a lallasheta dole hakan kuwa tayiwa mahaifin ta biyeyya, shi kuwa jin yadda take fidda sautin kuka da yadda hawaye ke zuba a idanun ta yasa ya d'an d'agota suna fuskantar juna fuskar ta ya d'aura kan tashi fuskar gemun ta kan nashi gemun hancin su na d'an gogar juna hannu yasa ya k'ara matsota jikin shi a hankali ya zaro harshen sa cikin lumshe ido ya d'an laso lips d'in ta da suke ta rawa da shek'i dan kukan da ta keyi, sai kuma ta bud'e idanun ta da sauri ta zuba mishi ido , shima ido ya zuba mata cikin sanyi yace. "Khairi kibar kukan nan haka nan ya isa, kiyi hak'uri ki rugumi k'addarar ki, shin bakya ganin hak'uri shi zaiyi maganin wannan yana yin da muke ciki, Khairi ina son na zame miki gata matukar muna tare zan zame miki GARKUWA bana da nufin cutar dake, ya zanyi k'addara tasa nine silar rabaki da burin ranki, amman abinda nake so ki gane wannan abin da kika gani Rubutaccen al'amari ne tun ina cikin mahaifiyata Allah ya rubuta min kece matata nine mijin ki." sai kuma yayi shiru yana shafa bayan ta, ita kuwa cikin kuka tace, "Hamma Umar nima ina son yiwa iyayena biyeyya na kasa Hamma Umar bani ce nasawa kai k'iyayyarka ba na kasa sonka bana sonka, Mustapha nake so." Rugume ta yayi da k'arfi dan zafin da kalaman ta sukayi mishi cikin zafin ya had'e bak'in ta da nashi cikin lumshe ido yayi mata wani irin zazzafan kissi har zuwa wani d'an lokacin saida yaji tayi luk'us a jikin shi cikin rawan murya kamar mai son yin kuka yace. "Ummul Khairi wata rana ! watara na zaki..! zaki soni, insha Allah watara na zaki soni , na tabbata bazaki dauwa dimun wa da'imu da k'iyeyya ta a zuciyar ki ba, sai dai ko zaki sonki a k'urerren lokaci." kai ta rink'a juyawa murya na rawa tace. "An rabani da wada nake so an had'ani da wanda bana so." sai ta kuma kife kanta a k'irjin shi cikin kuka tace. "Hamma Umar kalli yadda ya Adam ya kumbura min fuskar a dokeni a zageni." hannun yasa ya shafa fuskar tata sannan ya mirgino ta gefe a hankali ya sunkuyo kanta fuskar ta ya rink'a shafawa a hankali cikin taushin murya yace. "Zan rama miki Khairi na kiyi hak'uri da mijin da Allah ya zab'a miki." hannun ta tasa ta kamo nashi ta mana a fuskar ta da tasha marukan ya Adam ciki sanyi ta saki kuka, shi kuwa Hamma Umar daga lallashi salon ya fara can zawa tuni ya fara koyar da ita darrusa masu ratsa jiki tana konce tayi zuru-zuru da ido gaba d'aya jikin ta sai rawa yakeyi hawaye kuwa kamar an b'alle bak'in pompo gaba d'aya ta firgita ga tsoro ga k'iyeyya a hankali ta fara tureshi cikin kuka da rawan jiki da murya tace. "Wayyo Allah na Hamma Umar bana sonka ka barni kar kayi min Katanga da Mustapha." hannayen ta ya kamo ya d'aura kan wuyan shi sannan ya cusa kanshi a k'irjin ta murya na rawa cikin rauni yace. "Bazan cutar da keba Khairi karki cutar dani kiyi hak'uri ki sama min nitsuwa ki tuna hak'ina yana kanki, ayyah Ummul ki amshi kaddararki kinga bamu san me yake boye cikin Rubutaccen al'amarinmu a nan gaba ba Khairi inci darajar aure mana Khairi ki tuna yanzu kika yiwa Abba al'k'awarin yin biyeyya ga zabin da ya miki." kuka ta saki da sauri mai cike da k'una cikin kukan ta k'ara k'amk'ameshi cikin sakin kuka mai d'auke da wuya damtsen hannun shi ta rik'e tare da cusa kanta cikin k'irjin shi, shi kuma Hamma Umar zuwa yanzu yayi nisan kiwo ya shiga duniyar dake cike da al'khairai bayaji baya gani bare ya fahimci halin da take ciki, a wannan ranar a wannan yamma cin daga lallashi Hamma Umar ya am she budurcin Ummul, gaba d'aya jinshi yake cikin tarin farin ciki da nishad'i jinshi yake tamkar an mishi bushara da al'jannah ba abinda yake iya furtawa sai k'amk'ameta ya keyi cikin sauk'e ajiyan zuciya yanata kissing nata tako ina tare da binta da shafa mai cike da tsantsar kulawa da farin ciki gaba d'aya ya kasa magana sai wani shunshunata yake tako ina, ita kuwa kukan abu da yawa take yi kukan wahala daya bata had'i da kukan takaici ga tarin tsanarsa da ta k'aji dan ya rabata da budurcin ta da ta dad'e tana yiwa Mustapha tana dinshi ga bak'in cikin dukan da ya Adam yayi mata ga tsoron fushin da Abban ta yake yi da ita, gashi ko numfashi ta fitar sai taji kamar tana fame ciwon da raunin da Hamma Umar d'in ya ji mata hakan yasa ta saki kuka cikin disashewar muryar tana kai mishi bugu tako ina cikin raunin da take cikin, tana kuka da rawan jiki tana. "Shi kenan Hamma ka cuceni ka zalum ceni na saneka nacema bana sonka!." baya iya gane halin da yake ciki bare ya sarara mata, ganin bai sarara matan ba ga wuya iya wuya tana sha hakan yasa ta rik'o wuyan shi cikin kuka da rauni murya na rawa tace. "Hamma ! Hamma kayi hak'uri na tuba kayi hak'uri Hamma kaina k'afafu na baya na cikina ciwo Hamma zaka kashe niii." sai kuma ta tura yatsun ta cikin sumar kanshi tana murzawa da k'arfi tare da murza kai idanun na zubda k'ollah sai wani irin numfashi take fizga da k'arfi, a haka har zuwa wani lokaci mai tsawo, sannan hankalin Hamma Umar ya fara dawowa jikin shi cikin rawan jiki ya zauna da k'er sannan ya jingina da jikin kan gadon jiki a mace ya jawota cikin shi ya rugume ta tsam a k'irjin shi kanta ya rink'a shafawa har zuwa gadon bayan ta, kanshi kawai yake juyawa yayin da tausayin ta ke ratsa mishi jiki da zuciya yana jin yadda hawayen ta ke zuba a kan k'irjin shi, k'ara matsota yayi cikin wata iriyar muryar da bata tab'a jinshi da ita ba yace. "Ana aspet ya zaujati na, ki gafar ceni Khairi na banyi nufin wahal dake haka ba yana yine ya juya dani har na k'asa control d'in jikina da zuciya ta ki yarda dani banyi nufin jikkata kiba." kukan ma gagarata yayi sai hawaye tana jin wata iriyar kunya mai tarin yawa da bak'in ciki yadda take manne jikin Hamma Umar a gida d'aya d'aki d'aya gado d'aya blanket d'aya sannan kan k'irjin shi fatarta da tashi fatar suna manne da juna duk wani sashi na jikinta ya zama mallakin Hamma Umar ba Mustapha ba , shi kuwa gaba d'aya ya gigice sai kissing nata yake tako ina murya na rawa yake cewa. "Khairi na nagode Allah ya miki albarka Allah ya faran ta miki kamar yadda kika faran tamin Allah ya sanya haske a rayuwar ki." sai ya kuma d'ago kanta ya manna bakin shi a nata yayi kissing na lips d'in ta sannan ya sumbaci goshin ta ya dawo wuyan ta har zuwa k'irjin ta inda nan take ya k'ara susuce wa, hannun shi ya murza kan fatar cikin ta, cikin tsananin happy yace. "Allah yasa nayi ajiyan baby, Khairi ina son inga gudan jinina Allah yasa kin samu ciki a wannan ranar Khairi zaki so d'an da zamu haifa ko? dan Allah shi kam ki sonshi d'an kine jinin kine karki tsane shi, zaki son shi ko??? ."... By *GARKUWAR FULANI* 濠电姷鏁告慨鐑姐€傞挊澹╋綁宕ㄩ弶鎴狅紱闂佽宕樺▔娑氭閵堝悿褰掓偐瀹割喖鍓伴梺姹囧€ら崰妤呭Φ閸曨垰鍐€妞ゆ劦婢€缁墎绱撴担鍝勑ラ柛鐘冲姍婵$敻宕熼姘辩杸闂佸憡鎸烽懗鎯板€寸紓鍌氬€峰ù鍥ㄣ仈缁嬭娑㈠礃椤旇壈鎽曞┑鐐村灟閸ㄥ湱绮诲☉銏$厓閺夌偞澹嗛ˇ锔姐亜椤掆偓椤戝顫忓ú顏勭閹艰揪绲烘慨鍥⒑閻熺増鍟為柣鈩冩礋閹鈧綆鍠楅埛鎴︽煙缁嬫寧鎹g紒鐘虫崌閺岀喖宕橀弻銉ュ及閻庢鍠栭崯鍧楀煝鎼淬劌绠i柣妯碱劜缁憋繝姊绘担渚敯妞ゎ偄顦靛畷婵嬪冀椤撶喎浠у銈呯箰閻楀﹪鎮¢妷锔剧闁瑰浼濋鍫濇辈闁挎繂娲犻崑鎾舵喆閸曨剛顦ㄩ梺鎸庢磸閸ㄧ儤绌辨繝鍌ゆ桨鐎光偓婵犲喚鈧绱撻崒娆戝妽闁哥偛顭峰浠嬪礋椤掑倵鏀虫繝鐢靛Т濞村倿寮崘鈹夸簻闁圭儤鍨甸埀顒佹倐瀹曞搫鐣濋崟顑芥嫼闂佸憡绺块崕鍗炩枍韫囨稒鐓曢悗锝庝簼椤ョ偟绱掗弮鍌氭灈鐎殿喗鎸虫慨鈧柍鈺佸暙閸旀帗淇婇悙顏勨偓鏍礉閿曞倸绀堟繛鎴炶壘椤ユ艾螖閿濆懎鏆為柍閿嬪灴閺屾稑鈽夊鍫濅紣婵犳鍠栭崐鍧楀蓟濞戙垹妫橀柛褎顨呭浼存⒑鏉炴壆顦︾紒澶婄秺閻涱喖螣娓氼垳鍞甸梺鍛婃处閸撴稑煤閹绢喗鐓涘ù锝囨嚀婵秶鈧娲忛崝鎴︺€佸鈧幃銏ゅ礈閹绘帗鏆㈢紓鍌氬€搁崐鐑芥嚄閸洖纾婚柟鎯х-閺嗭附淇婇婵勨偓鈧柡瀣Ч閺岋繝宕堕妷銉т痪闂佸搫鎷嬮崜鐔煎蓟濞戙垹绠涢梻鍫熺⊕閻忓牏绱撴担鎻掍壕闂佸憡鍔﹂崰妤呮偂韫囨挴鏀介柣鎰灥閸熸媽鍊村┑鐘灱濞夋稓鈧凹鍓熼崺鐐哄箣閿曗偓閻擄繝鏌涢埄鍐︿沪濠㈣娲滅槐鎾存媴閽樺澶勭紓渚囧枟閻熴儵鎮鹃悜绛嬫晬闁绘垵妫欓弲婵嬫⒑闂堟稓澧曢柟宄邦儏铻炴繝濠傜墛閳锋垿鎮归幁鎺戝婵炲懏鍔欓弻鐔煎礄閵堝棗顏� *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柣鎴eГ閸婂潡鏌ㄩ弴鐐测偓鍝ョ矆閸喐鍙忔俊顖氱仢閻撴劙鏌涚€n亜鈧悂鈥﹂崸妤佸殝闂傚牊绋戦~宀€绱撴担鍝勵€岄柛銊ョ埣瀵濡搁埡鍌氫簽闂佺鏈粙鎴︻敂閿燂拷8闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柣鎴eГ閸婂潡鏌ㄩ弴鐐测偓鍝ョ矆閸喐鍙忔俊顖氱仢閻撴劙鏌涚€n亜鈧悂鈥﹂崸妤佸殝闂傚牊绋戦~宀€绱撴担鍝勵€岄柛銊ョ埣瀵濡搁埡鍌氫簽闂佺鏈粙鎴︻敂閿燂拷 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 濠电姷鏁告慨鐑姐€傞挊澹╋綁宕ㄩ弶鎴狅紱闂佽宕樺▔娑氭閵堝悿褰掓偐瀹割喖鍓伴梺姹囧€ら崰妤呭Φ閸曨垰绠涢柍杞拌閸嬫捇寮撮埗鍝勵槸椤繈鎳滈悽闈涘及闂傚鍋勫ù鍕緤閼恒儳顩查柛鎾楀懐锛滈柡澶婄墑閸斿秹藟閸儲鐓涢悘鐐插⒔濞插瓨顨ラ悙鍙夊枠闁糕斁鍓濋幏鍛村礈閼碱兘鍋撻悜鑺モ拻濞达絿鎳撻婊呯磼鐎n偄娴鐐村姇椤垹鐣濋埀顒佺闁秵鈷掑ù锝囨嚀椤曟粎绱掔拠鎻掆偓鍧楃嵁婵犲啯鍎熼柕濞垮劜鏉堝牆鈹戦悙鍙夘棡闁搞劎鎳撹灋妞ゆ牜鍋為悡娆撴偡濞嗗繐顏╁┑顔肩墦閺岋絽鈹戦幇顏堝仐闂佸搫琚崝宀勫煡婢跺á鐔兼倻濡椿鍟嬮梺璇叉唉椤煤濮椻偓閺佸啴濮€閳ヨ尙绠氬┑顔界箓閻牆顬婇鍡欑=濞达絿鎳撻弫楣冩⒒閸曨偄顏紒宀冮哺缁绘繈宕堕懜鍨珖婵$偑鍊栫敮鎺楀磹閹间礁鏄ョ€光偓閸曨兘鎷洪梺鍛婄缚閸庡崬鈻嶈箛娑欑厱閻庯綆浜濋ˉ鐐电磼閺冨倸鏋涚€殿喗鎸虫慨鈧柍鈺佸暙閸旀帗淇婇悙顏勨偓鏍礉閿曞倸绀堟繛鎴炶壘椤ユ艾螖閿濆懎鏆為柍閿嬪灴閺屾稑鈽夊鍫濅紣婵犳鍠栭崐鍧楀蓟濞戙垹妫橀柛褎顨呭浼存⒑鏉炴壆顦︾紒澶婄秺閻涱喖螣娓氼垳鍞甸梺鍛婃处閸撴稑煤閹绢喗鐓涘ù锝囨嚀婵秶鈧娲忛崝鎴︺€佸鈧幃銏ゅ礈閹绘帗鏆㈢紓鍌氬€搁崐鐑芥嚄閸洖纾婚柟鎯х-閺嗭附淇婇婵勨偓鈧柡瀣Ч閺岋繝宕堕妷銉т痪闂佸搫鎷嬮崜鐔煎蓟濞戙垹绠涢梻鍫熺⊕閻忓牏绱撴担鎻掍壕闂佸憡鍔﹂崰妤呮偂韫囨挴鏀介柣鎰灥閸熸媽鍊村┑鐘灱濞夋稓鈧凹鍓熼崺鐐哄箣閿曗偓閻擄繝鏌涢埄鍐︿沪濠㈣娲滅槐鎾存媴閽樺澶勭紓渚囧枟閻熴儵鎮鹃悜绛嬫晬闁绘垵妫欓弲婵嬫⒑闂堟稓澧曢柟宄邦儏铻炴繝濠傜墛閳锋垿鎮归幁鎺戝婵炲懏鍔欓弻鐔煎礄閵堝棗顏� *Jama'a ku tayani duba a cikin wad'an nan sunaye ina sukayi kama Aysha Ali Garkuwa da Safiya Abdullahi musa huguma ni dai a ganina basa kama toh amman me yake rikita wasu Reedars da suke zuwa gareni a matsayin nice Safiya Huguma? kuma abin mamaki ko nace musu ba ita bace basa yarda wai sai suce bana dai son yin magana dasu ne, hoh ni Aysha na koma Safiya GARKUWA ta koma Huguma Safiya fans naki na sani ciwon kai ki kawo agaji sun cika min gida duk sun shanye min d'an furana da nono mai sanyi na koresu sunki tafiya wai sai dai na kaisu hareki wayyo ni GARKUWA na karb'i bak'ina na karb'i na Huguma wallahi sunk'i yarda kan cewa ba Huguma bace ban san ina suke samo number ta ba ace musu tak'i ce, Reedars kunji Safiya Huguma itace mai Abadan GARKUWA kuwa itace mai Rubutaccen al'amari Allah yasa Ku gamsu da wannan bayanin na kan pagen ga Ku ruga a guje kuje ga Huguma na tabbata zata karb'eku cikin aminci wlh ni GARKUWA ba nice Huguma ba Safiya ki shirya amsar bak'in ki zan korosu da sandar Fulani zan basu tukuicin man shanu da nono濠电姷鏁告慨鐑姐€傞挊澹╋綁宕ㄩ弶鎴狅紱闂佽宕樺▔娑氭閵堝悿褰掓偐瀹割喖鍓扮紓浣瑰姈椤ㄥ棝骞堥妸銉建闁糕剝顨呴埛鎺楁⒑鐠囧弶鍞夐柛鈺傜墵婵$敻宕熼鍓ф澑闂佸湱鍋撳娆撴偟閺冨倻纾藉ù锝勭矙閸濈儤淇婇銏犳殻鐎殿喛顕ч埥澶愬閻樼數鏉搁梻渚€娼ч…顓㈡⒔閸曨垱鍋熼柨鏇楀亾闁宠鍨块幃娆撳箵閹烘挸鈧垳绱撴担绛嬪殭闁稿﹣绮欓幃妯尖偓锝庡枟閳锋垿鏌熺粙鎸庢崳缂佺姵鎹囬弻鐔煎礃閺屻儱寮伴悗娈垮枟婵炲﹪骞冨▎寰㈠酣顢栫捄銊ф晨濠碉紕鍋戦崐鏍礉閿曞倸绀堟慨妯诲閸嬫挸顫濋悙顒€顏�* *k*ai ta juya cikin wahala da galabai ta, shi kuwa k'ara rugume ta yayi cikin aminci da cikar farin ciki, murya a raunane yace. "Khairi d'an Allah kar k'iyeyya ta tashafi Abinda Allah zai azurta mu dashi." bata kulashi ba sai yunk'uri tayi da nufin tashi zaune amman kuma sai ta koma jikin shi da k'arfi ta fad'a kanshi cikin rawan jiki da murya ta saki wani sabon kuka hannayen shi ta damk'o da k'arfi har tana karkarwa murya a raunace tace. "Wayyo Allah wayyo Nenne na wayyo ya Usman Hamma Umar ya ketamin haddi ya kasheni." abin ma dariya ya bawa Hamma Umar wato ita a zaton ta zata iya tashi hartayi rashin mutunci sai kuma shegen raki da rauni, ruggume ta yayi yana murmushi fuskar cike da happy har cikin ranshi yake jin dad'i karb'e budurcin Khairi sarkin tsiwa yana ga yanzu kam zatayi mubaya'a ta hak'ura a zauna lafiya, kanta ta kife kan damtsen hannun shi cikin takaici ta datsa mishi cizo mai zafi, idon shi ya rumtse da k'arfi tare da sake mata hannun cikin rauni yace. "Ahhh shihhhhh Khairi cijeni in har cizon zaisa ki huce amman dan Allah karki sake cewa na keta miki haddi shin kin manta cewa, *ana zaujiki* ni mijin kine amman kike cewa na keta miki haddi." bata kulashi ba sai kukan ta kuma sakewa ganin haka ya mik'e zaune cikin tarin kunya ya jawo blanket ya rufe su dan shi da kanshi bai san meyasa yake k'asa control d'in kanshi ba a kan Khairi sai yayi abu yazo yana jin kunya shi da kanshi bai san ma cewa shi yana da shawa'a ba da har zata sashi zaucewa, ido ya lumshe ya jawo bosses d'in shi ya saka a hankali ya jawo ta jikin shi k'irjin ta ya manna kan nashi cikin kauda kai ya jawo zanin ta ya d'aura mata a jikin ta sannan, ya kontar da ita gefen shi ya d'an yi mata rumfa da k'irjin shi bakin su ya manne wuri d'aya tare da tallabo kanta yayi mata wani irin kiss mai cike da sak'onni masu kauda tunanin mutun, itama shiru tayi tana kallon fuskar sa shiko idanun shi a lumshe, a hankali ya zame bakin shin tare da bud'e idanun shi da tuni sun sake k'ak'k'an cewa sunyi jazir sai ya kamo lips d'in shi yana tsotsa tamkar yaro yana kallon ta cikin wani irin yanayi sai ajiyan zuciya yake sauk'e wa, itama idon ta rumtse sannan ta kamo lips d'in ta daya gama tsotsewa yanzu ta ciza ta ciki kuma taci gaba da tsotsar lips d'in, sunkuyo wa yayi tare da kauda kai hannun shi ya cusa cikin k'irjin ta bak'in shi ya kai dai-dai kunnen ta cikin rad'a yace. "Zo muje in miki wonka Khairi zakiji sauk'i." shiru tayi tana kallon fuskar shi d'aya kawar tana jin yadda yake murje mata k'irjin zuwa yanzu mamaki Hamma Umar yake bata ga wani irin tsoron shi da take ji, Shi kuwa ganin batayi magana ba ya sunkuyar da kanshi ya d'an laso lips d'in ta sannan ya juya ya nufi toilet ita kuwa ido ta tsura mishi tana kallon surar jikin shi tana mai cike da takaici wai Hamma Umar ne mijin ta , ruwan d'umi ya had'a sannan ya dawo ya d'auke ta cid'ak, suna shiga cikin toilet d'in ya tsayar da ita, sai kuma yayi maza ya ruggumota jin wani irin k'ara da ta saki sannan ya kalli k'afafun ta gaba d'aya sai rawa suke kamar mazari alamun bazasu iya d'aukar taba, k'ara ruggume ta yayi cikin tausawaya ya rink'a shafa kanta tare da cewa, *"Aaspet* sannu." rugume shi itama tayi tana yarfa hannu , k'ara matsota jikin shi yayi yana cewa. *"Bas bas bas* ya isa ya isa kiyi hak'uri *bitirajjaki* khairi, ki dakata." kuka takeyi har lips d'in ta na rawa dan azabar da takeji, kamota yayi cikin kauda kai ya kunce zanin sannan ya kamo hannun ta suka shiga cikin baf d'in ruwan d'umin a hankali ya zaunar da ita sannan shima ya zauna ya rink'a gasa mata jikin ta da ruwan d'umin yanayi yana cemata. *"ana aspet*" ita kuwa hannun shi kawai ta rik'e gam ta cusa kanta a k'irjin tana jin ruwan d'umin yana ratsata, a haka cikin lallama ya mata wonka tsab sannan yasa ta tayi wonkan tsaki shima wonkan yayi sannan ya jawo towel ya d'aura a k'ugunshi sannan ya dagota itama ta tsaya lokaci d'aya sai hawaye car-car a idanun ta, sunkuyo wa yayi yana kallon yadda har yanzu k'afafun ta na rawa a hankali yace. "Har yanzu kina jin zafi?." gini ta dafa ta fara tafiya a hankali tana yarfa hannu d'aya hawaye na zuba murya can k'asa tace. "Mugu kawai ka ketani ba ko imani kana kuma cemin har yanzu inajin zafi." ya jita sarai amman sai yayi murmushi ya d'ago ta ya kaita d'aki zanin gadon ya tattara ya duk'un k'une yana b'ata fuska dan baya son ganin jini a rayuwar sa tsikar jikin shi ke tashi, wani zanin gadon ya shimfid'a bayan ya gyara wurin ya zaro doguwar riga ya zira mata sannan ya kimtsa kanshi, yana gayawa ana kiran sallan maggariba d'an haka ya shimfid'a musu carpet yaja su sukayi sallan makariba tare da insha don lokacin ishan yayi, sannan ya mik'e ya shiga kitchen ferfesu ya had'a mata da tea sannan ya gasa mata nama ya had'o komai kamar mai jego yazo ya ajiye a parlour, cikin d'akin ya koma konce ya sameta kan carpet d'in tana ta rawan sanyi gaban ta ya tsuguna cikin kula yasa hannu ya shafa goshin ta da wuyan ta zafi jau yaji alamun zazzab'i, baiyi magana ba sai dagota yayi ya dawo parlour da ita zama yayi ya jawota jikin shi cup d'in tea d'in ya jawo a hankali yace. "Khairi dan Allah ki dena kukan kisha tea sai in baki maganin insha Allah zaki samu sauk'i." kai ta juya mishi alamun bazata shaba sai hawaye, matsota yayi jikin shi cikin tsuke fuska yace. "Zaki Sha ko sai nayi na biyu?." cikin rawan murya tace. "Hamma Umar zan mutu kayi hak'uri." "Toh kisha tea in baki maganin." tsoron shi yasa ta d'an sha tea d'in sannan taci naman kad'an daga nan ya bata maganin, sannan ya kunna TV a inda ya samu tashar Bollywood sun Sa film d'in *kal ho naa ho* sai ya jawota jikin shi ya rugume ta yana jin yadda take rawan sanyi jikin ta kamar wuta sai ajiyan zuciya take sauk'e wa, tana manne a jikin shi tana kallon tv a haka har bacci ya tafi da ita. 11:00 pm ya mik'e da ita a jikin shi dan yaji gari yayi shiru kai tsaye d'akin shi ya wuce da ita yana zuwa ya kontar da ita kan gadon shi daya sha gyara sannan ya dawo parlour ya kashe komai na wuta sannan ya koma d'akin shi, wonka ya sakeyi sannan yayi al'wala yazo yayi ta nafilfili har zuwa 12 sannan ya jawo qura'anin shi ya fara karatu cikin sauti mai sanyi murya cike da tauhidi da tajwidi gaba d'aya ya hallarto da kushi'inshi, haka yayi ta karatu har zuwa k'arfe 2 na dere sannan ya mik'e a hankali ya zauna bakin gadon yana kallon yadda taketa duk'unk'unewa alamun sanyin takeji, konciya yayi gefen ta cikin sauk'e ajiyan zuciya a hankali ya jawota gare shi, hannun shi yasa yana shafa fuskar ta da ta d'an kumbura tayi ja dan kuka, ita kuwa cikin baccin taji d'umin jikin mutun kusa da ita haka yasa sai k'ara matsoshi takeyi tana caku moshi, ido ya tsura mata ganin yadda ta tsuke bak'in ta ta manna shi kan k'irjin shi murmushi yayi ganin gaba d'aya ta cakumo wuyan shi, ta rik'e shi gam sai murza k'afafun ta takeyi a jikin shi, haka yasa lokaci d'aya ya fara dabur cewa jawota ya kumayi sannan ya cusa hannun shi cikin rigar ta ya rink'a d'an yi mata tausa, ita kuma sai mik'a takeyi tana lumshe ido, a haka ta k'ara tunzuro buk'atar shi, tuni ya susuce a kanta jiki na rawa ya zare mata rigar sannan ya rink'a murzata da juyata, cikin gigin bacci ta ji salon daya zarce tunanin ta a hankali ta bud'e idanun da sauri ta fara tureshi a firgice ta rik'o hannu shi murya na rawa tace. "Wayyo Allah Hamma Umar ka tausaya min mana kasheni kake son yi ko? zafi wallahi." rufe ta yayi da k'irjin shi a hargitse yace. "Ahh! Ahhh! bazaki mutu ba kiyi hak'uri ki nitsu bazan ji miki ciwo ba wallahi zakiji ba wuya." ina ita kam tureshi takeyi tuk'uru, shiko ya rigada ya gama d'imau cewa, dan haka bai sarara mata ba har saida ya samu nitsuwa , ita kuwa gaba d'aya ta sake bata ko numfashi mai k'arfi, haka ya kwana mak'ale da matarsa sai sanya mata al'barka yakeyi yana shafa kanta, bai san cewa ita kam Ummul bata cikin hayya cinta tana jinshi tana kuma ganin shi amman ta k'asa magana bare kuka sai hawayen dake bin fuskar ta ko yatsarta bata iya motsawa, A haka suka kwana sai da Asuba da yayi mata wonka ne ta dawo haiyacin ta tun a toilet d'in ta rink'a kuka tana magiya da rok'on shi, ya maida ta gidan su ita kam zata koma gun Nennen ta, a haka sukayi sallan Asuba suna idarwa ta tasa sabon kuka tana rawan jiki dan yunwa da wahala da bacci ga zazzab'i tace. "Wallahi ni gida zan koma ka medani gun Nenne na dan Allah Hamma Umar ka meyar dani gida." ta k'arishe maganar cikin rauni, shi kuwa ido ya zuba mata tare da cewa. "Meyasa zan medeki gida? en kin koma me zaki ce musu?, kin san Adam kuma inya ganki a gida kin san me zai miki kam ko?." kai ta tonk'oshe cikin raunin fuskar cike da k'ollah da tsoro tace. "Ayyah dan Allah Hamma ka kaini gun Nenne na ka hana ya Adam dukana plxx zanje gun Nenne na." sai ta kuma kife kai jikin gado ta rink'a sheshshek'a, ganin yadda gaba d'aya jikinta ya nuna bata da lafiya yasa ya matso gareta ruggume ta yayi a hankali yace. "Toh ya isa haka kibar kukan bari in had'a miki breakfast ko." zame jikin ta tayi ta zauna tana goge k'ollan dake bin fuskar ta, shi kuwa kitchen ya shiga ya had'a musu breakfast sannan ya ajiye musu a parlour , amman fir tak'i cin abin cin tuni mayafin ta na hannun ta ita dai a tafi, haka yasa shima baici komai ba wonka yayi ya shirya sannan ya dawo parlour, tana ganin shi ta mik'e tare da binshi da harara k'asa k'asa, shi kuwa ido ya zuba mata ganin k'atuwar jakar da ta ciko da kayan kamar wacce zata koma, gashi ko tafiya da k'er takeyi ba yadda baiyi ba ta ajiye jakar tak'i ta rege kayan ma tak'i, murmushi kawai yayi ya karb'a mata jakar suka fita sannan ya rufe gidan, suka shiga mota suka kama hanyar potaskum d'in, tunda suke tafiya ba wanda yayiwa d'an uwanshi magana. A gida potaskum kuwa gaba d'aya mutanen gidan kowa na y'an harkokin shi, Abba ma yau yana gida Ya Adam da ya Sadik da Aliyu duk suna parlour Nenne ita kuwa Nenne tana parlour Abba ya Usman kuwa yana parlour Hajjajo suna d'an tab'a hira duk da zuciyar shi bata da nitsuwa, gaba d'aya tunanin shi na kan Ummul lokaci guda numfashi sa ya fara cushewa , jin hakan yasa ya sallami Hajjajo ya fita dan yaje ya b'uya yayi ta kuka dan in numfashi sa ya fara cushewar da tunanin sai yayi ta kuka yake jin dama-dama, haka yasa kai tsaye ya nufi harabar gidan motar shi ya bud'e ya shiga ya rufe kanshi ya kifa kai a jikin siterin ya rink'a kuka mai ciwo a zuciya. 10:12 na safe Mati mai gadi ya bud'ewa Hamma Umar gate d'in gidan yana shiga gefen motar ya Usman yayi parking, kasan cewa glass d'in motar Usman tintek ne Hamma Umar bai ga Usman d'in a ciki ba, shi kuwa Usman ya gansu so baya son ya fito Hamma Umar yaga fuskar sa a yadda yayi kuka yanzu yasan zai saka d'an uwanshi a firgici yasan Hamma Umar zai gigice in ya ganshi shiko baya sun Hamma Umar ya gane yana da wata matsala. Su Hamma Umar d'in kuwa yana yin parking Ummul tasa hannu ta bud'e marfin motar da niyar zata fice, hannun ta ya kamo da sauri ya jawota jikin kujerar, gyara zaman shi yayi ya d'an juyo gareta tafin hannun shi ya manne da nata tafin hannun ido ya d'an zuba mata cikin sauk'e numfashi sannan ya kuma lumshe idon a hankali yace. "Khairi gudu na kikeyi ko? sauri kike kibar inda nake ko?." hannun ta rink'a k'ok'arin kwancewa ta k'asa dan ya hard'e yatsun ta cikin nashi yatsun kallon ta ya kumayi a hankali yace. "Ke baki iya sallama mijin ki ba ko?." a kufule cikin jin tsanarshi tace. "Eh d'in ban iya ba ba'a koyamin ba." murmushi yayi cikin zafin nama ya fizgota jikin shi tare da matsota sannan ya d'an d'ago fuskar ta, harshen shi ya d'an zaro tare da kad'a mata shi sannan ya lumshe yace. "OK haka nefa Ashe ban koya miki ba, karki damu toho yanzu in koya miki yadda akeyi." ido ta zaro ganin yadda ya ruggume ta baki ta bud'e da niyar mishi tsiwa, sai kuma ta zaro idanun woje jin yadda ya manne bak'in shi da nata yana mata tsotsar lolly pop, shi kuwa sai lumshe ido yakeyi, ya Usman kuwa tunda yaga Hamma Umar d'in nashi ruggume da Ummul a take yaji numfashi sa na fizga zuciyar shi na harbawa da k'arfi kamar zata faso k'irjin shi ta fito zufa ta fara keto mishi tako ina a take jijiyoyin jikin shi sukayi rud'u-rud'u k'irjin shi ya dafe da k'arfi jin kamar ana soka mishi allurai, ido ya rumtse da k'arfin dai-dai lokacin da Hamma Umar yake kissing d'in ta, wani irin tarine mai k'arfin ya turnu k'eshi gaba d'aya ida nunshi suka firfito hannun yasa ya to she bak'in sa wai dan kar Hamma Umar d'in yaji, amman ina tuni tarin ya kufce mishi tarin yakeyi sosai har numfashi sa na fizga da k'arfi tuni ya fara gigicewa yana buga jikin motar, shi kuwa Hamma Umar jin tarin a cikin motar B'iyayen nashi yasa ya zame bak'in shi daga jikin Ummul d'in cikin tsoro da mamaki yadda tarin ya sark'afe mishi da sauri ya nufi gaban motar har jikin shi na rawa ya bud'e marfin motar, yana bud'e wa Usman ya fad'o jikin shi, shi kuwa ruggume shi yayi da k'arfi tare da zaro idanun cikin tsananin tsoro da firgita gaba d'aya jikin shi rawa yakeyi ba abin da yake furtawa sai jujjuya kan Usman d'in yakeyi yana cewa. "Usmaaan ! Usmaaaaaan!." sai kuma ya k'ara matsoshi jikin shi ganin wani irin yunk'uri da Usman d'in keyi, shi kuwa Usman k'irjin shi ya rik'e tare da damk'o hannun d'an uwanshi yayi wani irin kakari da k'arfi har jikin shi na karkarwa , aman jini ya rink'a yi bak'ik'k'irin dashi guda-guda sai ya damk'o hannun d'an uwan nashi yayi kakari, ita kuwa Ummul gaba d'aya karkarwa takeyi da dafa jikin motar tayi tana tafiya a hankali har ta isa gaban su hannun ya Usman d'in ta rik'e da k'arfi cikin gigicewa da tsoro ta saki wani irin k'ara mai k'arfi kawai sai ta fad'a jikin Hamma Umar d'in a sune, shi ma ya Usman lokaci d'aya numfashi sa ya fara d'auke wa, Allah sarki Hamma Umar gaba d'ayansu ya had'a ya ruggume su cikin tsinkewar jijiyoyin jikin shi gaba d'aya ya zame ya zauna a k'asa kanshi ya rink'a murzawa a jikin motar Usman cikin wani sauti mai tsananin rauni yace. "Usmaaan kar kayi min haka Usman karka barni ni kad'ai Usman wazai meye min gurbin ka wayyo Allah wayyo d'an uwana wayyo Ammina ina kike Usman zai tafi ya barmu wayyo Abba d'an uwana zai tafi ya barni ni kad'ai ba Uba ba d'an uwa." ruggume Usman da Ummul d'in ya kumayi da k'arfi Abba ya rink'a kira da k'arfi dai-dai lokacin daya ga numfashi Usman yana ficew.... By *GARKUWAR FULANI* 婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戝鈧倿鎸婃竟鈺嬬秮瀹曘劑寮堕幋鐙呯幢闂備浇顫夊畷妯衡枖濞戞碍顐介柕鍫濇偪瑜版帗鍋愮€瑰壊鍠栭崜浼存⒑濮瑰洤鈧倝宕板Δ鍛﹂柛鏇ㄥ灠閸愨偓濡炪倖鍔﹀鈧紒顔煎缁辨挻鎷呴崫鍕戙儵鏌涢悩鍐插濠碉紕鏁诲畷鐔碱敍濮樿京鏉搁梻浣告啞閹哥兘鎳楅幆鏉库偓瀵哥磽閸屾艾鈧嘲霉閸ャ劊浠堢紒瀣嚦濞戙垹绀冩い鏃囧閹芥洖鈹戦悙鏉戠仧闁搞劌婀辩划璇测槈閵忥紕鍘撻柡澶屽仦婢瑰棝藝閿斿浜滄い鎺嗗亾妞ゆ垵顦~蹇撁洪鍕唶闁硅壈鎻徊鐑樻叏閸ヮ剚鈷戦柣鐔哄閸熺偤鏌i埄鍐╃闁诡喗顭囬埀顒婄秵閸犳鍩涢幋锔界厵缂佸瀵ч幑锝囩磼閻樿櫕宕岄柡宀€鍠栧畷姗€寮婚妷銉ュ強闁诲孩顔栭崰鏍疮閸ф鐓濋幖娣妼缁狅綁鏌eΟ纰卞姕缂佹唻绻濆缁樻媴娓氼垱鏁銈庡亜椤﹂潧鐣峰┑瀣唨妞ゆ挾鍠庢禒褍顪冮妶鍛闁绘锕幃锟犲Ψ閿斿墽顔曢梺鐟邦嚟娴兼繈顢旈崼婵囪緢闂佹寧绻傚ú鐘诲磻閹捐埖鍠嗛柛鏇ㄥ墰椤︺劑姊洪幐搴㈢8闁搞劎鍎ょ粚杈ㄧ節閸屻倖妗ㄩ悗鍏夊亾濠电姴鍠氶埀顒€顦辩槐鎾诲磼濞嗘垵濡介梺鍝ュ仜椤嘲顫忔禒瀣妞ゆ帒鍊甸弨铏節閻㈤潧孝婵炴潙鍊垮顐﹀礃閳瑰じ绨婚梺鍦劋閸ㄧ敻鍩€椤掍焦鍊愮€规洖鎼悾婵嬪礋椤戣姤瀚奸梻浣告啞缁哄潡宕曢崡鐐╂瀺闊洦绋掗悡鏇㈡倵閿濆簼绨兼い銉у仧缁辨帡寮崒姘亪閻庢鍠楅幐铏叏閳ь剟鏌嶉埡浣告殭闁告梹甯楁穱濠囨倷椤忓嫧鍋撻弽顓炵闁挎洖鍊哥粈鍫熺箾閹寸偠澹樻い銉﹁壘铻栭柨婵嗘噹閺嗙偤鏌嶉柨瀣伌闁哄本绋戦埥澶婎潨閸繀绱e┑鐘愁問閸犳牠宕愰崸妤€钃熸繛鎴欏灩濡﹢鏌涜椤ㄥ懎顕f导瀛樷拺閺夌偞澹嗛ˇ锔剧磼婢跺﹦绉洪柣娑卞枛铻e〒姘煎灣閸炵敻姊洪崨濠冨闁告挻绋戠叅闁圭虎鍠楅悡娑樏归敐鍥ㄥ殌濠殿喖绉堕埀顒冾潐濞插繘宕濋幋锔衡偓浣割潨閳ь剟骞冮姀銈呯闁圭粯甯楅弳銏㈢磽閸屾艾鈧悂宕愰悜鑺ュ殑闁割偅娲栫壕濠氭煙閹咃紞闁哄棴闄勬穱濠囶敍濠靛嫧鍋撻埀顒勬煛鐎n亞效闁哄矉绻濆畷鍫曞Ψ閵壯傜棯闂備礁鎼幏瀣礈閻旂厧钃熸繛鎴欏灩缁犳盯姊婚崼鐔衡姇闁诲繐鐗忕槐鎾存媴閹绘帊澹曢梻浣告啞閸旓箓宕板Δ鍛亗闊洦鎸撮弨浠嬫煟閹邦厼鐏ラ柛鐔稿閸婃潙鈹戦悩顔肩伇婵炲绋撻埀顒佸嚬閸撶喖宕洪悙鍝勭闁挎洍鍋撻柣鎿勭節閺屾盯鍩勯崘锔挎勃婵犮垼顫夊ú婊呮閹惧瓨濯撮柦妯侯槺婢跺嫮绱撴笟鍥ф灍闁荤喆鍎甸幃楣冩倻缁涘鏅梺缁樺灥濡瑩寮插┑瀣拺闂傚牊绋撴晶鏇㈡煙瀹勯偊鍎忛摶鐐寸節婵犲倻澧涢柍閿嬪灴閹綊骞侀幒鎴濐瀳濠电偛鎳忛崝娆撳蓟閻旂厧绀勯柕鍫濇椤忥拷 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 1闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌i幋锝呅撻柛濠傛健閺屻劑寮撮悙娴嬪亾閸濄儳鐭嗛柛顐ゅ枑閸欏繑淇婇姘变虎闁绘挻鍔欓弻娑氣偓锝庝簻閳ь剚鎮傞垾锕傚锤濡や礁娈濋梻鍌氱墛缁嬫垿锝炲畝鈧槐鎾存媴閸濆嫷鈧矂鏌涢妸銉у煟鐎殿喖顭锋俊鎼佸煛閸屾矮绨介梻浣侯焾閺堫剛绮欓幋锔绘晜闁跨噦鎷�9闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌i幋锝呅撻柛濠傛健閺屻劑寮撮悙娴嬪亾閸濄儳鐭嗛柛顐ゅ枑閸欏繑淇婇姘变虎闁绘挻鍔欓弻娑氣偓锝庝簻閳ь剚鎮傞垾锕傚锤濡や礁娈濋梻鍌氱墛缁嬫垿锝炲畝鈧槐鎾存媴閸濆嫷鈧矂鏌涢妸銉у煟鐎殿喖顭锋俊鎼佸煛閸屾矮绨介梻浣侯焾閺堫剛绮欓幋锔绘晜闁跨噦鎷� *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戝鈧倿鎸婃竟鈺嬬秮瀹曘劑寮堕幋鐙呯幢闂備浇顫夊畷妯衡枖濞戞碍顐介柕鍫濇偪瑜版帗鍋愮€瑰壊鍠栭崜浼存⒑濮瑰洤鈧倝宕板Δ鍛﹂柛鏇ㄥ灠缁犳盯鏌嶆潪鎷岊唹闁稿鎹囧鎾煑閸濆嫷妲告い顐g箞閹虫粓鎮介棃娑樺強闂傚倸顭崑鍕归崟顓炵筏闁兼亽鍎抽々鏌ユ煕閹炬鎳愰敍婊堟煛婢跺﹦澧戦柛鏂跨Ч钘熼柛顐犲劜閻撴盯鎮橀悙鎻掆挃婵炴彃鐡ㄩ〃銉╂倷閸欏鏋犻梺绯曟杹閸撴繈骞忛崨鏉戠闁肩⒈鍏橀崑鎾绘倻閼恒儮鎷绘繛杈剧悼閹虫捇顢氬鍛<閻庯綆鍋勫ù顔筋殽閻愭潙濮囨い顐犲灩閻f繈鍩€椤掍胶顩查梺顒€绉甸埛鎺懨归敐鍥ㄥ殌妞ゆ洘绮庣槐鎺旀嫚閹绘巻鍋撻崸妤冨祦濠电姴鍟崕鐔兼煏婵炲灝鍔滈弶鍫濈墕閳规垿鎮欓崣澶樻!闂佹悶鍔庨幊鎾圭亱濡炪倖鐗滈崑鐐烘偂濞嗘挻鍋℃繛鍡楃箰椤忊晛鈹戦鑲╁ⅵ闁哄矉绲介埞鎴﹀箛椤忓牆浠愰梻浣告惈鐞氼偊宕濆畝鍕叀濠㈣泛谩閻斿吋鍊绘俊顖涙た閸熷姊虹拠鍙夊攭妞ゎ偄顦叅婵せ鍋撻柡浣稿暣婵偓闁炽儴灏欑粻姘攽椤旂晫绠撻柣顓炵墕椤﹪顢旈崱娆戯紳婵炶揪绲块幊鎾诲极妤e啯鈷掗柛鏇ㄥ亜椤忣亞绱掑畝鍐摵缂佺粯绻堝畷鍫曟嚋閸偅鐝栧┑锛勫亼閸婃牜鏁幒妤€纾归柟闂寸閺勩儳鈧厜鍋撻柛鏇ㄥ厴閹锋椽姊洪崨濠勭細闁稿骸宕埢宥堢疀濞戞瑧鍘遍柣搴秵娴滄繈藟閻愮數纾奸柡鍐ㄥ€搁弸娑氣偓娈垮枟閹歌櫕鎱ㄩ埀顒勬煃閳轰礁鏆欓柛鏃€甯楁穱濠囨倷椤忓嫧鍋撻弽顓炵闁挎洖鍊哥粈鍫熺箾閹寸偠澹樻い銉﹁壘铻栭柨婵嗘噹閺嗙偤鏌嶉柨瀣伌闁哄本绋戦埥澶婎潨閸繀绱e┑鐘愁問閸犳牠宕愰崸妤€钃熸繛鎴欏灩濡﹢鏌涜椤ㄥ懎顕f导瀛樷拺閺夌偞澹嗛ˇ锔剧磼婢跺﹦绉洪柣娑卞枛铻e〒姘煎灣閸炵敻姊洪崨濠冨闁告挻绋戠叅闁圭虎鍠楅悡娑樏归敐鍥ㄥ殌濠殿喖绉堕埀顒冾潐濞插繘宕濋幋锔衡偓浣割潨閳ь剟骞冮姀銈呯闁圭粯甯楅弳銏㈢磽閸屾艾鈧悂宕愰悜鑺ュ殑闁割偅娲栫壕濠氭煙閹咃紞闁哄棴闄勬穱濠囶敍濠靛嫧鍋撻埀顒勬煛鐎n亞效闁哄矉绻濆畷鍫曞Ψ閵壯傜棯闂備礁鎼幏瀣礈閻旂厧钃熸繛鎴欏灩缁犳盯姊婚崼鐔衡姇闁诲繐鐗忕槐鎾存媴閹绘帊澹曢梻浣告啞閸旓箓宕板Δ鍛亗闊洦鎸撮弨浠嬫煟閹邦厼鐏ラ柛鐔稿閸婃潙鈹戦悩顔肩伇婵炲绋撻埀顒佸嚬閸撶喖宕洪悙鍝勭闁挎洍鍋撻柣鎿勭節閺屾盯鍩勯崘锔挎勃婵犮垼顫夊ú婊呮閹惧瓨濯撮柦妯侯槺婢跺嫮绱撴笟鍥ф灍闁荤喆鍎甸幃楣冩倻缁涘鏅梺缁樺灥濡瑩寮插┑瀣拺闂傚牊绋撴晶鏇㈡煙瀹勯偊鍎忛摶鐐寸節婵犲倻澧涢柍閿嬪灴閹綊骞侀幒鎴濐瀳濠电偛鎳忛崝娆撳蓟閻旂厧绀勯柕鍫濇椤忥拷 *Wannan shafi naki ne kad'ai Firdausi Sodaggi ke da members naki na matan k'warai na baku kyautan wannan shafi gaba d'ayan shi婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戝鈧倿鎸婃竟鈺嬬秮瀹曘劑寮堕幋鐙呯幢闂備浇顫夊畷妯衡枖濞戞碍顐介柕鍫濇偪瑜版帗鍋愮€瑰壊鍠栭崜鎵磽娴g懓濮堟い銊ユ楠炲牓濡搁妷顔藉缓闂佺硶鍓濋〃鍛村煕閹烘鈷戦悹鍥у级閸炲鏌涢埡鍌滃⒌濠碉紕鏁诲畷鐔碱敊閸撗勬緫闂備礁婀遍崑鎾愁焽濞嗘挻鍋熼柡鍐ㄥ€荤壕钘壝归敐鍕煓闁告繄鍎ゆ穱濠囶敃閵忕姵娈婚悗娈垮枦椤曆囧煡婢舵劕顫呴柣妯兼暩閺夋悂姊绘笟鈧褔鈥﹂銏♀挃闁告洦鍨遍崑鐔兼煥閺囨浜鹃梺瀹狀潐閸ㄥ潡骞冨▎鎾崇闁圭儤鎸搁埀顒夊灣缁辨挻鎷呯粵瀣闂佺锕g划娆撳箖濡皷鍋撻敐搴℃灍闁抽攱鍨块弻鐔虹矙閹稿孩宕崇紓浣哄У閹瑰洭寮婚悢鐓庣闁哄被鍎卞浼存倵濞堝灝鏋熷┑鐐诧躬楠炲啫鈻庡銏犻叄椤㈡牜鎹勯妸褎鏅ㄦ繝纰夌磿閸嬫垿宕愰弽顓炵闁挎洖鍊哥粈鍫熸叏濡顣抽柛瀣尭椤繈鎮欓鈧锟�* *QAULIKI HAQQUN SAFIYYA HUGUMA婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戝鈧倿鎸婃竟鈺嬬秮瀹曘劑寮堕幋鐙呯幢闂備浇顫夊畷妯衡枖濞戞碍顐介柕鍫濇偪瑜版帗鍋愮€瑰壊鍠栭崜浼存⒑濮瑰洤鈧倝宕板Δ鍛﹂柛鏇ㄥ灠閸愨偓濡炪倖鍔﹀鈧紒顔肩埣濮婂搫效閸パ€鍋撻妶澶婇棷闁挎繂顦拑鐔兼煛閸ラ纾块柣銈傚亾濠电姷鏁告慨鎾窗濮橆剦鐒介柟閭﹀枤绾捐棄霉閿濆嫮鐭欓柛婵堝劋娣囧﹪顢曢姀鐘虫閻庢鍠涢褔鍩ユ径鎰潊闁绘鏁搁弶鎼佹⒒娴e摜鏋冩俊妞煎妿缁牊绗熼埀顒勫灳閺嶎偀鍋撻敐搴濈按闁衡偓娴犲鐓熼柟閭﹀墯閳绘洘淇婇悪娆忔处閻撴瑩鏌涢幋娆忊偓鏍偓姘炬嫹 ALMUSLIM AKUL MUSLIM婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戝鈧倿鎸婃竟鈺嬬秮瀹曘劑寮堕幋鐙呯幢闂備浇顫夊畷妯衡枖濞戞碍顐介柕鍫濇偪瑜版帗鍋愮€瑰壊鍠栭崜鎵磽娴g懓濮堟い銊ユ楠炲牓濡搁妷顔藉缓闂佺硶鍓濋〃鍛村煕閹烘鈷戦悹鍥у级閸炲鏌涢埡鍌滃⒌濠碉紕鏁诲畷鐔碱敊閸撗勬緫闂備礁婀遍崑鎾愁焽濞嗘挻鍋熼柡鍐ㄥ€荤壕钘壝归敐鍕煓闁告繄鍎ゆ穱濠囶敃閵忕姵娈婚悗娈垮枦椤曆囧煡婢舵劕顫呴柣妯兼暩閺夋悂姊绘笟鈧褔鈥﹂銏♀挃闁告洦鍨遍崑鐔兼煥閺囨浜鹃梺瀹狀潐閸ㄥ潡骞冨▎鎾村€烽柛蹇擃槸娴滈箖鎮楅敐搴℃灈缂佺媭鍨堕弻銊╂偆閸屾稑顏� ZADAKILLAHU FIKHRAN WA ILMAN婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戝鈧倿鎸婃竟鈺嬬秮瀹曘劑寮堕幋鐙呯幢闂備浇顫夊畷妯衡枖濞戞碍顐介柕鍫濇偪瑜版帗鍋愮€瑰壊鍠栭崜浼存⒑濮瑰洤鈧倝宕板Δ鍛﹂柛鏇ㄥ灠閸愨偓濡炪倖鍔﹀鈧紒顔肩埣濮婂搫效閸パ€鍋撻妶澶婇棷闁挎繂顦拑鐔兼煛閸モ晛鏋旂紒鈾€鍋撻梻濠庡亜濞诧箓宕欒ぐ鎺戣Е闁告侗鍨崇壕钘壝归敐鍕煓闁告繄鍎ゆ穱濠囶敃閵忕姵娈婚悗娈垮枦椤曆囧煡婢舵劕顫呴柣妯兼暩閺夋悂姊绘担鍝ユ瀮婵℃ぜ鍔庣划鍫熺瑹閳ь剟鍨鹃弽顐熷亾閿濆簼绨撮柡鈧禒瀣厽闁归偊鍓氶埢鏇熶繆閻欐瑥娲﹂悡娆撴煕閹存瑥鈧牜鈧熬鎷�, WAYATTAQINALLAHU JAMI'AN婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戝鈧倿鎸婃竟鈺嬬秮瀹曘劑寮堕幋鐙呯幢闂備浇顫夊畷妯衡枖濞戞碍顐介柕鍫濇偪瑜版帗鍋愮€瑰壊鍠栭崜浼存⒑濮瑰洤鈧倝宕板Δ鍛﹂柛鏇ㄥ灠閸愨偓濡炪倖鍔﹀鈧紒顔肩埣濮婂搫效閸パ€鍋撻妶澶婇棷闁挎繂顦拑鐔兼煛閸モ晛鏋旂紒鈾€鍋撻梻濠庡亜濞诧箓宕欒ぐ鎺戣Е闁告侗鍨崇壕钘壝归敐鍕煓闁告繄鍎ゆ穱濠囶敃閵忕姵娈婚悗娈垮枦椤曆囧煡婢舵劕顫呴柣妯兼暩閺夋悂姊绘担鍝ユ瀮婵℃ぜ鍔庣划鍫熺瑹閳ь剟鍨鹃弽顐熷亾閿濆簼绨撮柡鈧禒瀣厽闁归偊鍓氶埢鏇熶繆閼奸娼愮紒缁樼洴瀹曪絾寰勭仦瑙f嫪闂備浇顕х换鎰邦敄婢跺娼栨繛宸簻缁犱即骞栨潏鍓ф偧闁伙絿鏁诲娲偡閺夋寧姣愰梻浣稿簻缁蹭粙顢氶敐澶婄濞达綀鍊借閺屾盯鍩勯崘鈺冾槶缂備胶濮靛銊ф閹捐纾兼繛鍡樺灱缁愭鈹戦悩顐e櫚闁稿鎸剧槐鎾存媴闂堟稑顬堥梺闈涚墛閹倸顕f繝姘╅柕澶堝灪椤秴鈹戦埥鍡楃仯闁稿簺鍊曢埢鎾寸節濮橆厼鈧敻鎮峰▎蹇擃仾缂佲偓閸愵喗鐓ラ柡鍥悘鑼偓瑙勬礃濡炰粙宕洪崟顖氱妞ゅ繐妫涘Σ鍥⒒娴e憡鍟炴繛鎻掔箻瀹曟繄浠﹂崜褜娲告俊銈忕到閸燁垶宕戦敐澶婄骇闁绘劖娼欓ˉ瀣磼婢跺顕滅紒缁樼洴楠炲鈻庤箛鏇氱棯闂備礁鎼幊蹇涙偂閿熺姴钃熸繛鎴炃氬Σ鍫ユ煕濡ゅ啫浠滅紒鐘虫そ濮婅櫣鎷犻懠顒傤唹闂佺懓鎲¢幃鍌炲春閻愬搫绠i柨鏇楀亾闁绘帗妞介弻娑㈠箛閵婏附鐝旈梺缁樼箥娴滎亜顫忓ú顏呭仭闁哄瀵ч鈧梻浣烘嚀閸ゆ牠骞忛敓锟�* *R*uggume su ya K'ara yi cikin tarin firgici yana tallabo kan Usman yana mannawa a k'irjin shi tare da rumtse ido da k'arfi yana fad'in. "ya rabbi ! Ya k'adir ! Allah kaine gatana kaine gatan dukan bayin ka Allah kaine mai rayawa da kashewa Allah kaine mai bada lafiya ya Allah ka jib'amci lamuran d'an uwana Allah ka rayamin d'an uwana, shima Usman k'amk'ame Umar d'in yayi cikin fitar hayya cinshi da azabar da yakeji, Ummul kuwa manne take a jikin Hamma Umar d'in tayi luf a sume, su Abba kuwa tun k'aran da Ummul tayi na fari sun ka fito cikin mamaki jin muryar Ummul d'in a gida ya Adam da Sadik kuwa jin muryar Hamma Umar yana kiran Abba da karfine yasa suka fito a guje gaba d'aya harabar gidan suka nufa, Hamma Umar kuwa gaba d'aya jikin shi rawa yake tsoro da firgicin zai rasa d'an uwan nashi gaba d'aya sai ya resa k'arfi jikin nashi haka ya zauna dir sham a k'asa yana ruggume dasu yana wani irin kuka mai cike da firgici da tsoro da kad'uwa gaba d'aya ya resa halin da yake ciki duniyar ta mishi duhu, su Abban suna fita da gudu sukayi inda suke jin sautin kukan Hamma Umar d'in da sautin fuzgar numfashin Usman d'in, suna zuwa Abba ya durk'usa gabansu cikin tarin firgici da ganin ikon Allah ya kamo hannun Usman cikin tashin hankali yake kiran shi. "Usman ! Usman ! Innalillahi." sai ya kumu kalli Adam da gaba d'aya jikin shi rawa yake cikin rawan murya yace. "Adam fito da mota mu tafi asibiti." sai ya kumma kalli Ummul dake kwance luf jikin Hamma Umar d'in tana sume cikin jin tsoron lamarin ya kalli Umar tare da cewa. "Umar meke faruwa da sune?." ina ya kasa magana sai k'ara ruggume Usman da ummul d'in yakeyi, shi kuwa Usman cikin tarin ya kamo hannun Adam d'aya juya zai fito da mota numfashi na fizga tare da zarewan idanu yace. "Ad..! Ada..! Adam Karku kaini asibiti Abbah Ku barni a gida." sai ya kuma carkewa da tari sai ya rink'a amayo da jini guda-guda bak'k'ik'irin dashi, cikin a man ya kamo hannun Umar d'aya gama mutuwan zaune yace. "Hamma na karku kaini ko ina ku barni a gidan ku maidani cikin gida." Hamma Umar kam kanshi ya kife a jikin Usman d'in cikin rawan murya da baki yace. "Usman d'an uwana ya za'ayi mu barka a gida a cikin wannan halin da kake kayi hak'uri muje asibiti." hannun Umar d'in ya rik'o dan ya fara jin numfashi sa na dawowa tunda ya amayar da bak'in jinin hawaye na bin fuskarsa zufa na ketomai tako ina cikin murmushi k'arfin hali yace. "Toh su asibiti zasu hanani mutuwa ne in lokaci na yayi? nasan dai mutuwa ce kuke tsoro kuma in lokaci yayi ba makawa Hamma Umar ka tunafa Abba ka sani tun ina yaro kuke fama dani ko yaushe muna hanyar asibiti ban workeba yanzu kuma ko anje ba lallai a samu nasara ba ko nasha maganin shi maganin abinda ya samu yake tayiwa in ya samu sauk'i sai ya k'ara sauk'i in ya samu ajali kuwa tofa ajalin yake tayiwa dan Allah Abba Hamma Umar ku maida ni gida bana son zuwa asibiti nan." Haka dole ba d'an suna soba suka koma cikin gida dashi, shi kuwa Umar Ummul ya ruggume sannan yabi bayan Abba dake tallabe da Usman, kai tsaye part d'in Hajjajo suka nufa a parlour suka zauna kan 3 str Abba ya kwantar da Usman shi kuwa Umar ya kwantar da Ummul kan 2 str , ya Adam kuwa dama tuni ya fita ya d'auko doctor dake duba Usman d'in. Bayan yazo ya duba shin yayi duk binciken da zaiyi ya gama sannan ya kalli Usman d'in dake konce a rigingine ya lumshe ido hawaye na bin fuskar shi sannan ya juyo ya kalli Hamma Umar dake zaune ya zuba mishi ido yana rik'e da hannun shi sannan ya kalli Abba dake k'ok'arin gyara wa Usman d'in konciya cikin kula doctor Ibrahim yayi ajiyan zuciya sannan yace. "Alhaji Hassan ko kuna lura da Usman sannan kunsan meke damun shi akwai matsalar da yake boyewa a zuciyar shi sannan kuma yasan zuciyar shi bazata iya d'aukar nauyin ba Usman akwai abin da yake matukar so bai samu ba, domin na duba na'urar dake cikin k'irjin shi tana zaune yadda ake so tana kuma taimakawa kamar yadda ta saba tana kuma harbawa jinin dai-dai misali kuma zataci gaba da aikin har nan gaba shekara 1 a lokacin zai cika shekara biyar da sata sannan za'a koma a canzata kamar yadda aka saba, yanzu wata matsalar ce ta daban kuwa ke damun Usman kuma zata iya jawo komai a rayuwar shi." yana rufe bak'in shi Usman ya bud'e idanun shi cikin salon sa na abin dariya ya fara magana cikin dariya da son badda matsalar tasa yace. "Uhummm wai ina son wani abu, toh niko mai zanso wanda Abba da Hamma Umar basu samamin shiba ni ba abin da nake so." Ido Nenne ta tsura mishi cikin tsananin tunani lokaci d'aya kuma ta fara tuno wani abin, Hajjajo kuwa ba abinda takeyi sai kuka, shi kuwa Hamma Umar ido ya tsurawa d'an uwan nashi cikin sanyi yace. "Me yake saka tarin da a man jini?." murmushi yayi tare da d'an shafa sajen shi yace. "You naga Anyi tayin maganin asibiti ba canji shine jiya naje na karb'o na wmzamai shine na jik'a nasha , sai gashi yana k'ok'arin fecewa dani barzaq." Murmushi ya kuma yi sannan yace. "Amman fa gsky naji sauk'i dana amayar da jinin." haka ya rink'a shashantar da abin shi kuwa doctor Ibrahim ya tabbar akwai matsala tare dashi. su ya Adam kuwa sun d'an samu nitsuwa ganin Usman d'in ya mik'e, Hamma Umar kuwa har yanzu zuciyar shi na cike da fargaba, Abba kuwa bayan doctor Ibrahim yabi suka fita tare yana k'ara mishi bayani, bayan su Abban sun fita ne Hamma Umar ya d'an juyo kusa da Ummul tafin k'afafun ta ya kamo yasa hannun shi ya rink'a murzawa yana jan yatsun k'afafun nata tare da kiranta. "Ummul ! Ummuuul !." sai kuma ya dawo ta kanta hannun shi yasa ta k'asan wuyanta yana d'an murzawa, nanma shiru sai ya manna hancin shi da nata sannan ya rufe bakinta da nashi, cikin lumshe ido ya rink'a fesa mata numfashin sa sannan yana zuk'o numfashin ta bak'in ta gaba d'aya nashi numfashin ya rink'a fesa mata cikin sa'a tafizgo numfashin sannan a razane ta kamo wuyan shi baki ta bud'e da nufin zata sake k'ara, sai yayi maza ya rufe mata bak'in da tafin hannun shi, haka yasa ta bud'e idanun ta sannan ta rink'a kallon su d'aya bayan d'aya, zame bakin ta tayi cikin sanyin muryar tace. "Ya Usman ! ya Usman ." ido ya d'an rumtse sannan yace. "Na'am Ummul ." jin muryar shi ta mik'e da sauri taku d'aya tayi ana biyun ta koma ta zauna ido na zubda k'ollah dan azaban ciwon da raunin jikinta ke mata, cikin sauk'e ajiyan zuciya Hajjajo tace. "Ke kuma meya sumar dake? sannan yanzu tafiya ma na gagararki." batayi magana ba sai kawai ta kama kuka, ganin haka Nenne tace. "Toh sarkin kuka ya isa haka taso mu tafi kiyi wonka sai kici abinci kiyi bacci." mik'e wa tayi cikin zubda k'ollah tafiya ta farayi cikin d'ingisa k'afafun ta tana d'an waresu tare da cije lips d'in ta, ganin haka tuni Nenne tayi gaba dan ta gano matsalar yartata itama Hajjajo shiru kawai tayi dan ta fahimci matsalar, shi kuwa Hamma Umar kanshi ya sunkuyar cikin tarin kunya da tausayin Ummul d'in sai hawaye yaji yana bin hab'arsa dan gani yake kamar ya gwada mata rashin tausayi tunda yasan yarinya ce, kunya yakeji ta rufeshi kamar k'asa ta tsage ya shiga, ganin hakan yasa su ya Adam duk suka zame suka fita itama Hajjajo kitchen d'inta ta shiga ta fara had'a wa Ummul had'in su na tsoffin shuwa'arab sannan tayiwa Usman d'in ma had'in shi na musamman ta kuma dafawa Usman abincin da zaici da kanta. A part d'in Nenne kuwa suna shiga kai tsaye bedroom suka wuce kan gado Ummul ta konta ta kife kanta tana kuka, ita kuwa Nenne toilet ta shige ruwan d'umi ta had'a mata mai k'unshe da sinadarai na gyaran jiki sannan ta had'a mata wani juk'o na musamman a cikin buta, tana fitowa taje kusa da ita cikin kulawa da tausayawa irin ta uwa da yarta ta kamo hannun ta ta zaunar da ita kafad'an ta ta dafa a hankali tace. "Ummul Allah ya miki albarka kiyi hak'uri mamana ki d'aure kinji ko ki denan kukan nan ya isa yanzu kin girma ya kamata kiyiwa kanki fad'a tashi kije kiyi wonka ki zauna cikin ruwan d'umin sannan kiyi amfani da ruwan butar nan." kukan ta kumayi cikin shogwob'a dan ganin Nennen ta na lallashin ta, da kukan ta shiga tayi wonkan sannan ta k'asa kanta lokaci d'aya taji jikinta duk ya wore, tana fitowa ta samu Nennen ta jona borner a ajikin wuta tana fitowa ta zuba mata wasu turaruka masu tsananin k'amshi sannan ta kalleta cikin kulawa tace, zoki tsuguna kiyi hayak'i da wannan." "toh " tace sannan ta matso gaban borner ita kuwa Nenne ta fita parlour, tsuguna wa tayi a kanshi hayak'in na shiga jikin ta wani irin k'amshi na ratsata, tana mik'e wa ta Jita garau hakan yasa ta kimtsa sannan ta koma bak'in gadon ta konta cikin jin wani irin baccin gajiya, Tana konciya Nenne na shigo wa had'in kaza ta karb'a mata wanda Hajjajo tayi mata sai ruwan tsumi mai dad'in sha, ajiye wa Nenne tayi sannan tace. "Taso kici abinci saiki kontan." ba musu ta sauk'o taci tasha dan tana jin yunwa, kuma yau tana jin dad'in yadda Nennen ta ke kula da ita wanda tunda ta nuna bata son Umar Nenne ta dena kulata sai yau d'in, tana gamawa ta koma ta konta tana kallon Nenne dake shirin shiga wonka cikin sanyi tace. "Nenne zazzab'i nake ji da ciwon kai." ba tare da ta kalleta ba tace. "Toh bari in gayawa Umar d'in yazo ya dubaki." fuska ta tsuke dan bata son abinda zai had'a ta dashi inuwa d'aya kuma gashi ta jawa kanta, bayan Nenne tayi wonkan ne ta shirya ta nufi d'akin Abba a tsakar gidan ta kalli Aliyu yana shirin shiga part d'in Hajjajo kiran shi tayi sannan tace. "Jeka kira Hamma Umar d'in ku kace Ummul bata da lafiya yaje ya dubata." "Toh" yace sannan ya nufi parlour Hajjajo yana zuwa ya samu Hamma Umar d'in yana zaune gefen Usman yana b'are mishi lemu, gefen shi ya zauna a hankali yace. "Hamma Anty Ummul bata da lafiya Nenne tace kaje ka dubata." kai ya gyad'a sannan yaci gaba da bawa Usman d'in kulawa, bayan ya gama bashi abinci ya bashi maganin sannan suka tafi part d'in su suna zuwa ya had'a mishi ruwan wonka, har cikin bathroom d'in ya rekashi kamar zaiyi mishi wonkan, murmushi Usman yayi tare da cewa. "Hamma yau wonkan ma zaka min ne?." "Kanaga ka girma ko?." kai ya sosa sannan yace. "Gaskiya dai Hamma na girma mai min wonka zai iya makancewa." K'eyan shi ya d'an buga sannan ya fita, shi kuma Usman wonkan yakeyi yana zubda k'ollah cikin tausayawa kanshi da d'an uwan nashi, bayan ya fito Hamma Umar ya shirya shi sannan ya kontar dashi kan gado ya zauna gefen shi yana shafa kanshi cikin sanyi yace. "Ammmi ta kiraka kana wonka nace mata kace min yanzu ka girma." ido ya lumshe yana jin dad'in yadda d'an uwan nashi ke kula dashi k'aunar shi na ratsa mai zuciya, ido ya lumshe cikin jin bacci yace. "Hamma ?." "Na'am Usman d'an uwana." kai ya jinji na sannan yace. "Ina sonka d'an uwana." kanshi ya rink'a shafawa yana cewa. "Usman duk duniya bani da tamkar ka ina sonka k'anina bani da buri a duniya daya wuce inga ka samu lafiya fatana a koda yaushe in ganka cikin farin ciki." ruggume juna sukayi sannan a hankali Umar ya kontar dashi sannan ya rink'a yi mishi karatu qura'ani a cikin kunnen shi murya cike da rauni, lokaci d'aya bacci ya tafi da Usman d'in, shi kuwa Hama Umar a hankali ya gyara mishi konciya sannan ya fito kai tsaye harabar gidan ya koma motar shi ya bud'e ya d'auki magungunan Ummul sannan ya nufi part d'in Nenne, yana shiga parlour ya samu ba kowa sai kuma yaji muryan Ummul dake magana da Anty Halima da woyar Nenne, cikin yin sallama ya shiga yana shiga ya zauna gefen Ummul d'in sannan yasa hannu ya karb'i woyar ya katse kiran , ita kuwa a fusashe ta juyo gare shi a nufin yin tsiwa, sai kuma tayi shiru jin yadda ya jawota jikin shi ya ruggume ta tsam a jikin shi sai sauk'e ajiyan zuciya yakeyi murya can k'asa yace. "Kun bani tsoro keda Usman in na rasaku bansan makomata ba Ummul Khairi ina tsoron abinda zai rabani daku, In babu Usman bansan ya rayuwa zata juya min ba." sai kuma ya k'ara matsota jikin shi d'umin jikinta na ratsa shi, ita kuwa tureshi takeyi tana k'ok'arin matsawa, jawota ya kumayi a hankali ya tallabo kanta kissing d'in ta yayi da kyau sannan yace. "Kiyi hak'uri my Khairi bazan sake wahala da keba." shiru tayi tana jin yadda yake fidda numfashin da sauri-sauri a haka har ya fara sauk'e ajiyan zuciya a hankali nitsuwarsa ta dawo jikin shi sannan ya bata maganin ya kontar da ita ya shafa fuskar ta sannan ya fita. A haka Hamma Umar ya wuni kula da k'anin shi da matar shi da derema haka ya kwana kula da Usman yayin da kewar Ummul ke cin jikin shi da zuciyar shi, koda gari ya waye haka ya wuni kula dasu, kuma Alhamhadullih duk sun mik'e musamman Ummul dan shi kam Usman k'arfin haline da son kontar da hankalin Hamman nashi, bayan Anyi salla isha ne Abba yace Hamma Umar su tafi tunda duk jikin su da sauk'i, bayan ya fita ne ya d'auko jakar Ummul ya bawa Aliyu ya kai mata cikin gida sannan yace . "In kaje kace tazo." "Toh" yace sannan ya nufi cikin gidan, a parlour Nenne ya samu su ya Adam cikin mamaki ya Sadik yace . "Jakar nanfa daga ina.?." "Ta Anty Ummul ce." Ya bashi amsa ya Adam ne ya kalli Ummul d'in cikin tsuke fuska yace. "Ba yanzu zaku tafiba?." Kai ta juya ido cike da k'ollah tace. "A a ni bazan komaba bani da lafiya." A hatsale ya bugawa Aliyu tsawa . "Maza ka meda jakar cikin motar Hamma Umar d'in ke kuma tashi kibi mijin ki ku tafi." shi kam Aliyu tuni ya juya da jakar ita kuwa hannun ta rink'a yarfa wa tana buga k'afafun ta tare da bud'e baki da k'arfi tana. "Ai Hamma Umar d'in ya yarda kuma bani da lafiya shike nan dan an tsaneni sai ayi ta korata a gidan mu." Kanta yayi da sauri yana zaro bel d'in k'ugunshi, ya Sadik kuma cewa yake. "Yauwa zaneta tunda bata jin magana." Ihu ta saki jin sauk'ar bel d'in a jikin ta a guje ta fita tana kuka, bayan Hamma Umar d'in ta tsaya tana tsalle da dire-dire tare da rik'e hannun shi , Abba ne ya fito dan jin kukanta yana zuwa ya kalli yadda takeyi sai murmushi yayi dan a fili yarintar Ummul take ganuwa, shi kuwa Adam tsawa yake buga mata yana. "Ki wuce ki shiga cikin mota." Abba ta kalla dan ko zaice ta dawo sai kuma ta shiga motar ganin yadda ya had'a fuska yana kallon ta, shi kuwa Abba cikin bada umarni yace. "Farouq shiga ku tafi. "toh." yace sannan ya shiga, Aliyu kuwa dariya yayi tare da d'aga tafin hannun shi ya saitasu da kanshi yana kad'a hannun tare da zaro harshen yana kad'awa Ummul cikin tsokana yace. "Bana gaya mikiba yanzu ke ba y'ar gida nan bane yanzu dagani sai Nenne na." ya k'arishe maganar yana rawa, Usman ne ya d'an roggoshi keyarshi yace. "Aliyu wato kaine d'an tada zaune tsaye ko." ita kuwa kuka tasa tana cewa. "Ya Usman ba kaga Aliyu ba." Murmushi yayi yace. "Muna sonki Ummul d'in mu ke y'ar gidan nance har Abadan." K'ollah ta zubda tare da cewa. "ya Usman kai kad'ai kake sona, nima ina sonka." Ido ya lumshe sannan yace. "Allah ya d'aiyiba." murmushi sukayi dukan su, shi kuwa Hamma Umar hannun Usman ya jawo ya d'an sunkuyo kanshi a hankali yace. "Ka kula da kanka d'an uwana ina son ka ina tsoron abinda zai cutar da kai." Murmushi yayi tare da cewa. "Nayi lafiya fa." Haka sukayi sallama suka tafi, Ita kuwa suna fita harabar gidan ta bud'e sabon shafin kuka, sunyi tafiya mai d'an nisa, Hamma Umar yana tuk'in hankalin shi na cikin tunanin halin da k'anin shi ke ciki, kamar a mafarki yaji Ummul tasa hannunta ta d'amk'o........ By *GARKUWAR FULANI* 濠电姷鏁告慨鐑藉极閸涘﹥鍙忛柣鎴濐潟閳ь剙鍊块幐濠冪珶閳哄绉€规洏鍔戝鍫曞箣閻欏懐骞㈤梻鍌欐祰椤鐣峰Ο琛℃灃婵炴垶纰嶉浠嬫煏閸繃鍋憸鐗堝笚閸嬫劗鈧懓澹婇崰鏍礈娴煎瓨鈷戞慨鐟版搐閳ь兙鍊濆畷鏉课旈崨顓囷箓鏌涢弴銊ョ仩闁告劏鍋撴俊鐐€栭崝锕€顭块埀顒傜磼椤旂厧顣崇紒杈ㄦ尰閹峰懘宕崟鎴欏劦閺屾盯鎮╅崘鎻掝潚婵犵绱曢弫璇茬暦閻旂⒈鏁嶆慨妯夸含閺夋悂姊绘担鍛婂暈闁瑰摜鍏橀幊妤呭箚閺夊簱鍋撶€靛摜纾介柛灞捐壘閳ь剙鍢查湁闁搞儯鍔婃禒鍫㈢磼鐎n収鍤︽繛鎴欏灩缁€鍐┿亜閺冨洤顥嶉柟鑺ユ礀閳规垿鎮欓弶鎴犱户闂佹悶鍔屽﹢杈╁垝鐠囨祴妲堥柕蹇ョ磿閸樻捇鏌℃径灞戒沪濠㈢懓妫濊棟闁挎柨顫曟禍婊勩亜閹哄棗浜惧銈嗗灥椤︻垶锝炶箛鎾佹椽顢旈崟顓у敹闂佺澹堥幓顏嗗緤閻戞ɑ鍙忛柛銉墯閳锋垿鏌i悢鍝勵暭闁哥喓鍋ら弻锝夊焺閸愨晝顦伴梺璇″枟椤洭鍩€椤掑﹦绉甸柛鐘愁殜閸╂盯骞嬮敂鐣屽幍缂備礁顑嗙€笛囧箲閿濆洨纾奸柣妯挎珪瀹曞矂鏌″畝鈧崰鏍х暦濮椻偓瀵濡烽妷銉ュ挤闂佽瀛╅鏍窗閺嶎厼鐤柛褎顨呴悡婵嬪箹濞n剙濡肩紒鐙呯秮閺岋絽螣绾板崬濮曠紓浣瑰敾缁绘繂顫忕紒妯诲濞撴凹鍨遍弫顖氼渻閵堝骸浜滄い锕傛涧閻e嘲鈹戠€n亜鍞ㄥ銈嗘尵閸犲孩绂掕椤啴濡堕崨顖滎唶闂佺粯顨呴敃顏堝箖閿熺姴唯闁挎柨澧介鏇㈡⒑閻熼偊鍤熷ù鍏肩箞椤㈡棃宕煎┑鍥发闂備焦瀵х换鍌毭洪悩璇茬;闁规崘鍩栭崰鍡涙煕閺囥劌澧版い锔哄姂濮婃椽骞愭惔銏紭闂佹悶鍔庨崕銈囩矚鏉堛劎绡€闁稿被鍊栧銊╂倵閸忓浜炬繝鐢靛Т閸犳岸鍩€椤掆偓椤﹁京妲愰幘璇茬<婵炲棙鍨垫俊浠嬫⒑閸濄儱浠滄い顓炲槻椤繑绂掔€n亞顦板銈嗗笒閸婄敻寮ㄩ搹顐ょ瘈闁汇垽娼у瓭濠电偞娼欓崐鍨嚕椤愶箑绀冮柍鐟般仒缁ㄥ姊洪崷顓炲妺闁搞劎鏁婚崺鈧い鎺嶇劍閸婃劗鈧娲栭幖顐︽偩濠靛绀嬫い鎴eГ鐎氬ジ姊绘担鍛婂暈缂佸搫娼″畷鏇㈠础閻愨晜鐎洪棅顐㈡处缁嬫帡鎮¢弴銏″€甸柨婵嗙凹缁ㄥ吋銇勯妷褍浠х紒杈ㄥ浮瀵噣宕掑顓犱邯闁诲孩顔栭崰妤呭箰閾忣偅鍙忛柍褜鍓熼弻宥夊煛娴e憡娈梺鍛婃⒐鐢绌辨繝鍥ㄥ€锋い蹇撳閸嬫捇寮介鐐殿槷闂佹寧娲栭崐鍝ョ矆閸喓绠鹃柟瀵稿仩婢规ɑ銇勯妷锕佸閾绘牠鏌ㄥ┑鍡樺櫣闁哄棛鍋ら弻宥夋煥鐎n亞浼岄梺鍝勬湰缁嬫垿鍩ユ径濠庢建闁割偅绻€缁憋絽鈹戦悩鎰佸晱闁哥姵鐗犲畷鎰板锤濡も偓閽冪喐绻涢幋娆忕仼婵☆偅锕㈤弻娑滎槼妞ゃ劌鎳庨锝嗗鐎涙ǚ鎷洪柡澶屽仦婢瑰棝藝閿斿墽纾煎璺猴功缁夋椽鏌e☉鍗炴灈閾伙絽銆掑鐓庣仯闁哥偟鏁诲娲川婵犲啫顦╅梺鍛婃尰缁嬫垹鍙呴梺鍦檸閸犳鎮″☉妯忓綊鏁愰崶銊ユ畬婵犳鍠栫粔鍫曞焵椤掑喚娼愭繛鎻掔箻瀹曟繈骞嬮敂琛″亾娴e壊娼ㄩ柍褜鍓熼獮鍐閵堝懐顦梺鍦帛鐢寮抽姀銏㈢=闁稿本鑹鹃埀顒佹倐瀹曟劙鎮滈懞銉ユ畱闂佸壊鍋呭ú鏍婵犳碍鐓欓柟顖嗗拑绱為梺鍝勬4闂勫嫭绌辨繝鍥舵晬婵犻潧瀚ч崑鎾诲焵椤掑嫭鐓涢悗锝庝簽鏁堥梺鍝勭焿缁绘繂鐣烽崼鏇炍ㄩ柕澹倻妫梻鍌欑閹碱偊骞忕€n喖绀堥柣鏃傚帶閽冪喐绻涢幋娆忕仼缂佺姵鐩濠氬醇閻旇 濮囬梺璇茬箰閻楀繒妲愰幘瀛樺闁圭粯甯婃竟鏇㈡⒒娴e憡鍟為柛鏃撶畵瀹曟澘螖閸涱喖浜楅棅顐㈡处閹告挳寮ㄦ禒瀣厽闁归偊鍘奸悘銉╂煕閻旂顎滈柛濠冩綑閳规垿鎮╅鑲╀紘濠电偛顦扮粙鎾诲焵椤掍礁鍤柛鎾跺枛瀹曟椽鎮欓崫鍕吅闂佹寧娲嶉崑鎾绘煟閹垮嫮绡€闁哄本鐩崺鍕礃閿旀寧鍕冨┑鐘灱椤煤濠婂懏顫曢柟鎯х摠婵挳鏌﹀Ο渚Ш濠㈣泛瀚槐鎾寸瑹閸パ勭亶闂佽崵鍠嗛崕鐢稿箖妤e啯鍊荤紒娑橆儐閺咁剟姊虹紒妯虹仴婵☆偅鐟╁鎻掆攽鐎n偀鎷洪梻鍌氱墛缁嬫挻鏅堕弴銏$厵鐎瑰嫰鍋婇崕蹇涙懚閻愬绡€濠电姴鍊绘晶娑㈡煃闁垮鐏撮柟顔肩秺楠炰線骞掗幋婵愮€虫繝鐢靛仜閹冲繘宕濆▎鎾宠摕闁绘梻鍘х粈鍕煏閸繃顥滄い蹇ユ嫹 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 2闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻锝夊箣閿濆憛鎾绘煕婵犲倹鍋ラ柡灞诲姂瀵挳鎮欏ù瀣壕闁告縿鍎抽惌鍡涙煕椤愩倕鏋戦柛娆忕箲娣囧﹪顢涘鍙樿檸闂佺粯鎸婚崝娆撳蓟濞戞埃鍋撻敐搴濈盎闁逞屽墯閹倿鍨鹃敃鍌氶敜婵°倓绀佸▓婵嬫⒒閸屾氨澧涚紒瀣灴閿濈偛鐣濋埀顒傛閹惧瓨濯撮柛婵嗗閳ь剙鐭傞弻娑㈠Ω閵壯冪厽閻庢鍠栭…閿嬩繆閹间礁鐓涢柛灞剧煯缁ㄤ粙姊绘担渚劸闁哄牜鍓涚划娆撳箣閿旂粯鏅滈梺璺ㄥ櫐閹凤拷0闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻锝夊箣閿濆憛鎾绘煕婵犲倹鍋ラ柡灞诲姂瀵挳鎮欏ù瀣壕闁告縿鍎抽惌鍡涙煕椤愩倕鏋戦柛娆忕箲娣囧﹪顢涘鍙樿檸闂佺粯鎸婚崝娆撳蓟濞戞埃鍋撻敐搴濈盎闁逞屽墯閹倿鍨鹃敃鍌氶敜婵°倓绀佸▓婵嬫⒒閸屾氨澧涚紒瀣灴閿濈偛鐣濋埀顒傛閹惧瓨濯撮柛婵嗗閳ь剙鐭傞弻娑㈠Ω閵壯冪厽閻庢鍠栭…閿嬩繆閹间礁鐓涢柛灞剧煯缁ㄤ粙姊绘担渚劸闁哄牜鍓涚划娆撳箣閿旂粯鏅滈梺璺ㄥ櫐閹凤拷 *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 濠电姷鏁告慨鐑藉极閸涘﹥鍙忛柣鎴濐潟閳ь剙鍊块幐濠冪珶閳哄绉€规洏鍔戝鍫曞箣閻欏懐骞㈤梻鍌欐祰椤鐣峰Ο琛℃灃婵炴垶纰嶉浠嬫煏閸繃鍋憸鐗堝笚閸嬫劗鈧懓澹婇崰鏍礈娴煎瓨鈷戞慨鐟版搐閳ь兙鍊濆畷鏉课旈崨顓囷箓鏌涢弴銊ョ仩缂佺姵鐩弻宥嗘姜閹峰矈鍞归梺绋款儐閹瑰洤顕i幘顔肩厬闁告繂瀚峰Σ鍛娿亜椤愶絿绠為柟铏矒閹粙妫冨☉妯哄挤闂傚倸鍊搁…顒勫磻閸曨個褰掑礋椤撶偟绛忛梺鍏间航閸庢娊銆呴弻銉︾厱闁圭偓顨呴幊鎰版晬濠婂牊鐓涘璺猴功婢ф垿鏌涢弬璺ㄐч挊鐔兼煕椤愮姴鍔滈柣鎾寸洴閹﹢鎮欓幓鎺嗘寖濠电偞褰冮悺銊┿€冮妷鈺傚€烽柛娆忣槸閺嬬娀姊虹化鏇熸澒闁告挻绻堥獮蹇涘川閺夋垹顦梺鑲┾拡閸忔﹢宕戦幘缁樺€婚柤鎭掑劗閹风粯绻涙潏鍓ф偧闁硅櫕鎹囬、姘煥閸涱垳锛滈柣搴秵閸嬪嫬霉椤旂瓔娈介柣鎰綑婵洦銇勯鐘茬仼闁伙絾绻堥崺鈧い鎺嶈兌椤╂煡姊洪鈧粔鐢稿煕閹烘嚚褰掓晲閸ャ劌娈屽銈嗘礃缁海妲愰幒鏃€瀚氶柟缁樺坊閸嬫捇宕稿Δ鍐ㄧウ婵犵數濮撮崯顖炲磿閻斿吋鐓忓┑鐐茬仢閸旀粓寮堕崼婵堝闁宠鍨块幃娆撳矗婢舵ɑ锛侀梻浣规偠閸斿酣骞婇幘鍦罕婵$偑鍊栭悧婊堝磻閻愮儤鍋傛繛鍡樻尰閸嬧剝绻涢崱妤冪妞ゅ繆鏅涢埞鎴︻敊閼测晛鈪甸梺鍝勭焿缁蹭粙鍩為幋锕€绠涙い蹇撶墕娴犳劙姊绘担鍛婃儓閻炴凹鍋婂畷婵嗙暆閸曨偆鍙€婵犮垼娉涜癌闁绘柨鍚嬮崐缁樹繆椤栨稒銇熼柛鐔奉儔濮婅櫣鎷犻崣澶婃敪濡炪値鍋勯ˇ顖滃弲濠殿喗銇涢崑鎾绘煛娴g鏆e┑顔瑰亾闂佺偨鍎寸亸娆戠不濮橆兘鏀芥い鏃傛櫕缁犳捇鏌i鐐靛妞ゎ剙锕、鏃堝幢濞嗘埊绱冲┑鐐舵彧缁插潡骞婇幘璇叉瀬濡わ絽鍟埛鎺楁煕閺囥劌浜滄い蹇d簽缁辨帒鐣濋崘顔兼懙缂備胶绮换鍫濈暦閸洘鍤嬮柛顭戝亝閻濇牕鈹戦敍鍕杭闁稿﹥鐗滈弫顕€骞掑Δ鈧壕褰掓煙闂傚顦﹂柡鍕╁劤閳ь剙鍘滈崑鎾绘煕閺囥劌鍘撮柟閿嬫そ濮婃椽宕ㄦ繝鍕窗闂佺楠稿畷顒勫煝瀹ュ牏鐤€婵炴垶鐟ч崢閬嶆煟鎼搭垳绉靛ù婊勭箞钘熼柣鎰暩绾惧ジ鏌¢崘銊モ偓鎼佸几濞戞埃鍋撳▓鍨灍闁规瓕娅曢幈銊╁焵椤掑嫭鐓冮柍杞扮閺嗘瑩鏌涢弮鈧敮妤佺┍婵犲洦鍊锋い蹇撳閸嬫捇寮介鐐殿槷闂佹寧娲栭崐鍝ョ矆閸喓绠鹃柟瀵稿仩婢规ɑ銇勯妷锕佸閾绘牠鏌ㄥ┑鍡樺櫣闁哄棛鍋ら弻宥夋煥鐎n亞浼岄梺鍝勬湰缁嬫垿鍩ユ径濠庢建闁割偅绻€缁憋絽鈹戦悩鎰佸晱闁哥姵鐗犲畷鎰板锤濡も偓閽冪喐绻涢幋娆忕仼婵☆偅锕㈤弻娑滎槼妞ゃ劌鎳庨锝嗗鐎涙ǚ鎷洪柡澶屽仦婢瑰棝藝閿斿墽纾煎璺猴功缁夋椽鏌e☉鍗炴灈閾伙絽銆掑鐓庣仯闁哥偟鏁诲娲川婵犲啫顦╅梺鍛婃尰缁嬫垹鍙呴梺鍦檸閸犳鎮″☉妯忓綊鏁愰崶銊ユ畬婵犳鍠栫粔鍫曞焵椤掑喚娼愭繛鎻掔箻瀹曟繈骞嬮敂琛″亾娴e壊娼ㄩ柍褜鍓熼獮鍐閵堝懐顦梺鍦帛鐢寮抽姀銏㈢=闁稿本鑹鹃埀顒佹倐瀹曟劙鎮滈懞銉ユ畱闂佸壊鍋呭ú鏍婵犳碍鐓欓柟顖嗗拑绱為梺鍝勬4闂勫嫭绌辨繝鍥舵晬婵犻潧瀚ч崑鎾诲焵椤掑嫭鐓涢悗锝庝簽鏁堥梺鍝勭焿缁绘繂鐣烽崼鏇炍ㄩ柕澹倻妫梻鍌欑閹碱偊骞忕€n喖绀堥柣鏃傚帶閽冪喐绻涢幋娆忕仼缂佺姵鐩濠氬醇閻旇 濮囬梺璇茬箰閻楀繒妲愰幘瀛樺闁圭粯甯婃竟鏇㈡⒒娴e憡鍟為柛鏃撶畵瀹曟澘螖閸涱喖浜楅棅顐㈡处閹告挳寮ㄦ禒瀣厽闁归偊鍘奸悘銉╂煕閻旂顎滈柛濠冩綑閳规垿鎮╅鑲╀紘濠电偛顦扮粙鎾诲焵椤掍礁鍤柛鎾跺枛瀹曟椽鎮欓崫鍕吅闂佹寧娲嶉崑鎾绘煟閹垮嫮绡€闁哄本鐩崺鍕礃閿旀寧鍕冨┑鐘灱椤煤濠婂懏顫曢柟鎯х摠婵挳鏌﹀Ο渚Ш濠㈣泛瀚槐鎾寸瑹閸パ勭亶闂佽崵鍠嗛崕鐢稿箖妤e啯鍊荤紒娑橆儐閺咁剟姊虹紒妯虹仴婵☆偅鐟╁鎻掆攽鐎n偀鎷洪梻鍌氱墛缁嬫挻鏅堕弴銏$厵鐎瑰嫰鍋婇崕蹇涙懚閻愬绡€濠电姴鍊绘晶娑㈡煃闁垮鐏撮柟顔肩秺楠炰線骞掗幋婵愮€虫繝鐢靛仜閹冲繘宕濆▎鎾宠摕闁绘梻鍘х粈鍕煏閸繃顥滄い蹇ユ嫹 *H*annun ta tasa ta damk'o siterin ta rink'a juyashi tare da murza shi da k'arfi tana. "Allah ka tsaya ni in sauk'a ehe, ni bazan koma gidan kaba ka sauk'e ni a nan zan tafi gidan Anty Halima." murza kan motar take da k'arfin ta, tuni motar ta fara yawo a tsakiyar titi ga ababen hawa dake ta gaban su da bayan su da gefe, gaba d'aya motar kanta ya kufce, a firgice yace. Innalillahi Ummul kin san abinda kikeyi kuwa?." fizge hannayen ta yayi da k'arfi cikin tashin hankali ganin ya nufi kan wani mai a dai-dai ta yana k'ok'arin hawa kanshi ita kuwa tak'i sakewa sai murzawa take tana. "Ka sauk'e ni a nan bazan koma gidan kaba bana sonka na tsaneka." Ido ya zaro cikin tashin hankali ganin saura k'iris ya taka wani mai reke da yake gefen titin gaba d'aya mutanen wurin sai rik'e kai sukayi suna. "Innalillahi subahanallahi." shi kuwa Hamma Umar cikin firgici da tsoron ganin zata sashin kisan kai gaba d'aya jikin shi sai rawa yake yi, cikin b'acin rai ya fizge hannayen ta sannan ya tura ta jikin sit d'in ta koma ta bugi jikin marfin motar sannan ta sake tasowa tana k'ok'arin sake rik'e kan motar, tsawa ya buga mata cikin zafin rai ya ware tafin hannun shi ya zuba mata mari d'aya wanda saida taga taurari na yawa a sararin samaniya kunnen ta saida ya bada sautin kiuuuu sannan ta kuma jin yayi dum lokaci d'aya zanen yatsun shi suka taso a farar fatarta tuni fuskar tayi jazir gaba d'aya ta rasa ina take dan marin ya gigitata, shi kuwa da k'er ya samu ya tsaida motar jikin shi na rawa zuciyar shi cike da tsoron karta sashi kisan kai yayi parking a gefen titin cikin sauri ya fito ya nufi gun mai reken da mai a daidaitan hak'uri ya rink'a basu, da sun hatsala amman ganin yadda yake basu hak'uri yasa sukace. "ba komai Allah ya tsare gaba a rink'a kula." "Toh nagode." yace dasu sannan ya koma cikin motar ya shiga ya zauna fuska a tsuke tamkar bai tab'a dariya ba, jan motar yayi da gudu ya kama hanyar damaturun, ita kuwa tunda ya zabga mata marin ta kife kanta kan cinyoyin ta ta rink'a kuka mai cike da takaici, bai kulata ba, ita kuwa kukan taci gaba dayi tana sheshshek'a, a haka har suka isa cikin damaturu a inda suna shiga hadari na tashi iska mai sanyi ya rink'a busawa tako ina sai walkiya ake da d'an rugugi alamu irin hadarin karshen damuna ce, suna isa yayi parking sannan ya koma ya zauna ya jingunu da jikin kujerar yana jin yadda take kuka, a zahiri mamaki yake irin tsanar da Ummul ke mishi sannan itace da laifi itace da kuka kuma har cikin ranshi yaji zafin marin da yamata, ajiyan zuciya ya sauk'e sannan yasa hannu ya d'an dagota ya jingina ta da jikin shi hannun ta ya kamo cikin sanyi ya cusa hannun kan k'irjin shi sai kuma ya kalleta a hankali yace. "Kiji yadda kikasa zuciya ta bugawa dan tsoron karki sani nayi kisan kai Ummul nine ba kyaso amman k'iyeyyar har tana k'ok'arin saki in kashe wasu a banza." sai kuma yayi shiru sannan yasa tafin hannun shi yana shafa fuskar ta a hankali yace. "Kukan ki nasa zuciya ta tayi nauyi sabida sai inga kamar na k'asa rik'e amanar dana d'auka ne kiyi hak'uri ki gafar ceni banyi niyar tab'a lafiyar jikin kiba." tureshi ta rink'a yi tana janye hannun ta, shi kuwa rik'e hannun yayi a hankali ya bud'e d'an durowan gaban motar wani d'an k'ara min kontena ya d'auko bud'e wa yayi sannan ya d'auko wani zoben Diamonds sai shek'i yakeyi tamkar tauraro yatsarta ya d'an d'ago a hankali ya zira mata zoben cikin sanyi yace. "Kinyi kyau matata yatsarki ta haska zoben." fizge hannun tayi dai-dai lokacin da ruwan sama ya fara sauk'a , bud'e motar tayi ta fice cikin kuka ta koma can tsakiyar harabar gidan ta tsaya tana kuka, ganin haka ya fito ya rufe motar cikin sauri yaje gabanta hannun ta ya rik'o tare da cewa. "Kiyi hak'uri zomu shiga cikin gida kar ruwan ya tab'a mu, kinsan ni bana son ruwan sama ya tab'a ni zai sani zazzab'i." cogewa tayi fir tak'i shiga daya kamo hannun ta sai ta dasa mai ihu, ganin haka ya rufe gidan sannan ya wuce ya shiga cikin gida a zaton shi ko zataji tsoro ta biyoshi, Abu kamar wasa ya shiga, ita kuwa sai tsuguna wa tayi a wurin ruwan yana ta sauk'a a kanta duk ta jik'e tayi jilik sai d'iga takeyi ga tsawa da walkiya da akeyi, parlour ya fito rik'e da leima ya nufi gunta, yana zuwa ya jawota jikin shi cikin rawan sanyi yace. "Khairi kiyi hak'uri mu shiga cikin gida kar mura ta kamaki d'an Allah mushiga ciki bana so ruwan ya tab'ani." Jin haka ta fizgota leimar ta cillata gefe haka ko iska ya debeta yayi woje da ita, shi kuwa da sauri ya d'ago hular rigar shi da take konce a kafad'an shi ya rufe tsakiyar kanshi dan in ruwan sama ya bugi kanshi yana sashi zazzab'i da ciwon kai mai tsananin, hannun shi kuwa ya hard'e a k'irjin shi tuni ya jik'e cikin rawan sanyi da karkarwa ya jawota jikin shi a hankali yace. "Toh aikin rama mu tafi cikin gida kiyi hak'uri k'anwata." cikin kuka tace. "Ban rama ba kam, kuma bazan shiga gidan kaba sai in zan rama marin da kayi min." murya na rawan sanyi yace. "Na yarda mu shiga saiki rama." baki ta tura sannan tace "toh." hannun ta yaja suka shiga cikin gidan , suna shiga d'akin ta ya nufa da ita, a gaban mirror ya tsaya da ita, cikin rawan sanyi ya cire mata mayafin nata sannan ya zuge zip d'in rigar ta yasa hannu zai cire mata rigar tayi maza a juya tana hararan shi tana cewa. "Ka barni in cire abina da kaina ." "Na barki nima bari inje in cire nawa." sai kuma ya bud'e durowa ya zaro mata riga da wondo wondon iya guiwa sai rigar mai d'an fad'in wuya ta yadda kafad'an ta yake fita inya ta saka kayane mai tashi da sulbi, kan gado ya ajiye mata sannan ya fita ya koma bedroom d'in shi, yana shiga ya canza kayan shi sannan ya fito ya nufi kitchen tea ya dafa musu mai zafi wai maganin sanyin, d'akin shi ya koma da niyar d'auko woyarshi yana rik'e da cups d'in yana juyowa da nufin zai fita kenan ya ganta tsaye a bak'in k'ofar shigowan fuska a had'e tace. "Zan rama fa ehe." Ido ya tsura mata cikin mamaki ajiye cups d'in yayi kan mirror sannan ya juyo a hankali yace. "Toh zoki rama." shigo wa tayi ta tsaya a gaban shi ta d'an d'ago kanta tana kallon fuskar shi, shi kuwa kollon d'an tsawonta yake tunda ko fuskarsa in zata kalla sai ta daga wuya da kai, kuma wai shine tana ikirarin tazo ta rama marin daya mata, cikin ranshi kuwa jira yake yaga iya rashin kunyarta zata mareshin neko k'ak'a, ganin tana ta d'ago wuya da k'afafun ta dan ta isoshi tsawo ta kasa, sai ya d'an rok'ofo kanshi ya sunkuyar dai-dai tsawonta cikin rumtse ido yace. "Rama." fuskar shi ta tsurawa ido ta d'ago hannun zata yarfa mai marin sai kuma tayi maza tayi k'asa da hannun sai hawaye car-car a idanun ta, shi kuwa jin shirun ne sai ya bud'e idanun shi ganin tana kallon fuskar shi tana kuka yasa ya d'an yi murmushi cikin kula ya jawota jikin shi ya ruggume ta kanshi ya sunkuyar dai-dai kan hab'arta daya maran a hankali ya rink'a fese mata iskan bak'in shi mai sanyi sannan yasa tafin hannun shi yana share mata k'ollah, ita kuwa cikin kuka tace. "Ni dai sai na rama amman ba, a fuskar kaba." murmushi yayi a ranshi yace. "Gaskiyar bahaushe wata fuskar tafi k'arfin mari." fahimtar da yayi bazata iya ramawan bane, sai ya mik'o mata cup d'in tea shima ya d'auki d'ayan ya fara sha yana lumshe ido cikin lallashi yace. "Kisha tea sai na goyeki a madadin marin." ajiye cup d'in tayi tace ita bazata shaba kuma shima ya ajiye sai ya goye tan, murmushi yayi ya ajiye cup d'in yana jin sanyi na ratsashi, tsakiyar d'akin ya dawo kan carpet ya durk'usa ya mik'e tsawonshi kamar mai konciya sai kuma ya d'an taso ya k'afa hannun shi a k'asa sannan ya mik'e tsawonshi , cikin sanyi yace. "Toh zoki hau." murmushi mugunta tayi dan tanaga bazai iya d'aukar nauyin taba, da sauri ta matso ta zauna a tsakiyar bayan shi sannan ta tonk'oshe k'afafun ta ta d'an ware hannun ta sannan ta had'a yatsun ta haka濠电姷鏁告慨鐑藉极閸涘﹥鍙忛柣鎴濐潟閳ь剙鍊块幐濠冪珶閳哄绉€规洏鍔戝鍫曞箣閻欏懐骞㈤梻鍌欐祰椤鐣峰Ο琛℃灃婵炴垶纰嶉浠嬫煏閸繃鍋憸鐗堝笚閸嬫劗鈧懓澹婇崰鏍礈娴煎瓨鈷戞慨鐟版搐閳ь兙鍊濆畷鏉课旈崨顓囷箓鏌涢弴銊ョ仩闁告劏鍋撴俊鐐€栭崝锕€顭块埀顒傜磼椤旇偐鍩f慨濠傛惈鏁堥柛銉戔偓閸嬫捇濡舵径濠囨7闂佹寧绻傞ˇ顖炴嫅閻斿吋鐓ユ繝闈涙閸熸帡鏌i弬鎸庢儓闁哄鐗撻弻娑樜旈崘銊ょ捕濡炪値鍋呭銊ф閹捐纾兼繛鍡樺姉閵堢増淇婇悙宸殶妞ゎ厼鐗愰悘瀣⒑閸涘﹤濮﹂柛鐘崇墵閹锋垿鎮㈤崫銉ь啎闂佺懓鐡ㄩ悷銉╂倶閳哄啰纾奸柣妯虹-濞叉挳鏌$仦鐣屝f繛纰变邯楠炲秹顢氶崨顔ф粍淇婇悙顏勨偓銈夊礈濞嗘搩鏁勯柛娑欐綑閻撴﹢鏌熸潏楣冩闁稿﹪顥撻埀顒傛嚀婢瑰﹪宕板Δ鍜佹晛闁糕剝绋掗埛鎴︽煟閻斿憡绶叉繛鍫氭櫊閺岀喖宕欓妶鍡楊伓 tana ta murmushi mugunta , dai-dai lokacin woyarshi ta rink'a suwa ita kuwa sai gyad'a kai take tana lumshe ido, yana kallon ta duk abin da takeyi, a haka har zuwa wani d'an lokaci sannan ya manna jikin shi kan carpet d'in ya kwanta yana maida numfashi, itako murmushi tayi sannan ta mik'e zata tafi, sai ya rik'o hannun ta ya fizgota jikin shi ya matseta gam cikin maida numfashi yace. "An gaya miki ni dokine da zan goyeki a banza, nima saina samu maganin sanyin da kika samin." Baki ta tura tace. "Toh ai ba ladan mari bane, kuma ni bani da maganin sanyi." "Kina dashi mana." "Toh ina yake?." hanun shi ya cusa cikin jikin ta tare da lumshe ido yace. "D'umin jikin kine kawai zai cire min wannan sanyin inba hakaba zai sani zazzab'i." tureshi tayi ta mik'e sai kuma ta d'an yi k'ara jin yadda yake murza hannun shi a kan k'irjin ta, murmushi yayi ya mik'a hannun kan gado ya jawo blanket sannan ya jawota jikin shi kan carpet d'in ya kuma rufesu da blanket d'in, hannun shi yasa yana shafa cikin ta a hankali yace. "Ina son Baby daga gareni Khairi kiyi Addu'a Allah yasa yau nayi ajiya a nan." tureshi takeyi shiko sai murzata yakeyi a hankali yace. "Kiyi hak'uri in kasance dake." Cikin fad'a tace. "Bana so." da sauri yace. "Karya ne kina so kam." hawaye ta fara zubdawa tana jin yadda yake murzata da juyata, ita kuwa, tureshi take d'an yi duk da yau yana binta a hankali ba zafi sosai, amman sai kuka takeyi cikin raki tana cewa. "Bana sonka na tsaneka." duk da yana cikin duniyar nitsuwa Amman yaji zafin kalamta gare shi, a ranshi yake fad'in. "Ko cikin yanayin da ma'aurata suke ruggume juna dayin musayan kalaman soyayya shi a cikin yanayin ma Ummul tureshi take a madadin ta mak'ale shi sannan kalaman k'iyeyya take fad'a mishi a madadin na soyayya kuma kuka take na jin tsanarshi a madadin tayi kukan gamsuwa, haka ya zame jikin shi ya konta gefe sannan ya jawota ya ruggume ta da k'arfi yana fidda nannauyan numfashin a hankali yace. " wata rana zaki soni Khairi , fatana Allah yasa jinin na ya gauraye da naki, ki haifarmin d'ana nasan shi kam zai soni." manne wa tayi a jikin shi dan ya gajiyar da ita ga kasala daya k'ara rufeta numfashi ta rink'a maidawa a hankali, cikin ranta kuwa fad'i take. "Tabbas in nayi garaje Hamma Umar zai d'irka min ciki ya barni da matsala." a haka da wannan tunanin tayi bacci a jikin shi, shi kuwa ruggume ta yayi har saida yaji baccin ta yayi nisa sannan ya mai data kan gado shi kuma ya gyara wurin yaje yayi wonka yayi al'wala yazo yayi ta nafilfilin daya saba da karatu qura'an, sai k'arfe 2:30 ya konta ruggume da ita. Washe gari da safe bayan ya gaba komai ya shirya ya fita, yana fita itama ta fita kai tsaye kemis na bayan layinsu taje k'wayoyin family planning ta seyo tazo ta boye wanda kullum sai tasha, acewarta bazata haihu dashiba in yana son haihuwa ya saketa ya auro wata. Haka rayuwa taci gaba da tafiya kullum sai tasha maganin a boye duk da ba wani bashi kanta takeyi ba, bayan ta fara shan maganin da kwana goma kawai ranan ya shiga ya samu tasha maganin kenan tana rik'e da sachet d'in, sosai Ummul taji tsoro da mamakin yadda Hamma Umar d'in ya birkice mata tamkar zaiyi hauka bata tab'a ganin baccin ranshi kamar na wannan ranar ba, ya rink'a surface mata fad'a daga karshe ya kwashesu yace zai kai ya nunawa Abba , ganin haka tayi ta kuka tana bashi hak'uri tare da cewa bazata sake shaba, ganin yadda ta nuna bazata kuma ba yaji dad'i ya yarda ya barta bayan yayi ta mata nasiha. Toh fa bayan sunyi haka da kwana biyu ta lallab'a taje wani prvt hospital ta shirga k'ariyar ta kan cewa da yardar mijin ta suko tunda aikin kud'i ne ba wani dogon bincike suka sa mata y'ar robarnan da ake tsawa a hannu suka d'inke mata, suka amshi kud'insu ko a jikin su, koda ta dawo haka tayi ta wasan b'uya da Hamma Umar d'in har saida wurin d'inkin ya worke ras ta yadda bazai ganeba, shi kuwa kullum addu'ar shi Allah ya bawa Ummul d'in ciki yanaga duk abin nata zai ragu inta fara haihuwa dashi. Yau Saturday tun safe Hamma Umar baije ko inaba yana gida ko parlour bai fitoba yana d'akin shi , dan ya fara gajiya da azabtar dashi da Ummul keyi, ita kuwa Ummul tun safe ta shirya a nufinta in taga ya fito zai tafi potaskum zatace zata bishi, ganin shiru-shiru bai fito bane har bayan sallan la'asar saita fito a hankali ta nufi d'akin nashi, a hankali tayi sallama tare da tura k'ofar ta shiga, kan gadon ta hoggoshi yana kwance yayi rigingine ida nunshi a lumshe ba komai a jikin shi sai towel dake d'aure a k'ugunshi alamun daga wonka ya fito, shiru bai amsa sallamar taba, shigowa tayi cikin d'aga k'afafun ta a hankali bak'in gadon taje ta tsaya tana son ta tasheshi ta rasa ya zatayi ta tasheshin gashi gaba d'aya ganin surar jikin shi na bata tsoro, a hankali ta durk'usa a bakin gadon cikin kauda fuska ta fara magana. "Hamma! Hamma! Hamma ka tashi mana." yana jinta yayi shiru kamar maiyin bacci a ranshi kuwa farin ciki yake da shigowar ta d'akin nashi, ita kuwa tashi tayi ta zauna gefen shi a bakin gadon a hankali tace. "Hamma yau bazaki je gida bane? Hama weekand d'in ma baza'a fitaba ni ina son zuwa inga Nenne na." murmushi ya d'an yi gano yawo take son fita shiyasa take wani yin ladabin kura ga mai akuya, mik'a yayi a hankali sannan yasa hannu ya jawota kan k'irjin shi hannun shi yasa ya rink'a shafa bayan ta a hankali yace. "Zamuje mana in kina so." Mutsumutsu ta rink'a yi cikin had'e fuska tace. "Ehh ina so mana ka tashi mu tafi." towel d'in nashi ya rink'a murzawa tare da jawo blanket ya rufe su sannan ya k'ara jawota jikin shi a hankali yace. "Bazan iya tuk'in ba sai an bani maganin." hannu tasa tana ture hannu shi da yaketa b'alle boturan gaban rigar ta mai dogon hannu wai duk dan ta boye tabon abin family planning d'in ne, shi kuwa ido a rufe ya zare rigar tata, sannan ya kuma rink'a shafa wutanta ido a lumshe a hankali har ya isa kan damtsen hannun ta da akasawa robar, ido ya bud'e jin kamar d'an k'urji a cikin hannun nata gashi da alamun kamar tabo, da sauri ya tashi zaune cikin hamzari ya d'ago ta ya manna ta a k'irjin shi sannan yasa hannu ya kamo hannun nata ya d'an daga, da sauri ya tureta cikin wani irin yanayi ya kafa mata. By *GARKUWAR FULANI* 婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戣棄鏋侀柛娑橈攻閸欏繘鏌i幋婵愭綗闁逞屽墮閸婂潡骞愭繝鍐彾闁冲搫顑囩粔顔锯偓瑙勬磸閸旀垵顕i崼鏇炵闁绘瑥鎳愰獮銏ゆ⒒閸屾瑦绁版い顐㈩槸閻e嘲螣鐞涒剝鐏冨┑鐐村灦绾板秹顢曟禒瀣厪闁割偅绻冮崑顏嗘喐閻楀牆绗氶柛瀣姉閳ь剛鎳撴竟濠囧窗閺嶎厼绀堝ù鐓庣摠閳锋垶鎱ㄩ悷鐗堟悙闁逞屽厵閸婃繂鐣烽弶璇炬棃宕ㄩ鍥风畵閺屾盯寮撮妸銉т哗闂佸憡鍔忛崑鎾翠繆閻愵亜鈧牠宕濋敃鈧…鍧楀焵椤掑倻纾兼い鏃傚帶椤e磭绱掓潏銊﹀鞍闁瑰嘲鎳樺畷顐﹀礋閹存瑥鍔﹂柡灞剧洴閹晛鐣烽崶褉鎷伴柣搴㈩問閸犳牠鈥﹂柨瀣╃箚闁归棿绀侀悡娑㈡煕鐏炲墽鐓紒銊ょ矙濮婄粯鎷呮笟顖滃姼闂佸搫鐗滈崜娑氬垝濞嗘挸绠i柨鏃傜帛閺呮粓姊虹捄銊ユ珢闁瑰嚖鎷� 婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戣棄鏋侀柛娑橈攻閸欏繘鏌i幋婵愭綗闁逞屽墮閸婂潡骞愭繝鍐彾闁冲搫顑囩粔顔锯偓瑙勬磸閸旀垵顕i崼鏇炵闁绘瑥鎳愰獮銏ゆ⒒閸屾瑦绁版い顐㈩槸閻e嘲螣鐞涒剝鐏冨┑鐐村灦绾板秹顢曟禒瀣厪闁割偅绻冮崑顏嗘喐閻楀牆绗氶柛瀣姉閳ь剛鎳撴竟濠囧窗閺嶎厼绀堝ù鐓庣摠閳锋垶鎱ㄩ悷鐗堟悙闁逞屽厵閸婃繂鐣烽弶璇炬棃宕ㄩ鍥风畵閺屾盯寮撮妸銉т哗缂備胶濮甸惄顖炲蓟瀹ュ棙濮滈柟宄扮焾閸炲綊姊虹粙娆惧剱闁圭懓娲ら锝夊箻椤旇偐鍘梺鍛婄箓鐎氬嘲危閸涘浜滄い鎰剁悼缁犵偤鏌熼搹顐ょ煉闁诡喕绮欏Λ鍐ㄢ槈濡搫鎸ら梻鍌氬€搁崐鎼佲€﹂鍕;闁告洦鍊嬭ぐ鎺戠妞ゆ挾鍋熺粵蹇涙⒑閸忛棿鑸柛搴㈠▕閵嗗懘寮婚妷锔惧幈闂佸湱鍋撻〃鍛村箠閹扮増鏅繝濠傜墛閻撴稑顭跨捄鐚村姛濠⒀勫灴閺屾盯寮捄銊愌囨寠閻斿吋鐓曟い鎰Т閸旀粓鏌i幘瀵告创闁诡喗锕㈤幃娆撳箵閹哄棙瀵栨繝鐢靛仦瑜板啴鎮洪妸鈹库偓鍐Ψ閳哄倸鈧兘鏌涘▎蹇fЦ闁哄濞€濮婅櫣鍖栭弴鐔告緬闂佸憡鎸荤换鍫ョ嵁韫囨稑宸濋柡澶嬪灩椤︻參姊洪懖鈹炬嫛闁稿繑锕㈠畷鎴﹀箻缂佹ê鈧鏌ら幁鎺戝姉闁归绮换娑欐綇閸撗勫仹闂佺娅曢幑鍥€佸顒夌叆闁告侗鍨抽敍婊堟煟鎼搭垳绉甸柛瀣闇夋い鏃傜摂濞堜粙鏌i幇顓熺稇濠殿喖娲﹂妵鍕敃閻樿尙浠奸梺浼欑稻缁诲牓宕洪埀顒併亜閹哄秷鍏屾い鈺傜叀濮婃椽顢楅埀顒傜矓閻㈢鐓曢柟鐑樺殮瑜版帗鏅查柛銉e妼濞堝苯顪冮妶鍡樼缂侇喖娴峰Σ鎰板箳閺冣偓鐎氭岸鏌熺紒妯哄潑闁稿鎹囧畷绋课旈崘銊с偊濠电姷鏁告慨鎾疮椤栫偛纾块柣鏂垮悑閻撳繐鈹戦悙鑼虎闁告梹绮撳鍫曞醇濠靛牆顣洪梺瀹狀潐閸ㄥ潡骞冨▎鎾崇煑濠㈣埖蓱閿涗線姊绘担瑙勫仩闁告柨閰i獮濠囧箻閸︻厺缃曞┑锛勫亼閸婃牠鎮у鍫濈;闁绘劗鍎ら崑鍌涚箾閸℃ɑ灏伴柛瀣у墲缁绘盯宕卞Δ鍐唶濡炪倕绻嗛弲娑㈠煘閹达富鏁婇柤娴嬫櫅閳敻姊洪崫鍕効缂佽弓绮欓崺鐐哄箣閿曗偓缁犳稒銇勮箛鎾跺濞寸姵鍔欏缁樻媴閸涘﹥鍎撻柣鐐村嚬閸嬪﹤鐣峰┑鍡欐殕闁告洦鍋嗛崣鈧┑鐘灱濞夋稖鐧岄梺缁樻煥閸氬宕愮紒妯圭箚妞ゆ牗绋掗妵鐔兼煕閻斿鍎旀慨濠呮閹风娀宕f径濠冩暘婵$偑鍊ら崑鍕囬婊冨疾婵犳鍠楅妵娑㈠磻閹剧粯鐓涘ù锝囶焾閺嗭絽鈹戦鐟颁壕闂備胶鍋ㄩ崕瀵镐焊濞嗘垹涓嶆慨姗嗗厴閺€鑺ャ亜閺冨倹娅曠紒鐘虫崌閺岋綁顢橀悙闈涱暫濡炪値鍓欓敃顏堛€侀弮鍫濆耿婵炲棙鍩婄槐鍐测攽閻愯埖褰х紒鎻掓健楠炲﹪骞樼拠鍙夌€俊銈忕到閸燁垶鍩涢幒妤佺厱闁哄洢鍔屾禍婊勩亜韫囷絼绨界紒杈ㄥ笒閻f繈宕橀鍏兼嚈缂傚倷鑳剁划顖滄崲閸繄鏆﹂柛顐f礃閸ゅ鏌涢…鎴濅簼闁绘繃鐗曢埞鎴︽晬閸曨偂鏉梺绋匡攻閻楁粓寮鈧獮鎺懳旈埀顒傚瑜版帗鐓欓梻鍌氼嚟椤︼箓鏌¢崟鈺佸姢闁逞屽墮閸樻粓宕戦幘缁樼厱闁哄洢鍔岄崢鎾煙闁垮銇濇慨濠冩そ瀹曘劍绻濋崟顓犵獥闂備胶顭堟绋跨暦椤掑嫬鐓濈€广儱鐗忛悿鈧┑鐐村灦閻熝囧储闁秵鐓熼幖鎼灣缁夐潧霉濠婂嫮绠為挊鐔兼煟閹邦喗鏆╃痪鎯с偢閺岋繝宕橀妸銉㈠亾閹间礁鍑犳繛鎴炲焹閸嬫挸鈻撻崹顔界亶闂佽鐡曞▍鏇㈠箞閵娾晛鐒垫い鎺戝閻撳啴鏌嶆潪鎵槮闁哄棙鐟╅弻娑㈠籍閳ь剛鏁Δ浣衡攳濠电姴娲﹂崐閿嬨亜韫囨挸顏ら柛瀣崌瀵粙顢橀悙娈挎Х闂備焦瀵уú鏍磹閸濄儳鐭嗛柛顐ゅ枔缁犻箖鏌熺€电浠╁瑙勆戦妵鍕Ψ閿曚礁顥濋柧缁樼墵閺屻劌鈹戦崱妯烘闂佸搫妫涢崑銈夊蓟瀹ュ鐓ラ悗锝庝簽娴煎矂姊洪崫鍕拱缂佸鍨块崺銉﹀緞婵犲孩寤洪梺鍓插亝缁烩偓缂佹唻绲介埞鎴︽偐閹颁礁鏅遍梺鍝ュУ閻楃姴鐣烽幇鏉块敜婵°倐鍋撻柦鍐枑缁绘盯骞嬪▎蹇曚患濠碘槅鍋呴敃銏ゅ蓟濞戞粠妲煎銈冨妼閹冲酣顢氶敐鍡楊嚤閻庢稒菤閹锋椽鏌℃径灞戒沪濠㈢懓妫濊棟闁挎柨澧界壕鐓庮熆鐠虹尨鍔熺紒澶嬫そ閺岋絽鈽夐崡鐐寸亪闁句紮绲介妴鎺戭潩閻撳海浠梺鍝ュ仧閺佽顫忓ú顏勫窛濠电姴鍟ˇ鈺呮⒑閸涘﹥灏扮紒瀣灩閸欏懘姊洪崷顓℃闁哥姵顨婇幃鈥斥槈濡繐缍婇弫鎰板炊閵娿儲鐣┑鐘愁問閸犳牜绮旈崼鏇炵劦妞ゆ帒鍠氬鎰箾閹绘帞绠荤€规洘绻堥獮瀣晜鐞涒€充壕濞达絽澹婂銊╂煃瑜滈崜鐔肩嵁閸愵喖顫呴柕鍫濇噽椤︻參姊洪崷顓犲笡閻㈩垱顨婂鎶藉閵忋垻锛濋梺绋挎湰閼归箖鍩€椤掍焦鍊愮€规洘鍔欓幃婊堟嚍閵夈儲鐣遍梻浣稿閸嬪懎煤閺嶎偄顥氬┑鐘崇閻撴瑩鏌熼鍡楁嫅缁辩偤姊洪崫鍕紨闂傚嫬瀚粚杈ㄧ節閸ヨ埖鏅┑鐘绘涧鐎氀囧磻閹捐鐒垫い鎺戝閻撴盯鎮楅敐搴濈敖閺佸牓姊洪崫鍕効缂佺粯绻傞悾鐑藉醇閺囩倣銊╂煏婢诡垰鍊诲Λ顖炴⒒閸屾瑧顦﹂柟纰卞亰楠炲繒鈧綆鍠栫粈鍫ユ煟閺冨倸甯堕柦鍐枑缁绘盯骞嬪▎蹇曚患缂備胶濮甸惄顖氼潖婵犳艾閱囬柣鏃囥€€婵洭姊虹拠鑼闁绘绻掑Σ鎰板箻鐎涙ê顎撻梺鍦帛鐢﹥绔熼弴銏♀拻濞达絽鎲¢崯鐐烘煕閺冩挾鐣电€规洘婢樿灃闁告侗鍠栨禍妤呮椤愩垺澶勯柟鍛婃尦瀵劍绂掔€n偆鍘介梺褰掑亰閸樺ジ鎮橀妷鈺傜厱闁绘梻顭堥婊堟煕婵犲啯缍戦柍瑙勫灴閹晠顢欓懖鈺€绱樻俊鐐€栧褰掑礉濞嗘挾宓侀煫鍥ㄧ⊕閺呮悂鏌ㄩ悤鍌涘 *RUBUTACCEN AL,AMARI* Page 2闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻鐔兼⒒鐎靛壊妲紒鐐劤缂嶅﹪寮婚敐澶婄闁挎繂鎲涢幘缁樼厱濠电姴鍊归崑銉╂煛鐏炶濮傜€殿喗鎸抽幃娆徝圭€n亙澹曢梺鍛婄缚閸庢娊鎯岄崱娑欑厱妞ゆ劑鍊曢弸鎴︽煕濞嗗繒绠插ǎ鍥э躬椤㈡稑顫濋崣妯挎闂備胶绮幐濠氬礉濞嗘挸钃熸繛鎴炲焹閸嬫捇鏁愭惔婵堢泿闂侀€炲苯澧柟顔煎€块崹楣冩晝閸屾岸鏁滃┑掳鍊撶粈浣糕枔濠靛鈷掗柛灞炬皑婢ф稓绱掔€n偄鐏撮柨婵堝仜閻f繈鍩€椤掑倹顫曢柟鎯х摠婵挳鏌涘┑鍡楊伌闁逞屽墮閻倿寮诲☉銏犖╅柕澹啰鍘介柣搴㈩問閸犳牠鈥﹂柨瀣╃箚闁归棿绀侀悡娑㈡煕鐏炲墽鐓紒銊ょ矙濮婄粯鎷呮笟顖滃姼闂佸搫鐗滈崜娑氬垝濞嗘挸绠i柨鏃傜帛閺呮粓姊虹捄銊ユ珢闁瑰嚖鎷�1闂傚倸鍊搁崐鎼佸磹閹间礁纾归柟闂寸绾惧綊鏌熼梻瀵割槮缁炬儳缍婇弻鐔兼⒒鐎靛壊妲紒鐐劤缂嶅﹪寮婚敐澶婄闁挎繂鎲涢幘缁樼厱濠电姴鍊归崑銉╂煛鐏炶濮傜€殿喗鎸抽幃娆徝圭€n亙澹曢梺鍛婄缚閸庢娊鎯岄崱娑欑厱妞ゆ劑鍊曢弸鎴︽煕濞嗗繒绠插ǎ鍥э躬椤㈡稑顫濋崣妯挎闂備胶绮幐濠氬礉濞嗘挸钃熸繛鎴炲焹閸嬫捇鏁愭惔婵堢泿闂侀€炲苯澧柟顔煎€块崹楣冩晝閸屾岸鏁滃┑掳鍊撶粈浣糕枔濠靛鈷掗柛灞炬皑婢ф稓绱掔€n偄鐏撮柨婵堝仜閻f繈鍩€椤掑倹顫曢柟鎯х摠婵挳鏌涘┑鍡楊伌闁逞屽墮閻倿寮诲☉銏犖╅柕澹啰鍘介柣搴㈩問閸犳牠鈥﹂柨瀣╃箚闁归棿绀侀悡娑㈡煕鐏炲墽鐓紒銊ょ矙濮婄粯鎷呮笟顖滃姼闂佸搫鐗滈崜娑氬垝濞嗘挸绠i柨鏃傜帛閺呮粓姊虹捄銊ユ珢闁瑰嚖鎷� *NA* *AYSHA ALI GARKUWA* 婵犵數濮烽弫鍛婃叏閻戣棄鏋侀柛娑橈攻閸欏繘鏌i幋婵愭綗闁逞屽墮閸婂潡骞愭繝鍐彾闁冲搫顑囩粔顔锯偓瑙勬磸閸旀垵顕i崼鏇炵闁绘瑥鎳愰獮銏ゆ⒒閸屾瑦绁版い顐㈩槸閻e嘲螣鐞涒剝鐏冨┑鐐村灦绾板秹顢曟禒瀣厪闁割偅绻冮崑顏嗘喐閻楀牆绗氶柛瀣姉閳ь剛鎳撴竟濠囧窗閺嶎厼绀堝ù鐓庣摠閳锋垶鎱ㄩ悷鐗堟悙闁逞屽厵閸婃繂鐣烽弶璇炬棃宕ㄩ鍥风畵閺屾盯寮撮妸銉т哗缂備胶濮甸惄顖炲蓟瀹ュ棙濮滈柟宄扮焾閸炲綊姊虹粙娆惧剱闁圭懓娲ら锝夊箻椤旇偐鍘梺鍛婄箓鐎氬嘲危閸涘浜滄い鎰剁悼缁犵偤鏌熼搹顐ょ煉闁诡喕绮欏Λ鍐ㄢ槈濡搫鎸ら梻鍌氬€搁崐鎼佲€﹂鍕;闁告洦鍊嬭ぐ鎺戠妞ゆ挾鍋熺粵蹇涙⒑閸忛棿鑸柛搴㈠▕閵嗗懘寮婚妷锔惧幈闂佸湱鍋撻〃鍛村箠閹扮増鏅繝濠傜墛閻撴稑顭跨捄鐚村姛濠⒀勫灴閺屾盯寮捄銊愌囨寠閻斿吋鐓曟い鎰Т閸旀粓鏌i幘瀵告创闁诡喗锕㈤幃娆撳箵閹哄棙瀵栨繝鐢靛仦瑜板啴鎮洪妸鈹库偓鍐Ψ閳哄倸鈧兘鏌涘▎蹇fЦ闁哄濞€濮婅櫣鍖栭弴鐔告緬闂佸憡鎸荤换鍫ョ嵁韫囨稑宸濋柡澶嬪灩椤︻參姊洪懖鈹炬嫛闁稿繑锕㈠畷鎴﹀箻缂佹ê鈧鏌ら幁鎺戝姉闁归绮换娑欐綇閸撗勫仹闂佺娅曢幑鍥€佸顒夌叆闁告侗鍨抽敍婊堟煟鎼搭垳绉甸柛瀣闇夋い鏃傜摂濞堜粙鏌i幇顓熺稇濠殿喖娲﹂妵鍕敃閻樿尙浠奸梺浼欑稻缁诲牓宕洪埀顒併亜閹哄秷鍏屾い鈺傜叀濮婃椽顢楅埀顒傜矓閻㈢鐓曢柟鐑樺殮瑜版帗鏅查柛銉e妼濞堝苯顪冮妶鍡樼缂侇喖娴峰Σ鎰板箳閺冣偓鐎氭岸鏌熺紒妯哄潑闁稿鎹囧畷绋课旈崘銊с偊濠电姷鏁告慨鎾疮椤栫偛纾块柣鏂垮悑閻撳繐鈹戦悙鑼虎闁告梹绮撳鍫曞醇濠靛牆顣洪梺瀹狀潐閸ㄥ潡骞冨▎鎾崇煑濠㈣埖蓱閿涗線姊绘担瑙勫仩闁告柨閰i獮濠囧箻閸︻厺缃曞┑锛勫亼閸婃牠鎮у鍫濈;闁绘劗鍎ら崑鍌涚箾閸℃ɑ灏伴柛瀣у墲缁绘盯宕卞Δ鍐唶濡炪倕绻嗛弲娑㈠煘閹达富鏁婇柤娴嬫櫅閳敻姊洪崫鍕効缂佽弓绮欓崺鐐哄箣閿曗偓缁犳稒銇勮箛鎾跺濞寸姵鍔欏缁樻媴閸涘﹥鍎撻柣鐐村嚬閸嬪﹤鐣峰┑鍡欐殕闁告洦鍋嗛崣鈧┑鐘灱濞夋稖鐧岄梺缁樻煥閸氬宕愮紒妯圭箚妞ゆ牗绋掗妵鐔兼煕閻斿鍎旀慨濠呮閹风娀宕f径濠冩暘婵$偑鍊ら崑鍕囬婊冨疾婵犳鍠楅妵娑㈠磻閹剧粯鐓涘ù锝囶焾閺嗭絽鈹戦鐟颁壕闂備胶鍋ㄩ崕瀵镐焊濞嗘垹涓嶆慨姗嗗厴閺€鑺ャ亜閺冨倹娅曠紒鐘虫崌閺岋綁顢橀悙闈涱暫濡炪値鍓欓敃顏堛€侀弮鍫濆耿婵炲棙鍩婄槐鍐测攽閻愯埖褰х紒鎻掓健楠炲﹪骞樼拠鍙夌€俊銈忕到閸燁垶鍩涢幒妤佺厱闁哄洢鍔屾禍婊勩亜韫囷絼绨界紒杈ㄥ笒閻f繈宕橀鍏兼嚈缂傚倷鑳剁划顖滄崲閸繄鏆﹂柛顐f礃閸ゅ鏌涢…鎴濅簼闁绘繃鐗曢埞鎴︽晬閸曨偂鏉梺绋匡攻閻楁粓寮鈧獮鎺懳旈埀顒傚瑜版帗鐓欓梻鍌氼嚟椤︼箓鏌¢崟鈺佸姢闁逞屽墮閸樻粓宕戦幘缁樼厱闁哄洢鍔岄崢鎾煙闁垮銇濇慨濠冩そ瀹曘劍绻濋崟顓犵獥闂備胶顭堟绋跨暦椤掑嫬鐓濈€广儱鐗忛悿鈧┑鐐村灦閻熝囧储闁秵鐓熼幖鎼灣缁夐潧霉濠婂嫮绠為挊鐔兼煟閹邦喗鏆╃痪鎯с偢閺岋繝宕橀妸銉㈠亾閹间礁鍑犳繛鎴炲焹閸嬫挸鈻撻崹顔界亶闂佽鐡曞▍鏇㈠箞閵娾晛鐒垫い鎺戝閻撳啴鏌嶆潪鎵槮闁哄棙鐟╅弻娑㈠籍閳ь剛鏁Δ浣衡攳濠电姴娲﹂崐閿嬨亜韫囨挸顏ら柛瀣崌瀵粙顢橀悙娈挎Х闂備焦瀵уú鏍磹閸濄儳鐭嗛柛顐ゅ枔缁犻箖鏌熺€电浠╁瑙勆戦妵鍕Ψ閿曚礁顥濋柧缁樼墵閺屻劌鈹戦崱妯烘闂佸搫妫涢崑銈夊蓟瀹ュ鐓ラ悗锝庝簽娴煎矂姊洪崫鍕拱缂佸鍨块崺銉﹀緞婵犲孩寤洪梺鍓插亝缁烩偓缂佹唻绲介埞鎴︽偐閹颁礁鏅遍梺鍝ュУ閻楃姴鐣烽幇鏉块敜婵°倐鍋撻柦鍐枑缁绘盯骞嬪▎蹇曚患濠碘槅鍋呴敃銏ゅ蓟濞戞粠妲煎銈冨妼閹冲酣顢氶敐鍡楊嚤閻庢稒菤閹锋椽鏌℃径灞戒沪濠㈢懓妫濊棟闁挎柨澧界壕鐓庮熆鐠虹尨鍔熺紒澶嬫そ閺岋絽鈽夐崡鐐寸亪闁句紮绲介妴鎺戭潩閻撳海浠梺鍝ュ仧閺佽顫忓ú顏勫窛濠电姴鍟ˇ鈺呮⒑閸涘﹥灏扮紒瀣灩閸欏懘姊洪崷顓℃闁哥姵顨婇幃鈥斥槈濡繐缍婇弫鎰板炊閵娿儲鐣┑鐘愁問閸犳牜绮旈崼鏇炵劦妞ゆ帒鍠氬鎰箾閹绘帞绠荤€规洘绻堥獮瀣晜鐞涒€充壕濞达絽澹婂銊╂煃瑜滈崜鐔肩嵁閸愵喖顫呴柕鍫濇噽椤︻參姊洪崷顓犲笡閻㈩垱顨婂鎶藉閵忋垻锛濋梺绋挎湰閼归箖鍩€椤掍焦鍊愮€规洘鍔欓幃婊堟嚍閵夈儲鐣遍梻浣稿閸嬪懎煤閺嶎偄顥氬┑鐘崇閻撴瑩鏌熼鍡楁嫅缁辩偤姊洪崫鍕紨闂傚嫬瀚粚杈ㄧ節閸ヨ埖鏅┑鐘绘涧鐎氀囧磻閹捐鐒垫い鎺戝閻撴盯鎮楅敐搴濈敖閺佸牓姊洪崫鍕効缂佺粯绻傞悾鐑藉醇閺囩倣銊╂煏婢诡垰鍊诲Λ顖炴⒒閸屾瑧顦﹂柟纰卞亰楠炲繒鈧綆鍠栫粈鍫ユ煟閺冨倸甯堕柦鍐枑缁绘盯骞嬪▎蹇曚患缂備胶濮甸惄顖氼潖婵犳艾閱囬柣鏃囥€€婵洭姊虹拠鑼闁绘绻掑Σ鎰板箻鐎涙ê顎撻梺鍦帛鐢﹥绔熼弴銏♀拻濞达絽鎲¢崯鐐烘煕閺冩挾鐣电€规洘婢樿灃闁告侗鍠栨禍妤呮椤愩垺澶勯柟鍛婃尦瀵劍绂掔€n偆鍘介梺褰掑亰閸樺ジ鎮橀妷鈺傜厱闁绘梻顭堥婊堟煕婵犲啯缍戦柍瑙勫灴閹晠顢欓懖鈺€绱樻繝鐢靛仜椤︽壆绮欓幘璇茬劦妞ゆ帊绀侀崵顒勬煕閹捐泛鏋涚€规洘妞介幃娆撳传閸曨収鍚呴梻浣瑰濞插秹宕戦幘缁樼厽闁瑰灝瀚弧鈧梺鍝勬湰閻╊垶宕洪崟顖氱闁挎梹瀵ч崟鍐ㄢ攽閻橆喖鐏辨い顐㈩槸鐓ゆ繝濠傛噺椤洟鏌熼幆褏鎽犲┑顖涙尦閺岋箑螣娓氼垱楔婵犮垼娉涚€氼喚妲愰幘瀵哥懝闁搞儜鍕憾闂備浇宕甸崰鍡涘磿閻㈢绠栧Δ锝呭暞閸婅崵绱掑☉姗嗗剱闁哄拋鍓熷铏圭磼濡櫣浠村┑鈽嗗亝閻熲晛顕i幓鎺嗘斀閻庯綆鍋€閹锋椽姊婚崒姘卞缂佸鎸婚弲鍫曞即閵忥紕鍘甸悗鐟板閸嬪﹪宕曡箛娑欐嚉闁绘劕顕弧鈧繝鐢靛Т閸婄粯鏅跺☉銏$厓闂佸灝顑呴悘鎾煙椤旇偐绉烘鐐扮窔楠炴帡骞嬪┑鎰偓铏節閻㈤潧浠滈柟鍐茬箻瀹曟繂鈻庨幘瀹犳憰闂佺粯姊婚崢褏绮堥崟顖涚厪闁割偅绻冮ˉ婊勩亜韫囥儲瀚� *I*do ya tsura mata yana k'ok'arin k'ara jawo hannun nata, ita kuwa da sauri ta janye hannun gaba d'aya har jikin ta na rawa sai ta konta a kife ta cusa hannayen nata k'asan k'irjinta ta konta kan hannayen tayi luf tana d'an mai da numfashi, shi kuwa k'ara matsota yayi cikin yanayin tabbaya yace, "Khairi me a hannun ki?" bata kula shiba sai d'an mirgino wa tayi jikin shi cikin yanayin yaudara ta d'an konta kan k'irjin shi hannun tasa ta cusa a bayan shi, Ido ta lumshe tare dasa hannun tana shafa sajen shi har zuwa kan k'irjin shi tanayi tana lumshe ido, shi kuwa gaba d'aya ta zuba mishi kasala duk jijiyoyin jikin shi sun mace, ganin haka sai ta sake konta wa ta juya mishi baya ta kifu, shi kuwa sunkuyowa yayi ya rink'a kissing na tsakiyar bayan ta yanayi yana murzata gaba d'aya ya gigice ya gigitata a haka ya samu abinda yafi kwana 12 bai samuba, ita kuwa abinda ta saba fad'a mai shi take furta mai, "Bana sonka ni na tsaneka". hakan ya tunzura shi ya murzata har saida yaji ya huce ya kuma gamsu, sannan ya juya mata baya cikin maida numfashi yace, " Sai ki nemo wanda kike son yazo ya kaiki gidan ko". rai a b'ace ta jawo blanket d'in ta hard'eshi a jikin ta ta mik'e tana jan shi tana, "Sai Allah ya saka min tunda saida kayi tayin pakala iya son ranka sannan yanzu kace bazaka kaini ba". tana fad'in haka tana k'ok'arin fita d'akin, shi kuwa har cikin ranshi yake jin dad'i dan ya samu gamsuwa da ita kuma ta d'an sake mishi, abinda bai saniba boye laifinta take sonyi, itako har taje bakin k'ofar fita tace, " Ni kuwa bazan sake zuwa d'akin nan ba kuma mutun ko yazo min d'aki rufewa zanyi". Murmushi kawai yayi ya bita da ido, dan sakarcin Ummul yarin tane a ciki, ba gashi yanzu buk'atar tace ta kawota ba har ya samu shima tasa buk'atar ta biya so yasan gaban ma hakane. Haka rayuwa tayi ta tafiya, Usman kuwa a gefen shi ciwo ba sauk'i kullum sai gaba gaba yakeyi. Yau Saturday tun safe Usman bai lek'a ko k'ofar parlour suba, Nenne kuwa gaba d'aya hankalin ta na kanshi ganin har bayan la'asar bai shigo ba yasa ta mik'e ta nufi part d'in nasu, a hankali tayi sallama, shiru bai amsa ba dan yana zaune a k'asa a bak'in gado ya kifa kanshi a jikin gadon yana kuka mai cushe numfashi, a hankali Nenne ta rink'a jin sautin kukan nashi, tare da tari mai yanayin ciwon zuciya, a hankali ta shiga cikin d'akin kai tsaye bakin gadon taje ta zauna cikin sanyi tasa hannun ta tadafa kanshi, da sauri ya d'ago kanshi yana goge k'ollah dake bin fuskar shi, cikin k'arfin hali yayi murmushi , ido ta zuba mai cikin tuhuma tace, "Usman a zaton ka bansan meke damun ka bako?" kai ya jinjina tare da yin murmushi yace, "Nenne bani da matsalar komai". ido ta sake tsura mishi sannan tace, " Ummul ce matsalar ai". cikin sauri ya rink'a juya kai yana jin kunya na ratsashi ya za'ayi ya k'asa control d'in k'aunar Ummul a ranshi har mutane su gane yana son matar d'an uwanshi, ita kuwa Nenne kafad'an shi ta dafa a hankali tace, "Ban tab'a zaton shak'uwar ka da Ummul ya zama so a tsaka nin kuba har aka d'aura auren Ummul da Farouq duk a zaton shak'uwace kawai a tsaka ninku, Usman na fara Azargin kana son Ummul ne bayan Umar ya tafi da ita gidan shi, tun lokacin da ka fad'i ka suma na gane akwai abinda kake b'oyewa a ranka, ban gaskanta hakan ba sai randa kukaje gidan Ummul kuka dawo nanma kai ta aman jini sai kuma randa su Umar d'in suka zo manna ka birkice, sannan tunda suka tafi baka samu sukuni da kowa ba kuma doctor ya shaida mana akwai abin da kakeso kuma kana b'oyewa, Usman ni yanzu nasan Ummul kake so". tunda Nenne ta fara magana yayi shiru yana kallon ta, saida ta furta "Ummul kake so". sai ya kife kanshi kan cinyarta ya saki wani irin kuka murya a hargitse ya rik'o hannun ta ya rink'a juya mata kai a birkice yace, " Asiri na ya tonu naji kunya har gaban Ubangiji na tunda matar aure zuciya ta ke so ina zankai wannan zunubin? naji kunya a idanun duniya na rasa wacce zanso sai matar d'an uwana shak'ik'ina wanda bayi da b'uri a duniya daya wuce farin ciki na". sai kuma ya kuma kife kai yayi ta kuka mai tarin firgici cikin rawan murya ya durk'usa gaban Nenne a hankali yace, "Nenne ki rufa min asiri ki tayani b'oye wannan sirrin nawa kodako zai zama ajalina dan Allah karki gayawa ko daga ni sai ke ". itama Nenne kuka takeyi sosai dan Usman ya zama abin tausayi, a hankali tace, " kana ganin a haka zakaci gaba da boye abin a ranka ne?" Kai ya jinjina a hankali yace, "Nenne taima kona zakiyi kisa baki Abba da Hamma Umar su barni intafi India inbar k'asar gaba d'aya na tabbatar zan samu sauk'in abin a raina in nayi nesa da Ummul". kallon shi tayi a hankali tace, in dai haka zai sama maka sauk'i toh ba matsala". Haka kuwa akayi Nenne ta ajiye Hamma Umar da Abba tayi ta rokawa Usman d'in a barshi ya tafi ai yace ya samu lafiya kuma daga can zai k'ara ganin doctor, shi kam Hamma Umar har cikin ransa baya son tafiyar da d'an uwanshi zaiyi amman Abba da Daddy sun yarda dole shima ya yarda, shi kuwa Usman ya fara shirin tafiya cikin happy da kewar d'an uwanshi da Ammin su abar k'aunar su ji yake kamar ya fasa tafiyar dan gani yake kamar shike nan ya rabu dasu kenan har abadan, haka dai ya d'aure ya tafi. Gidan Alhaji Bello kuwa mahaifin Mustapha gaba d'aya rayuwar Mustapha ta juya ta canza Mustapha ya zama abin tausayi dan tabbas har cikin ransa yake son Ummul mahaifin shi kuwa ganin ya rasa Ummul d'in ne yasa yace zai had'a shi da y'ar k'anwar shi, yau tun safe aketa fama da Mustapha iyayen shi sun sashi a gaba kan batun auren amman sai ya d'ago ya kallesu fuska cike da k'ollah yace, " Daddy ni ba zanyi aure ba Daddy dan Allah kuyi hak'uri ni bana son auren ,bazan iya auren bafa". Ido Daddyn ya zuba mishi cikin sanyi yace, "Mustapha shin kana fushi da hukuncin Ubangiji ne? ya za'ayi kace bazaki yi aure ba bayan kuma kana da damar yin auren ashe dan ka rasa Ummul bazaka so y'ar uwarka Amina ba shin ko zakaci gaba da son matar aure?" kai ya rink'a juyawa yana zubda k'ollah yace, "Daddy bana son Amina kona aureta bazata ji dad'in zama da niba Daddy bana son cutar da ita". Mahaifiyar shi ce ta kalleshi cikin tausayawa tace, " Mustapha wata rana zaka so Amina na kuma tabbata zatayi ma biyayya tunda dama ita tana sonka kuma indai mun isa da kai toh ka aminci da auren nan". a hankali ya mik'e cikin rawan murya yace, "Shike nan Daddy na aminci indai hakan zai saku farin ciki". murmushi Daddy yayi cikin jin dad'i sannan suka bishi da Addu'a, shi kuwa yana fita d'akin shi ya nufa a parlour ya konta a k'asa yayi shiru yana tuno irin shirin da yakeyi na auren Ummul kawai sai ya rink'a kuka yana istgifari dan tuno cewa Ummul fa yanzu matar aure ce, haka akayi ta shirin auren Mustapha da Amina.. Gidan Hamma Umar kuwa tun randa Ummul taje d'akin Hamma Umar d'in ya kusance ta daga Wannan ranan , rayuwar Ummul ta fara canzawa wani irin abin al'ajabi da tsoro ya rink'a bibiyar Ummul, tun daga yamma cin wannan ranar Ummul ta farajin hannun ta da akasawa robar family planning d'in yana mata wani irin nauyi sannan sai taji hannun kamar ba a jikinta yaje ba gaba d'aya sai zuciyar ta ta rink'a tsinke wa wata iriyar kasala ta rink'a rufeta, a haka a daddafe tayi sallan maggariba da isha, cikin kasala ta zame ta konta kan sallayar da nufin zatayi bacci , Amman sai ga wani sabon al'amari mai ban tsoro kuma, bayan ta konta tayi Addu'a sannan ta lumshe ido a hankali bacci ya fara fizgarta, lokaci d'aya bacci mai dad'i ya d'ebeta, Amman cikin baccin sai taga Hamma Umar yana rik'e da jariri fari tas mai kyau yaron sai kuka yakeyi shi kuwa Hamma Umar sai ya mik'e mata jaririn ita kuwa sai ta ture ta juya ta gudu can gefen su, shiko Hamma Umar d'in sai yasa yaron a kafad'an shi yana lallashin jaririn yana ta zirga-zirga shiko jaririn sai kuka yakeyi da k'arfi, ganin haka ta tashi a firgice al'wala taje ta kumayi sannan tazo ta kumayi Addu'a sannan ta sake kwanciyar bayan kamar minti 30 bacci ya sake d'auke ta, still cikin baccin ta sake ganin Hamma Umar zaune cikin jarirai sai kuka sukayi da k'arfi duk sun cika gidan da kuka, a hankali ta rink'a ganin jariran sun dawo gareta sunata kuka shima Hamma Umar ya koma gefen su yana kallon jariran yana zubda k'ollah, haka ta sake farkawa a firgice, Toh fa haka Ummul take rayuwa ba bacci data rumtse idanun ta sai taga ana binta da jarirai suna kuka har abin ya fara zame mata ko a gyegyed'i takeyi sai tayi tajin kukan jarirai ga hannun ta kuma yamma nayi yake fara ciwo ta kuma k'i ta gayawa kowa Hamma Umar kuwa ko sabgarta ya dena shiga , sai ya kwana nafilfilin shi yana mai rok'on Allah ya azurtashi da haihuwa kullum Addu'ar sa Allah yasa Ummul ta samu ciki dan yana son haihuwa tare da ita sai azumi da yake yawan yi dan ya rege k'arfin sha'awarsa tunda yasan ba kulawar Ummul zai samuba, itako Ummul zuwa yanzu har tsoro take dere yayi da zaran yamma tayi bata da sauran kwanciyar hankali. Yau juma'a tun safe Hamma Umar yake d'akin shi yana ta karatun qura'an har zuwa 12 sannan yayi wonka ya shirya sab cikin fararen tufafi sai k'amshin turaren shi na du'a'ul jannah yake yi sannan ya fito hannun shi rik'e da sallaya a parlour ya samu Ummul zaune cikin yanayin bacci dan yau koda safen da zaran ta rufe ido sai taga ana mik'o mata jarirai gaba d'aya baccin sai yasa mata ciwon kai ga hannun ta da takeji kamar ba nataba gashi dai ba kumbura yayi ba amman jin hannun take kamar dutsi, tana ganin shi ta matso gaban shi cikin yin mik'a ido a lumshe tace, "Hamma Umar a bani maganin bacci mana". bai kalleta ba bai kuma yi magana ba har yaje bakin k'afa sannan yace, " sabida me? zan baki maganin bacci?" "Bana samun bacci ne shiyasa". " baki da lafiya ne?" "A a ni lafiya ta lau". Juyawa yayi ya d'an kalleta sannan ya girgiza kai ya fice, koda akayi sallan juma'a potaskum ya nufa kai tsaye gidan Inna ya nufa ranar ko lek'a gidan Abba baiyi ba dan tunda Usman ya tafi baya son zuwa gidan sosai, yana zuwa ya wuni da Ammin su sunata hira ya kira Usman d'in ma a woya sun dad'e suna hira, shine bai nufi hanyar damaturu ba sai bayan sallan ishah sannan ya kama hanyar, ita kuwa Ummul gaba d'aya ta birkice bacci na shirin zautar da ita sai zirga-zirga takeyi da zaran ta konta in tayi baccin minti 30 dai toh sai mafarkin jarirai, shi kuwa Hamma Umar yana isowa kai tsaye bedroom d'in shi kawai ya nufa, wonka yayi sannan ya konta rik'e da woyar shi yana magana da Ammin shi yana shaida mata ya isa lafiya, ita kuwa Ummul a hankali ta samu baccin ya saceta, bacci mai nauyi cikin nisan baccin ta fara juyo kukan jarirai ba adadi kukan sai k'ara matsota yake har taga jariran sun cika kan gadon nata sai kuma taga hannu wani mutun ya yarfa mata mari sannan ya nuna mata wani fili mai kyau inda ta haggo Hamma Umar yana zaune rik'e da jariri yana ta kallon ta yana murmushi tana cikin mamaki ina Hamma Umar a samo yaron nan sai taji an kuma yarfa mata marin tare da buga mata tsawa, " tashi kije ki karb'i d'an ki". A firgice ta farka da jin marin tayi kamar a zahiri, lokaci d'aya wani irin tsoro ya rufeta gaba d'aya jikinta sai zufa ke tsatstsafo mata hannun ta kuwa sai rawa yake kar-kar, sai kuma taji kukan kululluka a saman d'akin ta, haka yasa ta mik'e cikin tsananin tsoro da gudu ta fito parlour sai kuma ta nufi bedroom d'in Hamma Umar d'in tana shiga ta ganshi zaune kan sallaya hannun shi rik'e da qura'an da gudu taje ta fad'a jikin shi gaba d'aya jikin ta sai tsuma yakeyi hannun tasa ta ruggume shi da k'arfi kanta take ta cusawa cikin k'irjin shi tana to she kunnen ta, da sauri ya kalleta cikin mamaki ganin yadda take boye kanta a jikin shi yasa shima ya k'ara ruggume ta sannan ya rufe qura'an d'in ya ajiye kan mirror , ita kuwa Ummul sai kuka takeyi cikin tsananin jin tsoro, kanta ya d'ago a hankali yace, "Ummul meke faruwa ne?" baki na rawa tace, "Hamma tsoro nake ji Hamma kullum bana bacci mafarkin jarirai nakeyi suna kuka suna hanani bacci". Jawota jikin shi yayi ya kara ruggume ta cikin mamaki yace, " jarirai kuma? toh banda abin ki Khairi kukan jarirai kuma me abin tsoro a ciki?". K'ara mak'aleshi tayi tana, kuka tace, "Suna da yawafa kuma yau har dukana akeyi". ruggume ta yayi ya mik'e da ita kan gado ya kontar da ita sannan ya konta gefen ta ya ruggume ta yana shafa kanta cikin sanyi yace, " kiyi shiru kibar kukan ba komai kinji ko". Ido ta rumtse sai kuma ta mik'e da sauri ganin wani hannun yana sa wuk'a kan damtsen hanunta dai-dai inda akasa mata robar , hannun ta rink'a turawa Hamman tana kuka tana, "Hamma ka cire min Hamma zasu yanke min hannun Hamma ka cire min". Cikin mamaki ya kamo hannun yana duddubawa tare da cewa, " Zasu yanke miki hannun kuma? me a hannun naki?" shiru yayi dai-dai lokacin da yatsun shi suka sauk'a kan inda akasa mata robar, d'ago hannun nata yayi da kyau ya duba wurin cikin rawan baki yace, "Family planning kikayi ne?" kai ta gyada mai cikin zafin da taji hannun yana mata, tureta yayi da karfi lokaci d'aya idanu shi sukayi jazir gaba d'aya jikin shi sai rawa yakeyi murya a hargitse yace, " fita min a d'aki ki koma can d'akin ki kisan hujjar da zaki gayawa ubangijinmu kisan yadda zakiyi da jariran dake binki suna kuka ki gaya musu dalilinki na hanasu zuwa duniya Ummul kiji tsoron Allah ki tuba ki koma gareshi tun lokaci bai k'ure mini ba". sai kuma ya kamo hannun ya matse da k'arfi har saida tayi k'ara mai cike da gigita, tureta ya kumayi sannan yace, "Idan Allah yace ehh toh fa ke Ummul baki isa ki ce a,a ba ki sani idan Allah ya k'addara sai kin haihu dani wallahi wannan robar bata isa ta hana cikina shiga jikin kiba". ita kam Umml sai zare ido take tana kuka, gaba d'aya tsoron shi ya rufeta, shi kuma murmurshin takaici yati wanda yafi kuka ciwo sannan ya nunata da yatsa yace, " kina so kija da yin rabbi toh gashi kinga ishara tun ba'aje ko inaba kinga duk abunda kikeyi koni ban saniba Allah ya sani, wallahi ki shirya me zaki cewa Abba da Adam da Sadik kome zasuyi miki bazan hanaba kuma zan gaya musu abinda kikayi zan kuma kaiki gabansu in sunga damage su tsireki ki kuma je ki samu mahaliccin mu tunda bakya tsoron Allah". kuka ta kamayi sosai tana, "Wayyo Allah na dan Allah Hamma ka rufa min asiri wallahi ya Adam zai kusan kasheni gashi ya Usman baya nan ba wanda zai ceceni kayi hak'uri wallahi bazan sake ba ya Sadik zai karyani Abbana zaiyi fushi dani Hamma wallahi bazan sake ba". Cikin tsawa yace, " ki dai ji tsoron Allah, kuma ki shirya da sassafe zamu tafi abunki ya fara bani tsoro na lura baki da tausayi". yana kaiwa nan ya fita ya bar mata d'akin, binshi tayi a baya tana ta magiya da tuba, bai kulataba ya wuce d'aya d'akin ita kuwa a parlour ta kwana tana magiya bata kuma samu ta rumtsa ba. Washe gari bayan ya dawo masallaci yana shiga parlour tabi bayan shi murya a disashe tace, "Ayyah Hamma na dan Allah kayi hak'uri wallahi bazan sakeba kaji na rantse dan Allah karka gayawa ya Adam". bai kulata ba ya fara shiri , ganin haka ta lallab'a ta d'auki woyarshi ya Usman ta kira, yana d'agawa cikin sanyin murya yace, " Hamma na ina sonka yauma nayi mafarkin ka nayi kewarku zan dawo". Cikin sanyi tace, "Ya Usman dan Allah ka bawa Hamma Umar hak'uri karya kaini gida kasan ya Adam mugune zai karyani". Hannun shi yasa ya dafe k'ahon zuciyar shi dake harbawa cikin sanyi yace, " Allah ya d'aiyiba min k'anwata, me kikayi wa Hamma na har yasashi fushi yace zai hadaki da Adam Boss?" Cikin sakarcin ta gayawa Usman abin da tayin, tanayi tana kuka, shi kuwa Hamma Umar ido ya zuba mata cikin tsananin bak'in ciki, shi kuwa Usman gaba d'aya ranshi ya baci bai tab'a jin haushin Ummul ba akan batun auren su irin na yau rai a b'ace yaja dogon tsaki cikin fad'a yace, "Ummul ki sani in kin cutar da Hamma Umar toh kin cutar da zuciyata duk duniya bani da kamarshi amman kike gaya min bakya sonshi bazaki haihu da shiba Ummul d'an uwana kikeyi wa haka, bazan hanashi ba bazan bashi hak'uri ba ya kaiki duk inda zai kaiki kuma kiji a bakina, nida kaina zan gayawa Adam da Abba". jin haka saita kuma fashewa da kuka ta mik'awa Hamma Umar d'in woyar baki na rawa tace, " Dan Allah Hamma Umar ka bawa ya Usman hak'uri dan Allah karku gayawa ya Adam". Woyar ya karb'a cikin k'aunar juna suka fara magana, Usman ne ya d'an yi shiru sana yace, "Hamma yanzu forko dai ka cire mata robar daga nan kuma kayi abinda ya dace da ita". A hakali yace, " Me zan iya yiwa Ummul, Usman duk hukunci da zanyi yunk'urin d'auka a kanta zai kasance na gaza rik'e al'k'awari da amanar dana d'auka". shiru Usman yayi sannan yace, "Toh ni zan gayawa Adam dan ajamata kunne". yana kaiwa nan ya katse kiran, shi kuwa Hamma Umar mik'ewa yayi ya yawo hannun Ummul d'in kai tsaye harabar gidan ya fita da ita, cikin mota ya sata, sannan shima ya shiga yana shiga ya figi mortar kai tsaye ya kama hanyar potaskum, tana ganin haka cikin tsoro ta kwanta kan....... By *GARKUWAR FULANI*