*🌈TSINTACCIYA🌈* NIMCYLUV _FITATTU HUƊU 🔥_ _1.Meke Coursing Masturbation??_ _2.illar Masturbation??_ _3.Let's talk about NOMA, Amfaninta ga matasa!!!!!_ _4.Sharrin Aljanu, da hanyar da suke shiga jikin mutum_ _A kakkaɓe zani jama'a💃🏽 ki tabbatar kin kammala girki before you start reading my book....... Ready goooo!!!_ EPISODE1️⃣ http://wa.me/+2348119237616 Safiyar garin Lahadin yau ta kasance safiya mai ɗumbin tarihi ga dukkan jama'ar da suke yankin Kano kuma a sassa daban daban, Dalilin Kwantaccen baƙin hadarin dake garin, kasantuwar yanayin damu na da muke ciki, kuma farkon watan Agusta. A hankali sassanyar iskar hadarin take Kaɗawa yayinda kuma dukkan baƙin hadarin yaywa samaniya tsinke, cikin nutsuwa baƙin hadarin ke joyewa zuwa jaa, alamar ko wanne lokaci ruwa na iya sauka. Wata ƙaƙƙarfar iska ce mai tafiya da rufin gidaje ta fara fatali da dukkan wasu abubuwa marasa nauyi, ƙarfin isakar da rugugin hadarin ya wuce tunanin dukkan mai tunani da dukkan alama yau ruwan na musamman ne. A hankali kuma gajimaren ke gudu yana haɗa jikinsa waje guda, cikin lokaci kaɗan samaniya tai wani irin jaa wanda ya wuce tunani mutane, ga wata ƙara da rugugi da hadarin yake, wanda ya haddasa tashin tsuntsayen daga saman bishiyoyi zuwa ma ɓoya. Ƙarfin gudun isakar da kuma yadda take fatali da dukkan wani abu dake kan hanya, ya sanya dabbobi fara gudu suna kuka, yayinda abeben hawa suka shiga tsayawa a saman shimfiɗaɗɗan titin Sabon Garin! "Shuuuu" haka sautin saukar ruwan saman ya bada Amo! Amon daya tsorata dukkan mutanan da suke waje, domin tunda aka fara damuna today is the first day! Da akai ruwa mai tsananin yawa wanda yake sauka da wata iska mai yaye dukkan rufin gidajen da basu da Kwari, saukar ruwan saman yay worse da yaywa al'amarin da yay Coursing wani irin hatsari mai munin gaske. Saukar ruwan saman bai hanata ko da motsi ba, bare tayi Attempting na gudu zuwa wani wajan domin tsira da lafiyarta. Tana zaune a saman wata kan bolar kasuwar Sabon gari, the way she's acting zaka san cewa akwai wani abu da yake tattare da ita. Farar macace mai matsakaicin jiki, ƙyakƙyawa ce sosai saukar long dark hair ɗinta zuwa gadon bayanta zai tabbatar maka cewa ita ɗin ruwa biyu ce wato _(Half-caste)_. Dukkan sassan jikinta rawa yake yana wani irin ɓari, na tsananin dukan ruwan saman, a dai-dai lokacin da kuma saukar ruwan saman ya juye zuwa saukar ƙanƙara yasa tai wani irin firgita tare da ɗago kanta sama. ”Yasubuhanallah!” hasken fuskarta shi kaɗai zai tabbatar maka cewa wannan ko a mahaukatan ita sabon kamo ce, idanunta sunyi jajirrr Jikinta na wani irin ɓari ta tashi tsaye _”Ya hayyu ya ƙayyum”_ ashe tsirara take babu komai jikinta sai dugun gashin daya rufe asalin kayan fuskarta. Idanunta ta ɗaga sama kamar mai tunani a hankali kuma bakinta ke motsawa yadda babu mai iya jin abinda take faɗa. Cikin nutsuwa kuma sautin maganar ke fitowa fili tana faɗin. _“Allahumma Innakaa, Afuuwun! Tuhibbun Afu-afuu Anniii”_ Sune kaɗai kalaman dake fita a bakinta, wanda Ubangiji ne kaɗai ya sahale mata faɗar su, da kuma ƙarfin Imanin da Zuciyarta ke dashi, amma banda haka yaya cikakkiyar Mahaukaciya mai yawo tsirara wacce ta maida kan Bola wajan kwananta, ruwan kwanta ya zama abin kashe ƙishinta, yayinda abubuwan kan Bolan suka zama abincin sawa a cikinta zata iya wannan salati¿ _ONLY GOD KNOWS_. A dai-dai lokacin ne kuma wata haɗaɗɗiyar mota Rolls-Royce Phantom mai tintak tai parking a wajan, cikin nutsuwa kuma aka buɗe Murfin motar aka fita, wani Babban mutum kuma attajiri ne ya fito yana gyara zaman laimar dake hannunsa. Idanunsa ya juya tare da sauke ganinsa akanta, wani irin lumshe idanunsa yay yana siɗe laɓɓansa da harshe kamar tsuhun maye. Cikin wata fitinannan Murya wacce buƙatar kasancewa da mahaukaciyar ya gama narkar da ita, ji yake J ɗinsa na wani irin fisga saboda ganinta da yay naked a gabansa. Frm head to toe yake binta da kallo! Cikin zaucewa ya ƙara ji J ɗinsa ta fara fisga to Yarinyar tai bala'in haɗuwa. A zuciyarsa yake faɗin. "Young innocent pretty gril aka haukata haka? She's different kyanta daban, komanta daban, that's illiteracy ji ɓeta kamar ƴar sarauta, so pretty my Lord! Yasubuhanallah, masu haukata Yarinyar nan sumbin gata, na samu full chances zaɓe zai zo min a dai-dai, kalleta her body is so soft ga idanu ka manyan kaya, look at her. Snatch waist wallahi zama ƊAN MAJALISA _(Members federal house of Representatives)_ Dole!” Ya ƙare zan can zucin yana wani sauke ajjiyar zuciya da shafa ƙirji. Motsin da taji a bayanta ya sanya ta juya da sauri ganin mutum dake can nesa da ita yasa ta razana sosai. Tsoro, firgici ya haɗe mata waje guda, Ada kafin shigowar sa cikin rayuwarta _DAMUWA_ ce, amma shigowar sa cikin rayuwarta a yanzu ya zama _ƘALUBALE!_ Kai ta shiga girgiza masa ta nayi baya, jikinta na kyarma da ɓari amma hakan bai hana shi ƙara kusantu ta ba, yana zuwa yasa hannu ya fisgota zuwa wajan motar, yayinda shima jikin nasa ya ɗauki rawa saboda wata kalar tsawa da akai. Kokawar kwace kanta ta shigayi, hakan yasa shima ya fara tayata kokawar it was like he is enjoying. Tana gab da ƙwace kanta ya wani dannata cikin motar tare da sanyawa motar lock yana shiga yaja motar da wani irin speed yabar kam bolar. http://wa.me /+2348119237616 *_Domin magana da marubuciyar kai tsaye danna nan_* *BAYAN SHEKARU 17* WUDIL/KANO STATE _Darki Lajawa Area_ Fitowa yay daga cikin ƙaramin ɗakin da yake ciki, hannunsu riƙe da Magirbi daya saƙala a wuyansa, Dattijo ne mai matsakaicin jiki, yana da kamala sosai. Cikin sauri ya rufe ɗakin saboda gaba ɗaya hankalinsa yay kan gonarsa. Yana ƙoƙarin fita yaji matarsa na faɗin. "Innalillahi, Malam!Malam! Malam kana ina ne" Da sauri wanda aka kira da Malam ya tsaya daga tafiyar da yake, gabansa na faɗuwa domin daga yadda ake kiransa kasan bana lafiya bane. Kallon Matar tasa yay yace "Ya..Ya Rabi wannan kiran hak ince dai komai lafiya ne?" Girgiza masa kai tayi tace "Malam inafa lafiya" gabansa ne ya sake faɗuwa kafin yace "Assha,Meke faruwa to, kinga sauri nake zani gona, kuma yau muna da baƙi a garin namu zasu taimaka mana akan Noman mu" Numfasawa tayi tace. "Malam ban ganta ba, tun dana farka ko karin kumallo banyi saboda fargaba yanzu ma gajiya nayi da zullumi nace bari na faɗa maka" Da sauri Malam yace "Kamarya? Babu yarinya kuma kikai shiru kamar baki san ciwon Yarinyar nan ba? Kamar bake kika haifa ba?" Girgiza kai tayi tace "wallahi Malam na ɗauka taje makara...." Da sauri ya tare ta hanyar faɗin "Wacce makaranta Rabi? Bayan satin daya shige ta gama zana jarabawar shiga aji huɗu na sakandare? Wallahi duk abinda ya samu Yarinyar nan ki kuka da kanki, ba zan lamunci wannan shirman a gidana ba, idan baki son riƙe ta saboda da lalurar da take da ita ina da inda zan kaita ta zauna har abada ko mai kamannin ta baki gani" Yana faɗin hakan yay cilli da Magirbin tare da yin waje. Shiru Baba Rabi tayi cike da zullumin halin da Yarinyar zata kasance. Tunda ya fita ko mai kama da ita bai gani ba, babu ma yara sam a unguwar dalilin ruwan da aka shimfiɗa a daran jiya, ko'ina na unguwar ya cika da ruwa, ko shi ya shiga wannan ruwan sai yay jinya amma ina yarinyarsa taje a wannan lokacin? Abu kamar wasa har ya fara shige tunanin Malam, al'amarin daya ƙara tayar masa da hankali kenan, yarinya ɗaya tilo da yake da ita wani ƙaramin kuskure yana neman yi masa nesa da ita. Yama manta da batun gona da kuma baƙin daza suyi a garin, tafiya yake sosai harya ƙarasa wajan wani tafkeken ruwa _(Wudil river)_ Kana kallon ruwan nan kasa duk wanda ya shiga ko kuma ya faɗa, ya faɗa kenan sai dai wani bashi ba, ruwan yay wani sama dan ma wai a hakan ya tafiya. Baka ganin komai sai haske da hayaƙin ruwan har wani ambaliya yake ya cika yay tafff. Tana tsaye a gaban ƙaton ruwan, kanta a ƙasa Idanunta a rufe, yarinya ce ko kuma nace matashiyar budurwa, ƴar kimanin shekaru 17 a duniya, baka iya tantance yanayin dirin jikinta saboda babban hijab ɗin dake jikinta. Fararan hannunta da kuma yatsun hannunta da take motsa su ne zai tabbatar maka da cewa farar macace irin farin nan mai mugun kyau, da ɗaukar hankali. Kanta yay tudu sosai kamar wacce tai acuci, fafaran ƙafafuwanta ko takalmi babu. A hankali ta ɗaga kanta tare da buɗe idanunta wanda eyes lashes suka kwanta luff a saman fatar idanun, hannunta ta sanya tare da kama gefen hijab ɗinta ta ƙanƙame Jikinta waje guda. Dadai ace ta auri wanda bata so, Tabbas gwamma kowa ya rasata, rayuwarta bata da amfani a yanzu damuwa tai mata yawa. Mene Amfaninta ne a yanzu? Ada rayuwar ta tambaya ce? Amma rayuwarta a yanzu ta zama Amsa, duk da irin wannan abun bai hana duniya tai mata wani irin kallo ba, mene yasa duniya ke son yin juyin wainar fulawa da ita ne? A hankali ta share hawayen dake silaluwa daga cikin idanunta zuwa saman fuskarta, cikin siririyar muryarta mai raunin gaske tace. "Am so sorry Baba, na kasa maka biyayya, I'm a bad girl ni ba ƴar ƙwarai bace, na ɗauka zan jure na ɗauka i can handle everything anything da zai farcing rayuwana, amma na kasa, Am sorry Ba..ba!!! Am sorry!" Ƙafa ta ɗaga zata faɗa cikin ruwan taji ana faɗin. "AKEELA! AKEELA!! AKEELA!!" da wani irin sauri ta juya ganin Babanta a bayanta can nesa yana zuwa wajan, kai ta shiga girgiza masa ta kasa cewa komai. Hijab ɗin jikinta ta tattare zuwa saman tana jan numfashi, Malam kuwa Murya ya buɗe ya shiga faɗin. "Akeela ki tsaya bazan aura maki kuwa ba, Akeela Ruwa..." Bai gama faɗin abinda yay niyya ba saboda wani irin bugawa da ƙirjinsa da yay ji kake "Tsundumm" ta faɗa cikin ƙaton kogin. Wani irin suman tsaye Malam yay, komansa ya tsaya na wani lokaci, tashin hankali da makomarsa ya cika masa zuciya. Da gudu har takalmansa na faɗuwa yay bakin Kogin duk da yadda idanunsa suke dishi dishi saboda ƙaran cin gani da yake da shi bai hana shi ganin wajan da Akeela ta faɗa ba, yana wani fidda ƙwayaye alamar numfashinta na fida saboda shigar ruwan cikin hanci da bakin ta. Da gudu Malam ya kwasa zuwa bakin hanya yana faɗin. "Jama'a ku taimakamin yarinta ta faɗa kogi, wai babu mutane a garin ne, jama'a!!!!" Hannunsa ya ɗura akai har wani jiri ke ɗiban sa, babu mutum ko ɗaya a hanyar. Sama da mintina 10 kafin Allah ya kawo wasu mutane wajan su biyar kana ganinsu kaga Manoma, da sauri Malam yasha gabansu yace. "Bayin Allah ku taimaki ran baiwar Allah, yarinya ta na cikin ruwa, ko taimaka min kada ta mutu da haƙƙi na" Kallon juna sukai kafin kuma gaba ɗaya suka bi bayansa saboda hannun wani da yaja. Suna zuwa wani mai suna Isiya yace. "Tab, ai wallahi idan kaga tayi rai sai ikon Allah" Wani mai suna Sunusi yace "Wanne batun rai? Ai Isiya wannan Yarinyar Shikenan ta riga mu gidan gaskiya" Wannan Maganar tasa Malam sakin kuka yana faɗin. "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, dan Allah ku daina faɗin haka wallahi yarinta tana raye bata mutu ba, gobe bikinta Tayaya ne za kace tamutu" Isiya ne yace "To wallahi dai ku ruwa bai kashe ta ba, kifi ya cinye ta ko kada tab wannan maliyan ruwan ko ƙarshe bai dashi" Jafar ne yace "To wama zai shiga wannan ruwan? Kasan bamu da wasu ƴan kwana kwana a wannan unguwar kafin su zoma komai ya faru" Sunusi ne ya ƙara leƙawa ruwan yace. "Allah dai ya jiƙan musulmi, amma wannan Yarinyar tayi shahada mutuwar ruwa baiwar Allah kenan" Da gudu Malam ya kwasa ya ƙara nufar kan hanya domin zuciyarsa ba zata jure jin wannan mugwayen alkaba'in akan Yarinyar kirki irin AKEELA ba. Yana zuwa kan hanyar dai-dai lokacin da wasu haɗaɗɗun motoci suka danno kai cikin garin Wudil a kuma dai-dai Wudil river. Motar farko wacce ta kasance Bugatti Veyron dark blue ce ta wuce da wani mugun sauri. Kafin ɗaya motar mai ƙirar Lamborghini Aventador blue black ta marawa motar gaban baya. Yana zaune a bayan motar idanunsa a rufe sanye yake cikin Modern fit suit nevy blue. Sai wani Monk strap na shoe daya sanya, ya ɗaura Rolex Oyster Perpetual a hannunsa, ƙyakƙyawa ne amma baƙi, his Elegant black skin sai ƙyalli yake, Babu wani abu mai haske jikinsa sai laɓɓansa da kuma idanunsa, he's dark-skinned yet handsome guy. Wasu irin idanuwa ne dashi masu sparkling cikin idanun duk mai kallonsa. A hankali ya buɗe idanunsa jin driver na faɗin "Subuhanallah" idanunsa ya gama buɗewa sosai ba tare daya kalli Driven yace. "What happened with the car?" Cikin girmamawa yace "Ƙaramin Mai gida wani bawan Allah yasha gaban mu Allah yasa ban taka shi ba" Yana latsa Wayarsa yace "Ok! Check him muga" Fita yay yana fita Malam ya miƙe yana riƙe ƙafa yace. "Yarinya ta dan Allah ka taimakamin ita kaɗai nake da ita" Da mamaki Driven yace "Bawan Allah lafiya, baka san hatsarin mota bane zaka sha gabanmu haka" Cikin kuka Malam ya bashi labari tare da faɗin "Dan Allah ka taimakamin tayi wajan mintina ashirin da faɗawa" Baya Driven yay tare da faɗin "Bari na faɗawa Karamin Mai gida" Yana faɗin ya nufi wajan motar back seat tare dayin knocking. Idanu BARR ADNAN (MD) ya ɗaga kafin ya buɗe glass ɗin motar ganin Driven sa yace. "Is everything okay?" Ajjiyar zuciya Driver yay yace "Wai Yarinyar sa ta faɗa wannan kogin na Wudil gashi babu kuwa kusa, shine yake neman taimako" Kallonsa kawai Md yay kafin yace "Is she a kid?" "Wallahi dai ban sani ba, amma hankalinsa a tashe yake" Malam dake can gefe yay saurin ƙarasu wa wajan yace. "Dan Allah ku taimaka" Da sauri Md ya ɗaga idanunsa domin idan ba gizo muryar take masa sai yaji kamar muryar Baffansa. Da mamaki Malam yace "A'a Adnanu kai ne? Maza fito maza kaji" Buɗe ƙofa Md yay ya fito fuskarsa ɗauke da Murmushi yace. "Baffa wacce ta faɗa ruwa kamar haka?" Girgiza kai kawai Baffa yay yace "a fara taimakon rai sai ai magana da baya" Gaba Baffa yay Adnan Md na biye da shi of course ya iya ruwa amma wannan ruwan ya wuce tunaninsa, gashi dai bai shirya mutuwa ba, Amma yay zai ne? da P.a yana kusa da sauƙi ma. Zare jacket ɗin sa yay tare da cire necktie ɗinsa, yana tattare hannun rigarsa yace "Baffa babu alamun mutum fa a wannan ruwan" Zuciyar Malam ya buga da ƙarfi kafin yace "Wallahi tana nan ta faɗa ka jarraba" Zare takalmin ƙafarsa yay yace "I'll try my own best, firstly clam down kaji" Gyara tsaiwa Md Adnan yay yana runtse idanunsa tsoro duk ya cikasa domin girman ruwan bana wasa bane da wani irin ƙarfi yay tsalle tare da faɗawa cikin Kogin.... *🌈TSINTACCIYA🌈* NIMCYLUV _FITATTU HUƊU🔥_ EPISODE2️⃣ http://wa.me/+2348119237616 “Tsundum” sautin Amon faɗawarsa cikin kogin ya bada, kafin kuma wasu manyan ƙwayaye su fara firfitowa alamar wanda ya shiga cikin ruwan yana fidda numfashi. Malam ne ya sauke Ajjiyar zuciya tsoro duk ya cika masa zuciya, Musamman like Md Adnan did! Yay Wani good jum before he fall in to the river. Cikin damuwa Malam ya kalli Drive yace "Yadai iya ruwan sosai ko? Nasan Adnanu gwamma shi da ɗan uwansa, bana son rasa rai biyu a lokaci guda, Akeela nada matuƙar muhimmaci a rayuwata haka Adnanu" Shiru Driver yay domin like serious bai san komai ba amma dai yasan Adnan na yawan shiga wani ruwa. Isiya ne yace "Uhm yadai iya ruwan ko?" Kallonsu driver yay kafin yace. "Not sure! Amma Ƙaramin Mai gida yana shiga swwiming pool sosai yana son wasan ruwa, ta takalmin taya, amma dai ruwa kamar wannan bana da tabbacin yana shigarsa" Malam ya kalli ruwan yace. "Allah ka taimaka ni, ka duba lamarin wannan yaran" Juyawa Driver yay yace "bari na kira taimakon kwanakwana incase" Wajan motar ya nufa ya ɗauki Wayarsa tare da fara shiga goggle yana duba yadda zai samu impormation na ma'aikatan mafi kusa da garin. Md Adnan wani numfashi yaja mai wahala yana jin yadda numfashin nasa ke wata fisga kamar zai bari ƙirjinsa. A hankali kuma ya ɗaga hannunsa zuwa sama kafin ya ware legs ɗinsa, idanunsa dake a rufe ya buɗe yana kumbura bakinsa tare da fidda numfashi. Girman ruwan da yadda yaga ruwa yay bala'in firgitar sa. Cikin sauri kuma yay baya da hannunsu yana ware ƙafa tare da fara nutsu cikin ruwan yana ninƙaya, ya ɗauki good 10minutes yana duban Akeela amma babu ita, yana ƙoƙarin juyawa idanunsa ya sauka akan ta tana jin wani reshe na baƙin ruwan daya riƙe mata riƙa. Hijab ɗin jikinta tuni ya zame yay gaba, gudun ya ƙara yana cimma ta yana gab da zuwa inda take wata igiyar ruwa ta riƙesa cikin kuma rashin Sa'a Wani irin ruwa mai yawan gaske ya tawo cure guda. Wani kalan ware idanu Md Adnan yay kafin yay wani yunƙuri na guduwa ruwan yay gaba dashi ji kake "Shuuuuuu" sautin gudan ruwan ya bayar. Dawo Driven yay yana faɗin "na kira, in sha Allah dukkan su noting will happen to them" Cikin damuwa Malam yace "Amma ko motsi babu, ji yadda ruwa ke gudu tsoro ya kamani sosai" "aifa da tsoro mutane har biyu ga wannan bawan Allan da gani bai saba da wahala ba" cewar Sunusi yana mai ƙara leƙawa cikin kogin. A can cikin motar Md Adnan Wayarsa ce take ta ringing kira na wajan uku kenan amma babu respond! A hankali motar da fara shigewa wani matashi ya fara knocking Ƙofar motar hannunsa riƙe da wayarsa yana ƙara danna number Md Adnan yana mamakin abinda ya tsayar da shi har yanzu bai ƙarasu ba gashi lokaci na tafiya. Daga cikin motar wani mutum ne mai kimanin shekaru 32 a duniya, yana zaune a back seat idanunsa maƙale da wani farin glass na haɗaɗɗun goyon nan. Sanye yake da wata fitinanniyar Double breasted suit dark Maroon. Gashin kan nan nashi yay kwance har wuya daga gaba ya kwanto, sai ƙyalli yake yasha Ginger Geminal Oil hair. Kakkauran laɓɓansa pink irin yirr ɗin nan lokacin zuwa lokacin yana taune su like his punishing kansa, fari ne tass irin farin nan da kai tsaye ba zaka iya tantance na wani ƙasa ko kuma jinsi ba, yana da kyau sosai looking soo damn sexcy and hot! Irin manyan mutanan ne masu tashe da zamani irin definition of classic masu fama da mahaukacin kuɗi na halak. Idanunsa ya janye daga kan haɗaɗɗiyar ƙaramar Apple system ɗinsa yana maida idanunsa Submariner Rolex ganin lokacin yaja ya ɗan saki siririn tsaki. Deep down kuma zuciyarsa na wani irin bugawa da ƙarfi, like something bad gonna happen to him. Irin mutanan ne da wahala ka fahimci sauyin fuskarsa, farin ciki da damuwa baya sanyawa kaga sauyi a saman fuskarsa. Yana da kamilalliyar fuska mai cike da ilhama da kuma tarin nutsuwa abu guda ke sauya masa tunani yaji ana masa ihu a saman kansa, ko kuma yaga anci zarafin wani ɗan Adam. Zame system ɗin yay tare da ajjiye ta a gefensa, cikin nutsuwa ya fara juyawa laɓɓansa yana motsawa a hankali. A taushashe sautin fitar amon muryarsa ke tashi yana faɗin. _“Asstagafirullah, Walahamdulillah, Wallahu Akbar”_ shine Amon kalaman dake fita a bakinsa. A karo na wajan huɗu P.a dake tsaye daga baƙin ƙofar ya ƙara Knocking ƙofar, taɓe baki yay kafin ya ɗaga hannunsa tare da danna glass ɗin motar yay ƙasa. P.a ne ya kalli mutumin cikin motar yace. "5times ina kiran number Md amma no answer" A karo na farko bayan sauke glass motar Dr. ABDUL-HAKEEM BUKAR BELLO ya ɗaga idanunsa tare da kallon P.a idanunsa kawai ya juya da sauri P.a yace. "Ok lemme try it" Ya faɗa yana ƙara danna number Md Adnan, kafin kuma gently ya miƙa hannunsa ya buɗe murfin motar, kamar bai so haka Dr A.b ya fito da ƙafarsa kafin kuma ya fito daga motar baki. Lumshe idanunsa yay saboda iskar ƙasa da ƙamshin sabbin shukokin da akai da suke dukan hancinsa. Yana da tsayi da faɗi jikinsa a murɗe yake ga wani faɗin ƙirji da yake dashi _(Physique chest)_ bayyanar ƙwayar idanunsa a yanzu ya tabbatar cewa shi ɗin _(Half-caste)_ ruwa biyu kenan. Zare jacket ɗin yay ya saƙala a hannunsa yana mai sassauta necktie ɗin wuyansa. "Sir har yanzu ga, gashi mun tara mutane sun taro mu kawai suke jira" Taɓe baki yay walking slowly ya nufi wani ma dai-dai cin waje da aka gyara yay ta tass ga kujerar da aka sanya masa. Maida wayar P.a yay zuwa aljihunsa yana mai mamakin abinda ya hana Md Adnan ɗaga wayar da kuma mamakin rashin ƙarasuwar sa is anything okay Babu damuwa ai rashin sanin dalilin shine damuwar. Waje Dr A.b ya samu wanda wasu jama'ar suke kiransa da AKEEM ya zauna yana mai sassauta haɗewar fuskarsa saboda ganin duk manya ne a wajan wanda shekarunsu, suka ja ainun. Cikin mutunci ya buɗe bakinsa a nutsu yace "Assalamu alaikum warahamatullah" Gaba ɗaya mutanan suka amsa masa kafin yay Shiru yin shirun nasa ne kuma yasa P.a dake gefensa a tsaye yace. Al'amarin ya girmi tunanin su Malam tashin hankali sosai ya bayyana akan fuskarsa yasan yadda ƙaninsa Bukar Bello ke bala'in son yaran nasa fiye da komai na rayuwarsa, yanayin komai saboda dasu ya hakan salwantar da nasa farin cikin just to see them happy, yaya zai kasance idan wani abu ya faru da Md Adnan? Wannan dalilin yasa baya barin su ko'ina sai companies ɗinsu da gida ko kuma ƙasar waje, he cares about his children yana mutuwan son su, ko zazzaɓin su baya jurewa musamman Mai sunan kawonsu. Driven Md Adnan ne yace "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un yanzu mene zance da Babban mai gida eh? Dan Allah? Yau warning ɗina akan na kula da driving ɗin Md Adnan ya kula dashi amma gashi shine ma yace ya shiga ruwan ƙilan dai yama kashe sa idan yaji labarin haka, domin yasan baƙar zuciyarsa. Malam ne yace "Ubangijin sammai da ƙassai ya kawo mana ɗauki, Wannan wanne irin tashin hankali ne eh?" Ya faɗa hawaye na zubu masa. Kafin kace wani abu tuni mutane sun taro wajan yara da manya, a dai-dai lokacin ne kuma motar kwanakwana ta ƙarasu suna zuwa suka fara aikin su nan da nan suka shiga cikin ruwan, sama da mintuna talatin babu Md Adnan babu Akeela. Tuni Driver ya fara kuka yana faɗin "shikenan wallahi na shiga uku wajan Babban mai gida, eh ina laifin ƴar kazar da nake ci na kwana katifa mai taushi ha banɗaki kamar ma kwanci, suttura kala-kala, eh? Duk banga haka ba ga ɗan ilimi dana samu na kan iya jin turanci ko yaya ne amma yanzu na tura masu ɗa cikin ruwa i can't forgive myself if anything happens to Ƙaramin Mai gida" Wayarsa dake ƙara ya duba ganin sunan Alhaji yasa ya ɗaga jiki na rawa yace. "Yallaɓai" gyara zama Alhaji Bukar Bello yay saman kujera hannunsa ɗauke da Mug yana shan coffee, yana sanye cikin Arabian Jallabiya mai taushi da laushi a ƙalla zai kai shekaru 63 amma jikinsa sam bai nuna ba, kyawunsa na samartaka na nan. Cikin ɗan sakin fuska yace "Bala" da sauri Driven yace "Na'am Yay.. Yallaɓai" ya ƙare maganar muryarsa na rawa, gaban Abbu ne ya faɗi haka kawai yaji zuciyarsa na tsinkewa cikin ƙasa da murya yace. "Bala where is my friends?" Shiru Bala driver yay yana zare idanu jin haka yasa Abbu miƙewa tsaye tare da goya hannunsa a baya a kaushashe Muryar nan babu wasa yace "Bala yarana" jin haka yasa Bala fashewa da kuka yace. "Tsautsayi da kauɗin harshe, Allah na tuba ka yafan...," Da sauri Abbu ya katse sa da faɗin "heeyyy Bala this is the last time da zan tambaye ke where is my friends? Ina cute two kids ɗina? Suna ina Eh Bala?" Haɗiye kukan Bala yay kafin yace. "Yallaɓai Ƙaramin Mai gida ne ya shiga ruwa kuma..." Gaba ɗaya ya faɗa masa abinda ke faruwa. Tun kafin ya gama jikin Abbu ya hau rawa idanunsa suka Kaɗa ganin yana ƙoƙarin faɗuwa yasa da sauri matarsa mai suna Hajiya Ayusher suna ce mata Ummi tayi saurin miƙewa yana ganin ta ya faɗa jikinta ya rungome ta sosai jikinsa na wani irin rawa bakinsa na ɓari yace "My Adnan My Friends ya rana Ayushertu" ya faɗa yana ƙara matseta a jikinsa. Jikin Bala Driver na rawa hannunsa wanda yake riƙe da wayar ya riƙe sosai yana faɗin "kai,kai! Ka tsaya mana wallahi yallaɓai bani da laifi idan ka kuran ina zan dinga cin shinkafa? Ina zan dinga cin naman nan naku mai daɗi da romo? Innalillahi wayyooo Ni Bala na shige su" Shiru yaji babu maganar Abbu sai Ummi dake faɗin "Subuhanallah, Abbu Meke faruwa da yaran namu? Didi! Didi! Mami" ta shiga kiran sunan mutane. Da sauri Bala ya koma wajan kogin har yanzu babu wani labari, ɗaya daga cikin ma'aikatan ne ya fito jikinsa duk ya jiƙe da ruwa. Da sauri Malam yau wajansa yana faɗin "Yaya! Wa aka fara cirowa" girgiza ma'aikacin yay yana sharce ruwan fuskarsa yace "till now babu wanda muka gani, ruwa ne yake da ambaliya daga ƙasa, Amma we're still searching in sha Allah za'a same su" Shiru kawai Malam yay tare da neman waje ya zauna yana ta sauke ajjiyar zuciya. A hankali p.a ɗin ya kalli mutanan wajan yace "Kamar yadda kuka sani, kai ya waye lokaci yazo wanda ba sai munce dole sai gwamnati ta taimaka mana Sannan za muyi wani abun ba, ko zamu jira gwamnati at least we have to..." Gyaran Murya Akeem yay da sauri P.a yace "Yes sir" kallonsu yay yace "kuyi hqr bakina yana juye zuwa wani harshe daban, yana da kyau mu fahimci cewa idan muka ce sai mun jira gwamnati Tabbas zamu mutu babu mallaki komai na rayuwa ba, idan nace komai ina nufin, Ilimi both buko da Arabic, ƴan ci, ƴanci na nufin ka samawa kanka abinda babu wanda zai wulaƙanta ka, babu wanda zai kanka yace dan Meye ne kai Wannan? Ka zama komai kai updating kanka daga old version zuwa latest version something new haka" shiru yay yana kallon yadda Akeem ya yatsuna fuska kafin ya ɗura da faɗin "mun samu saƙon ku daga office ɗin mu dake AKEEM BETTER FARMING INSTITUDE A.B.I na samu sanarwar daga wajan H.o.d Ni kuma na faɗawa Md Adnan, Md ya faɗawa C.E.O na wannan makaranta zance maku ne ko ma'aikata? Bama duba messages ɗin da bana e-mail bane, amma muhimmacin garin da kuma albarkatun noma da muke dashi a wannan garin me albarka Sir Akeem kuma Dr Abdul-hakeem Bukar Bello C.e.o of Akeem better farming institute yace a shirya tafiya kafin yace fara gabatar da aikinsa da Za'ai a channel ɗin M.hausa dake GOtv and DStv yanzu muna son ɗaya daga cikin ku ya faɗa mana matsalar ku" Wani babban kuma mai ɗan shekaru ya miƙe bayan yay godiya ne ya ɗura da faɗin. "A kullum muna fuskantar barazana daga wajan manyan mutane wanda suka tsoratar damu da faɗin sunayen su" Akeem da idanunsa ke ƙasa yana zuciyarsa na tsalle kamar zata faso ƙirjinsa ta fito saboda faɗuwar gaba ya ɗaga idanunsa ya kalli mutumin kamar bazai magana ba sai kuma yace "Uhm" yana faɗin hakan yay shiru da sauri kuma P.a ya miƙa masa gorar ganin yana shafa ƙirjinsa cikin ƙasa da murya cike da tsoro mutumin yace. "Sunce mu bar masu gonakin mu akan kuɗi dubu ɗari biyar biyar ga dukkan mutumin daya sanya hannunsa a kan takardar, za suyi ma'aikata, da farko Bamu san wacce kalar ma'aikata bace, yaran mu masu tashi sune abin tsoro, mun yarda da noma, kuma itace arziƙin mu da dukkan wanda yake ƙasar Nigeria, Noma toshan arziƙin mu kuma kwanciyar hankalinmu mu manoma, wasu nayiwa noma kallon wani abu nada ban amma da ace mutum zai san amfanin noma da kuma ribarta to hatta samarin da suke da kwalin jami'a tabbas zasu ajjiye dugun buri su tawo gona domin yin Noma, babu buƙatar kuɗi gonakin mu muke buƙata, ƙauyen dake gaban namu sun amince bisa shawara dana masu har Abin yake neman juyewa zuwa tashin hankali, shine yasa muke neman taimako daga gareka ka shiga wannan lamarin muna buƙatar gonakin mu" ya faɗa yana haɗe hannayensa waje guda, ganin hakan yasa gaba ɗaya mutanan wajan suka miƙe suna haɗa hannayensu waje guda. Da sauri Akeem ya miƙe yana fidda numfashi domin baya ƙaunar wani babba ya duƙa masa. Wata haɗaɗɗan jotter da pen P.a ya bawa Akeem cikin sauri ya fara rubutu mai cike da tsari daga ƙarshe ya rubuta. _From Akeem better farming institute_ To _marasa tsoran Allah masu son ci da gumin wasu_ Sign ~Abb hero~ Yana gama rubutawa ya miƙawa P.a idanunsa ƙasa dan bai so ake ganinsa kafin a hankali cikin fitar wata Amon murya irin golden voice ɗin nan yace. "Ku ɗauka ku Alhalin Abdul-hakeem Bukar Bello ne, babu abinda zai samu lafiyar ku, Alhalin ku, duniyoyin ku" yana faɗin hakan ya juya walking slowly irin tafiyar nan mai ɗaukan hankali. Cikin sauri kuma a ransa ya furta "Adnan" da sauri ya nufi mota ganin hakan yasa P.a yabi bayansa motar ya shiga kana yana da gudu hankalinsa gaba ɗaya yay kan ɗan uwansa yana mutuwar son ganin nasa, he Loves him yafi son komai zai faru ya same su tare. Wayar Md Adnan ya kira amma babu answer hakan yasa Murya can ƙasa yace. "Uhm p.a drive faster" Gudu ya ƙara suna zuwa dai-dai wajan taron jama'a Bala driver na ɗaga kiran Akeem ganin sunan Blood yasa Bala ya shiga uku. Bai tsaya jiran jin abinda Bala zai faɗa ba, da sauri p.a ya fito daga motar yana buɗewa Akeem murfin motar, kai tsaye idanun Akeem ya sauka akan Baffansu. Da sauri Malam ya miƙe ganin Mai sunan kawonsu yace. "Kaga abinda ya faru ko? Daga zuwan Adnanu ya haɗu da aljalinsa" da wani irin kallo Akeem yabi Malam yama kasa gane mene sauke faɗa. Ka kaff Malam ya bawa Akeem labarin abinda ya faru, nan da nan fuskarsa tai jajirrr saboda tashin hankali amma ko kaɗan babu wani alamar tashin hankalin cikin ƙwayar idanunsa saboda shegen shanye abune dashi a rai. Zame jikinsa yay daga wajan Malam kai tsaye wajan ruwan ya nufa Malam na faɗin "A'a Mai sunan kawo kada mu rasaka dan Allah ka tsaya.." kafin ya gama magana tuni Akeem ya faɗa cikin kogin nutsu ya fara cikin ruwan cike da ƙwarewa yake sarrafa ruwan tamkar dai wanda ya san kanshi babu jimawa idanunsa ya sauka akan wani Abu mai duhu, cikin sauri yay wajan yana zuwa yaga mace saƙale jikin reshe ƙarasawa yay wajanta yana mai ɗan ƙara ware idanunsa ganin babu Md Adnan babu Labarinsa wani iri tsoro ya kamasa cikin damuwar ya nufi wajan Yarinyar yana zuwa yay wani irin..... *🌈TSINTACCIYA🌈* NIMCYLUV _FITATTU HUƊU🔥_ EPISODE3️⃣ http://wa.me/+2348119237616 *_domin magana dani kai tsaye👆🏾_* Tura kansa dake cikin ruwan zuwa waje yay yana haɗa numfashi, cikin wata kasalalliyyar murya mai cike da alhini yace "I got her" yana faɗin hakan kwanakwanan suka cilla masa duguwar igiya ya kama tare da ɗaura igiyar a ququnsa. Cikin saurin ya nusa cikin ruwan kafin a hankali ya kama igiyar data riƙe ƙafar Akeela. A hankali ya kunce igiyar gaba ɗaya Akeela tayi baya tare da fara yawo a ruwan zata matsa can gefe saboda ruwan da yake gudu sosai, Fararan tafin ƙafafuwanta yabi da kallo, sunyi wani mugun haske kamar jini zai zuba a jikinta saboda farin da take dashi. Tattausan hannunsa ya miƙa tare da jawo tafin ƙafarta "kittt" ya jata da zuwa inda take ƙarar tawowar wani ruwa ne ya daki kunnansa da sauri ya fisgota yana runtse idanunsa tare da sanya dukkan hannayensa ya wist ɗinta ya wani ƙanƙame idanuna da hannunsa dake bisa jikinta ko motsi ya ƙiyi. Ya ɗauke dukkan Numfashinsa yana jin sanda ruwan ya shige ta gefensu kamar zai tafi dasu. Zaro kanta dake jikinsu yay sai a lokacin idanunsa ya sauka akan fuskarta _Tsarki tabbata ga Ubangijin daya halicci sammai bakwai da ƙassai bakwai, Ubangijin daya halicci wannan duniya ya kuma halicci wannan surar dake hannun Akeem_ faɗin asalin kyan fuskar Akeela bata baki ne, tana da wani irin sahihin kyau, wanda ya wuce tunanin mai tunani, idanunta a rufe suke ruff amma eye lashes ɗin nan da suke dugwaye slick dark blck sunyi kwance saman kumburarrun idanunta, ga dugun hancin nan mai kyau sosai, wanda ya tsaya dai-dai tsagen laɓɓanta wanda suke da kauri sunyi jajir dasu. Gashin kanta data ɗaure da ribbon tuni ya wargatse ya baje yana yawo cikin ruwa sai ta zama kamar wata aljanar cikin ruwan da mutanan suke faɗa. Taɓe baki Akeem yay kafin cikin zafin nama yay wani cillata bayansa ya goyata sosai kafin ya gyara zaman igiyar jikinsa. A hankali ya fara ta suwa sama cikin ƙwarewa kwanakwanan na ganinsa suka fara jawo igiyar ruwan. P.a ne yabi Ubangidan nasa da kallo yana tuna wani abu daya wuce amma ya rasa ko menene, amma Tabbas ganin Akeem goyo da Akeela ya tuna basa wani abu mai mata tuƙar muhimmacin a rayuwarsa. A fili Malam ya furta "Allahamdulillah biii rahmatiikaa" Suna zuwa bakin ruwan yay wani irin baya yana daga tsaye yay wurgi da Akeela ta faɗi ƙasa ji kake "timmm" kanta ya bugu ƙasa amma ko motsi ba tayi ba saboda bata hayyacinta ta jima da sumewa. Jikin Akeem na wani irin kyarma da rawa idanunsa sunyi jajir jijiyoyin kansa sun yi bala'in tashi sai wuci yake na zafin zuciya da kuma sayin ruwan daya gama ratsa dukkan kofofin jikinsa. Kai tsaye wajan Bala driver ya nufa, ganin haka yasa P.a ya mara masa y domin yasan anything can happen idan Akeem ya ƙarasa domin a wannan karan ɓarin da jikinsa yake ya bayyana asalin zafi da kuma ƙuncin da zuciyarsa keyi, ya bayyana how sad he's. Yana zuwa ya kalli Bala driver murya can ƙasa yace. "Car keys?" Zare idanu Bala driver yay kafin ya fashe da kuka yace "Dan Allah dan Annabi kayi min suttura Babban mai gida, ka tausaya min kada ka kuran i don wanna lose my job dan Allah, dashi kawai nake kula da iyali na, na sani a made a mistake amma bani na tursasa Ƙaramin Mai gida shiga ru..." Gigitacciyyar tsawar da Akeem ya daka masa yana faɗin "Heyyy, car keys nace kaban, kada ka tunzura ni ka bari zanyi Shari'a dakai da ita kanta tsinanniyar datai Coursing wannan abun i hate her, idan ina da rai da lafiya billahi I'll take a revenge, you'll see mene zan, common my friend bani" da sauri Bala driver ya miƙa masa tarin kyes ɗin, huci kawai Akeem yake idanunsa a ƙasa domin duk abinda zai bai fiya kallon mutum ba, gyaran murya yay jin haka yasa p.a faɗin Md Adnan's phone's, his I.d card" wayar ya miƙa masu kafin ya ɗauki walet ɗin dukkan wani card da ake amfani da shi ya bawa P.a. Kai tsaye mota Akeem ya nufa zai shiga ko takan Yarinyar baibi ba, kafin ya shiga motar P.a yace "Sir" da sauri ya juya yana dafe kansa cikin haɗewar fuskarsa nan nashi yace "what again P.a Al'kaseem Yahya gama?" Yadda ya kira full name ɗin P.a yasa kowa na wajan kallonsa a sanyaye p.a yace "Abbu" ke kira. Kamar bazai amshi wayar ba sai kuma ya amsa walking slowly yake tafiya yana baje gashin kansa wanda ruwa ya jiƙa daga can ɓangaren Abbu yace. "Son" marai-raice fuska yay ba tare da yace komai ba, jin haka yasa Abbu faɗin "Are You okey?" Nan ma shiru yay bai ce komai ba hakan yasa Ummi dake gefensa faɗin "Is everything okay?" Didi dake tsaye riƙe da bakin zani tsohuwa ce sosai shekaru sun ja tace. "Ihuu jama'a, bana faɗa ba? To kai dai Bukari ka haifi ɗa baka haifi halinsa ba, yaro baƙin hali yay masa yawa a to ai duk duniya ba sun shaida, jiya kana gani ilahirin tsiran daka kawo min ta tasss yabi dare ya sace, to ɓarawo ne fa? Banda maye waye ne zaice wani tsire ehe? Ai saini da cinsa ya zame min dole amma ina dai ba faɗin wasa wallahi Bukari ka nemawa ɗan ka magani bana son na fita ana min cune da baki ana gata can, jikanta maye ne, mece cin nama da zaro harshe waje....." Shiru tayi Saboda saukar Muryar Akeem da taji ta wayar tana faɗin "Keeee!" Zare ido Didi tayi sai kuma ta fashe da kuka tana zare bakin zabi tana faɗin "to! A nan gidan duniya idan ban sawa Audil albarka ba wa zan sawa? Eh? Ta ka samu Iyaye da basu san komai ba ina nan ina jan casbie sai da nayi salati miliyan tamanin da shida to astagafirullah kamar dai bakai haka ba" Girgiza kai kawai Abbu yay kafin yace. "Friend ina son?" Ajjiyar zuciya Akeem ya sauke kafin yace "Abbu she killed my brother ta kashe mana Adnan" Miƙewa Abbu yay kafin yace "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Adnan ya mutu?" Wane kalar zabura Didi tayi sai ga zani a ƙasa tama ƙasa magana. Ummi bakinta ta rufe saboda kukan da yazo mata da sauri tayi bedroom ɗinta, Mami kuwa idanunta kawai ta ƙurawa Abbu Allah yasa raguwar yaran duk suna makaranta Amani kuma tana bacci. Cikin dauriya Abbu yace "Stay there Abdul-hakeem, in sha Allah on my way yanzu nan kuje gidan Baffa" yana faɗin hakan ya kashe wayar tare da nufar part ɗinsa.. Ƙasa Mami tayi da kanta sai sauke Ajjiyar zuciya take, Didi kuka kuka ta fasa tana faɗin "Wanne gantalallan ne Adunan? Laa Muhammadur Rasulullah S.a.w ku tare ni kada naje ƙasa" Kwantar da Akeela akai a ƙasa Taɓa jikinta Malam yay yaji wani mugun sanyi, a dai-dai lokacin har sarkin ruwa yazo amma neman duniya babu Md Adnan gaba ɗaya suka rankaya zuwa gidan Baffa, suna zuwa Malam yace "Rabi maza haɗu min gaushi" babu jimawa ta dawo ɗauke da gaushi Miƙewa yay yana fita yace "maza sauya mata kaya Wannan na jikinta yay sanyi da yawa" Murmushi kawai Baba Rabi tayi yana fita ta miƙe tsaye tare da kunce bakin zani wata ƙaramar (Laya) ta ɗauko tare da samun kan Akeela wajan tsakiyar kanta ta haɗa da Layar ta rufke gashin wajan layar da shige ciki. Wani Murmushin ta sakeyi ita kaɗan tasan abinda take kafin ta sauyawa Akeela kaya ta rufe ta da zani jikinta yay sanyi sosai kamar ƙanƙara. Har lokacin Akeem bai shigo gidan ba, yana cikin mota sallah kawai ke fito dashi. Wajejen Magrib Abbu ya ƙarasu daga kano da Wudil, har lokacin kuma Akeela bata farka ba, jiki a sanyaye Abbu yace "Baka da laifi, infact Adnan taimako yaje yi, Allah kaɗai yasan abinda ya samu Adnan, yana ruwan? Mutuwa yay? Tafiya ruwan yay dashi no one's know! Tabbas idan nace banji zafi da baƙin cikin abinda ya faru ba nayi ƙarya, amma ni musulmi ne waman ƙaddararllahu haƙƙa ƙadrihi, kuma Innallaha ba'assabirin zanyi addu'a zan saka ai idan har Adnan n raye Tabbas zai dawo gare ni" Jinjina kai Malam yay kafin yace "haka ne, Ubangiji yasa Adnanu yana raye yaron ƙwarai" Miƙewa Abbu yay yace "Ina ita yarinyar ya farka ne?" Girgiza kai Malam yay yace "A'a muje ka ganta" gaba Malam yay Abbu ya bisa a baya cikin tafiyar nan nashi irin na Akeem yana sanye da wata bugaggiyar shadda dark Ash sai jaddara sai ƙamshi yake. Malam ne ya fara shiga sai Abbu yana shiga idanunsa ya sauka akan Akeela gaba ɗaya tunaninsa ne ya tsaya cak, zuciyarsa na wani irin harbawa Kallonta yake tamkar zai cinyeta ko ya mayar da ita ciki, wani irin kallo ne mai kama da wanda ya kamo da soyayya! "Bukar! Bukar!" Da sauri yaja numfashi yana shafa ƙirjinsa kafin ya kalli Malam da sauri kuma ya juya yana kallon Akeela dafe ƙirjinsa yay ji yay wani mugun so da ƙaunar Akeela ya sauka a zuciyarsa har yana jin idan bai aureta ba zai iya mutu.... 😂 Alhaji ka taro match, mata biyu? Eh? Yara sama da biyar kaga ɗanya sabuwar nona kace kana so? Jama'a me kukace anya Abbu bai so zuciyarsa ba???? ANJIMA DA FARA PAYMENT TUN KAFIN NA FARA POSTING *TSINTACCIYA* NRML GRP: ₦300 VIP: POSTING SAFE+YAMMA ₦500 ACCT NO: 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S BANK NAME: UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *FITATTU HUƊU🔥* TSINTACCIYA Nimcyluv Baƙar fata Autar manya DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAN Mss flower Gaba ɗaya 800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman Fidelity Bank, masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* For more information😇 http://wa.me/+2348119237616 *🌈TSINTACCIYA🌈* NIMCYLUV FITATTU HUƊU🔥 _Dedicated to *ELEGANT ONLINE WTITER'S* Ina maku sahihiyar ƙauna mara algus❤️❤️_ EPISODE 4️⃣ http://wa.me/+2348119237616 *_domin magani dani kai tsaye_* Jiyayi Numfashinsa na wata iriyar fusga lokacin daya sauke idanunsa a saman ƙirjinta, cikin sauri ya zame idanunsa yana shafa fuskarsa. Bai taɓa ganin halittar da yaji yana mutuwar so, irin son nan mai zautar da mutane irin Akeela, at least zai iya good 35yrs ko sama da haka, kusan jiƙarsa ma take ba ƴar ba, ko zai haɗata da yaransa sai dai suyi age mate da Aleema. Malam ne yay gyaran murya kafin yace "zauna mana Bukar" zama yay still idanunsa akan fuskar Akeela kamar zai haɗiye ta, saboda wani mugun kyau da tayi masa a fuska, ga ƙirjin nan dam, so Ma sha Allah, But even her lips are looking luscious succulent and irresitable every tensed man. Shafa fuska ya sake yi kafin yace. "Baffa badai Akeela tayi wannan girman ba?" Murmushi Baffa yay yace "Wallahi Bukar" "Allah sarki, the last time dana ganta tana primary 2 ne" cewar Abbu ya faɗa murya a shaƙe. A sanyaye Baffa yace. "Kayi hqr Bukar garin ceto ƴar dana haifa ɗan cikin ka yay asara nasa rayuwar" kamar Baffa zai kuka saboda damuwa cikin damuwar shima Abbu yace "haba Baffa, da abinda ka haifa da nawa ai duk ɗaya ne ko? Blood is thinker than water, koni i can do anything for this innocent gril, she deserved it" Murmushi Baffa yay zuciyarsa na masa zafi sosai Kafin yace. "Ban san mene yasa Akeela tayi hakan ba, tana da hankali amma lalurar da Ubangiji ya jarabce ta dashi na neman zautar da tunaninta" da Mamaki Abbu yace "lalura?" "Eh! Tana da Amosa nin jini (SIKILA), wanda ke sonta tunda yaji labarin ciwonta yace ya fasa, bazai iya zama da mai ciwon SIKILA ba, haka nan taje ta shafa masa, shiyasa na yanke shawarar bawa wani auranta mai suna Malam Buba, yana da mata uku yara goma tsoho ne domin ya girme min, yace yaji ya gani zai zauna da ita a hakan, tun lokacin Akeela ta daina walwala na san bata son shi, to idan bata Aure sa ba wane zata aura? Eh? Kasan yadda ciwon SIKILA yake kamar Annoba a wannan lokacin musamman a wannan lokacin damuna da muke ciki, wannan dalilin yasa ta nemi kashe kanta ta wuta da bala'i" Shiru Abbu yay Mamaki duk ya kamasa, yarinya like Akeela da ciwon SIKILA? Allah Al-hakkamu kenan bowayi gagara Misali. Gyara zama Abbu yay cikin serious tone voice yace. "Cutar sikila ko amosanin jini na ɗaya daga cikin cututtukan da za'a iya cewa na neman zama ruwan dare, saboda yadda ake yawan samun yin aure tsakanin masu rukunin jini AS da AS ko SS da AS, amma Abu mafi muhimmanci Shine babu yadda za'ai ba tare da gamayyar ƙwayayen haihu ba mutum ya samu SIKILA, babban jahilci ne ma gamai cewa za'a shafa masa, ai ba tari bane, ko H.i.v SIKILA zan iya haɗata da Asthma, amma Baffa batun zaka aura wa Akeela wani can banza bai taso ba, kai mata aure inda ake sonta kuma za'a kula da ita, na tabbatar he loves her just of her beauty and.." Shiru dan baya jin iya cewa wani abun. A hankali Baffa yace "To Bukar yay zan? Wayewar inda kuke da nan akwai bambanci sosai" idanunsa akan Akeela yace "Allow me to go with her, ka bani ita, zan haɗa ta da miji na gari wanda zai kula da ita, tai cikakken ilimi inda zakai farin ciki zan haɗa ta da yarana" ya faɗi maganar ba tare daya shirya ba, domin ji yake ko mintina goma bazai iya ba tare daya kalli Akeela ba, yay hakan ne saboda ya samu very close to her ya dasa mata masifafan son sa a Zuciyarta wanda Turawa suke cewa _ETERNAL LOVE_ yasan kuma soyayyarsa da ita ba zata taɓa zama _FORBIDDEN LOVE_ ba. Jin muryar Sarkin ruwa a bakin ƙofa na sallama yasa Baffa Miƙewa cikin sauri yay waje. Yana fita Abbu ya miƙe, cikin tafiyar nan wacce ya kejin kansa ontop, a hankali ya ƙarasa inda Akeela ke shimfiɗe kamar ma matacciya, Ƙirjinta dake sama da ƙasa ya kalla ganin hakan yasa ya tabbatar she still alive. Tsaye yay a kanta yana sauke numfashi tare da lumshe idanunsa slowly kuma ya ƙara buɗe idanunsa, kamar zai juya sai kuma ya sunkuya dai-dai kanta yana Kallon Zallar kyan fuskarta. Hannunsa ya sanya ya ɗan ƙara zame zanin kanta nan take sumar kanta ta bayyana irin sosai ɗin nan gata rabi baƙa rabi jaa. Wani cute smile yay yana yin ƙasa da bakinsa zuwa saman fuskarta bakinsa ya manna a goshinta tare da bata wani special kiss wanda ya kejinsa best kiss in his whole life. Baffa ne ya kalli Sarkin Ruwan kafin yace "fatan an samu Adnanu ɗin?" Girgiza kai Sarkin Ruwan yay yace "gaskiya babu wani labari, amma dai ga abinda muka samu" ya faɗa yana miƙawa Baffa rigar jikin Md Adnan karɓa Baffa yay yace "to mungode ƙwarai shi kuma Allah ya bayyana mana shi, idan yana raye ya kai sa hannu na gari" da Ameen Sarkin Ruwan ya amsa. Har Baffa zai juya sai kuma ya nufi motar Akeem yana zaune zuwa lokaci ya zame rigar jikinsa daga shi sai singlet murɗaɗɗan ƙirjinsa ya bayyana, ga sumar nan har lokacin na zubda ruwa, banda sauke numfashi babu abinda yake. "Mai sunan kawo" Baffa ya kira Akeem, gently ya ɗaga kansa tare da sauke ganinsa akan Baffa kallo guda yay masa ya ɗauke kansa yana taune leɓansa tare da lumshe gajiyayyun Maraitattun idanunsa. "Nasan kana jin haushin na ne ko? Kana ganin kamar da gangan nai hakan ko, to wallahi tsananin son da nakewa yarinya ta yasa nai haka amma nama fika baƙin ciki a yanzu haka" Shiru Akeem yana danna system ɗinsa ba zaka taɓa cewa dashi Baffa yake Magana ba, fuskarsa looking okay Babu wani sauyi. Sanin halin Akeem yasa Baffa juyawa. A tsaye Baffa ya samu Abbu yana kallon Akeela kafin yace "to ko dai kwana za kuyi ne?" Girgiza kai Abbu yay yace "A'a yanzu zamu tafi in sha Allah" da sauri Baffa yace "to bari na kwaso kayanta ko" kallon Baffa Abbu yay kafin yace "haba Baffa no need, Akeela is like my daughter zan mata komai" murmushi Baffa yay hawaye na saukar masa domin gani yake ƙanin nasa kawai daurewa yake rashin Md Adnan ba ƙaramin babban giɓi bane a rayuwarsa. Baba Rabi ce ta shigo idanunta yay jaa sosai irin taci kuka ta ƙoshi, kafin ta kalli Abbu tace "Mungode sosai Alhaji Bukar Allah ya bayyana mana Adnanu cikin aminci" "Ameen" kawai Abbu yace domin sosai zuciyarsa ke masa zafi kuka ne kawai da bazai ba, amma ganin fuskar Akeela na yaye masa wani ƙuncin. Baffa ya nufi wajan Akeela zai ɗauke ta da sauri Abbu yace "A'a Baffa, Ni da zamu tafi tare bari na ɗauke ta" Hannu yasa ya ɗauke ta sassanyar Ajjiyar zuciya Abbu ya sauke yana jin zuciyarsa na sanyi sosai, wani mayataccen Murmushi Abbu yay tare da fakar idanun Baffa yay wani tura ƙasa tsakiyar wuyanta... *🌈TSINTACCIYA🌈* NIMCYLUV FITATTU HUƊU🔥 Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE* *I selling MTN data with this cheap price* *MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance. *Validity 1 month* *Airtel,9mobile and Glo* *also available.* *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR Call 08066268951* EPISODE5️⃣ Http://wa.me/+234811237616 Bayan sallar magrib motocin su suka fara shigowa cikin haɗaɗɗan titin _Railway quarters Nasarawa, Kano_ A gida mai number 112 suka fara shigar da motocin bayan gatekeeper ya buɗe masu ƙaton gate ɗin. Motar Abbu ce a farko shida Bala driver sai Akeela dake kwance a baya. Mota ta biyu kuma P.a a ciki shi ɗaya yana janta motar ƙarshe kuma Oga Dr Abdul-hakeem Bukar Bello ne zaune ya ɗura hannunsa guda ɗaya a saman string motar ɗaya hannunsa kuma ya tsakiyar kansa yana hargitsa sumar kansa, a hankali kuma yake sauke ajjiyar zuciya ajajjere. Zafi da raɗaɗi da zuciyarsa ke masa na tawowa da Akeela da Abbu yay yafi komai baƙanta masa, cos she's the reason behind anything daya samu Md Adnan. Bama ya so ya buɗe ido yaga yarinyar shiyasa yau zamansa cikin motar tare da lumshe idanunsa yana so Abbu ya shige da ita domin ta riga data zame masa mujiya. A hankali Abbu ya buɗe back seat tare da zura kansa cikin motar, dim! dim!! dim!! Haka zuciyarsa ke bugawa aduk sanda ya kalli ƙyakkyawar fuskarta wata nutsuwa ta saukar masa. Zama yay cikin motar tare da miƙa hannunsa gaba ɗaya biyun ya jawota sosai very close to him, hannunsa dake rawa yasa tare da yin baya da gashin ta wanda ya sauke wai wist ɗinta, Lumshe idanunsa yay cikin ƙasa da Murya yace "Uhm baby na mai kyau, nine ko?" Ya faɗa yana shafa kanta sai kuma ya cireta sama tare da fito da ita daga cikin motar, dai-dai kunnanta kamar wacce ta kejin sa yace. "I'm your dad, your boyfriend uhm baby kina cin abinci kuwa? You are so light Baby" ya faɗa yana tafiya da ita kamar wani mai sabon jini bayan yay jika da ita. P.a dake tsaye ya ɗauke idanunsa a hankali kuma yabi bayan Abbu da some things na Md Adnan. Tsayawa Abbu yay tare da danna wani ma danni a hankali ƙofar ya fara ja baya tare da buɗewa ciki ya shiga babban Parlo ne daga cikin ƙofar, iya haɗuwa ya haɗu komai na Parlo Ash ne daga kujeru zuwa Flowers da labulaye anything dai. Ga ƙatuwar cineme kusan rabin bango sai deep frizer mai gida wajan uku,ga senter table a tsakiyar mai ɗauke da wata ƙatuwar flower jikin bangon parlon duk Album ɗin ayatul kursiyu ne, da fatha e.t.c Daga can bayansa yaji ana faɗin. "Ya..yah kamar dai ƴan gudun hijira kuka faɗo mana gida babu ko Sallama? A'a babu ruwana kuda Allah tun dai duk musulmai ne a gidan da haka nan kamar ƴaƴan arna zaku faɗu mana gida, ai ko ƴan dama ne ku kwayi sallama musan da zuwanku kuma musan abinda zamu baku" Kallon Didi Abbu yay kafin yace. "Afuwa Didi" Taɓe baki tayi kafin tace "A'a astagafirullah mene kuma afuwa fisabilillahi kamar dai nace akan Bukari siya min tsire? A'a ni rayuwar duniya mai sauƙi na ɗauke ta, Wacece wannan kuma Aljanu take ko shan Inna ce ta kamata" Ta faɗa Idanunta akan Akeela wacce take jikin Abbu. P.a Murmushi Yay domin yana son dramer tsohuwar kafin yace. "Barka da dare Didi" Washe baki Didi tayi tace "A'a ƙasimu ince dai ka samu matar aure? Yooo ba Gwamma kai ba ko babu komai zan baka shawara mai kyau kabi, kaga dai babu dangi iya babu na baba jinƙai da tausayi irin nawa nasa aka baka aiki gashi kuma yanzu nace kaje wajan yarinyar idan ubanta har yanzu yaƙi yadda ta Aure ka kawai kayi mata ciki kaga ko babu komai dole a baka ita ka aura ni wallahi yarinyar ba tayi min ba" shi dai Shiru kawai yay yana Murmushi ita a dole shawara ta bashi idan kuwa haka ake bada shawara da an shiga uku. Kwantar da Akeela Abbu yay a hankali kuma fara faɗin. "Ummi!! Mami!!" Mami ce ta fara fitowa idanunta ya kumbura sosai saboda kuka, baƙa kana ganinta kaga mahaifiyarsa Md Adnan zatai shekaru wajan 42 tana sanye cikin wani haɗaɗɗan lace, Zama tayi a kujerar dake farcing Abbu ba tare da tace komai ba. Not too long Ummi ta fito daga part ɗinta hannunta riƙe da wata ƙyakkyawar Yarinyar zatai shekaru 4 haka fara ce sosai kamanin Akeem zane raɗau a saman fuskarta Amani kenan jika a wajan Alhj Bukar Bello ƴar kuma wajan Dr Abdul-hakeem Bukar Bello. Zama Ummi tayi kusa da Mami tana sanye cikin wata orange ɗin lafaya tai mata kyau sosai zatai shekara 45 haka amma jikinta a murje yake sosai har tafi Mami gogewa da kuma wayewa. "Barka da dare ya hanya" Ummi ta faɗa murya ƙasa. Kallon su duk yay kafin fuska a ɗan haɗe domin bai fiya sakin fuska ba idan ba keɓewa yay da matansa ba yace. "Kunga abinda ya faru da Adnan ko? Jikina yana bani yana raye kuma komai jimawa zai dawo gare mu, i believe cewa komai sai Ubangiji ya tsara mu ɗauki hakan a wata sabuwar ƙaddara daga Allah wacce ya jarabce mu domin gwada imanin mu, ko yarda na yarda cewa hakan ya faru ne dalilin shigarsa ruwan, amma ruwan ne dai kawai ya zama sanadi amma tuntuni Ubangijin AL-ARSHI ya tsara faruwar hakan a Lauhil Mahfouz..." Da sauri Didi tace. "Sadaƙallahul Azeem,amma dai Bukari ka cuce mu da baka zama malami ba ka rasa mai zakai sai siyasa, ai yasin naji daɗi daka sauka daga kujerar mulkin baki ɗaya, ai da wallahi har govmet hausi ɗin zani nace bada yawo na ni Uwarka idan suka zaɓe maka, haka kurum na fita waje a dinga shunani da baki ana gata can ɗan ta yana handime kuɗin jama'a" Ta faɗa tana cuna baki gaba, shi dai Abbu bai ce komai ba domin yasan rikicin tsofa ne. "To! Ubangiji ya dubi idanun mu ya sanya Adnan yana raye ya kuma dawo gare mu, Allah ka dubi halin da muke ciki" A sanyaye Mami tace "Ameen" idanunta na ƙara kawo ruwa ajjiyar zuciya Abbu ya sauke kafin ya kalli Akeela yace. "Ɗiyar Baffa ce da Baba Rabi dalilinta Adnan ya faɗa ruwan kuma Thank God Dr ya ciro ta..." A nan ya kwashe labarin kakaf abinda ya faru ya basu. Ihu da kuuu Didi tasa zani na faɗuwa tace. "Kun kashe min Adnanu wallahi hisba zan kaiku" Tana faɗin hakan ta nufi waje a hanya taci karo da Akeem dake shigowa fuska ya haɗe sosai ko alamun annuri babu. Ganin haka yasa Didi washe baki tace. "Yooo yanzu naji bayani ai cewa nayi bari na leƙa naji mai gidan Shiru fa" Bai ƙara kallon ta ya matsa can gefe sallama ma ciki yay kai tsaye upstairs ya nufa wajan part ɗinsa. Ganin haka yasa Abbu faɗin "Dr kazo ka duba Akeela" jin sunanta yasa Akeem yaji kansa ya sara Mami kam Miƙewa tayi domin tunda taji a kanta Adnan ya faɗa ruwa taji wata muguwar tsanarta ya cika Zuciyarta. Da ɗan sauri Akeem ya ƙarasa haurawa saman ko takan Abbu bai bi ba ganin hakan yasa Ummi faɗin. "Bari na duba ta" Ɗaukan ta Abbu yay zuwa part ɗin yaransa mata, ɗakin duhu alamar duk sunyi bacci On yay na wutar bedroom ɗin Aleema,Afaf duk suna kwance wajan Ameera da take zuwa hutu ya kwantar da ita, lokacin tuni Ummi ta ɗauko kayan aiki, cikin sauri ta fara duba ta ganin har yanzu da ruwa a cikinta yasa ta danna cikin da sauri sai ga ruwa na fita. Tana ƙara dannawa Akeela tai hau yin tari. Wata Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya Abbu ya sauke tana gama tarin kuma bacci ya ɗauke ta, sai da Ummi tayi mata injection kana ta ɗaura mata drip Abbu yi yayi kamar bazai fita ba ganin kallon da Ummi ke masa yasa ya ɗan shafa kansa yace. "Miss You dear, let's go" Gaba yay ta bisa a baya kana ta jawo masu ƙofa, Daman p.a tuni yay masu sallama ya tafi gida. A hankali bakinsa ke motsawa yana tasbihi can ƙasa zuciyarsa, saboda zafin da zuciyarsa ke masa, cikin haɗaɗɗan parlonsa ya shiga komai na Parlon white ne. Ya haɗu sosai har ba'a magana, kai tsaye wata corridor ya bi hadle ɗin ƙofar ya buɗe, wani irin lumshe idanunsa yay tare da sauke wani maraitaccen numfashi yaja tare da saukewa, saboda wani sassanyan ƙamshi daya daki hancinsa ya sashi lumshe idanun da bai niyya ba. Tura kansa cikin bedroom yay bakinsa ɗauke da wata kamilalliyar sallama yana maida ƙofar ya rufe. Derect bathroom ya nufa yana mai zare kayan jikinsa, a saman hanger ya saƙale tare da sakarwa kansa shower, a hankali yake sauke ajjiyar zuciya yana jin yadda ruwan yake dukan saman fresh skin ɗinsa. Bayan yay wankan ya ɗaura alwala kana ta ɗauki wani long white towel ya dauraia wist ɗinsa, ko kansa bai tsane ba ya fito ruwa na sauka daga sumar kansa zuwa ƙwantaccen gashin ƙirjinsa. Wani irin ɗaci bakinsa yake masa rabon da yaci abinci har ya manta wajan fridge ya nufa ya ɗauki Apple da cake ya fara ci bai wani ci da yawa ba ya ajjiye. Wasu haɗaɗɗun nightwear slik Pajamas milk colour, a hankali ya miƙe tare da goya hannunsa a bayansa ya ɗan fara tafiya yana mai karanta addu'a yana bin duk kusurwa ɗakin da tofi bayan ya gama ya kwanta saman bed ɗin tare da jan duvet ya rufe jikinsa, gaba ɗaya ya ƙasa bacci tunda matarsa ta rasu wajan haihuwar Amani baya iya cikakken bacci ya saba da jikin mace sosai duk da auran kamar na dole ne bai so amma ya saba da jikin matarsa ainun. A haka bacci ya ɗauke sa. Misalin 4 na dare ta shiga buɗe idanunta wanda sukai mata nauyi kanta na sarawa sosai, hannunta mai ɗauke da carnoner ta kala ɗan marai-raice fuska tayi kamar wata ƴar baby Wanda ya sanya manyan dimples ɗinsa bala'in lomawa. A hankali kuma ta shiga bin bedroom ɗin da kallo sosai gabanta ya faɗi ganin bata dan ɗakin ba, jiki babu ƙauri ta miƙe tsaye tana Miƙewa gashinta ta sauka har wajan manyan ass ɗinta. Da Mamaki tabi jikinta da kallo ganin wata Robe Nightgown silver wacce ta sauka iya laps ɗinta gaba ɗaya manyan gwayen ƙafafuwanta suna waje ga wani gashi da yay kwance lub a saman fatar ta. Shanyayyun idanunta wanda kullum suke a Lumshe ta ƙara buɗe, jikinta babu ƙwari ta nufi ƙofar data gani, tana tafe ko'ina na jikinta moving yake kamar tarwaɗa. A hankali ta buɗe ƙofar ta fita ita bama ta san dare bane sai da ta fito parlon daga duhu ga wani masifafan sanyi na Kaɗawa, da sauri ta matse jikinta waje guda ta shiga taune bakinta kamar wata ƴar turawa haka ta zama cikin nutsuwa take tafiya harta isa tsakiyar Parlo tana zuwa zata shige taji an sanya mata ƙafa baya tayi tare da hantsilawa zata faɗi wata kuma ƙyakkyawar Ajjiyar zuciya ta sauke jin ta faɗa saman ƙirjin mutum... 😂Abbu ya biyo dare jama'a *TSINTACCIYA* Na kuɗi ne kada ki siyi litaffi na idan kin san zaki fitar🤷🏾‍♀️. NRML GRP: ₦300 VIP: ₦500 POSTING SAFE+YAMMA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK, PLEASE MASU VIP IDAN DA HALI A TURAN TA BANK NA AKWAI P.O.S MA A GARI. EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *FITATTU HUƊU* BAƘAR FATA Autar manya DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower Gaba ɗaya 800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank, masu tura kati kuyi magan ta nan 08167888934, za ku tura Evedance of payment ta nan 08142105218 ƴan uwa na Niger ga number ku +22796515805 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 Http://wa.me/+2348119237616 EPISODE6️⃣ Ƙamshin haɗaɗɗan turarensa ne ya daki hancinta wanda ya sanyata saurin janye shanyayyun idanunta tare mai dasu ta rufe, Wani irin harbawa Zuciyarta keyi tana jin wani matsananci tsoro na shigarta, gata dai male male a jikin mutum amma ta kasa wani ƙwaƙƙwarar motsi bare tayi tunanin zame jikinta. Yana zaune saman kujera 1 seater yana sanye cikin wani tattausan wando 3gauter sai farar singlet wacce ta kama jikinsa sosai ta fito da 6pack na jikinsa idanunsa a lumshe yana sauke numfashi, yayinda gudun da zuciyarsa ya ƙaro fiye da baya, Idanunsa dake a Lumshe ya buɗe a hankali ɗan taune bakinsa yay jin yadda take masa sukur sukur a jiki kamar wata macijiya. Hannunsa ya miƙa ta gefen lafaffan cikinta yana jin yadda take sauke ajjiyar zuciya cup of coffee ɗin sa ya ɗauka, gently kuma yay baya tare da kwanciya a jikin kujerar. A hankali yake spending coffee ɗin a bakinsa ya ɗauki wajan 10minute kafin ya shanye coffee ɗin domin daman ƙa'ida ne sai ya sha Wannan coffee ɗin na Subhi da cikin dare kamar wani buzu ko labarabe. Ajjiye cup ɗin yay cikin nutsuwa kuma ya sanya tafin hannunsa duk biyun tare da zurasu ta tsakiyar hammatar ta caraf ya ɗaga ta tsaye yana yatsuna fuskarsa. Tsaye Akeela tayi kanta a ƙasa, kunya duk ya kamata through ba taga fuskar wanda ta zauna a cinyarsa ba, amma dadɗan ƙamshin parfume ɗinsa ya sanya tasan cewa shi ɗin daban yake ko a cikin maza. Musamman yadda taji Physique chest ɗinsa dake cike da ƙwantaccen gashi lub! lub!!.. A razane ta sauke ajjiyar zuciya tare ƙanƙame Jikinta waje guda, naman jikinta ya wani irin rawa da ɓari dalilin saukar wani masifafan ruwan sanyi da taji tun daga tsakiyar kanta har ƙasan ƙafafuwanta, da alama ma ruwan daga cikin fridge aka ɗauko shi. Idanunta da sukai wani irin juyewa suka ja ta buɗe da niyyar ganin wanda ya zuba mata ruwan. Amma kamar walƙiya tuni Akeem ya haura upstairs babu mai cewa Shine yay punishing ɗin ta da wannan ruwan sanyin domin babu wani sign daya bari a wajan. Abinka da mai ciwon ciki wanda jininta yake double SS tuni jininta yay wani daskarewa, tare da tsaya mata waje guda, a hankali kuma wata ƙwaya ta tsaya a tsakiyar jijiyar ƙafarta tare da lanƙwashewa kamar laushe. Cikin ƙaramin lokaci ƙafarta ta fara wani irin matsanancin ciwo kamar ana sanya gatari ana datsa ɓargo da ƙashin ƙafarta haka ta keji. Tsananin azabar da yay mata yawa ne yasa ko kuka ta kasa sai wani irin fitinannan numfashi da take gumi na yanko mata. A hankali ta sulale tare zubewa a saman carpet ɗin parlon cikin wani irin wahalallan sabon yanayi ta kwanta tare da ɗura ƙafarta a saman kujera ta shiga jujjuya kanta tana sakin wani gigitaccen kuka iya zuci mai bala'in cin rai. Gashi babu Folic acid da paludrine a kusa da ita bare tasha ko taji sauƙin abin. Dukkan hannunta ta sanya a ƙafarta ta riƙe gam "ɗib! ɗib!! ɗib!!" Haka jijiyoyin ƙafarta suke harbawa alamar ciwo yayi ciwo a hankali kuma ciwo ya fara yawo a jikinta daga ƙafa zuwa kwankwasonta bata samu bacci ba sai wajan kiran sallar farko na Subhi. A hankali yake sakkowa daga strains ɗin benen part ɗinsa, yana sanye da Embrodiery Islamic jallabiya white colour, wacce ta kasance mai santsi da taushi tana da half hand daga gaban ƙirjin kuma a ɗan tsage take.. A hankali yake tafiya kamar bai so cikin nutsuwa bakinsa ke motsawa alamar tasbihi yake ga Ubangiji. Hannunsa a goyo da bayansa yana taka ƙafafuwansa dake sanye cikin Mon mule slippers masu kyau.. A tsakiyar parlon ya tsaya idanunsa a rufe babu jimawa Abbu ya fito daga part ɗinsa shima sanye da jallabiya milk irinta Akeem. Babu wanda yay magana a haka suka jera zuwa masallacin dake cikin estate ɗin nasu. Rutse idanunsa yay da tuni su uku ne suke tafiya amma waccan shigiyar Yarinyar mai siffa da aljanun ruwa taja masa a rasa mafi muni a rayuwarsa. Bayan an idar ya zauna zaman azkar ƙarfe 6 dai-dai suka fito daga cikin masjid ɗin zuwa gida. Kai tsaye Akeem kitchen ya nufa yana zuwa ya samu Ummi a ciki sanye da ƙaton hijab har ƙasa, kallonsa tayi tana Murmushi, a sanyaye murya can ƙasa yace. "Sabahul khair Ummina" Mug ɗin hannunta dake cike da coffee ta ajjiye a hankali ta ƙarasu wajansa yana ganinta ya ɗan zube a ƙasan gwiwoyinsa tare da zame wular kansa, hannunta ta ɗura a saman sumar kansa kafin tace. ”Sabahul khair Hero” Murmushi Yay irin Murmushin nan da idan ba ita ba ko Abbu babu mai ganinsa sai Md Adnan. Addu'a ta shiga yi masa kafin gently ya miƙe, ganin yadda take kallonsa yasa ya ɗan kwaɓe fuska yana lumshe idanunsa cikin narkakkiyar murya yace. “Ummi” Hannu tasa ta ja dugun hancinsa tace "Allah ya kyauta maka, ƴarka tayi taɓara kai ma kayi" Shi dai bai ce komai ba, maimakon ya fita daga kitchen ɗin sai yay zamansa akan kujera yay hakanne kuma saboda bai son fita yaga Akeela. Fita Ummi tayi sam bata kula da Akeela ba kai tsaye part ɗinta ta shige. Abbu da ya tsaya da Bala driver yana bashi hqr ne ya shigo cikin parlon kai tsaye kuma idanunsa ya sauka akan Akeela wacce take baccin wahala a saman carpet.. Da sauri ya nufi inda take yana faɗin. "Ya Salam Babyna bacci a Parlo a ƙasan carpet why?" Ya faɗa yana tsugunawa tare da sanya hannunsa gaba ɗaya ya ɗauke ta zuwa jikinsa, Ajjiyar zuciya ya sauke yana ƙara kallon fuskarsa wacce tai jajirr idanunta ya kumbura sosai. Cikin tausayinta da kuma masifafan sonta dake ƙara zautar da Abbu a hankali ya manna bakinsa a saman goshinta tare da sumbatar wajan karaf a idanun Akeem taɓe baki yay da kuma sauri ya juya tare da komawa kitchen ɗin. "Sorry nine ko, sorry Babyn Abbu muje na goyaki kiyi bacci sosai, i promise to you cewa ba zaki kuma kuka ba, I'll be your side kinji Babyn Abbu na" ya faɗa yana ƙara shafa fuskarta tare dayin part ɗin yaransa da ita. http://wa.me/+2348119237616 *_wannan book ɗin na kuɗi ne biya 500 a saki a vip ko kuma 300 a nrml grp_* Abbu na shigewa Akeem ya fito fuska kamar hadari babu walwala baki ɗaya, kai tsaye wani room ya shiga yana shiga ya kunna hasken ciki, ɗakin karatu ne yana shiga wajan kujera yaje ya zauna tare da lumshe idanunsa yana sauke numfashi. Not too long da zamansa a buɗe ƙofar a hankali aka shigo, Amani ce ƙyakkyawar Yarinya mai fuskar Akeem. Washe bakinta tayi da gudu ta nufi wajan Akeem tana faɗin "Hero na" ware gajiyayyun idanunsa yay tare da mai da idanunsa kan Amani kallon da yay mata yasa ta tsaya tare da juyawa da sauri ta fita tana dawowa tace "Salamu Alaika" wani fitinan Murmushi Yay mata yana jin wani sanyi a ransa yace "Wasalamu alaiki Amani Abdul-hakeem Bukar Bello" ya faɗa yana lumshe idanunsa tare da ware mata hannayensa cikin jin daɗi ta faɗa jikin Mahaifin nata tace. "Azunnu annaka bikhair?" Shafa bayanta yay tare da sumbatar goshinta yace. "Lafiya lou and you" Murmushi tayi tana sumbatar goshinsa tace "Ana bikhair" Lumshe idanunsa yay yana ƙara rungome ta a jikinsa yana jin wani so da ƙaunar Yarinyar nasa na shiga zuciyarsa, zameta yay a jikinsa yace "sit" Zama tayi tana kallonsa sosai kamar bazai magana ba sai kuma yace "biya haddarki" a hankali tai rufe idanunta kamar yadda taga yanayi kafin ta fara karanta masa inda yay mata, tana cin karatun ne Afaf da Aleema suka shigo sanye da manyan hijabai, nan da nan walwalar fuskarsa ya ɗauke zubewa sukai bakinsu na rawa suka fara gaida shi. Suna tsaye ko Kallon su bai ba yaci gaba dayiwa Amani karatu. Bayan ya gama ya kallesu har zai magana sai kuma ya fasa. Hadda suka bashi kana ya ɗura masu da karatu. Suna cikin karatun ne Aka buɗe ƙofar Abbu ne ya shigo cikin tashin hankali ganin hakan yasa duk yaran nasa suka kallesa a kiɗime yace. "Dr Saboda Allah ba danni ba kazo ka duba Yarinyar nan she's in critical condition ciwonta ya tashi bana son yay worse da yawa" Shiru Akeem yay tare da ƙara haɗe fuska ganin hakan yasa Abbu faɗin "saboda Allah, saboda matsayina na mahaifi please Abdul-hakeem Bukar Bello" Miƙewa tsaye yay ba tare da yace komai ba ganin hakan yasa Abbu yabi bayansa, Akeem kam ji yake kamar ya zunduma hannu aka yay ihu dan baƙin ciki. A bakin ƙofar ya tsaya Murya a can ciki yace "Kaje Abbu I'll check her" yana faɗin hakan ya buɗe ƙofar ɗakin ya shiga tare da rufewa girgiza kai kawai Abbu yay ya juya. Tana kwance saman bed ɗin sai juyi take domin a yanzu bata iya tantance inda yake mata ciwo a sanadin ruwan da Akeem ya sheƙa mata.. Hannunsa ya harɗe a ƙirjinsa cike kuma da tsanarta ya ƙarasa inda take tsaye yana jin kansa na wani irine sara masa zuciyarsa na harbawa sosai. Ganin bata hayyacinta gaba ɗaya yasa gently ya zaune a gefen gadon tare da sanya hannunsa ya wani irin fincikar ƙafarta wata razananiyyar ƙara ta saka jikinta na kyarma da sauri ta tashi zaune tana cije bakinta tare da yarfar da hannayenta Jikinta sai ɓari Yake gaba ɗaya rigar jikinta ya zame gashinta ya hargitsa sosai.. A karo na farko ya ƙara Kallonta kafin ya daka mata wata gigitacciyyar tsawa ƙarfin tsawar da kuma rashin sabon jinta ga halin ciwo da kuma matsanancin tsoron daya shigi Akeela yasa gaba ɗaya tai wani irin juyi tare da faɗawa jikinsa ta wani irin cusa fuskarta a tsakiyar ƙirjinsa jikinta duk rawa yake domin dam bata saba da kind of this abubuwan ba. Tsaki Akeem yaja yana taune bakinsa kafin a hankali yasa hannunsa yay cilli da ita daga jikinsa, kanta ya daki frame ɗin gadon wani irin runtse idanunta tayi azaba biyu ta haɗe mata. Bayan ya fita daga bedroom ɗin ne Akeela ta fashe da wani irin kuka, gashi ita magana sam bata tsarinta bai dame ta ba, wani irin zafi da ciwo ta keji a ranta, wanne irin mutum ta haɗu da shine? Me tayi masa da har zai dinga cin mutuncin ta har haka? She don't even know him balle tai wani abu na rashin dai-dai amma yana nuna ko ina kula infact ma shine yaja mata wannan masifar na tashin ciwon nata. A yanzu ba ciwon ke sanyata kuka ba, domin idan da ana sabawa da zafi da kuma raɗaɗin ciwo da yaci ace ta saba dashi, amma a kullum idan ya tashi a sabo ta kejinsa, ciwon sikila ya wuce tunanin dukkan mai tunani ko mai haihuwa ba lallai taji azabar da suke ji ba. Kifa kanta tayi a tsakiyar cinyoyinta tana wani irin kuka mai cin zuciya. Akeem na fita derect wani side ya shiga ashe ƙaramin clinic ne, wata injection ya haɗa guda biyu fuskar nan nashi babu walwala sam. A haka ya gama haɗawa ya fito yana fitowa ya tsaya idanunsa akan Didi wacce ta ciko plate da farfesun naman cow head. tsareta yay da idanu domin mamakin naman data kwasa yake amma fuskarsa sam bata bayyana yanayinsa ba, harara ta maka masa tace "to ba sai dai kaci kanka ba, ai dai lalura ce bata shige kan kuwa, jiya jiyan na dakta ya gama gayawa Bukari naci nama na ƙoshi, to wallahi nidai li'ilafi ƙurash kaci kanka nama na kurr aniya bil aniya ato" Girgiza kai kawai yay tare da nufar part ɗin su Aleema. "Ɗan banza fuska kamar karas in sha Allah sai Ubanka yay maka auran dole, masifa sai cin yaro take shi kenan shan lemun tsami" _(shan lemon tsami baya rage sha'awa sai ma amfani da yake wajan inganta Mani, more impormation kiyi attending class ɗin we are all Women wanda zan gabatar da grp na Vip ɗin Tsintacciya 500 kacal)_ Parlo ta koma lokacin Abbu ya fito cikin wata dakakkiyar shampoo dark blue anyi masa ɗinkin jamper da babbar riga. Ya haɗu sai ƙamshi yake zubawa, Didi na ganinsa ta fashe da kuka tana faɗin. "Sai a gaya min cewa bani na haifi Bukari na kawosa duniya ba, da za'a dinga yi min gori a gidan ɗan dana haifa" Kallonta yay yana zama dai-dai nan Mami ta fito cikin wata milk ɗin valisco sai ƙamshi take zama Abbu yay yace "Gori kuma Didi?" Bakin zani ta cire ta face majina tace "A'a to ba dole nace gori ba gashi nan Audil yana cemin kura bani da aiki sai cin nama, kuma dai ai naga lalura ce ko ba gaskiya ba? Babu ruwana fisabilillahi nidai na basshi da Allah bance ka faɗa masa masifar sa ta ƙare masa akai wallahi" Akeem a hankali ya tura ƙofar ɗakin ya shiga tana cure waje guda lokacin su Aleema sun gama shiryawa tuni Drive ya tafi kaisu makaranta su da Amani. A ɗan fakaice ya kalleta dugun gashinta wanda yake zube har saman bed ɗin ya kalla taɓe baki yay aransa yana faɗin "har ƴan ƙauye sun iya ƙarin gashi mtwss" Gently ya ƙarasa inda take zaune tana sauke ajjiyar zuciya har yanzu jikinta ɓari yake. Baya jin zai ɓata lokacin da wajan yiwa Wannan stupid gal ɗin magana yay mata wata iriyar muguwar tsana wacce bai taɓa yiwa kuwa ba. Yana daga tsaye ya ajjiye injection ɗin a gefensa cikin wani ɓacin rai ya sanya hannunsa tare fisgota daga kan gadon har sai da ƙashin ta yay ƙara. Cije bakinta tayi bata son yin wani motsi saboda ciwon da jikinta yake mata, Nightgown ɗin tabi jikinta ta wani manne dukkan Jikinta ana gani ga fure fresh skin ɗinta sai glowing take. Hannunsa ya miƙa dai-dai lokacin daya ɗauko allurar ta buɗe shanyayyun idanunsa wani irin zare ido tayi domin ba'a taɓa yi mata allura ba wata mugun jin tsoran allura take. A sanyaye a hankali kuma ta shiga girgiza kanta har lokacin kuma bata kalli fuskarsa ba, jikinta na rawa ta ɗaga ƙafarta zata gudu da wani saurin ya sanya hannunsa ya fisgota ta zuwa jikinsa.... Free pages sun kusa kammala🤗 kada ki siyi littafi na idan kin san zaki fitar banwa kuwa dole ba please. *TSINTACCIYA* NRML GRP: ₦300 VIP :500 SAFE YAMMA POSTING. 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *🔥FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA Autar manya SULTAN mss flower DATTIJON ARZIƘI Real ladingo Gaba ɗaya 800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman Fidelity Bank, masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218 *AUTHOR NOTE* _muhimman pages da romantic page suna cikin paid Page's kawai wannan matakin labari ne Wannan😁And wanda suka biya NRML GRP wallahi Azeem posting ba kullum ba, today posting tommorow babu😉kada kuce ban faɗa ba, Vip ko kakkaɓe zani za kusha karatu😍🤷🏾‍♀️_ *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 Http://wa.me/+2348119237616 EPISODE7️⃣ Idanunta tayi saurin kullewa tana jin yadda haɗaɗɗan Baccarat rouge (Maison Francis) parfume ɗin sa ya wani daki hancinta, al'amarin daya haddasa mata lumshewar idanunta, jikinta na wani irin rawa domin this is the best time a tsayin rayuwata da wani ya riƙe ta har ya sanyata a jikinsa so close to him, abin sai ya zama wani Extraordinary to her. Ajjiyar zuciya ta sauke a hankali ta ɗaga hannunta da suka sauka a saman ƙirjinsa tana wani motsawa saboda zafi da zugin da ƙafarta ke mata yasa sam ba zata iya jure tsaiwar ba, a hankali ta fara yin ƙasa zata zille naman jikinta na wani irin motsi gaba ɗaya jijiyoyin ƙafarta har bawa suke saboda tsananin ciwo.. A karo na biyu Akeem ya ƙara ware gajiyayyun Maraitattun idanunsa tare da sauke su akan Akeela, wani irin lumshe idanunsa yay yana taune bakinsa ji yake kamar ya shaƙe ta ya wuta dama ganinta baki ɗaya a gidan. Buɗe idanunsa yay yana jan wani mugun tsaki shi dai Abbunsa ya gama dashi, ganin yadda take ƙoƙarin zillewa daga jikinsa ya gently ya gyara tsaiwarsa, tare da ɗaga left hand ɗinsa ya wani manna shi a saman waist ɗinta slowly kuma ya haɗa ta da lafiyayyan jikinsa a hakan yana jin yadda naman jikinta ke rawa na tsananin azaba, cikin nutsuwa kuma ya fara murza Nightgown ɗin dake jikinta da sauri ta buɗe lumshasshun idanunta for the frist time ta sauke idanunta akan kamilalliyar fuskarsa. Wani irin ƙyakƙyawan bugawa Zuciyarta tayi, zata iya cewa bata taɓa ganin Mutum mai mugun kyau kamar Abdul-hakeem Bukar Bello ba, ƙwayar idanunsa kaɗai zata zautar da mace dalilin daya sanya koshi karan kansa ba kowa yake kalla da idanunsa ba, fuskar nan kamar tai tsartuwar jini saboda wani irin fari da yake da shi, ga wani haɗaɗɗan kewayayyan ƙwantaccen sajansa wanda ya taho da sumar kansa ya ke waye fuskarsa dashi da wani gashin baki amma akwai gemu da saje mai ɗaukan hankali. Ga bakinsa kamar na mace Ƙarami laɓɓansa masu kauri jajaye wani yirrrrr dasu very cute and softness. Da sauri ta rufe idanunta domin ba zata iya ci gaba da kallonsa ba wani mugun tsoransa ta keji, laɓɓanta ne suka shiga rawa gaba ɗaya suka jiƙe da yawo a karo na farko ta fisgi kalmar "Uhm..dan Allah kada kayi min zan mutu uhm" ta faɗa tana runtse idanunta sosai bugun Zuciyarta na ƙaruwa. Taɓe bakinsa yay irin ko a jikinsa ɗin nan kima mutu waye yay asara, gumi ne ya shiga tsastsafo mata a tsakiyar goshinta tsakaninta da Allah take gudun allura, jin yaci gaba da murza rigar jikinta yana son fito da ass ɗinta waje yasa ta matse jikinta domin bata taɓa ganin sabon iskanci irin haka ba sai yanzu ko hannu ba'a taɓa riƙe mata ba, da sauri ta sanya tattausan tafin hannunta wanda ya jiƙe da gumi ga wani irin ɗumi da yake da shi ta riƙe hannunsa tana girgiza masa kanta kamar wacce take shirin shiɗewa tace. "Dan Allah banso, kaji...uhm kada ka kalli jikina" Wani zaro idanu waje yay wato saboda jikinta take wannan abin jikinta ɗin banza yay uwar me dashi, village gal like her ma harta san wani ɓoye jiki. Wani cije lips ɗinsa yay yana ƙara haɗata ta da jikinsa domin bai zo nan dan kallan wani part of her body ba, banda ɗoyi Meye ma jikin yake yanzu ma sai yaje yay wanka ysin. Wata Ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya ta sauke tare da ware dukkan hannayenta ta wani zura su ta tsakanin hammatar sa ta wani irin ƙanƙamesa sosai lokacin daya caka mata allurar cike da zallar mugunta. Cije bakinta tayi jikinta na rawa kafin ta wani fashe da maraitaccen kuka mai ratsa zuciya tare da kifa kanta a ƙirjinsa, ba taɓa sanin akwai mugunta irin haka ba, ana faɗin zafin allura bata taɓa sanin haka allura keda mafifaffan zafi ba sai yanzu, ji tayi ta ƙara jin haushinsa bata sanshi ba amma daga jiya zuwa yanzu yay mata abinda ko maƙiyinta ba lallai yay mata shi ba. Ajjiye emtyn injection ɗin yay tare da sauke fuskarsa a tsakanin wuyanta cikin wata kasalalliyyar murya mai ratsa zuciya yace. _“I would rather waltz with the devil of loneliness than tango with a devil like you. I hate you.”_ ya faɗa yana wani jan numfashi tare ƙara sauke kansa a wuyanta cikin wata husky voice idanunsa na wani ruwa ruwa yace. _“Do you know the real meaning of the world Selfish? Take a look into the mirror and you will find out. I hate you_, ke selfish ce kin kashe min ƙani ke gaki nan You still alive kina shaƙar iskar duniya, _You killed my brother_ wallahi na tsane ki bana son ko buɗe idanu na ganki _I hate you.. I hate you, I hate you! You stupid gal witch!!!_ Ya faɗa yana wani cilli da ita tare da hankaɗata baya Allah yasa da bed kusa da ita gaba ɗaya tai bed ɗin ta faɗa saman sa "Auchhhiiii!!" Ta faɗa tana tura ƙaramin bakinta gaba saboda zafin burgewar da tayi, abinda bai sani ba tunda yay mata allurar bacci yay gaba da ita, gyara kwanciya tayi wani nauyayyan bacci ya ɗauke ta. Cike da zallar ɓacin rai yake taka ƙafafuwansa a nan Parlo ya samu Abbu da Ummi da Mami harda Didi wacce bacci ya ɗauke ta a saman carpet bakinta ɗauke da ƙashi tana tsotsa. Kai tsaye upstairs yay yana wani irin fitinannan taku kamar wani ɗawisu, kai tsaye bathroom yay tare da zame jallabiyar jikinsa akan wannan Village girl ɗin yay late a wajan aiki. Wanka yay ya fito ɗaure da towel kafin yay ɗauki handrayer ya fara gyara sumar kansa, lotion mai ƙamshi ya shafa a saman fatarsa kana ya ɗauki body spray ya fesa, nan da nan sumar kansa ta kwanta luff har wuya jan laɓɓan nan suka ƙara yin yirrrrr dasu. Wajan closet ɗinsa ya nufa ya ɗauki Sunset Suit Nevy blue ya sanya kana ya ɗura jacket a sama kafin ya sanya white necktie. Wani half cover shoe ya sanya black kafin ya ɗauki briefcase ɗin sa, wayoyinsa ya ɗauka ya sanya a aljihu gently ya fita daga part ɗin yana tafe yana duba Rolex ɗinsa na Companyn Patek philippe. Lokacin daya fita bai samu kowa ba sai Didi wacce take bacci kai tsaye fita waje yay dai-dai lokacin da P.a ya shigo bai tsaya amsa gaisuwar P.a yau da kansa ya buɗe ƙofa ya shiga back seat ganin hakan yasa P.a yiwa motar key ya fita da gudu. Kai tsaye Audi baƙo way suka nufa inda *AKEEM BETTER FARMING INSTITUTE A.B.F.I* Babban waje ne babba babu mai iya ganin girmansa domin makaranta ce guda ta kuyar da aikin noma, da kuma taimakon mutane, kai tsaye sashin ma'aikata yay tun daga reception aka fara gyarawa ga Hero nan, ga Hero nan hannu kawai yake ɗaga masu har ya isa Elevator yana tsaye kafin ta buɗe ya shiga lift ɗin ya danna 8floor a dai-dai 8floor ɗin ta tsaya ya fito ta office ɗin Md Adnan ya fara shigewa yana wani irin runtse idanunsa sosai. Kafin ya nufi office ɗinsa wanda aka rubuta Ceo haɗaɗɗan office ne mai kyau da tsari domin hadda ƙaramar cineme da deep frizer ga wasu a.c masu kyau. Kujera yaja ya zauna a hankali ya buɗe System ya fara aiki. Ya jima yana dannawa kafin ya ɗauki telephone line ya danna wasu Numbers ɗagawa akai cikin girmamawa akace. "Mun ɗaga kira daga sashin karɓar ƙorafi Tayaya zamu iya taimakawa maka Dr Abdul-hakeem Bukar Bello Ceo? Lumshe idanunsa yay yana sauke numfashi kamar bazai magana ba sai kuma yace "Uhm Something new?" Cikin nutsuwa matar tace "Yes sir! Mun ƙara samun takardar ƙorafi daga Ƙauyen Wudil akan matsalar ƙwace masu gona, zuwa yanzu Mutanan sun fara yi masu ta ƙarfi" Tsayawa yay daga danna keyboard ɗin ɗin tare da sauke hannunsa a fuska yana shafa gemunsa cikin ƙasa da Murya yace. "Uhm! Su waye ne?" "Binciken da mukai ya tabbatar da cewa wasu Manyan shugabannin ƙasa ne suke sun yin kwacan Wannan gonakin domin su kafa wani company kuma an tabbatar da cewa Wannan company na magani za suyi kuma irin haramtattun Drugs ɗin nan masu kashe mutane, suna son yi a Wudil saboda ruwan dake wajan zai hana aji wari da kuma shaƙar hayaƙin maganin" Miƙewa yay tsaye ba tare da yace komai ba ya kashe wayar baki ɗaya. Daga 8floor ya sakko zuwa reception a nan ya samu p.a fita yay daga cikin sashin gaba ɗaya ya nufi ɓangaren koyar da ilimin noman. Tafiya yay mai ɗan nisa kafin yazo ƙarshen wajan wani ƙaton fili ne a ƙalla za'a iya gida sama da ashirin ga wasu ƙanan kurayen ganye sun fara fitowa alamar shukar ta fara huda. ga yara a wajan da manya hadda ƴan primary school, cikin nutsuwa ya zare takalman ƙafarsa tare da naɗe hannun rigarsa cikin gonar ya shiga tare da ɗaukan Adda ya fara yanke ciyawar da tai tsayi ganin hakan yasa gaba ɗaya yaran suka fara yin aikin da yake. *_littafi na paid book ne, 500 for vip 300 for nrml grp idan zaki siya dan ki fitar na yafe😂🤷🏾‍♀️_* Http://wa.me/+2348119237616 A can gida kuwa Didi ce ta fito daga cikin gidan zuwan compound da sauri Bala driver ya ƙarasu tana ganinsa tace "Bala maza buɗe min mota" buɗe bayan motar yayta shiga kafin ya tayar da motar gatekeeper ya buɗe masu da sauri suka fita suna fita motar Abbu na shigowa. A hankali Driven sa yay parking ajjiye jaridar daily trust ɗin hannunsa yay ya fito yana gyara zaman babbar rigarsa kai tsaye cikin babban parlo ya shiga da sauri Amani dake zaune ta riga da wando tana shan chocolate da ice cream ta miƙe tana faɗin "Oyoyo Grandfa" Ɗaukan ta yay yana faɗin "eyee matar mai kama da Hero" Murmushi tai masa kafin yace "how was your school?" Tana sauka jikinsa tace "Allahamdulillah Grandfa" ganin babu kowa a Parlo ya san kuma su Aleema basu dawo ba kai tsaye ya nufi part ɗin yaran nasa yana sakin wani irin Murmushi domin ya azabtu da rashin ganin Akeela sosai. Didi na cikin motar Bala driver yace "Hajiya Didi ina zan kaiki?" Kyaɓe fuska tayi tace "ofishin hisba" jinjina kai yay babu jimawa suka ƙarasa da sauri har tana ƙoƙarin faɗuwa ta shiga ciki tana shiga wajan mutane uku suka miƙe da sauri tace "A'a yaya..nace yaya haka kamar dai ana yaƙi bana son gantali babu ruwana wajan ogan ku nazo" ɗaya daga cikin su yace "Hajiya gani" wani kallo tai masa tace "Malam ogan ku nace yaya zakai min tsaye kamar sandar rake" wani ne yace "shine ogan" haɓa ta riƙe tace "Muhammadur Rasulullah S.a.w a'a babu ruwana akace hisbar malamai ne anya Wannan ya iya fataha ma, Tuf astagafirullah ai karatu kuma dai azuci yake Malam ƙara na kawo" Kallonta yay sosai kafin yace "ok Hajiya tame" fashewa tayi da kuka tace "Ubangiji dai ya haɗani da gantalallan jika abin yay masa yawa ga sata ga maita" Cikin nutsuwa Abbu ya tura ƙofar ɗakin tun daga door way ya fara jiyo sautin shassheƙar kukan ta, da sauri ya rufe ƙofar tare da shiga ciki. Tana zaune tayi wanka sanye take da Black Silk short robe sai wata Halter top data ɗura a sama, ta rufke gashin kan nan nata da ribbon ya sauka har baya sai ƙamshi take, wani irin harbawa zuciyar Abbu tayi kamar wanda ake ja da mayan ƙarfe haka ya nufi inda take ba tare da zato ba Akeela ta jita akan.... Me Abbu yake nufi ne😂😂 na kusa gama free pages tabbas daɗi na neman yi maku yawa. *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 Http://wa.me/+2348119237616 EPISODE8️⃣ Cinyarsa! Wata ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya mai sanyi Abbu ya sauke yana lumshe idanunsa, da sauri Akeela ta ɗaga jiƙaƙƙun eyes lashes ɗinta zuwa sama kafin a hankali ta buɗe idanunta tare da sauke Kallonta a fuskarsa Abbu wacce take dab da tashi. Wani sassanyan Murmushi ya sakar a hankali kuma cikin sakin fuska yace.. "Babyna Daughter na" Ƙuri tayi masa da idanu, saboda kamarsa da Mutumin ɗazo, she's a cleaver gal amma muguwar taɓararriyar mai saurin kuka, ko dan yawan ciwonta ya sanyata kuka ohhhu?! Tana da ilimi sosai musamman na addini bata wasa da sallah sam komai tana da tsari. Murmushi Abbu ya sakar mata yana shafa sumar kanta dai-dai fuskarta yace. "You're wake up Babyn Abbunta how do you feel now? Ya jikin?" Ya faɗa yana manna mata kiss a goshinta a hankali ta zame jikinta daga kan cinyarsa tana ɗan marai-raice fuska kamar zatai kuka da sauri tace "no don't cry kinji" kai ta ɗaga masa tana lumshe idanunta can kuma ta buɗe murya can ƙasa kamar bata son yin magana tace "uhm who are you?" Shafa cikinsa yay kafin ya gyara zamansa tare kama fararan hannunta wanda suke da mugun taushi kamar auduga yace. "Ok let me introduce myself to you" shiru yay yana kallon tana jin wani irin masifafan yanayi a kanta kafin ya numfasa yace. "I'm Abubakar Bello, but some of people knowm me as Bukar, I'm the second born Of my parents, ina da big bro but he's passed away wajan shekaru masu yawa, babban yaya ne shine your father, Isma'il Bello kenan, we lost our father good 30yrs kenan, ina tare da my mother we called her Didi zaki ganta kamar su ɗaya da Aleema, seriously i love her irin sosai ɗin nan more than anything dake nan duniya, bayan ita ina da yara 4 my first son ɗina yafi komai muhimmacin a rayuwarta his name is Abdul-hakeem Bukar Bello zaki iya cewa Yaya, ko hero ko Hamma like yadda Fulani suke faɗa, sai Adnan we lost him shima amma komai ya faru it was a destiny, sa kuma Aleema sai auta Afaf amma yanzu bani da wata Auta sai ke Babyn Abbunta" ya faɗa yana jan hancinta, ɗan Murmushi tayi wanda yasa numfashin Abbu kusan ɗauke wa, domin wannan Shine karo na farko da tayi Murmushi wanda ya haddasa lomawar dimples ɗinta tare da teeths gave ɗinta wacce take siririya sosai, numfashi ya sauke yace. "Ina da mata guda biyu ta farko sunanta Ayusher we called her Ummi, sai Khadijertou muna ce mata Mami, Nayi karatu mai yawan gaske, ni mai kuɗi ne the richer old man, ada nayi siyasa sosai amma yanzu na sauka, yanzu ina business ne ina da Manyan companies a nan 9ja da kuma ƙasashen waje, ina da manyan contact, ƙwangila kala-kala Allahamdulillah ina duba na ƙasa na ina taimako samuna bai tashi a banza ba, and duk da hakan komai na gidan nan Akeem ke yinsa baya using Kwabo nawa tashi yay ya nema duk yawan dukiyarsa shi ya nema da kansa babu sa hannu na, yana da faɗin rai koni sai nayi da gaske nake juya sa dan yana mugun suna ne yana da biyayya yana da ilimin addini fiye da tunanin mutum I'm so proud of him Wannan shine kawai" Kallonsa tayi ba tare da tace komai ba shi dai yaji daɗi yana da kirki amma wannan ɗan nashi bashi da mutunci ko kaɗan, har yanzu ta kasa mance abinda yay mata har yanzu kuma tana jin ƙamshin turarensa a jikinta kamar zai zautar da ita. Bata san mene yasa ba sai kawai ji tayi kuka ya kwace mata, da Sauri Abbu yace "Subuhanallah what happened ina ke maki ciwo" girgiza masa kai tayi tana kwaɓe fuska tare da tura baki gaba "Okey tell me mene ne?" Cikin shassheƙar kuka tace "Baffa na bai so na, he doesn't care about me zai haɗani da wani mai fitsarin ƙwance and ƴarni ɗin nan zaiwa Aure uhm" ta faɗa tana ƙara fashewa da kuka ita tana ganin ai kamar abin kunya ne a gareta mutane suji za'ai mata Aure wata muguwar kunya ta keji kamar me. Bakinsa ya buɗe yace. "No one's forcing you to get you marriage Babyn Abbu Autata Ohyyyah come here" ya faɗa yana jawota jikinsa tare da fara rarrashinta wani sabon sonta ya ratsa mata zuciya. Akeela kam ganinsa take tamkar Baffanta Musamman da taji yace shi ƙanin Baffan tane. Gyara zama Didi tayi tana kallon mutumin tace "Shikenan lashe baki yana tsotse laɓɓansa dan Allah Wannan ai sai ya jamin abin faɗa ko ba haka ba? Mugun hali kuwa bai bar kuwa ba ranar nan balango nace ya siyo min yaƙi to dan Allah ina imani a nan? Taimako nefa abin ma da dukiyar tasa babu san tayaya akai ya rata ta ba, ai ba kayi magana ba ace Hassada bace ba" ta ƙare maganar tana goge hancinta gaba ɗaya mutanan wajan Murmushi suke domin sun fahimci kawai rikicin tsofa ne murmushi mutumin yay kafin yace "In sha Allah Hajiya babba zamu kirasa" da sauri tace "kuce Ubanwa ya faɗa maku a'a babu ruwan ai assurru ma'al sirri koba gaskiya ba, kawai ai faɗa masa ko dan tsire da kaza mai zafi ce yana kawo min" jinjina kai yay yace "to shkknan yadda kikace haka za'ai" tashi tayi Bala driver yana biye da ita a haka suka nufi mota tana shiga ya jata zuwa gida. A wajan 6 na yamma motar Akeem tayi parking a parking space, P.a ne ya fito tare da buɗe masa ƙofa, gently ya fito da ƙafarsa yana wani lumshe idanunsa tare da sauke ajjiyar zuciya a hankali yake motsa bakinsa yana tasbihi a ransa, ya gaji sosai domin rabin aikin a hospital yay ga program ɗin da zai fara a M.hausa channel, a hankali ya wani ya motsa fuska yana cije bakinsa wani siririn tsaki yaja ganin kallon da P.a ke masa dariya p.a yay kafin yace "Sorry sir" banza yay masa yana shigewa cikin gidan, juyawa p.a yay zuwa gida. Lokaci daya shiga Afaf ce a Parlo da Aleema sai Akeela dake kwance saman duguwar sofa tana bacci gashinta duk ya rufe mata fuskarta, ga wani ƙaramin Teyana wide-leg trousers dake jikinta sai Applique logo detail t.shirt jikin nan nata sai glowing yake. Wani series film suke kalla mai suna My perfect husband a zee world. Da sauri Afaf tace "Wlcm Hero" harara ya watsa mata cikin sauri ta ɗauki remote tare da kashe kallon. Ɗauke kai yay ya nufi upstairs, yana shigewa Akeela ta sauke ajjiyar zuciya yana dafe ƙirji dariya Aleema tayi tace "Laa! so you're pretending kenan ai kam zan faɗa masa" kwaɓe fuska tayi tana langwaɓar da kanta gefe alamar "No" ba tare da tace komai ba kuma. Wanka yay ya sauya kaya zuwa Racing jersey da tracksuit trousers, a hankali yake sakkowa daga steps ɗin benen idanunsa a lumshe yunwa ya keji sosai sai baza ƙamshi yake yana tafiya kamar so, kai tsaye kitchen ya nufa domin samun mayen nasa Coffee da ice cream domin ya duba gaba ɗaya ya shanye ice cream part ɗinsa, yana shiga ya rufe ƙofar kitchen ɗin tare da jingina da jikin ƙofar ya harɗe hannayensa a ƙirjinsa. Tana tsaye a kitchen ɗin tana haɗa tea sai zabga madara take a mug ga kyawawan ƙafafuwan ta a waje ƙafarta sanye cikin wani slippers ga laft tummy ɗinta a lafe ya ƙara fidda shape ɗinta, a sanyaye take komai kamar bata so tana gamawa ta ɗauki mug ɗin tana juyawa idanunta ya sauka a kansa tsananin tsoro da gigicewar da tayi yasa gaba ɗaya ta saki mug ɗin cikin rashin Sa'a gaba ɗaya tea ɗin yay masa ka! Nan da nan fuskarsa tai ja idanunsa ya ƙanƙance ya wani haɗe fuska ta mau a hankali kuma ya fara takawa zuwa inda take tsaye.... *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 Http://wa.me/+2348119237616 EPISODE9️⃣ Jikin Akeela na wani irin ɓari tayi baya tare da manne bayanta a jikin canter ɗin kitchen ɗin ta wani matse idanunta, laɓɓanta na wani irin Kaɗawa tana taune su gaba ɗaya ta jiƙasu da yawo, rawar da jikinta yake ya ƙaro. A hankali Akeem yake takuwa zuwa inda take fuskarsa a haɗe tamau babu walwala sai ƙwantaccen sajansa dake ta sheƙi tsaye yay a gabanta yana ƙare mata kallo, ƙara matsawa yay kusa da ita very close to her har tana jin yadda Numfashinsa ke fita ga mayataccen ƙamshin turarensa dake dakar mata hanci. Kamar zai matseta haka ya tsaya a gabanta kafin a hankali ya ɗaga ƙafarsa tare da sauke ta a saman ƙafarta ya wani irin murzawa. Innalillahi wani irin azaba ta ratsa mata jiki har tana jin yadda ƙashin yatsunta yay ƙara baki ta buɗe zata kuka yay saurin sanya hannunsa tare fisgota jikinsa ya haɗata da Physique chest ɗinsa ya matse ta sosai cikin wata lallausar Muryar mai amsa kowa da sanya mutum zullumi da tarin fargaba yace. "Shittt!!! Kul Kimin kuka" wani irin matse idanunta tayi wani kalan tsoran Akeem take kamar mutuwa haka take jin tsoransa komai nasa da banne look what he did to her amma yana cewa kada tayi kuka gashi still ƙara murje yatsun ƙafarta yake. Hannunsa guda ya ɗura akan waist ɗinta ya ƙara holding jikinta a nasa very tight. Ɗaya hannunsa kuma yana kan laɓɓansa daya nuna mata alamar tayi shiru ɗib tai shiru kamar ruwa ya cinyeta amma jikinta yana wani irin vibration, ga wani masifafan ƙamshin turarensa wanda yake sanyata jin bacci zuciyarta na wani irin bugu beating fast fast har Akeem na iya jin yadda ƙirjinta ke ɗagawa, ko da wasa ko baiyi tunanin kallon wajan ba domin babu haka a ransa.. Ƙara murje yatsun yay da sauri ta buɗe idanunta tare da buɗe baki tace "Auchhhiiii wayyooo Baffana" ta faɗa tana girgiza kanta tare da motsawa zata gudu daga jikinsa yadda kake tsoransa zaka ɗauka ma'aikatan ɗaukan rai ta gani. Hannunsa dake saman lip's ɗinsa ya zame tare da sanya hannun ya tallafo haɓarta zuwa wajan fuskarsa fuskar nata yay so cute a hannunsa musamman eyes lashes ɗinta masu mugun tsayi da yawa. Cikin wata husky kamar wanda akai forcing nasa dole yay maganar yace "kee!!" Da sauri ta buɗe idanunta tare da sauke Kallonta a gashin ƙirjinsa dake kwance fuska ya ƙara haɗewa kamar zai fashe yace "look at into my eyes witch" girgiza kanta tayi tana ƙoƙarin sakar masa kuka cikin wata ƙaramar tsawa yace "heeey!!" Muryarta na rawa tana ƙanƙanme jikinta waje guda tace "Am sorry but I can't do this" lumshe idanunsa yay sosai yana jin wani abu mai kama da mugunta na taso masa a hankali kuma ya buɗe idanunsa tare da sakar mata wata gigitacciyyar tsawa haɗi da faɗin "keee" Innalillahi tsawar da tayi mata yawa ne da kuma rashin sabo da tayi da ita haɗi da gigicewar da tayi yasa kawai ta faɗa jikinsa ta wani ƙanƙamesa tana sakin maraitaccen kuka haɗi da faɗin "am sorry ha....ban sakewa Hamma Akeemmm!!" Ta jaa! Sunan nashi ta rufe fuskarta a tsakiyar ƙirjinsa gaba ɗaya jikinta rawa yake sosai. Gaba ɗaya ta firgita da tsawar da yay mata domin tunda take a rayuwa babu wanda ya taɓa yi mata something like this to wama ta sani gaba ɗaya even friends Wannan bata dasu ita ɗaya take rayuwarta ita kam da zama a wajan mutum irin Akeem gwamma ta koma inda ta fito. Sauke numfashi yay tare da jan wata iska zuwa cikin hancinsa, yadda Jikinta ke rawa yasa gaba ɗaya take neman yarda su a ƙasa, taƙi yarda ta buɗe idanunta balle ga kallesa sai tura fuskarta take cikin ƙirjinsa. Wani irin taɓe baki yay kafin yay baya kaɗan tare da jingina da canter cikin wata kasalalliyyar murya can ƙasa yace "Uhm hold me tight kafin na ɓallaki" jin haka yasa ta ƙara tura hannunta in between his hammata tana ƙanƙamesa sosai kamar zata koma cikinsa, ganin yadda ta rungomesa irin rungumar nan ta neman tsira da rai rungumar da babu wanda ya taɓa yi masa ita sai Amani yasa ya wani shafa sumar kansa kamar bazai magana ba sai kuma yace. "Duk abinda nace kice You are" da sauri ta ɗaga masa tana ƙoƙarin zame Jikinta daga nasa yace "don't ever try" dole ta koma tare da kwantar da kanta a ƙirjinsa tana sauke numfashi a wahalarce. Gyara tsaiwarsa yay Muryar nan nashi kamar ana buda algaita yace "witch" bakinta na rawa tace "i am" tsaki yaja yana ƙara murje yatsun ƙafarta yace "pairy, mumu jakaness, emty head" wani runtse idanunta tayi sharrrr kuma hawaye suka zubo mata muryarta na rawa tana son fashewa da kuka tace "i am" shafa lafiyayyiyan gemunsa yay yace "aljanar ruwa, Kidnapper mai cin naman mutane ƴar yankan kai" kuka na kwance mata tace "i am" wani shu'umin Murmushi Yay Wanda ya jima bai irinsa ba kafin yace "Uhmm mai warin hammata" wani raunataccen kuka ta fashe da shi tama kasa magana hannunsa yasa ya zareta daga jikinsa harya juya sai kuma ya dawo ya ɗauki mug ya fara haɗa coffee ko inda take bai ƙara kalla ba, yanzu haka sai yay wanka domin shi da gaske warin take masa sbd rashin tsoran Allah irin na Abdul-hakeem Bukar Bello. Ya gama haɗa coffee ya nufi wajan ƙofa tafiyarsa ma kaɗai abar kallo ce har zai fita sai kuma ya tsaya cikin wata kakkauran murya yace "ki faɗawa wani kiga sai na bawa karnuka sun cinye namanki" yana faɗin hakan ya fita. Zubewa tayi a wajan tana sakin wani sabon kukan gaba ɗaya taji ta fara tsanar zaman gidan saboda shi. Yana fitowa idanunsa ya sauka akan Didi tana zaune saman kujera an ɗura ƙafa ɗaya kan ɗaya tana ganin ta washe baki "kaga irin albarka, kai dai kaji daɗin ka tausayinta kaɗai yasa a soka baka da ƙyashi ko kaɗan shiyasa nace babu wanda zan faɗawa zaka siyo min nama, ato kaf Duniyar nan wa kake dashi mai sonka da sanya maka albarka ai sani ɗin dana zame maka dole na haifi gantalallan Ubanka" banza yay mata yana zaman kan sofa a hankali yake sipping coffee ɗin a bakinsa, Ummi ta fito daga part ɗin Abbu yana biye dashi da alama alwala yay idanunsa ya juya ganin babu Mami yasa ya nufi part ɗin ta. A can cikin bedroom ya sameta zaune ta zabga tagumi idanunta yay jajir a gefenta ya zauna yana Kallonta a hankali itama ta kallesa kafin kuma kuka ya kwance mata bakinsa ya buɗe yace "come here" da sauri ta ƙara jikinsa tana fashewa da kuka sosai, bai hanata ba sai da tayi mai isarta kafin yace "Mami nasan dole kiji zafi domin ke ɗin uwa ce, duk yadda zanji ciwon abin ba kamar ke ba, amma wallahi bana baccin kirki kullum da damuwa nake kwana, ya Adnan yake? Wanne hali yake ciki? Yana raye? Baya raye? No one's know, amma dukkan abinda ya samu bawa rubutacce ne daga Rabbil izzati mai kowa da komai, ko da ba'a ce ruwa ya faɗa ba Tabbas zamu nemesa mu rasa, amma har yanzu jikina yana bani Adnan yana raye koma zai dawo garemu in sha Allah, so kiyi hqr kiyi accepting Wannan destiny ɗin you're muslim a musulmi should trust ƙaddara good or bad ok!" Kallonsa tayi kamar yadda yake kallonta kafin tace "Abbu ina jin babu daɗi ƙwarai rashin ɗa ba ƙaramin abu bane, kullum ina addu'ar Ubangiji ya kare min Adnan aduk inda yake,amma idan na kalli wannan Yarinyar zuciyata zafi take inside of kai punishing ɗinta akan dalilinta muka rasa Adnan amma ka ɗauke ta ka sanyata cikin yaranka me kake expecting idan wani abu ya samu ɗayan su?" Tunda ta fara magana yake kallonta kafin yace "jinina kike son na wulaƙanta Khadijertou? Ɗiyar yayana Baffa zan ci zarafi, ko bayan raina nasan Baffa zai kula da komai na iyali na mene yasa kike son ni naci zarafin tasa ƴar ƙwaya ɗaya tilo? Please bana so ki barni da masifar da take shirin kunno mini please" shiru tayi masa tana sauke ajjiyar zuciya, Miƙewa yay da ita kafin yasa hannu ya share mata hawayen cikin damuwa yace "Ni Ubane kuma mijine mai adalci, amma hakan ba zai sanya naƙi bin abinda zuciyata keso ke muradi ba" da rashin fahimta Mami tace "Me kake muradi Abbu" hancinta yaja yace "time zaizo Ohyyyah go and pray" "bana yi" zare ido yay yana faɗin "eyee baƙin ciki ido biyu Allah ya Bukar Bello ba'a ɗakin Mami yake ba dana shige" ya faɗa yana ficewa. A hankali Akeem ya miƙe kai tsaye suka nufi Masjid suna fita Akeela ta fito da sauri idanunta duk yay jaa sosai ga lip's ɗin nan yay wani pink yirrrrr dashi. Didi ce ta tafka satali tace "Innahu sulaimanu wa Innahu Bismillahi Meye haka kamar wata munafuka kuma jama'a na shiga uku ke zonan" kwasa Akeela tayi da gudu tana nufar part ɗinsu dan Didi ta iya bala'i da surutan tsofa. ABUJA *Aso Rock Presidential Villa* A hankali ya murɗa handle ɗin ƙofar ya shiga cikin wani makeken bedroom kusan dai gidan Shugaban ƙasa wasting time ne tsayawa description nasa just imagine. Tsayawa yay yana ƙare mata kallo kafin a hankali yace "Meema" shiru tayi kanta a ƙasa ta tura hannunta a tsakanin cinyoyinta sai sauke Ajjiyar zuciya take.. Wata macace zatai sa'ar Akeem shekarunta kusan 32 amma idan ka ganta zaka ɗauka bata shige 25 ko 26 ba tana da kyau sosai fara tass da ita gashinta ya sauka sosai.. Ganin yadda tai masa shiru yasa ya girgiza kai tare da faɗin "ohh Rabbi ka kawo min ɗauki" ya faɗa a hankali ya gyara zaman babbar rigar jikinsa babban mutum ne shekara wajan 65 to 67 fari ne kamar Balarabe wajanta ya ƙarasa yana zuwa ta ɗaga kanta a tsoro ce domin kullum cikin firgita take kwaɓe fuska tayi har zatai shiru sai kuma tace "Dad" gashinta ya tattare tsaf kafin ya sanya ribbon ya haɗe mata su yace "oyaa stand up" tashi tayi a hankali har yanzu idanunta a ƙasa yace "Your Mom told me har yanzu baki breakfast ba what exactly wrong with my darling eh?" Kwaɓe fuska tayi kafin tace "Dad how is he?" Dafe kai yay yace "Ya rabbi Wannan mutumin ba kuwa asiri yay maki ba Meema? Mun tsinci Mutum a hospital daga zuwa zaga marasa lafiya kince dole dole a ɗauke shi na ɗauke sa gashi can ana kula dashi amma dole sai an fita dashi waje" kamar zatai kuka tace "Dad why?" Shafa kanta yay yace "come with me" Kallon Mahaifin nata tayi PRESIDENT AHMED ADIL kenan. Kama hannunta yay kai tsaye ratsawa yay ta haɗaɗɗan parlon yarinyar tasa kafin ya nufi wani corridor a nan zaka samu main Parlo iya kar haɗuwa ya haɗu wata mata ce zaune tana kallon Aljazeera zatai shekara 54 tana sanye da wata haɗaɗɗiyar shadda ko'ina na jikinta sheƙi yake ga wasu gold a hannunta murmushi tayi tace. "Ok dake kaine ta kulaka ko yayi" Murmushi Dad yay mata kafin yace "Meema kullum jin kanta take wata ƴar baby look da aure tayi da wajan yara biyu uku har huɗu gareta" dariya Mom tayi tace "aifa" hannunta yaja yace "bari na karata wajan mutumin ɗan yanzu bazan ƙara barinta fita ba" "Adawo Lfy Ur Excellency" fita yay kafin ya shiga Elevator kai tsaye kuma da shiga ya dannawa lift ɗin 1floor, tana kusa dashi sai Ajjiyar zuciya take saukewa a haka suka sauka jama'a kuzo kuga haukan securities sai ku ɗauka yaƙin duniya ake, da sauri aka buɗe masu ƙofar wata lafiyayyiyar mota, kai tsaye wani Aso Rock Clinic Gulps suka nufa motar guards na biye dasu. Sun ɗan jima suna tafiya a cikin gidan kafin su ƙarasa gaba ɗaya guards ɗin sukai masu rumfa Meema dai sai ɓoyewa take domin tsoran mutane take sosai. A haka suka isa wani Dr ya tarɓesu bayan President Ahmad Adil ya zauna ya dubi Dr yace "Yaya jikin nasa?" Ajjiyar zuciya Dr yay kafin yace "To da sauƙi amma he's in critical condition sosai" gaban Meema ne ya faɗi da sauri ta riƙe Dad kafin Dr ya ɗura da faɗin "He lost his memory and fuskarsa ma ta lalace baki ɗaya..... _Ki guji haƙƙin wani domin bala'i ne wallahi sosai fa, idan kina son this book ki siya akan 500 ko nrml grp 300 nidai bazan yafewa dukkan wanda zai karanta bai biya ba haka kukai min akan ABU MALEEK_ *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 Http://wa.me/+2348119237616 EPISODE 1⃣0⃣ Kuka Meema ta sanya wanda ya ƙara tayar da hankalin President Ahmad Adil,cikin damuwa yace "he looses his memory? I understand,but problem ɗin fuskar fa? How long zai kasance cikin rashin sanin wane ne shi?" Kafin Dr yay magana Meema tace "i don't understand Dad,loosing memory kamar ya?" Cikin nutsuwa Dr ɗin ya kalleta kafin yace "everyone forgets things atimes,how often have you misplaced your car keys or forgotten the name of a person you just met,some degree of memory problems as well as a modest decline in other thinking skills,is a fairly common part of ageing,there's a difference,however between nrml changes in memory and memory loss associated with alzheimer's disease and related disorders,and some memory problems are result of treatable condition Madam Meema Ahmed Adil" shiru tayi idanunta yay rau rau zai kawo ruwa kafin a hankali tace "kenan bazai iya tuna waye shi ba? Balle ya tuna abinda ya faru dashi,more explanation please" farin glass ɗinsa ya ɗauka tare da sanyawa cikin nutsuwa yace da Meema "he looses his memory,he can't remember anything about his life,and normal age-related kin gane ba? Memory loose doesn't prevent you from living a full productive life for example,you might occasionally forget a person's name,but recall it later in the day,amma tunawa lokaci guda it's difficult,you might misplace your glasses sometimes,or maybe you need to make lists more often than in the past to remember appointment or tasks. These changes in memory are generally manageable and don't disrupt your ability to work,live independently or maintain a social life" Dr ya ƙare maganar yana sauke numfashi baya jin hausa ko kaɗan hakan yasa dukkan wani bayani da zai yi dole sai dai yay da yaran nasara Ingilishi kenan. Kasa magana Meema tayi bata san mene yasa ba amma wani mugun jin tausayin mutumin take kafin a hankali tace "alright yanzu dole sai the same abinda ya faru da shi ya sake faruwa zai iya tuna waye shi?" Ta faɗa abinda Dr ɗin ya faɗa,jinjina kai yay kafin yace "sure" miƙewa President Ahmad Adil yay yana kama hannun Meema kafin yace "Dr ka shirya komai na tafiyar cikin week ɗin nan za'a fita dashi" ya faɗa yana jan Meema zuwa waje,kallonsa tayi tana kwaɓe fuska kafin tace "Dad" ba tare da ya kalleta ba yace "what again Meema?" Idanunta na kawo ruwa tace "Dad i want see him please! Please Dad" tsayawa yay yana kallonta kafin yace "Look Meema wannan ba age ɗin soyayya dashi bane,infact kin girme masa respect yourself ok?" Ƙasa tayi da idanunta tana jin ranta babu daɗi kafin tace "Dad ni fa ba?" Tsareta yay da idanu kafin yace "kefa mene? Uhm gayan naji" girgiza masa kai tayi kafin tace "nothing" kama hannunta yay tare da shiga cikin mota securities suka rufa masu baya. Can cikin gidansa suka nufa bayan sun ƙarasa Meema ta fito da sauri ba tare data tsaya Dad ɗinta ba,murmushi kawai Dad yay domin hakan da tayi yasan fushi tayi. A bakin shiga lift ya sameta tana ganinsa tai saurin shigewa tana danna 3rd floor,rabuwa yay da ita ya nufi wata daban yana shiga ya danna shima,a parlor ya sameta tana maƙale jikin Mom tana surutai wanda ita kaɗai ta san mene take cewa,kallon juna sukai shi da matarsa kafin Mom tace "yanzu kuka fita lafiya amma ji har abin ya motsa" cike da so da ƙaunar ƴar tashi ya kalli Meema wacce zufa ke yanko mata sai surutu take ita ɗaya murmushi yay kafin ya ƙarasa tare da kama hannunta yace "Allah sarki Mamana,Ubangiji yana sane dake kinji nothing will happened to you again,ina nan kinji i'm always be by your side kinji" ya faɗa yana yin gaba da ita tare da nufar side ɗinta,suna zuwa ya zaunar da ita bakin bed kafin ya fara bin bedroom ɗin da kallo,a hankali ya ɗauki wayarta tare da kunnawa yace "ke ƴar gidan shugaba ce,President's daughter,ya kike son maida kanki middle class ne eh? U have to be classes lady irin manyan matan nan,ni da na keso ki fara fita kina rage min wasu manyan ayyukan tunda kinga ba ni da wanda zai taimake ni ba ni da wani babban ɗa,soon zaki fara fita zuwa wasu Company,wai ke nan sunan babbar likita,a haka zaki zama babbar baƙuwa a wajan taron sickler day ɗin,haaaa! Taɓ su Meema ƴan ƙasa na gari a nan tare dasu I.d card voters card anya kin taɓa voted na Dad ɗinki ma?" Murmushi tayi masa tana ƙwace jakarta bai kulata ba,a hankali ya zauna a gefe ganin wayar nata empty ba komai gata sabuwa dal iphone 13pro max,transfer kati yay mata na 50k kana ya sai mata data cikin sauri ya shiga play store tare dayi mata download na I.G whatsapp,twitter sai wattpad da okoda books tare da games da app na qur'an da azkar,buɗe mata komai yay da wani special name Meema_ President's daughter,wayarsa ya ɗauka tare da yi mata sending na picture ɗinta,ɗora mata shi yay saman profile kana ya bata yana faɗin "yanzu kika fito Mamana,oyah tashi ki fara duba wayanki gashi nan ki yi abinda kike so na tura maki 500k a acct naki" dariya ta masa tace "thank you Dad i love you" Murmushi yay mata yana miƙewa yace "love you too Meema,kinfa girma good 32 to 33 yrs amma abu ya saki gaba kamar yaƙi please ki yita addu'a,ki samu kiyi aure kamar ko wacce mace i don't know what wrong with your mother bata damu ba sam,ina cikin mutane hankalina na kanki ki taya ni kula da kanki,ahha! Ba na son facebook domin zaki iya gani ana zagin Dad ɗinki ranki ya ɓaci,ina yin abinda naga zan iya,amma kin san halin mulki,mai makon jama'a su tayamu da addu'a sai su bimu da zagi,bayan bama da laifi domin na saman su ke take komai,ki kula da kanki akwai guards naki guda ashirin duk inda zaki,make sure tare kuke,ok?" Jin shiru yasa ya juya,ashe tuni bacci ya ɗauke ta shi kaɗai yake abinsa,girgiza kai yay tare da ƙarasawa wajanta ya gyara mata kwanciya,a hankali ya shafa kanta tare da sumbatar goshinta,fita yay yana rufe mata ƙofar bedroom ɗin. Washe gari Dad da wuri ya fita zuwa wajan meeting wanda zai zauna da ƴan majalisu na dokoki wato _(National assembly)_ na ƙasa baki ɗaya,akan lafiya musamman ciwon sikila wanda ya zama kamar Annoba. A hankali Meema ta fito sanye da silhouette da VGOLD palazzo trousers wanda yake da faɗi sosai daga ƙasa kamar skirt daga waist ɗinta kuma ya ɗame ta irin sosai ɗin nan ba zaka taɓa cewa tayi shekaru har 33 ba,tayi rolling kanta da wani haɗaɗɗan vail,a hankali take tafiya kamar wata ɓarauniya tazo dai-dai parlor taji ance "mrng mai satar hanya" ajiyar zuciya ta sauke tare da faɗin "Mom" sai kuma ta juya tana murmushi,zama tayi tace "mrng Mom?" "Mrng how are you? Ina zaki haka ko breakfast baki ba?" Shiru tayi sai kuma tace "kamar nayi ko? A'a banyi ba,kai na yi" girgiza kai Mom tayi tana ajiye system ɗin gabanta,wato al'amarin Meema kullum ɓaci yake kamar da sauƙi sai kuma ta ƙara komawa ruwa "bama ki tabbar kinyi ba kenan ko,eh?" Taɓe baki tayi domin Mom faɗa gareta yanzu zata hargitsa ta,miƙewa tayi ta fice daga cikin gidan baki ɗaya. A can waje kuwa wata mota ta shiga cikin sauri guards suka nufota,da sauri ta ɗaga masu hannu driver yaja da gudu tana faɗin "aso rock clinic gulps za kai dropping nawa" ta faɗi hakan tana buɗe network ɗin wayarta,kai tsaye wattpad ta shiga ta fara dube dube domin tun sanda Dad yay mata settings ɗin komai bata taɓa wayar ba sai yanzu,har ta shige wani book sai kuma ta dawo baya taga ansa _Our secret_ (Sirrin mu) shiga tayi tana zaune ta karanta Episode 1 to 5 lokacin da tazo wajan da Airah ta kewa Sheikh kiss kanta yay wani mahaukacin sarawa a firgice kuma tai wani irin.... Sannu sannu za muje sai wata rana ba zamu dawo ba💃🏻💃🏻ashe haka ake son book ɗin nan? Na kusa kammala free pages bana son zuwa wajan daɗin walle🥲🔥😂 a nuna min soyayya ku siya. Allahamdulillah dai group 2 ya kusa cika na Vip🤷🏾‍♀️ *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 http://wa.me/+2348119237616 Special thanks to *_Hawwa'u My Real Smasher_* EPISODE1️⃣1️⃣-1️⃣2️⃣ Dafe kanta Jikinta ya shiga mahaukacin rawa jijiyoyin kanta suka mimmiƙewa, wasu abubuwa suka fara gilmawa ta cikin idanunta a hankali kuma take lumshe idanunta cikin nutsuwa bakinta yake motsawa a hankali take furta _“Ya hayyu ya ƙayyumu”_ shine kawai abinda yake faɗa drivern ne ya ɗan tsaya da gudun da yake tare da juyawa ya kalli Meema cikin girmamawa da bata matsayinta yace "Madam is everything okay?" Jinjina masa kai kawai tayi a hankali tai baya tana kwanciya a jikin kujerar motar da sauri kuma ta ɗauki wayar ta tura ta cikin hand bag ɗinta. Ganin sauyin yanayinta yasa Driven ya fara da ita a hankali har suka isa clinic ɗin fitowa yay da gansa sosai mamaki ya kamasa ganin bacci take hankalinta kwance babu abinda ya dame ta, ya daɗe tsaye a kanta yama rasa mene zai mata, a hankali ya fara buga kujerar da take kai yana faɗin "Madam! Madam!" Idanunta ta buɗe tana ya motsa fuskarta ba tare data kallesa ba ta fito daga cikin motar kai tsaye cikin haɗaɗɗan Clinic ɗin Wanda Manyan likitoci suke ciki tana shiga Dr dake kula da mutumin ya fito Murmushi Yay mata yace "wlcm Madam Meema Ahmed Adil" Murmushi tayi masa wanda ya sanya yay ƙasa da kansa domin kwarjini gareta sosai ga shirme da manta abubuwa gaba ɗaya kanta bashi da saiti "how can i help you?" Taji Dr ɗin ya faɗa cikin ƙasa da murya tace "please ina son nai magana dakai prvtly firstly kuma ina son ganin sa please kaji?" Jinjina mata kai yay kafin yace "follow me" bayansa tabi tana sakin murmushi a cikin wani haɗaɗɗan room mai masifar kyau ba zaka taɓa cewa mara lafiya bane a ciki waje ya bata ta shige ciki idanunta na kansa, yana kwance flat gaba ɗaya an sanya masa wasu na'ura a jikinsa fuskar nan nashi manne da bandeji kansa ma haka, baƙi ne his Elegant black skin ɗin nan nashi sai ƙyalli yake, babu abu mai haske a Jikinsa irin foot ɗin sa da tafin hannunsa a hankali kuma Numfashinsa ke sauka, he's dark-skinned yet handsome zai iya shekaru 29 to 30 kujera taja ta zauna kusa dashi a hankali ta kama hannunsa idanunta na kawo ruwa cikin ƙasa da Murya tace "you're my brother as frm today, I'll take good care of you kaji babu abinda zai sameka, i love You irin so na ƴan uwa in sha Allah zaka tashi you'll be fine ji nake kamar na sanka tun can baya" Shiru tayi kafin ta ƙara riƙe hannunsa tace "Nima zaka zaka kula dani ko? I'm scared ina jin tsoran mutane, kaga nan nima wai babba ce fa kullum Dad sai yace na zama babba classes lady zaka kuya min komai ai ko? Zaka dinga zuwa mall mall dani da park za muna hira ko?" Ta faɗa hawaye na sakko mata, mamaki ne ya kama Dr domin yaji ana faɗin Meema bata da wani cikakken hankali shiyasa mahaifin nata baya fita da ita amma the she's talking yanzu zaka ɗauka mai cikakken hankali ce Allah Al-hakkamu kenan. Murmushi ta saki jin ya riƙe hannunta dake cikin nasa, juyawa tayi ta kalli Dr hawaye da dariya na kwance mata tace "You see ba? I'm lucky wallahi he loves me I'm so happy" ta faɗa kuka na ƙwance mata kamar wacce ta tuna wani abu kuma ta miƙe tsaye tana kallon Dr kafin tace "let's go" fita yay tana biye dashi a baya har office ɗinsa zama yay kana ta zauna tana faɗin "i need your help Dr but kada Dad yaji please" jinjina mata yay kafin yace "what the you want?" Shiru tayi tana tunani sai kuma tace "Ina son a sawa wannan mara lafiyar fuskar wani" idanunsa ya ware yace "fuskar wa kikeso asa masa to?" Ya faɗa cikin harshen turanci "bani da photon sa amma dai ina da photon a idanuna da zuciyata" Wayarsa ya ɗauka yace "ok bari na kira arteries muga" tana zaune yay waya not too long wani mutum ya shigo ɗauke da kayan drawing ajjiye komai yay a hankali Meema take masa bayanin komai tana faɗa yana zanawa Murmushi tayi tana jin wani mugun daɗi na ratsa Zuciyarta ta sauri Dr ya miƙe tsaye idanunsa akan zanan cikin ɗaga murya yace "wannan ai photon tsuhun ɗan majalisa ne (Members federal house of Representatives) Hon Bukar Bello.. A hankali yake sakkowa daga strains ɗin benen yana sanye da wata ɗanyar shadda fara dal da ita ɗinkin babbar riga da jamper, ya ɗura wata half jaddara a saman sumar kansa wacce tayi kwance lubb da ita, ƙafarsa sanye cikin wani Black half shoe na Gucci mai tsananin kyau. Yana tafe yana maƙala Rolex ɗinsa na A.lange & Sòhne yay wani irin mahaukacin kyau idan kaga Akeem zaka ɗauka wani Balarabe ne fuskarsa tai wani fresh ga wata haiba da zallar nutsuwa fuskar nan babu yabo babu fallasa as usual yana tafe yana lumshe idanunsa tare da motsa bakinsa. Abbu dake downstairs yace "Akeem yau dai ka makara kamar ka manta yau Friday" caraf Didi ta amshe zan can tana faɗin "yoooo Allah na tuba zuciya ce babu alkairi, mugun abu yay masa yawa faɗa yake nema dani saboda an faɗa masa ni sallamammiya ce irinsa to ba'a gantale nake ba, wallahi Bukari ina faɗa maka kaji tsoran ka nemawa ɗan ka magani gani kuke ina wasa amma billahi wannan yaron ba lafiya ce dashi ba" Murmushi Abbu yay yace "Didi kunfi kusa da mijin naki fa" wani zaro ido tayi tace "wa ɗin? To wallahi li'ilafi ƙurash banda a ido aka haifi Audil wallahi da cewa zanyi ba jinin ka bane, saboda tsabar maita ka kalli yadda yake jajir dashi kamar wannan yaron na yama sunan Film ɗin..." Ta faɗa tana kallon Afaf wacce ta fito daga part ɗinsu da sauri Afaf tace "Shuria khana, na Film ɗin maheyk" tafa hannu Didi tayi tace "Yawwa Shimam irin albarka shifa kai Muhammadur Rasulullah s.a.w wlh mugun halinsu ɗaya" A hankali Akeem ya gama sakkowa tsittt wajan ya ɗauka sai muryar Didi ta fara faɗin "Astagafirullah satali saboda Annabi albarkacin juma'a" Murmushi kawai Abbu yay a hankali yay gaba Akeem ya fara masa baya kamar wasu abokai kai tsaye mota suka nufa gaba ɗaya kuma back seat suka shiga driver yaja sun ɗan fara tafiya Abbu ya kalli Akeem yace "Ina son sanya Akeela makaranta what's your opinion?" Taɓe baki yay ba tare da yace komai ba ganin hakan yasa Abbu faɗin "Abdul-hakeem" marai-raice fuska yay kamar zai kuka yace "for God sake Abbu mene nawa ni" da mamaki Abbu yace "Akeem! what wrong with you? Ƴar uwar taka jikinka itace Meye ruwanka cikin lamuranta Are You at of your sense?" Haɗe fuska Akeem yay ba tare da yace komai ba a yanzu haushin yadda Abbu yake son fifita shi da village gal ɗin nan ya keji cikin damuwa Abbu yace "ashe zaka iya wulaƙanta jinin ɗan uwana jinin Baffanka har haka Abdul-hakeem? Akeela is your sister kamar Aleema da Afaf mene yasa kake haka ne?" Ɓata rai yay yana sauke numfashi kafin yace "Abbu ni kawai i hate her ne" wani sassanyan numfashi Abbu ya sauke yana mai jin daɗin hakan a ransa shi kaɗai yasan mene zuciyarsa ke faɗa masa a haka suka ƙarasa babban masallacin juma'a dake nan nasarawa gra. A can gida kuwa su Akeem na fita Akeela ta fito a sanyaye kamar wata munafuka tana sanye da wata haɗaɗɗiyar open abaya blue black ta ɗura wata hula mai gashi a kanta, cikin nutsuwa ta ƙarasa shigowa ciki ganinta yasa Ummi faɗin "Daughter kin fito?" Ƙasa tayi da kanta tana wasa da yatsun hannunta Miƙewa Mami tayi tare da barin main Parlo ɗin gaba ɗaya taɓe baki Didi tayi tace "to ita dai rayuwar guda nawa take? Ban dai gantalewa da son zuciya irin na mutum, idan ka riƙe ɗan wani baka san wazai kula da naka ba fisabilillahi mugun abu ƙarara" Murmushi Ummi tayi tace "have a sit daughter" Afaf ce ta kama hannunta tana faɗin "Ummi wallahi tsoran Hamma Akeem take kamar ranta" taɓe baki Aleema tayi tace "ba dole ba, mutum sai faɗa da miskilanci wallahi gabana har faɗuwa yake idan na jisa kai wallahi munyi missed Hamma Adnan Allah ya dube mu" Ummi dake Miƙewa domin haɗa lunch tace "Za kuyi bayani bari yazo" da sauri Didi tace "Tsila (Akeela) ke dai babu ruwanki da shiga tsabgar wannan mutumin kada kuma ki biyewa su Shimam wallahi shawara nake baki bani da mugun abu ko kaɗan" ita dai Akeela da idanu kawai take kallonsu kafin tai magana taji ƙamshin turarensa da kuma zazzaƙar muryarsa yay sallama cikin parlon Abbu na bayansa da sauri ta kulle idanunta ƙirjinta na wani irin bugawa, babu wanda ya kalla cikin parlon part ɗin Mami ya nufa tana zaune a Parlon ta watching TV Akeem yay sallama Murmushi tayi tace "wlcm Hero" shigowa yay tare da zama saman sofa yana ɗan lumshe idanunsa kafin a hankali yace " Ma'ul khair Mami" Murmushi tayi tace "yawwa yaya aiki?" Yana lumshe idanunsa yace "Allahamdulillah Mami" kafin Mami tayi magana Amani ta shigo tare da faɗawa jikinsa tana faɗin "Abbie na" satar kallon Mami yay yaga basu take kallo ba da sauri ya rungume Amani yana bata peak a goshinta yace "little na" dariya tayi tace "Abbie na kayi kyau kamar new Aunty" ware idanunsa yay irin bai gane ba ɗin nan tace "Abbie Anuty Akeela tana da kyau" haɗe fuska yay yace "لاأريدالشوشرة" (ban son surutu). Shiru tayi masa domin tasan halin Abbien nata miƙewa yay Mami tace "Uba da ƴar duk babu kunya ka daure dai kayi wani Auran a samu more children's" shafa fuskarsa yay tare da ɗaukan Amani ya fita, ita kaɗai ce a parlon duk sun tafi taya Ummi shirya Lunch can nesa da ita ya zauna domin yunwa ya keji shiyasa ba zai iya komawa part ɗinsa ba, buɗe ido tayi a hankali tare da sauke ganinta a kan ƙwantaccen sajansa wanda yay mata masifar kyau bata taɓa ganinsa da manyan kaya ba kenan sai Friday Friday yake sawa? Ta tambaya a ranta, wani irin sahihin kyau yay kamar Balarabe Amani dake jikinsa ta zame tace "Abbie ka ganta tana da dimples irin nawa da naka Allah" Murya can ƙasa dai-dai kunan Amani yace ،أنت" إجلس معتزلا" Wato _Ke! Zauna dai-dai_ jin abinda yace tayi shiru tare da komawa ta zauna tana jan gemunsa. Fitowa Abbu daga part ɗinsa idanunsa akan Akeela ganin Akeem zaune a parlo abinda bai taɓa ba kenan yasa kawai ya nufi dinning room gently Akeem ya miƙe da sauri Amani ta zame hannunta ta nufi wajan Akeela ogan kuwa tunda ya zauna bai kalleta ba, tana jin Ummi na kiranta kasa tashi tayi domin jinta take wani uncontactable a cikin su. Bayan sun kammala yin lunch ɗin Akeem ya haura sama Abbu kamar yay ihu ya keji domin tun safe bai samu damar yin magana da Akeela ba bare yaga ƴar shagwaɓar data saba yi masa. Da daddare bayan sallar Isshā duk suna zaune a parlo iya yaran Aleema, Afaf da kuma Akeela Amani tuni tayi bacci ya jima da shigowa amma gaba ɗaya basu san ya shigo ba hankalinsu na kan film ɗin This is fate da ake na karan da firita, gyaran murya yay yana zuba hannayensa a cikin hannun jallabiyar jikinsa da sauri gaba ɗaya suka juya tare da kallonsa a kusan tare da Afaf da Aleema suka shiga faɗin "lailatan Sa ida" wato barka da dare haɗe fuska Akeem yay cikin wata tsawa yace "duk Shegiyar dana ƙara gani da Wannan kayan uhm" ya faɗa yana duban ƙananun kayan dake jikinsu bakin Aleema na rawa tace "Ayyah Hero banmu ƙara sawa" wata tsawa ya daka mata yace "ku ɓace min da gani" Akeela tafi kuwa firgita jikinta na wani irin ɓari ta miƙe zata gudu da wani irin sauri yasa hannunsa ya riƙe wist ɗinta tare da wani irin juyo da ita ya haɗata da..... 😂 nifa na rasa gane kan bawan Allan nan Akeem what de you nufinka eh? Remain 1 page free pages ya ƙare 🤷🏾‍♀️. *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 _Will Akeem ever fall for Akeela? The way she has fallen for him??_ http://wa.me/+2348119237616 EPISODE1️⃣3️⃣ Jikin bango da sauri kuma ya saketa jin foot steps alamar wani zaizo, kama hannunta yayi ba tare daya kalli fuskarta ba ya fara janta zuwa upstairs Akeela tsoran da yay mata yawa ne yasa ko magana ta kasa, Jikinta ya ɗauki ɓari sanin bata da wani mataimakin sai Allah yasa tabi bayansa babu gardama amma tuni hawaye ya fara bin kyakykyawar fuskarta, Da wani irin ƙarfi cike da Zallar mugunta yake janta zuwa samansa, suna isa bakin ƙofa ya sanya fararan hannunsa masu ɗauke da wasu kwantaccen gashin dogwaye luff dasu, cikin nutsuwa ya murɗa handle ɗin ƙofar tare da turawa tsayawa yay bakin ƙofar still bakinsa na motsawa alamar tasbihi yake, idanunsa ya buɗe sosai tare da saukewa a saman laɓɓanta wanda suke jajirrr dasu sunyi pink yirrrr dasu, da sauri kuma ya ɗauke idanunsa yana taɓe fuskarsa shiga cikin parlon nasa yayi, Akeela kanta a ƙasa ta riƙe bakin buhhh ɗinta wacce ta tsaya mata iya cinyoyinta gaba ɗaya fararan dogayen ƙafafu wanta ana ganinsu, wani ajjiyar zuciya ta sauke tana ƙara ƙamƙame Jikinta bakinta na rawa sosai, ba tare da tunanin komai ba taji ya sanya hannunsa tare da fisgarta zuwa cikin parlon nasa, maida ƙofar yay ya rufe binta yay da kallo from head to toe kafin a hankali ya shige zuwa ciki, Kai tsaye wajan fridge ɗinsa ya nufa a hankali ya durƙusa tare da sanya hannunsa ya buɗe fridge ɗin power horse ya ɗauka tare da ice cream da cake wanda cinsu ya zame masa kamar masifa. Saman doguwar kujera yaje ya zauna tare da zube kayan hannunsa a kan center table, cikin nutsuwa ya sanya hannunsa ya zame jallabiyar jikinsa nan da nan murɗaɗɗan jikinsa ya bayyana, ko ina na jikinsa a murɗe yake Musamman Physique chest ɗinsa ga wasu manyan nonuwa da yake dasu nipples ɗin nan sunyi yirrr dasu, tsakiyar ƙirjinsa duk gashi ne wanda sukai masa kyau matiƙa. Cake ɗin ya ɓare a hankali yay Bismillahi tare da buɗe bakinsa ya sanya, zaƙi da kuma daɗin cake ɗin ya haddasa masa lumshewar idanunsa yana sauke ajjiyar zuciya, baya yay tare da jingina da jikin sofar gently kuma ya miƙa hannunsa ya ɗauki remote ya kunna channel ɗin N.c.c ya fara kallon Labarai gyara zama yay sosai ganin an nuna zaman majalisa wanda ake a babban zauren Majalisar Dinkin Duniya da ke birnin New York a ƙasar Amurka KENA BETANCUR POOL/AFP. Idanunsa ya buɗe sosai ya zubawa zauran idanu wanda ake taron cikinsa wato United Nations. Shugaban zauran Akeem ya kalla mai suna Abdul-ƙhadir Azeem (Chief of Staff) fuskar mutumin babu walwala kana kallonsa kasan ba kirki zai ba, a hankali kuma aka nuno shugaban lafiya wanda yake faɗin. "June 19th was officially designated as World Sickle Cell Awareness Day,The international awareness day is observed annually with the goal to increase public knowledge and an understanding of sickle cell disease, and the challenges experienced by patients and their families and caregivers, kowa ya san cewa wannan rana a ita ake Wannan taron kuma ake tattaunawa da masu ciwon skila tare da family nasu, while mun ware manyan likitoci guda mace ɗaya namiji ɗaya wanda za suyi muhimman bayani akan wannan ciwo na sikila, mutum na farko shine Dr Abdul-hakeem Bukar Bello, sai kuma Dr Meema Ahmed Adil President's daughter, wanda za'ai taron ne a babban asibitin dake Nigeria a garin Kano wata Asibitin Murtala Muhammad, Wannan zaure na United Nations ya ware adadin kuɗaɗen kimanin 100.25m domin taimakawa masu wannan ciwon" shiru yay saboda tafin da aka ɗauka. A hankali Akeela ta buɗe idanunta tare da sauke idanunta akan cineme ta kalli mutumin dake bayani, she's was shock da taji labarin domin kaf Duniyar nan ta ɗauka cewa ita ɗaya kawai take da wannan wahalalliyar ciwon. Samun kanta tayi da son jin ragowar zan can, ana August gashi ance june kenan da sauran lokaci sai wata shekarar ma, cos already time ya shige. A hankali Akeem ya ɗauki ice cream ɗin ya fara sha, a ransa yana ta tunanin Wacece Dr Meema ganin irin wannan sabgar bai damesa ba yasa kawai ya cire tunanin hakan a ransa. Shi ya riga daya mance da itama gaba ɗaya a ɗakin, hakan yasa yaci gaba dayin abinda ya shafe sa, a lokacin kuma tunanin ƙauyen ne a ransu ya ɗauki niyyar a wannan weekend ɗin zai je yaga Meke going. A can downstairs kuwa Abbu ne kwance a bedroom ɗinsa Mami na gefensa tayi shiru tunani fal a ranta, abu biyu ne ya shige mata ga rashin Adnan ga kuma matsalar mijinta, a koda yaushe suka zo kwanciya 5mins yay masa yawa wajan kawowa, tana da ishasshiyyar lafiya a lokacin da shi burinsa ya cika ya samu gamsuwa a lokacin ne ita kuma masifar sha'awar ta zata motsa, ta rasa da waye zatai sharing damuwar ta, ita kaɗai take fuskantar Wannan problems ɗin na rashin gamsuwa ko hadda sauran mata kamar ta. Kuka ta fashe da shi da sauri Abbu ya buɗe idanunsa tare da miƙewa yace "Mami" bata kallesa ba kuma batai shiru ba ganin hakan yasa yace "please dan Allah stop cry Meke damun ki? What happened to you Khadijertou?" Cikin kuka tace "what should i do? Eh? Jina nake kamar zan mutu You older than me, buƙatarka na biya shikenan, You doesn't care about me ya nake I'm ok ko mene, na samu nutsuwa ko yaya? Kullum cikin ciwo nake me kake so nayi eh?" Kallonta yay yama kasa Magana daman yasan wannan zan can ne baki ya buɗe zai magana tace "look! Abbu baka sona is Okey, amma kana son nabi maza ne? Abinda banyi da ƙuruciya ta ba sai yanzu, idan problem ɗin daga nine I'm ready to accept it kuma na gyara na nemi magani, amma zama haka ba zai yiwu ba, I'm so horny bana iya bacci wallahi billahi ni da ace ka raɓeni gwamma na zauna hakan nayi managing kai na hakan nan, amma ace 2mint da kwanciya mutum ya samu gamsuwa ni kuma ko ohhho! wacce kalar azalce haka ta hauni" kuka ta fashe dashi sosai tana riƙe cikinta dake matsananci ciwo zuwa Mararta. Kasa magana yay sai miƙewa yay kawai tare kama hannunta ya jawota tare da bata side hug. Akeelah Hawaye ne ya sakko daga cikin idanunta zuwa saman fuskarta cikin tausayin kanta ta ƙara ware idanunta akan t.v tana jin bayanin da ake, a hankali shugaban lafiyar yace "zamu sakko da wannan taron wanda zamu gabatar soon, saboda yawan mace mace da kuma tarin masu sikila da muke dasu yasa dole a gabatar cikin wata mai kamawa in sha Allah period zamu sanar da mouth, day, time" Jiki a sanyaye ta miƙe a hankali kuma ta zare hular kanta tare da wani irin baza gashin kanta ya sakko har waist ɗinta ta zama kamar wata ƴar India she look like Maheyk. Jikinta yana wani irin Kaɗawa ta ƙanƙame Jikinta waje guda walking slowly ta nufi inda Akeem yake zaune ya shagala da shan ice cream ɗinsa yana danna system ɗinsa hankali kwance ba zato ba tsammani yaji Akeela tayi wani irin.. Dan Allah dan Annabi, dan darajar iyayenki da kimar da suke dashi a wajanki kiji tsoran Allah idan kin siyi littafi na kada ki fitar, kuɗin karantawa kika biya bana mallaka ba, idan taimako kike sonyi zaki iya biya ba ya zama mallakin ki a sakarwa kowa as free ki samu lada😍👏🏻 haƙƙin mutum masifa ne sosai wallahi. *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* FITATTU HUƊU🔥 http://wa.me/+2348119237616 EPISODE1️⃣4️⃣-1️⃣5️⃣ Faɗawa jikinsa tare da sakin wata gigitacciyyar ƙara wacce ta sanya Akeem saurin ware narkakkun idanunsa tare da sauke ganinsa a kanta, wani irin murɗewa jikinta yake tamkar ba mutum ba, ga wani rawa haɗi da kyarma da ɓari da naman jikinta ya shigayi kana ganin Akeela kasan she's not on her right sense, irin something is fishy ɗin nan. Gajiyayyun idanunsa kawai ya sauke akanta yayinda zuciyarsa ta shiga wani irin masifafan harbawa fuskarsa babu walwala ko kaɗan, baƙin ciki da haushin yadda ta faɗa masa jiki yafi masa komai ciwo, cikin ɓacin rai bai ba duba condition ɗin da take ciki ba ya wani irin Miƙewa tsaye da sauri tare da sanya hannunsa ya fisgota haɗi da mannata jikin bangon parlon nasa, idanunsa na wani irin ruwan zallar bala'i ya mannata da jikin bangon tare da sanya hannunsa a wuyanta ya shaƙeta yadda Jikinta ke rawa haka nasa ke rawa, yama kasa magana saboda tsananin ɓacin rai, cikin tsananin ɓacin rai ya buɗe bakinsa cikin wata kakkausar murya yace "you're mad jakaness, jikina sa'anki? Eh? I'll killed you village gal" ya faɗa jijiyoyin kansa sun fito sunyi raɗa raɗa idanunsa yay Wani mahaukacin jaaa gaba ɗaya ya fita a hayyacinsa ba zaka ɗauka mai hankali bane saboda yadda yake huci kamar kumurcin Maciji. Cikin wata iriyar Murya mai tsanani taushi da kuma amsa kowa Akeela ta buɗe bakinta tare da faɗin "mune zaka kashe ko ita? Duk abinda zakai a yanzu mu zakaiwa domin ita ɗin bata da wani laifi mune ne muka ziyarce ka" wani irin kallo yay mata har zuwa lokacin idanunta a lumshe suke suna zubar da ƙwalla, girgiza kai yay yana wani irin taune bakinsa cikin ransa yake faɗin "za'a rina gayyar aljanu kawai" ɗago idanunta yay wanda sukai wani irin bala'in jaaa kafin a hankali Murya babu wasa yace "open your eyes" girgiza masa kai tayi zaka ɗauka tasan abinda ta keyi kafin tace "i can't" cije baki yay yana wani ƙara shaƙe mata wuya cikin ɗaga murya yace "Open your eyes" da sauri itama ta sake girgiza masa kai tace "ban mu iyawa" kafin Akeem yay magana Didi wacce ta shigo tayi saurin faɗin "tsinannu gantalallu, to ubanwa kuka ajjiyewa a Jikinta? Wallahi Ii''ilafi ƙurash, tub! tub! tub! To basai kuci kanku ba Allah kurwarta ɗaci gareta" ta faɗa tana riƙe zani dake neman faɗuwa a hankali Abbu ya shigo sai Mami kana Ummi ta shigo sanye da hijab idanunta akan Akeem kasa magana tayi dan she can't believe ace wai Akeem yayma Akeela haka. Cikin ɓacin rai Abbu yace "Well-done Abdul-hakeem Bukar Bello, Well-done" ya faɗa yana ƙarasawa wajan da sauri Akeem ya saki wuyan Akeela tayi wani luuu zata faɗi cikin zafin nama Abbu ya rungome ta a jikinsa yana ƙara kwantar da ita cike da ɓacin rai a kuma karon farko na rayuwarsa ya kalli Akeem yace "what nonsense! Eh? Kasheta zakai eh Dr nace mekai mata da harta suma haka eh?" Shiru Akeem yay kansa a ƙasa idanunsa a lumshe wani irin baƙin ciki da kuma tarin tsanar Akeela ya ƙara nunkuwa cikin zuciyarsa, a karo na farko na rayuwarsa ta dalilinta a yanzu ta sanya mahaifinsa yana ɗaga masa murya a all his life har kawo yanzu bari wannan bata haɗa shi da Abbu ba amma yanzu da girmansa da komai har ƴar ajjiye akan Wannan yarinyar mai kama da TSINTACCIYA a idanunsa mahaifin zai masa faɗa, Ummi dake tsaye tace "Akeem" a hankali ya ɗaga idanunsa wanda sukai jajirr ya kalleta kamar bazai magana ba sai kuma yace "Ummi..," wata tsawa ta daka mai wacce tunda yake bata taɓa yi masa irinta ba kafin tace "shut up! Akeem this is not how I train you ƴar Uwarka jininka? Eh Akeem? Where is your heart da har zaka sanya hannunka ka shaƙe wuyan yarinya nan, U hate her is your problem amma baka da ikon da zaka sanya hannunka a kanta idan har ba kuskure ta aikata ba, ko dan ciwonta ai ka daga mata haba, bata zo nan daka a wulaƙanta ta ba, baka san Wacece ita ba ko Do you know what gal has been through? Ka ban mamaki baici ace kayiwa jinin Baffa haka ba, da kasan waye Baffa da bakaiwa abinda ya haifa haka ba wallahi zan baka mamaki" Mami wacce ke tsaye ranta duk ya ɓaci domin har cikin ranta take jin faɗan da akewa Akeem wai kuma akan wannan Yarinyar cikin jin haushi tace "haba Ummi it was a mistake wanda kowa nayi kunsan Akeem ba mai shiga sabgar mata bane, inside of ku tambayi dalilin zuwan ta part ɗinsa sai ku hau yaro da faɗa" da sauri Didi tace "A toh! Yau ni naga ruwan masifa ai she daman indo ba ƙaunar yaron nan kike ba? Kai ma da laifinka wallahi idan nace ka kaf faɗin gidan nan nine kawai ke sonka to daman idan bani ba wazai so ka ai nice dolenka" Kai Akeem ya ɗaga tare da kallon Abbu a hankali kuma ya kalli Ummi da sauri kuma ya nufi saman sofa ya ɗauki car key ɗinsa ya nufi fita waje, cikin sauri Ummi tace "Akeem where are you going ina ne zaka nine kayiwa zuciya?" Ko tsayawa bai ba bare ta sanya ran cewa zai dawo, hankalin Abbu ne ya tashi domin yana masifar son Akeem kamar ransa, ya rasa Adnan bazai saken da zai rasa Akeem ba salati Didi ta fasa tace "Huuuu! Jama'a mun shiga uku wanne irin gantalallan Bukari ya samu ne? Anya ba'a sauya maka shi a asibiti ba wannan baƙar zuciya har ina, to wallahi sai dai kaci kanka tass" wani irin Miƙa Akeela tayi a jikin Abbu bakinta na motsawa a hankali kuma tace "Abbu Hamma Akeemmm kada ya fita" da sauri Didi tazo tana dungure mata kai tace "Annamimiyya mai zubin munafukan farko ashe kina ji kikai shiru waike salammiya" yanayin Akeela yasa Ummi saurin cewa "Abbu anya ba mutanan ɓoye bane kuwa?" Kafin Abbu yay magana Akeela ta fasa wata gigitacciyyar ƙara tare da zabura ta nufi waje da gudu, cikin sauri Abbu ya mara mata baya yana faɗin "Akeela! Akeela!!" Ganin yadda take gudun kamar barewa Abbu bai san lokacin da yace "Babyna, Babyn Abbunta Stop" daga Ummi har Mami babu wanda yasan me yake nufi, cikin zafin nama kuma Akeela tai waje gaba ɗaya kasancewar ƙofar a buɗe take saboda ficewar Akeem daga cikin gidan. Kai tsaye gate ta nufa shima yana buɗe gaba ɗaya ta fice daga cikin estate ɗin tana sharara uban gudu, daga ita sai Nightgown gashinta duk a zube tamkar mahaukaciya a haka ta nausa kan titi babu ko slippers. Fitowa Abbu yay zuwa complete ɗin yana faɗin "Bala, Isa, Rabi'u" ya shiga kiran driver da gatekeeper da mai shukar Flowers, amma gaba ɗaya babu ko wanne bacci duk suke, jin shiru yasa Abbu komawa da gudu cikin gidan dai-dai lokacin kuma su Afaf suka fara daga baccin da suka fara domin duk da wuri suke bacci. Car key ya ɗauka ya fito da sauri Mami tace "Ina zaka at this time?" Bai ko kalleta ba ya nufi wajan ɗaya daga cikin motocin sa ya shiga key yay mata ya fita da gudu tare da barin estate ɗin, kuka Didi tace "Bukari ka kawo masifar duniya gidanka" cikin damuwa Ummi tace "Didi Aljanu ne da Yarinyar wallahi kuma sune suka tashi" wani zaro ido waje Didi tayi tace "Muhammadur Rasulullah s.a.w shine ke kuwa kikai min shiru itana da surutu yau na shiga wallahi gidan zan bari" juyawa Mami tayi ta shige ciki Ummi ba haka da gudu Didi tabi bayansu har zaninta na faɗuwa. Akeem kuwa yana fitowa kai tsaye motarsa ya nufa idanunsa a Lumshe ko ganin gabansa ba yayi, wani irin zafi da tafasa zcuiyarsa ke masa, yana shiga motar ya jata da gudu bayan ya danna wani hargitsastsan horn da dauri Isa ya tashi daga baccin da yake ya buɗe masa gate fita yay da motar yana ƙara gudun motar tafiya yay mai nisan gaske har yabar gaba ɗaya cikin Rail way ɗin kafin ya nemi hanya yay parking motar, kansa ya kifa akan string motar yana sauke wani zazzafan numfashi jikinsa duk rawa yake amma har kawo lokacin fuskarsa bata nuna damuwar da yake ciki ba sai idanunsa kawai da suka sauya kala. Akeela kam gudu kawai take tana bin sahun motar Akeem tun tana gudu kaɗan har ta fara mai yawa, kasancewa gudun ba nata bane na Iskane yasa itama ta fice daga cikin Rail way ɗin, Akeem na zaune cikin motar yana sauke numfashi a hankali ya ɗaga kansa dai-dai lokacin da Akeela tazo ta gaban motarsu ta shige, bayanta yabi da kallo yana ganin yadda take gudu tamkar mahaukaciya tun yana iya ganinta har ta ɓace masa da gani, taɓe bakinsa yay a hankali yay baya tare da kwanciya a jikin kujerar motar yana maida numfashi tare da dafe kansa wanda matsanancin harba masa. Duk inda Abbu yake tunanin ganin Akeela ya duba amma babu ita tashin hankalin mara misaltuwa ya sauka akan fuskarsa, yasan Akeem tun inda yake sai kula da kansa Amma Akeela waye ta sani a wannan garin? Musamman Wannan hargitsastsiyar unguwar tasu, jiki babu ƙauri ya koma gida har wayewar gari basu runtsa ba,Didi data rufe idanunta zata buɗe da sauri tana faɗin "Muhammadur Rasulullah s.a.w" washe gari wajan ƙarfe 8 na safe lokacin tuni Abbu ya gama bada cigiyar Akeela both side t.v Redio, a hankali motar Akeem take shigowa cikin estate kai tsaye kuma gate ɗin gidan su ya nufa yana zuwa Isa ya buɗe mata gate ya shiga tun kafin ya fito daga motar cikin ɓacin rai da kuma tashin hankali Abbu ya nufi kan Akeem gadan gadan domin rashin Akeela dai-dai yake da rasa rayuwarsa.... Hhhhh Akeem you're too selfish baka da kirki ko kaɗan😒 *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA* *🌈TSINTACCIYA🌈* NIMCYLUV FITATTU HUƊU🔥 Writer of Abu Maleek Sirrin mu Uncle ne Kwaila ce The new emir Jidda Juyayi Izzar so Moon Lamrat Raino ne sila Ranar Aure na Ƙaddarar mace Ashe ƴar babata ce TSINTACCIYA http://wa.me/+2348119237616 MASU SIYA SUYI MGN👆🏾 EPISODE1️⃣6️⃣-1️⃣7️⃣ Yana zuwa bakin ƙofar ya tsaya yana jiran fitowar Akeem, gently ya buɗe ƙofar ya fito idanunsa a lumshe ga yadda jijiyoyin kansa suke a mimmiƙewa fuskarsa tayi jajirrr da ita alamun har yanzu yana cikin ɓacin rai. Ganin Akeem cikin wannan halin wanda bai taɓa ganinsa a ciki ba yay saurin faɗin "Dr" idanuna da suke a Lumshe ya buɗe tare da sauke ganinsa akan fuskar Abbu,wani irin bugawa zuciyar Abbu tayi saboda wani irin jaaa da idanun Akeem sukai har wani ruwa suke fitarwa. Muryar sa na rawa yace "what... what happened to Akeem?" Lumshe idanunsa yay kana ya buɗe kamar wanda baya son yin magana ya buɗe baki da ƙyar yace "noting" yana faɗin hakan ya nufi shiga cikin gidan da idanu kawai Abbu ya bisa yana mamakin baƙar zuciya irinta Akeem. Girgiza kai kawai yay tare da nufar cikin gidan kai tsaye part ɗinsa ya nufa, Akeem na shiga Amani na ganinsa ta miƙe tana faɗin "Abbie na" bai ko kalli inda take ba sai hannu daya sanya yama ture ta kai tsaye upstairs ya nufa yana dafe kansa yana jin yadda Amani ke kuka amma yau banza da ita, Didi dake zaune tayi saurin faɗin "Au! Yarinya ba sai dai kiyi tayiwa Ubanki istigifari ba, daɗin abin ko kashe ki yay shine ya haifa a toh" Aleema ce ta kama hannunta tana rarrashinta kasancewar weekend ne duk suna gida. Akeem na shiga side ɗinsa rest room ya nufa cire farar jallabiyar jikinsa yay tare da saƙale ta a hanger, fure fresh skin ɗinsa ta bayyana wani irin ƙwantaccen baƙin gashi ne a saman mararsa mai matuƙar ɗaukan hankali jikinsa a sanyaye ya nufi cikin tube tare da shigewa ciki, wani irin sauke numfashi yay a hankali kuma ya ƙara nutsewa cikin ruwan dake cike har bakin tube ɗin, zafin da zuciyarsa ke masa ya sanya gaba ɗaya yama mance a cikin ruwa yake, idan ya tuna irin faɗan da Ummi da Abbu sukai masa sai yaji wani abu ya tsaya masa a ƙirjin, cikin ficewar hayyaci da kuma zallar damuwar dake ransa ya ƙara nutsa kansa cikin ruwan a hankali kuma ruwan ya fara shige masa cikin baki da hanci. A hankali wata baƙar mota mai ƙirar Audi RS5 ta fara shigowa ciki Nasarawa daga farko farkon Nasarawa harya gifta sai kuma ya dawo baya a hankali yana zare baƙin glasses ɗin dake idanunsa, saurayi ne ɗan kimanin shekaru 27 yana sanye da wani farin voyal wanda yay masa kyau sosai kasancewar sa farin bafulatani kana ganinsa Kasan cewar kuɗi sun zauna masa, a hankali yake tafiya da motar zuwa baya kasancewar shike driving ɗin ganin hakan yasa wanda ke kusa dashi yace "Ajmal me kake haka ne?"shiru Ajmal ɗin yay domin baya jin akwai abinda zai iya faɗa, a hankali ya gama tsayar da motar tare da buɗe murfin motar ya fito ganin hakan yasa Karim yay saurin fitowa yana faɗin "wallahi kaifa ba hankali gare ka ba, kana ganin aikin dake gabanmu dole ne a wannan satin mu samu mu shawo hankali duk raguwar jama'ar" ina Ajmal baya gane yaran domin tuni idanunsa suka sauka akan fuskar Akeela dake kwance a ƙasan wata bishiya wallahi wallahi a wannan lokacin duk wanda yaga Akeela dole zuciyarsa ta buga domin ba zaka taɓa cewa ƴar hausawa bace, tana kwance kanta na zubda jini saboda wata muguwar faɗuwa da tayi gaba ɗaya kayan baccin dake jikinta sunyi wani bala'in yin datti gashinta ya wargatse yay ɗai ɗai, tsaye Ajmal yay akan Akeela yana jin zuciyarsa na bugawa, a hankali kuma ya tsuguna a gabanta dai-dai lokacin da Karim yake ƙarasuwa wajan cikin sauri yace "wai Ajmal meke damunka ne? Baka tsoran abin cutarwa ne? Kilama ba mutum bace Aljana ce, ina ka taɓa ganin mace mai gashin wannan?" Banza Ajmal yay masa domin yadda idanunsa suka sauka akan fuskarta yasa baya fahimtar komai dukkan wani abu na kansa sai da ya kunce, hannunsa ya miƙa tare da tattare sumar data rufe mata fuska cikin sauri ya rufe idanunsa yana faɗin "Ohh God" Karim yay saurin faɗin "is she died?" Girgiza masa kai kawai Ajmal yay yana ƙoƙarin sanya hannunsa ya ɗauke ta Abbu dake ƙarasuwa wajan yace "Akeela! Allahamdulillah" Da sauri ya sanya hannunsa ya ɗauke ta tare da kallon Ajmal yace "thank you son, wallahi tun jiya mukai missed nata yanzu na ƙara fitowa ne, kamar daga sama na hangeka ji nai kawai ina son ganin Meke faruwa cikin ikon Allah kuma naga Akeela thank you" jinjina kai kawai Ajmal yay yana shafa wuyansa sosai ya gane Abbu amma shi Abbu sam bai gane waye Ajmal ba, kamar bazai magana ba sai kuma yace "Dad! A nan kuke ne?" Kallon Ajmal Abbu yay yana karantarsa sai kuma yace "eh cikin Railway quarters no 112" idanunsa akan fuskar Akeela yace "ok Thank you" yana faɗin hakan ya nufi cikin motar tare da zama wajan driving ba ganin hakan yasa Karim shima ya shiga cikin motar da gudu Ajmal yaja suka bar wajan, mai makon yaje inda zashi sai kawai ya juya kan motar ya nufi hanyar gida da Mamaki Karim yace "wai Ajmal Meke damun ka ne?" Cikin ɓacin rai Ajmal yace "ban sani ba, banza shege munafuki kawai haba" ya faɗa cikin ɓacin rai yana ƙara sharara gudu. Abbu shima cikin farin ciki ya nufi motarsa bai yadda ya ajjiye ta a back seat ba a nan saman jikinsa ya barta key yaywa motar ya juya zuwa gida tun a hanya ya kira number Ummi da sauri tai picking call ɗin tana faɗin "Something news?" Cikin ƙasa da murya yace "I've seen her Ummi on my way yanzu" Murmushi tayi tace "Allahamdulillah" A wahala Akeem ya ɗago kansa daga cikin ruwan yana sauke wahalallan numfashi a hankali kuma ya buɗe idanunsa da sukai wani mahaukacin ja, ya jima cikin ruwan kafin ya fito ya ɗauki bathrobe ya sanya a jikinsa, ruwa na zuba a jikinsa ya fito kai tsaye ya nufi cikin wani special bedroom ɗinsa Yana zuwa ya rufe ƙofar da key, derect bed ya nufa yana zuwa ya faɗa tare da jan duvet ya rufe jikinsa tass domin wani mugun bacci ya keji, kamar yadda ya saba haka yanzu ma ya jawo pillow ya rungome a tsakanin ƙirjinsa yana sauke numfashi a haka bacci ya ɗauke sa da tunanin yadda zai rama abinda akai masa akan wannan yarinyar. Ummi da Didi ne suka miƙe lokacin da Abbu ya shigo da Akeela a hannunsa, kai tsaye part ɗin su Aleema ya nufa da ita, Ummi na biye da shi Mami ko motsawa ba tayi ba idanunta akan cineme, yana zuwa su Afaf suka miƙe fuskarsu ɗauke da farin ciki, kwantar da ita yay cikin nutsuwa Ummi tace "bari na duba ta" gefe Abbu ya koma yana jin kamar ya kori kowa ya jata jikinsa ya rungome ya lallasheta da kansa amma no way ahlinsa na wajan dole yaja da baya da yaga yana neman zama wani uncontrol sai kawai ya fice daga part ɗin, a hankali Ummi ta zauna idanunta akan Akeela tace "Afaf jeki kawon warm water a bowl with towel" "ok Ummi" bathroom tayi ta shiga haɗa ruwan zafin kana ta fito ɗauke da towel ɗin "drop it and leave and you too Aleema" ficewa duk sukai gently Ummi ta zamewa Akeela rigar jikinta babu ko bra a jikinta cikin tausayin ta Ummi ta shiga goge mata Jikinta da ruwan zafin, sosai ta kasa mata Jikinta ta shafe ta da robe kana ta sauya mata kaya zuwa Sleeve Bodycon mai sauƙin nauyi saboda zafi ake da alama akwai ƙaramin hadari a ƙasa, kwantar da ita tayi ta rufe da duvet gudun a.c ta ƙaro mata ba mai cutarwa, fuskarta tabi da kallo ganin yadda take sauke ajjiyar zuciya a jajjere, fita tayi daga bedroom ɗin a Parlo ta samu su Afaf ɗin suna buga game ficewa tayi daga part ɗin nasu baki ɗaya. Ummi na fita Akeela tai wani irin juyi tare da buɗe idanunta abinda basu sani ba idanunta biyu kawai har yanzu mutanan na kanta ne irin aljanun nan ne masu mugun abu wanda sai ansha wahala kafin suyi magana ma. Parlo Ummi ta dawo kusa da Mami ta zauna ba tare da tace komai ba, a hankali Abbu yake tafiya cikin tafkeken bedroom ɗinsa hannunsa goye a bayansa sai numfashi yake fitarwa, gaba ɗaya yama rasa yaya zai yi baya jin daɗin komai burinsa kawai yaga fuskar Akeela, wani murmushi yay yana jin daɗi domin sai yanzu ya tuna da Ƙofar dake bedroom ɗinsa wacce kai tsaye hanyar tayi har parlon su Aleema, jikinsa na rawa ya buɗe ƙofar tare da fita su Afaf na tsaka da buga game su kaga Abbu kamar daga sama kallonsu yay yace "bari na mata magani" jinjina kai kawai sukai, bedroom ɗinsu ya nufa jikinsa har wani tsuma yake tana zaune ta tura kanta cikin tsakiyar cinyoyinta, ƙarasawa yay tare da faɗin "Babyn Abbunta zo nan gani nazo rarrashin ki" shiru bata motsa ba hakan yasa ya ƙarasa inda take yana zuwa ya jawota jikinsa yana shafa kanta tare da faɗin "Babyna" jajayen idanunta ta ɗaga ta kallesa cikin wata kakkausar murya tace "Abbu Akeem" zuciyar Abbu ce ta buga da ƙarfi cikin damuwa yace "me Akeem zai maki" kuka ta sanya masa ko kuma aljanun suka sanya masa cikin wata iriyar Murya mara daɗin saurara tace "Akeem muke son gani Abbu" sai a lokacin Abbu ya fahimci ba ita take Maganar ba, shafa kanta kawai yay yana faɗin "sorry Babyna kina shan wahala ko? Dana aureki zan bar ƙasar dake" wani irin kallo tayi masa tace "kai ma baka da lafiya Abbu Meye Wannan a jikinka?" Bai tsaye jin zan canta ba ya ɗura bakinsa a kunnanta ya shiga yi mata addu'a, miƙa ta fara yi kafin kuma a hankali jikinta ya saki bacci mai nauyi ya ɗauke ta, Murmushi Yay yace "Babyna zaki sanya zuciyata bugawa idan kina kiran sunan Akeem, Tabbas ni kaɗai zaki so nasan Akeem bai taɓa cewa yana sonki amma yadda kike da mugun kyan nan masu kawo maki hari suna da yawa, ni kawai zaki so zaki zauna dashi, zan koyar dake zallar so da kuma ƙauna ta Akeem kuma duk yadda za'ai a watan nan sai na tura shi Germany zai nesa dake sai yay Shekaru masu yawa lokacin tuni kin zama tawa zai dawo" ya faɗa yana shafa kanta a hankali ya sumbaci goshinta.. *Singapore* Khoo Teck Puat Hospital A hankali motar tai parking Meema ce a gaba sai mahaifinta President Ahmad Adil yana Cikin Wata dakakkiyar shadda dark blue mai kyau sai sheƙi yake, yayinda ita kuma take cikin wata milk ɗin abaya da red ɗin Stones tayi rolling kanta da vail tayi kyau sosai, hannunta riƙe da waya ga wasu manyan guards kai tsaye cikin female sugical world suka nufa shiru asibitin saboda asibiti ne na masu kuɗi babu hayaniya ko kaɗan, cikin sauri Meema ta buɗe ƙofar office ɗin Dr ɗin ba tare dako permission ba, yana zaune yana duba wasu files Meema ta shiga tana faɗin "Dr what happened i saw your miss call" Murmushi yay yace "Na kira na faɗa maki yau za'a buɗe fuskar ƙaninki" wani daɗi taji da sauri ta rungome Dad tace "Dad bana faɗa maka ba" hannunta ya riƙe yace "ok be careful" Miƙewa Dr yay cikin so much respect ya shiga gaisar da Dad kafin yace "follow me" binsa sukai a baya har suka nufi wani room 11 buɗe ƙofar akai Dr na gaba Meema na baya sai Dad, cikin sauri ta zame hannunta ta nufi inda yake a kwance da kayan marasa lafiya Murmushi tayi tana riƙe hannunsa, ɗumin hannunta daya ratsa tafin hannunsa yasa yay sauri riƙe hannunta domin yau gaba ɗaya ba tazo hospital ɗin ba kamar yadda ta saba, kayan aiki Dr ya ɗauko Meema jikinta har rawa yake domin ta matso ta ganshi, cikin nutsuwa Dr ya fara ware masa bandejin fuskarsa yana cirewa, bakinsa ne ya fara bayyana mai ɗauke da jajayen laɓɓa, sai kuma hancinsa a haka har aka gama buɗe masa fuskar, idanunsa a rufe ruff fuskar Abbu kwance a saman nashi fuskar Dr ne yace "Congratulations now open your eyes" slowly ya shiga buɗe idanunsa kai tsaye ya sauke ganinsa akan fuskar Meema babu ko kifta idanu, cikin farin ciki Meema tace "Bro na" shiru yay mata bai ce mata komai ba ganin hakan yasa ta kwaɓe fuska tace "why baya magana?" "Ai sai ya koyi komai ba, kinga aiki ya sameki" Dad kam tunda aka buɗe fuskarsa yaji gabansa ya faɗi sosai ya san me fuskar amma mene haɗin Meema da wannan gske har ta sanya aka sawa wani ita? hannunsa Meema ta kama tace "I'm your sister" cikin kwaikwayon Abinda ta faɗa yace "I'm your sister" wani irin Murmushi Meema tayi tace "A'a ba haka za kace ba" kallon Dad tayi tace "Dad his name please" buɗe baki Abbu yay yace "Asheer" "Wow! Nice name" Meema ta faɗa tana faɗin "as from today sunanka Asheer amma zanna ce maka Bro ni kuma kace Sister" dry Dr yay yace "tab kina nufin a yanzu duk zaki koya masa komai? Mudai nan kafin ku tafi zamu kuya masa wanka,Sallah, cin abinci komai" Asheer kuwa tunda ya ɗura idanunsa akan Meema yaƙi ɗaukewa domin tsoran kallon mutanan wajan ma yake, miƙewa tayi zata ɗauko masa mirror da sauri ya riƙe hannunta yana juya idanunsa, da ƙyar dai ya sake ta lokacin da yaga kansa a madubi kansa ne yay wani irin sarawa da sauri ya saki madubin a ƙasa ji kake tasssss ya fashe a ƙasa cikin sauri kuma cike da tsoran abinda yayi ya ɓoye fuskarsa a bayan Meema.. Today is Monday yau Akeem ya tashi da azumin Litinin da Alhamis kamar yadda ya saba, rabonsa da ganin Akeela wajan sati guda kenan, domin ko zama yanzu ba yayi a Parlo, a hankali ya fito daga motarsa lokacin ana ta kiran sallar magrib kai tsaye pampo ya nufa tare da ɗaura alwala, ko cikin gida bai shiga ba ya nufi cikin masjid ɗin, lokacin daya isa ana jiran zuwan liman amma Shiru ganin an rasa wanda zai ja sallar sai kawai yay gaba tare da tada kabbara, nutsuwa kowa yay a hankali cikin zazzaƙar muryarsa mai daɗin gaske ya fara fidda kira'a yana fidda makarijil huruf, a can gida kuma Akeela na zaune domin ita sosai azumin ya wahalar da ita kuma ta saba tana yinsa ne, idanunta ta buɗe jin sautin Muryarsa ya daki kunanta rabon da taji Muryarsa haka harta mance, Miƙewa tayi saboda wani sanyi da jikinta yay a hankali ta nufi bathroom ta ɗaura alwala kana ta dawo tayi sallah ji tayi jikinta babu daɗi sai kawai ta zame hijab ɗin ta nufi bathroom, cikin sanyin jikinta ta buɗe ƙofar ba tare data rufe ba ta fara kwaɓe kayan jikinta ruwan zafi ta sakarwa kanta tana sauke ajjiyar zuciya. Bayan an idar da sallah Akeem ya fito Abbu na bayansa a haka suka nufi gida babu kowa Parlo duk Sallah suke, part ɗinsa ya nufa Akeem kuma ji yayi yau babu abinda ya keso sama da zuma yasan kuma Didi kawai ke Shanta, part ɗin ta ya nufa a hankali ya shiga lokacin tana Sallah, wani daɗi yaji domin baya son masifar ta a yanzu, fridge ɗinta ya nufa gaba ɗaya robar zumar ya ɗauko Didi kam banda zare ido babu abinda take da taga abin bana wasa bane sai ta fara "ehem! ehem!" Ko Kallonta bai ba ya nufi waje ai da sauri tace "Assalamu alaikum" miƙewa tayi tana faɗin "Muhammadur Rasulullah s.a.w Audil sata ƙiri ƙiri Ubangiji dai yau ya nuna min ɓarawon zumata" jin tana kiran sunansa kuma ya tabbatar part ɗinsa zata bisa cikin rashin makamar yi kawai ya faɗa part ɗin su Aleema ga mamakinsa sai yaji tana faɗin "Munafikin ai na ganka" da sauri ya juya yana duban inda zai ɓoye ganin ƙofar bathroom a buɗe ya wani faɗa ciki da sauri yana murzawa ƙofar key..... *LAST FREE PAGE'S* 😂Akeem daga nan kawai ka ƙarasawa Akeela wanka ina sane na tsaya a nan mai son ci gaba ya biya a nan na kawo ƙarshen *FREE PAGE'S* NA BADA FREE PAGE'S DAGA 1 ZUWA 17 IYA ADALCI NAYI LITTAFIN NAN BABU TSADA NRML GRP 300 VIP 500 SHINE KAWAI, DAN ALLAH IDAN BA SIYA ZAKI BA KADA KIYI MIN MAGANA PLEASE👏🏻. 1. WACECE AKEELA? 2. WACECE MEEMA? 3. IS HE FALL IN LOVE WITH AKEELA? 4. ABBU ZAI AURI AKEELA? 5. MEYE TSAKANIN MEEMA DA ABBU? 6. MENE MAKOMAR LAYAR DA BABA RABI TA SANYAWA AKEELA? 7. ADNAN WANDA YA ZAMA ASHEER ZAI DAWO WA FAMILYN SA? YA BATUN MUTANAN WUDIL DA GONAKIN SU? KUNA GANIN ZA'A IYA HAƊUWA TSAKANIN ASHEER DA AKEEM A WORLD SICKLE CELL AWARENESS DAY? 8. WHO WIN BETWEEN ABBU, AKEEM, ASHEER, AJMAL WAYE ZAI SAMU AKEELA A CIKIN SU??? AKWAI DRAMER AKWAI LOVE UWA UBA ROMANCE BAZAN ƁOYE MAKU BA😂 ADDINI ILIMI BABU WANDA BABU KAWAI KO FARA BIYA KUƊIN KU AYI DAKU🤗. ƳAN NIGER SUYI MIN MGN KAI TSAYE ZAN MUSU BAYANI. *TSINTACCIYA* NRML GRP ₦300 VIP: 500 SAFE YAMMA POSTING 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 *NOTE* NRML GRP POSTING BA KULLUM BA🤷🏾‍♀️ IDAN ZAKI SAI BOOK ƊINA DOMIN KI FITAR NA YAFE NA FAƊA MAKU ZALLAR SOYAYYA NE A WANNAN BOOK ƊIN MAI TSAYAWA A ZUCIYA, VIP MUTANAN AMANA HAJIYOYI POSTING BOTH SAFE YAMMA ZA KUSA KARATU💃🏻NASAN HAR KYAUTAR KUƊI SAI KUNYI MIN. *FITATTU HUƊU🔥* BAƘAR FATA AutaR ManyA DATTIJON ARZIƘI Real ladingo SULTAAN Mss flower gaba ɗaya ₦800 Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu sulaiman fidelity bank masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 zaku tura Evedance of payment a nan 08142105218 *SARAUTAR MARUBUTA*