********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar Bismillah Rahmani Raheem By Khadija (KMU) Page 1&2 Tafiya takeyi a hankali kanta a sama har ta isa inda take saida Awara hada kayan suyar ta tayi wanda daman an riga an kawo mata su tun kafin ta taho nan da nan ta fara soya awarar ta nan da nan ta fara ciniki as usual kafin kace kwabo ta saida awararta ta amshe kudin ta tass Yara uku ta samu tace su daukar mata kayan awarar ta saida yaran sukayi gaba ta biyosu A hankali take tafiya wadda kamar dagan gan take yinta dogayen kalaba ne guda hudu a kanta wanda suka zubo mata har gadon bayanta gashi nan nata bakir kirin earpieces ne a kunnenta tanajin wakar rush by ayra star daidai majalisar su tareeq tazo wucewa zayyad ne yace gafa demoness nan ja’afar ne yayi dariya yace to kaje ku gaisa yace ka rufamin asiri tareeq ne yace bullshit yace meyasa kuke maida kanku baya wai sai yayi shiru zayyad ne ya kwashe da dariya nasan mi kakeson kace miyasa muke tsoronta to ai naga kai baka tsoronta don Allah I dare you to go and confess your love to her right now dan iska inji zayyad shidai ja’afar dariya kawai yakeyi abinshi. Tareeq cikin muguwar hasala ya nufi daidai inda take. Hurriya jin wakarta takeyi hankali kwance da yar karamar wayarta Mai malatsi kallon tareeq tayi da idanunta masu kyau wanda duk bala’in ka baka iya minti daya cikinsu frowning face dinta tayi tana raising brow daya irin miye matsalar ka kasa kallonta yayi kallonshi tayi in a mocking way tace ka fara gadi ne ko kana bina bashi the girl is beautiful not just beautiful but extremely beautiful she’s got this flawless caramel skin that looks like miloo and creamy milk that are put together to give her this perfect and flawless skin idanunta are dark brown which made her look intimidating she’ thin and tall the girl is almost perfect with nothing left for people to criticize sai dai bata kama da Nigerian’s kwata kwata she’s more like an Ethiopian tareeq da banda kallonta ba abinda yakeyi don he can swear wannan yarinya sune hurul tin wato masu kyaun duniya Hurriya ta kalleshi tace hey i’d slap you but that will be animal abuse ta ida maganar da wani tone na raini get lost tace tareeq da daman kamar abinda yake jira kenan yayi sauri ya nufi wurin abokanashi da suna ta kallon drama tasu Hurriya saida tazo ta saitin su ta kallesu tace bunch of idiots sannan ta wuce tayi hanyar gidansu dukansu bayanta suka bi da kallo wanda gashin kanta kawai ke lilo Da yar sallamarta ta shiga gidan da take zama, tabawa bata amsa ba itama Hurriya ko a jikinta ta kusa shiga dakinta kenan taji tabawa nacewa shigar mutum kadai ta isa kasan kowaye mutum a hankali tayi maganar yadda bata tsamanin Hurriya taji abinda tace saidai fa Hurriya Allah ya horeta da ji don kamar giza gizo haka take dawowa Hurriya tayi saida taje saitin tabawa ta zuba mata idanun ta masu masifar kyau saidai ba maisan kallon su saboda abinda suke fiddawa wato flame ta kalli tabawa tace gwara ni nawa a bayyane yake naga taki diyar kuma kullum cikin hijab take Amman sana’ar ta wato saida jiki from this man to another ta amso maku kudi kullum ita ake kallo a matsayin ta kirki nice ta banza Tace and i don’t give a damn because people always think about what they see and believe what they want to believe so I’m at your service shegu masu kan kwarya tana gama maganar ta shige dakinta tabawa da ta hangame baki bude duk inda sabo ma ta saba Amman Abun Hurriya kullum kara karuwa yake Hurriya kam risho ta fiddo ta kunna ta dora ruwa ya mutu ta juye abokiti ta shiga ban dakin su tayi wanka tayi alwala wata hijab ta nemo sannan tayi sallah duk da cewar sallahr bata wani iya ba Sosai ba Amman tana kokar tawa sosai hijab din ta ajiye sannan ta ciro kudin awarar da tayi ta fidda kudin siyyarta sauran kuma na adashe ne da takeyi abinta. Yunwa ta dan dameta don haka ta zari dari biyu ta fito jeans ne a jikinta sai wata yar karamar riga maroon ta fito duk inda ta gifta kallonta ake but she don’t give a damn saida tayi tafiya mai dan nisa sannan taje wani shago ta siyi indomie guda daya ta juya ta koma gida dan risho dinta ta kunna ta dafa indomie din tana gama ci ta kwanta sai bacci domin ta gaji bata samu asuba ba don sai karfe shidda ta samu ta tashi daga baccin tsakar gidansu ta fito ta shiga tayi alwala sannan tayi sallah. Wani blue din wando ne jikinta sai t-shirt Mai zanan zaki fuskar ta fayau sai dogon gashinta da ta nade sosai gidan mai-anguwar su taje hade da sallamarta a tsakar gida iske matar gidan wadda Kamar ita take jira wanke wanke aka fiddo mata ta zauna tayi abinta bayan tagama tayi shara da sauran ayyyukan gidan. Kallonta laminde tayi wadda tagama dafa shayi zata kaima Mai unguwa tace Hurriya angama ne daga mata kai Hurriya tayi wadda ta samu kujera ta zauna tana jin wakarta ,ta saba indai Hurriya ce duk yadda kaso kayi fira da ita bata baka dama abinda ya kawota shi kawai zatayi ta kama gabanta Laminde bayan ta kaima mai unguwa karin kumallo ta zuba ta mika ma Hurriya itama shayi da bredi amsa tayi ta cinye ba tare tace ta gode ba tana kallon Hurriya tagane nufinta don haka ta miko mata dari biyu kudin aikinta sannan ta kama hanya ta tafi gida saman katifar ta haye ta danyi bacci bayan ta tashi daga bacci ta wanke fuskarta sannan ta fita ta bada kudin adashen ta wanda take zubi kullum Tana fitowa daga gidan adashen ta nufi yar karamar kasuwar da take siyen waken suya da murmushi Saminu ya tarbi Hurriya ya gaisheta as usual don duk idan zata zo wurin shi bata taba gaishe shi ba sai ya kasance yana gaisheta da kanshi saboda ko zata kula ta gyara Amman ina idan ya gaisheta zata daga kafada ne taki amsawa yasan batasan dogon bayani tafison duk abinda tazo ayi mata shi lokacin da takeso don haka yace Hurriya bani da wake yau amman ga ashiru can ki siya a wurin shi daga kai Hurriya tayi ta nufi ashiru dake awo kallonshi tayi da idanunta tace a bani wake kallonta yayi sama da kasa sannan yace kindai san kudin waken Hurriya batace mashi komai ba har ya fara zuba waken cewa tayi batasan shi ta nuna mai kyau tace ya zuba mata ashiru kam ya bata fuska yayi banza da ita ya cigaba da zuba wake Hurriya batace mashi kala ba ya miko mata waken bude ledar tayi kamar tana dubawa ashiru yace malama ki bani kudina kina wani leka abu kamar An cuce ki bani san shegantaka idan bakiso ki bani kayana Hurriya batace kala ba daukar ledar waken tayi ta juye mashi abinshi sannan ta sanya tiya ta auni mai kyau ta juye a ledar ta ajiye mashi kudin shi ashiru da mamakin ta ya kamashi daman waye baisan shi a kauyen ba saboda fitinar shi masifarfe ne na bala’i kuma tijarare don haka saitin da Hurriya take tafiya ya tsaya yace yau rashin tarbiya da rashin da’ar kaina tazo karuwa to baki isa ba don wallahi yau sai na cin mutunci ki don ba’a haifi wani a garinan da Zaici man mutunci In kyaleshi ba daga hannu yayi da niyyar marinta Hurriya bata matsa ba kuma batace kala ba saidai flames din idanunta da suke fita a idonta bama gaskiya bane don wani mugun kallo tayi mashi wanda ya sanya dole saida ya aje hannunshi kasa sannan tace I dare you to slap me tayi wani tauna lebenta sannan tace sakarai waye duk garinan bai sanka ba da molesting yaran mutane ba kowa yana tsoron ka saboda rashin mutunci ka and you’re here calling me a whore ko cikin ni dakai waye babban dan iska ta nuna kanta tace ni ko kai sannan tace to idani karuwa ce dakai nayi karuwancin ko kuma da tsoho shiru ashiru yayi sannan ta kara zuba mashi wannan idanun nata tace daga yau na karajin kayi abinda bashi bane sai na kira ma hukuma sun tafi dakai sun bama karensu ya cinye ta ida maganar tana mashi kallon cewar Ina maka gargadi tace sakarai Dan Akuya sannan tayi gaba abinta tabar ashiru da sakin baki da kowa na layin mamakinta yake saboda abinda bai taba faruwa ne ya faru shikanshi ashiru kasa matsawa yayi daga inda yake lallai hausawa sunyi gaskiya yaro baisan wuta ba sai ya taka. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar By Khadija (KMU) Page 2&3 Hurriya tana soya awarar ta mutane nata siye maza a gefenta suna zaune a benci wasu ta zuba masu a plate wasu kuma a leda Ashiru ne yazo inda take saida awarar ya fara surfa ruwan Bala’ da masifa yace yau sai ya kona mata fuskar da take takama da ita cikin garin Hurriya batace mashi cikanka na shikuma ashiru karshen kulewa ya kulu Hurriya mutumin ya cika mata kai da hayaniya yana neman daga mata hankali mazan wurin kowa kallonshi yake da mamaki saboda idan shi ashiru tijara ne to ita demoness ce without any emotion Hurriya da taga abin nashi yaki ya kare ta mike tsaye ludayi ta dauka ta debo mai mai shegen zafi ta watsa mai akafar damar shi sannan ta kalleshi tace kalma daya na karaji daga bakin ka to sai na juye maka man awarar nan duka a munmmunar fuskar ka wawa dakai Ashiru da azaba ta isheshi ihu ya saki yana kallon rashin tsoro a idonta kuma ya tabbatar da cewar zatayi mashi abinda yafi hakan matasan mazan dake wurin dariya kawai suke suna ihu ashiru kam daya rasa mi zaiyi sai ya juya yana dangeshi har ya samu ya bar wurin da take saida awarar Hurriya kam hidimarta ta cigaba don duk ihun da yan maza ke mata bata kalli kowa acikin su ba har ta gama ta amshe kudinta tass Hada kayan da ta soya awararta tayi sannan ta samu yara tace suzo su daukar mata tare suka jera kunnenta da earpiece as usual wakarta takeji ta overloading don yadda take bin wakar kamar ita ta rairata har suka zo kofar gida kallon yaran da suka kawo mata tayi sannan ta zaro goma goma ta basu aiko nan da nan sukai ta tsalle suna ihun murna Hurriya ta shiga gida da yar sallamar ta . Tabawa ko kallon inda take batayi bare ta amsa mata itadai Hurriya d’âge kafada tayi saboda tana kwasar adashenta Zata canza gida mai dan dama dama ta siye yar babbar wayarta da dan kayan abinci sai kayan sawar ta don Hurriya Allah yayi mata son sutura saidai bata da halin sanya expensive kayan Amman dai tana kokar tawa. Tana shiga dakinta ta cire dan wandon da ta sanya ta sanya bomshort sannan ta fito tayi wanka tayi alwala ta shirye cikin wata yar rigar ta half gown ta kabbara sallah da sauri ta gama Cire hijab din tayi ta fito ba karamin kyau tayi ba cikin jar rigar wanda duka dogayen kafafunta a bude suke banda salki babu abinda sukeyi Hurriya yau batajin dora tukunya don haka taje wurin iliya Mai shayi tace ya soya mata kwai guda daya sai ya bata ruwan lipton da biredi mazan dake zaune a wurin dukan su hankalin su na kanta Amman ba wanda ya isa ya tunkareta. Ilya ya bata abinta ta amsa ta kama gaban ta Shidai iliya maganar gaskiya yarinyar na burgeshi don duk garin nan bata daukar raini don ga kyau na fitar hankali gashi ba wanda ya isa ya tunkare ta ga Kuma sai shigar da ta ga dama Amman dai ba wanda ke binta da maganar banza don mafi yawan yan garin nan kusan duk sun bada kansu kuma kullum zaka gansu cikin shigar mutunci amman banda ita shigar banza ce irinta turawa wadda tsantsar turawa keyi Hurriya ta gyara zama sannan ta cinye duk abinda ta siyo tasha ruwa ta wanke hannunta ta dan kishingida kanta saman katifa kafin ta samu a kira sallahr isha’i ta dade tanajin wakar don har isha’i ta gifta bata sani ba saida taji bacci yadan fara figarta sannan ta tashi tayi alwala tazo ta kabarta sallah Kwanciya tayi a hankali bacci ya dauketa. Yau dai ta tashi sallahr asuba tana dadewa bata tashi ba Daidai lokacin asuba don mafi yawan lokuta sai safiya take sallah to yau ta tashi Daidai asubar don har raka’atanul fijr tayi duk da batasan cewar sallahr ta micece ba Amman tasan anayita kafin sallar asuba tana gamawa ta linke hijab ta koma baccin ta Karfe takwas na safe Hurriya taje gidan mai unguwa as usual matar Mai unguwa ta fito mata da kayan wanke wanke sannan tayi shara da sauran ayyuka ta biya ta da kudin aikinta karin kumallon yau a leda tace ta juye matashi idan taje gida sai taci. Hurriya ta zauna tana maida numfashi bayan ta huta kadan ta dauki kwano ta juye taliyar da take da zafi saida ta fita ta daurayo hannun ta sannan ta dawo ta fara ci bintu ce ta shigo dakin Hurriya tana kuka ta kwanta saman katifar Hurriya cin abincin ta cigaba dayi bata tanka ba har saida ta koshi taje ta wanke hannunta,batace ma bintu kala ba don earpieces ta sanya tanajin wakarta Bintu da tagama kukan ta tabbatar ya isheta sannan tayi ma Hurriya magana Hurriya da taga alamun tagama kukan ya sanya ta cire earpiece din ta kalleta Bintu tace Hurriya idan ba zuwa nayi wurin ki ba baki taba zuwa wurin da nike Hurriya tayi shiru bata ce komai ba Bintu tasan daman ba zatace komai din ba murmushi bintu tayi don duk garin nan tafi kowa sanin halin Hurriya tasan cewar Hurriya din tayi kewarta kwana biyu da bata ganta ba Amman tasan cewar baza ta taba tambayar lafiya ba saidai idan Bintu ta fada mata don haka bintu ta rike mata hannu tare da sakin murmushi a hankali Hurriya ta zare mata hannunta ta kalleta irin kallon kinsan banason ana tabani bintu ta turo baki tace kiyi hakuri Bintu ta kalleta tace nidai bazaki kara ganina ba tunda bazaki tambayeni lafiya ba Hurriya ta kalleta sannan tayi shrugging kafadar ta tana kokarin mikewa Bintu da tasan hali tace zauna nagaya maki a hankali Hurriya ta zauna bintu ta kalleta tace lalu ya dawo shekaranjiya da daddare na fito zanzo wurin ki na hadu dashi a zaure a buge yana ganina ya taho yana kokarin rike mani kugu sai na kauce shikuma da yaga haka sai ya chakumo ni daganan muka fara kokowa dashi bugu kadan nayi mashi shine ya fadi kasa nikuma da naga haka na ruga cikin gida na kwanta Shine fa yau sai ta fashe da kuka Hurriya dai tanajin ta don ita bata iya lallashi ba ko kadan saida ta gama kukan sannan ta cigaba da bata labari shine yau larai da lalu suka hau ni da duka wai sai sun kasheni suna ta dukana shine na rugo na taho wurin ki Hurriya bazaka iya gane miye a fuskar ta ba fuskar nan blank koda yake ita duk bala’e baka iya reading emotions dinta don fuskar nan kullum a hade take Muryar ta mai dadi don ba fluent hausa take ba saboda mixed din yaren Ethiopia da English da take dashi ta kalli Bintu tace kinajin yunwa Bintu ta daga mata kai taliyar da ta rage saura ta bata Bintu ta amsa da godiya Hurriya tana kallon yadda take cin taliyar tamkar wadda bata tabacin abinci ba. Bintu bayan tagama cin abincin ta kalli Hurriya da kitson kanta ya Dan fara tsufa tace In kwance maki kitson nan girgiza mata kai tayi alamar Aa Bintu turo baki tayi tace kai Hurriya shiru tayi ba tare da ta tanka ta sannan ta dauki tsinke ta fara kwance kalabar Murmushi Bintu tayi don tasan halin Hurriya na rashin son wani ya taba mata ko yatsa Fira suka fara har ta gama kwancewa ta sharce kan Bintu tace Hurriya kinada gashi damani Hurriya ta yamutsa fuska sannan tace inaso in rage gashin yana damuna Bintu tayi dariya tace don’t even start don ba kyau shrugging Hurriya tayi sannan tace I don’t bloody care Bintu da tasan halinta sai tayi shiru tabar maganar. Tare sukaje kasuwa inda ta saba siyen waken Awara da murmushi mutumin ya tarbesu Bintu itama maida mashi murmushin tayi Hurriya kam ba wani murmushi bare gaisuwa don Bintu sai washe baki take suna gaisawa dagan gan yace kinga murmushi ma sunnah ne a musulunci dariya tayi Mahnoor da tariga tasan da ita yake kwata kwata bata damu ba. Hurriya jam da tagaji da surutunshi cikin zakin muryarta da accent dinta mai dadi tace mashi ya sanya mata waken idan kuma ya cigaba da surutu zata canja wurin siye saboda ita ba magana ya kawota ba she’s here for a business tana kallon tsakiyar idonshi tayi maganar murmushi yayi sannan ya zuba mata waken ta amsa ta kama gabanta. Ashiru kam tunda yazo yake kallonta yana zaginta a ranshi yayi alkawarin bazai taba yafe mataba don lokaci kawai yake jira ya dauki fansar shi Hurriya yau tare suka soya awara itada Bintu banda murmushi ba abinda Bintu takeyi don duk wanda yace abashi awara sai tayi mashi murmushi Hurriya kam ita take soyawa suna gama soyawa suka tattara komai suka tafi gida. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar By Khadija (KMU ) Page 5&6 lokacin da suka dawo anata kiraye kirayen sallah magriba Don Hurriya zaiyi wuya takai bayan magrib a wurin suyar Awara Bintu tayi alwala sannan ta shigo dakin kallon Hurriya dake kwance saman katifar tana jin waka tayi idonta a lumshe suke Bintu ta kalleta tana admiring irin kyaun da Allah yayi mata long lashes dinta da suke kwance kamar tayi fixing dinsu dogon hancin ta sai kuma cynical mouth dinta banda glowing ba abinda fuskar ta take because of her smooth and flawless skin a hankali ta kalli shafefen cikinta wanda kamar bata sanya mashi komai Hurriya is extraordinary beauty duk wanda ya kalleta yasan tana da kyau kuma har ka gama rayuwarka da ita baza ka lura da wani muni nata ba saboda kana kallonta a kullum tana kara maka kyau irinsu ne wanda ake gasar kyau dasu kuma tayi imani da cewar idan daHurriya zata fito gasar kyau ba abinda zai hanata cin wannan gasar irinsu ne za’a iya biyansu ko nawane don su kasance manya manya models irin nasu france da america Everything about her is screaming perfection with nothing left to criticize Sallah Bintu ta kabbara har tagama sallah Hurriya bata matsa konan da can ba Bayan Bintu ta gama addu’a ta kalli Hurriya tace Hurriya ki tashi kiyi sallah lokaci na tafiya Hurriya kam da batajin Mai take cewa don ta kure volume a burin yar garuwarta Bintu kara mata magana tayi shiru tayi Bintu da taga kamar batajin mi take cewa sai ta sanya hannu ta taba ta Aiko kamar an tsunkuli Hurriya din da a firgice ta tashi tana Bintu wani irin mugun kallo ta Hurriya kallon take sosai Bintu kam da tasan yadda Hurriya ta tsani wani ya tabata don tanada tabbacin idan wani ne ya tabata ba ita ba to saukar mari ne kawai zaiji Hurriya tace Bintu don’t ever repeat this mistake again Bintu tace ki tashi kiyi sallah lokaci na wucewa Hurriya ta daga mata kai sannan taje tayi alwala da sauri tayi sallah don Bintu kallon yadda take sallah kawai sannan girgiza ta kai kawai Hurriya ta kalli Bintu sannan tace kina jin yunwa Bintu tace inajin yunwa Hurriya Hurriya daure gashinta tayi saboda wanda tayi taji yana damunta so take tasamu lokaci ta rage gashin don ya kara taruwa da yawa gashi bata san takura tana gama gyaran gashin ta kalli Bintu tace bari na samo manah gari can shagon Bintu tace zan rakaki Tare suka jero suna tafiya su biyu duk inda ta gifta kallonsu ake ba Kamar Hurriya don crop top ce jikinta pink sai wani bakin wando gashin kanta ta da yake a bude sai sheki yake har suka zo shagon da ake saide saide Da murmushi a fuskar shi yace Hurriya mi za’a baku gari tace ya sanya masu na dari sai sugar na hamsin gyadar hamsin Hamza da murmushi yace su Hurriya gari za’a sha wani kallo Hurriya tayi mashi ai sai ya fara to to sannan ya miko garin da suga da gyada Bintu ta amsa sannan tace mun gode Hurriya dai banza tayi dasu dukan su. Suna shigowa suka ga talatu a zaure itada tasi’u hannunshi sanye cikin rigarta tana ta dariya kasa kasa kwata kwata basu lura dasu Hurriya ba da suka shigo don Bintu ba karamin tsorota tayi ba don sauran kadan ta fadi Hurriya kallo daya tayi masu ta dauke kanta tayi gaba har ta sanya kanta taji maganar su kasa kasa tasi’u yace ya za’ayi da yarinyar can ne ni wallahi duk unguwar nan ba wanda yake burgeni Kamar ta yarinya shigar banza kuma Kamar tsohuwar baturiya Amman ace duk unguwar nan gani nan bari ina da burin in lasa wannan yarinya nima tasi’u yace ma talatu dariya tayi sannan tace Hurriya ai karuwa ce ta karshe kawai dai ta iya allonta Ganin Hurriya da tayi a tsaye saida gabanta ya fadi wani irin mugun kallo take mata fuskar nan kwata kwata babu emotion tana a yadda take kamar kullum tasi’u ta kalla cikin ido hannun tasi’u dake cikin rigar talatu ta kalla sannan cikin muryarta mai dadi ta kalleshi sannan tace nima ka sanya hannunka cikin rigata tana kallon tsakiyar idanunshi tsotsar bakinta tayi kadan tace ka sanya hannuka cikin rigata mana Shiru tasi’u yayi yama kasa kallonta duk ya daburce don wani irin kwarjini da tayi mashi kilan saboda kyaunta take da irin wannan kwarjini frowning face dinta tayi in a mocking way tace kai dan akuya ne? Are you mad kallon shi tayi sannan tace kaje ka kalli kanka a madubi sannan tazo saitin talatu kallon cikin idanunta tayi sannan tace miye ma’anar karuwanci shiru tayi talatu tace ina tambayar ki shiru tayi Hurriya tace sana’ar kice keda tabawa and please stop sleeping with young boys masu empty pockets idan zaki kwanta da namiji gwara ki nemi baban tasi’u yadda idan yagama zai baki koda dari biyu ce wadda zaki iya cin tsire wawaye makwadaita. Earpiece dinta ta maida tayi cikin gida abinta kamar batayi komai ba she hate nonsense mutanen yanzu you’v to stand and for yourself ita batama ga dalilin da zaisa mutum ya zageta tayi shiru ba she doesn’t care ko waye kai zata kalli tsabar idonka tayi maka daidai abinda kayi mata Amman dai ba ruwan ta da kowa kawai miskila ce ta karshe and don’t talk behind her back saboda Allah ya bata wani irin ji sosai kilan shine baiwarta Don tana iyajin magana daga nesa Sosai wadda nisanta ya wuce tunani Amman cikin ikon Allah zataji lokacin da bata ma iya hausar ba Sosai don ko magana taso ta fada ma mutum marar dadi to ba lallai yaji mi take cewa ba saboda she’s using British and Amacharic Amman yanzu idan ta yanko maka magana kamar daman asalin yaren hausan takeji don duk kalmomi mararsa dadi ta iya amfani dasu. Bintu kam har ta jika masu garin tanata jiran Hurriya din tazo domin susha suyi sallah su kwanta Bintu ta kalli Hurriya tace ina kika tsaya ahankali tace waje tasan bata cika san magana ba don ta tsani unnecessary zance don haka Bintu taja Bakinta tayi shiru Tare suka sha garin don ita Hurriya a hankali take sha don har tagama shanye nata Hurriya bata shanye ba tanajin waka tana kada kanta Bintu murmushi tayi sannan ta fita ta wanke kofin tayo alwala sannan ta kabbara isha’i tana gama sallah tana lazimi saiga sallama Hurriya idonta lumshe Amman duk abinda Bintu suke cewa tanajin su Bintu ta kalli Hurriya tace Hurriya na tafi baba ya dawo yace a kirani tana goge dan hawayen da ya zubo mata Hurriya tayi shiru kamar bataji mai Bintu take cewa ba sannan Bintu ta fita tana dan gyara ma Hurriya labule. Bintu na isowa kofar gida gabanta ya fadi don batasan mi zata tarar ba a gidan a hankali tasa kanta a soron Gidan tana tafiya kamar munafuka lalu da suka shirya abunsu da larai daman yasan dole zata dawo gida shiyasa ya tsaya zaure ya tarbeta saboda ya lalubi rabonshi Daidai inda take yazo yana wani munafukin dariya yace wa naka ma matsowa ya farayi tana matsawa baya yana Dariyar har saida ya kawota karshen bango riketa yayi gam yana dariya yellowing hakoranshi suna bayyana kugunta yarike yana kokarin sanya mata hannu cikin riga tureshi tayi yayi baya ya kalleta sannan yace ni zaki ture to yau Mai rabani dake sai Allah kugunta ya rike aiko suka fara kokowa karfinta ne ya fara karewa sosai Hurriya da take kallon ikon Allah zuwa tayi daidai inda yake ta dauke lalu da mari a harzuqe ya dago da niyyar sauke ma kowaye ya mareshi ruwan tijara saidai da kyar ya iya hadiya maganar shi da kuma yawun dake bakinshi kallonta yakeyi da yar crop top din da ko cibi bata rufe mata ba sai bakin wandon dake jikinta gashin kanta kam ba’a daure ba tunda lalu yake bai taba ganin halitta mai kyan mahnoor ba saidai kyawawan idanunta da Allah ya basu matukar kwarjini Hurriya ta janye bintu daga wurin lalu tana mashi wani irin banza kallo da kyawawan idanunta cikin muryarta mai dadi da tace duk randa na karajin wani Abu makamancin haka ya faru sai kaji a jikin ka sakarai mai karamar kwakwalwa Bintu kallon Hurriya tayi sannan tace nagode Hurriya kam baka iya karantar yanayinta don ta kwarai wurin shutting emotions dinta Tare suka shiga inda suka tarar abbanta na kwasar tuwo larai na kusa dashi Larai na lura da shigowar su ta saki wani munafukin murmushi Abbanta da ya kula dasu aiko zumbur ya taso da hannunshi duk miya zai mari Hurriya cikin sauri ta rike hannunshi tana rikewa ta saki don kamar ta rike kashi tana kallonshi Abba da ya harzuka yace daman kina wurin wannan shedaniyar marar tarbiya marar addini. Hurriya a kalleshi sannan tace babban shedani ya wuce bayanka wanda har zai tsallake kafa ya tafi gantali ba tare da tunanin halin da diyarshi zata fada ba a hannun kishiyar uwa bakasan mi taci ba bakasan mi tasha ba baka san wazai lalat maka diya ba kallon Larai da tabata fuska tana kallonta tayi sannan tace koda yake ba abin mamaki bane tunda duka jikin ka daure yake da asiri. Rashin addinina da Rashin tarbiyata duka dauka nayi a wurin wanda baisan hakkin diyarshi ba ido cikin ido tace sakarai wawa mijin tace Bintu da take kallon komai tasan a haka Hurriya na ganin mutuncinta tasan idan tayi wani abun ba zataji dadi ba. Hurriya ta kalli Bintu sannan tace ai baki jin yunwa ko Bintu ta daga mata kai tace muje dakinki Hurriya na gaba Bintu na baya har suka zo dakin kallonta tayi mata da ido ta shiga kuka take shirin yi Hurriya ta nuna mata alama da tai shiru. Abba da Larai kam sunsan halin shegiyar Hurriya ldinan da ta zame masu karfen kafa a cikin garin nan don bata da mutunci Hurriya tazo ta kallesu sannan tace idan har naji ko harar Bintu kunyi to zan kira maku hukuma ta kada kai ta bar gidan lalu da yake boye yana kallon su duka ya fito yana kallon Larai yace wacece wannan Larai ta kalleshi tace fitacciyar marar kunya kenan don haka duk abinda tace to ba mamaki zata iya aikata shi. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar By Khadija (KMU) Page 7&8 Gida Hurriya ta koma tana shiga ta kwanta a katifar tana tunani bata gama tunanin ba bacci ya dauketa sai karfe bakwai ta tashi ruwa ta dan kashe sannan ta juyeshi cikin bucket tayi wanka kanta ta fara wankewa sannan wanka tayi alwala saida ta sanya gashin kanta saitin fan ya bushe tukunna scissors ta duba inda take ajewa bata gani ba dubawa tayi sosai bata gani ba tsoki tayi ta gyara gashinta ta daureshi kawai don taso ta yankeshi saboda gashin ya fara yi mata yawa wani dan karamin box ta fiddo can cikin kayanta ahankali ta bude tana kallon sarkoki guda biyu masu masifar kyau Rufe box din tayi ta maida sannan ta fiddo wani jeans blue ne sosai Amman yanada dan fadi kasan shi sai tsagar dake a cinyoyin wandon da gwiwar wandon shiryawa tayi cikin wando ta sanya bakar riga yau kawai taji tanason ta sanya dan kwali don haka ta zaro wani blue and black vintage scarf ta daura ma kanta saida tagama shiryawa tsaff sannan ta dan murza dan oil turaren ta mai saukin kudi Saida tagama komai sannan ta kabbara sallahr asuba don har takwas da mintuna tayi da sauri tagama komai ta nufi gidan mai anguwa . Tadan makara yau wurin aiki tana shiga laminde tace kina raina Hurriya yanzu nike da niyyar daman In sanya a Duba ki ko lafiya Hurriya ta share tambayar da tayi mata tace ina kayan murmushi laminde tayi ta fiddo mata kayan yau cikin sauri take komai saboda yau zata kwashi adashenta kuma tanaso ta siye kaya saida ta tabbatar tagama komai don ko laminde ko Bankwana batayi ma laminde ba ta fito Hurriya kam saida taje gida ta fiddo asusunta har ta maida wurin maida asusun ne wani dan box 📦 ya fado a hankali ta bude tana kallon sarkoki guda biyu da banda kyalkyali ba abinda sukeyi maidawa take kokarinyi kawai sai a ranta tace bari ta sanya it’s been a long time a hankali ta warware sarka guda daya wadda plain ce kawai Amman gold ne a sarkar ta sanya Kallon dayar sarkar take wadda kamar diamond ce Amman stone din anyi mashi carve da H Maidawa tayi a box din sannan ta sanya shi a aljihun wandonta Emotions din da taji ya fara taso mata ne ya sanya kawai ta cire kudin asusun wanda suka kama dubu takwas ta tafi gidan Asabe wadda ta kasance uwar zubin adashen Hurriya ba sallama ta shiga gidan a tsakar gida ta iske asabe tana shan rake Asabe saidai ganin mutum tayi a kanta don ta tsoro ta matuka Hurriya ta kalla daga sama har kasa tace Nagode ma Allah kece cikin gidanan namu da ace bake bace da sai anjimu dake yau Hurriya kallon Asabe tayi fuskar ta babu alamun murmushi ko daya tace nazo kwashe kudina Dariya Asabe tayi sannan tace oh kece fa kwasar karshe kusan kowa yasan halinki shiyasa duk angama maki zubin adashen ki tun kafin ma kizo ta ida maganar da dariya hurriya batace mata kala ba saidai ta jawo kujerar dake kusa da Asabe ta zauna Asabe tace kinga bari na dauko maki kudin ki labule asabe ta daga ta shiga daki sai gata tafito da yar lalitar tsaff ta kirga ma Hurriya dubu sha biyar da dari takwas tace ga kudin ki kece daman zaki ida zubin yau shine zai kama dubu sha shida kenan Hurriya amsar kudinta tayi daman hannu biyu tayi zubin na wata biyu kenan kuma itace kwasar karshe ta hada da dubu takwas din da ta fiddo daga asusun ta wanda suka kama dubu ashirin da uku Amsar abunta tayi ba tare da tace ta gode ba asabe har zata wuce asabe tace yawwa Hurriya ga fa irin kayan da kike sawa gwanjo ki duba Hurriya alama tayi mata da ta miko cike da murna asabe ta shiga daki don tasan indai Hurriya ce sai ta siye kayan kusan dubu biyar indai tanason Abu zata siya gashi ita bata taya kaya duk yanda aka batasu saye takeyi Kulli guda asabe ta fitoda kayan tana nuna ma Hurriya murmushi tayi tare da bude kayan tace kalla Hurriya kallon da Hurriya take ma kayan kawai zai tabbatar maka da cewar sun burgeta a hankali ta fara zabar kayan masu kyau har kusan kala goma sai hula kala uku Asabe ce ta kalleta sannan tace Hurriya gafa wata jalabiya zatayi maki kyau ki hada da ita Hurriya kallon jalabiyar tayi sannan tace ta sanya mata da murmushi asabe ta sanya hada wani dan kwali Mai silbi sai hijab Mahnoor kallonta tayi sannan tace nawa ne duka kudin kayan Asabe ta gyara tsayuwa sannan tace dubu shida Hurriya ba tare da bata lokaci ba ta kirgo dubu shida ta bama asabe Asabe kam dadi kamar ya kasheta daman tasan Hurriya bata da bakin ciki indai tanason Abu zata siya à yadda ka batashi leda ta dauko ta kwashe ma Hurriya kayan sai zuba kam godiya take da addu’a Hurriya bata bi takanta ba ta fito daga gidan ta nufi gidan mai unguwa cikin aljihun wandonta ta sanya kudin tabo aljihun tayi kawai sai taji dan karamin box dinta tsoki tayi ta maida kudin a dayan aljihunta Da isowar ta kofar gidan mai unguwa taga kofar gidan cike da motoci fararen bus ne na hias masu kyau ga yara da iyayen yara shake a wurin A hankali Hurriya ta kutsa kai gidan mai anguwa samudawan dogarai ta gani sai mazurai suke da idanu frowning face dinta tayi ganin su da wasu uniform ga kuma rawani daure a kansu hango laminde da Hurriya tayi ne ya sanyata kutsa kai har inda take ganin ta , Duka wurin kallonta suke ba tare da ko kyaftawa laminde kam kallonta take tana mata alama da ta fita Amman Hurriya ba tare da ta kula kallon da ake mata ba ta iso har inda take fuskar ta sai fidda wani irin kyau take Amman kwata kwata babu murmushi ko sauki a fuskar ta laminde ta kalla sannan tace namanta ban amshi kudin aikina ba laminde tace oh oh bari na dauko maki Mai unguwa kallon Hurriya yayi cike da tausayinta saboda ya tabbata baza ta koma gida ba yau don kallon da dogarawan kadai ke mata ya isa ya baka amsa laminde ta fito da Dari biyu ta bata tana kallon ledar hannunta da kuma wuyanta gaban laminde ne ya fadi ganin sarkar gold din da ta fito baro baro a wuyanta tasan zalincin dake masarautar Qamar don haka a hankali tazo saitin Hurriya gabanta na faduwa saboda kada wani ya lura da abinda zatayi itadai Allah ya Sani tana kaunar Hurriya har cikin ranta duk da ita bata nuna wata alamar girmamawa amman a haka take kaunarta a hankali tazo ta gyara mata wuyan riga tare da zurma sarkar cikin riga Hurriya kam wani irin kallo take mata murmushi laminde tayi sannan tace kada ki yadda wadanan dogarawan suga sarkar dake awuyan ki a hankali tayi mata magana yadda ko mai unguwa da yake nesa dasu bazai iya ji ba ki kula da kanki Hurriya . Hurriya a daga kai tayi tana rike da ledar kayan ta ta doshi hanyar fita wata tsawa aka daka mata Daidai ta kai kofar akace ke yar matsiyaciya ina zaki Hurriya cigaba tayi da tafiyar ta wata tsawa ce aka kara daka mata ke kaskantarciyar karuwa ina zaki Hurriya bata taka ba kuma bata juya ba tsaye tayi tana jiran isowar ko waye da yake mata tsawa har haka don tun lokacin da ya fara tasan da ita yake Salati laminde takeyi ta kalli mai unguwa dake gefe sannan tace ka taimakeni ka rufama yarinya asiri kasan halin Hurriya Daidai take da duk wanda ya kwana ya tashi kasan masarautar Qamar basu da imani mai unguwa shiru yayi Kowa ma shiru yayi yana kallon ikon Allah Hurriya da take tsaye fuskar ta blank baka iya cewa ga yanayin ta Kumurci yazo saitin ta sannan ya daka mata tsawa wadda saida ta girgiza kusan kowa a wurin Amman Hurriya ko gezau duk da saida yan hanjin cikinta saida suka kada Amman tayi kokarin gyara tsayuwarta tana frowning fuskar ta Mai fidda zallan kyau tana kallon cikin idanun kumurci Kumurci kallonta yake da mamaki sannan cikin daga murya yace kaskantaciya yar gidan matsiyata wadda tarbiya gabaki daya bata wadata iyayenki ba har suka baki ba yana magana cikin hargagi da wulakanci yana kallon ko ina na jikinta Hurriya tace Are you mad kana hauka ne cikin zazzakar muryata mai dadi da dadin sauraro saboda yanayin maganarta hankalin kowa ya dauku ya dawo kanta tarbiya bata wadata iyayena ba kai kuma jahilci ya wadata naka iyayen tunda gashi kana juya abinda suka koya maka cikin doddar kwakwar ka Animal Asshole Kumurci banda radadi ba abinda zuciyar shi takeyi don ba’a taba maida mashi martani irin yau ba kuma cinkin mutane daga hannunshi yayi zuciyar shi banda tafarfasa ba abinda takeyi zai sauke a fuskar shi Hurriya ganin marinta zaiyi da sauri ta cire dankwalin da tadaura yau cikin sa’a ta sanya dankwalin ta rike hannunshi tana rikewa tayi sauri ta saki kamar ta kama kashi kowa kallonsu yake itama tana kallon cikin idonshi tace Kana hauka ne ?sai tadan tsotsi bakinta kadan Kumurci kam kallonta yake har baya kyaftawa tunda yake baitaba ganin mace mai kyaun ta ba don lokacin da take mashi magana ya kura mata ido har gold din dake ratsin hakoranta biyu saida ya gani saboda irin kallon da yake mata Hurriya kam lura da hakan yasa tayi shiru tana kallon tsakiyar idanun shi Kumurci kallon dogon sumar gashinta yake don baitaba ganin wani da irin gashinta ba ko subira da take take takama da kyau da gashi Hurriya ta fito don nata cike yake ga tsawo ga yawa wannan yarinyar dole ya tafi da ita masarautar Qamar Hurriya daukar ledarta tayi tace wawa dan akuya sannan ta kama hanyar kofa Kumurci kam daya saki baki yana kallon ta Sauran dogarawan kam kallom Kumurci sukeyi don ya kasance Azzalumi kuma marar Imani Amman yau wata yar matsiyaciya yar talaka kuma karawu zata zauna ta Gaya mashi magana Laminde kam tsoro da fargaba ya cika mata ido tanason Hurriya bata kaunar wani abu ya sami yarinyar dama bata zo ba saboda ta sani sarai bazasu barta lafiya ba. Kattin dogarawan dake tsaye gefenta ne suka tare mata hanya a hankali ta dan ja baya jin saukar wata azababbar dorina ya sanya ta juyowa wasu ta gani guda biyu dukan ta suka farayi ba ji ba gani da wani irin rashin imani suke dukan ta laminde kam kuka take don duk bulala daya idan akayi mata sai ji takeyi kamar ita ake duka mai unguwa saidai dauke kai yayi Hurriya kam tana durkushe don tun bulala daya da sukayi mata ta durkusa ta dukar da kanta ta hade kafafunta da gwiwowinta dukanta suke ba ji ba gani duk wanda yaga Hurriya sai ya tausaya mata don idonta sun kada sunyi jawur kukan zuci take wanda yafi ko wani kuka zafi da radadi fargaba da tsoro duk ya cikata laminde matar Mai unguwa kuka takeyi kamar ita ake bugu kasa jurewa tayi ta rugo ta wurin saitin masu bugun ta dan ture Hurriya aka zabga mata bulalar Ai laminde fitsari ne kawai bata saki ba saboda azaba Hurriya dago jajayen idanunta tayi ta saukesu akan laminde kukan da Hurriya zata iya cewa rabon da tayi shi har ta manta ne yazo mata laminde kallonta tayi ta girgiza mata kai ta daina kuka Bulalar suka kara zuba ma laminde Hurriya zuwa tayi ta ture ta tana masu wani kallo Mai unguwa ne ya kalli dogarawan sannan idonshi na taruwa da kwalla yace don Allah kuyi hakuri ku taimaka kuyi hakuri ta gane kuskurenta yanzu Saminu ya kalli Kumurci wanda yake kallonsu yana kallon Hurriya wadda tayi ligis Kumurci yace sharadi dayane zamu baku Mai unguwa yace ka fadi koma wani irin sharadi ne zamu cikashi In Sha Allah murmushi yayi sannan yace ko matarka ta bimu masarautar Qamar ko kuma wannan matsiyaciyar ya nuna Hurriya shiru Mai unguwa yayi Hurriya da idonta sukayi jajir ta dago tana kallonshi wani murmushin mugunta yayi mata laminde tayi sauri tace ni zanje wallahi ku kyale yar marainiyar yar nan ku taimaka don Allah Hurriya kallon laminde take wadda banda kuka ba abinda take matar ta sota duk da hali na kin kulawa da take bata Amman bata taba gajiyawa da ita ba laminde ta kalli maiunguwa da idon shi sukai ja tace ga Hurriya nan don Allah ka kula da ita Maiunguwa cewa yayi laminde tare zamu tafi mubar Hurriya a garin nan ni zan biki murmushi tayi tace idan mun tafi kuma mubar ma wa ita? Hurriya da zuciyarta tagama karewa ta bude baki kamar tana tsoron magana tace I will go with them cewa tayi banji Mai kikace ba Hurriya tace zan bisu Kumurci wani murmushi ya saki yace da kin taimaki tsohuwar da take tsugune tana rokona Don wannan matar idan har ta bimu sai na sanya ta Zama baiwa mafi kaskanci a masarautar Qamar kuma sai na tabbatar da ko wani kaskantar bawa ya kusanceta yayi dariya Hurriya kam idonta kadai inda ka kalla zakasan tana cikin zallar bacin rai ga galabaitar da duk tayi laminde girgiza kai kawai take tace ba inda zaki ni zan tafi tana kuka tana girgiza kai Hurriya kam abinda bata tabayi ba shi tayi lallashi don bata iya ba ma kwata kwata Amman daga jin yanayin muryarta zakasan kokari ne take tana magana zan dawo zan kira shine abinda tace Kumurci kam kokarin turata ya farayi juyawa tayi ta kalleshi tace kada ka sake ka taba ni da kazamin hannunka a irin yanayin da tayi maganar zaka san ba abinda bazata iya ba idan har ya kara Kumurci kallonta yayi yaga yadda idonta ba wani abu wai shi tsoro shiru yayi sannan yace yarinya zaki gane kurenki a masarautar Qamar don karnukan suna da yawa ya fada a zuciyar shi. Hurriya jikinta duk ya mutu saboda dukan da akayi mata laminde kuka kawai takeyi don abun yafi karfin ta Jikinta sai kyarma yake ledar dake yashe ta kayanta ta dauka Kumurci ya kalli mutanen da dogarawan yace su fito su tafi kamarshi ake jira aka tasa kyayar samarin suna turasu kamar jakuna Hurriya gashinta duk yayi budu budu saboda bata maida dankwalin da ta cire ba lokacin da zata rike hannun Kumurci shikam Kumurci da ya juyo ya kalli yadda take struggling yakejin gabanshi na faduwa saboda yadda yakejin zuciyar shi ya kosa su isa masarautar su Mai cike da zallar zalincin he can’t wait to have her in his bed Cikin hiace din emirates din ake ta tura maza saida aka cika mota guda uku Hurriya dai tana tsaye bata matsa ba saboda duk duniya ta tsani taji jikin wani kusa da ita gashi duka marmatse suke saidai fa ko zata mutu a wurin bata shiga motar nan don waye ma baisan Hurriya Faisait hamood ba duk wanda yayi gigin tabata da hannunshi saidai yaji saukar mari Daya daga cikin dogaren ne yazo ya zuba mata bulala ke yar matsiyaciya shiga banza tayi dashi don wani bansan kallo tayi mashi bata ko daga baki ba ballantana yayi tunanin zata bashi amsa kara mata wata bulala yayi har tana durkushewa kasa da kayanta shegiya matsiyaciya ki wuce ki shiga Dukanta ya fara kamar Allah ya Aiko shi yana zagin Hurriya da ta shiga motar Amman shiru tayi saidai fa ba hawaye amman idonta sunyi ja saboda radadi da azabar da take ciki Kumurci ne ya buga mashi tsawa yace shaho ya isa hakanan shaho badan ya gaji ba ya daina dukan ta ya lura wata isa gareta alhalin ita din ba kowa bace face kaskantarciya Kumurci ne yazo saitin da take yace Mai kike jira da bazaki shiga ba banza tayi dashi kamar batasan da ita yake magana ba kara tambayar ta yayi banza Hurriya tayi dashi har cewa yayi zai kira shaho ya kara mata still bata ko motsa ba Hurriya kam taki ko matsawa kowa mamakin Kumurci yake da aka ga yana lallabata saboda waye baisan Kumurci ba saida Hurriya ta mula sannan tace ban iya zama kusa da kowa cikin motar I want to seat alone kallon yadda take magana yake fuskar ta a daure kuma kamar tana bashi order abun ma dariya yaso ya bashi Amman da yake Kumurci ne yayi saurin murtuke fuska ya kalli motar da duk maza ne a ciki sannan ya fitoda mutum biyu yace ta shiga da kyar take tafiya Hurriya saboda dukan da tasha ,har ta kawo wurin cikin motar kayanta gam a hannunta kamar daman sune rayuwarta kusan duka mazan saida suka juyowa suna kallonta saboda kyaunta ga gashin dake yawo a bayanta tsawa Kumurci ya buga masu dukansu suka shiga taitayinsu Hurriya bayan ta zauna ta fara sauke ajiyar zuciya tunani take yanzu to ina rayuwa zata kaita lokacin da bata tsammani haka ya faru da ita saidai duk inda zata tana fatar Allah ya bata ikon jurewa don ga dukkan alama sun nuna ba wurin jin dadi bane a hankali ta duka ta nemo safa cikin kayanta ta sanya dukar da kanta tayi yadda ba wanda zai iya ganinta ta cire sarkar dake wuyanta da kuma dayar sarkar ta sanya su cikin safarta harda kudinta duka ta sanya su wayarta ce kadai ta bari a aljihunta tafiya ne suka fara Sosai don tunda ma aka fara tafiyar Hurriya wani bacci ya dauketa tafiya sukayi sosai don kusan tafiyar awa biyar sukai don lokacin har amfara kiran sallah la’asar shine suka tsaya domin yin sallah Hurriya jin hayaniya ya sanya ta bude idonta a hankali nan taga sun tsaya masu gyada nata tallah masu rake panke awara duk da sauransu cikin rashin kuzari ta sauko Amman jikinta yayi mata mugun tsami don da kyar take tafiya wasu panke manya guda biyu ta siya aka bata canjin ta sannan ta koma chan gefe ta zauna ta fara cin abunta A hankali take ci ba don dadi ba sai don yunwa Hurriya taji ankira ta da mamaki ta dago kanta sai taga Bintu. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar By Khadija (KMU) Page 9&10 Mika ma Bintu fanke daya tayi kato cikin jin dadi ta amsa tace nagode Hurriya ,shiru Hurriya tayi tana kallon yadda Bintu ke cin panke a hankali ta kara kiran mai fanken cikin muryarta Mai dadi kara mika mashi kudin tayi tace ya bata na dari guda biyu ya kara bata mika ma Bintu tayi amsa tayi tace inason ki Hurriya sannan ta rinka cin fanken kamar bata taba cin abinci duniya ba Girgiza kai Hurriya tayi Bintu ce tace ma Hurriya kalli abinda dogarawa can keyi Hurriya mun bani Hurriya kallon saitin da dogarawan suke tayi taga sun sanya sun jera layi layin maza daban na mata daban Hurriya batasan ma cewar akwai mata ba sai yanzu da tagansu jere a layi kallon Bintu tayi tace tare dawa kukazo Bintu da har ta fara kuka ta kalli Hurriya tace da wadancan azzaluman dogarawan daga kai Hurriya tayi tace ya akayi kika biyosu kuka Bintu ta fara tace muna zaune a tsakar gida saiga kawar Larai nusaiba ta shigo daki suka shi itafa Larai nusaiba tace ga yan masarautar Qamar nan sunzo zasu dauki ma’aikata da bayi. Shine tace kawai ta tura ni aiki ba bauta ba suna biyan kudi Sosai kuma ita za’a rinka bama kudin ina labe inajin su har nusaiba ta fito kallona tayi tace kuma naji ance sun fison mata kyawawa kuma kinga Bintu ba daga baya ba sai Larai tayi dariya tace kedai bari ba karamin taimakona kikayi ba nusaiba zan yadda kwallan mangwaro In huta da kuda gshi kuma Abun riba biyu dariya kawai nusaiba tayi tace ai kin yanman albashin nata ko?? Larai tayi dariya tace abinda yafi albashi ma don bakaramin taimakona kikayi ba suka kalli Bintu Larai ai nasan ubanta baida matsala nusaiba kenan ya bani matsala ma yaga ikon Allah Bintu ta kalli Hurriya dake kallonta shine fa suka sanya na biyo dogarawan Hurriya daga mata kai kawai tayi ta juya saitin dogarawan tana kallon tsantsar zalincin da sukeyi Maza da matan dake jere a layi ake cajewa duk abinda aka ganka dashi sai a amshe har cikin riga suke lalubar matan cikin tsantsar zalinci abun gwanin ban takaici Hurriya a hankali ta zaro sauran kudinta dake cikin aljihu ta sanya su cikin safarta gyara safar tayi yadda ba wanda zaiga abinda ke a cikin kafarta cikin sa’a kuma ba wanda ya kula da lokacin da ta dauke kudin Shaho ne da yake kusa da Kumurci suna zaune suna kallon duk abinda ake don kamar sune manya kaga wata yarinya Mai kyau kamar ita tayi kanta nifa bantaba ganin mai kyau irinta ba dogon gashinta ya bani mamaki nace anya bahaushiya ce kuwa ko yanayin shigarta kadai zata nuna maka haka saidai fa kaga yadda take kallonmu girgiza kanshi yayi Kumurci nifa idanuwanta tsoro suke bani Kumurci yarinyar can fa na cikin hadari saboda karnukan dake masarautar mu fa sunada yawa gashi ba babba ba yaro don ko nifa sai na lasa yana karasawa da lashe baki Kumurci wani kallon banza yayi mishi wanda ke hade da gargadi shiru shaho yayi cikin ranshi yace wallahi sai na lasa ai kaima nasan manufar ka munafuki Wani dogari ne ya kalli saitin dasu Hurriya suke kai tsinanu yan gidan matsiyata kuzo nan Hurriya ko motsi batayi ba Bintu tace mata Hurriya ki taso don Allah mu tafi kadasu dake mu banza Hurriya tayi da ita don maganar duniya taki ta tashi su Kumurci da shaho duka suna kallon abinda ke faruwa Bintu zuwa tayi ta shiga layi kwalla na zubo mata dogarin kau cikin hasala yazo saitin Hurriya kallon shi tayi cikin ido shine ke sanya hannunshi acikin rigar mata tashi tayi tsaye tace da uwarka da ubanka sune manyan matsiyata da har suka haifo wanda baisan dajar halitar mata ba kaskantarce kuma duka halayenka ke defining kaskanci Bullock wata muguwar ashariya shaho ya saki yace kaga wannan yarinyar Kumurci shuru yayi kowa ma shiru yayi yana jira yaga abinda zai faru Azuciye dogarin ya daga bulalar ya zuba mata a baya,mata da mazan wurin duka tsigar jikinsu tashi tayi suka juya itakam Hurriya kwalla ce ta zubo mata abinda ta dade batayi ba a rayuwarta wato kuka ta kasance a kullum rayuwarta ita Mai kukan zuci ce har tana jin dama zata iya irin kukan da Bintu keyi kilan ta samu sanyi ko yayane a ranta bulalar da yayi mata har cikin kanta taji azaba matuka wanda ta durkusa kasa hawaye na zubowa Daga hannunshi yayi da niyyar kara dukanta Kumurci ya rike hannun yace ya isa haka Garba ajiye hannunshi yayi ba don yaso ba sannan Kumurci ya yace tayi shiru sannan yace ki iya bakin ki idan ba haka ba to kina hanyar da bazata bullar dake ba don masarautar Qamar sai yayi murmushin mugunta Hurriya tana durkushe a hankali ta shafo hawayen don ta tabbatar da idan nagaske ne kallon hawayen tayi fa dagaske sune tasan ba lallai ta kara maimaita irin wannan kukan ba saboda yau sau biyu tayi kuka sannan ta kasance zuciyar ta Mai rauni ce saidai idan kaganta zakayi mamakin minene ya sauyata har haka da ba abinda yake girgiza ta ko ya bata mamaki kuma fa rashin ganin mutumcin kowa duk girman ka Daidai take da kowa don ko yaro yajefeta da magana sai ta maida mashi martani da wadda tafi tashi zafi shine kawai abinda ke sanya ta magana ko sai kuma idan tana tare da Bintu don Bintu zata iya awa tana mata magana baifi ta bata amsa daya ba saboda miskilancin ta Bintu har ta saba. Kumurci kallonta yake saboda yasan akwai matsala a masarautar nan idan har Hurriya ta shige ta don ya lura bazata taba saukar da kanta kasa ba don haka yake tunanin hanya daya zai bi don tasamu barin masarautar batare da ansamu matsala ba shine yace baiwa ya samota kuma yaroki alfarmar ta zama Baiwa hakimi shine kawai mafita anma ta cigaba da haka baisan a hannun wazata mutu ba don princes da princesses din masarautar nan basu da imani ga kuma dayar matsalar don Kumurci yayi nadamar tahowa da Hurriya don yasan ba karamar wuya zatasha ba don ko yaran sarki kadai sun isheta don sun tsani wani yafisu kyau duk da daman masarautar kyawawa akafi kaiwa saidai ba wanda san dalili to zai iya rantsewa tunda ake kai kyawawan mata a masarautar baitaba ganin Mai kyaun wannan yarinyar ba don su kansu yaran mai martaba sai sun raina kansu. Kallo daya zakayi mata kasan ta jigata ba karamar jigatuwa ba ma don wandon dake jikinta duk yayi datti fuskar ta kuma duk ta kumbura ga babu annuri kwata kwata saida fa annurin kyanta nan don sai salki takeyi Kumurci yace ki tashi ki shiga mota mu tafi yanzu bada hargagi yayi mata maganar ba don zuciyar shi ta dan karye kadan Kallonshi tayi da idanunta masu kyau da wani kaifi Kumurci ya daga mata kai tare da fatar kada tayi kafiya irin wadda tayi dazu. A hankali take takawa amman zaka iya hango zallar mulki dake cikin tafiyar tata har ta shiga motar a hankali Kumurci girgiza kai yayi don ya hango kurar dake tafe da ita saidai Allah ya kyauta don aikin gama ya riga ya gama. Bintu kam lokacin da ta koma layi cikin sa’a ba ba wanda ya lalubeta saboda hankalin kowa da ya koma kan Hurriya tanajin su karime dake gabanta cikin layi suna dariya suna cewa Allah ya kara sa’ade ce tace kinsan dadin da nikeji yadda ake bugun Hurriya karime tayi murmushi tace naki kika sani ni yarinya ta dade tana bani haushi shegiya ga isa ga iko sai kace wata shegiya sa’ade tace bata da mutunci Hurriya kinga cin mutunci da tayi ma mahaifina kuwa harda watsa mashi man awara akafa bayan tagama zazzageshi cikin mutane karime yo naji maganar tana yawo agari ki bari idan munje mu hade kai mu ci ubanta don ni ta dade tana bani haushi don kiga duk anguwar mu ace mazan ita kadai suke kallo to yanzu lokacin mune idan munje muyi maganin karuwa Mai ma maza jiki. Bintu duk tanajinsu don harda kukan ta wurin da suka ce mata karuwa don tasan karya sukeyi Allah ya saka maki Hurriya inji Bintu ta fada cikin ranta. Hurriya da ta koma wurin zamanta ta jinginar da kanta jikin window tana rufe idonta saidai kyarma kawai takeyi tana harhade hakoranta ga sanyi da ya isheta dankwalin da ta daura ta rufe gashinta dashi ta koma ta kwanta saidai sanyi ya matsa mata don bata daina jinshi ba ledar kayanta dake gabanta ta jawo saboda Asabe hada kyautar doguwar hijab tayi mata don lokacin har ta kawo zaure Asabe ta kwala mata kira a hankali asabe ta mika sabuwar hijab doguwa maroon tace Hurriya ko bazaki sanya ki fito ba ai nasan kina sallah to ki rinka sallah da ita inda so samu ne ki rinka fita da ita sai kuma ta tabe baki tace nasan yaudarar kaina nike ba inda zaki da ita tace Hurriya ki godema Allah don wallahi inasonki duk wanda yaji nayi kyauta sai ya kusa suma saboda mamaki kindai sanni da san kudin tsiya Hurriya batace mata komai ba har tagama maganar ta sai Hurriya ta mika mata ledar alamun ta sanya Asabe kam sauri ta dauko ta sanya Hurriya ta tafi ba godiya bare sallama. Hijabin ta lalubo ta sanya ta dunkune kanta ciki a hankali bacci ya dauketa. Sosai suka sha tafiya har suka iso Babbar masarautar Qamar bata sani ba don kowa ya fita a motar ya barta Kumurci ne ya kula da babu ita don har anfara kada kyayoyinsu Kumurci ya bude motar yazo inda take bacci da yake bai san sunanta ba don haka yace ke ki tashi mun iso shiru Hurriya tayi saida yayi mata magana kusan sau uku sannan ta bude idon wadanda sukayi mata nauyi Sosai har lokacin tana jin jikinta na kwankwatsa Kumurci yace ki fito munzo kuma kada kiyi ma mutane kafiya da rashin kunya don kece zaki sha wahala Hurriya da batajin karfin jikinta kwata kwata don ko yadda take numfashi zaka iya lura tashi tayi ta rungumo kayanta saidai tana tafiya biyu ta sake su Kumurci da yayi gaba yaji karar kayan da tasaki don haka ya juyo ya kalleta sannan ya daukar mata kayan suka fita duk da suna zuwa ana sallahr magriba don duhu har yafara Bayyana Amman bazaka iya gane cewa rana ce ko dare ba saboda haske da ya wadaci ko ina a babbar masarautar Qamar Masarautar kanta abun kallo ce girmanta gari guda ne tunda ga floor din dake kasan masarautar da ginin da akayi mutum zai gane cewar masarauta ce maiji da tsantsar dukiya kuma da karfin mulki .saidai Hurriya ba Abu daya wanda ya burgeta don kallo daya tayi ma komai wanda bata kara kallon wani Abu ba Su Bintu da su karime kam Murna sukeyi kamar su ciji duwawunsu basu san masarautar Qamar, bawuri bane da ya kamata ace ya burgesu ba ko su kasance masu farin ciki Don masarauta ce wadda take cike da tsantsar zalinci da rashin imani.Kusan duk wadanda sukazo dasu sakin baki suke suna kallon ko ina. Tasa keyarsu akayi ana bugunsu kamar tumaki suka shigo ciki inda ba abinda kake gani sai dagorawa dake tsaitsaye fuskar su hade kamar zasu je yakin basasa hannunsu daya narka narkan bulali Dayan kuma hannu dogayen bindigu kowane,Ba wanda bai firgita ba da ganin wadanan dogarawan don fuskar su babu alamun sassauci Hurriya da da kyar take tafiya saboda zazzabin da take wani bakin dogari ne ya sakar mata bulala wadda saura kadan ta fadi da kyar ta cigaba da tafiya Kumurci da yaga banda dukansu ba abinda akeyi yayi dauriya yace basu bane bayin ,Dukansu tsaya sukayi suna kallon Kumurci saboda dokar masarautar ce duk wanda yafi ka matsayi dole kabi umarninshi kuma duk abinda zaiyi ba wanda ya isa ya dakatar dashi saidai idan har akwai wanda yafika matsayi zai iya hanaka to Kallon Kumurci suke da idanunsu masu sawa mutum ya shiga zullumi Kumurci da duk ya tsure yace Allah ya gafarce ku Kumurci yana Neman sassauci. Saminu ne ya iso don kusan duk yafi su matsayi ya kallesu yace lapya?cike da rusunawa ya fara mashi bayanin abinda ya faru wani kallo Saminu yayi masu wanda nan take suka bar wurin ya kalli Kumurci yace ka shiga dasu ciki kuma duk wanda ya tareka kace ni na baka umarni shiga dasu daga ciki sannan ya bar wurin. Kallon su shaho yayi da yan matan da suka taho dasu da mazan,saitin Hurriya ya kalla yaga tanajan numfashi da kyar ta hade gwiwar ta da kanta,tunda aka tsaidasu ta kwanta Kumurci ba karamin dadi yaji ba lokacin da yaganta da hijab ya tabbata da ace ba hijab jikinta da yanzu wani ya shiga dakinshi da ita gashinta kuma da tuni an datse saidai cikin ikon Allah ta rufe duka jikinta harda kusan rabin fuskarta. Tafiya sukayi inda suka kara nitsa kansu cikin masarautar sakin baki kusan Dukansu sukayi don haduwar masarautar tafi bayyana yanzu akan wurin da suka baro a baya kuyangu ne da bayi da hadimai wadanda basu da iyaka kowa da hidimar da yake kuma kusan kowa da kalar uniform din dake jikinshi wasu green and red wasu green and orange wasu green and yellow wasu green and blue. Su karime kam yau sun samu Tv don suna kashe ma kwarkwatar idon su haka suka rinka tafiya don daga inda suka baro zuwa inda sukazo yanzu tafiya ce Mai wani irin nisa don dukansu sun gaji shaho yace a kira uwale uwar bayi ta raba masu aiki tun yanzu Kumurci ya daure yace ai kasan ka’idar abun dole sai sunkai gobe saboda jakadiya tana shiyar uwargijiyar ta yanzu to bari na nemo uwar bayi Shaho ya tafi don nemo uwar bayi ba tare da wani bata lokaci ba sai gashi sunzo fuskar ta ba annuri bare fara’a Kumurci ne ya gaisheta cike da girmamawa ya mikasu wurinta Kumurci Kallon Hurriya data gama galabaita yayi cikin aljihun shi ya fiddo paracetamol da ibuprofen ya bata kin karba tayi don kusan sau uku yana mata magana ta amsa Amman ko kallon inda yake batayi ba bare har ya sanya ran zata amsa a ranshi yace zaki sha wuya ne a masarautar nan don duk kafiyar ki sai kin ajiyeta don dubunki ma sunyi sun gama Kumurci ya dora mata maganin saman hijab sannan ya juya ya bar wurin,su karime kam sai kallon yadda ta zukana sukayi she looks so pale and weak yanayin da ba wanda ya taba ganin ta dashi tunda take rayuwarta she’s always strong and fierce don haka Dukansu da mamakin yadda take suke sai Abu na biyu da ba wanda ya taba ganin ta dashi wato hijab tunda duk wanda ya kwana ya tashi ba wanda ya taba ganin Hurriya da hijab a unguwar su shiyasa suke kallonta da mamaki uwar bayi ce ta kallesu tace wai Lapia kukayi tsaye kallon mazan tayi tace zata kira halliru ya shigar dasu ta kalli su Bintu tace su tafi. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: Masarautar Qamar By Khadija (KMU) Page 11&12 Uwar Bayi ce gaba suna biye da ita tafiya sukayi Mai nisan gaske kafin su iso wani babban gini kallon wurin su Bintu suka rinkayi ita dai Hurriya ta kosa ta kwanta don kiris ya rage mata ta daina tafiya saboda kasusuwan ta da suke kwankwatsa kusan dukan su itace karshe wurin tafiya uwar bayi ce ta shiga dasu cikin ginin wanda yake da bangare iri da iri a ciki Kuyangi ne kowace da uniform dinta suna hidimar su tunda suka shigo yan matan dake zaune suke binsu da wani irin kallo Hansa’u ta tabo barira tace kinga mun samu sabbin zubi yau Barira da take kallon Ko wanne a cikin su daya bayan daya cikin izza da takama tace uwar Bayi daga ina aka samo mana sabbin tumakai su sa’ade da karime duk suka bude baki Hurriya da tanajin sun saidai ta kanta takeyi Uwar bayi kam batace komai ba ta wuce suka bi bayanta Hansa’u ta kalli barira tace kinga yan mata tsala tsala nifa harna hango wacce tayiman Barira yadda take zaka dauka wata diyar sarkice saidai kawai saboda tafi su mukami kuma tanada saurayi a cikin dogarawan don haka take baza nata mulkin a inda ya kamata cikin izza da mulki tace kudai bi a hankali kada wata acikin ku ta shiga gonata sannan ta tashi tana wani juyi wanda kamar dagan gan takeyinshi su Hansa’u Dukansu biyota sukai abayanta. Uwar Bayi wani babban daki ta kaisu wanda yake da Bayi kusan duka manya mata ma ko ina shimfede da katifa kowa kallonsu yakeyi da tausayi don ace yara da kuriciyar su sunzo azzalumar masarautar nan don neman abun duniya but basusan cewar lalatar rayuwar su sukazo yi ba don a masarautar tasu miye ba a aikatawa na kazanta babu shi Duk abinda baida kyau shi akeyi ga zalunci. Uwar Bayi ta kalli yan matan da tazo dasu tace to nidai ga makwanci don haka ku nemi inda zaku kwanta kafin gobe tayi a rarraba maku wurin bacci Dukansu godiya sukayi mata sukaje neman wanda zai taimaka yadan rabasu kafin zuwa goben da tace. Hurriya kam tana duke bata motsa ba bare tayi i tunanin tafiya Uwar bayi ta kalleta tace kiyi maza kije ki nemi wurin kwana ko ki kwana a kasa tunda ba’a gidanku kike ba Hurriya dagowa tayi ta kalleta wani irin kwarjini tayima Uwar bayi Uwar bayi batace komai ba ta tabe baki ta fita. Bintu kam har tasamu wurin kwana matar Mai kirki kamar ma budurwa ce ita ta kara Bintu kuma katifar katuwa ce zata ishesu su biyu Tunawa Bintu tayi da Hurriya don ba taganta ba tunda suka iso a hankali ta fara o dubata kafin ta hango ta zaune a tsakiyar dakin cikin sanyi sai kallonta akeyi da sauri Bintu ta nufi inda take tace Hurriya a hankali ta dago idonta da sukayi jajir ta zuba ma Bintu hankali tashe tace Hurriya mike damunki baki lafiyane? Subahanallah ta dora hannunta saman goshin Hurriya & tureta tayi da sauran karfin daya rage mata tace How dare you touch my Royal Body maganar na fita da karkarwa saboda kyarmar da takeyi Bintu tace kiyi hakuri don Allah hankalina ne ya tashi dana ganki haka Bintu tasan cewar Hurriya na bala’in sonta duk da cewar bata nunawa amman idan Bintu na mata labari hankalin ta duka take bata ko Daga yanayinta zakasan tanajin dadin ko wani irin labari Bintu ta bata kuma tasan har abada bazata samu kawa irin Hurriya ba don ako da wani lokaci itace Mai tsaya mata tsayin daka a rayuwarta ta kwatar mata yanci a wurin kishiyar uwa da shikanshi mahaifinta don ba wanda baisan irin muzgunawar da suke mata saidai Hurriya ba ruwanta haka zatazo tazage su tass kuma tayi masu babban kashedi na idan suka kara matsa mata zata dauko masu hukuma kuma sunsan halinta saboda ta taba dauko ma Larai da baban Bintu yayi magana tace a hada dashi saida Bintu tayi sati daya a wurinta lokacin abinci duk idan zasu ci sai ta tambayi Bintu mizasu siyo kuma duk abinda Bintu ta gani tanaso sai ta siya mata shi wani lokacin da kanta take tambayar Bintu Abu kaza yayi maki idan tace Eh zata sai mata shi kamar batasan darajar kudinta ba kuma idan har Bintu tazo bata kara kwana a katifa sai a kasa saboda Hurriya ba wanda ya isa ya taba koda hannunta don tasan wannan halin nata duk wanda yayi gigin taba ta sai ta sauke mashi mari Bintu ma kafin su saba kusan sau uku tana Marinta saboda yawan kai hannu jikinta daga bayane saidai ta tureta tayi mata kallon kada ta kara. Kallon Hurriya tayi tace mata sanyi ke shigar ki muje ki kwanta banza tayi da ita Bintu kuka ta fashe dashi tana ma Hurriya magiya ta tashi sanyi Amman ina kusan duka mutanen dakin kallonsu suke Bintu kam da taga Hurriya taki tashi sai ta kwanta kasan siminti tana kuka tace mata don Allah ki tashi idan har baki tashi ba nima anan zan kwana Hurriya kallonta tayi cikin muryarta mai cike da rashin karfi tace Bintu ki shekara a kasa idan kin tashi Bintu da tasan wacece Hurriya tayi mata sanin da ba wanda yayi mata shi don tabbas Hurriya dagaske take ta shekara kwance a siminti itadai batasan mi ya faru a rayuwar Hurriya ba daya maidata haka kamar dutsi Fashewa da kuka Bintu ta karayi sannan ta tashi tanayi mata magiya kallon yanayin Hurriya tayi wanda banda hakoranta dasuke gabgab ba abinda sukeyi wani kuka ta kara fashewa dashi mai tsuma zuciya ta fara hadata da Allah mutane duka kallonsu sukeyi suna mamakin irin son da Bintu keyi ma Hurriya ita kuma Hurriya ta kafe kamar kafurar farko sa’ade tace kibar shegiyar ta mutu kowa ma ya huta kafura Mai bakin hali Karime tayi caraf tace tun ba aje ko ina ba karshen karuwa yazo namu dai muyi kallo duk jiji da kan mutum dole ya ajiye shi don ubanshi zaici yayi anan. Hurriya duk tanajinsu duk da ciki ciki sukayi maganar ta yadda bazata iyaji ba ,saidai sunanta fa Hurriya Faisait Hamood. Magana daga nesa komin kasa da murya da mutum zaiyi sai taji ta kamar gizo gizo haka take Allah ya bata kunnuwa kamar ba irin na mutane ba saboda kaifin ji da suke dashi. A hankali ta fara wani irin tari harda sarkewa salati Bintu ta rinkayi tana kuka da tarin ya tsaya ba abinda take sai karkarwa Bintu a hankali ta rage tsawonta tana kuka tace ki taimakeni Hurriya ba kanki zaki taimaka ba Hurriya tunda nike baki taba musu da duk abinda nace inaso ba sai kinyi mani shi don Allah ki taimakeni ki tashi ba don halina ba Hurriya kallon Bintu tayi da idanunta masu kyau saidai sun rikida sun koma jajawur saboda azaba don har jijiyoyin idonta ana gani Hurriya tashi tayi a hankali ta fara takawa saidai kafafunta banda kyarma ba abinda sukeyi Bintu ta dafata saboda kada ta fadi tureta tayi da sauran karfin da ya rage mata har Bintu na faduwa kasa tana binta da wani kallon cikin muryar ta da ta shake tace kina hauka ne ,Bintu kuka take tana girgiza kanta tace Aa to sai ta kasa maganar tana Neman faduwa Bintu da sauri tazo ta tarbeta kada tafadi kasa daga Hannunta Hurriya tayi da basu da karfi sosai ta wanka mata mari tana kallon Bintu da sai kuka take sannan ta sake ta Mutane kallon dramar kawai suke wasu lokaci daya Tsanar Hurriya ta kamasu saboda rashin mutuncinta suna jin tausayin Bintu wasu kuma zaginsu kawai suke suna cewa marar sa mutunci zasu zubda hali daga zuwansu duk munsan ma’anar abinda kukeyi hmm mutane sun iya judging din abinda bashi bane Har sun manta da cewar yau su Hurriya da Bintu suka zo bare suyi irin hallayar da suke magana. Hurriya da kanta ta taka sukazo har inda Bintu ta samu wurin kwana Bintu kam dadi ta rinka ji don har ta goge hawayen ta. Habiba kallo daya tayi ma Hurriya ta washe mata baki tace sannu yanmata Hurriya ko kallon inda take batayi ba bare ta sanya ran zatayi mata magana Bintu kallon Hurriya tayi tace bari tayo alwala, waje ta fita sannan ta dawo ta gyara hijab dinta ta fara rama sallolinta har tagama Hurriya idonta a rumtse yake don ta jinginar da kanta jikin katifa. Bintu bayan tagama addu’arta ta kalli Hurriya tace in samo maki abinci Hurriya daga mata kai tayi alamar Eh Kallon habiba Bintu tayi tace ina zan samo mata abinci Habiba tace muje in raka ki kitchen ki amso naku abincin to inji Bintu don haka tabi bayan Habiba suna tafiya akan hanya sai habiba ta dan wuce Bintu itakuma Bintu tana ta tunani tana tafiya. Habiba juyowa tayi baya sai taga Bintu na tafiya kamar wacce zata fadi dawowa tayi ta rike mata hannu gam tace kina tunaninta ko ?kada ki wani damu zaki samu wadanda suka fita komai a masarautar nan wacce zata kula dake kuma ta soki sai ta farayi mata tafiyar tsutaa acikin hannu tace Ko nima idan kika bani dama zan maye maki gurbinta Sai ta tsunkuli Bintu a waist dinta tana kashe mata ido daya itadai Bintu kallon ta kawai takeyi ba tace uffan ba don batasan inda zancen nata ya dosa ba kallon habiba tayi tace muje ko naga lokaci na tafiya Dariya habiba tayi tace gaskiya kinason wannan yar tawalwalar ki nima inason inga ana kula dani haka shiyasa nike kaunar ki don daga gani kinada kulawa ko kukan da kikayi mata kadai ya isa ya nuna hakan Gaskiya inasonki nagode kawai Bintu tace sannan tace muyi sauri kada tayi bacci murmushi habiba tayi ta rike mata hannu suka fara tafiya da fan dan sauri sauri itadai Bintu tanajin yadda take mata tafiyar tsutsa da hannu har suka kai babban kitchen din da ake dafa ma bayi da kuyangi da masu aiki abinci ba’a wani hantare su ba saboda sanin sune sabbin ma’aikatan da suka zo don suna bukatar Abinci don habiba tayi masu bayani Plate biyu aka basu cike da tuwo habiba ta amsa ita kuma Bintu tayi tsaye tana kallo ana miko mata plate din Habiba ta kalleta tace ki amsa mana bata fuska Bintu tayi tace ba shinkafa ne? Kallonta mai bada abinci take da mamaki tace ke yar Gidan maysiyata ki amsa idan ba haka in maida ki kwana da yunwa shegiya har MU zakiyi ma iyayi alhalin agidan ku ba lallai kina samun kalar shi ba Habiba ta mintsinota Bintu ba domin ranta ba haka ta amshin abincin saboda tasan ba lalle cewar taci tuwon ba Suna zuwa suka ga Hurriya ta kara dukunkune wa don ta kara makurewa wuri daya kamar da alama sanyi takeji Bintu tace Hurriya ki tashi ki ci abinci A hankali ta bude fuskarta tana kallon Bintu da take kuka a hankali tace ya akayi kuma?Share Hawayen ta Bintu tayi tace Hurriya don Allah ki ci abinci kada ki ce bazaki ci ba akwai nisa fa inda muka amso kuma kinga baki lafiya tana sakin baki kamar karamar yarinya Dan tsotsar bakinta Hurriya tayi kamar daman sararta ce ta daga mata kai Cike da jin dadi Bintu ta miko mata tuwon Habiba dai tana kallon ikon Allah kwano ta samu ta debo ruwa sannan taba Hurriya ta wanke Hannunta ta fara cin abincin a hankali ta dan ci ba laifi tanajin ta koshi ta ture plate din ta kalli Bintu ,da sauri ta kara miko mata kwano ta zuba mata ruwa ta wanke hannunta Habiba cike da kaudi da son ta samu shiga tace Hurriya ga magani kisha na ciwon kaine Da zazzabi Hurriya ko kallon inda Habiba take batayi ba don a hankali ta sanya hannuta cikin hijab aljihun wandonta anan ta fito da magungunan da Kumurci ya bata hannun Habiba har lokacin yana tsaye tana bata magani cikin muryar ta da take da alamun rashin lafiya tace Bintu bani Ruwa. Da sauri Bintu ta bata ruwa ta shanye maganinta kallon habiba Bintu tayi tace kiyi hakuri tana da wuyar sabo ne Amman tana da kirki zaku saba In Sha Allah .Bari in tafi in samo wurin kwana sai Hurriya ta kwanta tare dake,Habiba murmushi tayi cikin yanga tace yi zamanki ki kula da abarki ba mai takura maku nizaje inda nima za’a kula dani,dadi sosai Bintu taji ta farayi mata godiya don tasan idan har Hurriya ta kwanta Habiba ta kwanta kusa da ita kilan za’a iya tashi aga habiba kwance saboda irin dukan da Hurriya zatayi mata kuma itakanta Bintu bazata taba bari ta kwana kasa ba saboda sanyi. Habiba ta fita tace matsiyata kuma ashe kunsan harka muje zuwa ta nufi dakin Su Hansa’u Aiko tana shigowa sukazo suka zagayeta sukace mata habiba ya bakin nan nagansu tsalatsala guda habiba tayi tace ayiri to ku kwantar da hankalin ku don ba wata wahala da zamusha wannan karan wurin jawo hankalinsu tace ai yan gidan matsiyatan suma duk sun san harka don wadda na bama makwanci ma baki gansu ba kamar zasu cinye juna nan ta kwashe labari ta basu tass dariya suka rinkayi suka ce gobe zasu zo ta nuna masu yan matan suna fata ma Allah ya sanya akawosu dakin Barira duka tana jinsu Amman batace komai ba don shiru tayi. Bintu kallon Hurriya tayi da ta fara gyangyadi tace ki kwanta ni zan kwanta kasa daga mata kai Hurriya tayi ta kwanta dukun kune cikin hijab dinta bacci ne mai wahala ya dauketa Bintu kam tagumi ta buga tana kallon Hurriya don ta hango wahalar da zatasha a masarautar nan don Hurriya bata durkusa ma wada sadai da alama waddanin sunyi yawa a masarautar kuma wahala zata sha don ko bata durkusa ma ma’aikata ba ai akwai ubannin gidansu da dole suyi masu biyyaya tana fatar dai Allah yasa kada su sha wahala don ganin Hurriya tana wahala tamkar itace take wahalar bazata iya dauka ba. Murmushi tayi ganin Hurriya ta tsotsi bakinta sai kuma ta turo bakin tana bata fuska alamar shagwaba magana tayi da wani yaren Bintu da take kallonta taji tana magana tana bata fuska da wani yaren da bata taba ji ba Don tasan yaren dai gaskiya babu kalar shi a Nigeria Kallon kyaun hallitar fuskarta takeyi yadda tayi ma fuskarta kamar wata baby magana takeyi cike da shagwaba murmushi Bintu tayi tace naga ranar da Hurriya zata daina daure fuskarta tana shagwaba haka tabb akwai ruwa da kankara ranar. Bintu bacci ta faraji don Haka ta kalli Hurriya ganin ta dukunkune wuri daya kuma ga space nan da yawa don haka ta raba gefenta ta kwanta nesa sosai da ita don kada cikin bacci Hurriya taji ta a kusa da ita ta tureta Addu’a tayi sannan ta runtse idonta bacci mai cike da gajiya ya dauketa . Karfe bakwai Bintu ta tashi har lokacin Hurriya bata tashi daga bacci ba ta makara don haka agurguje ta kama ruwa hade da alwala tazo tayi sallah .Tana gama Sallah taje inda taga sauran yan uwanta karime tayi ma magana tayi banza da ita don haka tayi ma uwale magana tace miye akeyi anan uwale tace zamu tafi ne za’a araba mana aiki bata ida magana ba saiga Uwar bayi tazo Kallonsu tayi tace saifa kun kula kubi a hankali kuskure daya a masarautar nan zai iya zamar mutum babban kalubale a rayuwarta, kowa amsa mata yayi sannan suka bi bayanta tafiya sukayi Mai nisa sannan suka iso katon wuri inda mazan dasuka zo duk sunja layi suma layi sukaja suna kallon kyawu da tsarin masarautar da babu wani Abuna more rayuwa da bai wadace ta ba. Kwance take a lallausar katifa wani Abu dake gefenta kamar wasan yara ya fara kara bude idonta tayi masu cike da bacci kokarin komawa take Amman karar ta hana ta karar wayarta ta hade da karar abunda yaketa wakar yaran tsoki taja tana maganganu da kuma mamakin wani marar sa’a ne ya tada ta daga bacci Amman bari Taga kowaye tana jawo wayar wani call din na kara shigo mata kallon wayar tayi da wani bacin Rai cikin muryar ta maidadi tace oh my God sannan ta ziro dogayen kafafunta wani Abu ta latsa saiga kuyangi guda Biyu sun shigo suna dukar da kansu kasa sannan cike da mugun girmamawa sukace Allah ya taimake ki Allah ya kara maki Nasara Allah yasa wannan Rana tazamar maki Ranar farin ciki da Albarka Batace masu kala ba sai da tagama Shan kamshinta sannan ta kallesu Dukansu ba wanda baisan ma’anar kallon da tayi masu ba don haka da sauri daya daga cikin kuyangar ta shiga toilet dinta ta hada mata ruwa Daidai yadda tasan tana amfani dashi kullum ta zuba mata flowers masu kamshin dadi ta wanke mata brush ta sanya mata macline Mai kamshi ta fito tana durkusawa tace Allah ya taimaki Batatuma Angama Dayar da take tsaye wacce har ta dauko pink towel dan dora mata towel din tayi sannan ta zame mata rigar tareda rumtse idonta ta yadda kada a samu matsala taga wata siffa ta jikinta cewa tayi ya isa don Haka ta juya Neela ta ida daura towel dinta ta shiga toilet din saida ta farayin brush tadan shafa wasu abubuwa na skin care sannan ta shiga bahon da aka hada mata ruwan wanka lumshe idonta tayi tadan fara wasa da ruwan saida ta dauki mintina kafin tayi applying showe gel dinta mai sanyi dadi ta wanke jikinta tass sannan ta fito [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: Masarautar Qamar By Khadija (KMU) Page 13&14 A hankali ta fito daga toilet din tana fitar da wani kamshi har tazo tsakiyar dakin da angyara shi tass kamar ba’a taba kwanciya ba vanity table ta zauna tana kallon kanta olive skin dinta sai glowing takeyi ringing din wayarta ne yayi kara wanda tasan ba kowa bace face kilan mahaifiyarta a hankali ta tashi kamar wadda batasan taka kasa saidai ba kasa bace batason takawa tsantsar sarautar dake yawo a jikinta ne bata fuska tayi ganin Mai kiranta kin dauka tayi har ta tsinke karar wayarta ne ta karayin kara dauka tayi ta kanga a kunnenta muryar mai dadi da sautin amo tana ratsa dakin don da tsiwa take maganarta liya wai lapia kike kirana kamar wadda ta ci maki bashi daga dayan Bangaren liya wadda tagama shiryawa tace I just missed my twin sister i decided to check on her ko nayi laifi ne Neela takirata da karfi tace liya da bacin rai a muryarta dariya liya tayi tace wallahi kiyi sauri ki fito ko In kira basai na fada ba kindai san sauran su idan na kirashi Neela tayi sauri ta dafe zuciyarta tace bansan kalar wasannan dariya liya tayi tace Don’t forget to wear green palazzo and white shirt Tun jiya na sanya akawo maki kayan so kiyi sauri kinsan mu suke jira tunda Mai Martaba da kanshi yace Aikinmu ne Neela da take saurarenta cike da taikaici tace I know I know go to hell Liya I hate you liya dariya tayi tace I love you Neela kashe wayarta tayi . Twin sister dinta kenan she always gets on her Nerves shiryawa tayi cikin kayan da Liya tace akawo mata tun jiya wandon palazzo ne na prada da wata rigar gucci da takalma da scarf Inner wears ta sanya sannan ta fesa turaruka masu tsananin tsada ta shirya cikin kayan wadanda elegance dinsu sun fito ko ta ina kayan ba karamin kyau sukayi mata ba don dan karamin scarf ta daura kusan duka rabin gashinta ya zuba a baya sai kamshin mai masu dadi takeyi Kallon kanta tayi A madubi sannan taga yadda tayi kyau murmushi tayi wanda ya fito mata da dimples dinta she’s proud of her beauty don masarautar tasu sai kana da kyau za’a san da existance dinka shiyasa subira tayi masu fintinkau saboda tsanin kyau da mulkinta Tunawa kawai da tayi da ita taji zuciyar ta na tashi bloddy Hell tace saboda tasan ta kusa dawowa ba dadewa Neela tace koda yake da da yanzu ba dayaba ,ba zata iya daukar iskancin subira ba zuciyarta ce tace kullum sai kince da da yanzu ba daya ba Amman kullum dayane saboda ba abinda kuke iyawa a gaban yarinya mai jin kan tsiya. Tsoki tayi ta fito katon parlon ta wanda yake cike da abubuwan more Rayuwa tunda ga floor din parlon da chandeliers din da suke à sama wanda suke bama ko ina wani irin haske wall bracket din kuma masu wani irin designs na royalty masu bala’in kyau fitilu ne ko ta ina haske kam har zai iyayi ma mutum illa saboda parlon baida wani hayaniya sosai don American parlor ne ko royal chairs babu kujerun l-shape designs masu kyau Tana fitowa kuyangin Dukansu suka dukar da kai kujerar dining daya daga cikin su ta ja mata ta zauna sai kuma daya daga cikinsu tazo da sauri ta zuba mata Irish da liver sauce sai coffee cewa tayi su ta zataci abinci don duk sunyi mata tsaye da sauri kuyangin suka fita waje suna jiranta tagama cin abinci ta take hankalin kwance saidai wayarta na hannunta tana duba wani abu a Instagram kara taji wadda karar ta kusa firgitata,Neela da tasan ba wanda zaiyi hakan sai liya don waye ya isa bama wanda ya isa liya janye plate din Neela tayi ta faracin chips din tace shey you’re here enjoying your breakfast nikuma banci komai ba haba Neela tana maganar tana dafe zuciyarta sannan tace Baki da kirki kallo daya zakayi Neela kasan ta gaji da halin yar Uwarta wadda kammanin su daya don idan zaka tsaya kana kallon su baka isa ka gane daya acikinsu ba,saboda kamanninsu. liya cin cips din take harda mugunta while Neela kallonta kawai takeyi har ta cinye sannan ta dauki coffee din dake gefenta ta shanye dariya tayi tace yanzu naji Daidai tashi mu tafi Neela hararta tayi tace liya daga yau kada ki kara shigo mani chamber dafe zuciyarta tayi sai ta bata fuska tace haba my twin kin sanya an raba mana chamber yanzu kuma so kike in daina shigowa chamber kwata kwata tana dafata tsoki Neela tayi ta ture ta dariya liya tayi tace muje Tare suka jero suna tafiya Dukansu kuyangin a bayansu wasu kuma a gabansu olive skin dinsu sai shining yake with the help of the sun don Duk bala’inka baka isa kace ga Neela ba ,ko liya saboda tsananin kammannisu moto ci aka bude ma kowace a cikinsu sannan suka shiga baya Daidai inda su Bintu da sauran mutanen da suka zo dasu suka tsaya Bintu da sun kusa awa uku suna jira Dukansu sun gaji ga yunwar da sukeji kamar mi saidai hankalin ta baki daya yana wurin Hurriya da har yanzu bata ganta a wurin ba. Kallon princesses guda biyu masu kama daya sukeyi su Dukansu kamar kauyawa maza da matan duka kallonsu sukeyi kyau, siga, gayu ,sa’ar rayuwa da mulki kawai suke gani lahaula wala kuwatta illah Billah kawai Bintu take cewa kamar rana haka suka fito don sun haske ko ina don kowa su yake kallo Kuyangin a gaba da bayansu sukuma a tsakiya Har sukazo inda aka tanadar masu su kadai don su zauna kujerun kansu abin kallone Su Bintu natsuwa sukai wurin ya dauki wani irin shiru liya da Neela kallon kowa sukeyi da isa kuma da sarauta da idanunsu masu kaifi Kuyangin kuma duk sun dukar da kansu a tsaye magana liya tayi da kuyangar dake kusa da ita Ita kuma ta isar da abinda tace ga uban kuyangu da bayi. Hurriya tun dazu ta tashi lokacin da ta tashi sai taga ba kowa a dakin don haka ta fito ganin kuyangu tayi duk suna ta hidimar su kowa da abinda yakeyi wanka takeson tayi don jikinta duk yayi tsami bata matsa daga inda take ba tsaye saiga Kumurci yazo da ledar kayanta da mamaki yake kallonta Saboda yaga sauran yan uwanta wurin da suke jiran Gimbiya Batatuma da Gimbiya shawata cike da mamaki yace ya akayi Bakije ba banza tayi dashi,Hurriya kamar bada ita yake magana saida ta jima sannan cikin muryar ta Mai tsanani dadi tace bani kayana ta ida maganar tana tsotsar bakinta kadan Kumurci kallonta yake yana kara tasbihi aranshi yarinyar Allah yayi mata tsananin kyau ga wani uban kwarjini da take dashi ita kam da tasan yadda daurewar fuska keyi mata kyau data rage daurewa tana dariya kilan mazan masarautar hankalin su bazai dauku da kyawunta ba Kallon kayan jikinta yayi tun na jiya ne wanda yaganta dasu ba hijab ko dankwali babu don duka gashin yayi baya ya sauka a bayanta tsaki Hurriya tayi tace malam ka samu Tv ne?kumurci da yadan daburce cike da borin kunya yace ga kayanki Hurriya kallon kayan tayi sannan tace ka ajiye zan dauka da mamaki yake kallonta don ba’a taba yi mashi irin haka ba Hurriya kam ta rungume hannunta tana kallonshi ido cikin ido kwarjin tayi mashi sosai don haka ya janye idonshi akwai abinda yakeson gaya mata Amman bai iyawa saboda yadda bakinshi yayi mashi nauyi juyawa yayi ya tafi ita kuma Hurriya tayi tsoki ta kalli wata kuyanga sannan tace ina zata tayi wanki Kuyangar sakin baki tayi tana kallonta don sauran kadan ta ruga saboda kyauwunta da gashinta kallonta kuyangar kawai takeyi Hurriya da ranta ya fara baci don ta tsani kallo itama cike da rainin wayau tace wai Tv na Zamar maki ne hajajju Aa baiwar Allah kinada kyau ina jiye maki tsoro ne ga kuma kina da gashi kuma naga shigar kamar bata musulma ba tsoki Hurriya tayi tace akwai wata doka ta sanya kayane? Girgiza mata kai kuyangar Tayi tace ina guje maki karnunkan masarautar nan ne maza da mata Hurriya tace kinsan fundamental Human right?girgiza kai tayi Hurriya akwai Right of choice yanzu idan naga dama zanyi yawo yadda nakeso kuma ba wanda ya isa yayi depriving right dina so shiga zanyi wadda nikeso hakajju iyakar ki kallo Kuyangar tace iyakata kallo kuwa shiga kuma duk wadda kika ga dama kiyi zaki basu labari ne a masarautar Qamar Hurriya dage rigarta tayi ta daureta daga gefe shafafen cikin ta wanda sai daukar ido yake sai kuma wata yar sarka ta gold da take like a cibinta ta fito kallon matar tayi tace kafin In fara bada labari ke ya kamata ki fara basu labari tace munafuka magulmaciya kuyangar mutuwar tsaye tayi tana kallon shafaffen cikin Hurriya ko kyaftawa batayi Hurriya tsoki tayi ta saki rigarta tace sakara munafuka ta barta baki sake don kam taji kunya kuyangar sosai Hurriya tayi gaba abinta tabar ta tsaye tambayar wata tayi aiko ba bata lokaci ta rakata har inda suke wanki bata da sabulu don haka ta kalli wadanda suke wanki a wurin wanda suma suke ta kallonta Tsoki tayi ta kalli wata da take kallonta kamar zata lasheta sabulu ta gani da ruwa a gefenta don haka Hurriya ta zuba ruwa cikin bokitin dake gefen yarinyar ta dauki kayan da tasan zata sanya yau saboda idan tace zata wanke duka zai dauketa lokaci don haka kala daya da zata sanya yanzu ta sanya wandone palazzo da yar top ta duka ta fara wankewa Hurriya tanajin ana kallonta a jikinta amman tanason ta gama wanki da takeyi saida ta gama wanke kayanta tass ta juyowa tayi ta kalli yarinyar dake mata wani irin kallo Hurriya ruwan kumfa ta diba ta watsa mata nan take ta juya tana soshe kanta Hurriya ruwan dauraya ta zuba taje ta shanya kayanta inda taga ana shanya ta ajiye mata bokitin yarinyar tace mata ki kawo sauran kayan ki in wanke maki naga ke bakuwace Hurriya banza tayi da ita ta jawo wayarta ta sanya waka ta samu wuri ta zauna tana bin wakar tanajin idanu sosai akanta amman ko a jikinta kallon kafarta tayi har dan kumburi tayi ita ba ma’abociya sanya safa bace amman ya zatayi tsaki tayi Alamun bushewar kayanta da ta ganin ya sanya ta dauki abunta ta tafi. wanka take Bukatar yi don jikinta duk ya dameta tanayin wanka fin sau biyu a rana jikinta har yanzu bai saki ba don tanajin radadi har yanzu a fatarta a waje ta hadu da Habiba Amman bata ganeta ba Hurriya sarai taganeta zuwa tayi inda Habibar take tace ki samo man ruwan zafi inyi wanka kallonta Habiba kawai takeyi Hurriya shiru tayi tana mamakin yan masarautar basu da aikin yi ne sai kallon mutane tsoki tayi wanda ya sanya Habiba cewa to bari in samo maki a kitchen mi zakiyi dashi? Shiru Hurriya tayi tana kallon Habiba tanason karantar ta saida tagama kare mata kallo sannan tace Bath shiru Habiba tayi alamar bata gane ba tace mata wanka da sauri habiba tabar wurin da niyyar nemo ma Hurriya Ruwan wanka bata wani bata lokaci ba sai gata da ruwan zafi lokacin har tana wurin Hurriya ta cire safarta habiba na dawowa ta mika mata kayan data wanke da safar alamar ta rike mata jiki na rawa habiba ta amsa sannan Hurriya ta shiga inda take tunanin toilet ne da kyar Hurriya take wanka a wurin saboda shegiyar kazantar dake ciki bata wani jima ba don watsa ruwan tayi ko sabulu babu ta maida kayan jikinta ta fito A inda tabar Habiba ta amshi kayanta sannan ta shiga katon dakin har inda suka kwana itada Bintu kallon katifar tayi taga an gyara tsaff tsaki tayi jin rashin brush din da batayi ba a hankali ta dauki madubi ta bude bakinta tana kallon hakoranta da suke farare jere yan kanana kallon abinda yake gefe da gefen hakoranta tayi golden wanda sai salki yake kurama abun ido tayi tana kallo sai kuma ta rufe bakinta tare da yin tsoki abubuwa da yawa sun dameta ba abinda tazo dashi na yau da kullum na rayuwa da ace bata siye kayan nanba da batasan yazatayi ba tunawa tayi da sauran kudinta aiko ta bude ledar kallon kayan tayi don tana gani tasan anyi mata bincike bata wani damu ba itadai damuwar ta kawai sarkokinta wadanda suke taimaka mata wurin cigaba da rayuwa a hankali tajawosu taga sai sparkling sukeyi zame rigarta tayi ta kalli tatoo din dake zane a jikinta sannan ta kalli zanen sarkar da akayi design da irin tattoo din jikinta a gefe, sai Stone din dake tsakiyar sarkar dake rubuce da H baro baro kallon dayar sarkar tayi zuciyarta na kuna so take tayi kuka amman tasan ba lallai ta iya kukan ba wani wando ta zaro yana da aljihu can kasa kuma daga ciki sannan ta sanya abinta tare da addu’ar kada a dauke mata kara kallon tatoo dinta tayi wanda yake a gefen bayanta jin motsi mutum ya sanya tayi saurin sakin rigar tareda sauke ajiyar zuciya habiba kallonta tayi tana kallon rabin jikinta da ya fito saboda rigar daman buttones gareta to da ta bude rigar kusan har cleavage dinta ana gani kuma bata maida buttons din ba lumshe ido Hurriya tayi Habiba kam tsaye tayi tana kallon jikinta wanda bata taba ganin fata mai sheki da kyalli irin tata ba tana tunanin ko twins albarka. Hurriya tanajin idonta a jikinta saidai batada energy na magana don duniyar tunanin takeson fadawa abinda ta tsana kenan rayuwarta don tunanin rayuwarta ta baya pure darkness ne wanda bata fatar wani ya tsinci Kanshi a ciki ,ta iya shutting kuma ta iya controlling emotions dinta abinda tasani shine idan har kaine kake da kanka to zaka iya controlling abubuwa da yawa saidai akwai abinda baka iya controlling saboda we’re human beings kuma Humans are weak. Please comment share and like Love you all [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar By Khadija (KMU) Page 15&16 Bude idanunta masu kyau tayi sannan ta sauke su à habiba da take binta da wani irin lustful look Hurriya zuba mata idonta masu kaifi da kwarjini tayi da sauri Habiba ta gyara tsayuwarta sannan tace kina bukatar wani Abu a hankali Hurriya tace comb da sauri Habiba ta kawo mata comb kallon dogon gashinta takeyi wanda kwata kwata bai kama dana yan Nigeria shiryawa tayi cikin wani brown palazzo sai red riga gashinta sakwa sakwa ta daureshi Habiba na kallonta kamar zata cinye ta so take ta taba gashin taji idan nata ne Amman tsoro ya hanata takalminta ta sanya ta fita batasan inda wurin yake ba saida ta tambayi wani ya nuna mata hanyar da zata bi duk inda ta wuce kallonta akeyi tanaji a jikinta kuma tasan ana kallonta saidai ta saba ko a garinsu haka akeyi mata irin wannan kallon tafiyar ma taki karewa saboda nisan tafiyar wurin. Uban bayi ya kirga su Amman ba mutum daya acikin mata kuma ance masu su talatin ne mamaki sosai ya kamashi don haka ya nufi inda twins suke Allah ya taimaki shawata Allah ya kara maki nasara Babu mutum Daya a cikin mata kuma su talatin ne liya da mamaki take kallonshi don ba’a taba samun irin haka ba kallon neela tayi saidai hankalin Neela kwata kwata bai tare da ita yana wani saiti daban don haka ba tare da bata lokaci ba ta kalli saitin da Neela take kallo inda Hurriya take tafiya kamar she own half of the world yadda tafiyarta take cike da izza liya da mamaki take kallon Hurriya kowa a wurin hankalin shi ya koma kanta fuskar ta fayau babu komai amman wani irin tsantsan kyau da annuri ne take fiddawa gashin kanta wanda bata daure ba duk ya zubo mata kowa bude baki yayi yana kallonta da mamaki don karime kasa shiru tayi tace uwale kamar Hurriya nike gani daga mata kai uwale tayi tace itace fa karime sanya hannunta tayi a baki tana cizon yatsa Hurriya ba inda ta tsaya sai a saitin Bintu banda faduwar gaba ba abinda bintu keji . Neela kallonta takeyi da wani irin mamakin gaske don tundaga kayan jikinta take kallo sannan tunda ga sama har kasa gashin kanta kam ko subira albarka bare ita daure fuska tayi ta murtuketa kamar Allah ya aikota ta taho kuyangin nabin bayanta cikin jiji da kai da isa da sarauta Neela ke tafiya har tazo inda Hurriya take tsaye kallon Hurriya tayi tundaga saman ta har kasanta gabanta ne ya shiga faduwa don tunda take bata taba ganin Epitome of beauty irinta ba the girl is almost perfect with nothing left for people to criticize not almost perfect ma she’s more than perfect kallon cramel skin dinta wanda yake glowing irin na wanda sukaji hutu. hutun ma anihin hutu ba muna hutu ba tayi wannan yarinya Anya ba cikinsu akaso ayita ba aka samu kuskure shine abinda tace kawai a ranta kallon cikakken gashinta takeyi wanda yake da yawa wanda daureshi sakwa sakwa amman dan ziri biyu na gaban gashinta sun dan sauko irin shigar da tayi bata da bambamci da irin tasu shigar Don bambamcin kayan nasu are damn expensive while her own is cheap cikin zuciyarta tace she’s beautiful she adjusted her self trying her very best to look normal kara matsowa tayi inda Hurriya take tayi ke tace cikin tsadaddiyar muryarta shiru wurin ya dauka kusan kowa ya juyo wurin domin bama idonshi abinci liya itama kallon ikon Allah takeyi daga inda take tsaye Neela magana ta karayi ma Hurriya cike da tsantsar mulki kuma da sarauta Hurriya dagowa tayi ta zuba ma Neela idanun ta masu matukar kyau da kwarjini Subahanallah kawai Neela tace don side view dinta ta gani bataga complète face dinta ba sai yanzu da ta dago tabb she wishes to be her friend because the girl is fucking beautiful saidai matsalar they are not in the same classes she’s far better than her kilan idan har tace tayi friendship da ita it will be a great insult to her a cikin masarautar kamar ta Neela baiwa ta zama friend dinta kai not in this life maybe in the next life Hurriya itama kallon ta take tana analyzing dinta don taki janye idonta daga cikin na Neela itama Neela hakan take a wurinta a cikin masu aikin da kuyangi da bayi ba wanda ya taba bata irin wannan kallon da Hurriya take bata saboda kwarjinin ta and she’s ahead of them they’re far different so they have to always stared at the flour whenever she’s around them nobody will dared to stared at her but this is a different story because Hurriya is not looking away or bowing her head kutt she’s giving her more like a deadful glared cikin isa da mulki tace Who are you Hurriya ta ta dan cije lebenta wanda kamar daman sararta ce Bintu ta rinka kallonta da pleading eyes dinta tana rokonta ta ido kada ta jawo ma kanta matsala ta taimaka Cikin muryarta mai zaki da dadin gaske da accent dinta na Ethiopia tace Hurriya Faisait Hamood she wasn’t expecting her answer to be like irin amsar da tabata she was surprised because tasan ma aikatan su basu wani jin turanci maybe kilan tayi ayyuka gidajen masu kudi shiyasa ta tsinci irin kalmomin turanci irin haka harda kayan dake jikinta kila ma kwance ne Cikin jiji dakai tace waye ya baki izinin wannan shigar da kikayi da gadara Neela ke maganar Liya na daga gefe tana kallon ikon Allah Hurriya shiru tayi tana kallon Kyakyawar fuskar Neela wadda batada bambamci data liya saboda tsantsar kamarsu Neela ta fara hasala Sosai don taga yarinyar tana Neman raina ma mutane wayau kuyangarta tace ta kira mata shaho aiko da sauri aka kirashi jikinshi na bari yazo yana durkusawa kallonshi tayi ta nuna mashi Hurriya aiko a take ya gane abinda take nufi wanda daman kamar jira yake Cikin tsantsar mugunta ya zuba mata bulala daya wadda saura kadan ta saki fitsari liya ce tazo da sauri tayi stopping dinshi tace kada ya kara dukanta wurin shiru ya dauka Neela na kallon Liya Hurriya kam kallo daya idan kayi mata zakasan bulalar ta shigeta saidai kwata babu alamun nadama sai wasu flames ma dake fitowa daga cikin idonta Hurriya ta bama liya tausayi sosai sadai batasan tayi Abu makamancin da zai iya zamowa disgi ga yar uwarta don haka ta janye Neela suka koma inda suke kuyangin su na rufa masu baya. Rarraba masu aiki aka farayi Har akazo kan Bintu ita Bintu ba komai aka bata ba sai mai aikin sashen Neela bayan angama da Bintu uban bayi ya karkato kan Hurriya girgiza kai yayi kadan sannan ya fara lissafo mata aiyukan da zatayi masu matukar wahala sashe biyu zatayi aiki sai kuma aikin bayi wanda wanda bayi ke irin wannan aikin saboda tsananin wahalar aikin to hadashi aka bata har aka gama lissafo mata aikin batace kala ba aikin ne masu azabar wahala aka jero mata don ko yadda uban bayin ke karanta mata ayyukan kadai ya isa kasan da gayya aka bata aikin Bayan angama raba ma kowa aiki saida suka jira liya da Neela suka bar wurin sannan suka tafi Uniform aka basu kusan kowa da kalar nashi uniform din don kusan kowa da matsayin shi itadai Hurriya Green and Red aka bata komawa tayi ta shirya cikin uniform din sannan ta linke kayanta ta maidasu a leda baya taje inda akeyin lodin wankin princes da princess da yaran masarautar mata da mazane a wurin banda tikar wanki ba abinda sukeyi sunayi ana zubo masu wasu kayan sai kara tila masu kayan ake ga alama ba wani Hutu daman tattare dasu Uwar bayi ta kalli Hurriya tace gashinan ki jona shiru Hurriya tayi Uwar bayi da take tsaye tana jiran amsa daga gareta jin shirun da yayi yawa ne ya sanya ta juyowa saidai mi wayam babu Hurriya babu alamunta Hurriya har ta isa inda akeyin wankin in a polite way tayi masu magana tare da tambayarsu abinda zatayi ba bata lokaci aka nuna mata wasu kallon tsantsar hallitar kyau da gashinta sukeyi don kowa a wurin ma ba kallon musulma yake mata ba andwho cares tunda basu take bauta mawa ba kuma mutane are good in making judgement sai suyi tayi Wanki takeyi tukuru don tanayin wanki don ta saba tunda ita takeyi ma kanta ma wanki she’s not lazy because life had taught her alot ko a garinsu duk aikin da tasan yana bada kudi to tanayinshi in order for her to make a living don haka ba wata matsala bace sosai a wurin ta don haka ta cigaba da wanki baji ba gani Tafiya takeyi wadda kallo daya zakayi mata kasan cewar ta gaji don yanayin tafiyar ta ne zai tabbatar maka don tunda suka fara wankin babu wata magana wato a huta don kamar jakkai haka sukayita yin sukola sai yanzu dasuka gama Cigaba tayi da tafiyar saidai dakin kamar an kara mashi nisa don taki kawo dakin har yanzu saida ta kara doguwar tafiya mai tsawo sannan ta iso dakin Bata wani bata lokaci ba ta dauko kayanta da ta bari a wurin habiba ta nufi sabon dakin da aka nuna mata dazu a matsayin nasu Dakin babba ne saidai bai kai wancan girma ba don wannan zai iya cin mutum ashirin saitin katifar ta ajiye kayanta duk da tanajin kiran sallah magrib da akeyi bai hanata kwanciya ba wani dogon Bacci ya dauketa Mai cike da gajiya tanaji cikin bacci uwar bayi tana mata magana akan zuwa dayan shashen da take aiki domin hada ma hakimi abinci tsoki tayi ta juya ta cigaba da baccin ta bata tashi ba sai karfe taran dare Hurriya hamma tayi tana kara gyara dogon gashinta wanda yadan sauko mata tsoki tayi don ba abinda take bukata irin wanka da ruwan zafi a yanzu saidai batasan inda zata samu ruwan zafi don haka ta fito ko ina tarr kamar ba dare ba tayi alwalar ta cikin dakin ta shigo sannan ta sanya doguwar hijab tayi sallah Bayan tagama rama sallolinta ta duba cikin kayanta ta zaro riga wadda batada hayaniya yar karama wadda ko cinyoyinta bata rufe ba ta sanya Kwanciya tayi taja hijab dinta ta rufe jikinta yunwa takeji amman bazata iyacin tuwo ba a takure take sosai don tariga ta saba da abinda takeso shi takeci tanason freedom rayuwarta amman kwata kwata tasan dole zatayi hakuri da wasu abubuwan. Manya matane su uku sai Hansa’u da barira sune cikon biyu haka suka shigo dakin su biyar suna shakiyanci suna dariya barira ce leader ga dukkan alamu yau zamusha dadi inji Hansa’u akwai sabbin zuwa ga dukkan alamu Barira ta kallesu tace saina fara zaba kafin ku zaba gaskiya Hansa’u tace angama shugaba tana dariya suwaiba ce tace ni kinsan nafison hidimar jakunna kafin dayan abun biyun ne sukayi dariya sukace muma sai mun fara shan dadi kafin muyi rabon jakkuna dariya suka kyalkyace da ita suka zauna inda ya zamar masu kamar chamber su a dakin Hansa’u ce ta bude leda ta fiddo rake mai zaki tanasha murmushi tayi tace kai kai wannan rake akwai zaki Allah yasa yanmatan dakinan suyi zakin wannan raken dariya suka kwashe da ita Wasila ce tace kinga nayi nan don haka duk inda taga jakunna indai na sabbin zuwa ne saida tadaukosu Hansa’u da suwaiba sai Aliya suka tashi sukazo inda su karime suke kwance da saraunsu suna tarkato yanmatan da suke wasu kwance wasu zaune Dukansu saida suka zaba suka darje acikin yanmatan sannan sukazo tsakiyar dakin Hansa’u da bata iya jira don haka ta fara zame kaya ba kunya ba tsoron Allah taja mardiyya dariya suka fara suna shewa mardiya kam abinda Hansa’u ta farayi mata bata taba jin irin shi ba don haka ta fasa wani irin kuka manya manya matan da suke tsaye suka gaura mata mari mai shiga jiki ba wadda bata gauwara mata mari acikinsu suna dariya Banda salâti ba abinda mardiya keyi Don Hansa’u ta fara janye mata suturar ta Barira wadda take shugaba acikin su ta taso tazo wurin tana kallon yan matan uwale tayi ma alama da tazo uwale banda kyarma ba abinda takeyi nan ta fara ja da baya wata irin muguwar faduwa kasa tayi wadda suwaiba ta sanya kafa ta shureta ta fadi kasa tana dafe goshi kuka uwale takeyi mai taba zuciya tana dafe goshin ta Barira tsoki tayi dallah sakara taso kema ai dadi zakiji bamu kadai zamuj dadin ba kuma da kun saba zakuzo kuna nema dakanku kinzo kina ma mutane kuka Wasila tayi wata shegiyar dariya sannan tazo ta take ma uwale hannu tace shegiya daga gani ma zaki yi jaraba ta kara halba ta tana tsirta mata miyau Barira tace ku shigo man da ita Suwaiba da wasila suka kamata suka kaita har makwanci Barira don ita har wani labule gareta wanda baka iya kallon komai dake cikin wurin Uwale sam taki bamaBarira hadin kai don cizo da tsunkuli ba wanda batayi mata da kyar Barira ta barka mata riga wani irin cizo uwale ta kaimata a cinya mai dan banza zafi aiko barira ta hankadeta uwale kam ta rugo a guje tana hawaye Barira sanya kayanta tayi ta fito itama tana bata fuska alamar taci wuya Kallonta su Mardiya da suwaiba da wasila sukayi sukace lafiya kallon uwale da take sharbar kuka tayi tace gatanan ta kusa illata ni don haka kuyi maganinta Dariya sukayi a tare ita kuma ta samu wuri ta zauna Dukan uwale suka farayi wanda kamar daman abinda ya kawosu duniyar kenan don basu ji basu gani hada halbinta sukeyi cike da mugunta suna wata yar iskar dariya ita kuma uwale kuka takeyi mai ban tausayi da taba zuciya Mutane na kallo Amman waye ya isa yace zaiyi magana don daurin gindi suka samu wurin manya ma’aikatan masarautar don sai suyi maka dukan tsiya kuma su kira mararsa imanin samarinsu suma su dasa Su Karime kam kyarma kawai sukeyi suna kallon ikon Allah wasu kam acikin su ma kuka sukeyi Hurriya baccin gajiya takeyi saida bata da nauyin bacci tun dazu takejin kuka da hayaniya saidai bata maida hankali ba ta koma baccin ta amman hayaniyar da kukan damunta sukeyi don duk sai juye juye takeyi cikin baccin tsoki tayi ta janye hijab din dake jikinta ta tashi takalminta kawai ta sanya ta fito ba inda ta tsaya sai wurin su wasila da su suwaiba wanda banda bugun uwale ba abinda sukeyi Hannunta duka biyun a bayanta sai gashinta da yayi loosing tie saboda bata daureshi da kyau ba Kamar hadin baki dukansu suka dago suna kallonta itama kallonsu takeyi wanda da alama idanunta basu gaji da bacci ba Kallon uwale Hurriya tayi wadda take durkushe tana kuka wasila ce ta kara kai mata mari sannan ta dago tana kallon Hurriya tace ke kuma fa babu wanda tace ma kala Hurriya Dukansu kallon yadda suke binta da kallo takeyi kamar wasu hungry lions Barira ce ta taho tana karairaya sannan ta kalli Hurriya a izgilance tace wa kike nema tanabin long slender legs dinta wanda rigar ta ko cinya bata gama rufe mata ba ,her legs shine like a sparkling water don wani salki sukeyi na tsantsar kyau hutu da jin dadi da duk suka bayyyana Cikin isa da kuma rainin wayau Hurriya tace Are you lesbians sai kuma tayi licking gefen bakinta taciji lebenta tace kuna neman mata ne ?kowa acikin zuciyar shi ba wanda baya muradin ta saboda basu taba ganin lafiyaryar mace mai kyau dinta ba don ko gimbiya subira albarka Barira ce ta taho cike da iyayi da kaudi tace kina son ki tabbatar ne ?sannan ta daga kai tace ma Hurriya Eh muna neman mata sannan ta lashe bakinta tace bari kingani matsowa tayi inda Hurriya take tsaye wadda kyakyawar fuskarta take blank she looks fierce and scary don da Barira tayi gigin kallon idonta da ta shiga taitayinta Hurriya kallon Barira takeyi wadda har tazo kusa da ita da alama kuma tabata take so tayi don har ta dora hannunta saman gashinta tana lumshe ido bude idonta tayi tar akan na Hurriya sai a lokacin taga yanayin fuskarta mai firgitawa sharewa tayi tana kokarin kai hannunta a cinyar Hurriya saidai saukar zazzafan tuwo da miyar da taji a fuskar tane ya sanya ta sakin ihun azaba don ta tabbata fuskarta ta kone wani irin kuka takeyi mai ban tausayi da taba zuciya Kowa kallon Hurriya da ta konata da tuwo a fuskarta yakeyi babu alamun ko tsoro ko nadama a fuskar Hurriya don da alama inda akwai saura to kilan Sai ta watsa mata a ko ina na jikin Barira Wasila ce ta taso da wani irin zafin nama da alama zata kaima Hurriya mari da sauri Hurriya ta kauce sannan ta kalleta ido cikin ido tace i dare you to slap me with your filthy hand licking lips dinta tayi sannan tace da ni Hurriya faisait Hamood na sanya an yaken yatsunki guda biyar And duk randa kika kwatanta yin haka I promise this ta nuna mata alamun sai an yanke hannun sannan ta kallesu wanda banda kallonta ba abinda sukeyi don ko daga idonka zai tabbatar maka da duk abinda tace zatayi zata iya Bintu hannunta rike da bakinta don mamakin yadda Hurriya ta kona Barira da tuwon da ta kawo mata yanzu saboda tasan duk yau bataci komai ba kuma ko a jikinta don yadda take acting kamar ba abinda tayi don ta san Hurriya zata iya yin fin haka indai maganar wani zai taba mata jikine daman Bintu tunanin Hurriyar bataci abinci ba don haka tace bari ta kawo mata tuwon tare da fatan Allah ya sanya taci sai ga abinda ya faru da tuwon da Kuma Barira Hurriya zuwa tayi ta kwanta ta mike kafafunta ta lumshe idanunta Bintu tarugo tazo tace Hurriya shiru Hurriya tayi Bintu ta kiranta yafi a kirga Amman shiru karshe ma saidai ganin bacci ya dauke tayi don alamar numfashin ta ya canza ya koma na mai bacci ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** 🌚Masarautar Qamar By Khadija (KMU) Page 17&18 Karfe 6:10 goma Hurriya ta tashi saboda ayyukan da take dasu yau murza idanunta tayi sannan tayi mika ba addu'a abakinta ba komai bata dauki komai ba don haka taje babban toilet dinsu ta kama ruwa sannan tazo tayi Alwala Tayi sallah wanka takeso tayi saboda tsamin jikin da takeji duk batajin dadi saboda Rashin cikakken wanka data sabayi don ta saba kafin tazo masarautar nan sai tayi wanka sau uku a rana kuma da ruwan zafi don batasan ruwan sanyi indai wurin wanka ne saboda ciwonta tsoki taja ba tare da ta cire hijab din sallahrba ta nufi babban kitchen Aiki akeyi a kitchen din sosai shigowa tayi wata yar babbar mace ta gani a gaban tukunya ruwan sai tafasa yake Daidai saitin matar Hurriya ta tsaya saida tagama kallonta don kamar bazatayi magana ba cikin miskilanci tace ruwa zafi zaki bani Dagowa inna hanne tayi don ganin isassar don batayi mata sallama ba sannan bata gaisheta ba sai ruwa zaki bani cikin tsiwa ta dago domin tsiyaya rashin mutunci saidai ganin kudin da Hurriya take mika mata datayi ya sanya tayi shiru ta fara washe baki tana toh toh miye zakiyi da ruwa yar albarka kamar don dole tace wanka amshe dari biyun inna hanne tayi tace samo bukiti in zuba maki kinji Hurriya juyawa tayi ba bata lokaci sai gata da bucket nan inna hanne ta fara zuba mata ruwan zafi masu yawan gaske har saida Hurriya tace ya isa sannan ta daina zuba ruwan Toilet ta shiga tayi lafiyayyen wankan ta wanda tasan zataji dadin jikinta Sosai a hankali ta shafa bayanta inda zanen tatoo ke kwance a bayanta wurin saitin wuyanta lumshe idonta tayi ta cizi lebenta masu kyaun gaske sannan ta fito tana tafiya ne a hankali kuma duk da safiya ce sosai tanajin yadda ake nunata Tana zuwa ta iske Bintu a zaune kamar bacci ma takeyi Don haka Hurriya ta shirya tsaff cikin uniform dinta wanda ta samu ta wanke jiya da kyar wadanda sukayi mata wani irin kyau na musamman fuskarta sai fidda annuri takeyi sanyi da takeji na safiya wanda yake shiga kanta ya sanya ta bude kayanta domin neman Hula Aiko ba tare data sha wahala ba sai gashi ta samu hula mai kyau ash colour hular irin ta sanyi ce duk a wurin asabe ta siye su Bata fuska tayi don tana dadewa bata daura ma gashinta wani Abu ba don sai idan abun ya kadota sosai .shine take rufe gashinta don a shekara baifi ta rufe gashinta ba sau hudu akwai lokacin da har shekarar ta kare bata damu da rufe gashinta ba idan ba wurin sallah ba Cikin kyankyami take rike da hular da sam bata wanke ta ba don duk kayan gwanjon duk hasken su sai ta sanya hannunta ta wanke su tas kafin ta sanya. Warware gashinta tayi wanda ya zubo mata har bayanta sosai don ma akai akai take rage gashin kanta da batasan yadda zai rinka takura mata ba kuma data rage nan da nan yake fitowa har yafi wanda ta rage din tsawo da cika da yawa Taba gashin tayi sannan ta dan shinshina ko yana wari kamshin coconut oil din da taji ya sanya ta dan saki ajiyar zuciya Daure gashinta tayi Sosai yadda duk bala'inka baka iya hango tukar don ta linketa ta sanya ta cikin gashin yadda ba mai iya gane yawan gashin ko tsawonshi ko yawanshi Bintu da ta bude idonta masu kyau ta kalli Hurriya tace kindawo daga mata kai Hurriya tayi tanabin ko ina na jikinta da kallo alamar rama kuma da yar damuwa tattare da ita Ganin Hurriya nabin ta da kallon minene matsalar ki ya sanya ta washe baki yan hakoranta suka fito tace Hurriya jiya nazo in ganki na kawo maki abinci Amman Saita kasa ida maganar alamar kamar tana kuka ta hade kafafunta da gwiwarta Hurriya ta duko tace Bintu miye ya faru waye ya taba ki fadamin shi. Daga muryar ta zakaji alamar kulawa duk da yadda take kokarin boye emotions a cikin maganarta ,duk wani mai tsantsar fahimta zai iya fahimtar damuwa a maganar ta Amman a yadda take maganar kadai sai mutum yace bata damu ba Hurriya kara matsowa tayi kusa da Bintu kamar tanajin tsoronta tana tambayar wai lafiyar ki kuwa ki fadamani manah itama maganar ta kubce mata da alamun shagwaba Wata irin kyakyawar runguma Bintu tayi mata sannan ta fashe da matsinacin kuka Hurriya dan ture ta tayi ta zame jikinta Bintu dagowa tayi ta kalleta da idanun ta da sukayi jajir ta kalli Hurriya da take bata fuska kamar kashi ya tabata kuka ta kara fashewa dashi Hurriya dafe kanta tayi tace ki daina kuka ki fadamin abinda ya faru shiru Bintu tayi kamar daman abinda ta jira ta fada mata kenan don haka tayi shiru kafin a hankali tace cikin muryarta mai rauni tace nayi kewar ummanah Hurriya inajin tsoro tana maganar hawaye na zubo mata shiru tayi sannan ta goge hawayenta tana kallon Hurriya data tsura mata ido tashi tayi zata mike Hurriya tace Bintu yadda ta fadi sunanta saida ya sanya tsigar jikin Bintu ta tashi don da wata irin kulawa ta fadi sunan Bintu kallonta takeyi da mamaki tace Hurriya tana zare ido  dan murmushi Hurriya tayi kadan wanda duka dimples dinta saida suka lotsa sakin baki Bintu tayi tana kallonta don tunda take a duniya bata taba ganin wanda murmushi yayi ma kyau ba irin Hurriya itakanta har goosebumps saida taji itada take ma mace kenan inaga ta fito tana murmushi bama dariya ba murmushi kawai tabb akwai matsala don ta tabatta duk inda ta matsa mazane zasu rinka binta kamar sleeves Dogs inaga tayi dariya ita kanta Bintu tunda take bata taba ganin mace mai kyaun Hurriya babu ta inda Allah ya rageta a fuskarta ko jikinta Gyaran murya Tayi ta kalli Hurriya da kamar tana cikin good mood a hankali Hurriya cikin muryar ta mai dadi da sanyi tace Mai kike tunani Bintu ke nake tunani yar dariya tayi wadda har saida hakoranta saida suka fito shiru Bintu tayi tana kallon ratsin gold din dake tsakankanin hakoranta wanda bata taba lura dasu ba sai yau tunda take da Hurriya idonta har wani sparkling sukeyi dimples dinta kam duk sun lotsa Bintu cewa tayi Hurriya daman kina dariya dan gyara fuskarta Hurriya tayi ta koma yadda take da sannan ta juya ba tare da tace komai ba Bintu kiran sunanta tayi Hurriya tsayawa tayi bata juya ba kuma batayi gaba ba Bintu matsowa tayi cikin rauni da sanyi tace Hurriya ki zama yar uwata wadda zan rinka fuskantar ta da matsala ako dayaushe don Allah kada ki Rabu dani ko ki juya min baya ni ko baza kiyi fira dani ba nizan yi maki fira . Inajin kadaici sosai wanda kwata kwata banda kwanciyar hankali ke kadai nike gani inji dama dama a raina don ni kallon yar uwa nike maki cikin muryar ta mai dadi Hurriya tace Bintu kin zama kanwata daga yau Bintu bata fuska tayi ta bayan Hurriya tace na girme ki Hurriya shiru tayi batace komai ba ta fita don tasan kilan ta makara dage kafadarta tayi sannan tace who cares Tana tafiya taji ana nunata saidai ta saba sosai safiya ce ga kuma sanyin da akeyi mai shiga kasusuwa Hurriya idan ka kalleta zakayi tunanin batajin sanyin don ba dankwali A kanta amman akwai hula a hannunta tafiya tayi Mai nisa kafin tazo bangaren daza tayi aiki Ma'aikata ne ta gani tun abakin kofar chamber sunata aikinsu a hankali ta shiga bangaren kallon parlon takeyi wanda komai na ciki ya burgeta tun daga ceiling din dakin har zuwa painting komai fari ne kallon chandeliers din dasuke jere a saman popn tayi wanda yake bada wani irin mahaukacin haske wanda yake neman tarwatse mata idanu kujerun parlon royals ne masu matukar tsada kuma very light saboda at first glance ba Lallai ka kirasu royal ba fa sai ka san furnitures Sosai zaka iya ganewa kallon dogayen labulen da aka jerasu tayi komai na parlon is rich and elegant carpet din wanda ya cinye katon parlon da kusan set of chairs guda hudu kuma dukan su luxury royal chairs ne Sai dining table dake cin kujeru guda shidda saida ta gama kallon komai magana taji daga bayanta don haka tajuya yar budurwa wadda bazata wuce sa'arta ce tagani sai kallonta takeyi kamar zata cinye ta baiwar Allah Amman ke ba yar najeriya bace shiru Hurriya tayi fuskar ta a hade bata ko amsa mata ba gyara tsayuwarta tayi sannan tayi murmushi tace hala kece sabuwar ma'aikaciya to muje In kaiki wurin mama rabi nan ma Hurriya batace mata komai ba don ganin irin kaudinta ta katon kitchen suka bi wanda Hurriya ke biye da ita har suka zo inda mama RaBI take Matar yar dattijuwa ce tsaye tana kallon sabbin ma'aikatan da aka kawo Zubaida tace mama rabi ga sabuwar Mai aikin da aka kawo saitin kunnen mama rabi tazo tayi mata rada tace kinga kyaunta sai tayi dariya tace akwai kallo a masarautar nan Amman fa shegiyat akwai miskilanci kamar jikar Qamar wata dariyar tayi tace itada tazo masarautar Qamar ai komai ta ajiyeshi tana dariya mai cike da zallar munafunci da makirci kuma da mugunta Duk abinda suke cewa Hurriya tana jinsu saidai basuyi tunanin don babu ko alamar hakan a fuskarta mama rabi tazo Daidai saitin Hurriya saida ta kare mata kallo sannan ta washe baki tace sannu yan mata Hurriya daga mata kai kawai tayi Mama RaBI abun ya bata haushi Amman da yake yar duniya ce sai ta share ba bata lokaci ta fara lissafo mata dokikin Imad shiru tayi tana saurare har tagama Hurriya batace kala ba Amman ga dukkan alamu ta dauka Mama RaBI ta kalleta tace ki gwada mata hanyar dakin zubaida tace muje ko tare suka koma itada zubaida har zuwa inda zai sada ka da dayan parlonshi kallon Hurriya zubaida tayi tace ki shiga idan kika wuce parlo na biyu zakiga dakinda yayi hanyar da tayi kasa Tohm sai ki shiga kasa din da kin wuce parlon to dakin dake kallon ki sai daki na hagu da na dama daga mata kai kawai Hurriya tayi sannan ta bude kofa ta shiga parlon wanda yake dauke da set of turkey chairs parlon ya hadu don har batasan wanda yafi kyau tsakanin na farko dana biyu ba Bata tsaya kallon parlon ba don ganin lokacinta ya tafi don ayyuka ne gareta da yawa don haka ta hau steps din da zasu kaita dakin kasa wanda kamar underground Parlon da tagani akasa saida kam ta tsaya ta gama kallo da yabonshi saboda komai da aka sanya a parlon zata iya cewa abinda ta fiso kenan kamar ita aka tambaya mi takeso ta fadi aka bi zabinta Cikin tafiyar ta mai kama da catwalk ta shiga dakin kallon dakin tayi wanda yake da matukar burgewa ba bata lokaci ta shiga gyarawa da sauri take komai bayan tagama ne ta shiga toilet din ta wanke komai tass Sannan ta fito ta kara shiga dayan dakin shima ta gyara komai da sauri takeyinshi kuma cikin rashin ha’inci don ko ina tayi mashi kalkal Sannan ta shiga dakin karshe tana bude kofar ta lumshe idonta ta dan tsotsi bakinta bude idonta tayi tana kallon ko ina banda kamshin turaren wuta ba abinda mini falon yakeyi Shiga tayi ta fara kakabe komai ba wani bata lokaci tagama sannan tayi mopping ta goge ko ina tass A hankali ta nufi kofar dakin da take kallonta ta bude kallon Komi take na dakin wanda yake fari subahanallah dakin ya hadu kowaye yake da dakin ta jinjina ma fashion sense dinshi Komi is extremely expensive and superb a dakin tun daga wall decors din dake a bango dakin hadaddun paintings ne da canvas masu matukar kyau da tsada wanda ko wani zane is worthing millions ba wani tarkace Sosai a dakin wanda alama ta nuna mata mai dakin bai son hayaniya Tsarin dakin ya taimaka mata wurin reading personality din young master dinta Kallon katon gadon tayi wanda bedsheets din da duvet din duka farare ne saidai daga inda take tana hangen irin laushin da Eskimon yake badawa Lura tayi da Akwai mutum dukunkune cikin duvet din don haka ta shiga toilet dinshi banda kamshi ba abinda yakeyi ta hada komai na wankin ta wankeshi kalkal . Kallon gadon Hurriya tayi tunanin yadda zata gyara wurin take cikin ranta tace why not ki tadashi idan kingama sai ya cigaba da baccin shi A hankali ta nufo saman gadon tunani yadda zata tadashi takeyi saboda batasan sunanshi ba vanity table ta kalla wanda ta hango brush na gashi dauko brush din tayi tazo Daidai saitin kanshi ta dan janye bargon inda taci karo da fuskar Imad yana baccin shi peacefully he looks so cute and handsome kallo daya tayi mashi tasan dan gayune don ko sumar kanshi wadda take acike irin ta gayu tasha gyara don banda salki ba abinda takeyi kallon dogon hancin shi tayi zuwa bakinshi wanda yake pink dan lumshe ido tayi sannan ta bude . brush din dake hannunta ta sanya a saman gashin kanshi tana heyy ka tashi bata fuska yayi sannan ya kara gyara kwanciya Hurriya kam da taga alamar ma dadi yakeji don haka ta maida brush din saitin kunnenshi tana mashi kamar tafiyar tsutsa Imad cikin baccin shi mai dadi yaji alamar Abu na yawo a kunnenshi babu abinda yazo mashi arai irin kyankyaso don shine abinda yafi tsana da tsoro a duniya a mugun firgice ya tashi yana cewa innalillahi wa’ina ilaihi raji’un ya diro yana tsalle yana kallon jikinshi yana dube dube kamar sabon shigar hauka Hurriya kam saura kadan tayi Dariya Amman ta dake yadda ta saba tayi gyaran murya don kwatakwata bai lura da ita ba zaro fararen idanunshi yayi yana kallonta sannan yace who are you Do you want to die banza tayi dashi tamkar yana magana da dutse Don har ta fara cire pillows din domin gyara gadon Ammar da tun dazu ya shigo domin neman tsokana wurin twin brother dinshi Amman wata marar Sa’a ta riga shi he’s enjoying their little drama saidai yana mamakin irin zeal din yarinya how dared she play with a prince dariya ke cinshi Amman yaki barin dariyar tafito saida ya gama kallon komai Amman ya gama jin tausayin ko wacece don yasan halin Imad Sarai don halinsu su uku to daban yake da subira da Imad kuma da Khalifa Qamar to Khalifa ai ba’a sanya shi ma a layi don nashi abun is too much kuma ya dade baya palace din so he can’t say much about him don he can’t remember when last ya ganshi to daman idan anaso Ayi maka hukunci a palace din to dama either akaika chamber din subira ko kuma Imad chamber su biyu nan suna da matsaloli Hurriya kam banza tayi dashi ta cigaba da aikinta don a wurin ta baida amsa ita dama she hate useless talks ta gama gyara gadon tass Imad da yake tsaye yana fuming don bacin ran da yake ciki zai iya karyata idan har batai wasa ba ba’a taba yi mashi irin abinda akayi mashi ba yau tun kam daga yarintar shi Ta shigo mashi daki ba tare da izininshi ba sannan ta tadashi daga baccin da yake mai matukar dadi don ta raina mashi wayau wai kuma da brush ta tadashi sannan bata gaishe shi ba and again yana mata magana tayi banza dashi ko bata iya turanci ba bata iya durkusawa ta fara bashi hakuri tana kuka tana rike mashi kafa Amman shine takeyin kamar ma batasan dashi a wurin ba gaskiya yarinyar nan must have a dead wish because she’s playing with fire Wata tsawa ya buga mata yace ke bakiji ana maki magana ba ko kurma ce Hurriya a hankali ta juyo ta zuba mashi idanunta masu matukar kyau da kaifi kallonta yake tundaga gashin kanta da yake a bude har zuwa fuskarta mai matukar kyau da annuri yace Do you want to die sai kuma ya tuna ba Lallai tanajin turanci ba magana yafaryi mata cikin muryarshi mai dadi kuma da dadin sauraro yace wacece ke? Dan tsotsar bakinta tayi sannan tace Hurriya Faisait Hamood sabuwar mai aikin ka Kin aikata laifuka don haka zaki amshi hukunci da ya kamata yana maganar with arrogance ne and full of himself Hurriya kallonshi take ba tare da ko kyaftawa ba tunda yake babu mai aikin da taba kallonshi ido cikin ido kowa acikinsu yana shakkar shi Amman banda Hurriya wadda take kallonshi kamar yadda Ammar ke kallonshi cikin muryar ta mai dadi da sanyi sai kuma maganar ta wanda yake nuna cewar tana da wani yare na daban tace babu inda nayi laifi tunda nazo a dokokin ance ba ruwana dakai kuma na kiyaye kuma ance bakasan hayaniya kuma banyi ihu ba ance idan kana Bacci kada in tadaka da magana kuma banyi magana nayi amfani da wancan abune wurin tada ka Sharrudan da aka gaya mata duka ta fada mashi shiru yayi yana kallon bakinta wanda yake da kyau da bakin lining a kasa wanda kamar ita ta zanashi Amman haka hallitar bakinta yake Zama yayi saman sofa ita kuma ta fara share wurin da vacum cleaner Ammar ya shigo yana wata irin dariya yana nuna Imad wanda ya rasa miye zaice Hurriya kallonshi tayi taga kamar su daya don suma identical twins ne kamar Neela da liya murmushi yayi mata sannan yayi mata wink bayan tagama komai zata fita tazo wucewa kenan Imad ya tadiyeta ta fadi goshinta da hannunta na buguwa da kyar ta tashi. 🌚Masarautar Qamar By Khadija (KMU) 19&20 Da kyar ta tashi  kallonshi tayi da idanunta masu wani kaifi Dukansu kasa gane expression din fuskarta sukayi she looks fierce and scary ta iya hiding emotion don fuskarta baka iya lura da farin ciki ko sadness ko happiness ta kware wurin hiding emotion dinta don haka fuskarta is neutral saidai idanunta ne suke bashi warning sannan ta sanya kafa ta tafi Because she was done ko mopping din batayi yayi da kanshi. Ammar dariya ke cinshi Amman ganin zallar bacin rai a fuskar shi ya sanya yace Husain waye ya tabaka banza imad yayi dashi ya tashi yaje ya kwanta saman gado ya runtse idonshi Ganin mulki da sarautar tashi ta matso ya sanya ammar ya fita idan ya sauko sai ya dawo Hurriya ranta bace yake Mai mutane suka dauki duniya ne itadai abinda ta sani a rayuwarta da mai kudi da talaka duk Abu dayane da yaro da babba duk Abu dayane da makaho da mai ido duk abu daya ne saboda duka suna amsa sunansu mutane batasan yawan tunani don haka ta nufi dayar chamber din Chamber zinariya kowa kallonta yake kuma ba wanda tayi ma magana abinda ya kaita shi takeyi don Allah ya taimaketa aikin kitchen ne Aiki sukeyi sosai don abinci akeyi kala kala wasu suna gyara inda aka bata wasu kuma  suna jera fruits a trays Hurriya kam wanke wanke kawai takeyi tana kifewa Sun dade suna aiki a wurin kafin a kamalla  Hurriya wuri ta samu tadan zauna Shugabar dake a wurin ta kalli Hurriya tace ku tashi kuje kukai abinci kuma ku tsaya har agama ci saboda idan suna bukatar wani abu Hurriya kallonta tayi ido cikin ido sannan tace bazanje ba daganan nagama aiki sai kuma abincin dare zanzo Amman ba zan kai abinci ba Shiru kitchen din ya dauka kowa yana kallonta baki bude Hurriya ba inda suka tsaya sai inda takeyin wanki tunawa tayi bata wanke kayanta ba don haka ta shiga dakin ta dauko kayan saida ta cire kudinta da sarkokinta da wayarta ta adanasu sannan ta nufi wurin wankin Wata yar karamar yarinya tazo wurin Hurriya kallon Hurriya tayi tace inason ki tayi dariya yan hakoranta na fitowa yarinyar tace kinsan miyasa nike sonki Hurriya ta girgiza kai tana kallon yarinyar tace Aa yarinyar dariya tayi sannan tace saboda kina da kyau shiru Hurriya tayi tana kallonta yarinyar tace kinsan mi ?kinfi kowa kyau a masarautar Qamar Sai kuma ta bata fuska alamar tanaso tayi kuka tace amman banason in rasaki kamar yadda na rasa fareedaa shiru Hurriya tayi don bata gane inda zancen yarinyar ya dosa ba Hurriya wadda bata iya lallashi ba tace kiyi shiru ki daina kuka sannan ta matsa daga gefen yarinyar ta fara wankin Hurriya duk tafi jin dadin aikin wanki kowa hidimar gabanshi yake ba wanda ya damu da wani don haka ba ruwanta da bata miyaun bakinta wurin magana Kayanta ta fara wankewa sannan ta cigaba da wankin da ake kawo mata wanki take sosai ga sanyi Duk sanyi bai dameta ba kamar yunwar da ta dameta don duk yau bataci komai ba wata irin yunwa takeji Imad kallon wayarshi yake wadda banda ringing ba abinda takeyi tun dazu khaleed ke kiranshi non-stop Amman yaki dauka saboda his new Maid has ruined his entire day saidai he made a vowed to ruined her life the way she ruined his mood she really messed with the wrong person wani kiran ne ya kara shigo mashi cikin yanayi na mulki da kuma izza ya dauka shiru yayi batare da yace komai ba Khaled yace kaifa dan rainin wayau ne kaifa kadai muke jira tun dazu don Allah kayi sauri cikin yanayi na mulki Imad yace please I will be there in the next five minutes Ya kashe wayar sannan ya tashi ya shiga toilet dinshi ya dade a toilet din kafin ya fito sannan ya shirya cikin hadaddun English wears dinshi wadanda sukayi mashi kyau Imad na fitowa ya iske Ammar da yake zaune a falon da yake link da bedroom dinshi yana kallon football babu wanda yake da access din shigowa wurin anyhow sai hassan dinshi wato twin brother dinshi Ammar tasowa yayi ya kalki danuwanshi wanda suke da matukar kama sannan ya bashi side hug Tunda ya kalleshi yasan cewar mood dinshi ba Daidai bane don haka yace twin mi yake faruwa dakai ne Don’t tell me har yanzu saboda sabuwar maid dinka kake wannan frowning face din dariya Ammar yayi mai kulewa sannan yace haba young prince kada fa ka bada mu ka saki ranka mana don Allah Zamuyi maganinta ta isa ta taba min husain dina ta zauna lafiya kada kacwani damu i will punish her myself Dadin baki Ammar ya rinkayi mashi har ya samu Imad yayi dariyar da bai shirya ba daman dariyar tashi a iyakar ta wurin Ammar din sai kuma kannenshi shi kuma Ammar daman baida matsala yana da fara’a sosai Fitowa sukayi tare wanda duk bala’en ka baka iya ganesu saboda matukar kamar su don wata irin kama sukeyi ba kadan ba they are identical twins kamarsu har tayi yawa Duk inda suka wuce durkusawa ake ana cewa Allah ya taimake ku Allah ya kara maku nasara har suka fito inda motoci suke parked iri iri cikin hanzari aka bude masu bayan wata red Bentley flying spur sannan bakaken convoy suka biyo bayansu Hurriya kallon kala biyun da idan tagama wankesu to shikenan tagama wankin tayi kololuwa wurin gajiya don daurewa kawai takeyi ga yunwa da take nukurkusarta Tsotsar bakinta tayi sannan ta maida hankalita ta cigaba da wanki shanya taje tayi har ta fara tafiya taji ana mai kyau mai kyau mai kyau tana haki har ta iso inda Hurriya take tasha gabanta Hurriya kallonta tayi kamar zatayi magana sai kuma tayi shiru yar kyakyawar yarinya karama wadda ta zauna kusada Hurriya kafin ta fara wanki dazu tace ina maki magana shine ki kayi shiru Hurriya again batace mata komai ba dariya wasba tayi sannan tace mata sunana wasba kefa ? Hurriya ko kallon inda take batayi ba ta kama gabanta. Wasba kallon inda Hurriya ta bari tayi sannan tayi murmushi ta nufi gidansu dake cikin masarautar. Hurriya kam tundaga nesa taga bakin dakin wurin ya cika yayi fam cike da mamaki ta karaso tana kallon mutanen da suka cika famm kamar hadin baki kuma suna ganinta sauran mutanen duka suka juyo suna kallonta Hurriya kam takawa ta cigabayi a hankali tana karasowa don ita haka Allah yayi ta idanun mutane basu takura mata saidai su kara mata confidence don haka ta tsakiyar su ta ratsa don duk kallon da ake mata ko ajikinta saidai wata fitinanniyar tsawa da aka buga mata wadda ta shiga duk wanda yake wurin Hurriya ita kanta tsawar ta shigeta saidai ta maze ta dago idonta cike da rainin wayau ta zuba ma wanda ya jefeta da tsawar tana zuba mashi idanunta masu masifar kyau. Kallonta yake tundaga tafukan kafafunta har zuwa kan dogon bakin gashinta kallonta yake yana hadiye miyau da kyar Hurriya kam lura da irin kallon da yake mata mai cike da zallar iskanci ya sanya tayi tsoki tace dan akuya maye ta nufi inda zai sadata da kofa saidai bata ida karasawa ba taji an kifa mata bulala mai matukar zafi Juyowa tayi aiko taganshi tsaye yana kallonta da idanunshi wadanda basu da kyaun gani Kallonta yayi sannan yace ke tsinaniya yar gidan matsiyata da ubanwa kike takama dashi duk masarautar nan da har zaki kona ma barira fuska tsotsar bakinta tayi sannan ta kalleshi ido cikin ido tace da ubanka nike takama a masarautar nan tana kallonshi shima yana kallonta wani irin kwarjini takeyi mashi don kwata kwata taki sauke idonta har lokacin idonshi na cikin nashi Kowa kallon dramarsu yake ana jiran kaura ya jawota yayi mata dukan da bazata iya gane ko kanta ba bare har ta zagi kaura ko ta kona mashi budurwa Shikam kaura he was lost in thought because he had never seen a beautiful human being like her she’s beautiful beyond words she’s just beautiful yadda take komai yake sanya mashi ganin kyauwunta gyara tsayuwar shi yayi domin ya bugeta kawai saiga kuyanga daga sashen Imad Kallonsu tayi tace mi yake faruwa ganin duk sunyi shiru ya sanya ta kalli Hurriya tace muje hakimi na kiranki Hurriya ba wanda ta kalla acikin su tabi kuyangar Suna zuwa suka shiga chamber hakimin wanda yana can ciki kwance a saman sofa Abinci ya gama ci sannan ya sanya aka fidda mashi kwanonin abinci wayarshi yake latsawa kafin bacci ya daukeshi mai matukar dadin gaske Hurriya kam tunda ta sanya aka gaya mashi Amman har lokacin bataji anyi mata iso ba don haka taje balcony ta zauna tayi shiru tana kallon masu wucewa Duk kuyangin dake wucewa kallonta suke da mamaki irin kujerar prince kika zauna tabb kina ruwa ba wanda ta kula bare tayi mashi magana Lumshe idonta tayi sannan tayi crossing legs dinta banda yunwa ba abinda takeji don duk wunin ranar bata sanya ma cikinta komai Baccin gajiya da taji ya fara daukarta ya sanya ta tashi ta koma ciki kitchen din ta shiga wanda tayi sa’a ba kowa kallon kulolin abinci tayi wanda aka jera abinci ne a table din kitchen island ba tare da bata lokaci ba ta shiga budewa abinci ne kala kala ga yankakun fruits wani plate mai kyau ta jawo ta zuba abincin ta faraci ahankali saida taci ta koshi don wanda ta rage baifi ace loma daya ba wanda har ta koshi sosai Mama RaBI ta shigo kitchen din tare da zubaida dukansu bude baki sukayi da mamaki suna kallon Hurriya da tagama cin abincinta hankali kwance salati mama rabi ta farayi tana kallonta sannan tace waye ya baki izinin cin abincin nan kinsan abinci waye kuwa kallonta Hurriya tayi da idanunta masu haske ba tare da tace komai ba ta dauki ruwan da yake jere a saman tray din ta fita. Mama RaBI kam ba’a tabayi mata irin abinda Hurriya tayi mata ba Kallon zubaida tayi wadda har lokacin bakinta bude yake sannan tace wai ina aka samo wannan shegiyar yarinyar ne mama rabi kinga wani kallon banza datayi maki sannan ta juya ta tafi shiru mama rabi tayi sannan ta Sauke ajiyar zuciya tace lallai yaro baisan wuta ba sai ya taka sannan ta kyalkyace da dariya zubaida wata dariyar gefen baki tayi itama sannan suka bar wurin Mama RaBI taji haushi sosai da hakimi bai basu fuska Ko kara bai basu damar wani ya kaimashi bare munafunci da tsaegumi Da wallahi sai tagaya ma Imad kaskantaciyar mai-aikin shi taci mashi abinci kwata tayi sannan tace ajuri zuwa rafi watarana tulu zai fashe Hurriya tafiyar ta Tayi wanda gari har ya fara duhu magrib ta gabato saida tayi tafiya mai nisan gaske sannan tazo bangarensu ta shiga Ta gaji sosai don ba abinda take bukata irin tayi wanka tayi bacci kallon bintu da take zaune tana hamma tayi wanda dama ga dukkan alamu Hurriya take jira Wuri ta samu ta zauna Bintu ta kalleta tace sannu Hurriya kindawo ne kinci abinci ? Daga mata kai Hurriya tayi batace ma Bintu komai ba Bintu kallonta tayi hamma tayi sannan tace saida safe daman jiran dawowar ki nike bari in tafi har ta juya tajiyo sautin muryar Hurriya daga bayanta tace kinci abinci da wata irin murna Bintu tajuyo tace naci a hankali Hurriya ta zaro naira dari biyu ta mika mata Bintu amsa tayi tana kallon Hurriya domin jin karin bayani lumshe idonta Hurriya tayi sannan ta tsotsi bakinta saida ta dauki lokaci sannan ta bude idonta masu kyau ta zuba ma bintu su tace idan kina bukatar wani abu ki siya can kasan makoshin tace ki kula da kanki sannan ta kara rufe idonta kamar mai bacci Bintu murmushi tayi tana kallon Hurriya da zallar kauna a idonta wadda idonta suke rufe dan tsalle Bintu tayi kamar karamar yarinya tace Ina kaunar ki Hurriya sannan ta juya ta tafi dakinsu Saida Hurriya taji tafiyarta sannan ta mike ta nufi babban kitchen din da ake dafa ko wani irin abinci Dubawa tayi ko zata ga matar jiya saidai akasin haka baba haule reza tagani don duk tafi kowa zama kusa da ita don haka ta nufi wurinta da bokitin baba haula reza kallo daya zakayi mata kasan cewar masifarfa ce ta ajin karshe Hurriya bokoti ta ajiye ahankali sannan ta kalleta in a commanding tone tace ruwa zaki zuba min Baba haule reza ta dago idonta a kankance ta fara surfa mata ashariya Hurriya bata janye idonta daga kallonta ba kuma batace mata kala ba Har saida tagama kumfar bakinta kowa kallon baba haule reza yayi acikin kitchen din sannan kowa ya cigaba da hidimar shi don inda sabo ta saba Hurriya saida ta tabattar da cewar baba haule tagama masifarta sannan ta zaro naira dari ta ajiye mata tana kulleta da idonta Baba haule kam kamar an daure mata baki don dauke darin tayi a inda Hurriya ta ajiye tana saka kudin cikin skirt dinta Bokitin ta janyo ta zuba ma Hurriya ruwan zafi masu yawan gaske ba tare da Hurriya tace kala ba taja bokitin ta nufi toilet ta gasa jikinta sosai da ruwan zafi. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar A story about a mysterious palace By Khadija (KMU) Page 21&22 Bata wani dauki lokaci sosai ba ta fito daga toilet din tana mai ya mutsa fuskarta don duk batajin dadi don kayan dake jikinta sune ta maida dalili kam da akwai zanen tatoo a bayanta bata kaunar ko wani dan mutum yaga tatoo din sam she’s not comfortable cikin masarautar Qamar don kwata kwata batada yancin dan adam kuma ita a rayuwarta ba abinda takeso irin yanci don haka ta tashi a rayuwarta tunda ta taso ba wanda ya taba depriving right dinta tanada ko wani irin freedom Tana da matukar tsafta don kaya basu iya mata 24hrs ajikinta bare kuma ace kuma tayi wanka ta maimaita kaya saidai da ace ta fita da daurin zani wanda duk zanen dake bayyane a bayanta zai bayyana ga idon mutane gwara ta maida kayanta Don haka da kayan ajikinta ta fito sannan tayi alwala ta shiga dakin Cikin natsuwa ta Cire kayan jikinta kallon inner wears din da ta siya dazu dasu sabulun wanka da brush tayi har da turare mai sanyi kamshi batasan ana kasa haja ba sai dazu da safe inda har tazo wucewa taga haule reza ta kasa kaya masu kyau har ta wuce ta dawo haule reza ba abinda bata saidawa saida Hurriya ta bata kudi sosai wurin siyen abinda takeso don saida ta tabbatar duk abinda take bukata ta siya sannan ta nufi bangaren Imad under wears ta sanya masu kyau sannan ta shirya cikin wata blue half gown da iyakarta gwiwar kafarta ta tsaya doguwar hijab dinta ta sanya sannan ta kabbara sallah rama sallolinta tayi duka bayan tagama sallarh ta kishingida jikin katifar ta lumshe idonta ba bacci take ba Amman dai tayi lamo Sunanta taji ana kira saidai ko motsawa batayi ba bare tayi tunanin bude idonta saida tayi mintuna Sosai kafin ta bude idonta ta zuba ma zubaida su da take tsaye wanda tagama kulewa don tunda tazo tasan ba bacci take ba Amman don bakin rainin wayau ace tanajinta tayi shiru ta kyaleta Zubaida ta kalleta tace Lallai ma Hurriya shine zaki zo ki kwanta wakike tunanin kinbar ma aiki sai ki taso tunda ba bayi kika ajiye ba Don ana bukatar ki a Aikin dare shiru Hurriya tayi batace kala ba don yaddda tayi kamar ma da dutse ake maganar Hurriya magana fa nike inji zubaida shiru Hurriya tayi saita lumshe idonta Zubaida kam iya jin haushi takai don cikin zuciyarta banda la’anar Hurriya ba abinda take saidai tayi mata wani irin mugun kwarjinin da bata iya maida mata magana Gajiya tayi da tsayuwa zubaida taja tsoki tayi tafiyar ta Hurriya kam shiru tayi don saida tayi kusan minti talatin kwance idonta kuma rufe kamar mai bacci Tashi tayi ahankali cikin yanayin natsuwarta ta sanya takalminta ta fita A hankali take tafiya wadda idan ka kalli yadda take tafiyar zaka dauka jinin sarauta ce dogayen kafafunta da suke bude sai salki suke sai tulin bakin sumarta wadda baka iya ganin jelar gashin saidai kwantaccen gashinta wanda ya fara tundaga goshinta farin wata ya haskata wanda ya taimaka wurin fito mata da tsantsar kyau na hallita duk wanda ya kalleta ya kara kallonta yasan mai kyau ce wato mai asalin kyau Kallonta ake gabas da yamma kudu da arewa duk da kasancewar darene Daidai saitin su barira da suke zaune a tabarma suna shan rake tazo zata wuce tanajin duka idanunsu dake yawo a kanta Amman ko a kwalar rigarta ta cigaba da tafiya tayi abunta Muryar Hansa’u ce ta doki kunnenta wadda take cewa barira gafa mutuniyar Barira shiru tayi tana kallon bayan Hurriya da dogayen kafafunta lashe baki tayi ta gyara zamanta batace komai ba Wasila ce tace har yanzu bamu dauki fansar abinda tayi maki barira ba Amman na rantse bataci banza ba Don ko yadda ta bata mana suna sai mun gyara mata zama sai na wulakanta yar matsiyaciyar can wulakanci mai muni sai kuma na hada mata tuggun da bazata iya warwareshi ba duka rayuwarta a masarautar nan sai na wulakantata wulakanci mafi wulakanci sannan in kaskantata kaskanci mafi kaskanci Sannan tazo har gadon baccinki barira sai yadda kikayi da ita Dukansu dariya suka sheke da ita tare dayin na’am da alkawarin da tayi kuma Dukansu sunce zasu tayata Hurriya duk tanajin abinda suke cewa duk da kam tafiya takeyi kuma tayi masu nisa kallon sakarkaru marar sa aikinyi tayi masu ta cigaba da tafiyarta Saida tayi tafiya mai nisan gaske kafin ta kawo chamber Imad Ahankali ta shiga kitchen din wanda tana shiga kamar hadin baki duka ma’ikatan da suke aiki a kitchen din suka jiyo suka kalleta acikin su ba wanda bai bude baki ba yana kallonta ba tunda daga sama har kasa Amman Hurriya shin ita ko ajikinta don idanun mutane basu daureta kwata kwata ko alama itadai Allah ya bata wani irin confindence wanda ba ko wani dan mutum yake da irinshi ba Hurriya bata fasa tafiya ba don tsakiyar kitchen din tazo sannan sai taga tukunyar da ake shredded beef din don haka cikin natsuwa taje ta fara motsa tukunyar Zubaida ce wadda ta kasa yin shiru cike da rashin kunya da wulakanci tace wai casu zaki ko coci Hurriya dagowa tayi ta zubama zubaida idonta masu kama da zaiba sannan ta tsotsi bakinta a hankali tace casu zamuje nida tsohuwarki da tsohonki idan mugama sheke aya sai mu tsaya ta coci muyi ibada Tayi maganar hankali kwance tana kallon kowa acikinsu wanda fuskarsu take dauke da mamaki Dukansu ba wanda bai saka wani abu acikin ranshi ba Wasu kuma cewa suke daman tana magana? Hurriya bayan ta tabbatar da shredded beef din yayi ta juyeshi a cikin food flask sannan ta dauki tukunya ba abinda ba’a nuna mata ba a bayani don haka tasan inda komai yake Ruwa ta zuba a tukunya sannan ta shiga store ta debo basmati ta kunna gas ta daura tukunya hadaddiyar biryani tayi masu don tana abincin tana rera waka nike gani tanayi tana dan juya kugunta har ta gama don kamar abincin na tura mata memories don tana enjoying Tazo ta kwaba pancake dinta ta soyashi mini sannan ta dauko chocolaté tayi dizzling dashi Tana aikinta tana wakarta tanajin idanunsu a kanta Amman kamar babu kowa a wurin Saida tagama yin komai ta dauko kula ta juye don abinci bai dauki wani lokaci ba tagama saboda karfin gas din dake da ci sosai Hadawa tayi a tray don dakanta ta jera hada wanda mama rabi tayi da wanda tayi don abinci suna da matukar yawa mutum ashirin zasu iyacin abinci don different varieties of food ne a wurin Bayan tagama sai ta nufi hanyar fita mama RaBI kamar tasan niyyarta don haka tace Hurriya kune zaku tsaya har su hakimi sugama cin abinci koda suna bukatar wani abu sai ku mika masu Bata matsa ba kuma bata dawo ba Amman ga dukkan alamu maganar ta shigeta zubaida da mama rabi da wasu kuyangu guda ukku suka fara fitar da tray din abincin da drinks da wasu manya manya non alcoholic wines Hurriya zuwa tayi ta dauki trays din wanda yake cike da wasu matsiyatan plate ta shiga parlon saida ba kowa a parlon it looks like Dukansu suna parlon gaba don haka Bata wani Bata lokacin ba ta shiga ba excuse ba sallama kallon mutanen dake zaune a tsakiyar parlon tayi duk twins ne kusan set uku masu matukar kama da juna. Liya wadda ta daura kafafunta saman jikin Neela in an annoying way itace ta fara lura da Hurriya kallonta take from head to toe shiru tayi batace komai ba duka sauran hankalin su yana akan abinda sukeyi Neela hankalinta duka yana Akan wayarta sai Amrah da imran da suke playing ps 5game duka hankalisu yana a wurin game din Liya kam satar kallon Hurriya kawai take wadda take jera abinda ta shigo dasu a dining kutt The girl is unparalleled beauty su zubaida duk sun dukar da kansu da kuyangin da suka shigo tare Kallon kafafunta wanda suke bude tayi tana kallon sumarta da take bude fuskar nan a hade take kamar an aiko mata da sakon mutuwa tanayi tana cije lebe wanda ga dukkan alamu sararta ce Liya kasa janye idonta tayi daga kallon Hurriya don tunda take masarautar Qamar bata taba ganin halitta mai kyaun Hurriya ba saidai gabanta ne yayi mugun faduwa tunawa da tayi ana jita jitar cewar masu kyaun masarautar su mutuwa sukeyi don ko a ma’aikata indai matane to ba’a cika kawo marar sa kyaun hallita ba saidai tunda take bata taba ganin Mai kyaun da ta kama kafar Hurriya ba wane subira an dade acikin masarautar Qamar ana bama subira sarauniyar kyau Amman wannan yarinyar tayi ma subira fintinkau don indai za’a hada kyaun subira da Hurriya to subira zata iya samun 30percent ita kuma Hurriya 70percent Babu abinda Allah ya rageta dashi don ita jikinta irin na models ne wanda turawa suke iya barnar da ko nawa ne garesu saboda su mallaki irin jikinta Sauke ajiyar zuciya tayi farar daya tausayin yarinyar yana kamata don tana da kyaun da ba kowani namiji bane zai iya dauke ido akanta ba sai kuma babban kalubalen dake masarautar duk da jita jita ne Amman ta dade tana tunanin anya abun ba gaskiya bane don itama ta rasa ma’aikantata Sosai wanda suka shaku kuma ta saba dasu saidai duk idan hakan ta faru akwai abinda jakadiya take fada mata saidai tun tana yadda har tazo tana putting Question mark. Imad ne ya shigo kallonsu yayi Dukansu sannan yace guys let’s eat dinner ku tafi kubar min part dina don duk kun cikamin part dina Ammar ne ya ajiye wayarshi wadda take hannunshi sannan yazo Daidai inda Imad yake ya dafa shi yace ya akayi ka kosa MU tafi kodai kodai sannan ya fashe da dariya Imad daure fuska yayi dagajin maganar Hurriya don yarinya ta bata mashi rai kuma ta rainashi shida ma’aikatan masarautar Qamar ke shakkar shi Amman yarinya yar Qarama tana Neman rainashi har sanyawa fa yayi a kira mashi ita kuma dagagan ya shanyata so yayi sai tayi awa goma tana jiranshi amman tayi tafiyarta idonshi idon Hurriya Amman sai yayi mata wukanci Dariya ammar ya cigaba dayi yace kodai har ka folla ne? Naga yarinya is beautiful ya ida da maganar da wata irin dariya Neela itama dariya tayi tazo saitin ammar tace who’s the girl dan dungurinta ammar yayi sannan yace magulmaciya yace ban fadi sannan yayi mata gwalo Dariya Liya tayi sannan tazo saitin ammar itama tace who’s the girl bro please tell me kasan ba ajin kanmu dariya yayi sannan itama ya dungureta yace magulmata bazan fada ba Dukansu tare suka jero sai yan kananun kannansu wadanda suke uwa daya uba daya masu bala’en kyau Amrah da hamdan kenan miskilai ne na karshe kuma yaran da basuyi ma kowa magana don duk da irin tsantsar kauna da take zagaye dasu wurin yayyayensu wadanda suke jinsu kamar kwai to idan ba yayyensu ba wanda sukeyi ma magana sun shaku da yayyansu Sosai saidai sarauta ajinisu take don wata sa’in miskilancin su harga yayyansu don tunda sukazo dinner a chamber imad wadda ta kasance duk sati sukeyinta saboda kowa yanada sashen shi to suna dadewa basu hadu ba sai Ammar ya kawo shawarar every Friday night suyi arranging cin abincin dare tare tohm haka sukeyi dukk satin duniya sai kuka suji damuwar junansu Tare suka iso katon dining din wanda yake cike da abinci kala kala zubaida kansu a kasa suka farayi masu kirari Allah ya taimake ku Allah ya kara maku nasara sunata yi masu kirari Duk acikinsu ba wanda ya amsa masu don ko kallon inda su zubaida suke basuyi ba zama dukansu sukayi ta Liya ce ta juyo tace masu we will serve ourself Hurriya tana tsaye tana kallonsu ita ba wanda tayi ma magana Liya dai na kula da ita su Imad hankalisu ma bai kai kan ma’aikatan ba bare suga Hurriya don su ma’aikatansu ko kallo basu ishesu ba. Hurriya tsaye tayi tana kallon kowane acikinsu ba tare da ta dukar da kanta ba Hamdan ne ya dago idanunshi daga kan iPad din dake rike a hannunshi cikin sa’a kam ya saukesu akan Hurriya da take tsaye fuskarta babu annuri kallonta yake Ko kyaftawa bayayi itama kallonshi take cikin idanu Neela ce ta kalli Amrah tace ki ajiye iPad dinan muci abinci turo baki Amrah tayi sannan ta ajiye iPad din muryar hamdan ce ta doki dining din dasuke yace you alamar yana kiran wata Dukansu yayyanshi dagowa sukayi suna kallon wadda yake kira kasancewar shi ba mai yawan magana ba don sukansu hardly ne su ji maganar shi saboda miskilancin shi Hurriya da take tsaye tasan da ita yake kallonta yayi sannan ya kara nunata da yatsa still banza tayi ta kyaleshi tana zuba mashi idanunta Imad wanda shima hankalin shi nakan wayarshi ya dago ya kalleta saida ya kalleta tundaga farko har karshenta aranshi yace Lallai ma yarinyar nan waye zata burge tazo masu a haka kamar zata club saidai bai iya yaudarer zuciyar shi ba Amman yarinyar gaskiya tana da kyau toh kila shiyasa take raina ma mutane wayau amman bari zaiyi maganinta aiko nan take ya bata rai ya hade fuska yana kallonta Ammar wanda shima kallonta yake bai ko kyaftawa saida ya tabbatar ya saisaita kanshi sannan ya kalli Imad da yake ta cin magani ya kwashe da dariya Hamdan ahankali ya karayi mata magana yace please come and join us banza ta karayi dashi Imad ne ya tashi ranshi bace Ammar yayi saurin rikeshi yana dannah dariyar shi Amrah ce ta taso tazo saitin Huriya cikin muryarta ta yarinta tace kizo muci abinci tare don Allah tana pleading dinta da hannu in a cute way Hurriya kallon yarinyar tayi mai bala’en kyau amman kallo daya zakayi mata kasan akwai kadaici tattare da ita shiru Hurriya tayi tana kallon hamdan da amrah wanda shima ita yake kallo da alamar tazo tayi joining dinsu Neela ce ta kallesu ta bata fuska sannan tace what are you doing Amrah Amrah bata fuska tayi haka zalika hamdan Liya ce ta taso tazo saitin Hurriya sannan tace please join the poor babys they love you Hurriya daga mata kawai tayi ta zauna family dinner din Zubaida kam kamar ta mutu saboda bakin ciki yarannan da basu tabayi mata magana ba don yaran Allah ya zuba masu mulki da sarauta basu kula kowa gashi yayyansu kamar su cinyesu haka sukejin su aransu idan sun soka tohm tohm yayyen sun soka idan sunki ka tohm suma sunki ka Hamdan ne ya kalleta cikin mulki da sarauta don kusa da kujerar da yake tazauna ahankali yace mata you’re beautiful shiru wurin ya dauka kowa yana saka Abu aranshi Imad kam zuciyarshi banda bugawa ba abinda takeyi saboda tsanin bacin rai Imad magana zaiyi Amrah ta rigashi ta hanyar dawowa saitin Hurriya tace ya sunanki please?hurriya kallonta tayi da idanunta masu kwarjini Amrah dafe zuciyar ta tayi ta hanyar cewa please stop looking at me like that way,you look intimidated .i know you’re more beautiful when you smile ok can you smile for me just once tana mata wink Hamdan dariya yayi wadda ta fito tundaga zuciyar shi sakin baki su Ammar sukayi suna kallon kannansu yare Hamdan yayi ma Hurriya ta hanyar cewa zaki bani diyarki idan kika haihu you’re beautiful but you’re lonely ta ko ina gaban Hurriya ne ya shiga faduwa tana kallon hamdan da ya tsare ta da idanunshi yana jiran amsarta Rabon da taji kalar yarenan har ta manta innallilahi wa’ina ilahi raji’un ta shiga furtawa cikin zuciyarta wadda take duka kamar ganga rabon da ta ambaci sunan Allah rayuwarta ta manta saidai acikin Sallah wadda batada tabbacin tana amsuwa ko bata amsuwa Hamdan ya saki wani killer smile wanda idan ka kalleshi zaka iya cewa babba ne wanda dudu shekararshi sha biyu a duniya shida twin sister shi Saidai Allah yayi mashi baiwa wadda ake kira wato smartness Shiru duka wurin ya dauko suna kallon Hurriya da Hamdan murmushi Hamdan yayi yace mata you look like princess Layla Al-Khasheem she’s my role model because speech dinta yana matukar taimakona did you know her ?dan murmushi yayi sannan yace i know you will not know her saboda celebrity ce a duniya baki daya duk wanda ya kalli Hurriya alokacin zaisan a tsoroce take don sam takasa boye firgicin dake fuskarta salati take Sosai acikin ranta Amrah ce tace she really look like Layla Al- khasheem sai yanzu da ka fada na lura Ammar ne ya kalli Hurriya yace sunyi kama Sosai ya sakar mata murmushi tare da cewa you look like Layla Khasheem daga yadda yayi maganar zakasan cewar Dukansu suna kaunarta don liya itama washe baki tayi Hurriya kam duk ranta ya jagule don kamar tana zaune saman kaya ko garwashin wuta haka takeji tsoro da fargaba suna kara cikata tanajin saukar idanunwan kowa akanta Amrah ce tazo saitin Hurriya tareda dafa mata kafada tace mata can you be my friend da wani irin karfi Hurriya ta ture ta ta fadi kasa fuskarta na nuna zallar bacin rai tace wa ya baki damar taba ni tana binta da idanun masu nuna zallar bacin rai saidai tana kokarin saita kanta saboda batasan yanayi fuskarta ya canza saboda da wuya Hurriya ta canza yanayin fuskarta zuwa damuwa ko farin ciki ko firgice ko kuma gazawa ko gajiyawa da rayuwa fuskarta akoda yaushe a yanayi daya take wato ta daurewa wadda za’a iya kiranta bata da mutunci Imad ne ya tashi yazo Daidai saitin Hurriya wadda take idonta har wani jaa yake kawowa Shima imad din rannshi a matukar bace shida neela zuwa yayi zai dauke ta da mari Ammar yayi saurin rikeshi Imad please don’t touch her ba tarbiyya bane dukan mace. Hurriya Dukansu kallonsu tayi ba tare da tace masu komai ba ta fita daga dakin Hamdan ne ya ruga zaibita Liya ta rikeshi Amrah kam kuka takeyi sosai wanda yasanya duka hankalin su ya dawo kanta Neela ta rungumota tana lallashinta Ammar shima lallashin yakeyi Imad tashi yayi ya shige daki zuciyarshi na tafarfasa sannan ya barsu a parlon Hurriya har bata ganin gabanta da kyar take tafiya ga dare da yayi ga sanyi ga fargaba abubuwa duk sun hade mata Da kyar ta kawo kanta dakinsu tsitt kakejin ko ina adakin wani irin shiru wurin ya dauka don da yawansu sunyi bacci . Ahankali ta kwanta tare da lumshe idonta tana fadawa duniyar tunani tambayoyi take ma kanta ina wannan yaron ya iya yaren Amarich sannan yace suna kama da Princess Layla Al-Khasheem shin har yanzu kamarsu a bayyane take itada Layla Zuciyar tace ta buga don tana tsoron kalubalen da zata iya fuskanta nan gaba idan har identity dinta ya fito fargaba tsoro kadaici duk sune suka suka cikata Bacci ne ya fara fizgarta Mai cike da gajiya ahankali baccin ya fara nauyi saidai saukar Ruwa mai matukar sanyi ajikinta ne ya sanya ta farkawa da sauri kuma a firgice bata Ida warwarewa ba taji an kara zuba mata ruwan mai matukar sanyi ga yanayin sanyi irin na farkon January Rungume jikinta tayi idanun ta da hakoranta na gab gab wani ruwan taji ankara zuba mata mai matukar sanyi numfashinta ne ya fara ja yana dawowa kirjinta yana wani irin duka gab gab kankame jikinta ta karayi numfashinta na rage sauri dariya suke a kunnenta suna ihu suna kashewa Tafiya su barira sukayi suka barta tana kokarin saisaita numfashin ta saidai mi ba abinda take gani irin past dinta rayuwarta ta tabaya yadda kawunta yake zuba mata ruwan kankara yana dukanta ne ya dawo mata kanta ne ya farayi mata wani irin nauyi sai wani irin duhu da ta fara gani sannan numfashinta ya dauke. Hello readers ya kuke tunanin salon labarin namu Ya akayi Hamdan yayi wani yare wanda Hurriya kadai takejin yaren Miye tsakanin Layla Al -Khasheem da Hurriya Faisait Hamood Ga Amrah da Hamdan da suke tsanin son Hurriya mi yasa suke sonta? Ga Barira da suke barazanar tsoma kansu a rayuwar Hurriya anya basu debo ruwan dafa kansu ba Ga wasba yar yarinya Karama da Hurriya ke burgeta Miye yake faruwa ne da kyauwawan masarautar Qamar wanda ya sanya ake kiran masarautar da mysterious palace Wacece Hurriya? Ku biyoni cikin labarin masarautar Qamar a hankali komai zai warware. Waye star dinmu a maza? Shaho,Kumurci,imad ko Ammar kuma Hamdan Muje zuwa kawai don salon labarin namu ya bambamta da kowani irin labari. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar A story about a mysterious palace By Khadija (KMU) 23&24 Kwance take male male cikin ruwa mai matukar sanyi wanda kwata kwata bata ko numfashi ba wanda ya lura bare ya ankara Da kyar suka lallashi amrah aka sanya kuyangu suka tafi da ita chamber dinta Mai matukar kyau da daukar ido ruwan wanka Neela tazo ta hada mata ta fito mata da kayan bacci sannan tayi mata addu'a tare da kashe mata wuta Liya kam tare suka tafi itada Hamdan don ba wanda yace ma dan uwanshi komai har suka isa chamber dinshi Ammar shima chamber dinshi ya nufa ya haye saman gado tare da lumshe ido yana tunanin duka abinda ya faru yau so yake ya hada komai wuri daya don samun ma'anar abun saidai ya kasa hada komai Amman yarinyar tayi matukar bata mashi rai donmi zata ture Amrah shiru yayi yana tunanin kilan tana da uziri don kowa da uzirinshi. Karfe 5:44 Allah ya kawo Bintu domin tada Hurriya sallah asuba saidai ganinta kwance ya sanya ta fasa ihu agigice tazo tarinka tadata tana Hurriya Hurriya ki tashi don Allah ki tashi ki daina bani tsoro inna lillah wa'inna ilaihi raji'un Bintu ta shiga furtawa tana bude ma Hurriya ido Amman shiru Ruwa ta debo da sauri ta yayyafa mata tare da shafa mata a fuskarta bude idonta Hurriya tayi wanda sukayi matukar jaa wani seizure numfashin ta ya fara tana tari mai sarkewa don kamar zata mutu haka numfashin yakeyi ga kuma tarin yaki sassauta mata Bintu banda hawaye babu abinda yake kwarara daga idonta don ta rasa mi zatayi wanda zai taimaka ma Hurriya saidai kukan Kirjin Hurriya taga yana sama yana kasa numfashinta yazama abnormal don abinda take yafi nada bintu sakinta tayi ta ruga ta fita aguje ta rasa ma inda zataje watar yar matashiyar budurwa tagani tace mata don Allah akwai likita anan yar budurwa tace Akwai inna hanne mai bada taimakon gargajiya idan ansamu mararsa lafiya godiya kawai tayi mata batasan ya akayi ba sai ganin ta tayi a kitchen. ganin kanta a kitchen datayi ya sanya ta fashe da wani irin kuka inna hanne ce ta kalleta tace ke kuma lafiya kike mana sintiri kina kuka Bintu zuwa tayi ta rike mata kafafunta tace ki taimaka mani ki ceci rayuwar Hurriya ta kusa mutuwa ki taimkeni yatsine fuska hanne tayi sannan tace wacece kuma haka Hurriya yar doguwa mai kyau tureta hanne tayi tace ni likita ce da zaki zo ki tsareni da magiya Ki taimake ni don Allah ko nawane nayi maki alkawarin idan ta warke zan baki shiru hanne tayi tana tunani kafin ahankali tace muje. Barira dasu wasila ne sukaje wurin da Hurriya take yashe kwance Hansa'u ce ta ture mata dogayen kafafunta ahankali Hurriya ta bude idonta wanda suke rufe hakoranta suna gab gab kirjinta na sama na kasa binsu take kawai da kallo dariya suwaiba tazo tayi tana take mata yatsun hannunta ita kuma barira ta take dayan hannun da nuna itadin watace tayi dariya tace yau zan kwanta da wannan kaskantaciyar baiwar sannan na sanya a farfasa mata jikinta sai inbi tada gishiri a ko ina kuma kullum kowa da kowa acikinku zai kwanta da ita sannan zansa bawa mafi muni da kaskanci ya kwanta da ita ta fasa wata dariya  su Hansa'u suma sukayi dariya Hansa'u ce ta kalli barira sannan tace ina fatar a aske mani gashi kanta murmushi barira tayi sannan tace angama Wasila ce ta fashe da dariya tazo ta haye Hurriya tare da kama hannun rigarta zata farka mata riga Hurriya kam ta kanta takeyi don numfashinta kiris ya rage ya kara daukewa Amman tana cikin tsananin tsoro don tabbas idan har ta bude mata baya dolene taga zanen tatoo din dake da tambarin daga inda ta fito nobody is allowed to see the tatoo idan ba haka ba rayuwarta will be at more risk don tatoo din shine yake rike da sirrin ko ita wacece miye zai faru da ita idan wani yaga sirrin dake Zane abayanta Shiru tayi zuciyarta da kirjinta na wani irin bugawa hannun rigar aka farke wanda hakan ya kasance daidai da daukewar numfashinta. Bintu da inna hanne da suka shigo yanzu wanda yayi Daidai da daukewar numfashin Hurriya da kuma ida farkewar hannun rigarta Wani irin kyakyawan mari inna hanne ta dauke wasila dashi tana binsu da wani irin matsiyacin kallo rike kuncinta wasila tayi ta fita daga wurin a hankali Hansa'u ta bita a baya sauran ma Dukansu suka bita a baya duk a masarautar nan ba wanda Suke tsoro irin inna hanne da reza dan daya hatsabibiyace daya kuma fitinaniya ga uban karfi Bintu kam rungume Hurriya tayi tana kuka inna hanne ta kalleta tace ta fita ta debo masu ruwan zafi Bintu ta tafi don samo ruwan zafin Taba Hurriya inna hanne tayi saidai abinda tagani saida ya girgiza ta daman har yanzu tanada aljanun da suka so bude mata ido kenan to mi ya kawosu miyasa suka karantar da ita bayanin Hurriya abinda rabon da tasan wani abu game da rayuwar wani andade Inna hanne kallon Hurriya take tana tunanin abinda tagani tattare da rayuwar yarinyar lallai Hurriya tana cikin hadari acikin masarautar nan don irin duhun da tagani da kalubalen dake lullube da ita sunan Allah kawai inna hanne take fada don ta dade bata ga Abu irin haka ba Don kwata kwata aljanun da suke son bude mata ido sun tafi tare da karfin ikon Addu'a da azkar don bata ganin komai tafi shekara goma rabonta da budewar idon jinnu sai wannan karon mi hakan yake nufi Akwai matsala babbar matsala tattare da rayuwar yarinyar nan A hankali ta daga rigar Hurriya a firgice tace masarautar Heral Inna lillah wa'ina ilahi raji'un ta ambata tana kallon zanen tatoo din Hurriya dake kwance agadon kafadarta ta baya kenan itace yarinyar da kusan shekara biyar dasu ka wuce akazo ana nema don kusan ko wace babbar masarautar dake duniya anje don harda masarautar Qamar akazo tare da alkawarin duk wanda ya samota akwai gagarumar kyautar da za'ayi mashi don dashi da zuri'ar shi hatta tattaba kunnenshi sun gama talauci saboda irin zunzurutun abinda aka alkawarta sannan kuma idan nameji ne zai aureta tare da nadashi sarautar kasar baki daya Shiru tayi tana hasko Labarin irin masarautar Heral da ake basu irin mulkin da akeyi da irin tarin arziki da daular dake shimfide a cikin kasar don masarautar na daya daga cikin jerin masarautar duniya da ake ji dasu Shiru tayi tana tunanin duhun da tagani tattare da Hurriya wanda ba'a masarautar Qamar kadai ya kare ba hatta masarautar Heral din idan ta koma zata fuskanci kalubalen da kilan zai iya sanadin rayuwarta don ko masarautar Qamar din Qalubalene da zai iya sanadin rayuwarta ko kuma ya tarwatsa mata duk wani farin ciki na rayuwarta wanda yarinyar ga dukkan alama ta dade ba farin ciki rayuwarta Inna hanne ta sauke ajiyar zuciya tana kallon kyakyawar fuskarta tana nazarin dalilin da aljanunta sukayi nuna mata bayanin Hurriya yarinyar abar tausayi ce saboda zagaye take da makiya  Amman In Sha Allah zata taimaketa da addu'oi Sosai da azkar masu matukar muhimmanci saboda tasan tsafin da akeyi a masarautar Qamar Bintu ce ta shigo aguje da ruwan zafi sannan ta ruga aiken da inna hanne tayi mata don amso mata magungunan hausa Bintu bata wani dauki lokaci ba sai gata da magungunan Kallon Bintu baba hanne tayi tace ta dan fita Bintu batayi musu ba ta basu wuri Maganin ta hada mata na lamoniya hade da sanyi sannan ta bude bakinta ahankali ta shiga bata don ko motsi batayi rabin maganin na shiga rabi na fita baba hanne kallonta take cike da tausayinta don itadai tunda ta taso rayuwarta A daji kuma babansu magani yake badawa itama har ta gaje shi to bata taba cin karo da makamanciyar lamoniya irin wannan ba Bayan tagama bata magani ta samu farin tsumma mai kyau sannan ta shiga gasa Hurriya da ruwan zafin Tana dora hannnunta ajikin Hurriya ta zabura Haka ta rinkayi da ta taba mata jiki sai ta zabura saida ta taimaka mata sosai wurin ganin gasa jikinta da magungunan gargajiya Wasba ce zaune à inda Hurriya tazauna jiya tayi wanki tana wasa da karamin icce wanda ke nuni da kamar Hurriya take jira Kallon hanyar da ta biyo jiya tayi saidai bata ga ko mai kama da ita ba Bata rai tayi tana turo baki ta tashi ta koma cikin gidansu Hurriya shiru shiru bata tashi ba saaidai Bintu na zagaye da ita kamar wacce zata gudu don har tayo aikinta ta dawo Inna hanne ta dade a wurin tana kula da ita kafin ta koma kitchen domin ayyukanta  saida Inna hanne tagama ayyukanta sannan ta dawo inda Hurriya take kwance hannunta rike da kofin shayi cikin hikima ta shiga zuba ma Hurriya ruwan shayin duk da rabi ya shiga rabi ya fito haka abun yake Bayan tagama bata shayin tayi tagumi tana tunanin ikon Allah tunda take bata taba tunanin ko a rayuwarta zata iya zuwa masarautar Heral ba saboda sai an ketare kasashe shin bama wannan ba itadin wacece ba kowa bace face ma'aikaciya a masarautar Qamar sai kuma Qaddara da ta hadata da long lost princess din Qasar Saidai Tana Addu'a Allah yabata ikon taimokon yar marainiyar yarinyar nan Allah kada ya sanya san zuciya ya debeta ta tona mata asiri Su kuma su barira zatayi maganinsu Lallai da ace sun san wacece ita da ko hanya daya basu isa su hada ba Don duk yan masarautar Qamar tafi karfinsu hatta sarkin idan tagadama tace a sauke shi daga kan mulki to tabbas babu tantama za'a sauke shi don masarautar su tana mulkin masarautoci da yawa a afirca so masarautar Qamar na ciki Ta dade tana tunanin sannan ta tashi ta fita tana fita saiga Bintu na shigowa dan sauke ajiyar zuciya tayi sannan tace ki kula da ita don Allah. Abun kamar wasa Amman har yanzu Hurriya bata bude idonta ba har anyi wata daya da sati daya Su barira suna sane da halin da Hurriya take ciki don har anfara yada jita jita su barira sunyi kisan kai saidai da yake su din suna da power sosai ba wanda ya tarbesu da maganar Saukin Hurriya daya data samu Inna hanne tayi bake bake ganin taji sauki don lallabata take kamar kwai kowa yana mamakin dalilin don baba hanne bata da irin wannan kirkin da take nuna ma Hurriya don itama ba Ruwanta da kowa Bintu kam ta zuge ta rame tass kallo daya zakayi mata kasan cewar tana cikin matsinaciyar damuwa . Imad kam shima ya shiga damuwar rashin ganin mai aikin nan don Hamdan da amrah duk sun gigita su don yanzu a chamber shi suke kwana Neela kam batasan mi zatace ba a al-amarin don tun tana kushe su yanzu ita kanta burinta da fatanta a samo Hurriya Imad yafi kowa damuwa don kowa kallo yake yasan inda take don yanzu haka suna tare da Ammar ne a balcony Ammar ya kalleshi yace twin Imad kallonshi yayi yana daga mashi kai dafashi Ammar yayi yace nifa na rasa gane mike faruwa wacece wannan yarinyar miye hadinta da Hamdan da Amrah mi yasa suke sonta har haka yaran da basu damu da kowa ba rayuwarsu Amman sun damu da ita fiye da yadda suka damu damu Shiru Imad yayi yana nazarin maganar saidai baisan yadda zai hada komai ya bashi ma'ana ba don haka ba tare da karayin wani tunanin ba yace Allah yasa lafiya dai Shiru Ammar yayi sannan yace ka tambayi ma'aikatan ko lafiya? Girgiza kai yayi yace mashi Aa Shigowar Liya ne ya sanya  Dukansu suka juya suna kallonta cikin jumpsuit din Rimowa wanda sukayi mata kyau sosai zuwa tayi gefen imad ta rike mashi hannu tace na samo labarin maid dinka ka kwantar da hankalin ka Ammar ne ya zagayo ya rike ma Liya hannu yace lafiya miye ya faru shima rike mashi hannu tayi , murmushi tayi sannan ta gyara zama tace kwantar da hankalin ka tana cikin masarautar Qamar A hankali ta zayyane masu duk abinda aka gaya mata ance bata lafiya har yanzu batasan inda kanta yake ba tundaga ranar da ta ture Amrah Shiru sukayi suna kallon yadda takeyi masu bayani har takai karshe ba wanda yace kala Ammar ne yace wani irin ciwo take Liya tace bansaniba Imad baice komai ba ya tashi ya bar masu wurin ba wanda ya damu da tashin da yayi saboda susan halinshi na miskilanci Hamdan kam ko da yagama jin bayanin da Neela da Liya suka gama mashi sai ya fara sauke ajiyar zuciya kallonshi suka rinkayi da mamaki don abinda basu taba gani bane Amrah ce ta shigo jikinta sanye da wani crazy jeans sai yar top kunnenta sakale da AirPod Dukansu kallon yar autarsu da damuwa ta bayyana a fuskarta sukayi Hamdan ne ya tashi yaje saitin da take sannan ya zare AirPod din kallon shi tayi ta dage mashi gira guda daya alamun lafiya Cikin muryar shi mai dadi yace I found her Amrah kallonshi take da alamar bata gane nufinshi ba murmushi yayi mata sannan yace the beautiful young lady bude hakoranta tayi tana kallon hakimi tace like seriously daga mata kai kawai yayi Amrah zuwa tayi ta rungume Hamdan tana mai tsananin murna Inna Hanne zaune tayi tana kallon Hurriya wadda fuskarta tayi fayau gashin kanta da girarta kwance sai bakinta da yayi pink ta riga ta gama sawa a ranta idan har Hurriya ta cike wata biyu bata samu sauki ba to zataje kauyensu ta taho da yayanta domin ya dubata Tausayin yarinyar takeji sosai don yarinya mai gata kamarta yaushe ne Zata jira wani maganin gargajiya saidai da yanzu tana asibiti kasar waje Maganar Bintu da taji ya sanya ta dawo daga dogon tunanin da ta shiga ta kalleta sannan tace kindai ci abinci ko? Daga mata kai tayi Wasba kije innani na kira wani karamin yaro ya gaya mata dauke kanta tayi daga kallonshi hawaye na zuba a idonta yau tasan dukan tsiya zataci bare tun dazu innani take kiranta Amman taki zuwa ta tsaya tana duba hanya ko zataga inda Hurriya zata bullo Tashi tayi tana kuka tana share majina har tazo dan karamin gidansu dake cikin masarautar Qamar Aiko tana shigowa innani ta rufeta da duka tana zaginta shegiya daga gidan ubanwa kike yar iska matsiyaciya tsintarciyar mage kin raina mutane ko ta cigaba da dukanta ba tausayi bare tausayawa har saida taga tana Neman daina numfashi ta daina dukanta. Hurriya a hankali ta fara motsa yatsunta kafin ta bude idanunta Bintu dake zaune ta saki tagumi jin motsin da tayi daga Hurriya ya sanya ta kalleta cikin mamaki taga idon Hurriya bude suna kallonta da wani irin jin dadi da murna Bintu ta nufota girgiza mata kai Hurriya tayi tana mata kallon kada ki sake ki tabuing Daga mata kai Bintu tayi tana ta hamdala Hurriya kuma kallonta kawai take yadda take murna Shiru Hurriya tayi tana tunanin wadanda suka sanyata jinya inda ace a masarautar Heral ne to babu abinda zai hana su bakunci lahira don abinda suka aikata hukuncinshi kisa ne how dare they messed with Princess wani evil smirk tayi don ita she’s someone that doesn’t take nonsense from anybody whether she’s princess or slave tasan sai tayi maganinsu ita batajira wani ya kwatar mata yanci da kanta da hannunta zata kwatar ma kanta yanci Hurriya bata da dadi ko kadan idan ka tabata zatayi masu salon azabar da ko a masarautar Qamar ba’a tabayi ma waninsu irinta ba because they almost killed her lamoniyar dake gareta is not an ordinary lamoniya ciwo ne mai hade da poison wanda yake babbar barazana ga rayuwarta all this while tasan Allah ke tsareta and nobody knows about her health condition don ko a masarautar Heral ciwonta is a secret duk wanda yasan da ciwonta sai yabar masarautar tare dayin nesa sosai da masarautar zatayi masu abinda idan akace gobe su kara bazasu kara ba tayi alkawarin sai sun biyata with bigger price Dukansu sai sunyi jinyar da tafi tata tayi wani evil smirk tare da rufe idonta masu kyau tana taune lebanta. [12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar A story about a mysterious palace By Khadija (KMU) 25&26 Bintu kallom Hurriya kawai take with pure love Hurriya lumshe ido tayi tana yamutsa fuska alamar jikinta na damunta Bintu tace bari in kira maki baba hanne ta kara dubaki Bintu aguje taje kitchen ta kira Baba hanne wadda take tuka tuwo ai tanajin ance Hurriya ta farfado ta saki muciyar ta rugo aguje sai dakinsu Bintu murmushi tayi tana biyota a baya A kwance suka iske Hurriya tadan tada kanta da bango ta lumshe idanunta dogayen lashes dinta kwance sai kyalli suke sai pink lips dinta da take dan cijewa Inna hanne kara kallon Hurriya tayi don ba karya tanada kyau kallonta ta karayi ganin irin kwarjini da kuma tsantsar mulki da yake bayyane ajikinta dama saidai idan baka gani Amman kallo daya zakayi ma Hurriya kasan jini sarauta ce bude idonta Hurriya tayi aiko da sauri inna Hanne ta sadda kanta kasa duk tasha jinin jikinta ta kasa motsi Hurriya kallo daya tayi mata ta kauda kanta Hurriya Bintu ta kalla tace Bintu ki samo man ruwan zafi inyi wanka da sauri Bintu tace to inna hanne ce tace kije kitchen kice nice na aiko ki a zuba maki ruwan zafi Bintu juyawa tayi ta fita domin amso ma Hurriya ruwan wanka Inna Hanne kam kanta duke a kasa Hurriya batasan ma Allah yayi wata hallita a wurin ba har Bintu ta kawo mata ruwan a hankali ta sauko kafarta wadda tayi mata nauyi da sanyi Bintu har tazo zata taimaka mata girgiza mata kai Hurriya tayi alamar bataso da kyar ta iya tashi ta fara tafiya a hankali Bintu ta shiga ta ajiye mata ruwan sannan ta bata brush da macline sai sabulun wanka Saida tayi brush sannan ta mika ma Bintu brush din ita kuma ta shiga toilet domin yin wanka Ta dade cikin toilette tana wanke jikinta saboda kyankyamin da takeji saida tayi kamar zataji ma kanta ciwo saboda yadda take dirzar jikin sannan ta dauraye jikinta ta fito tana mai jin matukar kyankyamin kayan da ta maida Hurriya dakinsu ta shigo inda tayi sa’a Bintu da inna hanne basu nan don inna hanne ce tacema Bintu suje kitchen tare domin dafa ma Hurriya abinci dajin haka Bintu taita murna sannan tabi inna hanne kitchen din kallon Bintu tayi sannan tace mi Hurriya tafiso acikin abinci shiru Bintu tayi sannan ta girgiza ma inna hanne kai alamar batasani ba don bata taba ganin Hurriya na cin abi da farin ciki ba don kullum cikin dacin rai take cin abinci kamar dole Inna hanne murmushi tayi ta debo dankali wanda bai kai goma ba sannan ta fere. Hurriya kallon ko ina tayi da yayi datti cikin yanayin natsuwarta ta amso tsintsiya wurin uwale da murna uwale ta farayi mata ya jiki daga mata kai Hurriya kawai tayi tazo ta gyara dan wurin ta share wurin tass Sannan ta cire kayan jikinta vaseline ta shafa ta bude ledar kayanta ta zaro jeans dark blue sai farar top mai shara shara saida ta sanya inner wears hade da vest sannan ta sanya rigar Kwanciya tayi ta mike kafafunta ta lumshe idonta tunani take neman ta farayi wanda sam babu lisaafin tunani a rayuwarta bude idonta tayi sai kam ga giftawar su barira kallonsu tayi Dukansu tana karantar su Inna hanne ce ta shigo itada Bintu inna hanne rike da yar karamar kula mai kyau Bintu kuma hannunta rike da ruwa da plate Da sallama suka shigo kallo daya Hurriya tayi mata tagane ta don itace matar da ta fara bata ruwan zafi. acikin zuciyar ta take tambayar kanta mi takeyi anan Shiru tayi tana kallon matar sai sadda kai take kamar munafuka tana durkusa mata alhalin ranar farko ba haka tayi mata ba Inna hanne ta zuba mata faten dankalin da tayi mata wanda yaji kayan miya ta mika mata Hurriya kallonta tayi ba tare da ta amsa ba don haka Bintu da sauri ta amsa tazo ta mika mata amsa Hurriya tayi sannan tace Bintu ta miko mata ledar kayanta ba musu Bintu ta miko mata ledar kayanta spoon ta dauka cikin kayanta saida ta daurayeshi sannan ta faraci lumshe ido tayi ta cigaba daci wanda alama ke nuni da tana enjoying abinci Dukansu kallonta suke inna hanne kanta a kasa saida taci Sosai sannan ta ture plate din Bintu ta kalleta sannan tace kin koshi daga ma Bintu kai Alamar Eh ta koshi Pure water inna hanne ta miko mata alamar ta ajiye tayi mata inna hanne ta ajiye mata dauka tayi ta fasa ta shanye Inna hanne ta miko ma Hurriya magani ba tare da tayi musu ba ta amsa tayi chokali uku ta mika mata murmushi inna hanne tayi tana mai jin dadi ganin Hurriya har tayi acknowledging dinta Kwanciya Hurriya tayi tareda lumshe idonta tana mai neman fadawa duniyar tunani tana tuna lokacin da idan ciwon ta ya tashi yadda iyayenta ke shiga tashin hankali sosai ganin tana Neman ta fada duniyar tunanin wanda bata cika son haka ba don haka ta tashi wayarta ta dauko wadda ta dade batayi amfani da ita ba ta kunna waka sannan lumshe ido tana bin wakar fire on fire by sam smith a haka har bacci ya dauketa Inna hanne bayan tagama aikinta ta shigo ta iske Hurriya kwance tana Bacci kamar karamar yarinya duk da bacci take amman zaka iya gane yadda ta hade fuska murmushi tayi sannan tace rigimar Duniya Hurriya bayan ta warke saida tayi kusan sati biyu bata fara zuwa aiki ba don so take sai sanyi ya gama fita daga jikinta tasss don a lamarinta batasan weakness ko kuma ace wani ya gane weak point dinta shiyasa saida ta tabattar da ta warke tasss sannan zata koma aiki Bangaren kam inna hanne kam hidima takeyi mata babu kakautawa don abinci masu dadi kala kala takeyi ma Hurriya Ruwan wanka kam kullum ita take tafasa mata ta kai mata toilet hatta kayan Hurriya kwana uku sukeyi sai ta daukesu ta wanke mata Duk hidimar da take ma Hurriya bata taba ce mata ta gode ba don kamar daman dolen ta ne ita kuma Inna hanne bata taba kallon Rashin kulawar da Hurriyyar take mata ba as wani abu ba Tana addu’a kullum Allah ya bama Hurriya ikon yadda da ita duk da ta fahimci Hurriyar kamar bata yadda da kowa ba A bangaren su Imad sun baza ido suna taso suga ko ta ina zata bullo don Liya ta bincika masu ance ta warke don Hamdan da Amrah kullum sai sunce zasu je Amman yan’uwan sunki barinsu saboda zai zama abun fadi a masarautar duk dasu ba ruwansu Fitowar ta daga wanka kenan daga ita sai zani sai kuma doguwar hijab dai dai zata shiga ciki su kuma suna fitowa Dukansu kallonta sukeyi tundaga dogayen kafafunta har zuwa kyakyawar fuskarta wadda babu fara’a saidai zallah kyau da annurin dake fita kafe su tayi da idanunta masu masifar kyau saidai baka iya jure kallonsu saboda yadda suke imnating danger flames ne kawai ke fita daga idanun acikinsu ba wacce bataji shakkarta ba saboda wani kwarjini da ta karayi masu Saida ta kare masu kallo tass sannan ta shiga daga ciki inna hanne da Bintu na ganin dawowarta suka tashi inna hanne ta kalli Hurriya sannan tace mi zakiyi yanzu cewa tayi sallah shimfida mata dadduma tayi sannan suka fita domin bata wurin saboda shiryawa don sun san bata sanya kaya wani na kallonta Wata doguwar riga ta sanya mai kyau saidai tana kama da abaya yau kawai taji tanason dan decent dressing dankwali ta daura ma gashinta wanda yake ta kamshin mai na soulmate don Hurriya na yawan wanke gashinta sai ta jirashi ya bushe ya gama shan iska tukuna ta shafa mai ta sharce shi. Hijab ta sanya tayi sallah hade da rama sallahr da ake binta don daman yaune karshe idan ta rama la’asar tohm sauran magriba da isha’i Tana gama sallahr inna hanne ta shigo wadda dama dama yanzu Hurriya na kula ta saboda tana kula da ita duk wani motives nata tana kallo duk da tana nuna halin rashin damuwa gareta ganin batada wani motives shiyasa ta kyaleta ta shigo rayuwarta kuma she knew she’s too smart itadin fa sunanta Hurriya Faisait Hamood she’s her fathers daughter wanda zai iya cutar da ita yanzu ai sai yayi babban shiri beside ba wanda yasan kowacece ita saidai she have to be very cautious duk dama ita din she’s always cautious Turarenta ta fesa mai saukin kudi sannan ta fito domin samun iska wayarta kirar burin yar garuwa sai a hannunta sai earpieces dake makale a kunnenta wakarta takeji wasba ce tazo inda take tana kuka tana sharbar majina kallo daya Hurriya tayi mata taganeta wasba yar karamar yarinyar ta dukar da kanta tanata sharbar kuka Hurriya batace mata komai ba har ta gama kukanta Saida tagama kukan sannan ta kalli Hurriya ta washe mata baki tace kinyi kyau kinfi kyau a haka Hurriya batace mata kala ba Amman tana kallon yarinyar surutai wasba ta farayi mata tace ina kikaje ne kullum sai nazo na jira inga ko zaki zo Amman baki taba zuwa ba sai yau yar dariya wasba tayi tace bari muga kwana nawa nayi banganki ba hannunta ta fara kirgawa kamar wata yar baby har saida ta kirga kwanakin da tayi bataga Hurriya ba tashi tsaye wasba tayi idonta na cika da kwalla sannan tace ki yawaita yin addu’oi Saboda banason na rasaki irin fareedaa you’re beautiful ta sakar mata murmushi sannan ta ruga ta tafi Kallon bayan yarinyar da take gudu tayi wadda damuwa ta bayyana a duka fuskar yarinyar Hurriya can kasan makoshinta tace what is wrong with the girl aranta tace ina ruwanki Kallon mutanen da suke wucewa suna kallonta tayi itadai tanajin wakarta tana kallon kowa da kowa Hurriya ta dade zaune a wurin don har saida taga magrib ta tafi zuwa dakinsu Sallahr magrib tayi bayan tagama ta nufi part din Imad ganin taji sauki don haka bari yau ta koma bakin aikinta Kitchen ta shiga ba sallama ba komai zubaida datake bakin kofa sakalau tayi da baki tana kallon Hurriya wadda bazaka ce mata yar aiki bace yadda tayi wani irin kyau kuma sai kamshi takeyi zubaida bakin ciki ne ya turniketa don bata manta yadda uban gidanta da Hamdan suka shiga damuwar rashinta ba Ta tsani Hurriyar nan don batada mutunci ko kadan gashi duk inda taje ita ake kallo duk sauran mutanen dake zaune sun zama banzaye indai tana wuri haka ko su Hamdan basu tabayi mata magana ba karewa ko maganar Imad bata tabaji ba Amman ga yarinya da tazo jiya jiya tafi ta matsayi abun gaskiya yana matukar bata mata rai Amman zatayi maganinta very soon don ba zata zuba mata ido ba Duk aranta take wannan sake saken Baba RaBI ce ta kalli Hurriya tace ya jiki kinsha ciwo ko daga yanayin maganar ta zakasan ba har cikin ranta tayi maganar ba jiran amsar Hurriya take saida tana juyowa taga batanan Dariya suka saki Dukansu yan kitchen din shiru baba rabi tayi sannan ta daure fuska Store ta shiga ta debo basmati tayi continental rice sai vegetables spaghetti wadda taji namomi sai kamshi take kowa kallonta yake amman ita kamar batasan anayi ba saboda earpiece ne ma makale a kunnenta Saida ta gama suka jera trays din akace su shiga sukai masu ba musu Hurriya tabi bayansu da nata tray din Basu tarar dasu a falo na farko ko a parlour na biyu basu nan sai a parlon na uku inda suka shiga kansu duk a kasa Hurriya kallo daya tayi masu ta dauke kanta suka shiga jera abincin Saidai tanajin idanun dake binta Ludo sukeyi Dukansu su shiddan kallo daya zakayi masu kasan suna cikin farin ciki kuma suna enjoying game din Hamdan ne yake kokarin cinye game din Neela kuma kiri kiri taki bashi dama Tunda Hurriya ta shigo Imad yasan ta shigo don lokacin data juyo ta kallesu with distaste yana kallonta saidai bata lura dashi ba shidai yana mamakin halinta na iko da raini wayau Because he never came across someone like her ba all his entire life komai nata ya bambamta bata tsoron kowa acikinsu abinda takeso shi takeyi yasan tana aiki yanda ya kamata indai ta fannin aiki ne baza a kamata da laifi ko ha’inci ba Bata gaishe da kowa sannan bata kula kowa he can’t read her duk yanda yaso ya dan fahimce ta ya kasa saboda ta rufe kowace kofa da dan mutum zai iya karantar ta Saidai akwai abinda har yanzu yake bude wanda ta kasa rufe shi duka she’s lonely saidai kallo daya idan kayi mata baza ka gane kadaicin dake tattare da ita ba saboda yadda ta rufeshi ta ko ina Liya ce ta kallesu tace please Quit the game for now your food is ready Ammar ne yayi saurin tashi yace daman yunwa nikeji ya nufo din dining su Hamdan da amrah suka biyo baya kowa yaja kujerar shi ya zauna Neela ce tazo ta zauna sannan Imad ne karshe Ammar ne ya dago zaiyi magana aiko cikin sa’a idonshi akan na Hurriya wadda itama shi take kallo tana karantar shi saidai he looks very familiar to her kamar tasanshi kallon imad tayi wanda ya zauna a wani miskilance ya lumshe ido yanajin saukar idonta masu kaifi shima kallonshi tayi Dukansu tasansu amman A ina?Ganin idan fa tanason tagano inda tasansu sai ta koma duniyar tunani wadda batasan hakan kwata kwata Ammar dariya yayi yace Hurry ya jiki please come and join us Hamdan yanajin ance hurry yayi saurin dagowa kamar hadin baki Dukansu suka rinka kallonta Amrah ce ta taso tazo wurin Hurriya wanda ta kasa boye murnarta alamun zata rungume Hurriya tayi saurin ja baya sannan tace kada ki tabani idan ba haka ba marinki zanyi daga mata kai amrah tayi stiill tana farin cikin ganinta Bude baki kowa yayi don jin furucin Hurriya na zata mari amrah saidai ba wanda yace kala saboda sunsan halin amrah indai akan abun da takeso ne yanzu ko maganar banza idan sukayi ma Hurriya to ba wanda zai kwana lafiya don idan ta farayi masu rigima da kuka to sai Allah Bude bakinta amrah tayi sannan tace Hurry please grant me a wish tana daga mata hannu alamar don Allah ta taimaka mata shiru Hurriya tayi ganin tayi shiru amrah sai tayi tunanin kilan Hurriya batajin turanci sai tace don Allah kiyiman abu daya Hurriya frowning brows dinta tayi ta kalleta mockingly tace mi kikeso dariya Amrah tayi tace don Allah muci abinci tare shiru wurin yayi kowa na jiran amsarta Ammar ne yayi breaking silent din ta hanyar cewa haba yar mai kyau please join us yana karya murya hade da kanne mata ido kamar mace trying to look funny Hurriya gyara tsayuwarta tayi sannan tace you Better stop acting that way if not I promise you’ll be a transgender by tomorrow morning saboda ka koma kamar wata amarachi Dariya kowa ya dauka shikanshi Imad duk yanda yaso kada yayi dariya saida ya dara Neela a ranta take maganar muryar Hurriya ta hadu ba karya don wani accent mai matukar dadi take amfani dashi wurin magana Ammar ba karamin dadi yaji ba yadda tayi mashi magana don bai tsammaci hakan ba don yarinya ya lura bata magana kwata kwata don idan bakayi dagaske ba zakayi tunanin bebiya ce . Hurriya zagayowa tayi taja kujera ta zauna kowa serving abincin shi yayi Serving ta farayi ahankali don komai ahankali ta zuba tundaga kan appetize komai nata accordling takeyinshi cikin tsari ba wanda bai kalli yadda ta fara cin abincinta ba don da appetizer ta fara sannan taci kadan shima main dish kadan taci yadda zata ida cin komai don a doka tun suna kanana ake koya masu table manners don shine yake determining they are from royalties kuma not an ordinary royal family Don haka they’ve to be always mindful of their table manners duk wanda yaga yadda take cin abinci yasan she’s from an elegant family because he the way she held her spoon ba kowa ya iya irinshi ba Ganin almost all of them are staring at her plate ya sanya a hankali tace bloody hell what am I doing cikin wayau da dabara ta lalata plate din ta canza salon cin Abincin. They ate in silence tana gamawa tasha ruwa sannan ta tashi kallonta Dukansu sukayi Hamdan ne yazo yasha gabanta sannan yace Hurriya we’re not done talking zaki bani diyarkin?i like you wani irin kallon banza Hurriya tayi mashi Hamdan turo mata baki yayi yace please Hurriya banza tayi dashi ta kama gabanta. Zubaida da suka gama kallon duka scenes din abinda ya faru bakin ciki kam zuciyar ta har kuna takeyi hmmm kawai take cewa cikin ranta Hurriya kam tana komawa ana kiran sallahr magrib Alwala tayi sannan tayi sallah bayan tagama ta nufi babban kitchen tareda crossing hannunta abayanta kallon yadda kowa yake hada hada tayi haule reza naganinta tazo wurinta saida ta kalleta tace yar nan naji ance kinsha ciwo Hurriya daga mata kai tayi Kallon Haule reza tayi sannan tace aiki zamuyi zan biyaki haule najin kudi ta daga kai Hurriya bayani tayi mata yadda komai zai kasance Sannan ta koma daki Bintu ta bama kudi ta siyo mata sabuwar reza da omo klin sai lemun tsami da gishiri kallonta Bintu tayi tana mamakin mi zatayi dasu saidai tasan kota tamabaye bata da amsa indai Hurriya ce don haka taje ta siyo mata duka abinda ta aiketa Isha’i Hurriya tayi sannan ta sanya earpiece a kunnenta tanabin waka Bintu tazo tayi mata saida safe sannan ta nufi makwancin ta Saida dare yayi sannan haule reza tazo da kularta wadda ta juyo tafasaasun ruwan zafinta Wurin Hurriya taje inda Hurriya take kwance don kamar ita take jira tanajin nishinta ta tashi Haule reza ta kalleta tace muje Hurriya daga ita sai hijab ta tashi hannunta rike da abinda ta aiki Bintu suka nufi wurin wasila don da ita takeso afara Hurriya tsayawa tayi tana kallon yadda komai ya fara gudana duk yadda Hurriya ta fada ma haule reza haka ta fara gudanar da ayyukanta don saida ta fara Gangarawa ta daura ma wasila kyale ta dode mata baki wanda tana tabata ta tashi daga Bacci tana zare ido saitin fuskarta wasila tazo ta kalla sannan ta kalli hurriya tace ayi anan? Hurriya girgiza kai tayi Haka haule reza ta rinka tambayarta saida tazo kan kafafunta sannan Hurriya ta daga mata kai Hurriya matsowa tayi tanuna mata Daidai inda zata yanka wurare biyar ne wanda duk idan aka taba ma mutum shi akafa tohm sai Allah haule reza kallonta ta rinkayi tana kallon rashin tsoro da rashin tausayin dake cikin idonta Wasila kam ihu ta rinkayi Amman sam baya fita kiyi mana inji Hurriya ba bata lokaci haule reza ta daura sabuwar reza mai matukar kaifi sannan taja wurin da karfin tsiya wani irin azababben ihu ta saki Amman to no avail saboda baya fita baba haule ta riketa sannan Hurriya ta fasa klin dinta guda daya ta zuba mata shi wani irin uban kara ta saki tana shure shure Hurriya murmushi tayi sannan ta barbada mata gishiri ta hada da matsa lemun tsami a ciwon Saida ta sanya haule reza tayi mata yanka biyar sannan ta barbada mata ingredients dinta Tun tana kuka har kukan ya daina fita ba imani kwata kwata tattare da Hurriya ta bude kular nan ta debo tafasassun ruwa ta watsa mata akafafunta duka biyun ai wasila suma tayi Haule reza kallon irin launin azabar da Hurriya take mata tayi tana mamakin rashin tsoro da rashin imanin yarinyar nan. Ta tabbata zuwa gobe kafarta tayi mummunar konewa . Haka Hurriya ta rinka binsu saida ta tabbata duka tayi masu azaba iri daya don duk saida haule ta daure masu baki sannan tayi masu yanka biyar biyar Hurriya ta zuba masu omo hade da gishiri da lemun tsami sannan ta kona kafafun da ruwan zafi Bayan sun gama tace a a aske ma Hansa’u gashin kanta tass ita kuma wasila da Barira har yanzu tana binsu bashi ta wuce ta nufi makwancinta Haule reza kallon bayanta tayi yadda take tafiya kamar tana tausayin kasa haka take takawa tunda take bata taba ganin mutum marar imanin Hurriya ba Duk ihun da suke da neman ceton rai da suke ko dar bare gizau haka Hurriya ta rinkayi masu launin azaba don tasan ba wanda bai suma ba acikinsu Tabb inji haule tace akwai kallo dai wurin nan saidai sune suka ja ma kansu daman ance in kasa wata ba kasan wataba. Hello fans yanzu zan rinka posting from Monday to Thursday saidai daga Friday zuwa Sunday ba post Idan kuma kun fiso a rinka skipping rana daya tohm I will be waiting for your opinions Love xoxo❤️👼🏽 [12/02, 4:54 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar A story about a mysterious palace By Khadija (KMU) 27&28 Kwanciya tayi Hurriya tareda sauke ajiyar zuciya don yanzu ne zata iya Bacci cikin dadi don idan batayi masu hukunci ba gaskiya ba sunanta Hurriya Faisait Hamood ba. Haule reza kam tana mamakin inda yarinyar nan ta samo kalar launin azabar datayi masu don bata taba ganin hakan ba saidai fa ba karya Hurriya muguwa ce tace sannan ta nufi makwancinta Yau da safe da aka tashi aka iske duka yan click dinsu Barira suna jinya don kusan ihun wasila ya tadasu don azaba ta ko ina takeji kuka kam yinshi take kawai don a halin da take ciki da za’a cire kafar to da tanaso indai har zata rabu da ciwon da takeji. Barira kam har garin Allah ya waye itada suwaiba to asume suke saida aka samu da kyar suka farfado irin ciwo daya ne Dukansu suke fama dashi Dukansu saidai kowa na mamakin wanda yayi masu wannan danyan aikin Hurriya yau ta samu ta tashi da wuri don har sallahr asuba ta samu damar yinta da wuri. Tanajin sai jaje akeyi Bintu ce tazo da gudu tana haki ta kalli Hurriya sannan tace naji abinda ya faru gasu barira Amman don Allah kece?kice bake bace don Allah kice man haka Hurriya kallonta tayi sannan tace nice Bintu And idan suka kara koda hararata abun da zanyi masu sai yafi wannan Bintu kallon Hurriya tayi sannan tace haba Hurriya miyasa zakiyi haka kinga kafafunsu idan kika gani sai sun baki tausayi wallahi dama kin kyalesu sunje da halinsu tunda yanzu suma zasu ce zasu rama kema zaki ce zaki rama kuma ance sarkin yawa yafi sarkin karfi kuma ma kinsan kaura saurayin barira ne sai ance shaho saurayin Hansa’u ne Bintu batasan duk maganar da takeyi Hurriya tayi tafiyarta Juyawar da zatayi taga ba Hurriya saidai ganin inuwar Hurriya tayi Hurriya tana fitowa saiga hauke reza wadda ta taya danyan aikin jiya Kallon Hurriya tayi tana washe baki sannan tace Hurriya naga sako nagode kuma don Allah inson kibani dama yadda idon akace gobe su kara to bazasu kara ba Hurriya shiru tayi mata har tagama babatunta batace komai ba Kitchen taje inna hanne na kallonta tazo tace Hurriya an tashi naji danyan aikin da kika aikata baki kyauta ba Hurriya dage girarta tayi tace banzo don inji kyautawa da rashin kyautawa wurin ki ba malama ki zuba min ruwan zafi in kama gabana Inna Hanne kallonta take kamar statue zata iya cewa tunda Hurriya ta tashi daga rashin lafiya to yaune ta samu jin muryarta mai tsayi har haka inna hanne wadda tayi curr tana kallonta tsarki ya tabbata ga Allah sannan tace lallai kedin gimbiya ce duk aranta take maganar don kwata kwata bataji haushi ba Inna Hanne daukar bokitin tayi ta zubo mata ruwan zafi suka jero tare inna hanne rike da ruwan Hurriya kuma rike da kayan wankanta har suka zo toilet Hurriya wanka ta shiga tayi sannan ta fito ta nufi daki Sai kallonta akeyi don ba inda maganar bataje ba ita tayi masu Hansa’u wannan hukuncin wasu ta burgesu wasu kuma ta basu tausayi wasu kuma zaginta kawai sukeyi but who cares Shiryawa tayi cikin uniform dinta wadanda sukayi mata kyau Sosai Comb ta dauka ta tsaga kanta hudu sannan tayi kalaba manya manya guda hudu wanda suka sauka har gadon bayanta nade gashin tayi har saida ya dawo Daidai keyarta sannan ta fesa turarenta ta fita Sashen imad ta fara zuwa aikam cikin sa’a ta gyara ko ina har dayan dakin shi wanda yake bacci Tanajin karar ruwa hakan ya tabattar mata da yana toilet don haka tana gama mopping ta fito ta wuce part din zinariya wanda tunda ta fara aiki bata taba gifta kofar data wuce ta kitchen ba Don haka tana zuwa tayi wanke wanke sannan ta fara hada breakfast tanajinsu suna gulma murya can kasa kasa Amman sautim maganar su radam a kunnen Hurriya wata a cikin kuyangin ce tace hmmm labari da dumi duminsa fa Kowa cewa yayi munajinki subira ta kusa dawowa fa ance sati mai zoo zata dawo, wata acikinsu ta fara salati tana jajanta masu subira fa suna cikin matsala ta dade batazo kasar nan ba don haka dayawa kilan sun manta wacece subira AI kuma ba lallai kowa ya iya manta subira ba saboda irin record din da ta bari Hurriya duk tanajinsu wata acikinsu tace shekara fa ta kusa zagayowa shiru Dukansu sukayi suna zare ido wata acikinsu tace nidai bani da kyaun da za’a rasani a masarautar nan Jakadiyar zinariya ce ta shigo ta kallesu tace me kukeyi ku wuce ku kai abincin Dukansu daga mata kai sukayi itadai Hurriya na aikinta Tana gama aikin ta fita ta nufi inda suke wanki tana zuwa ta iske wasba tana wasa da dan icce tana ganin Hurriya wasba ta saki iccen ta rugo wurinta tana dariya tace tun dazu nike jiranki Hurriya bata ko kalleta ba tayi gaba inda ta saba wanki Kayan ta fara wankewa wasba kam ta samu wuri kusada Hurriya ta zauna tana ta bama Hurriya tatsuniya mai ban dariya duk intayi sai taga Hurriya fuskarta daure sai tace bari in canza haka wasba ta zauna tana bama Hurriya labarai masu ban dariya Amman Hurriya ko murmushi batayi ba bare dariya Wasba kuma taki tafiya sai can wani yaro yazo ya kirata ance ana kiranta tashi tayi ta ruga tana tsalle ta juyo tayi ma Hurriya alama da hannu Inasonki Hurriya tsoki tayi ta cigaba da wankinta tana waka Yunwa ce ta fara galabaitar da Hurriya saboda tun tashinta yau bataci abinci ba don haka tana ida shanya kayan ta nufo dakinsu Harabar wurin tagani tasan cewar ba lafiya ba don haka ba tare da bata lokaci ba kutso wurin Kowa ita yake jira a taron mutanen da akayi ta riga tasan da haka bata damu ba taja kai tana niyyar shiga wurin shaho ne ya tare hanyar yana watsa mata idanunshi masu firgita ma mutane lissafi itama kalloshi tayi tare da tsirtar da miyau a kafarshi tace disgusting kaura ne yazo a 360 don ranshi yana matukar tafarfasa da wannan makirar yarinya mai kyau sai kace ita tayi kanta duk masarautar nan waye ya isa ya taba barirarshi ya kwana lafiya babushi Sai ita ta watsa mata tuwo a fuska gashi kuma tayi masu wani irin salon launin azaba tabbas yau sai ya wulakanta cikin zafin nama kaura ya daga dorinar shi zai zuba mata Hurriya da yau itama ranta yagama baci don bazata iya tuna when last tayi irin bacin ran nan ba ta rike dorinar da karfi tanayi mashi matsiyacin kallo wanda ke dauke da tsantsar mulki da kuma izza tace the moment you beat me with your filthy hands you’re going to be executed ta matso tana mashi whispering tace kana kuskuren dukana to hukuncika kisa Ta saki bulalar ta tsotsi bakinta cikin isa da mulki tace duk wanda bai fasa dukana ba acikin ku Amman ku tabbata duk wanda yayi gigin kara tabani a masarautar nan da sunan duka to sai ya amshi laifin shi na taba lafiyar Hurriya Faisait Hamood this is a promise and try me and see ta watsa masu wani wukantacen kallo tace jakuna daku matsiyata ta shige cikin dakin tana barin kowa baki bude Kaura da shaho kam kamar wasu duwatsu haka sukayi don sungani à idanun yarinyar duk wanda ya kara tabata to kilan lahira zai bakunta yadda ta furta kisa kuma yadda ta nuna hukunci mai tsanani mutum zai amsa saidai tayi matukar kunyata su Shiru Dukansu sukayi tareda juyawa suka tafi cike da borin kunya Ikon Allah yan wurin kowa ya rinka fada to miyasa basu daketa ba mi tace masu har haka watsewa akayi kowa da alajabin wannan Hurriyar Sa’ade da karime suna kallon komai sa’ade ce tace wallahi na tsani waccar shegiyar Hurriyar karime tayi wata dariya tace naki akeji amman ki bari zamu yi maganinta a masarautar nan tunda kowa ya gagara maganin shegiyar Bintu ce ta gifto matsawa tayi saitin su tace kafin kuyi maganinta ni Zan sanya tayi maganin ku mutanen kawai tana kallon yadda suka zare ido alamun shakka dariya tayi ta shige ciki Sallah ta iske Hurriya nayi Bintu kallon yadda take sallar kawai tayi ta girgiza kai ta zauna tana jiran tagama sallahr Bayan ta sallame sallahr ta juyo ta kalli Bintu wadda take gyangyadi murmushi Hurriya tayi wanda batasan tayi shi ba don da sauri ta maidashi sannan tace Bintu Bintu adan firgice Bintu ta tashi Hurriya kallon katifa tayi sannan tayi ma Bintu alamu data kwanta Ba musu Bintu ta kwanta wani irin bacccin gajiya ya dauketa murmushi Hurriya tayi sannan ta dauki wayarta da ta amso chargy dazu wurin haule reza Bude wayar tayi wani tunani yazo mata da sauri ta cire tunanin waka ta kunna ta kishingida nesa da Bintu Inna hanne ce tazo da plate da kula na abinci kallon Hurriya tayi da ta lumshe ido tanajin waka sam batason wakar da Hurriya keji don akwai abubuwa da yawa gabanta karatun AlQur’ani ya kamata ta rinka ji ba waka ba Amman Hurriya is not helping matters Murmushi tayi ganin yadda take bin wakar Inna hanne tace Hurriya Hurriya saida inna hanne ta daga murya Sosai Hurriya ta tashi kallonta tayi ta dage mata gira alamun lafiya shigowa tayi tare da ajiye kular sannan tace abinci na kawo maki daga mata kai Hurriya tayi sannan ta koma ta kwanta ta dade bata motsa ba don har inna hanne ta tafi idonta rufe Saida taji yunwa na damunta Sosai sannan ta bude idonta tare da cizon lebenta ta sauko ta zuba shinkafa da mai da yaji hada maggi mai tauraro Kamar tanajin tausayin cikinta haka ta fara cin abinci har saida taji ta koshi sannan ta ajiye cokalin tasha Ruwa Yau ya kama wata daya kenan da kona masu su barira da Hurriya tayi su kuma su shaho da kaura tunda Hurriya tayi masu warning dinan basu kara zuwa ba Amman sun kudirta aransu abinda zasuyi mata mai muni ne Bintu kam da Hurriya sun zama tamkar yan uwa don Hurriya har ta fara bude mata wasu abubuwan duk da she’s not allowed to do that saboda she’s not to trust anybody in this life saidai mi after all she’s human being too tana amsa sunanta yar adam don haka itama tanada émotions kamar kowa kawai ta iya boye émotions din nata saboda emotions dinta babbar barazana ce a rayuwarta bata yadda ace wani Abu yafi karfinta ba tunda ita har takeda kanta so she have full control of herself don haka she control everything around her herself her maids kowa da kowa saidai yanzu kanta kadai zata iya controlling Bintu ba karamin son Hurriya take ba don ita kadai take kallo taji sanyi a rayuwarta ko kuma ince a masarautar Qamar bata da kowa sai Allah sai Hurriya Ita kanta Hurriya idan har kasan mi kakeyi yadda take kallon Bintu kadai zai nuna maka tana matukar tsantsar Qaunarta don idonta har wani gleaming na pure love yakeyi Yanzu haka ma Bintu ce ta siyo masu awara da rake itada Hurriya Zaune suke saman wani dakali su biyu Hurriya ba dankwali a kanta gashin kanta duka ya zuba a gadon bayanta don bata daureshi ba Kallon wurin da wasba ke zama tana wasa da icce Hurriya tayi kafin ta sanya hannu cikin awarar wadda ta tauna sai kuma tayi murmushi wanda duka dimples dinta suka lotsa dan gleam din dake a gefen idonta ya kara fitowa Bintu lahaula wala Quwatta illah billah kawai take ambato Lallai babu karfi da iko sai gurin Allah wanda yayi hallitar nan ba tare da makusa ba ita Hurriya wani irin kyau ne take dashi har haka? Shin gwara da ya kasance bata dariya da ace tana dariya tabbas da dariyar ta zamar mata babban kalubale a rayuwarta acikin masarautar wani irin kyau take gani kota Ina gaban Bintu banda faduwa ba abinda yakeyi ita mace ma kenan wai tohm inaga namiji Hurriya ta dage girarta daya ta kalli Bintu sannan tace kallon na miye? Ba komai inji Bintu kasa rikewa Bintu tayi don da farko batayi niyyar fadar abinda ke cikin ranta ba cewa tayi MashaAllah Hurriya kina da kyau Hurriya batace mata komai ba ta kara sanya a wara a bakinta. [12/02, 4:54 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar A story about a mysterious palace By Khadija (KMU) 29&30 Saida taci awarar kusan guda hudu sannan tasha raken wanda aka daddatsa guda biyu Bata Qara cema Bintu komai ba ta sauko Bintu nagani Hurriya ta fara tafiya itama ta sauko tana cewa Hurriya jirani banza Hurriya tayi da ita aiko Bintu ta rugo ta samu suka jera tare tana haki Tana shiga aka fara kiran Sallahr magriba sallah sukayi sai ga inna hanne ta shigo wadda yanzu Hurriya na bata amsa yanzu idan tayi mata magana kallonsu tayi Dukansu Hurriya nagama sallah ta linke hijab sannan ta dauki wayarta ta makala earpiece inna hanne tace Hurriya kidan rufe kanki don Allah tunda dare yayi kinji Ko kallon inda take Hurriya batayi bare tasan ran amsa ta fita zuwa part din Imad Ba inda ta tsaya sai part din Imad wanda zasuyi tafiya gobe kuma yace mata tare zasuyi parking she must come Ba kowa parlon don haka ba inda ta tsaya sai bedroom dinshi yana zaune ya mike kafafunshi yana amfani da MacBook sai Qamshi dakin yake na turaren wuta mai sanyin dadi Lumshe ido Hurriya tayi sannan ta bude idonta masu kyau ta tsotsi lebenta Batace mashi komai ba ta bude duka wadropes dinshi akwai wani wuri dake da jerin tarin designers suitcase, Daya daga ciki ta dauka mai matukar kyau da tsada na Bottega veneta ta ajiyeshi sannan ta fara shirya mashi kaya tunda ta shigo yake kallonta ta karkashin ido don ba karamin kyau tayi mashi ba kallon doguwar sumarta yakeyi sai kafafunta da suke waje don rigar da ta sanya tsaga gareta sosai A ranshi yake tambayar kanshi who is this mysterious girl wadda take neman dagula mashi lissafi ji wata seductive shiga da tayi wadda duk wanda ya kalleta sai yaji wani abi tunda ga kanshi har zuwa tafukan hannunshi Don yanzu yafi kowa sanin Hurriya da zai iya cewa dagangan takeyi saboda tayi seducing dinshi ko kuma ta ya kulata Tunawa yayi ko kallo na biyu batayi mashi bare har ta kasa dauke idonta daga gareshi don ko gaisheshi batayi ba wani dogon conversation din da ya taba shiga tsakaninsu bare harma yace donshi takeyi she’s so unique and classy may that’s why he started to like her Hurriya tanajin idonshi akanta murmushi tayi sannan ta cigaba da hada mashi kayanshi kaya take shiyar mashi masu matukar tsada da kyau kallon yadda take komai yake yi Hurriya tunanin da batasan tayi saida tayishi dan the more tana kallon su Imad da Ammar take ganin tasansu and the most funniest thing ever shine tagano imad dasu Ammar maternal cousins dinta ne mamansu da babanta uwarsu daya ubansu daya they used to come too their palace lokacin suna yara Ammar and Imad are her best friends kuma sune favorite cousins dinta ba kamar Imad saboda lokacin they don’t get along but deep down she was his favorite person itama Hurriya haka yake a wurinta she used to annoyed him har sai ta tabbatar da ta sanya shi kuka tukuna saboda zuciya gareshi idan tayi mashi abu saboda bacin rai shi kuka yake Bata iya kirga yadda takesa shi kuka sai kuma ta dawo tana bashi hakuri Ammar yayi ta yi masu dariya She doesn’t get along with the female twins duk da sune mate dinta Amman basa shiri saboda suna mata kallon mutum mai girman kai da nuna isa Because she’s from Heral palace Ita kuma Hurriya she doesn’t care at all don ko da ace sun shige mata tohm zalintar su zatayi because alokacin Hurriya muguwa ce duk salon mugunta ta iyata mamansu itace favorite person dinta don tana matukar son Aunty Banafsha saidai tana shekara goma rabonta da su Imad da Aunty banafsha lokacin zataje Mexico akwai fashion school din da zatayi acan tohm kusan kowa saida yazo a yanuwanta sukayi bidding dinta farewell murmushi tayi tana tuna childhood dinta a hankali tace how times flies Imad yanajin sautin murmushinta shima murmushin yayi daman tana dariya kodai he misheard her ne gaskiya baiji da kyau ba Duk abinda Hurriya tasanya mashi mai kyau ne da tsada tunda yake bai taba ganin Mai great fashion sense dinta ba how did she know expensive abubuwa irin haka kuma tasan duk yadda kayan zasu bada ma’ana who is she?what is her identity?only God Knows sai kuma Hurriya din da kanta. Bayan tagama ta zage komai sannan ta gyara komai ta juyo saitin Imad wanda ya kauda kanshi saboda kunyar data kamashi yana kallonta gyara murya yayi sai ya rasa mi zaiyi ita kuma Hurriya taki ta daina kallonshi Dage girarta tayi sannan ta rungume hannayenta tace why are you staring at me kallonshi takeyi da idanunta masu kyau tana tsotsar lebanta imad shima gyara murya yayi yace wake kallonki yana dage gira daya harar shi tayi in an annoying way tace you manah sannan ta fita shiru Imad yayi yace kada fa ace wannan yarinyar ta rainani lallai ma I will Deal with her Hurriya tana fitowa ta iske amrah da Hamdan sai ammar a balcony suna zazzaune Ammar ne yace hurry ba gaisuwa banza tayi dashi ta cigaba da tafiya da sauri Hamdan da Amrah suka taso Amrah tayi saurin rike mata hannu Hurriya kallon Amrah tayi alamar ta saketa da sauri Amrah ta saki hannun Hurriya tana rike kunne alamar tayi hakuri daga mata kai Hurriya tayi Hamdan ne yace Hurriya Guess what?shiru tayi batace komai ba bata rai Hamdan yayi yace Hurriya you’re not funny at all I won’t share the story with you shrugging kafadarta tayi though tanason taji mi zai fada mata because she’s starting to like the twins saidai mi batada lokacin batawa tafiyarta ta fara da sauri Hamdan yasha gabanta yana bata fuska dariya amrah ta farayi masu Hamdan kallonta yayi sannan ya kara cewa guess what?ganin tayi banza dashi ya sanya yace tunda bazakiyi guessing ba ni bari na fada maki we’re going to Ethiopia 🇪🇹 tomorrow In Sha Allah Gaban Hurriya ne ya fadi don batasan inda zasuje ba sai yanzu da yake fada mata ta dai san gobe zasuyi tafiya Ahankali batare da tasan maganar ta fito ba tace ethopia daga mata kai yayi sannan yace mata eh manah Do you want to know why I was so happy ? Daga mashi kai tayi alamar ehhh murmushi yayi yace I will get to see Layla Khasheem she’s my cousin all this while bansaniba sai ba’a dade ba fa Ammar yake fadamin suka barni inata hauka ashe yar uwata ce ma it will be my first time to be in Heral palace I can’t wait oo har na kosa naga yanda masarautar take don labarinta da ake bani na kasa yadda akwai masarauta irin haka i will get to see it with my own eyes and zanga my grandparents sannan yayi dariya Gaban Hurriya banda faduwa ba abinda yakeyi Heral palace can zasuje kenan gobe itafa? Heral palace nan ne fa asalinta nan ne gidanta Amman ta gagareta Because of abubuwan da suka faru Shiru tayi wanda ta fada duniyar tunani past dinta iyayenta wanda batasan ta tuna komai da ya faru Amman ya zatayi karar hoton da tajine ya sanyata dawowa daga duniyar tunanin da take neman fadawa kallon Hamdan da wayar dake hannunshi kirar iPhone 14proMax tayi inda ya dauki hotonta shida ita Hamdan yace idan mun isa i will tell Layle Khasheem about you sai in nuna mata picture dinki taga yanda kuke kama Da wani irin bacin rai Hurriya ta amshe wayar tareda yadda ta kasa Qarar fashewarta kawai akeji Idonta har ya canza launi saboda tsananin bacin rai Hamdan shima ranshi ne ya fara baci don shima badai zuciya ba kallonta yayi da muryarshi wadda bata wasa ba yace Hurriya how dare you yana mata wani banza kallo itama kallon takeyi mashi tace And how dared you took a picture of me without my consent kallonta Hamdan yayi wanda yake nuna tsantsar bacin rai yace what did you think of yourself girl you’re nothing here but just a filthy maid me kika dauki kanki bari kiji in fada maki ma if You’re feeling great you’re not great don kinga anayi maki magana ba komai ya sanya ake maki magana ba saboda kinyi man kama da Layla Khasheem isn’t it something great a whole prince took a picture of à fouling smell maid like you bari kiji you stink and you’re disgusting kuma kedin ba komai bace face kaskantaciyar baiwa wadda ta fito daga tsatson kaskantattu mutane shas bai ida fada mata kalmar shasha ba yaji saukar maruka guda biyu a tare bai ida juyowa ba ya karajin ta sakar mashi lafiyayyen maruka biyu kara daga hannunta tayi ta kara sauke mai wani marin tana kallonshi da idanunta da suka kada sukayi jawur kamar an zuba mata barkono muryarta har wani shakewa take saboda bacin rai tace And who are you to say that Hamdan shima muryar shi ba dadi yace how dared you slapped a prince with your stinky hands ya nufota alamar zai mareta Amrah ce tayi saurin rikeshi tace haba Manah Hamdan calm down stop please miye haka Ammar ne yazo wanda tun farkon abun yana kallon abinda ya faru duk da Hurriya ce bata da gaskiya Amman sam Hamdan bai kamata yayi mata irin rashin kunyar nan ba kuma ta wani fannin shima Hamdan baida gaskiya Kallon Hurriya yayi tare da matsowa inda take da niyyar bata hakuri wata irin tsawa ta daka mashi looking so angry 😡 tace Ammar don’t say a word here it’s between me and Hamdan kuma wallahi sai yaji ajikinshi this is a promise gobe idan akace ya karayi ma wani rashin kunya bazai kara ba ta ida maganar da wani irin bacin rai ta kama gabanta Hurriya har bata kallon gabanta how dare him take ta cewa how dare him har tazo dakinsu duniyar tana bata haushi Hamdan kam wata irin ajiyar zuciya ya saki sai kuma ya fashe da kuka tare da rungume Ammar yace inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un Ammar what did i did na kwafsa did i just yell at her wani kukan ya kara saki yace zaginta fa nayi da iyayenta na bani ya zanyi idan Hurriya ta daina kulani i just like her why? Amrah da takejin conversation dinsu ta harareshi in a disgusting way tayi tafiyarta ta barsu “Ammar patting bayan shi ya rinkayi yace it’s okay kadaina kuka kada ka damu zatayi hakuri” a hankali ammar ya rinka kwantar mashi da hankali tare da yi mashi alkawarin zasu bama hurriya hakuri gobe kafin su tafi daga mashi kai kawai ya rinkayi har ya samu ya lallashe ya rakashi chamber dinshi Hurriya ba abinda tayi face kwanciya tare da lumshe idonta duka abinda ya faru na dawo mata hakan da tayi shine Daidai idan har ya nuna ma wani ilta acikin Heral tohm tabbas she will be at risk rayuwarta zata kasance cikin hadari Mutane iri biyu ke nemanta da masoysnt da kuma makiyanta kuma ita kam batasan kowa yaganta a cikinsu she will wander around the world she will be freed from all those fights of powers zata tsaya a masarautar Qamar har taga yadda Allah zaiyi da ita Yau ta kama su hamdan zasu tafi duka ma’aikatansu da dogarawa da kuyangu ba wanda bai masu rakiya ba zuwa airport ba Neela kam kallon kowa tayi tanason taga Hurriya ta ina zata bullo?saidai shiru bata ganta ba kallon Liya tayi sannan tace wai ina Hurriya Liya murmushi tayi tace I don’t know Imad shima sai kallon wurin yake yaga ta inda zata fito Amman bata ba alamar ta Hamdan kam kamar yayi kuka saboda takaici gashi Amrah ta dauke mashi magana kwata kwata duk yanda yaso yayi magana da ita sai tayi banza dashi Kallon kowa yayi saidai kwata kwata ba gifcin Hurriya kuka ya fashe dashi tareda rungume Ammar dake kusa da Hamdan Ammar lallashin shi kawai yake tare bashi hakuri yana yayi shiru Announcement din da suka ji ne ya sanya su tashi wadanda suka yo masu rakiya suna dukar da kai Ammar riko Hamdan yayi sannan suka nufi jirgin Ma’aikatan Saida suka tsaya suka tashi sannan suka juya. 🌚Masarautar Qamar Page 31&32 Karfe 3:44 jirginsu yayi landing tun a cikin airport din ake masu wata irin busa da algaita ga wasu mutane tsaye gigantic da wasu kaya da basu taba Ganin wasu irinsu ba Durkusa masu kawai ake ana gaishesu Dukansu a They’re from the imperial family kenan inji wasu wadanda sukayi landing tare dasu Imad Imad frowning fuskar su sukayi hade da takaicin wannan durkusawar da akeyi masu saboda islamically ba kyau Amman basuji ko an fada masu saboda basa practicing musuluncin sosai duk da cewar musulmai ne Amman abinda sukaga dama shi sukeyi ba tare da sanin sun aikata laifi ba Amrah da Hamdan bude baki sukayi Ganin yadda akayi masu kneeling tare da dukar da kai Ammar tsoki yayi cikin ranshi sannan yace Raise sannan suka tashi tare da ce masu welcome Wasu mahaukatan bakaken jeep ne akayi masu convoy dasu a kowace bayan motar an rubuta Heral palace motocin kusan guda ashirin sai farar limousine a tsakiya bude masu cikin limousine din akayi ana durkusa masu Imad ya fara shiga su Hamdan suka biyo baya zama sukayi cikin motar wanda yake kamar wani parlo wani dim light blue da red yana kawowa sai kuma ya dauke Différents varieties of meals da small chops ne a cikin motar Liya ce ta lumshe ido tare da cewa Heral palace is freaking rich wannan motar itace latest limo of 2022 worthing shiru tayi tace gaskiya kudinsu yayi yawa .Neela tabe baki tayi tace aifa mun bani da extravagance life har sai an sanya mutum yaji baisan komawa masarautar Qamar Imad baice komai ba Hamdan ba wani spirit tattare dashi don rungume da ammar yake kamar wani yaro Basuci komai ba har suka iso Heral palace Din Busa da algaitu ne akeyi kota ina Mutane kam basu da adadi kowa da irin abinda yakeyi Hamdan da Amrah sakin baki sukayi suna kallon komai don All their life basu taba Ganin masarauta mai kyaun wannan ba everything is screaming rich and elegant tun daga kasan masarautar har sama Daidai inda ake taron aka bude masu mota Dukansu suka fito sannan aka sanya ma kowanne acikinsu alkyabba mai matukar kyau da tsada banda kamshi ba abinda alkyabbar takeyi Neela da Liya murmushi sukayi ganin yadda duk suka rikice da masarautar masarautar Heral kenan duk idan mutum ya dawo sai yaga canji bare wannan karan canjin da yawa sosai Duk inda suka gifta durkusawa ake ana masu kirari har suka zo inda ya kamata su zauna ja masu kujera akayi Basu dade ba aka fara annoucing shigowar sarki da matarshi kowa a wurin natsuwa yayi tare da sadda kai har saida sarki ya shigo tare da zama kallon saitin da suke yayi murmushi sarki Hamood yayi ya tashi ya nufo inda suke hannun Hamdan ya kama tare da shafa kanshi murmushi yayi yana kallon kamanninshi da Banafsha Amrah ya kalla yace mata amarya ta Hamdan da Amrah sukayi sauri suka gaisheshi yadda suka ga yan masarautar nayi Haka su Neela suka gaishe shi kallonsu yayi tare da yin murmushi a hankali yace Hurain itama yanzu tazama yan mata kamar su ya fada cikin ranshi murmushi yayi yanajin wani Abu aranshi saboda babu rana da zatazo ta wuce baiyi tunanin Hurain ba yana tunanin ko tana raye ko ta mutu Allah shi yabar ma kanshi sani don ba inda baisa a nemeta ba saidai Duk maganar Dayace babu ita babu alamunta itace favorite jikarshi saboda tsananin mulkinta da izzarta kuma kamanninta shi ta dauko da mahaifiyar Faisait wato bahiyya mikati shiyasa Allah ya jarabce shi da sonta yana fatan duk inda take Allah ya sanya tana lafiya sannan tana cin abinci Muryar Imad ce ta dawo dashi daga tunanin da ya shiga sakin Hamdan da amrah yayi sannan ya rungume imad da Ammar Yana tambayar su lafiya Dukansu suka amsa mashi lapia lau mutane wurin ba wanda idonshi ke kansu don kowa ya sadda kanshi matarshi kam kamar ta mutu saboda bakin ciki don ya manta da kowa dake wurin ba wanda yake ganin a wurin sai marayun jikokinshi. Hurriya ta dade tana bacci yau saboda tasan su Ammar sun tafi dagangan taki rakasu Airpot din tasha baccinta yanzu tagama aikinta ta nufi wurin wanki saidai bata ida kai wurin wankin ba taji ana busa Algaita ana kida hayaniya ake kota ina Khalifa Qamar ake cewa Khalifa Qamar Khalifa Qamar Khalifa Qamar Totsar bakinta Hurriya tayi tace Nonsense ta nufi wurin wankinta saidai maganar kawai takeji ana Khalifa Qamar ya dawo subira itama ta dawo salati taji anayi ana cewa wai daman Khalifa Qamar har yanzu yana a masarautar Qamar aiko muna cikin matsala don ance Khalifa Qamar makaho ne saidai baida mutunci ko kadan haka itama subira Hurriya tanajinsu saidai wankinta kawai ta cigaba dayi Tunda tazo take mamakin rashin ganin wasba da ba tayi yau ba duk da batayima yarinyar magana amman tana enjoying company dinta sosai wankinta ta cigaba dayi tare da cire tunanin yarinyar a zuciyarta Amman wata zuciyar na cewa taje ta dubata saboda hakan bata taba faruwa ba tsoki tayi ta cigaba da wankinta ta jima tana wanki kafin tagama ta koma daki dan ko sallah batayi ba saidai tana zuwa kwanciya tayi saidai hayaniya da kidan da akeyi shine ya hanata baccin da take so tayi kunnuwanta duk an cika matasu ba abinda takeji sai khalifa Qamar tsoki ta karayi tare da runtse idonta Da wani irin gudun masifa convoy din motocin suke tafiya acikin masarautar kowani mahaluki ya matsa daga inda yasan zasu wuce don ko daga yadda kaga suna tafiya kasan shidin mai zafi ne Busa da algaita kawai ke tashi wurin hade da sunanshi da ake ambata wato Khalifha Qamar Motar tsakiya wadda take itace kadai iri daya a convoy din Roll Royce aka bude mashi inda yake zaune idonshi a rufe looking so mighty walking stick dinshi mai masifar kyau da daukar ido tafara saukowa kafin shima ya biyota baya sunanshi kawai ake ambata a wurin A hankali ya fara tafiya mai dauke da mulki da izza don yadda yake tafiyar ko sarki albarka walking stick dinshi ta Brass cane wadda ta zama encrusted with Swarovski elements don Swarovski element na crystals din ba karamin taimaka ma sandar tayi wurin fiddo da tsantsar kyau da tsadar ta tayi ba the flamboyant design glittering Swarovski element crystal doesn’t stop at the handle don ba a handle din sandar kawai ya tsaya ba don har kasan shaft din dauke take da glittering Swarovski element Kallo daya zakayi ma handle din sandar da shaft dinta kasan cewar they are made from high quality brass wanda yake lullube da crystals yadda yake tafiya kadai zakasan lallai wannan jinin sarauta ne kuma sarautar a jikin shi take yawo ba haye yayi ba gado yayi ko fuskar shi babu alamun sauki bare rahma he’s not young because he looks 36/37 he’s huge and gigantic don Khalifha Qamar sunanshi Amman inda ya fito anfi saninshi da cobra blind snake saboda shidin kamar ba mutum yake ba saboda yadda yake he exude danger that is susceptible to a lifetime harm that leaves you wondering what is different about him that no other human being has. He’s intact kamar kowani mutum mai lafiya saidai his aura,peril and danger that always follow him behind wanda ba kowa yake da hakanba. a business world ana kiranshi da cobra blind snake saboda poisonous dinshi da danger dinshi a masarautar su kuma ana kiranshi da Khalifha Qamar Tafiya yakeyi rike da sandar shi sai glasses din dake a fuskar shi wanda dan mutum bai isa ya hasko idonshi ba saboda makantar dake tattare dasu Wucewa yake ta mutane kusan kowa yana durkusawa yana gaisheshi amman a wurin tamkar baisan dasu ba don ko kallo basu isheshi ba wani acikin security dinshi yazo wanda da alama kamar hakan dokace a wurin shi a hankali kallonshi yayi sannan ya kalli security’s din yace they’re all fired chief of security din ya sara mashi tara da bowing yace okay sir ya tafi Chief of security din ya dawo yana kallonshi tareda tunanin hali irin na Khalifha Qamar chief of security yace a zuciyarshi ko miyake expecting daga Khalifha Qamar a reptile without any emotion. Duk masarautar ta dauka Khalifa Qamar ya dawo Khalifha Qamar lmakaho ya dawo. Gafa Khalifha Qamar kam ya fans kunajin dadin labarin namu ko kuma dai da sauki tohm gafa wani shi kuma wai Khalifha Qamar shima kamar baida kirki Amman ku biyoni domin muji labarin Khalifha Qamar din. Anan na kawo karshen free page na wannan Littafin ya Koma na kudi saboda wani dalili na daban [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: 🌚Masarautar Qamar The mysterious palace By Khadija KMU Page 35&36 Shiru shaho da kaura sukayi suna sauraren abinda zubaida take fada wanda kamar ba gaskiya ba don basuyi tsammanin haka ba kuma sun sa rai sosai da kyar shaho ya sauke ajiyar zuciya sannan yace mata shi kenan wani lokacin kada ki damu muna tare murmushi tayi sannan tayi fari da ido tace nagode ta wuce abinta Shaho kallon kaura yayi sannan yace mashi to yanzu miye abun yi?Rada ce yayi mashi sannan suka kyalkyace da dariya suka tafa kamar wasu mata suka bar wajen Hurriya har yanzu idonta a lumshe yake tanajin waka inna hanne ce ta shigo ta kalleta sannan tace Hurriya kitashi kici abinci kada ulcer ta kamaki A hankali Hurriya ta bude idanunta masu masifar kyau ta zubama inna hanne su wadda fuskar ta ke nuna alama da tausayi da damuwa Cizon bakinta tayi ta kara kallon inna hanne domin tabbatar da irin kallon da take mata wanda tafi tsanar irinshi a rayuwarta ta tsani irin wannan kallon wanda ke cike da tausayi saboda itadin ba abar tausayi bace bata bukatar tausayin kowa a rayuwarta she’s all alone in this battle of life don haka bata bukatar wani sympathy daga wurin kowa she will win the battle all by herself Kallon inna hanne tayi cikin idonta aiko ba shiri inna hanne ta sauke idonta kasa Hurriya zama tayi tareda bude kular da tayi mata spaghetti taji kifi sosai plate ta amsa ta zuba batasan mi yasanya Allah ke hadata da mutanen kirki masu sonta ba duk da cewar bata cancan ci hakan ba Kallon plate din tayi inna hanne tace ki samu kici abincin da zafi batace mata komai ba kuma bata fara ci ba har saida inna hanne ta fita sannan ta fara ci Taci taliyar Sosai saboda yau tadan ji yunwa saboda bataci abinci ba bayan tagama cin abincin wani bacci ya kwasheta. Karfe 8:00 ta tashi na safe don haka agurguje tayi alwala tayi sallah sannan tayi wanka ta sanya uniform sannan ta nufi bangaren gimbiya Shiga tayi kitchen dama iyakarta kitchen tunda ta fara zuwa sashen aikin bata taba wuce kofar kitchen din ba kuma bata taba yima kowa magana ba kullum tanajinsu suna kananun maganganu da munafucin irin na gidan sarauta Amman bata taba cewa kala ba Kallonta kowa yakeyi don ta saba da irin kallon amman na yau ya bambamta kallon kowa tayi sannan tace munafukai bunch of useless sannan tazo ta fara aikinta sakin baki sukayi suna kallonta don akwai iyaye manya wanda sun haifeta amman ba ruwanta ta zagesu Saida ta tabbatar tagama duk abinda ya dace sannan ta nufi kofar fita kiran sunanta akayi tareda cewa zinariya na kiranta batace komai ba ta bude kofa tafita abinta shiru sukayi kowa yana ayyana abubuwa cikin ranshi saidai sun san cewar ta debo ruwan dafa kanta. Hurriya ba inda ta tsaya sai inda ta saba wanki ba tareda bata lokaci ba ta fara aikinta as usual ta dade tana wanki saidai tanayi tana kallonn inda wasba ke zama tana zuba mata labari kullum kasa janye idonta tayi don haka tana gama dauraya tayi shanya sannan ta nufi hanyar da taga wasba na yawan fitowa akwai yar tafiya don saida ta shanye titin sannan ta fara hango wurin kamar unguwa shiga tayi cikin unguwar wasu yara tagani suna wasa magana tayi masu wanda ya sanya su daina wasan suna kallon tsantsar kyaun hallita da gashin da Allah yayi mata Dukansu ba wanda ba kallonta yake ba dage gira tayi tareda kallon idanunsu wanda ya sanya sukaji ta cika masu idanu tambayar su tayi gidansu wasba aiko kamar jira suke ta tamabayesu cike da murna suka rakata har kofar gidan dari biyu ta basu tace su raba sannan ta shiga cikin gidan wanda baida girma amman dai ginaun Bulo da bulo ne Murna yaran sukai i tayi sunajin dadin kudin da tabasu suna mata godiya da addu’a Babu ko sallama ta kutsa kai ta shiga daga ciki inda takejin ihun yarinyar da shasheka Dukan wasba kawai takeyi wanda kamar Allah ya aikota wasba kuma shimfide a kasa bata lpy sai tazuba mata ruwan randa mai sanyi gaske tukuna take zuba mata dorina tana don ubanki karya kike ba wata rashin lafiya da kikeyi sai kin wanke kayan can shegiya mayya tsintarciyar mage bata mage dukanta kawai takeyi tana zagin iyayenta Hurriya kam tsayawa tayi tana kallon ikon Allah ranta na kara baci bata cika shiga rayuwar mutane ba ita haka Allah yayita kuma batasan ana shiga rayuwarta saida mi bazata iya zama tana kallon ana Neman kashe Wasba Shiga cikin gidan tayi sannan tazo saitin matar tana watsa mata wani kallo da idanunta masu kwarjini cikin tsiwa da gadara matar tace ke kuma daga ina shegiya la’anarna halan kema zuwa kikayi domin ceton ta Tau bari kiji inagaya maki wanda suka fiki ma sun barni don ba wanda ya isa ya kwaci wannan tsintarciyar magen cikin gidan nan tana rike kugu tana watsa ma Hurriya wani kallon banza Hurriya batace kala ba tana kallonta har tagama kumfar bakinta A hankali Hurriya tazo saitin wasba tana kallonta duk ta rame ta fita hayyacinta Hurriya sam bazaka iya karantar abinda ke fuskar taba Dagota tayi sannan tace sannu kinji bata gama fadar sannu ba taji anja mata gashi abinda kam tafi tsana arayuwarta kenan wani ya tabata hakan yana triggering dinta wanda har monster in her mutum zai iya gani A hankali ta juyo domin kallon isasshen saidai ko mamaki babu uwar rikon wasba ce kallon hannunta Hurriya takeyi wanda yake rike da gashinta tana mamaki is she kidding her dayan gashin Hurriya ta fara ja wanda ya sanya Hurriya Tayi saurin janyewa tareda dauketa da kyakyawan mari rike tana watsa mata wani kallo me ma’anoni Rike kuncinta tayi tana lailayo wani ashar ai bata ida kai aya ba Hurriya ta kara wanka mata mari Kallon bukitin da ta cika da ruwa Hurriya tayi aiko ta dauko ta sheka mata shi duka wanda ya sanya ta faduwa tana shesheka Hurriya bulalar da ta yadda ta dauka ta fara zabga mata ita ko ina ajinkinta da tsantsar mugunta da keta ihu takeyi kota ina tana Neman taimako acece ta Amman shiru ba wanda ya lekota saida Hurriya ta tabbata tayi mata blue and black sannan taje wurin wasba har zata tada wasba wata roba ta dauki hankalinta Robar yaji ta hango aiko ta nufi yajin sannan tazo saitin fuskarta ta zazzage mata shi ihu take tana kiran sunan makwabtan ta Amman ba wanda yayi yunkurin taimaka mata Hurriya riko wasba tayi wanda zata iya cewa abinda bata taba ba all her life kenan wasba kam murmushi tayi tana kallon Hurriya tanajin kamar taga mahaifiyarta har sunzo zaure Hurriya ta tuna da har yanzu bataga jini na fita a jikin matar nan ba anya zata iya bacci yau batare da taga jini na fitowa ba cewa tayi dan zauna sannan ta koma ciki Hurriya Kallonta tayi ko motsi batayi alamar ta suma Amman a haka Hurriya taje ta take mata hannu tare da murzawa yadda ko bata kare ba tasan akwai gocewar kashi ko babu gocewar kashi akwai targade tafison tayi jinya kamar yadda ta sanya wasba jinya Ba inda ta tsaya sai dakinsu sannan ta kalli wasba tace ta kwanta ta huta zata samo mata abinda zataci wasba murmushi kawai take tana binta da kallon kauna Kitchen Hurriya ta shiga bata iske inna hanne a kitchen din ba saidai haule reza don haka Hurriya wurinta ta nufa tace mata ta zuba mata abinci ba bata lokaci haule reza ta zuba ma Hurriya abinci da yake tana yinta sosai amsa Hurriya tayi batare da tace ta gode ba ta nufi dakin ta kalli wasba tace tashi kici ahankali wasba ta tashi sannan ta karbi abincin a hannun Hurriya tayi bismillah ta faraci taci abinci sosai Hurriya cikin kayanta ta lalubo wani magani da aka bata farkon zuwanta masarautar Qamar ta mika mata tace ta sha .amsa tayi tana yamutsa fuska alamar batasan magani Ganin irin kallon da Hurriya takeyi mata ne ya sanya ta hadiye maganin hade da ruwa. A hankali yake saukowa daga saman bene ba abinda bai Ganin ba ta CCTV caméra inda akayi mashi barbade yana kallonsu da duk abinda suke cewa jin takunshi da isowarsa ya sanya kowa ya shiga taitayinshi Takunshi wanda yake bayyanar da kamala kuma da taurin kai sai kuma aura dinsh da take zagaye dashi Tunda suka ji takunshi kowa ya shiga tsananin fargaba da shakku don ya cika ko ina a parlon da kwarjini da girman shi fuskar shi babu alamun sassafci ko sauki idon shi rufe da glasses mai kyau da tsada sai walking stick dinshi wadda ta kara fito da dressing dinshi Dukansu dukawa sukayi har yazo katon dining dinshi kallonsu Dukansu ya shigayi yana karantarsu bude kulolin yayi na different varieties na abinci sannan ya tsaya a dake ya dage table din baki dayanshi banda karar fashewar Abu ba abinda kakeji a wurin plate da abincin suna tararatsewa komai yana zubewa kasa cikin tsananin bacin rai yake kallon duka munafukan fuskokin su da suke kallon kasaa ya buga masu wata muguwar tsawa yace how dared you ba wanda acikinsu hanjin cikinshi bai kada ba saboda tsawar da ta ratsa ko ina na falon ida juye komai yayi kara kawai kakeji wani abu ya danna aiko nan da nan sai ga cheif of security ya shigo kallonshi yayi sannan yace they’re all fired kuma kayi punishing dinsu according to my rules how dared they messed with their future king .chief of security ya dukar da kanshi yace yess your league cikin bacin rai ya koma kasa don ko abinci bai bi takanshi ba Kuyangin suka biyo chief of security din banda kyarma ba abinda sukeyi don sun san kashinsu ya bushe don Allah ya taimakesu ba Khalifha Qamar dakanshi yayi masu hukunci ba Ba inda suka tsaya sai babban prison din dake cikin palace din chief of security sai kamewa akeyi duk inda ya gifta don shima kamar boss din nashi yake fuskar nan tashi kullum babu dariya anan aka watsa su sannan ya bada dokokin yadda Khalifha Qamar yakeson ayi masu azaba . Hurriya kam tsayawa tayi tana kallon wasba wadda tana gama shan magani bacci ya dauketa kallon yadda take sauke ajiyar zuciya tayi sannan ta fita wurin Bintu ta nufa inda take zaune tayi uban tagumi kallonta Hurriya tayi sannan tace mike damunki a firgice ta juyo ta kalleta sannan ta turo baki fashewa Bintu tayi da kuka tana kallon hurriya zama Hurriya tayi kusa da ita tana sauraren kukan da takeyi har saida tagama sann Hurriya ta kalleta da ayar tamabayar miye ya sanyata kuka Bintu kallon Hurriya tayi tace ina cikin damuwa ina tsoron kada wani abu ya sameki Hurriya har yanzu banda sukuni tun ranar da naga kina kokowa da numfashin ki. Hurriya shafa kanta tayi sau daya wanda kamar ta shafa kashi don tana shafawa ta sauke hannunta murmushinta mai sanyi wanda ke fiddo mata da aininhin kyau da kuma wata boyayyiyar charisma da kwarjini tayi hakoranta farare tass da kuma Gold dinta dake tsakankanin hakoranta gefe da gefe Bintu kallonta kawai takeyi tana fatar Hurriya ta kasance a irin wannan yanayin a har abada ba irin yanayin da zata rinka daure fuskaba Murmushin daga zuciyarta ya fito wanda ya kasance har cikin ranta kuma zata iya kirga murmushin da ya fito daga zuciyarta irin wannan tunda ta baro masarautar Heral wannan shine na biyu ko kuma Kallon Bintu kawai takeyi Bintu har ta bude baki zatayi magana saiga wasu kuyangu biyu sunzo wai Gimbiya zinariya na kiran Hurriya . [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: 🌚Masarautar Qamar The mysterious palace By Khadija (KMU) 37&38 Hurriya kallon wasba tayi wadda har ta fara warwarewa inna hanne ta samo masu aron katifa inda Hurriya ta kwana jiya da yau kwana biyu da suka wuce taje kiran da zinariya tayi mata saidai yadda matar ta rinka kallonta kamar zata cinyeta ne ya bama Hurriya haushi Sosai don har saida ya zamana cewar Hurriyar ta gaji da kallon da take mata tayi tafiyarta zinariya kam abinda ya bata haushi sosai itadin wacece face kaskantatciya wadda bata da gata Hurriya kam tafiyarta tayi don bata ga amfanin tsayawa inda akeyi mata irin wannan lusful look din ba Don kawai bata bukatar wani ya kara tabata a masarautar nan da sunan duka da ba abinda zai hanata ta buge idon zinariya yadda idan ance ta kara kallonta haka gobe bazata Kara ba saidai tasan girman abun da take tunanin aikatawa ne don as a maid how could she messed with someone like her shiyasa don haka duk hukuncin da akayi mata bazata iya retaliating ba bata cikin yanayin buge idon kawai ma shiyasae don this is not an excuse to her because she doesn’t give a damn at all yaushe ta fara tunanin abinda zaije ma ya dawo saidai idan bata ga damar yin abun ba sunanta fa Hurriya Faisait Hamood murmushi tayi kadan sannan ta cigaba da kallon wasba wadda dan kwalinta yadan zame Kallon cikakiyar sumarta Hurriya tayi wadda take da yawan gaske da cika saidai gashin yayi dukun dukun ga dukkan alamu ba’a kula dashi Ahankali ta taba gashinta wanda itama takejin ya takura ma rayuwarta don tana bukatar aski idan ta aske nata sai taba ma wasba itama ta aske nata don gashin yayi masu yawa Khalifha Qamar zaune yana kallon masu aikin da ake shigowa dasu yanzu kusan batch na bakwai kenan Amman har yanzu ba wadanda sukayi mashi Don idan ankawo sai ya tashi yayi analyzing kowacce acikinsu saidai Dukansu ji suke suna cikin wani bala’i da masifa saidai kwata kwata baya saukakawa kowanne acikinsu don duk wanda aka kawoshi chamber din Khalifha Qamar to ba’ason shi ba’a kaunar shi fitinar shi da izzarshi ta ishi kowa Cheif of security wanda ya shigo da kuyangu kusan guda goma kallonshi yayi yana jiran command daga wurin oganshi kuma uban gidanshi saidai baice kala ba ya tashi ya hau sama Yasan nufin shi har yanzu basuyi ba cikin rashin gajiyawa da halin yarima ya korasu sannan ya fita zuwa nemen wasu Khalifha Walking stick dinshi ya canza da wasu kaya masu matukar kyau sannan ya fito yana takunshi mai girgiza makiya har ya iso inda convoy dinshi suke kallon security’s dinshi da suna Ganinshi suka fara dukar dakai alamar gaisuwa yayi ya dade yana kallonsu Alama yayi da sandar shi da abude mashi mota da sauri aka bude mashi farar limousine dinshi ya shiga da tsantsar mulki hade da lumshe ido yanajin kamshin da ya mamaye ko ina a motar sannan suka fara tafiya Da wani irin mugun gudu suke tafiya kowa basu wuri yake don a yadda suke tafiya basu keda asara ba sai wanda ya haye masu Wani katon fili ne inda wurin yake dauke da manya manya mutane daga masarautoci daban daban zaune ana kallon polo din da ake bugawa wanda a shekara sau daya akeyinshi Jiniya ce wadda sarki kawai akeyi ma irinta tohm irinta tawagar Khalifha Qamar sukeyi don wata irin kara jiniyar takeyi wadda saida hankalin kowa ya dawo kansu Kowa ya saki baki da kunnuwa yana jiran yaga wani issashen ne haka Mai martaba sarki Faizan Qamar wanda yake zaune akan kujerar girma ta mulki ya kalli motocin da suke shigowa wurin da wani irin mugun gudu murmushi yayi yana kara gyara zama The Devil is back Don basai an fada mashi kowaye ba makahon Kaninshi ne ya dawo wanda hakan bai bashi mamaki ba ko kadan don an sanar dashi zuwanshi don yana sane da duk abinda ke faruwa a chamber dinshi murmushi yayi na kasaita Saidai abinda ya bashi mamaki mi ya kawo Khalifha a filin polo don tunda ya fara makanta shekara goma bai taba zuwa ba sai yau Akwai kallo kenan koma miye a hannun rigarshi yana jiran yagani Bude mashi kofa akayi sannan ya sauko da kafafunshi. girman hallitar shi da kuma annurin sallahr fuskarshi ya fito sosai wanda ya sanya ma masu kallonshi shakkar shi Brass Nautical folding stickc ce rike ahannunshi na dama yana dogarata cike da mulki Ba wanda zai kalleshi yace mashi makahone don ko lokacin da yayi makanta ba lallai Kagane cewar shidin makaho bane saboda yadda ba wanda yake taimaka mashi da hanya kuma da alamari na Rayuwa Ya fito a cobra dinshi dangerous and poisonous don aura dinshi ta cika ko ina Ba inda ya tsaya sai inda wurin da taron manya mutane suke zazzaune kallon kujerar da yayanshi yake zaune yayi While yayan shima idonshi akan Khalifha murmushi Khalifha Qamar yayi wanda mutane suka fi bama irin murmushin suna Devil smirk Girmamashi ake ana gaishe shi duk inda ya wuce wata kujera akazo aka ajiye mashi ya zauna suna kallon polon Kusan kowa a wurin a ranshi yake tambayar mai ya kawo Khalifha Qamar nan wurin miyake yi yana makaho wanda bai gani saidai ba wanda ya bari maganar ta fito Murmushi Khalifha yayi don haka yayi ma chief of security dake gefenshi alama aikam da sauri ya matso Chief of security yana gama magana da Khalifha ya nufi wurin wani wanda ke rike da usur magana yayi mashi a kunne. Manage this please ba yawa pagae din yau. Very busy Share ,comment and like Love you all [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: 🌚Masarautar Qamar The mysterious palace By Khadija (KMU) 39&40 Announcement din da akaji coach din nayi ne ya sanya hankalin kowa ya karkata ya koma wurin shi fargaba ce ta mamaye mai martaba sarki Faizan wanda yake zaune kan kujerar mulki Wurin shiru ya dauka kamar babu kowa a wurin cikin karfin da Allah ya bashi ya mike zuwa filin polo din hannunshi rike da sandar shi Wani kosasshen doki ne aka fito dashi fari Mai wani irin kyau da daukar ido chief of security ya mika ma sandar shi sannan ya haye dokin Wanda yaci wasan polon daga masarautar kano ya fito don haka idonshi akan Khalifha Qamar wanda yake makaho mizaiyi yanzu kuma bayan angama wasa kuma ya za’ayi ayi wasa tsakananin mai gani da makaho gaskiya kilan barcin rashin ido to yana da tabin hankali na musamman don ba wanda ya taba cinshi a fagena wasan polo bare kuma makaho Gaskiya an mutunci shi da kuma kimarshi saboda a rasa dawa za’a hadashi wasan sai makaho Tun kafin aje ko ina zaiyi maganin shi, Khalifha kallonshi yayi sai kuma ya maida hankalinshi wurin dokin Tambayar su akayi sun gama shiryawa dayan yaron ya bada amsa while Khalifha Qamar yayi shiru Ganin kallon da Khalifha yayi ma chief of security aiko nan da nan chief of security din yace yerima ya shirya da wani irin zafin nama Khalifha ya fara gyara dokin shi Mabusa aka hura masu wanda yasanya acikinsu kowa ya fara buga wasanshi Ba wanda hankalinshi bai karkata wurin wasan ba saboda abun da mamaki makaho da buga wasan polo Fargaba da tsoro ya cika zuciyoyin mutane da dama wanda aciki harda Danuwanshi wato Sarki Faizan Qamar Zuciyoyin mutane da yawa sun buga jin ana announcement na cewar Khalifha yaci wannan wasan Rabonshi da irin wannan wasan shekara Goma kenan kuma ko a shekara gomar da suka wuce Khalifha Qamar bai taba faduwa wasan polo ba don duk inda yayi sai yaci Yanayin sarki Faizan ya canza Sosai ba abinda fuskarshi ke nunawa irin zallar bacin Rai da damuwa Anya Khalifha bai warke ba abinda ya tambayi kanshi kenan Ya akayi yaci wasan?to ai Khalifha Qamar da zuciyar shi yake gani bada ido ba don ba abinda bayayi duk da baida ido polo ne kawai ya Daina wannan kuma ba wanda yasan dalilin hakan Sarki Faizan tausar zuciyar shi ya farayi a hankali yace haba dai kadaina irin wannan tunanin Khalifha shida ya gani kilan har abada amman ina Galadima ne yadan karkato yayi mashi rada wanda a wani irin duniyance launin fuskarshi ta canza ta dawo mai dauke da murna Saukowa yayi daga kan dokinshi sunanshi kawai ake kira wato Khalifha Qamar Dan sarki Qamar yadda yake tafiya zai tabbatar maka dacewar shi din sarki ne don kwarjinin shi bugun xuciyar makiya da yadda yake tafiya kamar yanajin tsoron taka kasa Amman acikin tafiyarshi zaka hango karfi kuma da jarumtar da Allah yayi mashi Sarki Faizan ne ya sauko daga kan kujerar mulkin shi yana mai jin faduwar gabar haduwar shi da Khalifha dan Karamin kaninshi kuma da ya zamar mashi babban kalubale a rayuwarshi Gardawan Guard din Khalifha ne suka zo da sauri suka tarbe saitin da sarki Faizan yazo tare da kareshi suna fitoda manya idanunsu waje da bindugu Shiru wurin ya dauka kowa idanunshi bude suna kallon ikon Allah sarki fa dakanshi Black Americans ne Guard dinshi Giant Kamarshi wanda daga gani they are loyal kuma sun san aikinsu Ba wani alama ta girma da suka bama sarki Faizan abu daya suka Sani cewar bai isa ya gifta layin da suka ja ba kuma tabbas idan ba Khalifha ko chief of security yayi masu magana ba bazasu taba barin shi ya wuce ba Da sanda Khalifha yayi ma chief of security alama da subar shi yazo aiko yana masu magana Dukansu suka matsa Murmushi sarki Faizan yayi tare da zuwa wurin Khalifha ba wani bata lokaci ya rungumeshi Khalifha shima rungumeshi yayi back tare da cewa it’s being a long time brother I miss you inji sarki Faizan Qamar Khalifha Qamar wani Devil smirk yayi tare da cewa nazo na amshe sarautar masarautar Qamar Rest assured kaga bazaka kara missing dina ba tunda muna cikin masarautar Qamar A hankali yayi maganar yanda ba wanda ya isa yaji face sarki Faizan Qamar Murmushi sarki Faizan yayi sannan yace banda abun Khalifha ka taba ganin inda makaho ya sarauci Al-umma Ko kallo Khalifha bai kara bin sarki Faizan dashi ba bare yayi tunani amsa ya nufi hanyar motar shi don shikam ya gama magana idan kuma yariga ya gama magana to ba wanda ya isa ya sanya shi ya maimaita miskili ne sosai Manya manya mutane ne sukazo wurin Khalifha da niyyar yi mashi magana amman security’s dinshi suka dakatar dasu ta hanyar daga masu hannu da nuna masu bindgogi Tashin kurar mota kawai kakeji a wajen wanda hakan ya sanya mutane dayawa cikin alhini da fargaba Sarki Faizan Qamar har baya Ganin gabanshi saboda tsananin bacin ran da yake ciki da kyar ya samu ya lalubo murmushi a fuskarshi yayi ma manya mutanen dake wurin sallama Khalifha Qamar cikin motane ya saki wani murmushin mugunta sannan ya kwanta akan kujera tare da lumshe ido. Wanda sukayi polo da Khalifha kam ya raina kanshi sosai don daga baya ya gane cewar Khalifha jarumi ne. Hurriya kam Al-Amarin zinariya yanzu ta rasa mi zatace saboda kullum akwai abubuwan da take badawa akai mata na duniya duk abinda ta bada kuma haka zata sanya a maidashi ba tare da ta kallah bare kuma har ya burgeta Wasba kam ta samu wuri don ba karamin son Hurriya take ba kuma dawowa datayi a wurin shine babban abu najin dadi data samu a masarautar Qamar Don tunda ta dawo wurin Hurriya komi za’a kawo ma Hurriya indai na ci ne tohm sai ta rage tukunna Hurriya ke cin abinci koda Hurriya kam bataci komai ba Allah ya sanya mata kaunarHurriya don tanajinta kamar wani bangare na jikinta Kullum sai ta nuna ma Hurriya tayi Bacci don haka Hurriya na kwanciya zata matso gefenta ta kwanta sannan tayi mata addu’a da taga ta fara motsi sai ta koma katifarta ta kwanta Hurriya kallon abubuwan da zinariya ta sanya a kawo mata da safe tayi shrugging kafadar ta tayi tare da tafiya inda take wanki don yanzu aikinta daya a masarautar don kwata kwata ta daina zuwa shashen zinariya aiki Wankinta takeyi tare da zura earpiece a kunnenta tanajin wakarta mai dadi tana cikin yin wankin uwar bayi tazo tare dayi ma kowa magana Dukansu suka matso wurinta domin jin mai zatace Yawwa Zamuje sashen Gimbiya subira da kuma yerima Khalifha saboda suna da bukatar masu aiki Don haka ku kiyaye nan ta fara gaya masu irin Dokokin na Subira da Khalifha duka Dokokin are strict Amman ya zasuyi dolensu ne tunda abinda ya kawosu masarautar kenan. Acikin duka mutanen data tara ba wanda bai shiga cikin damuwaba da tashin hankali ba saboda inda zasuje aikin Hurriya kam duk da earpieces ne a kunnenta tanajin duk abinda suke cewa Uwar bayi bata ce mata komai ba don tasan gaba da gabanta aljani ya taka wuta tasan very soon zata shiga hankalinta ta daina wannan jiji da kai din da izzar don mutum biyu mararsa sauki a masarautar sun dawo. Uwar bayi tayi gaba a hankali suka bi bayanta har zuwa sashe magajiya Zama wato subira tafiyace mai nisa Amman kwata kwata Hurriya yanzu ta daina ganin tafiya saboda har ta saba Bayan sun iso kowa ta nemi wuri ta tsaya domin jiran Gimbiya subira don ta fito taga idan sunyi mata Zaune take a wata matsiyaciyar kujera mai kyau sanyi da kamshin turaren wuta mai dadi da tsada sai kafafunta acikin wani ruwan mai kumfa mai matukar kyau da daukar ido Idonta sanye da wani haddaden designer glasses mai matukar kyau da tsada itadin kyakkawace ta ajin farko don wani irin luminous skin gareta wanda yake brightening kamar sunshine skin dinta kam flawless ga smooth skin dake fidda wani uban glow tanada wani irin dogon gashi wanda yake bude anyi mata gyaran ponytail gashinta brown hair ne mai matukar kyau wanda kallo daya zakasan ana kashe mashi kudi wurin gyaranshi Tana da dogon hanci mai kyau wanda ya fito kamar biro idonta sun hadu don wani irin double eyelid gareta wanda suka fita sosai eyeballs dinta wani kalan dark brown ne mai shining Itadin mai kyau ce kuma tasan da haka Kallo daya idan kayi mata zakasan bratty ce ta ajin karshe don yadda take wani yamutsa fuska kamar kashi pedicure akeyi mata wanda har angama soaking kafar gyaran kafar za’a fara Gyaran nails akeyi mata nails dinta masu bala’en kyau very cautions matar takeyi mata saidai subira da wayarta na a hannunta tana dariya sai kam hannun matar ya goce tare da yankarta kadan Duk abinda ke wurin tsayawa yayi domin sun san rashin mutuncinta Saukar kyakkawan marin da sukaji ne wanda ya sanya kowa shan jinin jikinshi Dukar da kanta matar tayi wani irin matsiyacin kallo subira take aikawa matar da ta kusa haihuwarta shiru wurin ya dauka Tashi subira tayi tsaye anan naga komai nata itadin doguwace saidai ba Sosai ba don baza’a sakota cikin jerin gajeru ba tanada wani irin figure mai daukar hankali don everything about her is screaming perfection Ture matar tayi sannan ta takata bayan takawar da tayi mata jawo kanta tayi baki daya ta sanya shi cikin ruwan kumfar da aka wanke mata kafar sannan ta fito da kan tana watsa mata kallon banza Numfashin matar yana kawowa yana daukewa Amman batausayi bare tausayawa Ta kalleta shekeke sannan tace ke kidahumar inace da sauri ta dukar da kanta tace don Allah kiyi hakuri Allah ya taimake Gimbiya kiyi hakuri don Allah Wani uban tsaki taja sannan ta haye sama kuyangunta na bayanta Ruwan wanka mai dumi aka hada mata fitowa kuyangar tayi tareda cewar Allah ya taimake ki nagama sannan ta fita subira batace komai ba don wayarta ke a hannunta cire bakin glass dinta tayi ta aje tareda shiga toilet din Saidai tana taba ruwan da aka zuba mata a komin wanka ta fara kwala ma kuyangar ta kira da sauri saro tazo tana durkusawa ruwan komin ta diba sannan ta watsa mata a fuska saro bata ida dawo hayyacinta ba ta kara watsa mata ruwa mai zafin gaske a fuska wani irin ihu ta kwalla tadiyeta subira tayi da tsantsar mugunta da gadara saida ta fadi akasan tiles din Saro yau taga bala’i a rayuwarta Sosai don saida ta hada mata ruwa ya kai sau ashirin tukunna akasamu yayi ba irin zagin da batayi mata ba yau ,zagin na cin mutunci ma da wulakanci kuka Saro ta rinkayi data fito duk wanda ya ganta kawai hakuri yake bata. Hurriya suna tsaye kusan awa dinsu ta uku kenan ga sanyi ita kadaice ma ta samu wuri ta zauna tanajin wakarta hankali kwance ta riga da tace idan har aka kara minti biyar ba’a fito ba to tafiyarta zatayi Kallon agogon wayarta tayi tareda tashi tsaye ganin lokacin da ta bada har yayi Saida ko fara tafiya batayi ba aka farayi ma magajiya zama wato subira iso Ba wanda bai shiga taitayinshi ba don kowa da hanzari ya tashi aka hau layi Hurriya kam da already akan layi take Sanye take cikin wata Long slip miu miu dress kalar grey melange kasan rigar kusan an tsagashi sai wasu matsiyatan heels 5inches Gashin kanta ya zubo har bayanta idonta cikin bakin glasses dinta mai kyau tayi kyau na daukar hankali don zaka dade kana kallonta ba tare da ka gano makusarta ba. Kamshin ta ya cika ko ina a wurin Kuyangu kusan guda bakwai abayanta Uwar bayi ce taje wurinta tare dayi mata bayani Cikin yanga da jiji da kai da tsantsar sarauta kuma da mulki ta fara bin ma’aikatan Duk wurin wacce tazo saita daga mata fuska tareda kallonta sannan ta sharrance mutum tsabb da sunayen dabobbi sannan ta sanya maka sunan dabba kuma ta kiraka da akuya ko tunkiya ka amsa. Ta rufe hancin ta tsaff don tace warin bunsurai sukeyi Marin da ta sauke ma yarinyar dake kusa da Hurriya shine ya sanya Hurriya tayi mata kallo daya sannan subira ta kara da take ma yarinyar kafa wanda kararta ya karade ko ina Amman ba wanda yake da tacewa bayan tagama zagin yarinyar hade dayi mata wulakanci da cin fuska ta karkato wurin Hurriya Subira kallon Hurriya ta farayi tunda ga sama har kasa fuskar nan ta Hurriya neutral batada wata damuwa don earpiece ne sagale a kunnenta Uniform dinta ne ajikinta don ta kwana biyu bata sanya normal kayanta ba yanzu tana yawaita sanya uniforms Subira kallon tsantsar kyau da aji take na hallitar Hurriya don tunda tazo wurin ko kallon inda take batayi ba kuma har lokacin bata fara kyarma ba yadda akeyi idan akaji takunta Tabb kawai subira take cewa don ita ba makauniya bace don ko makaho ya laluba su da ita da Hurriya yasan Hurriya ta fita kyau Tabb first in history Subira gyara tsayuwarta tayi cike da gadara kuma da mulki da isa tace ke gorilla 🦍 ta bugama Hurriya tsawa Hurriya tsaff tanajinta amman bata ko kalli inda take ba ta kalli gabas Saukar kyakkawan marin da taji wanda ya sanya tayi saurin dafe kuncinta ba tare da ta kalli saitin da marin ya fitoba a har yanzu Ke wacca irin kidahumar dabba ce inji subira Hurriya saida ta dan mari kanta don taji dagaske ba bacci take ba Don tunda take rayuwarta ba wanda ya taba sanya hannunshi a fuskarta da sunan mari sunanta fa Hurriya Faisait Hamood diyar babanta kuma jikar sarki Hamood tabb Hurriya bata ida dawowa daga duniyar tunanin data shigaba taji saukar tsinin takalmin subira a kafarta Runtse idonta Hurriya tayi tanajin zafin har cikin kwakwalwarta Subira tace Ke waca irin jahila kucaka tunkiyace Hurriya wadda idan ka kalli idonta idan kasan mi kakeyi dole ka ruga kayi ta kanka Kallon subira tayi sannan ta tsotsi bakinta tace da mamanki da babanki sune manya jahilai kucakai kuma dabbobi Da wani irin zafi nama subira ta daga hannu zata mareta wanda Hurriya itama da sauri ta rike hannuta Tana rikewa ta sakin hannun kamar kashi tare shammacarta ta wanka mata wani wawan mari kafin ta ankara ta kara mata wani Mari Hurriya ta rinka bata wanda baida iyaka subira banda ihu ba abinda takeyi Hurriya kam kwatakwata marinta datake yaki calming anger dinta don haka ta daina marinta ta shiga jamata gashinta cikin azaba da muguwar keta how dared she slapped a royal princess Hurriya fa Faisait Hamood mari fa tunda take a rayuwarta ba wanda ya taba marinta kuma ta takata da heels masu tsini ta fito da jini a jikinta she will never let this slip Kara jan gashin Hurriya take saidai hakan shima bayi mata ba banda ihu ba abinda subira takeyi Cikin zafin nama ta cire dogayen takalman subira inda subira ta ta fadi warwas tana kuka Da takalman duka biyu Hurriya ta rinka kwada ma subira duka kuma kota ina dukanta Hurriya take ihunta kawai ake ji Mutane sun taru sai salati suke amman ba wanda yayi yunkurin hana Hurriya. Hurriya saida ta tabbatar ta ji mata ciwo don idan bataga jini jikinta ba tohm sam bata iya Bacci Bata ko kalli kowa ba cikin mutanen ta sanya earpiece dinta ta koma dakinsu don tana bukatar wanka duk duniya ba abinda ta tsana irin ace ta taba wani she need a bath. 🌚Masarautar Qamar The mysterious palace 41&42 Saida mutane suka tabbatar Hurriya tagama cin uban subira tukuna sukazo suka fara riketa suna sallati don duk Hurriya taji mata ciwo wanda da kyar aka dauketa aka shigar da ita Chamber dinta Jakadiyya suka nemo wadda tana Ganin halin da subira take ciki ta hau salati Tana sanar da ubangiji kallon kuyangun tayi tace garin yaya hakan ta faru Nan aka kwashe labarin tass aka gayamata shiru jakadiya tayi tana jin jina abun a ranta saidai wani ihu da subira tayi ya sanya tayi sauri tazo inda take tana tambayarta lafiya Idon subira kwalla da hawaye kawai suke fiddawa na azaba ta nuna mata wani wuri a bayanta tace zafi Jakadiya sannu tayi mata sannan ta shiga toilet da kanta ta hada mata ruwa masu dumi Sannan suka kamata aka shiga da ita Gashi akayi mata wanda duk wanda yake a sashenta saida yaji ihunta ko ina na jikinta zafin ciwo ne ga rauni Saida jakadiya ta tabbatar da ta gasu sannan ta fito ta shiryata lokacin har Doctor ya iso yana jiran subira domin ya dubata. Tun kafin aje ko ina magana ta karade ko ina abinda Hurriya tayi wasu kam ta burge su sosai don ba kowa yakeda confindence din bugun diyar sarki ba Amman ita ta zane tass saidai da yawa wasu sunji tausayin Hurriya saboda sanin halin subira bazata taba kara barin Hurriya tayi bacci mai d’adi ba acikin masarautar don azaba ce zata rinka sanyawa anayi mata. Hurriya kam ba inda ta tsaya sai babban kitchen tana yamutsa fuska kamar ta taba kashi Tana zuwa cikin sa’a ta samu inna hanne a kitchen din aiko tana Ganin Hurriya ta taso sannan ta kalleta ta sadda kai ,Hurriya tace ruwan zafi inna hanne ta daga mata kai ta samo bucket ta zuba mata sannan ta dawo ta kalli Hurriya tace naji abinda kika aikata Hurriya meyasa baki tausayin kanki damu da muke tareda ke baki tunanin duk abinda ya sameki a masarautar nan kamar mu ya taba ne?Aaqv. Q Hurriya daukar bokitin ruwan wanka tayi batare ta bata second glance ba ta nufi toilet cikin sa’a taga wasba Aikenta tayi ta dauko mata kayan wankanta Hurriya wanke jikinta tayi sosai sannan ta fito ta daura Alwala duk inda ta gifta nunata kawai akeyi ana kananun maganganu Hurriya kam ko ajikinta wasba kam tsalle kawai take tana kallon Hurriya har suka iso daki Wasba bata shiga ba saboda tasan Hurriya zata shirya yanzu. kuma batasan ana kallonta don haka ta tsaya waje gashinta Hurriya ta gyara sannan ta sanya kaya marar sa nauyi Yau kwana uku kenan da faruwar dukan da Hurriya tayi ma subira don mutane dayawa suna jiran tsammanin ganin yadda zata kaya Saidai shiru. Hurriya bata da damuwar komai don tanazuwa tayi aikinta kullum na wanki Subira jikin ya samu dama Sosai Amman tasha wuya Sosai don wani ciwon jiki ta rinka fama dashi sosai ko ina na jikinta ciwo yake mata idonta idon Hurriya abinda tayi mata sai tayi matashi tenfold don ba’a taba wulakanta kamar haka ba tunda take rayuwarta kuma wulakanci ma daga filthy maid dole ne ta dauki hukunci Sarki Faizan Qamar a wani katon parlo wanda yake da matukar girma da daukar ido babu abinda parlon baiji ba na more rayuwa don wasu expensive chandeliers da suke bada haske kota ina expensive sets of royal chairs da aka shimfida a parlon komai na parlo is perfect don wani sanyi da kamshi dake busowa a kota ina Kallo Daya idan kayi ma parlon zakasan an zuba dukiya ba yar kadan ba don parlon Saidai ace end of Discussion Kaida kawo kawai yake a parlon fuskarshi dauke da damuwa da fargaba Wayoyi ne kusan Guda uku a saman side table s23ultra sai iphone 14pro max guda biyu s23ultra din ya dauka tare da dannah number Galadima in a very commanding voice sarki Faizan Qamar yace yana bukatar ganinshi yanzu Ba’a dauki lokaci mai tsayi ba saiga galadima yazo yana durkusawa yana gaishe da sarki Faizan cikin wani yanayi yace tashi Tashi yayi sarki Faizan yace kaje wurin Aikin wuka kace yayi mani Duba akan Khalifha Da sauri galadima yace to angama ranka ya dade yayi kirari sannan ya fita. Zinariya cikin tafiyarta ta takama da isa taje part din subira inda take kwance ana mata massage isowa akayi ma zinariya har cikin part din subirar kallon subira tayi from head to toe sannan tayi murmushi tace you’re indeed beautiful subira Shiru subira tayi batace kala ba zinariya data riga daman tasan halin subirar bazata taba ce mata kala ba Murmushi zinariya tayi tace tunda kika dawo masarautar Qamar baki zo kin gaisheni ba ta ida maganar a wani irin gadarance i don’t care ko ki gaishe ni ko akasin haka nazo ne nabaki warning Subira idonta akankance ta dago tana kallon zinariya da mamakin warning din da take magana don tasan tunda tadawo gari nan bata hada hanya da ko wani ma’aikacinta ba don tasan wacece zinariya tasan kaidinta da sharrinta don ita ba ko wace kazanta take tabawa a masarautar Qamar ba kuma akwai abubuwa da dama idan akace bazata iya ba Zinariya ita idan ana sallah ba’a magana kallon subira zinariya tayi sannan tace ba komai ya kawo ni wurin ki ba sai dalilin Hurriya naji abinda ya hadaki da ita don haka kada ki kuskura kiyi mata wani Abu idan kuma baki dauki abinda na fada maki yanzu ba tohm kinsan sauran Kinfi kowa sanin zinariya a masarautar nan basai na fada maki sauran ba tana gama maganar ta kakkabe alkyabbar ta tabar subira da sakin baki Shiru subira tayi tana cizon yatsa don tasan zinariya tasan mi zata iya da wanda bazata iya ba saidai duk abinda Hurriya tayi mata sai ace ta tashi a banza gaskiya bazai yiwuba Shiru tayi tana tunanin tasan halin zinariya tunda har tazo tayi warning dinta haka she’s capable of doing everything to protect the girl murmushi tayi don wani tunani yazo mata a hankali tace idan kinsan wata bakisan wata ba Sanyawa tayi a kira mata uwar bayi ba bata lokaci uwar bayi tazo tana durkusa ma subira cikin yanayi na jiji da kai tace tana bukatar Hurriya ta dawo aiki a shiyarta uwar bayi da mamaki a fuskarta saidai bata isa jin ba’asi ba don haka ta amsa mata da angama ranki ya dade Hurriya kwananta biyu kenan da fara zuwa sashen subira aiki don tunda akace zata koma da aiki a wurin bata musa ba Bintu hada kukansu itada wasba Hurriya kam bata ga abun damuwa ba saboda tasan abinda ya kaita shine zatayi tadawo Itama subira bata wani damuw da al-amuran Hurriya don kowa yayi mamakin hali na ko in kula da take nunawa don kwata kwata ba kyara bare zagi bare hantara babu ko daya tun mutane na jiran suji abinda subira zatayi ma Hurriya har sun hakura Yau watan Hurriya daya gam a part din subira aikinta takeyi tsakaninta ga Allah don ita Bata da kwiyu sam sam Karfe 8:00 ta tashi ba yadda wasba batayi tashinta tayi sallahr asuba ba kiri kiri takiyi ta koma bacci saida takwas tayi mata sannan ta tashi tayi sallahrta bayan tagama sallah ta tattara kayanta da sukayi datti ta wanke su tasss Tana shigowa taga inna hanne kallon Hurriya tayi sannan tace Hurriya rigima saida nace ki bari in wanke maki shine kika wanke da kanki a hankali Hurriya tace ki huta Kallon wasba wadda wayar Hurriya take rike a hannunta tayi tace wasba yar gidan Hurriya muje ki amso mata ruwan wanka da murna tace to inna hanne .Bintu ce ta shigo ta kalli Hurriya tace Hurriya kinsan ashe har yanzu su Hansa’u basuyi hankali ba sunce idan suka warke sai sun sabauta ki don Allah kibi a hankali kinji Hurriya kallon Bintu tayi sannan ta daga mata kai alamar taji inna hanne suka fita itada wasba Hurriya brush dinta ta dauka da kayan wankanta ta fita Wasba ta kawo mata ruwan wanka saida tayi brush sannan ta bama wasba brush din ta shigar mata dashi ciki ita kuma ta shiga wanka Lokacin data fito har lokacin wasba na wurin na jiranta tana ganin fitowar Hurriya tayi murmushi tazo suka jera suna zuwa wurin dakin tababama Hurriya brush dinta ta ruga ta nufi wurin Bintu. Hurriya murmushi tayi Ganin yadda take tsallatsalle sannan ta shiga ciki madubi ta kalla sannan ta kalli sumarta da kullum kara cika mata kai takeyi wanda batasan haka samm Tsoki tayi sannan ta dauki comb ta sharce gashin tare da shafa mashi mai raba gashin hudu tayi gida hudu sannan tayi ma kanta kalaba manya guda hudu Kalabar ba karamin kyau tayi mata ba don kamar wata yar baby ta maidata ta sauka har tsakiyar bayanta Mai ta shafa sannan ta bude kayanta tana kallo ta dade bata sanya normal wears ba yanzu ta saba da sanya uniform dinta don tanafin wata yanzu bata sanya kayanta ba face uniform kullum saita wankensu kuma Tsoki tayi ta fitoda wata farar riga mai matukar hasken gaske ta sanya inner wears ta sanya rigar CropTop ce rigar wanda ta fito mata flat stomach dinta wanda yake da adon zinari a cibinta sannan ta sanya blue jeans trouser mai fadi Ta murza turarenta mai saukin kudi ba karamin kyau tayi ba jinta take Daidai yau sosai kilan saboda tafi ganema wannan shigar sosai frowning face dinta tayi sannan tace it’s been a while sannan ta nufi part din subira Wani irin kyau na fitar hankali tayi don kamar wata baby haka ta koma tafiya take cike da izza da mulki har ta iso part din subira subira kam daga stairs taga shigowarta wanda saida taji gabanta ya fadi Ba abinda ya dauki hankalinta irin adon dake cikinta wanda tana hango siririn Gold din dake tsakiyar cikinta Kin janye idonta tayi daga kallon da take mata wanda cikin sa’a Hurriya tayi mata wani kallo aiko da sauri subira ta basar Kitchen ta shiga ta fara wanke wankenta hade dora breakfast. Subira kam ta kasa goge zinarin da tagani ajikin Hurriya da kuma irin shigar da tayi don tunda tazo bata taba ganinta ba uniform ba tsoki tayi tareda cewa yaune dai karshen ki acikin masarautar nan mayya Suna cikin aiki ne aka fara shela cewar subira na bukatar kowa acikin ma’aikatan ta awaje anyi mata sata Bude baki kowa acikinsu ya farayi ana jimamin waye yayi wannan satar Hurriya ajiye wukar da take yanka albasa tayi tareda wanke hannuta ta sake nade gashinta sannan ta fita Ma’aikata kuyangu hadimai bayi ne masu matukar yawa kowa ya jera layi saboda za’a cajesu hade da caje kayansu Hurriya kam ko ajikinta tana kallon yanda kowa ke kyarma shiru wurin ya dauka Sosai saiga subira ankawo mata kujera Zama tayi cike da yauki da takama tana kallon duka mutanen dake wurin kallon Hurriya tayi sai kuma ta saki murmushin mugunta. [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: 🌚Masarautar Qamar The mysterious palace 43&44 Wata irin chajewar wulakanci ake masu don ko ina ake caje mutum har akazo kan Hurriya Kallon matar da take chaje yan uwanta tayi da niyyar zata fara caje Hurriya Hurriya kam wani irin kallo ta aika mata dashi mai cike da kashedi da kuma gargadi matar ahankali tabar wurin Hurriya tana sosa kanta don ba inda labarin Hurriya baije ba a masarautar wadda zata iya dukan kamar Gimbiya subira kuma gatanan tana zaune lafiya a masarautar ita wacece da zata yima Hurriya laifi gaskiya ba ruwanta Don haka sub sub tabar wurin ,subira da take zaune akan kujera murmushi kawai tayi don tana kallon komai daga inda take don har yanzu ba’a fara wasan ba Ba wanda ba’a fito mashi da kayanshi ba don duk wadda take tsaye a wurin saida aka fito mata da jakar kayanta ko kullin kayanta haka akazo ana warwatse kayan mutane Jakkar Hurriyace aka juye kayanta wanda kamar nata ne karshe salatin da aka farayi ne ana nunata shine ya maido hankalinta daga inda take kallon tantabarun da suke soyayya wanda alama ya nuna basu da wata damuwar duniya a rayuwarsu Sunanta kawai ake kira ana nunata cikin natsuwarta da calmness nata ta juya tana kallon mutanen da suka zuba mata ido suna barauniya ce ashe banda sarkar Gimbiya subira hada wasu sarkoki da kudade acikin kayanta Hurriya kallon saitin zubaida tayi inda take rike da sarkoki biyu mafi muhimmanci kuma da hadari a rayuwarta sai kuma wani pendant shima a hannun zubaida Kallon kowa takeyi a wurin tunda take rayuwarta bata taba shiga bacin rai irin bacin ran da take ciki yanzu ba kuma ba saboda satar da aka laqa mata ba aa saboda sarkokin da ba wanda ya kamata yasan da zamansu face ita saidai mi anyi mata abinda bazata taba yafewa ba don ko taso ta yafe ba lallai ta iya hakan ba Inda sunsan daraja da kimar sarkokin da kuma hadarin su da basuyi gigin fiddo su ba Ba wanda zai iya gane yanayin da take ciki saboda Allah yayi mata baiwar boye duk hali da zata shiga ko ace tana cikin wani yanayi Ranta a matukar bace yake batasan ta aikata abinda bashi ba a wurin don yadda ranta yake bace ba abinda bazata iya ba Wata irin mahaukaciyar dariya akayi tareda jefo mata kalmar daman ashe barauniya muke zaune da ita bamu Saniba ba kama ba alama ashe abun kunyar da mutum ma yake aikatawa kenan sai kuma yazo yana hura mana hanci yana cika yana batsewa inji karime wadda take kusa da zubaida Subira na zaune akan kujera tana kallon expression din Hurriya wanda ta kasa karantar ta sam Amman yanda abun yake tafiya yana sanyata nishadi sosai Zubaida ce tace kuna son kusan wacece barauniyar tamu kowa daga kai yayi dariyar mugunta tayi sannan ta nuna saitin Hurriya inda take a tsaye tana kallon kowanne acikin su Amman baka iya gane yanayinta Kunga abinda ta sata ta daga sarkar subira mai matukar kyau da tsada wata dariya tayi tace ashe na manta barauniyace ta dade tana sata bamu sani ba kunga abinda ta sata Hurriya da wani irin zafin nama ta iso wurin Zubaida ta wanka mata mari tareda amshe sarkokinta guda biyu wanda bata kaiga dagasu ba tana watsa mata wani irin kallo Kallonta subira tayi sannan ta taso har inda Hurriyar take Daidai kuma da wasu manya manya Dogarawa suka zo kowanne hannunshi rike da zabgegiyar dorina Subira na ganinsu tayi murmushin nasara sannan ta kalli Hurriya tace ashe daman kedin ballagarazar barauniya ce kaskantarciya halan gadon satar kikayi daga tsaffi ta fashe da dariya sannan tace talaka haka kuke a ko yaushe sai kun nuna halin ku na kudin cizo banda halin kudin cizo ashe hada sata ma kike tohm Alhamdulillah yau anyi walkiya ashe banda sarkata hada wasu sarkokin tayi maganar cike da tsantsar wulakanci da rainin wayayu Hurriya kallonta tayi tanajin cewar kilan idan batayi wasaba wannan yarinyar kilan saita fidda mata yatsa daga jikinta shiru wurin ya dauka subira dariya tayi tace ba tare da wani bata lokaci ba ki durkusa har kasa bisa gwiwowin ki kibani hakuri kawai sannan ki kawo sarkokin hannunki Wani dan iskan kallo Hurriya ta bita dashi sannan tace hakuri zan baki ko tace subira ta daga kanta tana jijiga jiki tsotsar bakinta tayi sannan tace my Ass over my dead body ta juya tana mai kara damke sarkokinta a hannunta da niyyar barin wurin saidai wata irin azababbiyar dorina data shiga a jikinta saida ta dafe kanta murmushi subira tayi tace ina jiran crowling dinki sannan kizo har inda nike ki bani hakuri filthy maid ta juya tana kada jikinta wadda tasha maxi dress dinta mai masifar tsada sai heels dinta ta koma saman kujera tana kallon show din da ta hada Alamu tayi ma dogarawan da su cigaba da aikinsu wanda daman su jiran haka sukeyi da wata irin kyata suke zuba ma Hurriya bulala wadda har saida ta kai kasa jin bugun take har cikin kanta don har wani gigita dukan yake wata tsawa suka buga mata tareda cewa ki durkusa kije ki bata hakuri matsiyaciya yar dangin matsiyata kallon dukansu tayi da bloodshot eyes dinta a wulakance tadauki lokaci Sosai don kamar bazata ce koma ba ta tsirtar da miyau tace over my death body Ko sarki ban iya duka mawa bare kaskantarciyar diyarshi ta sannan tace kune sakarkaru bayi wadanda suka gaji tsiya ta ida maganar da tabbatar masu haka Don ko zasu kasheta a wurin nan bazata durkusawa ko sarkin garinba bare sakarar diyarshi saboda a masarautar su babban laifine ace descendant din royalty na Heral palace ya durkusa ma wani babu wanda yakai suyi ma hakan kuma har yanzu ba’a haifeshi ba. Dukanta suke kota ina tareda cewa ta basu sauran sarkokin dake wurinta amman ina After all her name is Hurriya Faisait Hamood babanta baida kafiya amman kakantane yake da wata irin kafiya babanta sanyi gareshi kankanta ne yakeda wani irin zafi idan ka taboshi kusan komai na kakanta ne ta dauko sarauta kafiya zurfin ciki kamewa duk na kakanta ne Basu ji basu gani don tace a amsar mata sarkokin Hurriya kuma dole ta durkusa ta bata hakuri Hurriya idonta jawur ta kafe don wani irin zafi zuciyarta takeyi mata kallon subira kawai takeyi subira kam dariya kawai takeyi Dawowarsu kenan daga spain yaje wani boardmeeting a matukar gajiye yake don ba abinda yake bukata irin hutuwa don yanzu suka shigo masarautar Qamar idonshi a lumshe suke yana cikin farar Lamborghini yayi relaxing kanshi. Bude idonshi yayi ta saitin inda dandazon mutanen suke a hankali ya lumshe idonshi don bai cika shiga hidimar da batashi ba Chief of security shine yake tukashi tsoki yayi ganin yanda mata sukayi blocking way din kwata kwata ba inda zasu gifta da sauri yayi connecting ya kira sauran convoys din yace su dakata ayi clearing hanyar Yasan halinsu sarai banna zasuyi don ba ruwansu da duk wanda zai gifta masu chief of security yayi ma Khalifha magana zaiyi clearing hanyar daga mashi kai kawai Khalifha yayi Chief of security wanda ya fito yana kallon mutane yana mamakim mai ke faruwa ba inda ya nufa sai wurin da yaga mutane sunfi yawa ya kutsa kai saidai cikin tashin hankali yazo wurin dogarawan da suke dukan Hurriya yace su bari dukanta Dukansu shiru sukayi mashi Kallon subira yayi don yagane ga dukkan alama abinda tace shine suke bi don haka yace zaku kasheta ki sanya su daina dukanta wata dariyar rainin hankali tayi tace kai asuwa tayi mashi rashin kunya ta zageshi tasss Ku tabbatar da ko zatayi yawo tsirara sai kun amsar min abinda ke hannunta sannan ta durkusa ta bani hakuri Shaho wanda zuwanshi kenan duk baiji dadi ba saboda badashi akayi show din ba yarinyar yana da alhakinta sosai don haka da zabgegiyar dorinarshi a hannunshi yazo da ita kallon dogarawan yayi sannan yace ku matsa Hurriya da duk ta jigata ta fita hayyacinta don ba kadan suka duketa ba ko ina na jikinta a farfashe yake saidai batajin ko zasu kasheta zata basu sarkarta sannan ta durkusa ma wannan wawiyar saidai she made a vow duk wanda ya sanya hannunshi sai ta sanya shi ya biyata ba tenfold ba thousands fold they will pay with biggest price Dukansu dake wurin nan Duk jininta da ya fita saita sanya nasu ya fita dubun nata wannan is a promise ko batayi promising ba tasan bata iya bacci idan har bata gansu cikin linkin ba linkin halin da suka sanyata ba Saukar bulalar da taji tundaga kanta har saman kanta ne wadda shaho ya zuba mata Tanada tabbacin inda ya buga mata a bayanta kayan jikinta ya fashe Tafiyarshi yakeyi wadda take dauke da sarauta da kasaita wadda take nuna shidin namijine sanye yake cikin wasu comme Des Garcons dark brown suit wanda suka fito mashi da kyau da haiba dinshi hannunshi sanye da jil sander wrist watch mai tsada komai nashi is screaming danger fuskarshi a hade take don ba karamar gajiya ya kwaso ba kuma ga dukkan alamu zai bata lokaci anan wurin he looks breathtaking handsome and coldhearted he looks superb in his suits saidai bazaka kara marmarin yi mashi kallo na biyi ba saboda hadarin shi. Daidai wurin da aka taru ya tsaya hannunshi rike da walking stick dinshi ta silver plated two horse cane,sandar tana featuring wani irin elegant horse mounted ne mai wani irin salki don kamar ya rike diamond,on a durable wooden shaft ,sandar may not be used for light balance kuma ba Daidai bane a sakar mata nauyi ba ko kuma wani orthopaedic support Khalifha ya hadu kuma dan gayu ne na gasken gaske don tun daga saman kanshi har kasan takalminshi designers ne mai mahaukatan tsada don shidai yana san extravagance life he always says miye amfanin neman kudi indai har bazaka kashe su ba. Hannunshi daya rike da sandar shi tunda ya tunkaro wurin aka fara darewa ana kallonshi Ba inda ya tsaya sai wurin taron. kallon kowa dake wurin yayi sannan cikin strong deep husky voice dinshi yace what’s the commotion here Subira kam yan hanjin cikinta banda kadawa ba abinda suke salati kawai take a ranta tana na shiga uku uncle Khalifha Qamar girgiza kanta ta farayi hawaye na taruwa a idonta Hurriya kam kwata kwata bataji don a hankali ta fara fita hayyacinta Khalifha kallonta yayi tana Neman faduwa kasa cikin yanayi na natsuwa a hankali ya durkusa tareda yi mata rumfa ta fada jikinshi a sume kallonta ya rinkayi tundaga kan dogon kalabar gashinta har zuwa kan shafefen cikinta dake sanye da adon gold kallon beautiful and innocent face dinta yayi sannan ya karkato inda rigarta ta fashe wanda har ta dan Zame ahankali yace disgusting cikin kasan makoshin shi sannan ya cire suit dinshi da hannu daya tareda yafa mata yadda zai rufe inda rigarta ya farke Kallon chief of security yayi sannan yace to the prison yess sir chief of security ya kalli Khalifha sannan yace what about the princess cikin izza yace all of them Dukansu Sannan ya dauki Hurriya kamar wata baby aka bude mashi mota ya sanyata tareda shiga ya zauna yana lumshe ido. [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: 🌚Masarautar Qamar The mysterious palace Last free page of Masarautar Qamar Wanda yakeso ya tura 300 ta wannan account din dari uku sai yayi screen shot ko kuma Kati airtel ACCOUNT NUMBER 3139107983 Khadija Mustapha first bank Katin waya airtel ta wannan number 08029520062 Sai a tura screenshot ta wannan number 08029520062 45&46 Idonshi lumshe sanyi ac da turaren wutan sai kuma kamshin turarenshi mai dadi ya sanya motar ta kara dadi kara relaxing kanshi yayi tareda lumshe idonshi yana kara shiga wani kalar yanayi na gajiya Ba inda suka tsaya sai part dinshi chief of security ya kalli oganshi da yayi relaxing sannan yace we’re here sir sannan ya zagaya ya bude ma Khalifha motar kallon hurriya chief of security yayi tareda cewa zan iya daukarta shiru Khalifha yayi sannan yace i will take her inji Khalifha Qamr tareda zagayowa ya bude kofarta ya dauketa ya shiga part dinshi da ita one of his room ya shiga da ita tareda kunna mata Ac . Dakin kamshin dadi kawai yakeyi sannan ya fito tareda rufe mata kofa cikin natsuwarshi ya shiga dakinshi tareda kiran chief of security yace yazo ya kaita hospital Chief of security wanda ya kada kan duk dogarin dayasan ya taba Hurriya harda subira suka tafi babban prison dake cikin masarautar suka turasu ba mutunci Sannan yazo ya dauki Hurriya kafin ya dauketa ne ya kalli Khalifha yace sir I think she passed out ahankali Khalifha ya dage kafadunshi sannan yace take care of that sannan ya juya ya koma ciki tareda sauke ajiyar zuciya Babban Dakinshi ya shiga tareda cire suits dinshi ba karamar gajiya yayi ba don haka ba abinda yake bukata irin ya samu good rest saidai bazai iya kwanciya ba tareda yayi wanka ba don haka ya daura farin towel dinshi cikin yanayi na natsuwarshi ya shiga toilet tareda sakar ma kanshi ruwa mai sanyin gaske ko ina yana shiga ajikin shi ahankali gajiyarshi ta fara sauka Hurriya kam ruwa chief of security ya sanya mata sannan ya kaita babbar asibiti private ta sai dan wane da wane wanda ya kai yake shiga asibitin don kusan Doctors dinma duk turawa ne da larabawa Yana zuwa aka amshe su hannu bibiyu sannan aka shiga da ita emergency don doctor din ya dauka accident tayi yanda farar rigar jikinta ta baci da jini Heral palace Babbar family dinner ce aka hada saboda dawowar layla Khasheem Hamood, Hamdan sam ba abinda yafi bukata irin su koma masarautar Qamar don ya bama Hurriya hakuri baisan mi yasa yakejin yarinyar har cikin ranshi ba Amman bari ya daina tunda bata sanshi Family ne antaru kusan kowa da kowa yasha ado nagani na fada ba karamar dinner bace aka shirya don wani irin babban family table aka shirya wanda yakecin fiye da mutum talatin kowa yasha ado nagani na fada Yanmata ne da samari hadaddu kuma yan gayu wanda kowa rike yake da iPhone yana basarwa su liya da neela suma suna zaune da wasu cousins dinsu Hamdan sam ya kasa gane kan Amrah tunda sukazo Heral palace don ba yadda baiyi da ita su dawo Daidai yadda suke a da Amman taki bari hakan ta faru ya rasa mike mashi dadi kwata kwata ya kosa su tafi don baida kowa anan duk bai saba dasuba sosai don shima yana da wahalar sabo Isowa akayi ma sarki Hamood da matar shi kujerunsu masu kyau suka zauna jikokinshi da yayanshi duk suka gaisheshi murmushi yayi tareda kiran amrah da take kallon Hamdan tana hararshi shi kuma Hamdan yayi mata alamar ban tausayi Kallon Dukansu yayi yana murmushi shafa kan Amrah yayi sannan yace mata mai ya hadaki da twin brother dinki a hankali yake mata maganar yadda ba wanda zai iyaji Shiru tayi tana turo baki alamar ba zata fada ba don haka ya kira Hamdan shi kuma yayi alamar ban tausayi Tambayar Hamdan yayi sannan yace minene ya hadaka da yar uwar ka ?? Dan bata fuska yayi sannan yace it started all because of Hurriya sarki Hamood yace Hurriya alamar tambaya ?wacece Hurriya maid din imad ce inji Hamdan kallon Hamdan sarki Hamood yayi irin to continue with the story because he’s interested .shikam Hamdan kamar daman abinda yake jira kenan ya fara bashi labarin Hurriya da isarta da mulkinta da kuma yadda ta raina kowa a masarautar Qamar kuma batajin tsoron kowa kuma da yadda yake Qaunarta saboda kyaunta Murmushi kawai sarki Hamood yake tareda son yaji karshen labarin Hurriya saida ba time don haka next time zai sanya akawo Hamdan ya cigaba da bashi labarin Hurriya kara shafa kan amrah yayi tareda cewa kiyi hakuri ki daina fada dashi kinji Hurriya ta yafe mashi idan kun koma zatayi mashi magana ni da kaina zan aika mata da sakon rubutu na tabbas zata cigaba dayi mashi magana kinji Amrah kallon kakanta tayi tace da gaske Hurriya ta yafe ma Hamdan daga mata kai yayi sannan yace waye ya isa yace bazai yafema jikan sarki Hamood ba murmushi tayi tare da rungume su both da kakan da Hamdan tace thank you grandpa kuma na yafe mashi murmushi yayi yanajin wani irin kaunarsu Allah y’a jarabce shi da son Banafsha da Faisait saboda sudin yaran kirki ne kuma sukadai ne yaya a wurin the most beloved wife dinshi sune abubuwan da yake kallo yaji dadi Amman duk da babu yayan yanzu saidai jikokin Sarki hamood Har yau har gobe yana kukan rashin Hurain gani yake kamar laifinshi ne gani yake bazai taba yafema kanshi ba idan ba’a samo Hurain ba ya Allah tana raye ko bata raye Allah kadai ya sani kuma duk sunyi iya kokarin su wurin nemanta Amman shiru . Zuciyar shi ce ta fara zafi gashi bai fito da maganinshi ba don haka yace ma su Amrah da su tafi su zauna Jikokin shi da yayanshi kallonshi sukayi wasu sun tausayi mashi wasu kuma haushi yake basu yadda ya dauki Hurain da muhimmanci ko kasarshi dashi kanshi bai dauka ba komai Hurain kamar ita kadaici diya kuma abun haushin ba diyarshi bace jikarshi ce Amman yadda yake sonta ko yayan da ya haifa baiso haka Imad ne ya kalli faisaaal yace wai har yanzu ba a ga Hurain din ba?bata fuska faisaaal yayi yace har yanzu ba’a ganta ba gashi mai martaba yaki cireta sam a ranshi shiru Imad yayi yace Allah ya bayyanata Ameen Ameen sukace tare Layla Khasheem Hamood ce ta shigo babban parlon da kowa da kowa yake a family din wanda daman isowarta kawai ake jira Cikin catwalk dinta wanda takeyi a stage kuma yake girgiza dubban mutane take tafiya dayawa maza cousins dinta are crushing on her Saidai ba fuska Because of how arrogant and ruthless she was don haka da yawansu bata baki sukayi suna kallon yadda take tafiya Hamdan kam he can’t believe cewar finally he’s meeting his crush for the first time she’s more beautiful in person ashe don duk shows dinta da ake nunawa ba’a taba dakko kyau dinta irin wannan ba yadda take tafiya kamar bazata taka kasa ba aji tsawo kyau na hallita duka Allah ya bata Sanye take cikin wani hadaddiyar cambre blue riga ta prada dogayen fararen kafafunta duka bude kamar zataje fashion show wasu matsiyatan heels ne a kafarta wanda kamar zasu kare saboda tsininsu don ba kowani dan adam bane zai iya tafiya da dogayen takalman ba skin dinta wani irin flawless sai wani walkiya da sheki yake tasha very nude and light makeup tana da wani irin high fashion sense don ta iya barnar kudi wurin sitira da accessories she get the vibes money swags fame and the looks and abinda yafi komai dadi shine she came from the top ten prestigious family in the world shiyasa takejin tafi kowa a wurin Wurin sarki Hamood wato kakanta taje ta rungumeshi tace I miss you granpa murmushi yayi tareda rungume grandaugter dinshi yace i miss you too Layla how are you ? Ya tambayeta murmushi tayi cike da shagwaba tace I’m fine tunda naganka murmushi yayi tareda shafa kanta sannan ya kalli kowa yace let’s eat our food Nan da nan ma’aikata suka fara shigowa ana jera abinci kala kala diffèrent varieties of foods and drinks don kusan ko wani kalar abinci akwai da drinks su non al-Alcoholic drinks masu matukar tsada da dadi Abinci kala kala wanda they are worthing alot of money komai na abinci a wurin is screaming rich Ba wanda bai hallara adining din ba akayi serving dinsu Dukansu ba wanda ba dan gayu bane kuma ba wanda baiji da kanshi bare su ba inda suka fi bama muhimmanci irin wurin cin abinci wato table manners shine yake defining dinsu anan zaka gane how prestigious and elegant they are Ba wanda kakejin maganar shi a wurin saboda abincin da akeci har saida aka gama cin abincin tukuna Sarki Hamood na gamawa yace bari ya huta saboda jikin tsufa rakiya yayanshi sukayi mashi. Kusan kowa ya dawo ya zauna iyaye ma tashi sukayi suka bar wurin Saidai aka bar yan mata da samari da yara sunata fira kowa da click dinsu anata fira ana raha Hamdan kallon Layla yayi data kame wuri daya ba kowa kusa da ita murmushi yayi sannan ya taka yaje wurinta Saidai yana zuwa Daidai wurinta gabanshi ya fadi saboda yadda kamarsu ta fito sosai da Hurriya dogon hancinsu da lashes dinsu Saidai idanunsu ne ba iri daya ba da bakinsu Amman sunyi kama sosai kamar tasu ta jini kallonta Hamdan yake ba ko kyaftawa yanason ya tabbatar da kamarsu Saidai Layla tafi Hurriya haske don ita layla fara ce sosai irin na turawa while Hurriya skin dinta is a bit darker than na Layla Saidai fa Hurriya tayi mata nisa a kyau fintikau bambamcin su ita mai kudi dayar kuma yar aiki . Hamdan magana yayi mata yace hy layla I’m Hamdan from masarautar Qamar though i don’t know About you being my cousin but i really like you and admired you since before I knew we’re cousins you really inspired me and motivated me and you’re my role model I’ve always look forward into meeting you in person because i want to know how outstanding your beauty is and of course i see how you outshone everyone one here you really deserve the reputation tunda ya fara magana Hamdan layla bata kalli inda yake ba tsaye yayi Yana jiran yaji kalma daya ta fito daga bakinta Saidai ba kalmar data fito bayan tagama jan lokaci sai MAD Hamdan kam tunda yake ba’a tabayi mashi kalar wulakanci haka ba don yarone shi mai halin manya bare kuma ya tsani rainin wayau saboda bai shiga harkar kowa rayuwarshi Amman fa Layler role model dinshi hauka fa tace wato shine mahaukaciya. Dariya aka kyalkyace dashi ana kallon Hamdan wanda yake tsaye kamar statue yana kallonta don he never expected that from her saboda ba haka take ba a yanda yake following din social media accounts dinta da kuma yadda ake fira da ita ashe she’s not nice she was facading ,wannan ne real image dinta. Gyara tsayuwarshi yayi sannan yace so it was all a facade very disappointed in you layla Khasheem you don’t deserve the reputation ya kike tunani fans dinki zasuji if i announced to the public how rude you’re wata irin dariyar rainin hankali yayi sannan yayi spitting miyau kusa da ita yace aikin Riya dai haramun ne idan mutun zaiyi abu yayi shi tsakanin shi ga Allah idan kuma bazaiyi ba yayishi tsakani ga Allah , I see No reason while someone would pretends to be nice while he’s ruthless to his own family yayi tsaki tareda cewa Ruthless Bitch ya bar wurin tabb ba Layler ba duk wanda yake a parlon saida ya girgiza da abinda Hamdan yayi ma layla ba wanda yake maganinta duk cikin masarautar sai Sarki Hamood dayake Allah ya dora mata kaunar sarki Hamood din shiyasa a Rayuwarta bata kaunar Hurain Faisait Hamood saboda yadda kakan nasu ya fifita akan kowa kuma duk iskancinta ba wanda take shakka irin Hurain ba wadda take tsoron shiga hidimarta irin Hurain don duk yadda take da takama da mulki da sarauta Hurain ta fita a ko ina rayuwarta Hurain tayi mata fintin kau Shiru parlon ya dauka don ba wanda ya taba gayama layla magana makamanciyar haka saboda itadin celebrity ce kota ina tayi masu nisa sannan batada mutunci batada kunya Imad murmushi yayi Because Hamdan is indeed his brother tare suka fita da Ammar da faisaaal Sai kuma yan biyu suka biyoshi tareda su kausar. Masarautar Qamar Kallon kowa yake ta cctv camera cikin masu aikinshi magana sukeyi kasa kasa wanda duka yanajin abinda suke cewa kuma yana kallonsu ya rasa miye yake damun mutane duk masu aikin da ake kawo mashi sai sun kokarin yi mashi barbade ko kuma suyi mashi sata saboda suna kallon shidin makaho ne while yana kallon komai da idonshi yanzu da ace bai gani kamar da haka za’ayita cutar shi kai mutane yanzu ba amana. Tsoki yayi tareda kiran chief of security dinshi yace acanzo mashi masu aikin chief of security cikin ladabi yace shikenan angama Yau kwana biyu kenan da zuwan Hurriya asibiti don allurar bacci doctor din yayi mata don data farka ba karamin taurin kai ta nuna masu ba aiko doctor din yaga kafiya don baita Ganin mai kafiyarta ba aiko tana magana da chief of security tana jeho mashi magana cikin izza da rashin tsoro doctor ya zagayo ta baya a hankali ya tsira mata allura wanda saura kadan tajima kanta ciwo da doctor din don cikin wata tsawa tace how dare you touch my body tareda rike mashi hannu baccin daya gama sanya ruwan allurar da tabbas kilan hakan zai iya zamar mata barazana a rayuwarta Yana gamawa ya fara sauke ajiyar zuciya don yarinya ta tsorata shi Sosai Murmushi chief of security yayi tareda ajiye kaya masu kyau na sawa yace a bata extra care duk da Khalifha baice haka ba Har yanzu wasba kuka takeyi Bintu da inna hanne hakuri suka rinka bata suna cewa Hurriya zata dawo kadata damu tayi hakuri suna lallashinta amman wasba sam bata ganewa saboda ba inda labarin abinda ya faru baije ba cikin masarautar Hurriya an zaneta Hurriya barauniya ce wasu sun yadda wasu kuma sunsan sharri akayi ma Hurriya.bintu da itada inna hanne kansu suna cikin damuwa kawai fada masu ne basuyi ba. Yau ta kama kusan satin Hurriya biyu a asibitin ta warke sosai don duk ciwon da takeji ta warke saidai fa doctor din yaci wuyarta don baita ganin mutum mai kafiyarta ba kwata kwata ba’a taba mata jiki hatta nurses din bata barinsu ko a taimaka mata zuwa toilet but duk abinda tayi baiga laifinta ba her beauty is to be hold ba karamin kyau Allah yayi mata ba toh duk abinda tayi baiga laifinta ba Hurriya jikinta ya koma kamar madara dan sati biyun da tayi a asibitin ba karamin kyau ta kara ba don kamar ta shekara a asibitin sai wani annuri take fiddawa ga wasu dogayen riguna abayas da chief of security ya kawo mata masu wani irin kyau da tsada idan ta sanya suna masifar yi mata kyau don ko gyalen bata yafawa don tunda ta fara samun sauki ta kwance kalabar dake kanta manya manya. Doctor din tunda Hurriya tazo sau uku ya tabajin maganarta a karamar karya idan kuma zaiyi babbar karya tohm zaice baitaba jin maganartaba sosai yake jinjina mata don mutum sai ya dauka bebiyace ko kurma . Yanzu haka zaune take ta mike kafafunta shirye cikin wata dark blue abaya wadda tayi mata kyau sosai gashinta a gyara yake ya zuba a bayanta idonta lumshe tana dan tsotsar bakinta tana kallon sarkokinta Wanda tunda ta damke su à hannunta har suka zo asibitin bata sakesu ba. Jin alamar za’a bude kofar ya sanya ta maida sarkokin tana bata fuska chief of security ne yazo Kallonta yayi yace mutafi batayi mashi musu ba ta daga mashi kai shine ya daukar mata ledar kayanta ita kuma ta biyoshi yana kallon yadda larabawan Doctors din suka rinka binta da kallo duk inda suka wuce amman ita bai dameta ba Kallonta yayi sannan yace ki rufe gashin kanki mana banza tayi dashi wanda kamar bataji ba Ganin yarinya yar rainin wayau ce don haka bai kara ce mata komai ba har suka iso masarautar Qamar . Suna zuwa a hankali ta bude kofar ta fita rike da kayanta da sarkarta Duk inda ta gifta tanajin yanda ake kallonta Amman ko ajikinta don ta saba kuma ba bakon Abu bane awurinta and she doesn’t care 🤷🏿‍♀️ . Dakinsu ta shiga inda ta iske inna hanne da Bintu duk sunyi tsuru tsuru wasba kuma tana Bacci.. [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: 🌚Masarautar Qamar 47&48 paid book gashi nan amana wanda yaci amana tsakaninshi dani kuma da Allah Khalifha he’s not liking duk wasu masu aiki da ake kawo masa baisan miyasa mutane basu da gaskiya da tsoron Allah ba in fact shi bai yarda da kowa ba kullum sai an canza masu aikin chamber dinshi sai kuma idan an koresu suje cikin masarautar suna zagin khalifahn suna fadin dagaske shi Dodone don ba wanda yasan mai yake aikatawa sai yaje chamber Khalifhan hakan ya sanyawa mutane shakku da rudani Sosai alhalin basusan shi ake neman kashewa ba Subira saida tayi lafiyayyun kwana uku tana prison don ba wani mutunci tsakanin su da ita ,ba princess bace ko Queen ce ba ruwansu Because they only follow their masters order don haka ba irin zuwan da Ba’ayi ba domin su saketa suka ki, Sauro kuda cinnaka ba abinda ba cijeta ba karshen wulakanci da cin mutunci Uncle Khalifha ya sanya anyi mata don tunda take ba’a tabayi mata cin mutunci irin wannan ba kuma Duk masarautar ba wanda ya isa ya daga maganar hatta sarki Faizan mahaifinta saboda Khalifha baida sauki sam saida yasan punishment din da akayi mata idan ance gobe ta kara bazata kara ba tukunna ya sanya aka saketa. Hurriya sati daya kenan daga dawowarta asibiti ta warke sosai sannan ta cigaba da aikinta kamar ko yaushe wasba kam kullum tare suke zuwa wankin don kamar Hurriya zata kara guduwa haka sukeji yanzu rayuwarsu gwanin ban sha’awa don Hurriya ta sake dasu Dukansu Sosai duk da bata da yawan magana amman ana yawan fira da ita haka zasu zauna karkashin wata bishiya da Bintu da inna hanne sai Hurriya da wasba ana fira mafi lokuta da dama itadai Hurriya bata cewa komai saidai tayi shiru tana kallonsu Amman tana bada hankalinta baki daya a wurin hakan kuma ba karamin dadi yake masu ba. Khalifha kwance a wata doguwar sofa idonshi snye da glasses Sai sandar Shi Mai matukar tsada sai kyalkyali take chief of security alamomi sun nuna ya gaji da nemo masu aikin Khalifha kullum sai a kawo mashi mutane talatin amman basuyi ba yanzu bai tsayawa test din don kallo daya yake gane masu ,Don kusan duka kalar mararsa gaskiya garesu Hurriya kallon uwar bayi tayi da take fada mata cewar zata koma aiki part din Khalifha tunda subira abinda ya fauru kenan .Shiru Hurriya tayi tana jin duk dokokin Khalifha din ita batada matsala aikinta kawai zai kaita ina ruwanta da wani Khalifha bullshit uwar bayi ta kalleta tace Amman fa zaki gana da Ayyo. Hurriya batace mata komai ba kuma itama Uwar bayi ta riga tasan bazata ce ba. Don haka ta fara tafiya Hurriya tabi bayanta har saida sukazo wani katon wuri chamber din babbace sosai don duk tafi chamber su Imad girma Wurin an kawata shi da adon flowers tare suka isa wurin da uwar bayi aiko da sauri Uwar bayi ta fara Allah ya taimakeki tareda uwar dakinki Allah ya kara maku nasara tanata kirari da Addu’a Ayyo tayi murmushi tace Ameen Uwar bayi.kallon hurriya Ayyo tayi wadda kamar batasan da wata hallita biyu a wurin ba don hankalinta kacokam yana akan wayarta tana canza waka. Ayyo kallon Hurriya tayi tun daga dogon gashinta har zuwa kafafunta mutum idan ba fada mashi akayi ba zai rantse da Allah ba ma’aikaciya bace a masarautar Qamar don wata red doguwar riga abaya ce a jikinta wadda tayi mata wani irin kyau gashin kanta kitso biyu ne wanda ta daureshi ya dawo kadan sumar gaban gashinta a kwance kamar ta yara sai kuma annuri da tsantsar kyau da fuskarta take fiddawa tunda Ayyo take bata taba ganin Mai kyaun yarinyar ba fararen idonta masu kama da zaiba saboda haskensu sai kuma golden brown eyes dinta da suke kara sanyawa ta zama unique acikin mutane Kallonta Ayyo kawai takeyi Because she has never seen someone with this kind of beauty tanada aininhin asalin kyau saidai mai take takama dashi a masarautar Qamar a yadda tayi ko uwar dakinta ba tayi mata haka . Ganin kallon da Ayyo take mata ya sanya Hurriya ta dage girar saman idonta alamun lafiya kike kallona Ayyo murmushi tayi don bata taba ganin yarinya mai kwarinta ba don gaskiya yarinyar akwai confidence batasan ayyo bane ko kuma tasanta ne dagangan tayi hakan don ta burge ayyo kai gaskiya batasan ayyo ba da bazatayi hakan ba.abinda Ayyo ta gayama ranta kenan Ayyo alama tayi ma Uwar bayi ta basu wuri da hanzarinta Uwar bayi tabar wurin kallon Hurriya tayi tace ta zauna Hurriya ba musu ta zauna tareda kallon ayyo cikin idonta tana dage gira irin make it quick I’ve things to do Ayyo murmushi tayi tana karajin yarinyar a ranta don tabbas wannan itace zata taimaka masu wurin Ganin karshen Khalifha Qamar. Aiki zakiyi mana inji ayyo zamu biyaki Hurriya kallon ayyo tayi don ita batada matsala da ko wani aiki tafison tayi aiki ko wani iri ne kuma wanda zai bata kudi don bata yadda da bara ko roko ba dom haka zatayi aikin. Ahankali Hurriya ta kalleta sannan ta daga mata kai murmushi ayyo tayi tana ayyana abubuwa a ranta don wannan yarinyar daga gani baza tayi matsala ba don taga batada magana. Kinaji shi wanda zakiyi ma aiki zaki rinka kula da duk wani motsi nashi abinda yaci inda yaje inda ya kwanta kuma har yanzu makaho ne ? Sannan akwai magungunan da zakina barbada mashi kinaji ana biyanki dubu dari duk wata .shiru Hurriya tayi sannan tayi twitching bakinta ta kalleta sannan tace yayi kadan ,Da mamaki ayyo ta kalleta sannan tace dubu dari fa Hurriya cikin aji da natsuwarta ta daga mata kai jinjina kai kawai ayyo take don duk wanda suke sawa aikin basu taba cewa za’a basu dubu dari ba Amman sauran cikin so da kaunar hakan don kamar anyi masu albishir da zuwa makkah haka suke murna amman wannan dubu dari tace bazata amsa ba Murmushi ayyo tayi don ta hango amfanin da Zatayi masu tace dubu dari biyu tayi?Hurriya kallonta tayi sannan ta dan ciji lebenta ta tashi tsaye tace make it 1M shiru ayyo tayi tana kallon bakinta da yake magana sannan tayi wata dariyar rainin hankali tace Miliyan daya fa kikace ?Hurriya daga mata kai tayi tana kokarin barin wurin don tagama magana bata amsar ko nawane idan bai kai 1M Har ta fara tafiya ayyo tayi saurin dakatar da ita don ta hango alamomin nasara tattare da yarinyar sosai ma yawwa tohm miliyan daya duka kudin aikin ki? Hurriya tana kallon wayarta tace duk wata miliyan daya sannan tayi tafiyarta batare da ta kara bata second glance ba. Uwar bayi tana tsaye tana jiranta har tazo inda ta tsaya kallon Hurriya tayi tareda cewa ya kukayi kun Daidaita shiru Hurriya Tayi mata.ita kuma ta kama bakinta bata sake cewa komai ba Daidai inda sauran ma’aikatan suke nan suka iskesu sannan suka nufi inda chief of security yake kallon yan matan yayi yana Addu’a Allah ya sanya karshen wahalar kenan don tunda suka dawo yake wannan aikin shi kanshi Khalifhan ba yadda ya iya shike aikin Chamber da kanshi saboda tsaftarshi Amman yana bukatar masu aikin saboda girman Chamber dinshi yana fatar cewar Allah ya sanya wannan karan adace duk cikin zuciyarshi yake maganar. Idonshi suka sauka akan Hurriya wadda fuskarta take a hade ba karamin kyau tayi ba cikin red rigar da ya kawo mata tana da kyau tanada aji duk a ranshi yake wannan maganar don zai iya rantsewa da Allah bai taba ganin mace miskila mai ajinta ba Wata Dariya yayi a ranshi yana fatar Allah ya sanya Hurriya tayi ma Khalifa kuma babu cuta a ranta. Kallonsu yayi sannan ya zabi wadanda zasu fara aikin kafin gobe ko jibi Oga Khalifha yayi firing dinsu don Khalifha kwata kwata bai jira. Kallon sauran yayi yace kuyi hakuri sun isa Hurriya harta juya yayi sauri yazo wurinta yace kina cikin ma’aikatan Khalifa kema batace mashi komaiba kuma daman shima baiyi tsammanin zatace mashi wani Abu ba Juyawa tayi ta shiga wurin ma’aikatan Khalifha murmushin da ba ko yaushe bane a fuskarshi chief of security yayi tareda juyawa ya farayi masu magana kamar haka don duk sharruddan Khalifha aka fada kuma ba wani aiki Sosai don ance banda sata banda cin Amanar oga Khalifha ta hanyar cutar dashi a abinci ku kiyaye duk wadda ta kiyaye zata zauna lafiya da Khalifha Qamar Hurriya shiru tayi don kamar taso tasan sunan tunani ta fara sai a hankali ta tuna shine wanda ake gulmarshi a masarautar nan kenan Palace and their issues duk tasan ire iren gulmace gulmacen da akeyi a masarauta don itama ansha maganganunta a masarautarsu So he was the mysterious person that everyone in the palace was talking about . Shrugging tayi alamar I don’t care daman ita miye ya hadata da abinda ba ruwanta Chief of security kallon Hurriya yayi yaji ta kwanta mashi arai saboda daga yanayin ta ita ba munafuka bace batada boye boye a yanayinta kaifi dayace don haka itace wadda ya kamata ta rinka kula da har wurin baccin Khalifa ya kamata ya huta shima khalifan Zuwa yayi saitin Hurriya sannan yace aikin ki yafi na kowa Because you’re going to be his personal maid please kada ki cutar dashi ko nawane zan biyaki You’re going to take care of him Day &Night i will pay you ko nawane you just have to name your price kinji. Shiru Hurriya tayi tana tunanin offer dinshi don Nigeria takeso ta bari shiyasa ma tace ma ayyo miliyan daya dazu ,ya kamata ta canza wuri saboda kawai she’s not feeling safe a masarautar Qamar din tanajin wani feeling na uneasiness kuma tunda ta fara jin wannan feeling din ya kamata ta bar masarautar saboda zuciyarta na bata cewar masu tracing dinta sun fara kokarin ganota ko kuma dai akwai abinda ke jiranta Shiyasa take bukatar taje saudiyya tayi ibada hade da extending din kwanakinta acan kilan idan ta tafi saudiyya tayi shekara biyu acan idan ta gama shekara biyu sai ta samu Europe country mai sauki taje can ta cigaba da zama koda Canada ce tasan ba zata rasa abinyi ba yanzu a kullum wannan tunanin take she’s desperate to get money ta tafi her instincts is telling her to leave this palace soon idan ba haka ba tohm something big is going to happen she’s having this feeling these days. Shiru tayi tana kallon cheif of security she can’t reject this offer ina tana bukatar kudi minimum 5mil maximum kuma 10mil she can do better she can do it ahankali cikin calmness dinta ta dage gira tace your conditions.murmushi yayi don yarinyar gaskiya tana burgeshi tanada aji ba kadan ba ga kyau na daukar hankali ga mulki ga miskilanci murmushi yayi sannan yace abinci sau uku a rana kuma ki tabbatar da duk abinda zaki bashi zaici sannan ke zakina gyara mashi daki ki hada mashi ruwan wanka hade da bedtime story idan yayi Bacci sai kiyi mashi addu’ar bacci and abu na karshe kada ki sake ki bari ya koreki saboda abinda yafi komai sauki kenan Shiru Hurriya tayi tana kallonshi bata ko kyaftawa har ya kai aya sannan tace nawane zaka biya? Murmushi yayi yace name your price money is not my problem.hurriya tsotsar bakinta tayi tace 2.5M everymonth chief of security murmushi yayi yace indai zaki iya it’s a deal a hankali Hurriya tace Deal sannan yace mata thank you. Har ya juya ya dawo yace mata na baki nan da 3weeks ya fara cin abincin da kika dafa idan har 3weeks tayi baici ba tohm the deal is canceled duk idan bakiyi duty dinki ba tohm bazan baki kudin ba.Shiru tayi ba tareda ta kara cewa komai ba don abun will be very tough for her because after all sunanta Hurriya Faisait Hamood ba komai take tolerating ba rayuwarta Amman it seems like she will tolerate so much of shit this time around da takeso tabar masarautar Qamar. Yau ta kama zata fara zuwa aiki part din Khalifha Qamar su dayawane ba ita kadai ba Saidai ita personal maid dinshi data zama aikinta ya bambamta dana kowa don haka da wuri ta tashi duk da daman yanzu ta rage makara sallahr asuba saboda idan wasba ta tashe ta a bacci tana komawa wasba zata cigaba da kukan karya har sai Hurriya ta tashi .Saidai ta kalli wasba din taje tayi alwala ta dawo tayi sallahr yanzu har ta saba. Uniform ne ta sanya sunata kamshin turarenta tun wanda chief of security ya siya mata lokacin da ta kwanta asibiti gashinta a daure yake wanda ya cika sosai yayi yawa ga tsawo don haka ta tattare shi ta daureshi tare da cusa tikar gashin cikin gashin yadda bazata fito ba. Tayi kyau sosai ba kadan ba don haka ta fito Daidai kofar ta iske uwar bayi wadda daman da alama Hurriyar take jira don haka tace mata Hurriya ahankali hurriya ta juyo tana kallonta Uwar bayi tace har an fito daga mata kai tayi.uwar bayi tace ayyo tana bukatar ganinki zaku ida maganar da kukayi jiya. Hurriya daga mata kai tayi sannan tace idan nagama aiki ta juya tabar mata wurin. Tafiyarta a hankali Saidai yau ba earpiece a kunnenta har ta kawo part din Khalifha Qamar kusan kowa yazo duk da safiya ce kallon abokan aikinta tayi wanda sai dadi sukeji da alama itama kallonta suka rinkayi kamar zasu cinyeta Ba wanda ta karayi ma second look acikinsu ta haura sama inda take tunanin tanan zata iya shiga dakinshi wow kawai take fada a ranta data faracin karo da parlon shi na sama komai na parlon look mysterious don bata taba ganin an kawata wuri da dark color ba kuma dark color din yayi kyau irin parlon shi ba hatta fentin parlon dark brown ne sai kujerun da aka kawata parlon dasu brown and black everything is screaming rich and elegant and everything look so mysterious and dangerous color din parlon kadai yagama defining waye mutumin komai na parlon yayi mata kyau and she fall for the dull color don itakanta batasan dark color nada kyau ba sai yau Because ita tafison light color because of how neatness she was so tafison light color for the first time wani abu ya burgeta wanda ba nata ba a rayuwarta tunda take rayuwarta wani ko wata baya burgeta ko abun wani ya burgeta babu Saidai ta burge mutane ko akwaikwaye ta haka rayuwarta take. Sauke ajiyar zuciya tayi ta bude dakinshi a hankali Saidai kamshin da taji ya sanyata lumshe ido duk da cikin kamshin tanajin irin danger da power da kamshin yake emanating dakin yayi wani irin dim Amman tana kallon yadda yake dukunkune cikin dark duve wanda ya rufe ko ina a dakin sanyin Ac dakin ya kaishi karshe duka Ac biyun da split da standing ac wanda sanyi ke ratsa ko ina a kashin mutumin . Switch ta kunna na wuta tana kallon dakin in awe saboda haduwarshi don komai dark brown ne mai matukar kyau da tsada ajiyar zuciya ta saki sanyin na kara shigarta tsoki tayi tareda kashe duka Ac din tana kallon komai neat and intact basai an fada mata ba mai dakin is a neatness freak don yadda aka jera komai da muguwar tsafta Ajiya kallon komai tayi ta shiga toilet dinshi wanda shima komai dark ne hatta towels dinshi dasu toileries dinshi Bata wani bata lokaci ba ta shiga wankin toilet din cikeda kwarewa kuma da iyawa ba ha’inci sam a aikin Hurriya koda tagama wanke toilet din saida ta maida mashi komai inda ta ganshi ta fito. Kallon yadda ya kwanta yana bacci tayi shiru tayi tana tunanin yadda zata tadashi tuna yadda ta tada Imad tayi ranar farko data fara aiki a wurinshi murmushi tayi a hankali don she missed them all Hamdan Amrah Imad and Ammar duka tayi missing dinsu harda liya da Neela she hope they are enjoying themselves in Heral palace obviously ma tasani A hankali ta fara neman comb Everything intact duk inda ta duba bata gani ba sai da kyar ta hango comb din daukar comb din tayi tazo saitin gadon tareda hawa saman gadon kadan Hurriya kamar tanajin tsoro ta fara zame duve din daya rufe kanshi dashi har saida ta sauke shi duka Kallon yanda yake bacci very peaceful tayi yaune ta fara ganinshi a rayuwarta hé’s handsome and mysterious kallon dogon hancin shi mai kyau da daukar ido tayi sannan tazo har bakinshi bakar sumarshi agyara take wani irin kamshi yake wanda takejin shi har cikin kanta snapout Hurriya tace ma kanta sannan ta gyara natsuwarta A hankali ta fara goga mashi brush din tun daga kanshi har fuskarshi kamar tana sosa mashi kanshi. Khalifa wani kalar yanayi ya fara shiga yadda take sanya brush a saman gashin shi. Da wani irin zafin nama Khalifa ya rike hannunta tareda bude idanunshi masu kyau da kwarjini Saidai bazata iya ganinsu ba saboda suna cikin glass din cikin wata deep strong voice dinshi yace how dared you touch my royal body Hurriya kam ta kasa cewa komai saboda yadda ta shiga shock how dare he touch her ta rasa mi zatayi mashi wanda zai kasance Daidai da yadda ya tabata Saidai ta kasa koda motsa hannun damanta don har yanzu Khalifa rike da hannunta yana binta da wani kallo Hurriya dagewa tayi ta taro miyau mai yawan gaske sannan ta tsirta mashi a fuska Da sauri Khalifa ya saki hannunta he never saw that coming miyau fa how dare her ?his filthy maid just spit at him Mad 😡 Hurriya kam ba wani remorse tattare da ita don wani deadly glared kawai take aika mashi don tabata da yayi Daidai yake da atsirta mata yawu acikin bakinta ko a fuskarta Khalifa cikin zafin nama ya jawota da karfin gaske tare da fadowa saman jikinshi. Q [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar P.49 Shiru Khalifha yayi yana kallon gashinta da ya sagale a kunnenta ta zaro ido tunda take ba’a taba yi mata abu kalar wannan ba how dared he touch her with his filthy hand Khalifha hannunshi zagaye da waist dinta cike da mugunta ya kara jawota tareda hade fuskarsu wuri daya don saura kadan bakinta ya shiga cikin nashi ya goge yawun data zuba mashi a fuskarshi da fuskarta sannan ya tureta ya mike tsaye cike da kyankyami ya nufi hanyar toilet dinshi . Hurriya kam kasa yarda tayi da abinda ya faru yanzu tunda take a rayuwarta ba wanda ya taba yi mata rainin da wannan so called master dinta yayi mata she can’t believe how he Hugged her without her consent. rules dinta ba wanda yake tabata he’s the first male person that break her rule tunda take wani namiji bai taba kama koda hannunta ba face mahaifinta sai kuma kakanta sai kuma past dinta da batasan tunawa shiru tayi don sam ta kasa yarda da abinda ya faru that inhuman prince almost kissed her she can’t forgive him gaskiya. Khalifha ya kasa yarda da abinda ya faru yanzu Ina ta samu audacity din dazata shigo mashi har dakinshi not dakinshi data shigo ma the way she woke him up and she dared to spit at his face bazai iya yafe mata ba A hankali ya daura towel dinshi tareda fitowa kallon yadda ta gyara ko ina na dakinshi yayi wurin yayi fes fes kallon small figure dinta da gashin kanta wanda ya kwanta ko ina yayi ,wani Devil smirk ya fito mashi. Har Hurriya tazo wurin vanity table bata lura da mutum ba don tazo zata goge madubi Goge madubin tayi cikin yanayin natsuwarta da kwarewa a aiki saidai juyowar da zatayi suka hada ido da yarima Khalifha tsaye yana kallonta jikinshi sai kamshin shower gel yake sai wani ruwa da ya kwanta mashi a jikinshi sumar kanshi mai matukar kyau da daukar hankali Hurriya kam wani kalar zare ido tayi tareda fasa wani kalar ihu ta rufe idonta da tafukan hannunta tayi hanyar kofa saidai ko tafiya bata fara ba ya tadiyeta tareda riko mata hannu ya dagota kallonta yake ta cikin glasses dinshi yana kallon zallar bacin rai wanda ya kasa boyuwa a fuskarshi cikin kokarin kwace kanta take Amman yaki barinta tayi hakan da kyar take hadiye miyau Tunda take ba’a tabayi mata abinda wannan Khalifhar yayi mata ba. Karshen cin mutunci yayi mata har sau biyu amman zatayi maganinshi.khalifha kallon idonta masu kama da zaiba yayi saboda hasken da suke fiddawa kwayar idonta mai masifar kyau don har wani gold gold gareta cikin deep strong husky voice dinshi yace who send you ? Hurriya idan zai bude zuciyarta to dole ya ruga saboda irin bacin ran da take ciki ta rasa mi zatayi mashi wanda zai saketa tunda baida mutunci baida kunya Khalifha kam ya tsareta da ido yana kallonta yana jiran amsarta Hurriya ta rasa mi zatayi all her life ba’a taba mata jiki shine rule dinta na farko ganin baisan ido ba aiko ta duka ta ciji hannunshi da karfi wanda Khalifha ko gezau baiyi ba Hurriya ganin yaki sakinta ya sanya ta tattaro yawun bakinta ta kara watsa mashi a fuskarshi aiko da gudu ya saketa. A guje tabar wurin tana sakin ajiyar zuciya kallon hannunta tayi zuciyarta na bugawa duk inta tuno yadda ya riketa sai taji wani irin haushi da bakin ciki jerk Ass tace sannan ta fita. Ba inda ta tsaya sai kitchen tana zuwa tace ma inna hanne ta zuba mata ruwan wanka inna hanne ba bata lokaci ta zuba ma Hurriya ruwan wankan Hurriya ba inda ta tsaya sai toilet saida tayi wanka na mutunci don duk inda ya taba ajikinta saida ta wanke sannan ta fito tana dan jinta Daidai ,kamshin turarenshi da dakinshi duk ya cika mata hanci yana barazanar dagula mata lissafi hade dajin haushin Khalifha yake koma waye Kaya ta sanya riga da skirt na English wears don skirt din Daidai gwiwarta ma ya tsaya sannan ta fito taje wurin Chamber din ayyo inda suke jiranta ba wani alamar sauki bare fara’a a fuskar Hurriya don gaba daya ko Khalifha yake or whatsoever ma ya gama bata mata rai Zama tayi a saman kujera ayyo ta kalleta tace nayi magana da uwardakina tace za’a biyaki ko nawa kikeso indai kin tabattar bazai koreki ba Hurriya daga mata kai tayi tace bazai taba korata ba kuma inda harna daina aiki sashen shi tohm sai kudaina biyana Ayyo kallon Hurriya take don ko yanayin da take magana tasan ba karya take ba don a yadda ayyo ta shahara ko karya daya mutum ya fadi zata iya kamashi Hurriya ta ajiye mata account numberta tace ina jira sannan ta juya tabar wurin . Galadima ya kalli boka yace to yanzu mi za’ace mashi Boka dariya yayi yace akwai matsala babba kuma akwai maganin matsalar duka acikin masarautar galadima sakin baki yayi yana kallon boka domin yana bukatar karin bayani Boka cewa yayi ka fada mashi akwai yarinyar da idan har ya sameta to ba sarki a masarautar Qamar ba kowace sarauta ta zai iyayi ya nemi yarinyar tanada matukar amfani a rayuwarshi. Shiru galadima yayi tareda buga tagumi wata dariya boka yayi yace sai kun mike tsaye wurin fa neman yarinyar don nakasa gane wani abu a kanta amman ka dawo nan da sati daya zan kara bincike galadima godiya yayi mashi tareda kara tambayar shi makantar Khalifha fa? Dariya yayi yace da kanku zaku gane idan lokaci yayi Shima sai kun mike tsaye lokacin ka ya kare Galadima da yasan tunda ya fada mashi lokacin tafiyarshi yayi to ba abinda zaisa ya cigaba da ganawa dashi don haka ya fita tare da jimamin alamuran dake neman tun karosu Duk da bai fada masu komai akan Khalifha ba Amman hakan bazai sanya su saki jiki ba Amman yace sai sun mike tsaye akan Khalifha sannan su nemo yarinyar indai har sarki Faizan yanaso ya cigaba da sarautarshi. Galadima jikinshi ba karamin sanyi yayi ba Amman haka ya tuka motarshi har ta kawoshi masarautar Qamar ko hutawa baiyi ba yaje chamber sarki Faizan sannan ya warware mashi komai Sarki Faizan sauke ajiyar zuciya yayi tareda kallon galadima yace to ya zamu fara neman yarinyar?bai fada mana ba Amman yace nan da sati daya In koma zai fada mana yadda zamu nemeta.shiru sarki Faizan yayi tareda shiga cikin tunani da fargaba kada fa dagaske Khalifha yazo ya amshe sarautarshi ne? Sauri yayi ya basar da maganar ba tareda ya yarda da abinda zuciyar shi keyi mashi waswasi akai ba. Galadima ya kalli sarki yace maganar yanmatan da za’a kawo wannan shekarar. shiru sarki Faizan yayi sannan yayi murmushi yace wannan ai ba matsala bace jakadiyya zata shirya komai yanda ya kamata Kuma ai an kawo mata cikin masarautarnan wannan shekara sosai har ance matan wannan shekarar sunfi na waccan shekarar kyau da komai Galadima murmushi yayi yace nima naji ana fadar kyawawan da aka samu a wannan sunfi na waccan shekara shekarar murmushi galadima ya karayi sannan ya hau yima sarki addu’a murmushi sarki faizan yayi tareda sallamar galadima. Sarki faizan tashi yayi yanata yawo acikin makeken parlon shi wanda yake shake da abun more rayuwa. Manage this please on &off nepa suka rinkayi mana. [5/28, 3:32 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 49&50 Sarki Faizan tunani kawai yake yanda zai tarbi abinda yake neman rusa shi gaskiya Khalifha ya mamayeshi sosai don baisan da dawowar shi acikin masarautar ba samm tunda ya tafi saida yayi shekara kusan 8yrs bai dawo ba sai yanzu ai da ya tanaji komai yanda ya kamata. Zinariya tayi shiru tana kallon kuyangarta tana fada mata duk abinda ya faru data bar masarautar shiru tayi tareda daura hannunta akanta tana magana cikin zuciyarta wato duk kashedin da tayima subira bataji ba saidai fa kuma wanda baya jira yayi hukuncin shi kamar yadda ya saba wani murmushi tayi na gefen baki don tana hango kura cikin masarautar nan. Hurriya duk yanda ta iya boye duk wani emotions da damuwa zaka iya hango damuwar dake kwance a fuskarta don wani tsoro tsoro takeji hankalinta duk yabar jikinta she need to leave masarautar Qamar as soon as possible don ko yau saida tayi mafarki marar dadi she need money she desperately needs money wani tunanin ya fado mata kodai tayi using kudin account dinta na Heral palace kwabar zuciyarta tayi da tabar wannan tunanin saboda tasan yadda har yanzu ba wanda ya manta da wanzuwarta acikin mutanane duk da cewar shekarun da suka shude Sarkokinta ta kalla ko zata saida daya ne daga ciki ita kanta sarkar idan ta saida ba karamar matsala zata zamar mata ba abubuwan sun hade mata. Bata kasance cikin mutanen wanda basu iya maganin damuwar su akoda yaushe ta kasance cikin mutanen masu kokarin magance damuwarsu duk girmanta .ta rasa minene mafita don bazata iya cigaba da aiki a Chamber Khalifhaba saboda watarana kilan zata mareshi ne kawai kuma duk aikin da tayi baza’a biyata ba idan tayi kuskure daya ko kuma a daureta and she don’t care. Ta tsani bossing a rinka bossing dinta around tunda take rayuwarta ba wanda yake bossing dinta but seems like Khalifha tun daga dull color din da aka kawatashi a parlon yayi defining Khalifha Ta riga tasan mafitar guda dayace shine tayima Khalifha aiki tanan ne kadai zata iya hada kudin da zata bar kasar nan. Kallon kanta tayi a madubi fuskarta tayi fayau wandone jeans blue Amman baggy ne sai bakar riga jikinta tayi kyau na fitar hankali wasba ta kalleta cikin yanayin damuwa tace Aunty Hurriya mike damunki kwana biyu shiru Hurriya tayi don ko kallon inda wasba take batayiba tayi tafiyarta tanajin yadda wasba ta kwalla ihu alamar kukan shagwaba murmushi Hurriya na gefen baki tayi tace bratty ta fita abinta. Bangaren Khalifha ta shiga wanda batayi gigin shiga dakinshi ba yau har an gama shirya mashi breakfast a full table dinshi mai kyau kuloli masu kyau da fararen plate sai cups masu kyau lokacin da Hurriya taje har angama jera komai a table din kallo daya tayi ma ma’aikatam da duk sukayi cirko cirko alamun mararsa gaskiya Hurriya wani wuri ta samu ta zauna cikin kujerun parlon tana kallon news a Tvn Tsaye yake a wani makeken daki wanda yafi bedroom dinshi girma dakin wani irin girma da kyaun gaske gareshi yana tsaye tareda kallon duk abinda yake faruwa a parlonshi ta na’ura. Duk abinda masu aikin sukayi kafin Hurriya tazo yana kallonsu don sabbin note na kudi ya sanya aka aje mashi a parlon acikinsu ba wadda bata zara kudin ba face Hurriya data shigo daga baya. Backward yayi tareda kallon yadda Hurriya take tafiya cike da yanga da aji cikin wata catwalk din da bai taba ganin wani yayi irinta ba tunda yake rayuwarshi. Fuskarta a hade as usual har zaman da tayi a kujera ya kalla sai a lokacin ya ganeta itace yarinyar da aka hada hold up saboda ita har ya dauketa ya sanya aka kaita asibiti ta raising brows dinshi yayi sama yace interesting. Wata slide door ce ya bude ya fito aininhin bedroom dinshi da yake kwana ya fito dakin sai kamshin turarenta wuta mai dadi da tsada yake Khalifha yanason turaren wuta sosai don da kanshi yake sayen turaren wuta masu matukar dadi da tsada. Sanye yake cikin wata riga tight ta house of versace black wadda tayi mashi kyau kuma ta fito mashi da charisma dinshi ba karamin kyau yayi ba wandon shi désigner Na Ralph lauren wanda ya daidatu da shigar shi walking stick dinshi wadda take screaming danger ya rike sannan ya nufi downstairs. Tun kafin ya ida saukowa daga saman bene ko ina ya cika da kamshin turarenshi mai dadi takunshi duk ya isar masu da sakon zuwanshi banda mutum daya wato Hurriya. Wani irin shiru parlon ya dauka kamar babu kowa acikin parlon sai karar tv da ac kawai ke tashi Hurriya hankalinta gabaki daya yana kan news din da akeyi na earthquake din da akayi a turkiya. Karar plate cups da kuloli kawai kakeji a wurin duk an watsa su kasa katsam tartsatsa kawai kakeji Batare da ta shirya ba kawai ta waigo domin karar ta shiga har cikin kwakwalwarta don kamar earthquake din da take kallo yanzu a tv yazo inda take haka taji Natsuwarta tayi saurin nemowa saboda bata cika barin rashin natsuwa tattare da ita ba Kallon saitin Khalifha tayi wanda yake tsaye da sandar shi fuskarshi babu alamun wasa don duk sun kusa rugawa masu aikin da suke kallonshi You’re all fired bunch of useless ya fada da wani irin karfi da tsawa Dukansu cikin wani irin firgici suka fara kokarin guduwa harda masu faduwa acikinsu saboda tsabar rudewa kafin kace komai duk sun bace a wurin Yasan tana a parlon juyowa yayi ya kalli saitin da take a hankali ya tako yazo wurin kallo daya tayi mashi tareda juyar da kanta . Khalifha cikin strong voice dinshi yace what are you doing?Do you want to die Hurriya shiru tayi ba tare da ta kalleshiba bare ya sanya ran zata amsa mashi Khalifha he was shocked saboda baya magana ba tareda mutum ya shiga hankalinshi ba He control everything around him wealth,feeling,aura emotions,maids,employees seems like he can’t control the girl that is seating right in front of him Cikin yanayin natsuwarshi ya sauke numfashi tareda kallonta she’s unparalleled beauty tanada kyau sosai saidai too bad he don’t like beautiful women Saboda most of them are cheaters Hurriya saida taga dama tukunna tace I’m not fired I will serve you your highness zanyi aiki a chamber dinan and trust me ba wanda ya isa ya koreni. Kallonta yake ta cikin glasses dinshi yana hango gaskiyarta a maganarta like she own the chamber wani Devil smirk yayi ya juya. Tashi tayi tazo inda ya bata da abinci ta fara clearing tasha aiki sosai don saidata tabbatar da ta gyara duk inda ya bata Allah ya bata sa’a kam tana juyowa taga babu shi Cikin zallar bacin rai yake waya muryarshi a kausashe yake maganar wadda kamar maganar business ce ta sanyashi magana cikin bacin rai shiru yayi don tabbas sai ya bar kasar nan yaje Germany da kanshi kuma baison ya tafi a irin wannan lokacin saidai gwara yaje da kanshi Because he can’t loose millions of dollars he values money saboda ya iya neman kudi duk daya fito daga gidan sarauta bai yadda yayi depending da arzikin masarautarsu ba don da kanshi ya nemi kudinshi kuma yayi making name a business world don a kasashen waje yake business dinshi he intimidates people by just his aura don haka duk wani business da zaiyi duk girman shi kuma duk wahalarshi da tsautsayi indai yazo wurin shi to ba komai bane a wurin shiru sai ya samu kudi with his hardwork and determination he had climbed far higher that a man intended to da kanshi yayi wahalar Neman kudinshi wanda idan yaso zai kwanta gida ba tareda ya fita nema ba kuma ba abinda zai ragu dashi indai arziki najin dadin duniya ne Amman yasan banashi bane don haka ya nemi na kanshi sai yanzu kawai wani bature wanda bai kai ba zai kawo mashi matsala he will handle that man yanda ya kamata After all his name is The blind reptile poisonous and dangerous Hurriya bayan tagama duk abinda ya kamata ta koma daki tagaji Sosai don haka tayi sallah tareda kishingidawa kafin dare yayi taje ta hada mashi abinci ta riga tagama sanyawa a ranta zata amshi aikinta hannu biyu kuma zata bishi lalama har ta samu ta amshi kudin da zata bar kasar Allah dai yabata ikon hakuri shine maganar. Bacci mai dadi ya dauketa wanda ba itace ta tashi ba sai daff da magriba saida tayi alwala tayi sallah sannan tayi brush don bakinta taji wani yanayi tattare dashi saboda duk yau bataci abinci ba. Tana fitowa ta iske Uwar bayi a waje tana jiranta kallon Hurriya tayi sannan tace ayyo tanason ganinki ba musu Hurriya ta daga mata kai sannan ta nufi inda zata iske ayyo Tana zuwa yau har parlon farko saida aka shiga da ita ba wani alamar kauyanci tattare da Hurriya ta zauna ayyo kallonta tayi tana mamakin halin jinin sarautar da take dashi kauda tunanin tayi cikin zuciyarta sannan ta miko mata wasu magunguna kusan guda uku Hurriya saida tagama karantar ayyo sannan ta amshi magungunan ayyo ta kalleta tace daya ki barbada mashi a abinci safe rana dare,Daya kuma a inda yake kwana daya kuma sai ki samo mana gashin kanshi Hurriya shiru tayi tana kallon ayyo saida ta dauki kusan mintin biyar batace kala ba kuma bata tashiba ahankali tace kudina fa? Ayyo rike kanta tayi alamar damuwa tace idan aiki ya kammalu Za’a tura maki wani dan iskan kallo Hurriya tayi matw tareda yadda magungunan kasa sannan ta juya tayi hanyar kofa ai aguje ayyo ta biyota tace yi hakuri yar nan yi hakuri kudi dai kikeso ko yanzu zanyi maki transfer yi hakuri dauka Hurriya ko waigowa batayi ba bare ayyo tayi tunanin zata dauki magungunan Takaicin iskanci da yarinyar nan ya ishi ayyo haba mi take takama dashi cikin masarautar shegiyar yarinya mai mugun wuyar sha’ani tayi tsoki ta cigaba da maganganunta ita kadai. Hurriya kado ta shigo part din Khalifha ba kowa wani irin sanyi kamshi parlon yakeyi lumshe idonta tayi aranta tace he’s a neatness freak ta dade tana enjoying ita kadai don batasan miyasa ba she’s in love with each and everything in his part ko saboda bata saba Ganin an kawata wuri da dull color bane sai a wurin shi Don tafi ganema bright color don haka heral palace komai nata was bright Amman dull color ya shiga ranta sosai don har ta fara tunanin itama ta koma dull color irin na Khalifha kamar wata mysterious girl tace a ranta sannan ta shiga kitchen kallon komai na kitchen din tayi intact don ko wood din dake kitchen din shima dark colorne cikin ranta tace blind man and his dark color Harkar abinci ta fara don yau jinta kawai take kamar a kitchen dinta na Heral palace she surely misses alot don aiki ta farayi tana waka tana rawa kadan cikin kwarewa da kuma aji da zallar miskilanci a rawar. Abubuwa tayi Sosai banda main dish da tayi harda su appetizer side dish dasu desert sai guava juice data hada Bayan tagama komai ta gyara kitchen din tass don kamar yanda takeyi lokacin da tana Heral palace haka tayi komai sannan ta jerasu a babban dining table din. Kwata kwata batasan baya nan ba don kawai aikinta tayi Sannan ta samu wata yar kujera tadan zauna. Kamshin turarenshi da kuma aura dinshi da taji shine ya tabbatar mata da isowar shi a parlon fuskarshi a hade as usual a hankali Hurriya ta taso sannan ta kalleshi cikin yanayi na girmamawa tace welcome back sir,trying all her very best to be a good maid shiru yayi batare da ya kalli ko gefen da take ba da wani irin sauri ta kara cewa your food is ready sir . Shiru yayi mata sannan ya haye sama Hurriya kam all her life ba’a taba rainata irin na yau ba she’s Hurriya Faisait hamood fa how dared him tana mashi magana zaiyi banza da ita. Zuciyarta ta rinka cewa caim down Hurain calm down you’re his maid kuma he don’t wanna talk right now then leave the fucking idiot abinda zuciyarta ta rinka ce mata kenan don haka ta nufi dining cikin natsuwa da miskilanci ta zauna Bude dishes din tayi sannan ta ciji lebenta ta lumshe ido it’s been a while bataci abincinta haka ba don haka ta zuba komai a plate dinta accordingly with the best table manner take komai Daidai cikinta ta zuba komai Bismillah tayi ta faraci abincin tana lumshe ido yanda take cin abinci kamar wata American royalty saboda table manners dinta. Khalifha tun daga kan shigowarta ya fara kallo har shigarta kitchen da yanda ta rinka waka da rawa tabe bakinshi yayi yace arrogant fool sannan ya cigaba da kallo dariya yayi kadan Ganin yadda take aikin cike da kwarewa kuma da sauri takeyi tana magana cikin wani British accent wanda bai tabajin wani dashi ba tunda yake wani irin fluently.English din kuma British who is she?? Kallon yadda take cin abinci yake da mamaki don tunda yake bai taba coming across mutum mai table manner dinta ba kamar wata royalty ta America kamar kuma ta russia wani irin masifar kyau tayi wanda tana tauna lasagna din da tayi murmushi yayi escaping a bakinta Khalifha he almost freeze by just looking at her wasu dimples ne both suka lotsa harta gold din dake tsakiyar hakoranta biyu saida suka fito Who is she?what did she want from me itama tazone ta illata ni?saidai abinda yafi bashi mamaki wanda har yanzu bai ganeba ba abinda ta barbada mashi kilan ita nata abun sai nan gaba. Takun shi Hurriya kawai taji tissue ta dauka ta goge bakinta wanda bai baci ba kwata kwata Bazaka taba cewa taci abinci a wurin ba saboda table din da plate dinta very tidy Khalifha cikin muryarshi yace jack ai da sauri jack ya shigo yana I’m here sir cikin yanayi na miskilanci yace feed all this trash to my dogs . Abincin da ta dafa shine za’a bama karnuka itafa ce Hurain wato Hurriya Faisait Hamood. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 51 Shiru Hurriya tayi tana kallon jack wanda ya dauki duka abincin da ta dafa Khalifha kam ko second glance bai karayi mata ba ya nufi kofar fita. Hurriya shiru tayi tareda bin bayanshi da kallo . A kwana à tashi ba wuya wurin Allah yau har tayi kwana hudu da farayi ma Khalifha aiki duk yanda tayi tunanin saukin abun baizo mata da sauki ba.Duk abincin data dafa mashi bai taba kallonshi ba bare har ma yaci ita kadai take wahalarta don zata dafa ne taci ta koshi sannan ya sanya abama karnu kanshi ba yadda ta iya. Fannin ayyo saida Hurriya taji saukar miliyan daya a account dinta na Nigeria sannan ta amshi aikin da suka bata don ta amshi maganin saidai har yanzu bata zuba mashi ba Ta riga ta yanke hukuncin aikin wata biyu zatayi a Part din Khalifha bazata bari shekara ta zagayo mata ba tana cikin masarautar Qamar kudin da zata hada zasu kai 7m dana part dinshi dana ayyo don haka tana gama umara sai ta wuce canada Bintu ce ta shigo duk ta rame kwana biyu sam basu hadu da Hurriya ba don Bintu naganin Hurriyar kamar ta juya kallon tuhuma Hurriya ta rinka binta dashi. Bintu kallon kasan siminti tayi Hurriya a hankali cikin zakin muryarta tace miye ya sameki ahankali Bintu tace ba komai shiru Hurriya tayi sannan ta rinka bin ko ina na jikinta da kallo sannan ta fita ba inda ta tsaya sai wurin inna hanne saida suka gaisa tace mata tanason ta bincika mata abinda ke damun Bintu.inna hanne ta bata assurance din insha Allah zata duba mata Hurriya ta nufi part din Khalifha abayace jikinta fara tayi mata masifar kyau don banda annuri ba abinda takeyi Part din yayi wani irin shiru karar Ac kawai kakeji bedroom dinshi taje ta gyara mashi fess hade da wanke toilet kwata kwata bataji motsin shi ba don haka tayi sauri tagama ta fito parlon Cikin sauri take komai don gyaran parlon ta cigaba dayi saida ta share ko ina tass tareda gogewa sannan ta hado ruwan mopping ta farayi goge parlon mai tsananin girma Mopping din ba kadan tayi ba saidai karar tafiyar da taji da kamshin da taji ya sanya tasan sunyi Baki kwata kwata bata juya ba don abinda takeyi shine ta cigaba dayi Prince maleek da fayroz sai Khasheem ne suke takunsu na sun isa duk cikinsu babu wanda ba wani bane don arziki ta ko ina ya bayyana ajikinsu sun hadu sosai don suma wasu irin manya ne gasu yan gayu cikin izzarsu suma da mulki suke tafiya har suka shigo da tsaddadun takalmansu cikinsu ba wanda bai taka mata mopping ba da tsaddadun takalmansu Juyowa tayi domin wucewa saidai abinda tagani ne ya sanyata tsayawa duk sun bata mata mopping din da tayi da takalmansu masu tsada kuma suna kokarin ida wucewa ta inda tagama mopping yanzu Zuwa tayi Daidai inda suke neman wucewa ta tarbe wurin tareda zuba masu idonta masu masifar kyau ba wanda acikinsu bai kalleta ba ba kamar prince maleek wanda izzarshi take yanayi data Khalifha Kallon kallo Dukansu suke ma juna Hurriya in a mocking way tayi raising brows dinta tace ina zaku? Kallonta sukeyi saidai cikinsu ba wanda ya santa a matsayin yar uwar Khalifha ko wata cikin yan matan gidan irinsu liya da neela don haka tabbas mai’aikicyar shi ce saidai kuma shigar da tayi ba irinta masu aiki bace Prince maleek langabar da kanshi yayi yana zuba mata idanunshi masu kashe yan mata, fayrouz shine yayi magana yace wacece ke? Shiru tayi batare da tace mashi kala ba Amman bata fasa kallonshi ba. Move from here inji Khasheem kallon kafafunsu tayi tace har sai kun cire wannan kazaman takalman naku Kallonta suka rinkayi irin did you know what you just said kazaman takalma fa takalmansu duk guda daya zai iya siyanta daga masu kai tayi saboda ba product din da bata Sani ba acikin takalmin kuma tasan duka kudinsu maleek sanya yake da bakin takalmin Nicholas Kirkwood babban designer kuma kayansu a extremely expensive and Are not common ko acikin designers product don idan baka kai shege ba ma duk girman ka duk kudin ka bazaka taba sanin companyn din ba amman isassu wadanda sun isa kuma masu manya manya kudi to tabbas zasu san mi ya sanya Daya acikinsu kuma ya sanya wani farin takalmi na Marcelo Burlon shima babban expensive designer ne worthing alot of millions Khasheem kuma ya sanya shima bakin takalma na Vera wanga Dukansu manya manya takalma ne daga designers company don ba irinsu fendi Versace ko Gucci bane wanda kowa ya sani Aa wannan sai ka kai da nisa sannan zaka iya sanin su Hurriya kallon maleek tayi tace Nicholas Kirkwood shoes fayrouz tace marcelo Burlon Khasheem kuma vera wang interesting tace tareda rike mopper tana kallonsu Dukansu kallonta suke in awe suna jinjina mata wani irin miskilin kallon maleek yake bin Hurriya dashi wanda shi kanshi baisan yana haka dinba fayrouz shima kallonta kawai yakeyi tareda washe baki ya matso kusa da ita hannunshi ya kai zai taba mata gashi aiko a take ta buga mashi mopper din dake hannunta a gwiwarshi rike wurin yayi yana ouch wash dariya Khasheem ya fashe da ita yana kallon Hurriya dake tsaye da mopper a hannunta da alamar idan ya kara zatayi abinda yafii haka wani silent murmushi maleek yayi tareda cewa ta basu wuri Hurriya kin matsawa tayi hannuta rike da mopper shiru sukayi suna kallonta ahankali cikin miskilanci da kuma aji tace appointment Dukansu kallonta sukeyi wai bataga shigarsu bane kodai bata ganewa ne? Gaskiya wannan yarinya ta gama rainasu fayrouz daya kasa rike Maganarshi ya juya kamar wani mace kalleni da kyau nayi kama da wanda saida appointment zai shigo nan Hurriya yanda ya juya ya sanya ta dage girarta tana mai kallonta mai dauke da raini kuma da kwarjini bude bakin da Khasheem yayi da niyyar magana ne bai kaiga yin maganar ba sai ga turaren Khalifha da ya cika ko ina da aura dinshi da ta canza Atmosphere din shiru duka wurin ya dauka Khalifha yana screat room dinshi tunda ta shigo part dinshi yake kallonta harta zuwansu fayrouz tunda yake bai taba ganin mutum mai confidence dinta ba kuma sosai yayi dariya ganin yadda ta buge kafar fayrouz yadda ta karanto takalman dake kafarsu ya bashi matukar mamaki who’s she? Wacece ita mi tazoyi Chamber dinshi yana yawan tambayar kanshi Akwai wani boyayyen abu tattare da ita she also look like someone from prestigious royal family Bai yarda da ita ba very soon yasan zai kamata red handed after all he’s Khalifha Qamar. Walking stick dinshi sai kyali take jikinshi wata grey rigar chloe ce sai dogon wando baki na Michael kors yayi kyau na fitar hankali don wani haske kawai fuskarshi take fiddawa ga kamshin shi da ya mamaye ko ina Fayrouz ne ya fara rungume Khalifha Khalifha shima rungumeshi yayi back sannan Khasheem da maleek sukayi joining hug din Hurriya tabe bako tayi tace Disgusting tabar wajen Khalifha yanajinta kuma yana kallon yadda ta mela baki irin tana kyankyamin rungumar da sukayi. Cike da kaunar juna suke kallon amininsu childhood friend nasu wato Khalifha Qamar ba karamin kewarsu sukayi ba don sun dade basu hadu dashi ba don baya barinsu suna zuwa fayrouz ne ya kasa rike maganar zuciyarshi yace Kayl who’s that rudr girl ahankali Khalifha yace my maid ba Khasheem ba hatta maleek saida réaction ya fito daga fuskarshi. Irin mai aikin ka Mad inji fayrouz yace but the girl is fucking beautiful and rude Maleek ne ya kalli Khalifha yace kayl I’m hungry [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 52 Hurriya duk zuwan bakin Khalifha ya isheta don fayrouz kamar bindinta haka yake indai har ta shigo part din to yanan makale da ita yana zuba mata surutu Hurriya kala batace mashi don aikinta kawai takeyi ba tareda tasan dashi ba a duk lokacin da yake. She’s not liking anyone of them don duk ta takura kamar yau basu nan don tunda ta shigo aiki bataji motsin kowanne acikinsu ba she wondered where are they don haka tayi aikinta cikin kwanciyar hankali tana gamawa ta nufi inda take wanki . Tana wankinta saiga wasba tazo tana haki kallonta Hurriya tayi tareda tambayarta lafiya wasba tace kizo ana nemanki Hurriya kallonta tayi tace wake nemana?wasba shiru tayi tana kallon Hurriya don batasanshi ba murmushi tayi sannan ta farayi mata kwatancen shi nan take Hurriya tagane chief of security ne dauraye hannunta tayi tamike sannan suka jera itada wasba suka tafi hanyar da yake suna zuwa wasba ta shiga daki Kallon Hurriya chief of security yayi tareda cewa kamar fa har yanzu yerima bai ci abinci ki ba and the deal is 3weeks and yau saura 1week idan bai cin abinci gaskiya I will not give the salary as you demanded ki sanya ya rinka cin abinci and bedtime story is a must. Hurriya kallonshi take ba tareda tace komai ba and she believes duk abinda ya fada na cewar bazai bata kudin ba to zai aikata Cewa tayi i will make him eat the food in good three days by then idan baici ba you should fire me kallonta cheif of security yakeyi irin kinsan mi kike fada kuwa Hurriya daga mashi kai tayi da wani irin confidence Murmushi yayi ganin yadda ta dage don shi yasan halin ogan nashi amman yarinyar akwai confidence Hurriya koda ta koma tunanin abinyi ta fara all of them are stressing her gasu ayyo da suka tura mata kudi batasan ya zatayi ba she doesn’t want to affect any innocent soul tasan hypocrisy na masarauta shiyasa har yanzu ta kasa yin abinda su ayyo suka sakata Convoy ne wanda suke zaune a baya cikin bakar mota Khalifha hannunshi rike da glass cup wanda yake dauke da non-alcoholic wine red a hankali yake sipping shida prince maleek sun kame wuri daya fayrouz ne ya kalli Khasheem yace i think I’m in love yanayi yana lumshe ido Khasheem yace with whom murmushi yayi yace with that mysterious girl I think i like her Khasheem yace wai wacece kake magana a hankali yace Hurriya prince maleek kam sauran kadan ya kware saboda yanda yaji maganar kamar saukar aradu Khasheem dariya yayi yace wannan yarinyar mai kama da kurame sannan Yayi wata dariya yace zanga yadda zata kula ka Fayrouz yace nine fa fayrouz ajuji yayi wani murmushi mai kyau Prince maleek tunda fayrouz ya furta maganar yanason Hurriya mood dinshi duka ya canza Khalifha kuma mutum bai isa yace ga mood dinshi ba har suka iso Bakar limousine dinsu ce aka bude masu suka fito su hudu ba karamin kyau sukayi ba Dukansu hudun babu na yardawa acikinsu kowa yana ji da kanshi kuma kowa ya hadu Suna dawowa Dukansu ba wanda bai gaji ba saboda wani aiki ne sukayi ma Khalifha yunwa ce ke nukurkusar kowa acikinsu don basu wani cin abinci kirki tunda sukazo palace din saboda rashin yardar Khalifha cookies kawai da fruits suke ci sai drinks Khalifha yama saba donshi kamar ba mutum ba don ko baici komai ba Lapia lau sukam they’re not liking rashin cin abincin nan. Tun daga bakin kofa suka farajin kamshin abincinta wanda ta kokarta sosai don different varieties of food ne tayi saboda Khalifha ko zayaci abincinta Fayrouz ne da Khasheem suka lumshe idonsu tareda saurin shigewa ciki sai Khalifha da prince maleek suka biyo daga baya Fayrouz sakin baki yayi tareda mutuwar tsaye yana kallon hurriya don zai iya cewa tunda yake yawo kasashe bai taba ganin mace mai kyaunta ba riga ce yar baka mai shara shara yar karama wadda bata ko rufe mata adon dake cikinta ba gyaran gashinta very matured yau saboda ba kitso bane kawai ta daureshi a bayanta ne sannan ta saki gashin Prince maleek kallonta yakeyi wanda shikanshi bai Sani ba don kwata kwata ya kasa dauke idonshi a kanta parlon shiru ya dauka Hurriya kam kallonsu tayi sau daya ta dauke kanta batasan wainar da ake toyawa ba jin shirun yayi yawa ya sanyata juyo kallon fayrouz tayi tareda dage gira daya tace lafiya kodai kana bina bashi ne? Murmushi yayi yace mata you look so breathtaking a hankali tace T for thanks don har ta juya sai kuma wani tunanin yazo mata wani irin dadi fayrouz yaji saboda kula shi da tayi Khasheem ne ya nufi dining table tareda budewa yace wow zamuci dadi fayrouz ne yace Hurry let me eat your food nasan it will taste delicious. Prince maleek shima a hankali yazo ya zauna Khalifha Qamar wanda yana shigowa kallo daya yayi mata tareda shigewa sama duk abinda ke faruwa yana kallo ta CCTV camera yana kallon yanda duka abokanshi ke bin Hurriya da kallo akai kaice ba kamar fayrouz da duk inda tayi idonshi na nan akanta Hurriya da kanta tazo tayi serving dinsu Because she knows it was her duty to do that accordingly ta zuba ma kowa abincin da tsari tayi serving dinsu Khasheem banda santi da lumshe ido ba abinda yakeyi Maleek abinci yanayi mashi dadi kuma yanajin dadin kallon yarinyar baisan miyasa ba fayrouz kam sai washe baki yake yanacin abinci Khasheem ne yace Amman wallahi Kyal ya gama damu yanzu akwai mai dafa irin wannan abincin a gidanan shine yake wahalar damu da cin cookies da fruit gaskiya it’s unfair duk tare suka rinka maganar Khalifha kallonsu kawai yake yana mamakin yadda suke cin abincin don kamar basu taba cin abinci ba. Hurriya saida ta dade zaune a kitchen tana tunanin ta inda zata fara don Khalifha kwata kwata baici abincin ba she desperately needs money don she have to work hard indai tanason ta hada kudin Kiran sallahr magrib da taji ya sanyata tashi ta nufi dakinsu saida ta kwanta ta huta sannan tayi alwala tayi sallah Bintu da wasba tare suka shigo Dukansu ba wanda baiyi murna da Ganin Hurriya ba don aiki na dan shige mata kwana biyu suna wuya bata zauna dasu ba.Ba kamar Bintu don inna hanne da wasba kullum suna ganinta Inna hanne ce tazo da tuwon masara mai dadin gaske don ko yadda yake turiri mutum ya isa ya gane ga man shanu data kwalala masu a saman tuwon kallon Hurriya tayi tace Hurriya kin shigo? daga mata kai Hurriya tayi Inna hanne tace bari na samo maki wani Abu da zaki dan ci don nasan baki san tuwo Hurriya cewa tayi na koshi a hankali cikin natsuwarta da miskilanci.wasba lumshe ido tayi tareda cewa kai wannan tuwon zaiyi dadi tareda kai hannunta Hurriya ce tace wasba don’t eat this food without washing your hands kada ki sake kici abinci nan ba tareda kin wanke hannun ki ba daga mata kai wasba tayi tareda fita domin wanko hannun bintu dariya tayi mata hade da gwalo turo baki tayi inna hanne dai murmushi tayi tace wasba sarkin rigima Bintu ta kalli Hurriya tace ya aiki a wurin makaho?kinajin dadi shiru tayi Bintu bata fuska tayi tace ki gaya mani don Allah Hurriya wani dan karamin murmushi tayi tace eh tareda daga mata kai har zata ce wani Abu sai tayi shiru ta kalli Hurriya tace bari na wanko hannuna. Saida suka wanko hannu tareda wasba suka dawo suka zauna inna hanne itama ta zauna inna hanne saida ta kalli kowa Acikinsu tace suyi bismillah atare sukayi sannan suka sanya hannu suka faraci a hankali .daga gani tuwon na kai masu karo Bintu ce ta bude baki zatayi magana Hurriya girgiza mata kai tayi tareda nuna mata da hannu tayi shiru.they all ate in silence saida suka gama ci bayan sun wanke hannu sun dawo Hurriya tace mata ba’a cin abinci ana magana ki bari daga mata kai Bintu tareda jin dadin correction din da Bintu tayi mata sannan tayu masu inna hanne Bankwana Hurriya wayarta ta dauka tareda sanya earpiece inna hanne kallonta tayi tace aikin zaki koma daga mata kai Hurriya kawai tayi inna hanne shiru tayi don batasan aikin dare sam bare aikin dare a masarautar Qamar yanada matukar hadarin gaske cikin sanyi murya tace ki kula kinji Allah ya tsare ya taimaka Daga mata kai kawai Hurriya tayi ta tafi. A parlo ta iske Khasheem da fayrouz suna kallon ball ai fayrouz yana jin motsinta ya tashi yazo wurinta biyota yayi har kitchen din da ta shiga sannan ta dora ruwan zafi ta zauna saman kujerun kitchen island shima jan kujerar yayi ya zauna yace miss world banza Hurriya tayi dashi ba tareda ta kalli inda yake ba . Oats dinta ta dama sannan ta zuba madara tareda zuba brown sugar ta dawo ta zauna a hankali take shan oats dinta shi kuma fayrouz ya kura mata ido yana kallonta tareda admiring dinta ko kyaftawa bayayi yanda take shan oats din kadai abun kallo ne don da wata irin natsuwa sosai take Shan oats din. Saida tagama shan oats din yace please I need a favor from you kallonshi tayi favor kuma daga mata kai kawai yayi haka yace mata please can we be friends Hurriya kallonshi kawai tayi ba tareda tace komai ba ta fita da dan sauri ya biyota yace mata bazan daina binki ba har sai kin amince man Hurriya kallon rashin sanin abinda yake kawai tayi ta hau sama. Tun daga parlon sama ta fara lumshe ido saboda wani kalar bacci da takeji a hankali ta bude dakinshi wanda yake ko ina duhu don wutar dakin kashe take Saidai sanyin dake ratsa sakin har ya fita hankali. Kunna wutar dakin tayi inda ta hango shi kwance idonshi sanye da glasses a rufe cikin natsuwa da kuma catwalk ta nufo inda yake a hankali ta dan leko fuskarshi tace sir nazo zan karanta maka bedtime story shiru yayi ba tareda yace komai ba Hurriya zuwa tayi ta jawo drawer bedside dinshi books ne masu dadi kuma favorite dinta ko acikin books din murmushi tayi tare da daukar littafin ta fara karantawa cikin muryarta mai dadi kuma da zallar British accent Khalifha kam tundaga saman kanshi har tafukan kafafumshi yakejin muryarta cikin wani irin yanayin natsuwa da dadi take karantawa. Shiru Khalifa yayi yana tunanin minene identity dinta ina ta iya turanci turancin ma na yan america Hurriya batayi aune ba tana karatu kawai sai ji tayi an rike mata hannu da wani irin tsorata da fargaba don batayi tunanin idonshi biyu ba kuma hankalinta gabaki daya yana akan littafin da take karantawa.kallon idonta masu kyau da matukar kaifi yayi wanda ta fito dasu waje haskensu na haska nashi idanun riko waist dinta yayi tare da hawa gadon don har ta kusa rungumeshi kallonta yake tundaga kananun gashinta da ya zubo gaba ya kwanta mata da baya a hankali cikin wata murya yace who send you?miye ya kawo ki. Masarautar Qamar 53 Hurriya ranta banda baci ba abinda yakeyi don wannan Khalifar mai ya dauke tane who give him the audacity to touch her duk lokacin da yaga dama abinda wani bai taba ba kallonshi takeyi ta cikin glashin shi Saidai bata iya ganin idanunshi shi kuma yana ganin komai She doesn’t want to cause any trouble saboda tanason ta amshi kudinsu tabar kasan cikin muryarta mai dadi tace ka sakeni please yana jinta sarai don wani kara lumshe ido yayi saida ya dauki mintuna sosai sannan yace sai kin fadamin wanda ya aiko ki Chamber dina Hurriya ganin bai gane yaren da takeyi mashi aiko ta manna mashi cizo mai zafin gaske a hannunshi da sauri Khalifa ya saketa yana mai kallonta Kallonshi tayi ta harareshi tareda cewa bastard can kasan muryarta lips dinta kawai suka motsa ba tareda saninta ba Khalifa yana kallonta ta cikin madubin idonshi. Juyawa tayi tareda sakin littafin zata nufi dakinsu bata kai bakin kofa ba Khalifa yace You’re not done with your work Juyowa tayi tareda hararshi tace sakarai Khalifa duka yana kallonta shi abun har mamaki yake bashi yadda batajin tsoronshi take zaginshi zaiyi lokacinta. Devil smirk yayi ya kara lumshe idonshi Hurriya haka ta dawo ta zauna ta cigaba da karanta mashi littafin tanajin numfashin shi ya fara canzawa ta tashi Saidai jin muryarshi tayi yana cewa where are you going ? Hurriya zama tayi ta cigaba da karanta littafin cikin gajiya don cikin ranta tana ayyana randa zai kaita karshe tasan ba hakuri zatayi ba idan ya cigaba da haka ta tsani bossy attitude dinan nashi Amman zatayi maganinshi very soon Bacci dukansu ya kwashesu duk basu sani ba Hurriya zaune a saman kujera kusa da gado shikuma kwance akan gado Kiran sallahr asubar farko ya tada Khalifa kallon Hurriya yayi data makure saman kujera wuri daya yayi gashin kanta ya sauka skin dinta banda glowing ba abinda yake kamar ba bacci take ba. Daga ganin yadda ta makure yasan sanyi ke gasata a hankali yace mata you deserve it my arrogant maid ya shiga katon toilet dinshi yayi wanka hade da alwala ya fito saida ya shirya ma masallaci yayi nafilfilolin shi sannan ya tafi masallaci. Baiyi tsammanin abinda ya gani ba don koda ya dawo saman gadonshi ya ganta ta kudundune tana bacci ga dukkan alama batayi sallah ba har yayi yunkurin tadata kuma ya share ya bude secret room dinshi ya shiga . Kwanciya yayi wani bacci mai dadi ya daukeshi. Hurriya bata tashi ba har kusan sha daya don mafarkai ta rinkayi masu dadi baccin yayi mata dadi sosai.hamma tayi sannan ta bude idonta masu kyau ta kalli dakin Hurriya tace aranta yaushe rabon data samu peaceful sleep haka gadonshi very cozy Saidai kamshin Khalifa ne ke dawainiya da ko ina na jikinta kamar tare suka kwanta ko tayi wanka da turarenshi don wani irin kamshin shi takeyi ko ina tsoki tayi ta gyara dakin tsaff sannan ta shiga toilet dinshi Saida ta wanke toilet din sannan tayi nazarin yin wanka kilan ta rage kamshin turarenshi da takeyi Saida ta zuba ruwa masu dumi a cikin bahon wanka sannan ta cire kayanta ta shiga tana shiga ta lumshe idonta don wani irin missing din toilet dinta ya taso mata ta dade cikin ruwan zafin bata fara wanka ba sannan ta kara fitowa ta hada ruwan wanka mai foam da kamshi ta shiga wani irin lumshe ido tayi jin kamshin shower gel din Khalifha it smells nice and dangerous don bata taba jin kamshin shower gel haka ba don baya sanyi kamshi kamar irin wanda take using Saida yana da dadi Saidai kamshin shi yanada karfi Wani silbi jikinta yake fiddawa kamar jikin tarwada kamar kada ta gama wankan haka Hurriya takeji don ta dade bata samu irin haka ba kawai ta sanya a ranta she will enjoyed more of this bath in the future don bazata iya kilan yadda tayi wanka a toilet dinsu ba this toilet will be hers daga yau and she will keep sleeping in his cozy bed tanason ta kara enjoying life dinta kadan kafin tabar nigéria Because she doesn’t know what is awaiting for her there. Dogon gashinta mai kyau da tsawo ta wanke shi tass irin wanki da rabonta dashi shekara da shekaru saida ta tabbatar ya fita sannan ta dauki hand dryer dake a toilet din ta busar da kanta tsaff ta rinka shafa designers man gashin shi mai tsada sannan ta fito taji dadi sosai kayanta sun danyi datti bazata iya barinsu ajikinta ba. Bude wadrop dinshi tayi sannan ta kalli kayan dake shake acikinta .latest branded designers ne komai a wurin dark colors sunfi yawa a kayanshi ta dade tana kallo kafin ta bude wata wardrobe din wanda girmanta kusan daki guda kayane sabbi dal wanda ba’a taba sasu ba Hurriya kallon komai take sannan tace extravagance abun kuma sai yadan bata dariya she just called someone extravaganza while lokacin da tana Hurain haka take akwai kayan da idan ta siyesu har ta bayar dasu bata taba sawa ba she loves shopping kuma everyyear ana canza mata komai na dakinta tun daga furnitures har zuwa kan clothing zata iya cewa all her life bata taba saka kayan da ba designer ba kuma babban designers brands wanda clothe din are worthing thousands and millions of dollars. Kuma zata iya tayi barnar kudi ta siye kaya da mahaukatan kudi Amman bazata taba sawa ba suna ajiye kuma kullum hakan bazai hanata fasa fita ta siye wasu kayan ba. Extravagance life kenan wasu bakaken hoodie ne tagani sabbi bakake ahankali tazaro su ta bude hermès tagani cikin natsuwarta ta kalli kayan tana fatar Allah ya sanya zasuyi mata don taganshi giant ne. Cikin yanayin natsuwarta ta fara sanya rigar sadai rigar har kusan gwiwowinta saida suka rufe mata wandon ta sanya shikuma inda Allah ya taimaketa baiyi mata yawa ba sama da kasan wandon rubber ne sai yadan kama kafarta she looks so cute and breathtaking ba karamin kyau na daukar hankali tayi ba don kayan sunyi mata kyau sosai Kayanta ta fito dasu sannan ta sauko kasa ta baya inda take ganin washing machine ta zuba kayanta da morning fresh din da take wanke wanke Washing machine nagama wanke mata kayan ta shanyasu tareda shigowa kitchen tunanin abinda zatayi ta fara mai sauki Dankali ta debo ta fere sannan ta ciro fresh liver dinta saida ta daura manta sannan ta wanke liver lokacin data gama wankewa har man yayi zafi ta zuba dankalinta Wani kyawawan hadi tayima sauce din kamshi sai tashi yake. Fayrouz ne ya shigo kitchen din cikin gayunshi sai kamshi yakeyi fuskarshi sai wani salkin kyau takeyi kallo daya zakayi mashi kasan cewar shidin dan gayu ne kuma dan kwalisa mai kudi Kallon gashin Hurriya yake wanda da ace zata bashi dama da ya taba yaji ko nata ne saida bashi da wannan damar har sai ya mallaketa he will look forward into mallakar wannan yarinyar komin wuya insha Allah . Tunda ya shigo tasan da shigowar shi duk da tabama kofa baya saboda Allah ya bata ji Sosai cikin muryarshi mai dadi yace mata hurry babe Hurriya banza tayi dashi ta cigaba da aiki fayrouz kam zama yayi saman kujera Saidai Hurriya ta rinka jin sheshekar kuka saida ta gama kwashe dankalinta tazo ta kura mashi ido irin namiji kana kuka ? Daga mata kai yayi yace i don’t need anything from you fa just a simple friend minene abun kin yadda I swear duk randa nayi misbehaving kar ki kara kulani please Hurain please Hurain gaban Hurriya banda faduwa ba abinda yakeyi don murya Al-Amr kawai takeji please Hurain ahankali tace mashi yayi shiru da hannunta tana kallonshi so cute and full of spirit why don’t her befriend him atleast ko ta koma there will be so much memories of the palace kuma he seems carefree and simple ga yanada barkwanci da shiga rai why not tayi keeping dinshi as only male friend din da tayi tunda tazo Nigeria duk a ranta take tunanin Muryarshi mai dadin sauraro yace mata please Hurain kallonshi tayi cikin natsuwa tace stop calling me Hurain sunana Hurriya dan durkusa kai yayi yace yess your royal highness daga mashi kai kawai tayi can we be friends please ? A hankali ta daga mashi kai wani irin ihu ya buga don yasan first step in a relationship shine friendship daganan sai a zama best friends daga best friends kuma sai azama lovers yasan wannan tactics din and he’s very sure it will work. Zuwa yayi ya rinka tayata aiki don pancake din kusan tare suka kwaba yana mata fira Hurriya bazatayi karya ba Amman gaskiya she’s enjoying his company don duk da bata cewa komai a firan to ta maida hankalinta da komai a kanshi Maleek ne ya shigo kitchen saboda yanasan yasha magani da ruwa marar sanyi tunda ya bude kofa yagansu duk da fayrouz shike maganar yana nuna mata yanda abin ya faru da hannu Ita kuma tana kallonshi da duk wani attention dinta wani irin bang bang yaji zuciyarshi nayi a hankali ya dafe zuciyarshi yana kara kallonsu Khasheem ne yazo tareda wani dariya yace miye nike gani haka Maleek fita yayi Hurriya taci gaba da aikinta kusan fayrouz ne ya taimaka mata wurin shirya table din sukayi setting komai tare Khasheem ya kalli maleek yace ka taho muci abinci a wani miskilance ya taso ya zauna saman table din Hurriya ita tayi serving dinsu ta sanya ma kowa Daidai sannan ta mika mashi har zata juya fayrouz yace Hurriya please i need a favor juyowa tayi tareda alamar miye please join us Hurriya bata wani bata lokaci ba ta zauna cikinsu don yunwa takeji daman. Khalifha ba abinda bai gani ba ta dakinshi yana mamakin audacity da zeal dinta har ta sanya mashi kaya . kamshin turarenshi mai matukar dadi ya daki kowa cikin kasaita da natsuwa sai kuma walking stick dinshi dake rike à hannunshi ahankali yazo ya zauna kallon su duka yakeyi ba kamar fayrouz da hankalinshi gabaki daya yana akan Hurriya Maleek ne cikin miskikanci yace Kayl join us for breakfast your maid is surely a genius Dukansu juyowa sukayi a mamakance did they heard right anya abinda sukaji Daidai ne a compliment from prince maleek fa dashi da Khalifha kusan halinsu daya na miskilanci don mutum zai iya kwana baiji a daga bakinsu ba to gwara Khalifa yanada zafi da fada don anajin fadanshi Time to time shi kuma maleek ba ruwanshi da shiga hidimar kowa Khasheem Dariya yayi maleek did you just compliment her daga masu kai kawai yayi Hurriya kam batace komai ba don Komi za’ayi a wurin ba zatace uffan ba indai ba gamacin abincinta tayi ba. Khasheem ya kalli Khalifa yace Kayl join us I’m sure you will like the food haka shima fayrouz yace cmon gee join the food da dadi saida suka rinka magiya sosai sannan ya zauna yayi bismillah ya faraci. Kallonshi suka rinkayi da mamaki don basuyi tunani zaici so easily haka ba. Hurriya wani irin dadi taji they really did help her in this battle don batasan ta yanda zata fara a cewa yaci abincinta ba, yau za’a sanya mata 2.5m ta riga tayi deciding tabar kasar with 3.5m tasan cewar kudin zasu kaita saudiyya. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: M.Qamar Short page Tunda Khalifa ya fara cin abinci wurin ya dauki shiru Sosai Ba wanda ya kara cewa uffan har saida suka gama Hurriya ce ta fara tashi kallonta Khalifa yakeyi cikin kayanshi data sanya a ranshi yace gaskiya batada kunya ba izini yar aiki ta bude maka wardrobe ta sanya kayanka kuma kamar batayi laifin komai ba Bayan sun gama cin abinci Khalifa da maleek suka fita.hurriya saida ta tabbatar kowa acikinsu ya gama cin abinci tazo ta kwashe duka kayan datti fayrouz ya biyota ya rinka tayata komai yanayi yana mata labarai masu tsananin ban Dariyar duk yanda Hurriya take daurewa saida fayrouz ya kawo zance data kasa rikewa saida tayi dariya kadan a lokacin Fayrouz kam sumar tsaye yayi yana kallonta don wani irin kyau kawai yake gani dimples dinta hakoranta masu kyau wanda bai taba ganin irinsu ba sai adon dake tsakankanin hakoranta yaji dadi da yaga dariyar Hurriya don yasan yau abinda zai rinkayi mashi yawo kenan har yayi Bacci.saidai yaji dadi sosai da Hurriya ta zamana cikin mata mararsa dariya da kilan sai ya kusa mutuwa inda tayi Dariyarta yaga ana kallonta. Hurriya ta dade a part dinshi tareda fayrouz sannan ta koma dakinsu tana zuwa tayi sallolinta da batayi ba. Inna hanne ta iske da wasba aiko da murna wasba ta tarbeta tace tayi missing dinta jiya da daddare daga mata kai kawai Hurriya tayi inna hanne kallonta take da kayan Khalifa har zata tambayeta ta fasa saboda tasan ko wacece Hurriya zata iya bada shedarta A wurin su inna hanne da wasba ta wuni bintu ma tazo ta zauna Hurriya idan ta kallesu tanajin wani irin nauyi azuciyarta duk da bata cika yadda wani abu yafi karfinta har haka ba don tasan bazata dade ba zata tafi. Amman hausawa sunyi magana da suke cewa sabo turken wawa tasan cewar zataji ba dadi idan har ta tafi Amman ya zatayi haka rayuwarta tazo mata Kwanciya Tayi bata wani dade da kwanciya ba bacci ya dauketa mai dadin gaske don ba itace ta tashi ba sai bayan magriba alamar period taji wanda tana fin wata da wattani batayi shi ba dan bata rai tayi sannan ta fita zuwa kitchen wurin inna hanne taje ta amshi ruwan zafi sannan ta nufi toilet ta gasa jikinta da ruwan zafi mai kyau Saida ta sanya pad dinta sannan ta shirya cikin pink rigarta mai kyau iya gwiwa ta tsaya mata turare ta fesa sosai ta kara shafa ma gashinta mai sannan tayi ma wasba Bankwana wasba kallonta ta rinkayi don kamar ta bita haka takeji Allah ya dora mata soyayyar Hurriya Tanaji tana gani Hurriya tabar dakinsu ta nufi dakin Khalifa Dukansu suna parlon ta shigo batare da sallama ba Saidai ganin mutum kawai sukayi wani irin kamshin dadi takeyi mai sanyi wanda ba wanda bai shiga hancinshi ba acikin mazan.fayrouz wani irin mugun kishi yakeji yanda take tafiyar catwalk wanda ta dauke ma kowa hankali a wurin banda mutum daya Harta Khasheem saida ya kalleta ya kasa janye idonshi daga kanta Kallonsu tayi sannan tace kallon na minene maleek basarwa yayi Khasheem ne yace girl can’t lie to you but you’re hot fayrouz ne yadan bugi kanshi yace please stop yana bata fuska Khalifa dai yanajin su Amman baice kala ba don tashi yayi ya haye sama ya barsu Khasheem ne ya kalli Hurriya yace I’m Hungry please give us food dan kallonshi tayi tareda daga mashi kai sannan ta shiga kitchen fayrouz ne ya biyota ya rinka yi mata fira. Koda suka gama suka jera table din Khasheem ya kira Khalifa ta landline yace yazo suyi dinner. Bai wani dauki lokaci ba yazo da fararen kaya na Loro Piana wanda suka fito mashi da haiba da kyau banda kamshi ba abinda yakeyi don wurin duk ya dauki kamshin shi Hurriya ita tayi serving kowa acikinsu sannan tayi serving kanta kamar ba yar aiki ba fayrouz kam dadi kasheshi ganin Hurriya ta zauna zataci abinci dasu they ate in silence don kowa yanaji da table manner dinshi Wani karamin parlo suka shiga Dukansu su ukkun Hurriya kuma ta tattara duk abinda sukaci ta wanke a kitchen saida ta gyara ko ina da komai sannan ta dauki ledarta data sanyo items dinta da zata bukata ta haye sama Dakin Khalifa kamar dakinta don tana shigowa ta shiga toilet tayi wanka mai dadi tanata wani irin kamshi kayanta ta sanya a washing machine din dake a toilet din ta wanke su tass sannan ta fito daure da bathrobe grey mai kyau Saida ta shafa mayukanshi tanayi tana bata fuska don everthing there ,is for men nothing feminine raising browse dinta tayi sannan ta bude wardrobe dinshi ta zaro sabuwar jallabiya milk ta sanya wadda ta rinka yimata yawo ajiki turarenshi ta fesa sannan tazo saman kujerarshi ta zauna shiru shiru bai dawo ba ta dade tana zaune don har tafi awa daya ga wani bacci datake bala’en ji ga sanyi da yake shiga har cikin kashinta Dabara ce tazo mata gwara ta kunna tv tayi kallo don tunda tayi wanka nan takejin wani irin bacci. Kunna smart tv mai matukar kyau da tsada tayi katuwa ganin Netflix account ya sanyata shiga har zatayi logging asalin account dinta na hurain ta tuna kawai sai ta sanya YouTube wakar stability ta ayra star ta sanya kawai Hurriya tafara enjoying wakar Amman tana cikin jin wakar batasani ba baccin gajiya ya dauketa. Agajiye yake don sai karfe 1:00 suka gama rapping off na aikin da sukeyi ba abinda yake bukata irin ya kwanta ya Sauke gajiyarshi . Yana shigowa toilet dinshi ya shiga tareda wanka bai tsaya wani kyale kyale ba kawai kayan bacci ya sanya yazo ya kwanta Saidai yana kwanciya yaji mutum ajikinshi tareda saukar numfashi da yake Khalifa ne ba tareda shakka bare tsoro ba ya bude idonshi tareda sauke matasu ahankali yake binta da kallo sannan yayi tsaki yace stubborn maid ya tashi ya bude screte room dinshi ya kwanta. Bai wani bacci Sosai ba don karfe 4:00 ya tashi ya gabatar da nafila har asuba sannan yayi wanka ya fita sallahr asuba har ya fito sallahr asuba Hurriya na dukunkune cikin bargo tana baccinta mai dadin gaske. Karfe 7:00 har yagama shiryawa haka ya fito falo inda duka abokananshi sun shirya kowa sai kamshi yakeyi ba karamin kyau sukayi ba don komai da suka sanya is screaming money don kallo daya zakayi masu ba lallai ka iya dauke idonka ba Saidai kwarjinin su bazai bari a tsura masu ido ba. Khalifha hannunshi rike da walking stick as usual mai tsananin kyau da tsada haka suka jero su hudu aka bude masu farar limousine convoy dinsu ya dauka sai airpot. Hurriya kam koda ta tashi mika tayi tana kallon dakin Khalifa mai tsari. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: M.Qamar 54 Kallon dakin Khalifa mai tsari da kyau tayi sannan ta sauko ahankali ta shiga toilet saida tayi activities dinta sannan ta tara ruwa a bahon wankanshi cike mai kamshi tayi wankanta mai dadi.sannan ta ziro dogayen kafafunta da banda silbi da salki ba abinda sukeyi cikin bathrobe dinshi da suke hang ta dauki sabuwa ta sanya sannan ta fito saida ta bude wardrobe dinshi ta samu kaya masu rashin nauyi kuma da alama zasuyi mata ta sanya Gyara dakin tayi tass tareda wanke toilet ta sauko kasa sannan ta shiga katon kitchen dinshi tayi yamrita da coconut milk masu dadi har tagama komai tayi arranging ba wanda ya fito shrugging kafadarta tayi irin I don’t care ta zauna ta zuba komai kadan kadan kuma dai dai cikinta a hankali ta rinka cin komai har tagama tana gama cin abinci ta shiga kitchen ta wanke kayan data bata sannan ta gyara kitchen din. Wani takarda ta gani a saman kitchen island ahankali takai hannunta ta dauka note din fayrouz ne yace mata tayi hakuri baiyi mata Bankwana ba they’re gone for a business a in Mexico she should take care of herself for him sannan yayi mata kalamai masu nuni da zaiyi missing dinta Hurriya kam cikin dustbin ta sanya takardar. Saida tayi bacci wanda ya isheta sosai sannan ta fita jikinta sanye da kayan Khalifa wanda duk inda ta gifta kallonta akeyi. Daidai zata sha kwana taga shaho da kaura suna kallonta kallonsu tayi sannan tayi tafiyarta. A bakin kofa tagasu Hansa’u da su barira da wasila da suwaiba Dukansu dai. Hurriya kam kallo daya tayi masu ta shige daki while su kuma sun kura mata ido tunda ta taho har ta bace masu dagani. Ahankali ta zauna sannan ta kalli wasba da take kwance tana bacci Hurriya kallon kamanninta takeyi don ko zata tuna dawa take mata kama Saidai hakan ya gagara, gashi gareta wasba sosai kuma baki mai kyau da cika irin na Hurriya Hurriya batasan ya akayi ba kuma batasan garin ya hakan ta faru ba Amman tanajin tsananin kaunar mutum uku a masarautar Qamar ko kuma mutum biyu saboda ai Bintu tun akauyensu take jin kaunarta har cikin ranta. Bata shirya ma hakan ba saboda tasan kalubale da sarkakiyar datake cikin rayuwarta kuma tasan cewar itadin ba mazauniya bace ako wani lokaci zata iya canza wuri Saidai ya zatayi itama she got heart like every human being she have feelings and emotions Saidai barrier dasuke dashi ta riga ta dakatar dasu yanda bazasu taba kawo mata cikas ba a rayuwa. Bintu ce ta shigo ta zauna kusa da Hurriya tana kallonta cike da so da kauna don babu abinda Hurriya batayi mata ba.Tayaya zata fara tunanin cin amanar Hurriya bayan tasan yadda Hurriya take kaunarta duk da bata nunawa idan har taci amanar Hurriya tabbas amanar Allah zata cita ina bazai yiwu ba . Hurriya kallon Bintu take tanaso ta karanci damuwarta don banda ramewa ba abinda takeyi kuma damuwa tsoro da alamar firgice duka ya nuna a fuskarta. Bintu kam duk ta tsargu sosai da irin kallon da Hurriya takeyi mata ba abinda take tsoro irin Hurriya ta tambayeta miye matsalarta don Hurriya nada matukar kwarjin idan kana kallon idonta bakasan lokacin da zaka fada mata gaskiyar lamarin ba. Bintu da sauri tace Hurriya bari naje na amshi aikina na kitchen ban karasa ba nazo nan. Daga mata kai kawai Hurriya tayi don ta lura da ita so take ta tsere mata.shiru Hurriya tayi trying to figure out what was bothering her friend Saidai to no avail ta rasa minene Amman zata gano da kanta. Bintu na fitowa a firgice kuma a tsoroce Saidai ganin da tayi masu kaura da shaho yafi firgita ta don batayi tsammanin ganinsu ba anan.kallonta Dukansu suka rinkayi irin muna jiran bayaninki ganin Bintu tayi shiru kamar bazata basu amsa ba shaho da baida hakuri yace ke malama kin zuba mata ko baki zuba mata ba.shiru bintu tayi cikin wani irin zafin nama ya wanka mata mari yace magana fa nike maki Bintu da wani irin rude ta dafe kai tace mashi zan zuba mata à abincin da dare yanzu tana kallona ne shiyasa ban sanya ba kaura ne ya kalleshi alamar ya kyaleta Bintu kam ajiyar zuciya kawai ta saki sannan ta dukar da kanta suna barin wurin ta samu wuri ta zauna Su barira ne da Hansa’u suka zo sukace shawara ta rage taki yarinya ki zuba ko karki zuba munafuka Barinta sukayi da sakin baki. Galadima kanshi akasa ya mika mashi farin kyale da zanen wani abu ajikinshi mai martaba Faizan ya kalleshi alamar yanason yaji karin bayani Allah ya taimake ka yace tana acikin masarautar nan Saidai har yanzu ya kasa ganeta Saidai wannan zanen tabbas ajikinta akwai wannan zanen don ba karamin aiki yayi ba kafin ya samo wannan zanen saboda akwai kariya tattare da ita sarki Faizan kallonshi yayi tareda mika hannunshi ya amshi handkerchief yana kallo wani murmushi yayi na gefen baki tatoo ne na Heral palace dole ake cewa wanda ya sameta zaiyi sarauta kowace iri. Galadima yace yawwa maganar da kayi man nayi ma jakaddiya magana tace ayi sauri ayi kafin Khalifa ya dawo Shiru sarki yayi yana nazarin abinda Galadima yace don tabbas a irin wannan lokacin ya kamata ayi abun nan don yadda Khalifa yabar masarautar ,don yanzu yana cikin shakka saboda yadda Khalifa yazo ba tareda ya sanar da kowa ba yasan zai dawo ba tare da ya sanar da kowa ba kuma koda yake sarki yasan Akwai abubuwa da dama da bazai iyayi ba agaban idon Khalifa ba saboda yasan waye Khalifa and what he’s capable of doing. Sarki yace ku samo matan kamar yadda akeyi ita kuma yarinyar ya za’ayi mu ganeta inji Sarki Faizan Galadima yace Saidai a sanya jakadiyya ta duba manah sai asan mi za’ace masu a masarautar. sarki na’am yayi da hakan sannan Galadima yayi Bankwana ya fita. Hurriya wayarta ta dauko tana budewa taga alert din 2.5m as promise don tun ranar da Khalifha ya faracin abinci chief of security ya cika alkawarinshi ya tura kudin ajiyar zuciya ta sauke don bazata wani bata lokaci a masarautar nan ba saboda kwata kwata zuciyarta na bata akwai matsala Kallon kudin dake cikin account dinta tayi 3.5m don su ayyo sun sanya mata kudin Amman batayi aikin ba ita bama wannan ba exist permit din da zata fita masarautar shima kanshi wani Abu ne batasan inda zata samo ba. Da ace chief of security yana anan da tayi mashi magana ya samo mata Saidai sam bata ganshi ba kwana biyu. Inna hanne tare suka shigo da Bintu bayan isha’i lokacin Hurriya har tayi wanka ta kwanta don yau wani irin bacci taji tanaji sosai inna hanne tace Hurriya ma har tayi bacci ashe, ga abincin da na kawo mata kuma, bintu ce tace ki ajiye abincin nan idan zan tafi sai intada taci. Inna hanne batayi tunanin komaiba ta ajiye abincin ta juya ita kanta wasba tana gama isha’i ta kwanta alamar ta gaji don wasba akwai hidima da yake batada aiki kwata kwata daga nan sai tayi nan kullum aikinta kenan ta tsokani fada ba wanda yake biye mata don kusan duk wanda ya kwana ya hantse yasan wurin wadda take zaune a wurinta don Hurriya ta zame mata uwa da uba ba kalar gatan da bata nuna mata duk abinda takeso najin dadi indai tanaso Hurriya bata taba gajiyawa wurin sai mata harta kudi zata zo tace ma Hurriya tana bukata haka Hurriya zata zaro ta bata Saidai wasba ta rinka dariya da murna taje ta kashe kudin Duk da Hurriya bata wani nuna alamar soyayya ko tayi magana dasu Amman kallo daya idan kayima inna hanne Bintu da wasba zakasan they’re very dear to her don yadda take kashe masu kudi take kyautata masu kamar batasan ciwon kudinta ba. Don ba’afi kwana hudu ba saida ta sanya aka dinka ma bintu da inna hanne sabbin hijabai masu kyau haule reza ta bama kudin aka dinko masu na Daidai karfinta harda sabbin takalma don taga Bintu batada wasu takalman kirki sai ta sanya aka siyo masu itada inna hanne gabaki dayansu koda aka kawo haule reza ta sanya ta kai masu aiko sukayi ta murna suna sanya mata albarka hade da addu’oi kala kala don sun san ba aikin kowa bane sai na Hurriya duk da tana nuna bata ita bace ba Amman ankare suke da ita acikinsu. Bintu kallon Hurriya ta rinkayi da take bacci peacefully kamar batada wata damuwa a duniya murmushi bintu tayi wanda yafi kuka ciwo tace ko bacci kike kedin mai kyau ce kuma mai kyawawan halaye duk da cewar kin ki bari muga kyakkawan halinki kin boyesu kota ina kamar yadda kika boye kanki ta ko ina ta yadda ba wanda zai iya fahimtar ki ko ya gane kedin wacece Amman Hurriya ke ta daban ce a rayuwarmu kin taimake mu alokacin da muke bukatar hakan kin kwatar mana yanci a lokacin da rayuwa take barazana a garemu anya zan iya aiwatar da abinda su shaho suka umarce ni ?anya ba kaina na zalunta ba ?don laifin dazan aikata bazan iya yafe ma kaina shi ba. Kuka ne yaci karfin bintu tana kallon Hurriya data dan sha lips dinta masu kyau da daukar ido long eye lashes dinta da suke kwance kamar ta sanya mascara double eyelid dinta wanda ya taimaka sosai wurin shaping idanunta sai dogon hancinta mai kyau wanda ya tafi kamar an zanashi she’s beautiful everything about her is beautiful don mutum ko shine karshen hasadda to sai yayi hakuri ya kyale Hurriya don duk bala’en hassadar mutum da kishi sai ya barta Bintu duk cikin ranta take karanta hakan a hankali ta jawo kular da baba hanne ta kawo mata sannan ta barbada maganin dasu shaho da kaura suka bata,saida ta tabbatar ba’a gane mi ta sanya don duk ta dan cakula shi don tasan yadda Hurriya take da kaifin basira da gane abu Hurriya is very smart daga kallo daya takan karanci abinda mutum yake tafe dashi tasha ganin yadda take dealing mutane sosai so she have to be very cautious A hankali ta fara ambatar sunanta shiru shiru bata amsa ba Bintu kara daga muryarta tayi yadda zatayi ringing cikin kwakwalwarta aïko hakan ta faru don cikin alamar bacci tace Bintu ya akayi ? Hurriya ki tashi kici abinci tun dazu inna hanne ta kawo kina bacci nace bari na tadaki tunda ta fara maganar Hurriya take binta da wani irin kallo Bintu tsarguwa Tayi tace kodai na kawo maki ruwa ne ki wanke hannunki Hurriya daga mata kai tayi aiko Bintu wadda takejin kamar tana saman kaya saboda irin kallon da Hurriya ta rinka jefo mata mai wuyar fassarawa bata wani dauki lokaci ba sai gata da ruwa da uban yawa a kwano tace gashi Tashi Hurriya tayi zaune har lokacin idonta bai bar kan Bintu ba saida ta wanke hannunta sannan ta janye idonta ta jawo kular Bintu banda faduwa ba abinda gabanta keyi Bintu Hurriya dagowa tayi ta kalli Bintu da tayi zugum don kamar za’ace mata arr ta arce sannan takai 1spoon. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 55 Ahankali takai 1spoon Daidai saitin bakin Bintu tana kallonta alamar ta bude bakinta taci abincin a zabure Bintu ta girgiza kanta tareda ja baya tace na koshi Hurriya na koshi fa. Hurriya shiru tayi sannan tace inci?bintu wasu irin kwalla suka rinka zubo mata masu zafi tana kallon Hurriya tace kada ki ci abincin Hurriya kallon bintu takeyi wanda duk wanda yaga kallon zai tabbatar da cewar she’s broken sannan ta girgiza kai .bintu kallon irin disappointing look din da take bata wanda bata taba ganin irinshi a wurinta ba ya sanya da sauri ta durkusa mata hawayenta nakara yawaita kamar an kunna famfo tace na tuba ki yafe mani Hurriya ba yin kaina bane bansan ya zanyi da raina ba kiyi hakuri don Allah tanayin maganar da wani irin tsoro da kuma tunanin irin hukuncin da Hurriyar zata iyayi mata kuka Bintu takeyi mai taba zuciya tareda narkar da rai tana rokon Hurriya gafara Amman shiru batace komai ba kallonta kawai takeyi Kiyi hakuri don Allah Hurriya kallonta Hurriya takeyi don ba abinda takeso taji ba so take taji miye dalilinta na cutar da ita saboda tasan Bintu ,wani Abu bazai taba sanyawa tayi tunanin cutar da ita ba indai ba babban Abu bane. Bintu kamar tasan bayanin da take bukata kenan don haka tace Hurriya lokacin da suka kirani wai zasu biyani har kaura yace yana sona zai aureni haka nace masu babu abinda zasuyi man wanda zaisa na yaudareki ko naci amanar ki sun dade suna bijiro man ta haka Amman naki basu hadin kai sai wani dare da suka tareni a lungu da wuka a hannunsu sukace indan har ban zuba maki maganin ba to idan suka tashi kashe ki zasuyi tareda wasba duka sai sun kasheku sai idan har na zuba maki maganin shine soyayyar da zan iya nuna maki don shine bazasu taba kasheku ba Kaura ne yace bazai taba bari wani abu ya sameki ba wannan alkawari ne yayi man ba abinda zasuyi maki kawai suna so ne su duba wani abu ne idan kinyi bacci Amman duk da alkawarin da sukayi man na kasa aikatawa share hawayenta tayi zuciyarta na karewa tareda shasheka a muryarta tace ba irin tsoratarwar da ban shiga ba bani iya cin abinci bani iya bacci duk saboda abinda suke fadamani na tsorotarwa Sai jiya da suka mareni dare nayi sukazo sukayi man gargadi da cewar idan har ban zuba makiba bazanji da dadi ba. Hurriya banda niyyar cutar dake Saidai niyyar kareki don Allah kiyi hakuri. Hurriya kallon Hawayen dake zuba a idonta take har muryarta ta fara sarkewa Hurriya alama tayi mata da tayi shiru ya isa yanzu ba lokacin kuka bane kinji na hakura inji Hurriya tana sakar mata dan karamin murmushi Bintu kasa yadda tayi yadda tasan halin Hurriya ya za’ayi tayi hakuri har da sauri haka Hurriya daga mata kai tayi alamar ta hakura ai da sauri Bintu tazo ta rungumeta.hurriya bata rai tayi tareda dagata sannan tureta Hurriya ta kura mata idanunta masu matukar haske da kyau tace mata Amman miyasa baki fadamin ba? bintu saddar da kanta kasa tayi don ganin wani kwarjin da Hurriyar ta karayi mata yau. Bintu tace ina tsoron yadda zan fada maki ne .hurriya wani genuine murmushi tayi mata sannan ta sassauta kallonta zuwa mai sanyi da sauki wanda tana dadewa batayi irinshi ba tace fatma ahankali Bintu ta dago tana kallon idonta wanda har wani maiko suke tsabar kyau da sanyisu abinda bata taba gani ba bintu tunda take da Hurriya shine irin wannan kallon mai kyau da sanyi. Murmushi tayi ganin mamaki kwance a fuskar bintu sai kuma ta daina murmishin tace kada ki kara haka kinji idan wani Abu ya sameni You’re not to be forgiven for the rest of your life koda na yafe maki Hamood bazai taba yafewa ba kinji .Duk abinda zai faru tell me ki fadamin we will face it together and fight it together abinda kike kokarin yi is betrayal koda kinyi shi da ace kinyi shi da niyyar protection don cutar dani sukeso suyi , don’t ever try something stupid kinaji. Bintu ta daga mata kai don wasu maganganun batasan inda ta dosa ba Amman tabbas abinda tayi kokarin aikatawa cin amana ne wanda ba wanda zai taba considering niyyarta da ace wani abu ya sake ya samu Hurriya da yanzu ya zatayi.bintu daga mata kai tayi tareda yin na’am sannan tace yanzu abinda zakiyi kije ki fada masu naci abincin zaro ido Bintu tayi tace kada suyi maki wani abu Hurriya tace ba abinda zasuyi man kidai fada masu cewar naci kinji ta ida maganar tare da lumshe idonta masu kyau.bintu daga kai tayi tareda hanyat kofa don isar da sakon Hurriya. Hurriya tasan abinda ke ranta it’s been a while since she played a dirty game wannan karan is not a dirty game she’s playing,it’s action. Itadin tayi takwendo lokacin da tana masarautar Heral kuma kakanta ya koya mata tareda cewa self défense ne ko an kawo Mata Hari she will be able to protect herself she always enjoyed the action don ta dade bata taba defeating kankanta ba who’s very strong and destructive don ranar da tayi defeating dinshi saida ya bata babbar saraauta wadda akayi shekara da shekaru ba’a bama wani sarautar ba saboda irin muhimmancita sai gashi ya bama yar karamar yarinya Hurriya , tareda wata babba chambre à palace dinsu yayi mata kyautar golds da diamonds da dawakai harda gaggarumar dinner ya hada mata damar she was always his favorite granddaughter and she knew that she would forever be his favorite.Hurain Faisait Hamood kenan bestfriend dinshi kuma jikarshi wadda yake jinta kamar shine ya durkusa ya haifeta Saidai ko a lokacin iyayenta basu san wasan da suke da kakanta saboda haka suke fada mata ita mace ce kuma they believe that nothing will hurt her saboda Akwai security’s ko ina a Heral palace don convoy din da take fita dashi a lokacin ko convoy din shugaban wata kasar albarka then why the self defense ?Da mahaifinta da mahaifiyarta sune suka hanata sukace tayi hakuri she’s not stubborn sometimes Saidai fa stubbornness dinta irin na kakanta bata cika yi ma mahaifanta ba , Saidai wani lokacin idan ta kafe din ba wanda ya isa ya hanata sai Allah don ko Hamood da iyayenta din Saidai hakuri. Mahaifiyarta is also from prestigious royal family of 🇲🇱 wadda Hurriya da ace ta dauko irin sarautar mahaifiyarta da ko maganarta ba wanda zai rinka ji saboda tsananin sarauta da iko da mulki nata Hurriya tana iya fin wata shidda bataji maganarta ba Saidai murmushinta wanda kullum yake dauke a fuskarta wanda yake nuni da irin zallah da soyayyar da take ma diyarta bata cewa uhm ko uhm uhm Saidai taita binta da kallo Amman bata cewa uffan idan Hurriya ta shigo har ta gama hidima da bidirinta bata cewa uffan.shiyasa ba wani sabo tsakaninsu Sosai tafi sabawa da kakanta akan iyayenta mahaifinta shima ba mutum bane maisan hayaniyaba saidai yana fira da da ita sosai don haka basu da damuwar komai tunda har mahaifiyarta tace ta daina takwendo itada kakanta ta bari don ranar taji doguwar maganar mahaifiyarta duk da a lokacin ta lura dacewar da kyar takeyin maganar ga dukkan alamu bata saba ba daurewa take don sosai tayi ma Hurriya nasiha tace you should stop doing that my dear you’re a girl kinji your father will always protect you and your husband kidaina kinji babanki bayaso kuma bayajin dadi. Tun daga lokacin Hurriya bata karayi ba ko kokarin yin hakan don har Hamood saida ya tambyeta dalilin da ya sanya ta bari hakanan tace mashi ,yasan halinta na rashin son kutse sosai a rayuwarta don haka ya kyaleta da sai ya sanya an bincika mashi Saidai baisan ya bata mata Daidai da rana daya saboda irin tarin kaunar da yake mata. Sauke ajiyar zuciya tayi ta kwanta tareda lumshe ido hoton mahaifiyarta da mahaifinta na dawo mata a idonta saidai batasan yawan tunani don haka tayi saurin cire abun aranta ahankali tace forgive me my dear parents Amman today she would show them aininhin Hurriya Faisait Hamood Bintu kallon shaho tayi dashi da kaura jikinta duk a mace yanda bazasu iya gano wani shirin da sukayi ba gabanta yana faduwa sosai don tana tsoron suyi ma Hurriya wani Abu Saidai she trust Hurriya kaura ne yayi dariya yace ko kefa ai yanzu kinga ba wanda zai cutar da ita kayanta ne kawai zamu bincika sai mu duba abinmu mu tafi ko shaho Shaho da banda cika da batsewa ba abinda yakeyi don yaune ranar fansar duk abinda ta tabayi mashi.cikin isa yace eh sannan ya kalli Bintu yace ke bace mana dagani ko kuma na fara ta kanki Bintu ai da sauri ta matsa ta nufi dakinsu. Saida suka samu wuri suka zauna tareda jiran dakin yayi shiru yanda baza’a jisu ba. Sun dade suna jira a wajen sannan suka shiga dakin inda bakajin motsin kowa sai wadanda aka hada baki dasu a mata sai kuma su shaho da kaura da suka shigo. Hurriya tundaga kafafunta har zuwa wuyanta a rufe yake don cikinsu ba wanda baiyi mamakin shigar kirkin da tayi ba yau don ko dazu sunganta as usual da dan skirt na jeans iya cinya kilan batasan sauro ya cijeta sukayi tunani Shaho ne ya kalli kaura yace shegiyar yarinyar akwai kyau. kaura kam lumshe ido yayi yace ga gashi ga kamshi don fa inajin kamshinta har a bakina murmushin mugunta yayi shaho yace yau zamu fanshe wulakancin da duk ta tabayi mana karshen jiji dakai da izza yazo. Shaho yace ban iya jira sannan ya karkato kanshi tareda shinshina gashin Hurriya wanda banda kamshin mayukan Khalifa masu tsada ba abinda suke kamshin na bugun hancin shaho yace jar uba yarinyar nan yar gayu ce kaji wani kamshi da gashinta yakeyi wanda yake barazanar fasa mani kai kaura ne yace dallah ka ishi mutane da surutai muyi sauri muyi abinda ya kawomu mu kama gabanmu. Shaho yace hakane sannan ya zura hannunshi saitin wuyan Hurriya. wani giggitaciyar kara ya saki don yadda Hurriya ta rike hannun tare da caka mai tsinke kitso mai tsananin tsini da zafi wanda ba zato ba tsammani don baiga tashinta ba Saidai saukar tsinke da yaji. Cikin tsabar mugunta Hurriya ta murde mashi hannu tareda maida hannun baya sannan ta kai mashi wani duka ta mike tsaye Dukewa yayi tareda rike cikinshi inda ta kai mashi duka yana gwanjin kukan azaba Kaura da yayi tsaye yana kallon irin action din da yarinyar tayi tsoki yayi tareda kallon kankantarta kuma da raina shaho da baiyi ta maza ba kalli fa yarinyar Kaura bude kafada yayi tareda karya wuyanshi saidai ji kake kass kass sannan ya taimaka ya dago shaho tare da tsaida shi tsaye dayake shima shahon namiji ne ya dake kamar ba abinda ya faru. Duk iya shegenta bata isa taci galaba akansu tunda su biyu ne Hurriya kam kallonsu tayi zuciyarta na tashi da bacin rai how dared they touch her royal body sunanta fa Hurriya Faisait Hamood the y really have messed with the wrong person nufota sukayi gadan gadan da niyyar dukanta tareda kadata ahankali ta juya ta dauko iccen data boye wanda basu lura dashi ba saida saukarshi da sukaji kowanne acikinsu .kafin su dawo hayyacinsu ta kara masu Kaura ne yayi ta maza tareda rikota aiko rikon da yayi mata yayi triggering dinta ta caka mashi tsinke dake a hannunta sai jini shaho da yake kokarin guduwa aiko ta buga mashi iccenta a kafa wanda ya durkusa da sauri tareda rike kafar Dukansu a durkushe kallonsu tayi wanda su kuma suka juya sun kasa kallonta Kallon hannunta da yake sanye da safa tayi wanda ba abinda take bukata irin tayi wanka ta wanke najasar data taba a jikinta na wadanan jakunan. Saidai ganin fa ba tabar masu tabon da zasu rinka tunawa da itaba batayi masu wani lahani wanda zata ga jini na fita ba ta tabbata sai taga jini na fita a kowanne daga cikinsu zata iya bacci yau ,daukar iccenta tayi sannan tazo inda suke zazzaune shaho da ya kasa magana alama yake mata da hannu tayi hakuri .har zata buga masu iccen wata idea tazo mata tsinke dake rike da hannunta ta durkusa sannan ta rinka caka ma kowa a gwiwar shi duka biyun aiko nan da nan jini ya fara fitowa saida ta tabbatar ciwon ya shiga jikinsu sosai sannan ta bugama kowanne acikinsu icce ta juya tayi tafiyarta Ihu kara kururuwa ba wanda basuyi Amman kusan ba wanda yake jinsu saboda baccin da kowa yayi. Bazata iya kwana hakaba batare da tayi wanka ba don haka kawai ta fito hannunta rike da fitilar wayarta da keys din part din Khalifha wanda aka aje mata saboda tana zuwa tana gyarawa.ba karamar doguwar tafiya bace tasha banda kukan karnuka ba abinda takeji Har saida ta fara gifto Chambers din princes da princess din ta fara ganin securitys da tsirarrun mutane. Bude kofar part din tayi tana shigowa ta lumshe ido tana maijin kamshin da parlon yake har cikin kanta, ba inda Hurriya ta tsaya sai dakinshi inda yake tsaff agyare banda kamshi ba abinda part din yake. Toilet ta shiga sannan ta hada ma kanta ruwa mai dadi da kamshi sannan ta cire kayan jikinta ta sanya su watching Machine ta dade tana gasa jikinta tareda wanka sannan ta fito daure da bathrobe grey gashinta ta wankeshi tayi drying ya zubo a bayanta Wardrobe dinshi ta bude ta fito da sabbin hoodie brown na bvlgari ta sanya hade da fesa turarenshi tana gamawa ta haye saman gadon Khalifa mai dadi wanda ya zama nata yanzu lumshe idonta tayi kaffn ace wani Abu bacci ya dauketa. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 56 Galadima ya kalli jakadiyya yace mata wacece waccan data wuce . Jakadiya da take bin bayanta da kallo tace bansan taba don ban taba ganin taba galadima yace mata kiyi kokari ki nemota sai a hadata da sauran matan nan .cikin gamsuwa tace shike nan, Hurriya har ta nufi dakinsu inna hanne na zaune idonta biyu da alama gyangyadi takeyi Hurriya na shigowa ta mike a zabure ta rinka kallonta Hurriya itama kallonta tayi tace lafiya ?inna hanne sauke ajiyar zuciya tayi tace lafiya lau. Hurriya alama tayi mata ta zauna sannan ta mika mata ruwa saida tasha sannan ta kara sauke ajiyar zuciya don tasan abinda Hurriya take jira taji ayanzu bazai wuce miye ya hanata zuwa ta kwanta sannan damuwar miye a fuskarta Murmushi inna hanne tayi tace kin tada mana hankali Sosai da bamu ganki ba wasba da kyar na lallasheta taci abinci tana gama cin abincin bacci ya dauketa gatanan kina ganinta ,Bintu ma da kyar na lallabata ta tafi ta kwanta Hurriya data gaji da tsayuwa don wani irin mugun sarawa kanta yake mata Don har kafafunta karkarwa sukeyi inna hanne da tana kula da ita don tun shigowarta tasan bata lafiya don idonta sunyi wani kalar sanyi tareda canza launi da idonta sukayi Murmushi inna hanne tayi ganin yadda Hurriya ke kokarin fada da ciwon don kada aga gazawarta don har ta zauna tareda jingina da yar katifarta wanda idan ba sanin Hurriya kayi ba idan ka kalleta zakace lafiyarta lau don yadda take kokari sosai wurin boyewar ciwonta Ganin inna hanne har yanzu ita take kallo ahankali ta maida jikinta saman katifar tareda lumshe idonta tace bacci ya daukeni a Chamber Khalifha ku daina damuwa da abinda bai kai asa damuwa ba ,maganar ta fito da wani irin huci da zafi don inna hanne saida taji hucin Sosai mai dauke da kamshin mouthwash ya bugi hancinta Inna hanne ba tareda tace mata komai ba tayima Hurriya saida safe ta fita Hurriya kam ko ida fita batayi ba ta sauke ajiyar zuciya sannan Bacci ya dauketa saidai wani irin nishi da shesheka kawai takeyi cikin baccin Inna hanne datake labe bata tafi ba ta fito tareda shigowa wurin Hurriya hankalinta tashe data kalli yanayin da take ciki ai inna hanne da sauri ta fita taje ta dauko magunguna da kasko cike da garwashin wuta tazo da sauri ta barbada mata wani magani banda hayaki ba abinda ya turnike wurin Hurriya kam tana shakar wannan hayakin gayen ta rinka wani uban tari mai sarkewa bude idonta tayi tana kallon inna hanne datake mata sannu amman tana cigaba da zagaye ko ina da hayakin Hurriya alama ta rinkayi mata da hannu ta dakata ta dakata Amman taki Hurriya numfashinta wani seizure yake yana dawowa saida inna hanne ta tabbatar da hayakin ya shiga ko ina najikinta tareda fita hayyacinta sannan ta sanya wani hayakin wanda ya taimaka ya fara calming Hurriya ahankali Sosai don sala sala hayakin yake fita dayan gayen data zuba Ahankali numfashinta ya fara daidaituwa sannan Bacci ya dauketa, inna hanne ajiyar zuciya ta sauke tareda godema Allah hade da jinjina ga yayanta.don tun lokacin data ga abubuwa akan Hurriya ta kaaa sukuni sam har saida taje garinsu inda taga yayanta sannan tayi mashi bayanin duk abinda ya faru a lokacin yayanta shiru yayi tareda mamaki hade da tausayin yarinyar da take gaya mashi don haka yace zai dage dayi mata Addu’a da sauka da sadaka itama yarinyar sai ta dage da azkar saboda makiyan da kikace shiru inna hanne tayi sannan tace nan fa matsalar take don kwata yarinyar abubuwan addini basu dameta ba don duk wani Abu dake nuni da mutum cikakken musulmi ne bata dashi don ko shigarta irin ta turawa ce don idan ba gani kayi tayi sallah ba zakayi tunanin cewar ba musulma bace sai kuma annurin musulunci da baya boyuwa a fuskarta. Shiru yayi yanajin bayanin da tayi mashi sannan yayi murmushi mai sanyi tamkar hakan ba abin damuwa bane cewa yayi ki tayata da addu’a Allah ya shiryata sannan kina dan nuna mata wasu abubuwan insha Allah zata gyara inna hanne bude baki tayi zatayi mashi bayanin halin Hurriyar murmushi yayi mata tareda yimata alama da hannu da tayi shiru gudun daukar alhaki don akan ce ko alkhairin mutum kafada zai iya zama laifi bare akasin haka Allah dai ya gafarta mana baki daya Ameen Ameen Inna hanne tayi mashi bayanin ciwon Hurriya ya dade shiru yana nazarin each and every detail sannan ya tashi ya debo magunguna wasu rare herbs ne wanda da kyar ake samo mashi su a daji hade da ganyen da za’ayi mata hayaki duka magunguna da ya bata ba wanda baiyi mata bayaninshi ba hade da fatan insha Allah indai aka dage anayi mata zata warke Daidai gwargwado tunda Akwai poison a ciwonta amman ya tabbatar ko bai warkar da ita ba wannan yana fatan zuwa gaba idan har ansamo mashi iccen itaciyar dayake nema shekara da shekaru to Zata iya warkewa har abada yana fatan hakan. Inna hanne shiru tayi tareda sauke ajiyar zuciya ganin yadda Hurriya take bacci hankali kwance ba karamin dadi taji ba sannan tayi mata addu’ar bacci don tasan batayi ba ta tafi itama ta kwanta. Karfe 11:50 Hurriya ta bude idonta tarr tana kallon komai da yake a dakin hamma tayi tareda jan numfashin ta cikin ikon Allah taji shi Daidai ziro kafafunta tayi ba karamin mamaki tayi ba don ciwon da takeyi a heral palace tayi wata da watanni batasan inda kanta yake ba irinshi tayi yanzu kuma manya manya hospital around the world amman sai tayi ka’idojin kwanaki data sabayi saita shiga coma Amman in just some minutes ta warke tass.indeed God is great yau ita taga miracle a rayuwarta how she wished her parents were alive to witness this day .inna hanne she really help her ta taimaka mata Sosai a yanda instinct dinta yake bata Tayi sauri tabar masarautar don kullum yanzu da tunanin yanda zata bar masarautar takeyi amman tarasa ina zata samu exist permit sannan wasba da Bintu da inna hanne dake yawan tsaya mata arai Duk da sunanta Hurriya Faisait Hamood ta rasa daina tunanin su da halin da zata Barsu ciki daman ba rabuwa ce akeyi ma kuka ba sabo ,shine matsala she’s always calculative and tasan yanda zata tafiyar da rayuwarta ba tareda wani Abu ya dakatar da ita ba ko yayi mata tsaye ta yanda bazata iya kaudashi ba sai akansu Bintu ta farajin haka,sunanta fa Hurriya Faisait Hamood abubuwa da dama basu gagararta a rayuwa amman wannan karan she’s really afraid of their fimal goodbyes don wata kila idan ta tafi har su gama rayuwarsu itama tagama rayuwarta ba lallai su kara haduwaba. Hurriya a hankali ta dawo daga tunanin da take sannan ta sauke kafafunta kasa tareda niyyar tashi saida wata kyakkwar runguma da taji a wurin wasba ya sanyata janyewa da sauri ajikinta ,wasba kam kara komawa jikin Hurriya tayi tana kuka mai taba zuciya gwanin ban tausayi tace Hurriya idan kika barni bansan ya zanyi da rayuwata ba sai tayi shiru ta rinka share hawayenta tace mahaifana babu su fareedaaa kawai nike da ita a duniya ita kuma ta tafi tabarni sai ta fashe da kuka tace sai ke kuma da nike da ita please kada ki tafi ki barni kinji?hurriya daga mata kai tayi sannan tayi mata alama da tayi shiru everything will be okay. Kafin su kara magana Bintu tazo itama ta rungume Hurriya tareda fashewa da kukan murna tace Hurriya kin sanya naji tsoro sosai don Allah kada ki kara tafiya ki barmu hurriya tureta tayi a hankali tana tsotsar bakinta tana kallonsu sai surutu sukeyi na kada ta kara bacewa don Allah how can she leave this innocent souls ?her heart can’t take it ina ,dayar zuciyarta kuma ta rinka fada mata ko kin manta ko wacece ke sunanki fa Hurriya Faisait Hamood you can do it you can do it dayar zuciyarta kuma ta rinka cewa you’re human too ,you also have feelings and emotions you’re not letting your feelings and emotions to control you but you also have heart like everyone so it’s normal to felt that way, Maganarsu ce ta dawo da ita daga tunaninta ganin hankalinsu har yanzu yaki kwantawa tace masu ina Chamber Khalifha jiya .sauke ajiyar zuciya kowanne acikinsu yayi sannan suka kwantar da hankalin su Jakadiya wadda tazo katafaren parlon Galadima wanda babu abinda babu na more rayuwa ma’aikata sai kai da kawo suke saida suka gaisa cikin mutunci sannan ta farayi mashi bayanin rashin Ganin Hurriya da tayima masarautar Qamar babu inda bamu duba ba don duk manya manya wurin danason ana aiki zan sameta na sanya a duba Amman har yanzu ba’a ganta ba,Galadima jim yayi sannan yace shikenan jakadiyya aikin ki na kyau da kaina zan dubata kafin nan da sati daya insha Allah .saida suka kara tattaunawa sosai yanda abun zai kasance da fara su gaggauta su gama kada Khalifha yazo.sun dade suna magana kafin su kare jakadiyya tayi mashi Bankwana ta tafi. Galadima yayi mamaki sosai da jakadiya ta fara zargin anya ba aljanah bace don irin neman da tace tayi mata tana tunanin fa ba mutum bace murmushi Galadima yayi tareda cewar shi zai nemota da kanshi ba. Shiru tsitt ko ina ya dauki masarautar don bakajin motsi komai sai na tsuntsaye sai kuma itace da suke kadawa Tawagar sarki Faizan ce wanda suka taho daman ya kanyi patrol acikin masarautar to inda ya fito babu wani mutum da zakaga yana yawoba ta inda yake har sai yagama. Hurriya sanye take da wata farar riga mai kyau wadda ta sauka har a collarbone dinta adai dai collarbone din akwai zanen star mai masifar kyau da daukar hankali irin wanda su kim Kardashian’s su keyi jikinta banda glowing ba abinda ya keyi da wani irin salki don skirt din data sanya dan karami ne sai gashinta data daureshi yasha gyara Wasu irin manya manya security’s ne giant sanye da uniform sai hadimai dasu Galadima sai sarki Hurriya wani irin sauri takeyi taje ta dauki wayarta data bari part din Khalifha akwai number ayyo dazata kira ta tambayeta exit permits Kwata kwata bata kula dasu ba kuma bata lura dasu ba ko acikin catwalk dinta wanda takeyi kamar dagan gan koda yake iya tafiya yana daya daga cikin éthiques wanda dole mace ta iya a masarautarsu Kwata kwata bata kula dasu ba saidai jin gam kawai kakeyi don wata kwana ce wadda zasu fita ita kuma zata shiga kuma sarki ne da Galadima a gaba shine ta buge daya daga cikinsu batasani ba Sarki faizan baki sake yake binta da wani kallon don all his life bai taba ganin mace mai kyaunta ba ya kasa ko motsawa bare ya taka Hurriya dan tsotsar bKinta tayi tareda cewa sorry a takaice tayi tafiyarta. Sarki faizan kwata kwata baiji zafin buge shin da tayi ba [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 58 Uwar bayi ce tayi sallama jakadiya na abayanta looking so mighty inna hanne ce ta amsa fuskarta babu yabo babu fallasa don acikinsu ba wanda batayi rayuwa dashi ba kuma babu wanda bata Sani ba so dayawa zuwan jakadiya yakan zama alkhairi ko sharri don ko daga ganinta yanzu tasan mai ke tafe da ita don alamu ya nuna ba alkhairi ya kawota ba. Don haka tayi tsaye tareda kare inda Hurriya take Hurriya kam tagane matar itace wadda tagani da daddare da Galadima it’s not her business don haka she’s busy pressing her phone ita kam jakadiyya shiru tayi tareda kurama Hurriya ido ta Daidai dan sakon da inna hanne bata ida rufewa ba. Tareda karema duk wata hallitar ta kallo Murmushi tayi tareda kallon inna hanne tace ba wurin ki muka zo ba ki matsa ki bani wuri inna hanne kam da wata irin dakakkiyar zuciya yanda takeji bazata iya matsawa ba komai zasuyi mata she will protect Hurriya no matter what duk da batasan mi sukazo yi mata ba inna hanne kamar bada ita suke ba don kare wurin ta karayi tana zuba mata wani kallo uwar bayi itama da wata kalar gadara take kallon inna hanne tace hanne ki matsa jakadiya daga shiyar sarki take bukatar Ganin yar matsiyaciya inna hanne wani murmushi tayi tace duk nan babu matsiyaci wata dariya uwar bayi tayi tareda daurewa tace dalla malama ki matsa tun kafin kiga na kai hannu jikink ganin taki matsawa uwar bayi kam cike da hanzari ta daga hannu da niyyar marin inna hanne saidai wani mugun taushi da laushin hannu kamar auduga ya riketa Kallon Hurriya Dukansu suka rinkayi wadda tayi saurin sakin hannun uwar bayi tana aika mata kallon kashedi duka wurin shiru ya dauka don jakadiya banda kallon rashin tsoro dake fuskarta ba abinda takeyi harta kasa cewa komai ga wani kyaunta da kyaun hallita don ashe ranar da suka ganta basuga komai ba yanzu da take kallonta kusa da kusa yanzu tagane mai galadima yake nufi. Muryar Bintu da wasba kawai kakeji kusan tare suka hade baki Dukansu tare da tambayar mai ya faru shiru sukayi ganin kamar ba lafiya tareda labewa duka suna zare ido Jakadiya wani murmushi tayi mai kyau tayi tareda cewa nazo abani Aron Hurriya ta ida maganar tana kallon inna hanne dasu wasba Wasba kam bazata taba mantawa da matar nan ba don itace mutum ta karshe da tazo ta tafi da fareedaa kuma daga lokacin fareedaa ba’a kara jin labarinta Kallon jakadiya wasba takeyi idonta sun cika da hawaye fam Hurriya batace komai ba itama haka uwar bayi don tun rikon da Hurriya tayi ma hannunta da kashedin da tayi mata da idanunta masu kyau ta shiga taitayinta Wani miskilin murmushi jakadiya ta karayi mai hade da hadari tace nazo Abani aron Hurriya inna hanne da zuciyarta banda tafarfasa ba abinda takeyi tace mata saidai ku dauki Arona don Hurriya bata da lafiyar da zatayi maku wani aiki amman nikam ko wani aiki ne zan iya a matsayin Hurriya shiru jakadiya tayi tana kallon inna hanne wanda da alamar idonta ya nuna ba abinda ba zatayiba indai akan tafiyar ne tasan irinsu da yawa bare kuma hanne itama da tayi suna a masarautar Amman ba abinda zai hanata tafiya da Hurriyar saidai wani iko na Allah don tasan yadda Galadima yabama yarinyar muhimmanci sosai idan har taje babu ita akwai matsala don ita har mamakin Galadima takeyi duk yanda ya rikice akan yarinyar kamar akwai wata akasa don baida aiki yanzu sai na maganar Hurriya don idan zasu hadu a rana sau biyar to sau biyar din nan sai yayi mata maganar wannan Hurriyar don haka bazatayi wasa da damarta ba ,yanzu ta gane cewar Hurriya itadin dole ayi zancenta kuma acigaba da zancenta don tunda take a rayuwar masarautar nan a mata bata dai bata taba ganin mace mai kyaunta ba hade da kwarjini miskilanci da izza kam ,tana shigowa tasan yarinyar nadasu na tashin hankali acikin ranta tace kodai itama jinin sarauta ce don izzarta batayi kama da wadda ba yar gidan sarauta ba don kwarjini da mulkin dake kwance e a fuskarta ya isheka bayanin komai da sauri ta kwabe zuciyarta daga yin shirmen tunaninta wai jinin sarauta a ina? kilan ta jejin sambisa ta zama Gimbiyarsu, gwara tazo tayi abinda ya kawota Kallon wasba da take kuka tayi sannan ta kalli Hurriya tace shikenan bari na ari hanne da sauran yan uwanki Bintu da wasba da inna hanne da sauri suka mika wuya tareda tabbatar mata zasuyi ko miye indai baza’a tafi da Hurriya ba jakadiya kam tayi mamakin irin kaunar da suke mata don a yadda suka nuna sun yarda a cucesu amman kada acuci Hurriya. Hurriya wani murmushi tayi a zuciyarta wanda bai fito kwata kwata ba ashe duniya Akwai wadanda ko baka hada jinin dasu ba zasu soka har haka wani irin feeling mai karfi take ji akansu she’s grateful for this kind of love they have showed her they won her heart sosai Sanye earpiece dinta tayi sannan ta tashi ta tako har inda jakadiyar take ta kalli cikin idonta tace mata I will work muje Kallonta Dukansu sukeyi ko wanne acikinsu kukan zuci yake sai wasba data kasa boye nata don Dukansu ba wanda yaji yayi na’am da bin jakadiya da Hurriya tayi, Wasba kam bazata taba mantawa da irin wannan yanayin ba yanda fareedaa ta tafi da jakadiya haka to itama Hurriya take binta wasba da sauri ta ruga ta riko Hurriya ta fashe da kuka tace don ALLAH Kidawo hurriya zan cigaba da jiranki ba dare ba rana kinji. Hurriya dagama wasba kai kawai tayi sannan tabi bayansu ,uwar bayi suna fitowa jakadiya tayi mata Bankwana daman ta daukota ne saboda tayi mata jagora wurin neman Hurriya Sun danyi tafiya Sosai saigaa wata black suv 2021 baka sai salki takeyi tazo inda suke jakadiya gaba ta bude ta shiga Amman sai taga Hurriya tsaye kunnenta sanye da earpiece jakadiya fitowa tayi ta bude mata sannan ta shiga jakadiya duk daukarta bata iya bude motar batasan cewar yau mulkin ya tashi Cikin masarautar suke yawo inda bata taba gani ba don tafiya ce sukayi mai matukar nisa kafin suzo wani babban gini mai matukar kyau Hurriya kam lumshe idonta tayi tunda ta shiga cikin motar Galadima kam kallonta kawai yake ta madubi motar ,har sukazo wurin jakadiya kam tana kallonshi yana kallonta tabe baki kawai tayi tace uhmmm. Koda suka iso Hurriya kin bude motar tayi har saida jakadiya ta bude mata sannan ta fito tana binsu a baya kanta a sama as always feeling so high and mighty har suka shigo katafaren building din wurin ya hadu karshe don everything is screaming extravagance and opulence komai gashinan na duniya irin luxury and palatial life Kallo daya tayima parlon mai tsananin kyau da daukar hankali duk abinda tagani a wurin ba bakonta bane don taga dubunshi abinda yafi shi a rayuwarta Don haka koda suka shigo she was calm as always wanda basuyi tsamanin haka daga gareta ba don duk yan uwanta yan mata da suka shigo kamar da daya duniya Anyi su kyautar gida da mota da kujerun makkah don sunga duniyar da basu taba gani ba abinci kala kala ba kalar naman da babu haka suka rinka cin abinci suna tsalle suna murna sannan aka ce ma kowa su tafi suyi wanka kowacce acikinsu tana fitowa ta iske kaya masu tsada da turaruka komai na yan gayu Masu wayau acikisu sun rinka mamakin miyasa akeyi masu haka mararsa wayau kam ba ruwansu don shan dadin su suke. Kallonta jakadiya tayi tace kije kiyi wanka Hurriya alamar ta nuna mata dakin tayi jakadiya kam da sauri ta kai Hurriya wani dakin mai tsabar kyau da daukar hankali don tundaga pop dake dakin har painting fari ne gado komai dakin ba karamin kyau gareshi ba. Jakadiya kaya ta mika ma hurriya alamar sune zata sanya amsa Hurriya tayi ba godiya ta ajiye gefen gado ta shiga toilet. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: M .Qamar 57 Short page Security’s dinshi ne sukayo cha zasu bita sarki Faizan yayi saurin dakatar dasu Galadima juyawa yayi har yaga bacewarta tareda godema Allah daya gano inda take aiki don yasan inda ta nufa chamber daya zai kaita ,wato Chamber din Khalifha saboda dead end da Chamber take dashi dakanshi yayi fencing dinshi alamar baisan kowa a kusa dashi ba kamar sauran yadda Chambers din suke ba Galadima ba kara min mamaki yasha ba to wacece ita a wurin Khalifha kodai ya fara Nema matan banzane? Gaskiya aa yayi saurin cewa a zuciyarshi dom yasan halin Khalifha sosai don akwai sharrin da duk bala’inka sai kabar mutum Saidai mai aiki Amman da mamaki don yasan yadda ake shan fama da Khalifha da masu aiki Haka suka bar wurin suka cigaba da aikin da sukeyi saidai sarki murmushi kawai yakeyi time to time har suka gama suka tafi. Hurriya kam ba inda ta tsaya sai part din Khalifha don ayyo take son ta kira kafin tabar garin ta bata exist permit don dazu dataje part din an gaya mata ayyo tafiya zatayi Hurriya trying number tayi sau daya bata dauka ba haka ta kara sau biyu shima sharewa tayi ta nufi dakinsu ta zauna saidai kallo daya zakayi mata kasan cewar tana jiran wani abu Bintu kallonta ta rinkayi sannan tace wai lapia Hurriya shiru tayi batace komai ba kawai sai ta kwanta ta kara dialing number saidai not recheable aka cemata don haka kawai ta kwanta kafin bacci ya dauketa Mai dadin gaske. Galadima ya sanya anyi mashi bincike mai muhimmanci Sosai akan hurriya don ba abinda bai Sani ba yanzu akanta he’s very interested in her don yadda yaji labarinta ba karamin dariya yayi ba yanda take ladabtar da mutane yasan halin masarautar su sarai mutum shike kwatar ma kanshi yanci kuma so dayawa an raina kananun ma’aikata don haka idan mutum ya bari sai manyasu su kasance suna cin zalinsu. Yaune da daddare ya kamata akawo yan matan daga ciki sai su sha maganin bacci su fita hayyacinsu Hurriya kam bacci tasha sosai don tana tashi taje kitchen wurin inna hanne ta zubo mata ruwan zafi taje tayi wanka saida ta gasa jikinta sosai sannan tana dawowa ta sanya deodorant dinta tun sauran wanda chief of security ya sawo mata lokacin da take kwance asibiti riga mai fadi tasanya sannan ta sanya jeans ta kwanta tareda lumshe ido sannan ta dauko sarkar Gold dinta mai wani irin kyau tana kallo tana shafawa wasba da Bintu tare suka shigo Hurriya kwata kwata bataji tahowarsu ba bare taji shigowarsu ai cikin wani irin sauri ta boye sarkar bayanta kwanciya tayi sannan tayi shiru ta runtse idanu kamar mai Bacci Amman ba Bacci takeyi ba tunanin yanda zata samu exist ne ko ta ramine tabi ta gudu daga masarautar Amman duk ta kasa tunanin mai kyau har magrib tayi duka tanajinsu suka tashi sukayi sallah sannan suka cigaba da hayaniyarsu inna hanne ce tazo da tuwo mai dadi da miyar kuka sai tururi yakeyi hurriya ta fara kallo sannan ta ajiye masu abincin aiko da murna Bintu da wasba suka fara yi mata kirari cikin yanayin natsuwa da kamalarta tace yanzu dai ku tafi ko wanke hannun ku da sauri har wani rige rige suke tsakanin Bintu da wasba Bintu kamar tsarar wasba yanda suke guje guje Inna hanne a hankali tace mata Hurriya ya jikin naki bata bude idonta ba tace I’m fine sannan ta bude idonta ta Zuba ma inna hanne su tace mata thank you for saving me nagode murmushi inna hanne tayi saidai basu ida rufe baki ba saiga jakadiya da uwar bayi, [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 59 Toilet ta shiga ta sakar ma kanta shower da ruwa mai zafi saboda tana bukatar wankan sosai don haka saida tayi wanka hade da tsarkake kanta tayi alwala ta fito toilet din Kallon kayan da aka kawo mata tayi masu kyau da tsadar gaske under wears dinta ta sanya sannan ta shafa mai kadan ta shirya cikin grey maxi dress ba karamin kyau tayi mata ba don bata wani cika sanya maxi dress ba rayuwartaba sosai. Saida ta shirya tsaff wanda kallo daya zakayi mata ka kara kallonta tsantsar kyau ilimi da wayewa da jinin sarauta su kadai ke magana a ko ina ,a hankali take saukowa daga part din inda banda ihu da kauyanci ba abinda ke tashi matane masu kyau a wurin kowa taci ado acikinsu mai kyau da daukar hankali suna mai cin abinci sunajin dadi kallo daya zakayi kasan suna cikin murna da farin ciki . Hurriya kusan duka a tare suke kallonta saboda karar takalmin 5inches dake kafarta they were all in awe wannan kuma fa kallo daya tayi masu wanda kusan duk sun hadu a sunacin abinci a dining, table din shake yake da different varieties of food and drinks desserts fruits ne appetizer babu dai tsiyar da babu sai lemuka masu kyau a ido da kuma dadi a baki masu tsananin tsada wanda daman ire irensu saidai à masarautar zaka gansu. Bata zauna cikinsu ba don haka ta nufi kitchen domin dafa ma kanta wani Abu don ita she wasn’t interested with all these ahankali take Neman kitchen din wanda har Allah ya bata sa’a tazo wani daki a hankali ta bude don irin kofar nan ce marar kara tana Ganin ba kitchen bane ta jawo kofar saidai bata ida rufewa ba taji ana cewa ehh duk sun saki jikinsu yanzu zan hada ma kowacce acikinsu shayi bata ida jin sauran maganar ba ta koma neman kitchen Saidai kuma taji bata bukatar komai maganar matar nan take dawo mata tanason ta cire ma’anar maganar ko kuma abinda take nufi Amman ta kasa don haka tayi shiru tana kallon ceiling din dakin da aka kaita. Knocking akayi mata saida ta dauki mintoci sannan ta tashi ta bude kofar tana bude kofar taga jakadiya cikin adonta na bakin lace mai kyau tana murmushi Hurriya dage girarta tayi irin ina jiran naji miye ya kawo ki Amman shiru batace komai ba banda murmushi ba abinda takeyi tace kinci abinci dai ko Hurriya kallonta take tanason ta karanci wani abu a fuskarta Amman taki the woman look fake don wannan dariyar da takeyi ba daga har cikin zuciyarta takeyi ba da alamar caring,cema Hurriya tayi ya kamata muje kici abinci saboda kada yunwa ta kama ki Hurriya dai sai kallonta take da fararen idonta jakadiya na juyawa tayi wani dariyar mugunta Hurriya najin sound din dariyar matar don haka ta rinka binta abaya Har dining din sukaje ta jawo mata kujera yanmatan sai binta suke da kallo tareda alamar burgewa Hurriya zama tayi jakadiya zata fara zuba mata abinci tace no i will serve myself ahankali ta ajiye plate din jakadiya tana cursing dinta acikin ranta don tasan karshenta ya kusa zuwa yau bada dadewa ba suna a wurin aka rinka kawo masu ice tea mai wani irin kyau da kankara harda Hurriya aka kawo ma tea din Saidai acikin yan matan jikinsu na rawa suka amshi ice tea din kowa ta kai bakinta, Hurriya kallon ice tea din tayi wanda shine taji ana magana akai kenan smirk tayi ta cigaba da cin abincinta cikin natsuwa ,kallonta jakadiya kawai takeyi, kasa daurewa jakadiya tayi tace Hurriya ga ice tea nan kisha shiru Hurriya tayi batare da tace mata komai ba ta cigaba da cin abincinta jakadiya kam tayi tunanin bataji ba duk da tafi tunanin ma taji rainin wayonta ne don ta kula yarinyar muguwar yar rainin wayau ce ,cewa nayi ga ice tea kisha Hurriya batace komai ba ta cigaba da cin abincinta har saida ta gama sannan ta amsa sai a lokacin jakadiya tagane taji kawai magana ce bataga damar yi ba tsoki tayi tareda kallon Hurriya data daga lemun zatasha wani dadi ne ya kamata ta juya da sauri zataje ta gayama Galadima good story din don yace sai ta kula Sosai Because daga ganin yarinya she’s smart tun kallon farko da yayi mata ya gane hakan don haka yace mata she have to be very cautious akanta she wasn’t expecting Hurriya zatasha shayin koda yake sune kadai suka san mi suka zuba ashayin kawai idan baka da gaskiya sai kaita kawo abubuwa a ranka haka ta kasance wurin jakadiya Hurriya kam tana tafiya tayi tsoki tace bad bitch sannan ta tungular da ice tea din daman ance idan baka iya kama barawo ba to shi tsaff sai ya kama ka toh abinda ya faru kenan ta tashi tsaye tana tafiyarta tana kallon sauran yan matan da ba abinda suka tasa irin son duniya because how would they not notice their motives perhaps they aren’t smart at all saboda ya za’ayi ka yadda da mutane su dauko ku dayawa sannan akawo ku building mai kyau a baku kaya na sanyawa masu tsada sannan kuma abaku abinci irin wanda suke ci and sai kuyi trusting dinsu a wannan ‘duniyar masu kudin da zasuyi haka batare da cimma wata manufarsu ba suyi don Allah kadan ne she believe they knew everything from the start using dinsu akeyi they’re just feeding their greeds while that’s the most dangerous thing da tasani sabado tasan too much greed can take one to his grave tsoki tayi tana kallon hadamar da suke tace bunch of ignorant people sannan ta haye sama tareda shiga dakin ta sanya makulli ta rufe sannan tabar makullin ajiki saboda she doesn’t trust them at all don kalar mutanen ne da they’ll go at any length su samu abinda suke so don taga haka Sosai a idanun jakadiya . Saida ta karayin wanka sannan tayi alwalar isha’i ta fito mai ta shafa sannan ta sanya wata farar silk night gown da aka kawo mata Banda kamshi ba abinda take don saida ta feshe kusan ko wani turare da aka kawo mata sannan ta zumbula doguwar hijab tayi sallarh isha’i sannan ta kwanta bata wani dade da kwanciya ba bacci ya dauketa Mai dadin gaske . Jakadiya kallon parlon takeyi duk yan mata ne Amman babu Hurriya babu alamunta kusan Dukansu bacci sukeyi da mamaki take bin kowa da kallo saidai ba gifcinta ko kadan shiru tayi tana tunanin inda taje don tunda har tasha shayin ya kamata ace tana kwance tana bacci jeka kadawo kawai takeyi tundaga katon parlon har zuwa dining Amman babu alamar ta ganin rashin Hurriya yayi yawa sai Zuciyarta tace taje ta duba ko tana daki cikin hanzari ta nufi dakin Hurriya ta shiga kwankwasawa kamar zata balla kofar Hurriya cikin bacci taji bugun kofa she hissed sannan tace who’s that Jakadiya sauke ajiyar zuciya tayi tace ki bude kofar Hurriya cewa tayi na fara bacci saida safe Wani abu zan baki kada ya lalace ki bude ki amsa Hurriya shiru tayi ta koma ta kwanta abinta lallai wannan matar batasan wacece Hurriya Faisait Hamood she’s the smartest girl in their palace and she believes that no one can outsmart her Tanajinta tana knocking amman tayi shiru ta gyara duvet din tareda rage ac ta cigaba da baccinta. Galadima ne yazo da wasu irin kyawawa mata kusan guda ashirin har part din sarki faizan wanda yake zaune cikin shigar shi ta alfamar fuskarshi sai annuri yake fiddawa na hutu da jin dadi Galadima ya durkusa ya gaishe dashi amsawa yayi tareda kallon shi ahankali cewa yayi an daura? galadima da sauri ya durkusa yace eh an daura murmushi yayi sannan ya tashi ya kallesu kyawawa ne na ajin karshe don wasu farare ne Mardiya aka kai mashi a daki sannan yayi ma Galadima murmushi ya shiga sarki Faizan kallon mardiya yakeyi tareda takaicin lalata rayuwar yara kanana da sukeyi Allah ya Sani bayasan kalar rayuwar nan wannan wace irin masifa ce ta gidan sarauta shi duk idan hakan ta faru yana mai dadewa yana shiga cikin damuwa ahakan yana ganin duk abinda yake sawa ayi masu gani yake bazai iya biyansu ba. So dayawa yakan tsaya yayi tunanin cewar dolene sarautar ?abubuwa da dama zaka sadaukar dasu saboda sarautar ya kan tambayi kanshi yayi hakuri yabarma Khalifha sarautar ya nemi yafiya , Saidai duk lokacin da yayi wannan tunanin sai yayi saurin kawar da tunanin don bayaso zuciyar shi tayi sanyi but guiltness din ina zai kaishi kananan yara yake sanya a daura masu aure wanda auren ko awa 48hrs bayayi wanda ma’anar auren kawai suyi consummating marriage din shikenan manufar auren ana gamawa kuma zai bada kudi Sosai ace a nisantasu da masarautar abasu gida da kudin sana’a da duk abinda ake tunanin zasu bukata. Abinda sarki faizan bai Sani ba duka basuyin abinda yake sanya su don ko auren ba’a daurawa don hakanan ake kawo mashi matan a wulakance suke fitar dasu a masarautar babu wanda yasan abinda yake faruwa sai su sai Allah, ko reward din da yake badawa ba wadda ake ba mawa acikinsu Allah dai ya kyauta Kallonta yake so innocent and beautiful ahankali fuskar Hurriya ta rinka dawo mashi tunda yake bai taba ganin mace mai kyaunta ba saidai yayi mamaki da bai ganta ba a masarautar saurin kawar da maganar yayi tareda kara kallon farar yarinyar dake kwance saman lallausan gadonshi. Hurriya kam yau da wuri ta tashi don tun ana kiraye kirayen sallahr asuba ta tashi don haka ta samu sallahr asuba da wuri don koda tagama sallah saida tayi wanka sannan ta samu ta koma baccinta mai dadi. Galadima banda bala’i ba abinda yake ma jakadiya na rashin Hurriya itakam jakadiya tsaye tayi tana mamaki don bataga abun tada hankali anan ba saida ma’anar data karanta a duk maganganu Hurriya wanda a bayyane komai yake ,shine yafi bukatar Hurriya may be when he’s done sleeping with her sai ya aika ma sarki ita hakane duk ya nuna a fadan da yakeyi don kamar zaiyi hauka. Karfe 11:00 ta tashi saida tayi bedding gadon data kwanta cikin tsari sannan ta gyara komai ta shiga toilet tayi brush hade da tsala wanka tareda wanke gashinta da shampoo mai kamshi na cantu da conditioners masu sanyi dadin kamshi a toilet din tayi drying kanta ya bushe Sosai sannan ta fito Zama tayi saman vanity table tana kallon kanta a mirror gashinta sai salki yakeyi mai ta fara shafama gashin sannan ta shiga combing dinshi yana sauka har abayanta hair style ta farayi ma kanta masu kyau duk wanda tayi sai taga baiyi mata yanda takeso ba don wanda ta kwance yanzu sai ya maida ta kamar wata baby ita kuma tafi bukatar abinda zai sanyata tayi looking matured don haka kawai ta daure duka gashinta ta nadeshi can tsakiya sannan ta sanya deodorant da sprays kallon kayan da aka kawo mata tayi wani wandone designer yayi capturing dinta wanda duk a farfashe yake ko ina ba kamar ma cinya shiryawa tayi cikin blue wandon crazy da farar riga Banda kamshi ba abinda takeyi fuskarta fayau sosai skin dinta Sai shining da glowing kawai yakeyi kallon kanta tayi a madubi ttaga she’s okay don haka ta sauko kasa Galadima da yake zaune a falon sumar zaune yayi yana kallon yanda take tafiya kamar dagangan takeyi kamshinta ya bade ko ina a parlon gashin kanta sai wani daukar ido yake a she’s natural ,everything about her is natural she’s almost perfect not just perfect she’s beyond perfection don ba wani abu da aka bar mata a hallita wanda za’ace ya zama abun kushe ga mutane babushi sai dai halaye Amman hallita kam babu kushe She’s beautiful and perfect beyond words don kalamai baza su iya rubutawa ba dogayen kyawawan hannuwanta wanda basu da komai amman suna da matukar tsari da daukar hankali don kamar bata daukar ko tsinke Ko wanne a wurin saida yasha jikinshi don harta yan matan dalala suka saki baki suna kallonta confidence dinta kam har yayi yawa Because all eyes on her Amman kamar ma kara gyara tafiyar ta takeyi kamar ma she’s looking down on all of them haka tazo ta ratsa su babu ko kallon arziki bare har suyi tunanin zatayi masu magana duk tabar kamshinta da kwarjininta da uwa uba mulki da sarauta Dining ta zauna tareda zama ta zuba komai accordingly yanda ta saba cin abinci ta faraci Duka idanun akanta yanmatan were all in awe don yadda take cin abinci cikin tsari tareda maida hankali abun burgewa ne sosai Galadima kam shan majina ya fara yana marmar da ido don gani yake duk abinda takeyi saboda shine she’s trying to seduce him she’s also a harlot don yanda take cin abinci kamar dagangan gani take. she is cautious saboda kawai ta burgeshi Cikin jiji da kai tareda baza babbar riga ya tashi yaje wurinta saida ya gama kalleta tsaff sannan yace Hurriya yan mata an tashi lafiya Allah ya sanya dai wurin yayi maki idan baiyi ba ma sai na sanya a canza maki Hurriya kamar batasan Allah yayi hallita a wurin ba ta cigaba da cin abincinta maganar duniya yayi mata tayi banza dashi shikam Galadima dizigin nan ya shige shi don ba’a taba ci mashi fuska ba irin wannan da mutunci shi da kimarshi wanda ba wanda baya respecting dinshi a masarautar dubannin mutane wanda idan yayi magana ake rububin amsa mashi don sunajin kamar sarki yayi maganar. Who’s she what did she think of herself maganar da yake niyyar yi mata kenan kafin ya furta mata maganar har ta tafi batare data san akwai mutum ba bare har tasan ita ake jira Galadima shiru yayi jakadiya kam da sauran yanmatan kasa gimtse dariyarsu sukayi suka fara kyalkyata ta irinta ban haushi. Galadima fuu ya fito yana Nema Hurriya don ya wulakanta ta saidai ba inda bai dubata ba kamar aljannah babu ita. Hurriya kam tana fitowa daga Chamber wani garden ta fara hangowa wanda babu abinda babu tunda ga nesa wurin yayi capturing dinta. Ahankali cikin natsuwarta take tafiya har tazo wurin tunda daga nesa yake kallonta har dariya yayi ganin yanda tayi twitching bakinta tareda frowning face dinta Garden din tazo sannan taje ta zauna saman swing tana kallon yanda bishiyoyi ke kadawa wani solace ne ya fara shigarta don har wani lumshe ido takeyi kamar kuma an tsikareta ta tashi Daidai iccan Ruman ta tsaya sannan ta katso guda daya akwai ruwa akusa da wurin yana ta zuba saida ta daureye ruman din sannan ta fara kokarin barewa Wani irin sligh murmushi tayi mai sanyi alamar it’s her favorite fruits kuma ta dade batasha shi ba saidai har ta dauki daya Because she can’t wait to taste it sai tunawa tayi a tsaye take, bata fara tafiya ba taji saukar muryar sarki faizan yace duk abinda kika dauka nan kamar sata kikayi saboda bana ki bane Hurriya juyowa tayi tare da zuba mashi idanunta masu kyau da kaifi saidai batace komai ba har ta koma wurin swing din ta zauna sannan ta fara shan ruman ahankali kallon yanda takesha cikin natsuwa da burgewa yayi don har wani lumshe ido takeyi alamar abun nayi mata dadi murmushi yayi ya cigaba da kallonta kamar ya samu tv har tagama Saida tagama tace mashi i will repay you in the future kallonta yayi yace ya za’ayi Na yadda saidai ki biyani yanzu shiru tayi tana kallonshi murmushi yayi mata mai kyau don shima badao kyau ba don a wurin shi subira ta dauko kyau Yace mata you can pay me now Hurriya tsotsar bakinta tayi sannan tace I don’t have anything to pay for now sarki Faizan cewa yayi just promise me with anything i ask daga mashi kai kawai tayi cewa yayi be my friend kallonshi tayi mamaki fal a fuskarta amman babban mutum zai zama friend dinta girgiza mashi kai tayi alamar aa sai yace mata you already promised me,so you can’t take back your words Zama yayi a swing din dake opposite dinta sannan yace mata kada ki damu I can be a father and also a friend at the same time daga mashi kai tayi Because he doesn’t look like someone da zai iya cutar da ita saidai batasan cewar sarkine zaune da kanshi Fira ya rinka janta dashi saidai abun mamaki bai taba ganin miskilin mutum irinta ba ta bashi duka attention dinta Amman hardly yaji tayi magana amman tabbas hankalita na akanshi kuma tanajin duk abinda yake fada saida bata cika magana ba, Saida firan yazo karshe tukuna ya farajin maganarta jefi jefi ta fahimce shi sosai ta magana ,kamar yana fama da damuwowi dayawa she knew alot of people like them they just need a shoulder to cry and a friend to rely on,she understands all the pain that he’s going through ,ta conversation dinsu shiyasa ta rinka kokari wurin tana taya shi magana. Sun dade suna magana saida call ya rinka shigowa wayar sarki Faizan non stop saidai yaki dauka Hurriya tace ya dauki wayar sai yaki ganin haka tayi mashi Bankwana may be he needs his privacy but trying to be kind itakam ina ruwanta Koda tabar garden din ba inda ta nufa sai dakinsu don duk yau bataje ba kada hankalisu ya tashi don tasan halinsu da sanya ma rai abu hada wasba kullum Hurriya takan zauna tayi tunanin yanda ta canza sosai kamar ba ita ba she réa do change alot don da bata barin damuwar kowa ya dameta ba abinda ta Sani irin kanta amman yanzu komai ya canza ba kamar da ba Galadima ne yake kiran sarki Faizan wanda baijin dadin hakan ba don ya kashe mashi firar da yake da his little fairy cikin tashin hankali Galadima yace aikin wuka yayi aike yace muyi sauri mu gano wannan yarinyar saboda masu nemanta sun yawaita gab wani abu yake da niyyar faruwa sannan kuma ya bada sako a fada maka Khalifa yana gani Sarki faizan wani irin fargaba da zullumi da tsoro kawai ya shiga abubuwa sunyi mashi yawo damuwa itace kullum abinda yake kwana yake tashi da ita kamar ya fashe da kuka yakeji kamar ya hakura yabar ma Khalifha sarautar kowa ma ya huta haka yakeji.saida ya dade kafin yayi magana sannan ahankali cikin yanayi na nagaji Sosai daga wannan sai wannan yace ma Galadima ku nemota ai akwai zanen tatoo din ko?Galadima cike da girmamawa yace ehhh sannan sukayi ban kwana Galadima wasu irin manya manya security’s da dogarai ya tara kamar za’aje wani fada ko yaki sannan suka nufi cikin masarautar inda masu aiki suke da niyyar neman Hurriya Faisait Hamood. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 60 Manage this page please banajin dadi sosai Banda ina lillahi wa'inna ilahi raji'un ba abinda inna hanne takeyi a kitchen don yanzu taji abinda haule reza take fada wai ana neman wata yarinya Saidai ta jikinta kawai za'a iya ganeta saboda zanen dake jikinta tabb hmmmm inji haule baku ga abin ba kamar yaki ko kuma nace sata don runduna guda suke yawo da ita Inna hanne banda salati ba abinda takeyi don tasan anzo wurin da ba'ason azo, Hurriya na cikin matsala don ta tabbata ita ake neman wannan wani irin tashin hankali ne da ba'a sanya mashi rana  subahallah kawai take fada don ta kasa cigaba da motsa shinkafar dake kan wuta banda kai da kawo ba abinda takeyi hasbunallahu wani'imal wakeel kawai take karantawa ita yanzu mafita kawai take nema wadda zata iya fidda Hurriya daga masarautar saidai a bakin haule taji ance curfew akeyi baza ashigo masarautar ba sannan baza'a fita ba toh minene ma fita. Saurin karasa abincin da takeyi tayi sannan ta fito daga kitchen din da wani irin sauri don yanzu ba abinda take bukata irin taga hurriya don haka dakinsu ta zarce aiko sai cin karo tayi da Hurriya wadda take kwance hankali kwance don tayi crossing legs dinta hannunta biyu ta dora saman kanta ta baya gashinta ya kwanta sai wani uban flat tummy dinta wanda mutum zai dade yana tunanin ina abincin da takeci? don cikin a shafe yake flat dinshi fuskarta na fidda wani kyau na bacci wato sleeping beauty Inna hanne cikin wani mugun firgici tazo tana kallon Hurriya da take kwance alamar bata da wata matsala a duniyar don ana cikin wannan halin tana bacci kallon Hurriya take da wani irin mugun tausayinta tana mamakin yadda karamar yarinyar kamar ta har take iya rayuwa a ko wani hali na rayuwa abubuwa sosai sun faru da ita a rayuwa wanda idan har mutum yanada karanci Imani Amman she’s always strong babu abinda ke girgizata ko ya tsorata ta. Inna hanne cikin dubara ta samu tabar wurin Hurriya don batasan ta tasheta a barcin. Hurriya a hankali ta bude idanunta wanda suke nuna alama ta gajiyawa wai ita har yaushe zatayi rayuwa irinta ko wani dan mutum miye ta tsare ma mutanen da sunki su rabu da ita a rayuwarta shiru tayi tsoro da fargaba duk ya cikata don ta hango storm din dake akwai nan gaba ako da yaushe tana mamakin yadda za’ace wai mutumin da bai san Allah ba wanda kuma ta kanji cewar babu wanda yasan gaibu sai Allah a wurin babanta yana yawan fadar haka sai kuma ace mutumin da baisan Allah baisan komai ba yazo ya Gaya maku abinda zai faru sannan ku yarda don takanyi wannan tunanin so dayawa a rayuwarta kuma hakan yana bata mata rai. Sai dai fa she made a vowed she promised to protect herself no matter what bazata taba bari wani yasan itace Hurriya ba koda kam za’a kasheta tagaji tagajei she’s tired of these things abinda tafi bukata yanzu rayuwarta shine ta huta ta manta da duk wata damuwa a rayuwarta tayi moving on she deserve to be happy again ya kamata ace itama tayi farin ciki kamar kowa saidai yanzu tunaninta bai fi ta yanda zata fara ba kuma ya zatayi ta magance komai don zuciyarta na gaya mata asirinta ya kusa tonuwa don wani irin feelings takeji irin wanda ta rinka jinshi kwanakin baya tayi tunanin cewar kafin matsala ta afka mata zata iya tsere ma matsala but everything seems inevitable don tanajin a jikinta kota tsira ko kuma ta durmiye saidai abu daya tasani insha Allah zata tsira sunanta fa Hurriya Faisait Hamood the one and only Hurriya Faisait Hamood from heral palace and masarautar Qamar she can survive this Bintu ne suka shigo tareda wasba sai hamma wasba takeyi Bintu ta kalli Hurriya wadda ta kalli gabas. [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: M.Qamar 62 Khalifha cikin bayan motar shi ya sanyata sannan driver ya bude mashi mota suka tafi ahankali ya kwantar da kanshi jikin kujerar motar sannan yayi kasa da kanshi yana kallonta kallon dogayen lashes dinta wanda suke kamar tayi fixing dinsu ,sajenta ya duba sannan ya karkata wurin kallon gashinta Fuskarta a daure wani slight murmushi yayi sannan yace stubborn bai daina binta da kallo ba don haka kawai yaji yanason kallonta Baisan dalili ba Amman kawai yau ya samu kanshi da yawan kallonta ahankali ya gyara mata gashin daya sauko mata ya rufe mata fuska. Lumshe idonshi yayi kamshin turaren motar yana shiga hancinshi yana mai jefashi cikin wani yanayi. Suna isowa aka bude mashi mota ya shiga ya fito hannunshi rike da ita kamar baby. Part din an gyara shi tsaf don ko ina sai kamshi yakeyi ba inda ya kaita sai katon bedroom dinshi ya dorata saman gadonshi don zaman da yayi da ita ya gane yanda take kaunar dakinshi ruwa ya debo sannan ya shafa mata ahankali a fuskarta Hurriya a hankali ta bude lumsassun idanunta wadanda suke cike da gajiya kallonshi take bata ko kyaftawa wanda shima haka nashi fannin baya ko kyaftawa wurin kallonta ,wani irin kallo suke bin junansu dashi wanda acikinsu ba wanda yasan ma’anar kallon da dan’uwanshi yake mashi Hurriya kam tsoki tayi sannan tace what is he doing in my dream tace maye tadan murguda bakinta kadan ta rufe idonta sai bacci Khalifha wani murmushi yayi yace my stubborn little maid saboda ai little ce don inda yayi auren wuri rayuwarshi kilan da first born dinshi ta kusa girmanta saboda he’s about 40 Khalifha kam tashi yayi tareda nufa dayan dakinshi wato secret room yana shiga ya cire kayanshi ya daura farin towel ya lumshe idonshi Toilet ya shiga sannan ya kunna cold shower ruwan yana shiga kota ina na jikinshi wani irin sanyi ke ratsa shi wanda ya taimaka wurin kwashe duk wata gajiya tashi. Hurriya kam bacci ta rinkayi mai rai da lafiya don saida tayi baccin sauke gajiya don duk saida gajiyarta ta sauka sannan ta tashi ahankali ta bude idanunta sannan ta kalli dakin Khalifha wanda banda kamshin shi ba abinda dakin yake Hurriya kamshin Khalifa ne yake dawainiya da duk jikinta don kamar shine a kusa da ita takeji frowning face dinta tayi sannan tace wannan kamshin fa ?ganin batada amsa ne ya sanya ta tashi da niyyar shiga toilet ahankali ta tashi Saida kafarta taji tadan amsa ahankali tace what caused this sai a lokacin ta tuna abinda duk ya faru gabanta ne ya fadi don wani fargaba da tsorone ya cikata don tuna halin da take ciki Sai a lokacin tagane cewar Khalifha ne tagani ba mafarki tayi ba daman she wondered why would she saw him in her dreams while he’s nothing to her cizon lebenta tayi tareda tashi ta shiga ciki toilet din wanka tayi da ruwa masu zafi sosai sannan ta fito daure da bathrobe dinshi cikin sauri take komai Amman komai yana tafiya da natsuwarta bataga ta zama ba yau ya kamata duk wata hanya tabi yanda zata tsere ma wannan bakar masarautar don ga dukka alama sun shirya mata sosai don sam baza su barta ba, don haka gwara taje tayi facing abun kuma tayi fighting dinshi bazata mika kai ba sai tabar masarautar nan safe and sound ahankali ta kalli sama tace In Sha Allah don lokacin da tana a Heral babanta yakan ce insha Allah acikin magana watarana ta tambayeshi ma’anar insha Allah aiko yayi mata bayani da kuma nuna mata girman hakan kuma da tabbatar mata cewa indai tace Allah zai mata abinda takeso kalmar ta fado mata a rai tareda fatan Hakan ya tabbata Kayan khafha ta sanya masu kyau kuma designers ko mai bata shafa ba ta fito ta nufi dakinsu aiko tana zuwa su Bintu suka taso da wasba da sauri ta kauce ma kowa acikinsu don ta tabbatar rungumeta zasuyi nan da nan suka fara tambayar lafiyarta lau ba abinda ya sameta ko ?daga masu kai tayi wasba ce ta share Hawayenta tace don Allah kada ki kara tafiya ki barmu kinji daga mata kai Hurriya kawai tayi Don tunanin da takeyi yanzu yanda zata bar masarautar nan Sarki Faizan sai kai da komowa yake da jin zancen Khalifha ya dawo hankalin shi kwata kwata ba’a Daidai yake ba ga tunanin yarinyar nan da baisanta ba da yabi ya dami kwakwalwar shi abubuwa da yawa duk sun hade mashi ya rasa miye yake mashi dadi Galadima ne ya shigo jikinshi na wani irin rawa yana bar bar don shi kadai ne ba’a tafi dashi ba cikin mutanen dake wurin don kaf harda su jakadiya an tafi dasu gidan yarin Khalifha abinda ya sanya bai tafi dashi ba chief of security saboda alakar dake tsakaninsu da sarki Faizan da kuma Khalifha shi yasa ya kyale shi amman Dukansu suna prison Sarki Faizan yana ganin shi yasan cewar ba alkhairi bane tattare dashi don yadda ya shigo a kidime aiko hakan ta faru bakaken labarai ne ya fada mashi guda biyu daya na dawowar Khalifha da kuma yanda ya sanya aka tafi da dogarai da security’s din shiru sarkin yayi don ya rasa abinda Zai fada kafin ya dawo daga tunanin ya kara daga mashi hankali da sakon boka don yace duk yanda za’ayi su nemo yarinyar nan ciki kwanakin nan idan ba haka ba akwai matsala Shiru yayi don ya kasa tunani sarKi Faizan don yasan bai isa acigaba da nemanta ba Khalifha na cikin masarautar nan Galadima ne yace Allah ya taimake ka ga wata yar shawara tawa mu gwada mugani ko zatayi daga mashi kai sarKi Faizan yayi wani irin murmushi yayi sannan yace mai zai hana kawai Khalifha yayi aure kamar yanda ta rinka faruwa dashi da Shiru sarKi Faizan yayi sannan yace Aa kasan duk wadda ya aura ranar take cewa saidai ya saketa Amman bazatayi auren ba ka canza wata shawara Galadima shiru yayi yace wannan ita kadai ce shawarar idan akayi auren da an fara shagali hankali mutane yadan dauke sai mu cigaba da dubata ana shagali ana dubawa. Sarki Faizan duk yanda yaki yadda saida Galadima ya rinka insisting har dai yace akai ma Khalifha takarda da sauri Galadima ya daga kai ya fita akayi rubutu ya kawo ma sarki yayi stamp yakai part din Khalifha Khalifha yana zaune a falo kafa daya kan daya yana amfani da iPad dake hannunshi don duka hankalin shi nakan iPad din saida akayi ma chief of security iso sannan ya shigo hade da sallama Galadima sallama ya karayi mashi Khalifha ba tareda ya dago ko bare ya kalleshi ba ya amsa sallamar shi bayan sun gama gaisawa wanda Khalifha cike da tsantsar mulki yake maganar don har lokacin bai kalli inda Galadima yake ba Galadima cikin yar kyarma don duk yanda kake kazo wurin sai kaji dar don powerful aura dinshi duk ta cika wurin , fara karanta takardar da sarki ya sanya akawo mashi yayi inda yake cewa gobe akwai daurin auren Khalifha da za’ayi bayan azahar kuma mata hudu zai aura Khalifha bai ko kalleshi ba ya tashi yabar parlon don ba abinda ya dameshi idan an tashi adaura mashi mata dari ya san cewar a ranar kowacce acikinsu zata nemi sakinta zasu gudu baisan miye ake turo mashi ba Amman koma miye bai damu ba sune suke auren kuma sune suke raba auren Galadima kam ya shaka lokaci kawai yake jira zai bama kowa mamaki acikinsu daga sarki Faizan din har Khalifha duk zasu dawo atafi hannunshi lokaci kawai yake jira. Koda dare yayi inna hanne tazo taga Hurriya ba karamin dadi taji ba ganin ba abinda ya faru da ita don ta saki jikinta Sosai tunda gashi tana kallonsu Bintu sunata cin abinci kowa yayi shiru baya yin magana inna hanne murmushi tayi don tasan aikin Hurriya ne zama tayi itama bayan sun gama cin abinci suka taba yar hira sannan tayi masu Bankwana ta tafi ta kwanta Saida ta tabbatar Bintu ta tafi ita kuma wasba tayi bacci sannan ta tashi ahankali ahankali ta fita don ganin ko akwai inda zata iya samu ta gudu Cikin sanda takeyin komai har tazo taron wasu yan iskan dogarai suna zaune suna shaye shaye aiko suna ganinta suka taso kowa acikinsu a buge yake yana cewa ina aka samu wannan kyakkawar yarinyr Hurriya kallonsu tayi don kyankyamin su Dukansu takeyi wani acikin su ne ya kawo hannu zai taba mata gashi ne aiko yaji an rike hannunshi Hurriya kallon wanda ya rike mashi hannu tayi shiru tayi tareda zuba mashi idanunta masu kyau wanda ke kara jefashi cikin kaunarta da sauri ya janye idanunshi daga nata sannan ya kalli dogarawan yace ku wuce ku bama mutane wuri,da sauri Dukansu suka bace a wurin Kumurci kasa kallonta yayi ita kuma kallonshi kawai takeyi Cikin natsuwa yace mata kinason fita ne Hurriya saida ta dauki lokaci as always sannan ta daga mashi kai murmushi yayi ganin ji da kanta har yanzu yana nan ba wanda ashe ya ladabtar da ita. Kallonta yayi sannan yace muje na taimaka maki Hurriya daga mashi kai tayi sannan suka fara tafiya duk inda suka gifto da anyi mashi magana sai yaje wurin ma’aikatan ya basu wani Abu sai su wuce saida suka zo Daidai bakin wani gate din da zai iya fiddasu palace din tace na manta wayata Kumurci kallonta yayi da mamaki ganin tana Neman komawa bayan duk wahalar da suka sha ahankali yace mata kiyi hakuri da wayar mana.Girgiza mashi kai kawai tayi sannan ta juya ta koma saida tayi tafiya mai nisan gaske ta fara hango dakunansu ga dare Kunnenta akwai ji don tana tafiya daga nesa taji ana waya ana cewa dole mu nemo yarinyar nan gobe ko a ina ta makale cikin masarautar nan don boka yace duk wanda ya sameta zaiyi sarauta ko dai na aureta kona kasance da ita Ai saboda auren Khalifha da za’ayi ba zai zargi kowa ba ko yayi tunanin Akwai Abu ke faruwa a masarautar don haka ba wata matsalar da za’a samu [5/28, 3:33 PM] +234 802 952 0062: Masarautar Qamar 61 Bintu shiru tayi tana kallom yanayin Hurriya Mai tsoratawar don idanunta sunyi sanyi kamar banata ba kodai batada lafiya ne shine abinda Bintu take fada aranta cikin kulawa tace sannu Hurriya naga kamar bakida lafiya ne shiru Hurriya tayi mata ta tashi ta fita Bintu murmushi tayi saboda hakan ba bakon abu bane a wurin Hurriya wasba ma shiru tayi don sai taji wani iri da taga Hurriya cikin wani yanayi Dukansu zama sukayi sukayi shiru suna kallon juna Hurriya kam inda take wanki da can taje ta zauna tana wasa da icce tana kallon nature a masarautar masu sanya mutane nishadi ahankali ahankali ta saki ranta she believe that they will never get what they want from her after all ita fa jikar Hamood ce Rashin mutumci kawai su Galadima sukeyi don da manya manya Guards wadanda suka kasance abun shakka ko wanne da bindigu acikinsu sai dogarawa wanda hannun su ke rike da zabgegiyar dorina fuskarsu babu wani annuri bare alamar sauki Sai manya mata wadanda suka kasance suke yawo tare dasu wanda suma dai babu sauki a tattare dasu koda ga kallonsu , su jakadiyya sune ke wani irin bincike mata tareda wulakanci da rashin sanin darajar yan mata don sai mutum ya cire kayanshi dagashi sai zani sannan a duba bayanshi agaban mazan daman bayan kawai ake dubawa don boka ya fadi inda za’a samu zanen ajikinta saidai ya kasa ganin fuskarta don wani irin bishi bishi takeyi mashi ta yadda koda shine bokan da yafi kowa iya tsafi bazai ganeta ta haka ba. Galadima wanda sun gama da dakin bayi ne don haka Hurriya ce ta fado mashi arai wata dariyar mugunta yayi don yasan yanzu ne zai iya zuwa ya dauki fansanr abinda tayi mashi, Har sun kama hanyar wani daki yace masu bana nan zasuje ba yace ga inda zasuje.ba wanda ya musa mashi haka suka jero kowa idan ka kalla acikinsu sai yan hanjin cikin mutum ya kusa kadawa Basu wani sha tafiya ba Sosai saiga su adakin su Hurriya wanda yake sosai da mutane aciki saidai tun kafi a ida yi masu iso kowa acikinsu ya natsu ya shiga taitayinshi Dakin shiru yayui don kamar babu numfashin biladama aciki Kallon matan yayi yace ku fara aikinku da kakkausar murya .Daya daga cikin dogarawan yace suyi layi ba musu suka jera layi Cikin sauri aka rinka zuge rigar uniform dinsu ta baya ana dubawa don da an duba naki sai ki koma gefe haka aka rinkayi hadasu bintu da wasba akan layin ba wani bata lokaci suke komai wasu kam hada mari matan ke kai masu Galadima shiru yayi tareda mamakin rashin ganin Hurriya a wurin don ga dukkan alama gashi har an kusa gama searching bata nan saidai tun kafin yagama tunanin da yake yaji wata acikin matan da yazo dasu ta bude Baki tana kallon kofa tace wacece wannan aiko kamar hadin Baki suka juya suna kallon yadda take tafiya in all her mighty She looks fierce and confident don wani jeans ne jikinta shima crazy wandon duk ya fashe saidai shi ba kamar wanda ta sanya rannan bane don wannan gwiwar ne yafi fashewa gashin kanta kitso ne guda hudu gashin ta nanadeshi ba karamin kyau kitson ya karayi mata ba don ya sanya ta kara looking very unique and classy yanda take tafiya kanshi abun kallo ne with so much mighty don kamar tana da sarautar rabin duniyar haka take takawa she’s beautiful tana da asalin kyau wanda idan akace ta zana kanta iya abinda zata iya yi ma kanta kenan inda ace zata fito gasa kyau toh tabbas Akwai 100% possibilities din dazata iya ci Because her beauty is beyond perfection Kamar an dauke wuta an kawo haka ta haska wurin kallonta kawai sukeyi they were all in awe don cikin mazan harda matan suma sun kasa janye idonsu daga gareta . Cikin wani irin confidence ta iso wurin saidai idan zaka bude zuciyarta fargaba ne fal da tsoron makomarta saidai tasan ta riga tazo bazata iya juyawa ba saboda sunanta Hurriya Faisait Hamood ba abinda ke firgita ta bare ya tsorotata jikar sarki Hamood ce fa. She knew that she would never allowed anyone of them to touch her with their dirty fifthy hands saidai batasan mi zatayi ba. Jakadiya kallon tafiyarta da izzarta tagama how could they not see that tuntuni ai basai an fada masu ba wannan Hurriya itace yarinyar da ake magana daga Heral palace why are they so blind that they couldn’t see that since, tafiyarta cin abincinta miskilancita rainin wayonta yayi solving equation din it’s not a coincident she must be the girl they’ve been searching for Galadima gabanshi banda faduwa ba abinda yake yi irin tunanin jakadiya ne shima ya darsu a zuciyar shi sadai dayar zuciyar shi tafi rinjaya da haba ba ita bace bazata taba zama jikar sarki hamood ba duk da alamamomin a bayyane suke Zata iya zama jikar tashi. Da sauri manya manya matan sukazo zasu taba Hurriya kallonsu Hurriya tayi tareda dage gira babu alamun tsoro bare kuma fargaba kallon su tayi ahankali sannan tace cikin muryarta mai dadi tace mi kukeso wani acikin dogarin yayi karaf ya amshe tareda cewa ubanki mukeso shegiya yar matsiyata,Hurriya ahankali ta dan ciji bakinta sannan tace ubana kakeso kallonshi tayi cikin idonshi idanunta cike da rashin tsoro da kwarjin tace ubana yafi karfin kaskantaccen mutum irinka sakarai wawa irinka har ka gama rayuwarka baka isa ka taka inda mahaifina yake ba sannan tace ko karen mahaifina baka isa ka bashi ruwaba bare kuma gugar takalmi har ka kai inda zaka ganshi kace shi kakeso raising brows dinta Tayi in a mocking way tace bawa kamar ka bai isa ba ta ida maganar cikin mulki gadara da jan aji Wurin kamar ita ake jira ta fara magana don har wani extraordinary shiru ya kara dauka wurin sosai har takai aya muryata kawai take fita cikin sautin amo mai dadi da kuma iya shirya kalamai Cikin zafin bakin ciki da kufula dogarin yace ni kike gayawa wannan maganar yau zaki gane waye matsiyaci tsakani na dake ,kallon matan da suke duba bayan yan matan yayi yace kuyi maza ku cire mata rigar ya matso saitin su hannunshi rike da bulala abinda ya Sani yau mai rabashi da Hurriya yau sai Allah don sai ya wulakanta ta ya kaskanta mai muni cikin bainar jama’a don yanda tayi mashi maganar banza sai ya huce akan jiknta don yanzu ya daukar ma kanshi alkawarin bazai iya Bacci ba idan baiga bulalarshi akan jikinta ba. Galadima yasan mi dogarin yake shirin yi amman bazai hanashi ba saboda shima cike yake fam da yarinyar she always gets on his nerves don shi baiki ta wulakanta ba wulakanci mafi muni Dogarin ya kallesu yace wai mi kuke jira tsoronta kukeyi manya matan masu duba bayan yan matan suka kalli guards da sauran dogarawan daga masu kai head of security din yayi alamar kuyi aikin ku kada ku fasa shima haka galadima ya nuna saidai kallo daya zakayi ma Hurriya kasan cewar batayi na’am da wani ya taba mata jikinta ba don wani irin kallo take watsa masu in a warning way wanda kallon cike yake da gargadi da kashedi Galadima kallonsu yayi yace mi kuke jira dallah ku dubata muyi mu tafi akwai sauran inda zamuje aiko yana gama maganar sukazo zasu taba Hurriya da zafin nama ta ture daya daga cikinsu da tayi sa’ar sanya hannunta saman wuyanta wani irin fury bacin rai kawai ke fita daga fuskar Hurriya Basu daddara ba mutum biyu suka karu suka cike hudu sukazo suna kiciniyar cire mata riga jakadiya acikinsu Hurriya wani irin murda takai ma hannun jakadiya da sauri ta saketa how dared you touch me with your stinky hands inji Hurriya ta fada tareda turesu wanda cikin muryarta zaka iya jin zallar bacin rai da kuma bakin cikin hakan da akayi mata Tunda tabar Heral palace bata taba samun ranar bakin ciki irin ta yau ba wasu matsiyata kazamai suke kokarin su tabata not just to touch her ma they’re trying to undress her this is unforgiving itace Hurriya Faisait Hamood nobody dared to touch her even in their palace except for 3people that was her father,her mother and her grandfather except them,nobody would tried that because they knew the outcome don bata da sauki don a Heral palace ace mistakenly cousin dinta ya matso kusa da ita da niyyar ko kai hannu kan yatsanta don ta daukeshi da mari sannan akawo mata ruwa agabanshi ta wanke hannunta ba komai bane, Sai a masarautar Qamar wanda basu kai ta hada hanya dasu ba ma wadanda ba blood relatives dinta ba sune suke tabata da kazamin hannunsu if her grandfather is were to hear this tasan da kilan yau masarautar Qamar tazama labari don kilan sai ya sanya an rusheta Cikin kulewa Galadima kuma ba tareda tunanin abinda zaije ya dawo ba yace ma Guard din su cire ma Hurriya riga now ya buga masu tsawa, Hurriya kam ba karamin gajiya tayi ba don sarkin yawa yafi sarkin karfi sosai don bataci abinci ba duk yau ga abinda ya faru itakam batada karfi don karfin daya rage mata kadan ne Fargaba ne da tsoro fal acikin ranta saidai bazaka iya ganewa ba saboda bacin rai daya rufe mata fuskarta,Dogarin da ta gama gaya ma magani shine ya kutso kai tareda jan rigarta Hurriya kam ta riga ta hakura tayi nata fadan yanzu saidai ta zuba ma sarautar Allah ido saboda karfin daya rage mata kadan ne da wani irin zafin nama da bakar keta yaja rigar saidai ji kake tass tass Sakin baki kowa yayi tareda kallon saitin Khalifha sanye yake cikin wasu hadaddun suits na Hermes wanda suka amshe shi tareda fito mashi da haiba da kwarjini he looks so dangerous and scary don aura dinshi da ta cika wurin mutum bai isa yagane yanayin fuskar shi ba, Hurriya wadda take neman faduwa idonta har rufewa sukeyi da sauri ya tallabota ta fada jikinshi yana mai riketa gam Kowa kallon shi yake da mamaki yanda akayi ya iya ganeta yana makaho da yawa a wurin suna cikin fargaba da tashin hankali saboda basu san Khalifha ba sai dai suna jin labarin shi don duk wanda ya kwana ya tashi masarautar yasan labarin shi wanda ako dayaushe cewa ake baida dadi sam. Rungume yake da Hurriya sannan ya juya ya kalli cheif of security yace mashi take care of them Wurin ba wanda baiji hantar cikin su ta kada ba don ba kowa ke son shiga harkar shi ba. ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** MASARAUTAR QAMAR NA KUDI NE CIGABANSA Naira dari uku kacal300 3139107983 Khadija Mustapha first bank Ko kuma katin mtn ta wannan number 08029520062 Ku tura screenshot ta a wannan number 08029520062 Saimun hade a paid group kasaitattun Mata masu ci da guminsu 🤷🏿‍♀️🙅🏿‍♀️