Duniya biyu mabanbanta[11/1, 11:41 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: _💫TWO DIFFERENT WORLD💫_ _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_ _BISMILLAHI RAHMANIR RAHEEM_ ✍️ M SHAKUR 1️⃣ FREE PAGE Ahankali yake saukowa daga stairs katafaren falon dako gidan shugaban kasa sai haka, yana sauka ahankali yana gyara zaman necktie din wuyanshi da hannu daya kasancewa dayan hannun na rikeda wata briefcase brown, daidai lokacin wata babban mace da a kalla zatai 57 tana sanye da shiga na alfarma tabude kofar wani daki wanda ga dukkan alamu kitchen ne sabida kamshin girke girke daya cika ko'ina tafito bayanta kuma wata maid ce dake sanye da uniform din masu aiki tana rike da babban warmer da alamu abinci ne aciki ta tsaya a bayan matan ganin uwar dakin nata ta tsaya itama, ganin matashin yasa batare data kalli maid dinba tace "kai kulan dining Shafa" sanan tacigaba da tafiya daidai matashin yakarasa saukowa daga stairs yakaraso gabanta, kafinma yay magana ta mika hannunta takai kan necktie din dayaketa fama dashi da hannu daya ta shiga gyaramai, dan murmushi yasaki cikin wata yar karaman natsassiyan murya yace "Barka da safiya Ammi" batare data amsashi ba ta sauke hannayenta kasa ganin tagama gyaramai ta kalli fuskarshi damuwa karara ya bayyana akan fuskarta amma saitai shiru batace mai komiba, kallon datake mai yasa adan shagwabe yace "Ammi, menen.....?" wuceshi tayi tai dinning taja kujera tazauna tadau mug tareda bude flask ta tsayaya ruwan zafi sanan ta waigo ganin har lokacin yana tsaye inda ta barshi yasa tace "anan zaka tsayane kana kallona ko ba break zakayi ba?" Ayanda tamai maganan yasa yagane fushi take dashi kuma yasan dalilin fushin, karasowa yayi yaja kujeran gefen ta ahankali ya ijiye briefcase din hannunshi kan dayan chair dat is next to him sanan yazauna ahankali, mug din shayin dayasha kayan kamshi ta turomai gabanshi cikeda fushi tadau plate mai kyau fari kal kal ta debamai soyayyan Irish sanan ta kallai babu alamun wasa akan fuskarta tace "pepper soup ko ketchup? Wanne zan samaka?" murya chan kasa yace "ketchup" daukan bottle din ketchup tayi tabude tazubamai a gefen chips din dayawa dan tasan Allah yazubamai son ketchup sabida shi kadai agidan nan takesa ayo cefane harda na ketchup dan shi kadai kesha ita haryau abin baimata bane ko dandane batayi. Turamai plate din tayi gabanshi zata zare hannunta daga jikin plate din yakama hannunta yarike hakan yasa tadago idanunta ta kallai, dan shiru yayi yana kallonta sanan yadan sauke ajiyan zuciya asanyaye, murya chan kasa yace "I promise bazan dade ba kinji Ammi please" dan lumshe ido tayi cikeda takaicin shi sanan tabude su, batason tamai masifa hakan yasa ta sassauta murya tace "gobe fa bikinka haba Waleed bazaka iya daukan break kahakura da zuwa aikin nan ba, yakamata kaje kaga Ilham ko, you suppose kaje kaganta kaji medame dame take bukata, yaufa dinner ku mesa kake hakane? Kai baka gajiya da aiki, safe aiki, rana aiki dare aiki dukkai kadai bakagajiya?" tai maganan sounding a bit harsh sanan tai shiru tana kallonshi, ahankali ya saukar da kanshi kasa kaman bazaiyi magana ba saikuma yace "am doing all wat am doing for Dad Ammi, I'm doing it for him" yay maganan tareda dago kanshi ya kalli mahaifiyar tashi sosai yaga jikinta yay wani irin sanyi, hannunta takai ahankali ta shafa full sajenshi dakeda mugun laushi yana kyalli sosai tace "Waleed, Boy listen" tai maganan ahankali tace "I know u are doing all this for your father and trust me, I know duk inda mahaifinka yake he is proud of you cus he gave birth to such eloquent hard working youngman da burinshi shine yataimaki Al Umma, but in this Life Waleed you need to balance somethings, bazaiyu kullum aiki aiki aiki ba, u are needed awasu wajajen, za'ayi bikinka but bikin baya gabanka kwata kwata kabar su Khaleel da Hammad sumaka komi that isn't right kagane?" gyadamata kai yayi ahankali, sanan tace "abinda nakeso dakai yanzu, I know how much this work means to you dan haka bazan hanaka zuwaba, kaje but ana tasowa daga sallan juma'a kadawo kazo kafara shirye shirye, take a break of 2weeks aure zakayi kaji" gyadamata kai yayi amman harga Allah yasan yanada rai da lafiya bazai iya yaki zuwa wurin aiki harna tsawo kwana goma shahudu ba but bazai iya gardama da Ammi ba. "now eat karkai latti" maganan Ammi ya katse shi hakan yasa ya karbi fork din datake bashi ya shigacin Irish din yana dangwalawa a ketchup, yadanci badayawa ba yadau shayin ya shanye sanan ya goge bakinshi yatashi yana kokarin daukan briefcase din yace "ina Mum Ammi? Naje dakinta bata ciki" murmushi Ammi tayi tace "Mum dinka nachan ana harkan biki, ni banmasan ina tanayi ba, wuce katafi sabida kadawo dawuri" gyadamata kai yayi yadau briefcase din yafito waje, babban compound ne mai bala'in girma sai amsa gaisuwan masu aiki yake, gaban wata jeep yayi da wani mutumi katoto ke tsaye agabanta yana sanye da bakaken suit, yana ganinshi yabude mai baya hakan yasa ya shiga ya zauna, yamaida kofar ya rufe sanan yawuce ya shiga mazaunin direba ya kunna motar aka budemusu Gate suka fita. Tafiyan wajen minti talatin sukayi kaman zasubar garin Abuja sanan direban yay horn agaban wani tangamemen Gate wanda sojoji guda hudu ke tsaye agaban wajen rike da bindigogin su da alamu gadi suke an rubuta WARBAI ORPHANAGE HOME AND HOME OF THE DISABLED (Gidan Marayu da Gidan Nakasassu) asaman tangamemen Gate din, sojoji na sarama motan alamun gaisuwa, aka bude gate din akayi daga ciki direba yaja motar suka shiga, titi ne har titi kaman sun shiga wani gari daban suka hau tafiya, manyan fulawowi sun ratsa dan dandamalin tsakiyan titin daya raba titin shiga da titin fita, babban wurine da girman shi zaiyi girman wani babban University, daga farko farkon babu wani gini ta wajejen sai sport yard, wajen kwallon, wajen buga long tennis, basket ball sune awajen, almost tafiyan 5 min sanan sukakai wajen wani tangamemen masallaci mai kyau gaske an rubuta WARBAI MASJID ajiki da larabci, sanan sai wani katon story building da aka rubuta Boys Section ajiki mai girman gaske, babu kowa agaban wajen sai wasu yan yara haka dake sanye da uniform na makaranta su kusan goma da wasu ma'aikata maza ke taredasu suna sanye da jeans saikuma riga dayakasance uniform ne dan yanada logo WARBAI ORPHANAGE HOME AND HOME OF THE DISABLED rubuce ajiki, yaran nakasassu ne dan wasu hannun guragu ne dasu, wasu idanunsu wani kala, wasu nada katon kai, wani kuma shanyayyen hannu saidai dukkansu atsaftace suke fes fes, kallo daya zaka musu kagane suna samun special kula, suna sanye da clean uniform da white sucks dinsu ga jakunkunan makarantan suke goyedashi da ko wanne akwai sunanshi ajiki sabida a dinga ganewa dan jakunkunan iri dayane sanan ajikin school bag din shima akwai logo orphanage home din akai, agogon hannunshi ya kalla ganin tara saura yasa anatse yace "stop the car" parking direban nashi yayi baijira yafito yabude mai ba yabude motan yafito cikin dan fushi dan yanayinshi ya nuna haka, yaran suna ganinshi sukahau ihu suna tsalle irin na yaran nan sukai wajenshi da gudunsu. "Teacher, Teacher, oyoyo" kowanen su burinshi yakamo hannunshi yarike kosu kamashi, murmushi yayi daya karama fuskarshi wani irin kyawu da cikan haiba, ahankali ya tsugunna dan tsayinsu yazo daidai cikin harshen turenci yace "Hello Children" suma cikin harshen turenci sukece "Hello Teacher" sosai yaran ke tsalle tsalle banda mutum daya cikinsu da yake kuka mara sauti sai hawaye yake sharewa da bayan hannu, maaikatan dake kallonsu cikeda girmamawa suka gaidashi. "Barka da shigowa Dr" bai tsaya amsa gaisuwan suba strictly yace "why are this children late? Maiya faru ba'a kaisu school dawuri ba?" daya daga cikin ma'aikatan ne yace "Dr gabaki dayansu basuyi homework bane antsaya amusu ne" "what happen da baku zauna dasu kun ko yamusu ba jiya? Kunzaci am paying you all ne dan kuyi yanda kukaga dama?" yay maganan babu wasa dan inhar kan yarane or duty nasu he can question, baya daukan raini, saisa suke mugun tsoronshi, cikeda girmamawa daya daga cikinsu yace "mun shafa'a ayakuri Dr, hakan bazai kara faruwa ba in sha Allah, dan Allah kayakuri" "sorry teacher" yaran suka fada ganin yanayin fuskarshi yanuna he's a bit angry, kasa magana yayi sabida sun bashi hakuri yadauke kanshi yamaida hankalin shi kan yaron dake kuka, tashi yayi ya daukeshi yace "why are you crying namiji?" murmushi yaron yayi yadaura hannunshi kan necktie dinshi yana kallo abin yama daukemai hankali, necktie din yakama yana kallon fuskar yaron yace "you like it?" gyadamai kai yaron yayi da sauri hakan yasa yay murmushi yace "okay zansa akawo muku naku anjima okay" washemai baki yayi yaron yayi cikeda jin dadi hakan yasa ya saukar dashi kasa yace "a tafi school to, bye" "bye Teacher" suka fadi dukansu atare sanan suka wuce school ya tsaya yana binsu da kallo, babu abinda yake so kaman yaga he's the reason behind this innocent children smile, yakai kusan 5min yana kallon yanda suke tafiya suna wasa suna tsalle tsalle maaiktan na tattarosu sanan ya kada kai yawuce yashiga motar da direban yabude mai sanan yamaida yarufe yakoma gaba yaja motar sanan suka tafi. Babbban gidan marayu ne da nakasassu, akwai wani dankareren building da aka rubuta kitchen and dinning ajiki, anan both ma'aikata da yaran gidan marayu ke zuwa suci abinci, wani babban story building ne dake kusada kitchen din shi kadai ne building din da aka katangeshi an rubuta girls section ajiki, sai ta dayan bangaren haggu wani babban school ne, akeai nursery har zuwa SS3 ga qualify teachers sanan akwai islamiyya inda kullum by 4 yara da manya zasu tafi islamiyya ai karatu 6 suke tashi kowa ya dawo gida dan lumshe ido yayi yana tunawa da mahaifin shi shi yasan he can never be like his father dan baitaba ganin the most generous person in this world like his father ba, baban shi nada taimako, ga son zumunci ga karfafama talakawa saisa bayan ya rasu he set up this orphanage home din in his memory dan lada yadinga kaiwa gareshi, setting it up wasn't easy within the first two yrs dayay establishing nashi government sukai approving sanan sukai licensing orphanage din dan a yanzu ko tsintar yara akayi saidai gwamnati subada izini akawo yaran gidan, sanan gwamnati nabada tallafi dudda baya bukatar tallafinsu he has morethan enough that can keep the orphanage running in the next hundred years. Ahankali yabude idanunshi jin motar yay parking, budemai direban yayi hakan yasa yafito yana bin parking space din admin block din dayaji flowers da kallo komi looking neat a perfect kaman a dubai, wani guy ne fari dogo dudda baikai Waleed din tsayiba yafito daga wani office yana sanye da bakin suit da necktie awuyanshi, hannunshi rikeda wata pad ta apple yana saukowa daga dan stairs din da bazasu wuce guda 10 stair case ba dazasu sadashi da kasa yana tunkaran su, hannu ya mikamai yana murmushi irin ta tsokana dinan yace "Ango I didn't expect to see u here today na dauka sai anjima zamu hadu a dinner" dan hararan shi yayi yace "Mr P.A tell me wat we got today?" dan dariya guy din yayi yace "P.A badadi abakinka dan baka saba cewaba malam, better call me da sunan da babana ya yanka raguna biyu ya lakaba min ARHAM ABDULLAH" dan murmushi yayi daya mugun lobar da dimples dinshi yawuce shi yafara hawa staircase din batare daya juyoba yacigaba da tafiya a binshi, sanin bazai sake cemai komiba yasa yadan dan danna screen din ipad din dayake rikeda shi yana biyeda shi abaya yace "all right let's see wat we've got here" sanan yadan sauke ajiyan zuciya yace "okay Boss, you have five major abubuwa da zakayi yau, number 1 is zakai magana da company Tata marcopolo dakasa su aikomana da 5 marcopolo buses dazamuyi amfani dashi for excursion dazamuje yankari game resort next week, sai the second thing is zaka shiga theatre by 9 surgery yaron nan dakeda outgrowth awuyanshi, abu na uku is zamuje girls section we need to inspect bunk dinsu da Iyami tamana complain are due for changes, abu nahudu kanada meeting da all the employees bayan sallan juma'a by 2:30, sai last abunda zakayi shine letter dakace zakama state government" gyadamai kai yayi daidai sun karaso gaban office dinshi, hannunshi yadaura ajikin wani glass haka dake manne agaban kofar, wani blue wuta glass din yakawo sanan yay scanning hanunshi sanan kofar tabude ya shiga ciki Arham biyeda shi, babban office ne, hadadden gaske dan tsayawa bayanin shi is a waste of time, office ne dayasha office furnitures na zamani, suit dinshi yacire yay hanging akan wani designers hanger sanan yawuce yaja kujeran shi ya zauna, shikuma Arham ya zauna a kujeran baki yana facing nashi yana jiranshi yay magana yaji amsan shi, agogon hannunshi Waleed ya kalla anatse sanan ya saukar da hannun yace "by nine zan shiga operation din, I think you will handle waya da company Tata marcopolo, and u will handle inspection of the girls section bunks, meeting with all the employees should be prospone cus banda time yau, you should tell secretary ya tura musu message kan na daga meeting din till further notice, tura letter ma to state government I don't think bazai yuwu yau ba maybe jibi nasami time zanyi, zaka iya tafiya kaje kai aikinka" kallonshi Arham yayi hakan yasa yace "wat?" ahankali Arham yace "talk to me X-Man, I know something is wrong with you, talk to me yaushe muka fara boyema juna issues?" dan hararan shi yayi yadauke kai batare dayace komiba, "X-Man" Arham yakirashi ahankali, cikin dan fushi Waleed yace "how many times do I need to explain this to you P.A time for work should always be time for work, ba'a hada aiki da friendship, please go and do your job I pay you for it, we will talk anjima" cikin fushi Arham ya tashi daga kan kujeran dayake kai yace "kasan problem dina dakai?" dago idanunshi dasuka dan chanza launi Waleed yayi ya tsareshi dasu, cikeda jin haushin shi sosai yace "you are so weak but u hide under the face of rudeness, you know what? You sucks, kuma kar Allah yasa kafada lemme go and do job din da you pay me for it" yabugi table din da hannu yay kara sosai sanan yajuya zai fita, sosai yaji wani iri kiranshi yayi. "Arha......" bugomai kofan yayi hakan yasa ya lumshe ido tareda daura hannunshi kan saman goshinshi yana nishi ranshi duk abace saikuma yadaki table din yace "f**k!" dan gajeren tsaki yayi yatashi, wani kofa dake cikin office din yaje, hannunshi yasa kan kofar itama kaman wanchan kofar yay scanning hannunshi sanan yabude mai ya shiga ciki, hadadden dakine da babu abinda babu aciki, gaban wani fridge yaje yabude, kwalaban wine ne kala kala, dauko daya yayi yadau glass cup yakoma kan hadadden Italian bed din dakin yazauna, yabude wine din ya tsiyaya a cup ya ijiye kwalban akasa sanan yadau cup din yakafa abaki ya shanye, zare cup din yayi daga bakinshi yana yatsine fuska sabida daci sanan ya ijiye glass cup din ya kara kallon agogon hannunshi, ganin tara saura yasa yafito, fita daga office din yayi ko kadan ranshi ba dadi yay hanyar babban clinic din orphanage din sai gaidashi ake amma baiko iya amsawa. Direct office dinshi ya shiga ya chanza kayanshi zuwa kayan shiga theater sanan yafito ya shiga theater din. [11/1, 11:41 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣ FREE PAGE Wajajen 12:45 yafito daga asibitin da akwai Dr and qualify nurses, yawanci in ya shiga ciki yaje ko operation zaiyi ko kuma wani critical issues ne da akai needing attention dinshi shine yake shiga ciki. Office dinshi yawuce yana shiga yaga wayanshi akan table inda yabarshi tana ringing, karasawa gaban table din yayi ya kalli screen din wayan Ilham yagani kan screen din hakan yasa yadauke kai yawuce ya shiga dakin dake cikin office dinshi, bathroom yashiga yawanko hannayenshi ya dauro alwala sanan yafito ya shirya cikin suit dinshi yabude kofa yafito daidai wayar tahau ruri karasawa gaban table din yayi yasa hannu yadauki wayan ya kalli screen din ganin Ammi ke kiranshi yasa ya danna yakai wayan kunnenshi. "yamukai dakai Son?" kasa magana ma yayi dan baisan me zaice mataba, kwafa Ammi tayi tace "anyway kanenka Abdul da Hasim sunzo although suntafi masallaci su dawo kaikuma sukazo nema sun gama komi na Hall din wai" ahankali yace "yanzu zan tafi masallaci daganan zan wuto gida" Ammi batace mai komiba ta katse wayan abinta, bude kofa yayi yafito yay wajen parking space direban shi dake hira dawasu ma'aikata awajen da sauri yataso yabudemai ya shiga cikin motar yarufo sanan suka wuce suka tafi, bai tsaya neman Arham ba dan yasan zasu hadu anjima kuma yanzu yasan aiki yake he's handling many things yau. Wuraren 3 suka shigo anguwan su ganin yanda kofar gidansu ya cika da jama'a yasa yaja wata gajeruwan tsaki yadau wayanshi, number Ammi shi yay dailing ringing biyu ta daga zaiyi magana yaji muryan Mom tace "Dan Yaro kana ina?" dan shiru yayi kafin ashagwabe yace "Mom ina waje I can't come inside mutane sunyi yawa" dan dariya tayi tace "to miskili mai tsoron mutane tunda cinyeka zasuyi, sangamemen katon namiji dakai kana tsoron taron jama'a, sa direban ka yazagayo ta bayan layi zansa abudema Gate din wurin" "OK Mom" katse wayan yayi yacema direba "muje tabayan layi" jan motan direba yayi suka zagaya kafin ma su karasa sukaga har anbude Gate din Abdul da Hasim yagani suka bude suna ihu ango ango ango, samari ne dudda basukai shi girma ba amman suna yanayi dashi saidai yafisu kyau nesa ba kusaba, parking direba yayi sukuma suka shiga maida gate din suna rufewa, saukowa yayi daga motan ya ballamusu harara suka kwashe da dariya, Hasim yace "Ya Waleed muje ka chanza mun karbo maka kayanka kaci gayu wife dinka needs u" baice musu komiba yawuce ya shiga flat din wajen suna biyeda shi, anan falo ya barsu suna hayaniyan su baice musu kalaba yawuce bedroom, kayan jikinshi yacire ya shiga bathroom wanka yayi yafito daure da towel, ayanda yake tafiya zaka gane babu abinda kemai dadi, shafa mai yayi ya shirya cikin wata bugaggiyar shadda mai light ruwan toka ta mugun haska shi sanan yadau turare zai fesa yaji anyi knocking kofar saikuma aka bude aka shigo, wata mata ce fara babba sosai tai kama da matar dazu saidai bata kaita girma ba da manyanta ga dukkan alamu kanwarta ce, ahankali yace "Mom" murmushi tayi ta maida kofar dakin tarufe takaraso gabanshi tana murmushi sosai tana binshi da kallo tace "wow kaga yanda kai kyau kuwa Dan Yaro na, I wish mahaifin ka na raye yaga wanan ranan da Walilin shi zaiyi aure, iyye kawo turaren kaga na fesamaka" karban turaren tayi daga hannunshi tashiga fesamai tana kallon fuskarshi ganin baya kodan murmushi, ajiye turaren tayi sanan takama kafadar shi ta zaunar dashi kan gado sanan tazauna gefenshi ahankali tareda saukar da ajiyan zuciya, hannunta tadaga tadaura ata bayanshi takamo kafadarshi hakan yasa ya kwanta da kanshi kan kafadarta ahankali sukai shiru tanajin yanda yake saukar da ijiyan zuciya sanan tafara magana. "dagani sai Adda umman mu ta haifa, Umma nada cikina Abban mu yarasu, awahale Umma tahaifo ni inada shekara 7 aduniya itama tarasu, wani mutumin anguwan mu, attajiri dake shiri da Abban mu kafin yarasu inji Adda shiya karbemu yacigaba da kulada mu ahaka marigayi mahaifinka daya kasance abokin shi yaga Adda ya aura lokacin inada shekaru 15 ta tafi dani gidan mahaifin ka, da ita da shi suka cigaba da rainona suna tarbiyantar dani nakasance nine first child dinsu, ahannun Adda nataso nai girma, tadauki lokaci mai tsayi kafin ahaifoka, Waleed kakosan dani da mahaifinka ne muka samaka sunan nan, Waleed" tai murmushi sanan tacigaba tace "u are everthing to me Waleed with a plus, nina raineka ita kanta Adda har mamakin irin son danike maka takeyi, saisa zakaci har yau bata taba kirana da Maman Hasim saidai takirani da Maman Waleed, na raineka na kula dakai to the extend ko numfashi ka fitar ina gane ta rashin lafiya ce kota farin ciki, Waleed I know Adda na sama dakowa, and nasan kowace irin hukunci tadauka a rayuwanka is for the best badan ta cutar dakai ba dan zan iya rantse maka kaine farin cikin mahaifiyar ka, kai kadai takesawa a ido taji dadi, u are her entire world, batada miji kaine komi nata, kasaki ranka, today is your day, auren ka akeyi, be happy, for once ka manta da wanan aikin Arham na nan I know yaron kirkin nan will handle everything, ka shirya kaje wajen Ilham kaji medame take bukata kabata bikinku ake, rabon dakeje wajen yarinyar nan zance anfi wata, haba Waleed so kake Adda tai fushi, kasaki ranka, and enjoy yarinyar nada hankali ga kyau, gata graduate, lawyer fa eh, kodan yanda Adda keson auren kaima saikaso, bakasan Adda nason tasami jika kota iya maida sunan mahaifin kaba, kome zakayi kasama ranka u are doing it for your mother wlh Allah zai baka ladan hakan, u are doing it for your mum, repeat after me I am doing this for my mother" dan shiru yayi kafin ahankali yace "I am doing this for my mother" murmushi Mom tayi tace "yauwa Dan Yaro, tashi to" tai maganan tana dago kanshi daga kan kafadar ta sanan ta sumbaci goshin shi ahankali kafin tasake shi, hulan shi tadauka ta shiga karyamai tace "ka kwashi kudin dazaka basu?" da sauri yace "su wa?" dan baisan suwa zaibama kudi ba, dan dariya Mom tayi ta kafamai hulan aka tace "zaka bama kawayen Amarya kudi suyi duk wata hidiman daya rage kagane" gyadamata kai yayi yatashi tareda bude drawer gefen gadon yadau kudi yan 1k rapa guda biyar yasa a aljihu Mom sai binshi da kallo take dan tadade bataga yay kyau hakaba kodan yawanci suit yake sawa oho, sanan yajuyo ya kalleta, murmushi tamai tace "muje" fitowa sukayi atare su Hasim na ganinshi sukahau ihu Mom takama baki tana kallonsu sanan ta kalli Waleed tace "ahhhh lallai Waleed kwana biyu baka lallasa marasa kunyan nan ba" harara Waleed ya watsa musu sanan yajefama Hasim key yace "let's go, u drive" tashi sukayi, Abdul yace "bye Mom" bye tamusu suka wuce suka fita gwanin ban sha'awa, Waleed na dudduba wayanshi ganin har yanzu Arham bai kirashi ba wanda inda normal ne da yanzu sunyi waya sama dasau uku, ijiye wayan yayi gefenshi yana yan tunane tunane, Hasim da Abdul sai hiransu sukeyi dan sune gaban mota har sukakai Wuse, agaban wani tangamemen gida sukai parking, shima gidan cikeda jama'a gate abude event ma akeyi dan sai raye raye ake, kashe motan Hasim yayi yajuyo ya kalli Waleed yace "ya Waleed kirata" wayarshi yadauka yay dailing number data kirashi dazu dayay saving da Ilham, ringing daya aka dauka kafin yamayi magana muryan wata mace ta ratsa kunnenshi. "Baby, Hello Baby, Dr" batare daya amsata ba yace "muna kofar gidanku" wani irin ajiyan zuciya ta sauke da saida yaji daga wayan tace "Omg, innalillahi, Baby na da gaske kana kofar gidan mu?" jin yay shiru bai bata amsaba takuma san bazai bata amsanba yasa tace "okay okay, bari naturo Salima ta shigo daku, ni bana gidanmu ina gidan Anty, amaryan Dady the next house na gaban gidanmu, uhmmnm bari, bari Salima tazo ta shigo daku" tafada sounding super excited tsabagen murna, kasan cewa yasan gidan amaryan baban nata yasa yacema Hasim ya gangara gidan gaban gidansu, hakan akayi Hasim yay parking gaban gidan, ko minti daya basuyi da parking ba wata budurwa doguwan tafito tana sanye da wata atampan biki taci makeup tazo gaban motan taredasa hannu tai knocking glass din motar dan bata iya ganin mutanen ciki, bude mota su Hasim dake gaba sukayi suka fito, cikeda fara'a tace "sannu ku da zuwa ina yininku" cikin fara'a Abdul yace "kawayen Amarya ansha kyau" dan dariya tayi tace "ina Dr? Amarya nachan takosa ta daura mijinta a ido" duk dariya sukayi Hasim yabude mai kofa, anatse yafito dan ko kadan baida garaje yana dan daddanna waya dan sako yake turama Arham, binshi Salima tayi da kallo dan all this while labarin shi takeji bata taba sa Dr a idoba, now she see abinda Ilham tagani ta mutum mai, guy din yahadu. "Hi Dr" tai maganan ayangance tareda mai waving hannu, dagokai Waleed yayi ya kalleta saikuma ya dauke kai yamaida hankalin shi kan abinda yake typing awaya yace "Hey" faduwa gabanta yayi ayanda yayi maganan cikin izza akuma kasalance sai taji ya mugun cikamata ido ga shakkan shi dataji all at a time, juyawa tayi ta kalli su Hasim tace "to bismillan ku, ku shigo" ta shiga gaba su Hasim biyeda ita, saida yatura sakon sanan yamaida wayan aljihu yabisu yana taku dai dai suka shiga gidan, yan mata ne dayawa a compound din ana yan abubuwa, wasu na pictures wasu na cin abinci sunci gayu sosai kowacce tasha makeup suna ganin su Hasim akadau guda ango ango, dariya Salima tayi tabude musu kofar falon da tuni kowacce mace tafice babu kowa ciki agyare tsaf suka shiga ta nuna musu kujure, sanan tawuce kitchen drinks takawo musu na alfarma tadan saci kallon Waleed dahar lokacin wayanshi yake daddannawa tace "ga drinks kusha bari nakawo amarya" sanan ta juya tai stairs, wani daki tabude ta shiga inda wata kyakkyawan yarinya ke zaune akan kujera da a kalla bazata wuce 25-26 years ba ana mata makeup, tana sanye da wata doguwan rigan ashobi white dayay mata shegen kyau mai makeup din na daura mata head da kyau, tana ganin Salima tace "kin shigo dasu Salima?" gyadamata kai Salima tayi tace "eh suna falo, ke Khadija dama haka Dr naki yake? My God he is damn cute but yanada wulakanci sosai wlh" murmushi amaryan tayi tareda juya idanu tace "don't tell me u expect handsome rich guy mai status nashi yazama kaman all this random guys you use to know on the street? Angaya miki irinsu Mubarak dinki ne? Cheap guys?" ta bushe da dariya mai makeup din itama tafashe da dariya, ganin mocking dinta Ilham keyi yasa Salima ta tashi ko kadan bataji dadin abinda Ilham tamata ba, tasaba da halinta dan sabawa amma ta tsani tacimata fuska agaban wasu, ganin ta tashi zata fita batare data cemusu komiba yasa da sauri Ilham tace "me haka kekuma daga wasa dadina dake saurin fushi Salima, yakuri to pls dawo kinga fa ke zaki kaini kasa bai kamata na sauka kasa nikadai ba kekuma wai bazaki gama min daurin bane?" da sauri mai makeup din tadauki pin tana sosokewa a ashoken. Dawowa Salima tayi ta tsaya akanta, karasa soke daurin tayi Ilham tamike ta kalli Salima ganin ta daddaure fuska yasa tawani fada jikinta tareda rungumota tace "dalla na face miki sorry please karki damu anjima zan baki labarin Dr kinji ni yanzu kiyakuri dan Allah" yanda duk takaiga fushi saida tai murmushi tace "shikenan" tace "kinga yanda kikai kyau kuwa kaman bakeba Ilham" murmushi tayi tace "yi sauri muje naga Dr dina" hannunta Salima takama sanan tabude kofan suka fita sau daya tasaci kallonshi ta sunnar da kanta kasa ganin bashi kadai bane, shi hankalinshi ma nakan wayan hannunshi yana danne danne yay wani irin kyau da saida taji gabanta yafadi hakanan taji wani kishi yataso mata yanzu duka matan dasuka cika gidan nan su ganshi ahaka, da kyar ta iya ta danne kishin suka cigaba da sauka daga stairs ahankali, Hasim ne da Abdul suka tashi suna murmushi "wow, Amaryan Ya Waleed" karasa sauko da ita Salima tayi tana musu murmushi sanan takaita harkan kujeran da Waleed ke zaune two sitter ta xaunar da ita a gefenshi tace "Dr ga amaryan ka nan nakawo maka yanzu kwa barni nahuta" maganan dayaji yasa yadan dagokai ya kallesu sanan yadauke kai, juyawa Salima tayi tai waving su Hasim tace "bari naje waje" da sauri Abdul yace "bari muma mubiyoki mubama love birds some space" dan dagokai Waleed yayi ya watsa musu harara suka kyalkyace da dariya suka fice abinsu falon yarage dagashi sai Ilham dake zaune kusada shi dukansu sunyi shiru. Almost 5min suna zaune basucema junansu komiba sanin zasu iya kwana ahaka bai cemata kalaba dan tasan magana wuya takemai yasa ahankali tamika hannunta dayasha lalle ta daura kan hannunshi daya ijiye kan laps dinshi ta kama hannun gam, atare suka dagokai suka kalli juna, tasake matse hannunshi dat feels so soft kaman hannun mace smiling, ahankali tace "Dr is our wedding are u not excited? I feel so happy because am getting married to love of my life, I love you so much Dr Waleed Warbai" tai maganan hawaye na gangarowa daga cikin idanunta, dauke kai yayi da sauri he don't really know abinda ma zai cemata, ko 1 single feeling baidashi akanta, ganin baice mata komi ba yasa cikeda son janshi zance tace "waye best friend din naka cikin wayan nan da kazo dasu?" ahankali yace "bayanan, this are my siblings" murmushi tayi tareda lumshe ido tana bala'in son jin yana magana, maganan shi dadi sosai wlh, voice dinshi bala'in dadi, murmushi tayi tace "yana ina shi? Maisa baizo tareda kaiba?" dan dagokai yayi ya kalleta suka hada ido sanan yace "I left him in the office you will see him later" gyadamai kai tayi cikeda sonshi tace "kayi kyau sosai" dauke kai yayi yace "thanks" yadanyi shiru saikuma yace "you look beautiful as well" wani irin cikakken murmushi tasaki cikeda jin dadi sosai tace "nagode Dr" sukai shiru, agogon hannunshi ya kalla sanan yadago kai ya kalleta hada ido suka sakeyi dan idanunta na kanshi har lokacin, hannunshi yatura cikin aljihu yaciro duka rapan kudin daya taho dasu ya ijiye mata akan cinya yace "use it for anything you need, will see you later" gyadamai kai tayi ya mike tsaye tashi itama tsaye tayi itama batai wata wataba tafada jikinshi ta rungume shi tsam tsam murya chan kasa tace "thank you Dr, sai anjiman kaji" sanan tasake shi da sauri yajuya yafita daga dakin batare daya kalleta ba yafita daga gidan. [11/1, 11:42 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 3️⃣ FREE PAGE Wuraren 4 yafito daga office dinshi ko kallon office din Waleed baiyiba yasauko yay wajen hadaddiyar motarshi ya shige yaja motar yadau hanyar barin gidan marayun, agaban wani gida dan madaidaici mai kyan gaske yay parking ya sauko, shiga gidan yayi yabude gate din sanan yakoma mota yaja motar zuwa cikin gida, parking yayi sanan yafito yaje yamaida gate din ya kulle yana bin tsakar gidan da kallo dayasha flowers ga interlock akasa dudda gidan baida wani girma sosai but yanada kyau, karasawa yayi ya shiga flat babba kwara daya da shi kadaine atsakar gidan, bude kofa yayi ya shiga falon da babu kowa ciki sai TV dake aiki gawasu hadaddun setin kujeru dasuka zagaye falon suka karama falon haske da kyawu, wucewa yayi ya shiga wata yar corridor da dakuna uku ke ciki, ahankali yake tafiya har yakai gaban dakin dashine last room din corridor yabude kofar dakin ya shiga, dakine mai kyau sai kamshi yake, ga Royal bed aciki sai kujera daya 3sitter komi na dakin fari harda curtains din dakin, wani babban frame na hotonshi ne ajikin bango, rage kayan jikinshi yayi yawuce yashiga bathroom din dake cikin dakin, wanka yayo yafito ya shirya cikin wata yar 3quater da farin singlet yazauna kan gado, wayarshi dayaga tana dan kawo wuta yasa yagane anyomai message, mika hannunshi yayi yadauki wayar ya danna, sako yagani daga Waleed. "Where are you My P.A🤣?" yay emojin dariya agaba alamun tsokana yake, tsaki Arham yayi ya cillar da wayan yay kwanciyar shi akan gadon tareda lumshe idanu yana sauke ajiyan zuciya. "Arham" muryan wata yar dattijuwa ta kwalamai kira, "Arham" aka sake kiran sunan nashi ana bude kofar dakin gabaki daya, bude idanunshi yayi dasuka dan chanza launi dan bacci yasomaji, wata mata ce da a kalla zatafi fifty ta shigo dakin tana sanye da doguwan rigan atampa dayasha stone work hannunta rike da charbi, tsayawa tayi chak ajikin kofa tana kallonshi cikeda mamaki ganinma bacci yasoma yi shida keda biki saikuma tace "ka shigo gidan kafi karfin ka shigo ka gaidani ko Arham" murmushi yayi na rashin gaskiya yana kokarin tashi ya zauna yace "yakuri Umma, danaga baki falo nasan kina ciki kina salla saisa nayo dakin straight dannai wanka, inayin wankan kuma shine na kwanta" gyadamai kai tayi alamun ta gamsu da bayanin shi tace "yana ganka adaki kaida yakamata kana tareda Waleed yanzu, banma dade da dawowa daga gidan nasuba munata yan aikace akace achan" shiru yayi baice mata komiba, hakanan ranta yabata wani abu ganin yasauke kai yasa tace "kai ba magana nake maka ba" juyowa yayi ya kalleta cikeda takaici yace "bazani bikin ba yaje yay bikin shi shikadai su Abdul samai komi" yanda yay maganan yasa Umma ta shigo dakin da kyau tayo kanshi tace "me kake cewa ne haka? Wai Arham maisa kai gabaki dayanka bahaggon mutum ne eh? Kadaisan Waleed bazai taba iya komi batare dakaiba ko? Kakuma fi kowa sanin cewa duk duniyan nan Waleed baida aboki saikai ko? Kana cewa su Abdul, wani irin su Abdul abinda zai fadamaka comfortably bazai taba gayama su Abdul kannenku ba, Arham abokin ka kokuma ma nace dan uwanka dakuka taso tare yau bikinshi shine zaka juyamai baya eh?" daure fuska yayi tamau baice komiba, ganin da gaske fushi Arham yake yasa ta zauna ahankali gefenshi, hannunta tadaura akanshi ta shafa kan ahankali cikeda lallashi kafin ahankali tace "maiya hadaku Arham? Kuda komu iyayenku bamu isa muji tsakanin kuba shine yau kakeso ajiku, maiya hadaku tell me" shiru yayi kaman bazaiyi magana ba saikuma yace "Umma Waleed is rude, very rude, yana controlling dina anyhow, yau ya shigo office so moody shine....." harya gama bama Umma labarin kallonshi take saikuma tai murmushi tareda sauke ajiyan zuciya tace "Arham nasha gayama ka chanza halin nan nak......." cikin fushi yace "dama nasan side dinshi zaki dauka saisa banso na gayamiki bama, nasan u will always support Waleed sabida sunada kud....." wani mugun kallo da Umma tamai yasa yakasa karasa maganan yasaukar da kanshi kasa yana wasa da yatsu, ahankali tace "Arham harga Allah am not happy da wanan dabi'un naka, abu kadan kadauke shi da zafi, Arham do I need to explain yanda yaron nan yake sonka? Saina fadamaka? Kaida bakinka kasha fadan Umma Waleed nasona, Waleed na sona, Arham akwai abinda Waleed baima aduniyan nan ba? He saw u on the street kana 7yrs old kana tallan ayaba, yaron nan kullum saiya fito yabika kuje ku saida ayaban tare kudawo, tun iyaye basu saniba har suka sani, Arham yaron nan Allah ya jikan mahaifinshi, Allah yakai haske kabarinshi saida yasa mahaifinshi by fire by force yasaka a school din dayake the biggest school a Abuja then, Turkish, adaukeku a mota adawo daku a mota, Arham kadawo dan gayu, kuka gama yasa kuka tafi same University a kasan waje ka karanta business administration shikuma medicine, baitaba aboki ba cus yasha fadamin Umma Arham is my everything, Arham is my blood, Arham is my this and dat, yaron nan kome zai saya kome za'a sayamai agida in ba'a sayo nashi da nakaba bazai karbaba, yaron nan bought this house for me, yasaimin car, handling everything that has to do with me, every end of the month saiyayo min har gobe dudda na nunamai yanzu kana aiki kanada kudin yimin komi but yaron nan yaki, yabaka job a inda yake shima, he carry u along a komi, in yananan he want to see u awurin with him, he did everything for us and look I will forever be grateful to Waleed har karshen rayuwa ta, dabadan Waleed ba da Allah kadai yasan inda muke yanzu maybe muna kwana a kasan gada, ankoremu agidan haya" tai dan shiru tana sauke ajiyan zuciya sanan ta nisa tace "menene aibun fadimaka dayayi cewa lokacin office lokacin aiki ne bana firan abota ba eh? Kowa dake da any dangantaka da Waleed yasan the way his world revolve around gidan marayun nan, kafi kowa sanin irin soyayyan dake tsakanin shi da mahaifin shi, bayan rasuwan shi yabude gidan marayun da sunan mahaifin shi, gabaki daya soyayyan dayakema mahaifin shi yay transferring nashi to gidan marayun ne, Arham idan Waleed wants to do good I think u should be the number person dazai bashi support, banda haka just take a look shima yadamu yana ganina agidan yazo wajena ya tambayan kadawo nace bansani ba, yamaka text kakimai reply, Arham karage zuciyan nan dan Allah karage, yanzu tashi kaje ka shirya katafi he needs u komi na hannunka kaji?" gyadamata kai yayi ahankali, dan murmushi tayi tace "right from day one Waleed has been a rude person but ahaka ai ka kawomin shi Umma ga abokina remember? Ka girmeshi yakamata ace kayi amfani da hankalinka and understand him better than anyone, babba babba ne yarona" dariya yadanyi hakan yasa tace "ko kaifa I sauri ina jiran ka a falo" gyadamata kai yayi tawuce tafita shikuma yatashi ahankali zaiyi wajen wardrobe dinshi wayarshi tadanyi kara juyowa yayi yadawo wajen yadauki wayan yabude sakon da sauri ganin Waleed ne. _"okay okay, I get it, you want me to say those words right? Sorry blood I know I was rude dazun nan but hey! Don't put too much pressure on me I might break, Ammi ne tamin fada dazu da safen nan but I am sorry for taking it out on you, please kazo su Hasim are driving me nut am about to loose it_ Dan murmushi yayi ya ijiye wayan batare dayamai reply ba yadauko wata bugaggiyar farar shadda ya saka dan akwai kayan dinner dazusu saka anjima da night ya feshe kanshi da turare, sanan yadau makullan motan shi yafito, tuk kafin ya iso Umma ta kafe kofar corridor da ido fitowa yayi hakan yasa ta murmusa tace "abokin ango da kanshi, agama nashi dakafana zanje wajen Ammin Waleed dama ita ke goyamaka baya wlh kokai aure kona bama wanan bazawaran datazo takanas tafadamin tana sonka dan kaji" dariya yayi yace "habadai Big boy irina zaki sadaka dashi Umma" dariya dukansu sukayi tace "dalla bacemin daga gani nisai kuma gobe in Allah yakaimu zan koma gidan" "alright bye Umma" "bye" tamai waving hand yana fita daga dakin, motan shi ya shige ya zauna ya kunna motar sanan yafito ya bude gate yana tunanin yakamata yadauko mai gadi fa fa fitar da motar yayi waje yadawo ya kulle Gate din sanan yadau hanyar gidansu, dayake Umma tariga tafadamai ta bayan layi shima ya zagaya yay parking akofar gidan sanan ya kashe motan yafito yana tafiya dai dai yabude Gate ya shiga gidan, tundaga tsakar gidan wajen yakejin hayaniyan su Hasim girgiza kai kawai yayi yabude kofan ya shiga falon duk waigowa sukayi suna kallonshi, harara ya watsa musu hakan yasa suka fashe da dariya Hasim yace "ga best man din ango nan ya shigo, iyye see the glow" da hannu ya nunamai kunnenshi hakan yasa da sauri Hasim yace "tuba nake Ya Arham" barin falon yayi yadauki hanyar bedroom dinshi ahankali yabude kofa dakin nashi daga Mom har Waleed din datakai spoon bakinshi danya karbi abinci juyowa sukayi suka kalli kofan, ganin Arham ne yasa Mom tasaki wani murmushi, dauke kai yayi daga kallon Waleed din dayadan murmusa kadan ganinshi sanan ya karasa gaban mom yadan rage tsawo cikeda ladabi yace "ina yini Mom" cikin wani irin jin dadi Mom tace "lpy lau Son, barka da zuwa, Allah yamaka albarka kaji, ina yawan fadama abokin ka ai duk duniya bazai taba samun aboki mai amana irinka ba ga girmama nagaba dashi, uwa uba ga kunya, kai Allah dai yabarku tare, kadinga hakuri da halin Waleed, dabi'un Waleed sai du'a'i jinshi yake kaman dan shekara biyu kagafa yanzu abincin nan wlh inda ban bashiba da bayici, ai nagode ma Allah yanzu zaiyi aure nahuta daman Adda tace ninenan nabata shi" tai maganan tana tallo keyanshi, yi yayi kaman zaiyi kuka saikuma yatashi ashagwabe yayi hanyar kofa da sauri Mum tace "ina zaka?" ahankali cikin yanayin maganan shi kaman na wanda yagaji yace "ni ruwa zan dauko" yana fadin haka yawuce yafita, ajiyan zuciya Mom ta dauka sanan ta maida hankalinta kan Arham dahar lokacin bai tashi daga gabanta ba tace "Arham nasanka yarone mai hankali da sanin yakamata ga abokin kanan kacigaba da sashi a hanyar kwarai, kacigaba da hakuri dashi, ka girmeshi, Waleed is still a child kawai girman jiki dayake da shine yasa a kemai kallo kaman wani babba but har yanzu baikai 30ba kaima kasani, Arham always watch his back kaji dan Allah, kafishi wayau always guide him for us kaga shi kadai garemu, Allah muku albarka dukanku, bari kaga nakoma cikin gida in yazo ga abincin shinan kasashi yaci kasan matsalan shi na Ulcer pls, Ulcer shi yatashi batamai da kyau" gyadama Mom kai yayi ta tashi tawuce tafita, tashi yayi ahankali yana kallon hadadden bowl din da pepper soup din fish keciki ga plate na white rice da spoon komi anjera kan tray, girgiza kai kawai yayi yanabin ko ina nadakin da kallo kafin ahankali yadaga kafarshi yay gaban mirror dakin yana tafiya ahankali, tsayawa yayi yana kallon turarukan wajen, hannunshi yamika ahankali yadauko wani da shi kadai ne baisaniba cikin turarukan wajen mai suna "Men of Chastity" ya shiga jujjuya turaren yana kallo kaman mai wani tunani, bude kan turaren yayi yafesa kadan ahannun subhanallah saida ya lumshe ido tsabagen dadin kamshin, bude kofa da akayi yasa yajuyo da sauri rikeda turaren a hannu, Waleed ne ya shigo rikeda bottle water a hannunshi maidan sanyi, binshi yayi da kallo kafin idanunshi su sauka kan turaren da Ammi tabashi jiya as gift, dan murmushi yayi ya shigo dakin yace "wanan turaren kake kallo, Ammi tabani shi jiya da daddare gift, gama kwalin shi nan kasa dazun nan nabude shi" yamai pointing wani hadadden kwali dakenan kusada kafarshi ja akasa a ijiye, tsugunnawa Arham yayi yadau kwalin yadaura kan mirror sanan yabude kwalin ahankali, kwalin kadai abin kallo ne, har zai rufe kwalin idanunshi suka sauka kan receipt din turaren dake cikin kwalin idanunshi suka sauka kan kudin turaren 2.8m, da sauri yace "wanan turaren ne 2.8 million X-man?" batare daya kalleshi ba Waleed ya sauke goran ruwan dake bakinshi yace "eh kaima kaga bai tsada bako?" yafada yana daukan plate din rice trying to see in zai iyaci da kanshi dan bai koshi ba, sosai Arham ke binshi da kallo yama kasa magana he just wish inama ace shine dandan Ammi shikuma Waleed dandan Umman shi, Waleed dan gatane da baitaba ganin irinshi ba tarairayan shi ake kaman egg, bai dauki kudi anything ba sabida yanada su in excess ma, kaman ance yajuyo yajuyo gani yayi har lokacin Arham kallon turaren yake yamayi nisa a tunani dan murmushi yayi yamaida kanshi kan abincin yace "take it blood" maganan shi yadawo da Arham daga duniyan tunani yace "take wat?" cikin halin ko in kula yace "the pef" da sauri Arham yace "are u crazy? Ammi tabaka gift ne zaka wani ce nadauka" murmushi yayi yana chakalan abincin yace "ai itama tasan everything two ake saimin me and u maybe ta manta ne tasayo just one this time around, anyway take it will order akawo min wani" wani irin murmushi Arham yayi yataho wajen da sauri yadan bugi kafadar shi yace "thank you ango, angon Ilham" dagokai yayi ya kallai tareda ballamai harara hakan yasa Arham yace "to me dalla, common chill, dan gatan Ammi I know yanda Ammi ke sonka dinan will choose the best girl for u, a princess kaman yanda kake a Prince to this family yar gata irinka" tabe baki yayi yatashi yace "nidai mutafi mosque" tashi Arham din yayi suka wuce suka tafi masallaci sallan magrib. [11/1, 11:44 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 4️⃣ FREE PAGE Direban gidansu Arham yatura dazasuje su dauko Amarya da kawayen ta to the event centre cus 9 za'a fara dinner dasu Hasim da friends dinsu, saida ya tabbatar sun tafi sanan yakoma cikin gidan, Waleed yasamu azaune kan kujera yana aiki da laptop dinshi ko ajikinshi kaman ba shine angon bikin ba, maida kofan Arham yayi yarufe ya karaso cikin dakin tsayawa yayi chak akanshi yace "muje ka shirya mutafi ai ba'a office kakeba yanzu kana gida" dan dagokai yayi ya kalli Arham din wata yar gajeren tsaki yaja yace "Omg wai why did u initiate this dinner stuff at the first place ma eh? Goddd! Mutum cannot rest again yayi abinda yakamata, am so so sick of this wedding, gosh!" girgixa kai Arham yayi ganin yanda yake masifa bil hakki ya karbe laptop din tareda shutting nashi down yarufe yarike ahannu sanan ya mikamai hannu yace "muje mushirya" ahankali yatashi Arham yabishi da kallo yana sanye da faran t-shirt sai wani 3quater short daya tsayamai wajajen gwuiwa shima fari, kafafunshi sanye cikin farin bathroom slippers, gashin kafarnan kwance lub lub irin na mugun dan hutun nan. Ahankali kaman wanda kwai yafashe wa aciki yake tafiya Arham yabude kofar hadadden bedroom dinshi suka shiga ciki, wajen wardrobe dinshi yayi yafito dawasu kaya da bama abude ba yazube su kan gadon sanan yabude ya shiga shiryawa cikin wata white suit na ermenegildo zenga, suit din yamugun fitting nashi daga kasan waje akamai order suit din aka tahomai dashi, sanan yadauki cover shoe dinshi na dinner sabo fil Black, designers shima na Testoni, tsayawa chak Arham yayi yana kallonshi yamugun yin kyau sai kallon kayan yake, juyowa Waleed yayi ya mikamai bow tie din dake hannunshi yace "tayani sawa blood" karban bowtie din Arham yayi yashiga samai kaman ba zaice komiba saikuma yace "amman wanan takalmin da suit din bashi mukaje muka sayo tareba a dunes ko?" girgiza mai kai yayi yace "Uncle yazomin dashi daga Ukraine jiya daya iso" gyadamai kai Arham yayi baisake cewa komiba yana gama samai yawuce yaje wardrobe yaciro wayanda suka sayo tare, yazaro tashi suit din black, dan abokan ango black suit zasu saka shikuma ango white, ya shirya tsaf sanan yataho key motar Waleed ya dauka yace "let's go" fitowa sukayi daga dakin, har zasu fita daga falon Ammi ta shigo dakin sun kusan cin karo, binsu tai da kallo yanda suka mata kyau sosai kafin ta sauke idanunta kan Waleed dayay mata wani irin kyau batasan lokacin data saki wani kayataccen murmushi ba, wucesu tayi tazauna kan sofa sanan takalli Waleed tace "zonan Son" tahowa yayi ahankali kaman wanda baison tafiya yazauna kusada ita inda take nunamai, hannunta takai tai cupping face dinshi tana kallonshi kaman yau tafara ganinshi kafin ta shafa fuskar tace "you look so much like your father today, kayi kyau sosai, Allah ya maka albarka kaji" dan lusme ido yayi yana danne abinda yakeji a zuciyan shi yace "Ameen" purse din data shigo dakin dashi ta ijiye agefenta tadauka tabude taciro rapas nayan dollars guda biyu tamikamai tace "gashi kama y'ata manni dasu" karban kudin yayi ahankali dan baiso yaki karba taji haushi, rungume shi tayi ahankali taredamai kiss akumatu tace "stop being sad, I love you son, kaci abinci kuwa?" juyawa da sauri Arham yayi yafita daga dakin ya shiga mota Waleed din yay zamanshi a mazaunin direba, he just wish inama shine Waleed, kome zaiyi iyayen shi basa tabamai fada komin girman abun, unlike him da kullum abu kadan Umma fada takemai, abu dan kankani sai fada, Waleed ko abinci ma abaki ake bashi, bodyguard ma saida sukai fada da Ammi sosai dan anso kusan 10 sudinga binshi da kyar ya karbi daya wanda yadawo direban shi, bama abari yasha wahalan neman mataba aka samomai yar gidan masu kudi, graduate lawyer fa dudda dai bai taba ganinta ba aka bashi, just look at suit din da uncle dinshi ya kawo mai daga Ukraine, suit din ermenegildo yana costing about 22 to 28000 dollars, suit din jikinshi kadai worth a fortune dan yakai almost 8.8million naira a kudin Nigeria, takalmin kafanshi na Testoni kusan 3m ne shima, gata da dadi is beyond tunanin kowa ko shima inda bai gani da idanunshi ba dabazai taba yarda ana bama yaro gata irin gatan da ake bama Waleed ba, why was he born from the poor home? Maisa Umma ta auri Abban shi wani Malam Muhammad Bala, malamin islamiyya? Yataso ko gidan kansu basuda shi sai gidan haya, gidan dakuna ashirin da biyu da bayi guda biyu daya na kashi daya na fitsari, daga baya kuma yazo yarasu ya barsu cikin talauci, Waleed ne ya shigo rayuwan shi ya chanza mai komi..... Bude motan da akayi yadawo dashi daga daga dogon tunanin dayaje Ammi ne tabude ma Waleed din kofar motan tana kallon Arham tace "son ina gajiya" cikeda kunya dan yafi sakewa da Mom sabida ita tanada raha sosai while Ammi batada raha tanada fada, bata cika wasa da yaraba, aduniya in tana tareda Waleed ne kawai zaka dinga ganin dariyanta da murmushi ta abanza, da farkoma ya dauka bata sonshi ne sai daga baya ya lura haka Allah yayi ta ita kawai bamai yawan wasa da sakema yara fuska bane, cikeda girmamawa ya sauke fuskanshi yace "ina yini Ammi, ya taro" tana kokarin saka Waleed dake mata wani shegen shagwaba a mota tace "Alhamdulillah Arham, ai tuntuni muna tareda mahaifiyarka ma wlh, mamanka akwai kirki, kaga Arham gashinan drive him safe please, saikun dawo, bye Son, have fun okay, if u need anything ka kirani zan aikoma dashi" ta shafa kan Waleed din dake tura mata baki tana murmushi, kunna motar Arham yayi yaja Ammi na daga musu hannu tana murmushi, saida sukadan yi nisa ahanya sanan ya kalli Arham din dayaga yay shiru kuma ba halin shi bane yamika mai rapas din dollars din da Ammi tabashi duka biyun yace "use this" da sauri Arham ya kallai saikuma ya maida kanshi kan tukin yace "a'a, abinda Ammi tabaka zan karba" murmushi yayi kafin ahankali yace "take it inada wanda zanyi amfani dashi already" "shikenan" Arham yafadi ahankali kafin yace "thanks blood" murmushi Waleed yamai baice komiba, ahaka har suka karasa event centre babu wanda yakara magana cikinsu, daman yawanci in suna tare Arham ne mai kawo hira shi Waleed iya kanshi um a'a kokuma yan maganganu kadan, parking yayi yace "ka zauna aciki, I need to confirm in Amarya ta iso dan tare zaku shiga Hall din" bai jira amsanshi ba yamaida kofan yarufe yay wurin entrance din daidai zai shiga Abdul suna saukowa daga elevator tareda Salima suna hira shiru sukayi ganin Arham, Salima tace "you must be Arham ko? Best friend na ango" dan murmushi Arham yayi yana binta da kallo tana sanye cikin asshobi kawayen Amarya pitch yace "yeah nice to meet you Mss Salima" murmushi Salima tayi tana kallonshi ganinshi shima kyakkyawa sosai saidai dudda kyanshi baikai kyawun Dr ba, kuma Dr yafishi kaurin jiki da cikama mutum ido, ganin kallonshi take yasa ya katse shirun yace "ina Amarya? Cus they're going in together" "eh tana wani daki asama where is Dr?" juyawa yayi yace "lemme get him" har wajen motan yaje yabude motan ya kalli Waleed dake dandanna waya yace "let's go ango" ballamai harara Waleed yasakeyi hakan yasa Arham yace "sorry mana ai kuma gaskiya nafadi kai angon ne" ahankali Waleed yafito yana gyara suit din jikinshi su karan kansu su Abdul da Salima kallonshi suke yawani irin yin mugun kyau cikin white suit din dasukai mugun fitting dinshi maida kofar Arham yayi yana kallonshi yace "muje" ahankali suke tafiya har zuwa gaban entrance din Salima takasa daina kallonshi, dan kallonta yayi sanan ya kalli Abdul batare dayace musu komiba, anatse Abdul yace "sannu da zuwa Ya Waleed" bai kallesu ba yacema Arham dake kusadashi "let's go" wucewa sukayi dukansu suka shiga lift din yakaisu 4th floor, wani daki Salima tabude tana kallon Arham dan Waleed mugun cika mata ido yake tace "ku shigo tana nan" shiga ciki tayi suka hada ido da Ilham datasha uban gayu anmata makeup tasaka wani gown white daya mata fitinannen kyau ita kadai zaune kan wani Royal chair tai kyau sosai, cikin tafiyan nan nashi mai daukan ido daidai ya sawo kanshi cikin dakin Arham biyeda shi abaya, ahankali ta mike tsaye tana kallonshi hada ido sukayi hakan yasa ya tsaya chak shima, wani irin dadi ne ya lullubeta batasan lokacin data saki murmushi ba da sauri tazo wajenshi batai wata wataba tafada jikinshi ta rungume shi, ihu dakin ya dauka Arham ya shigo dakin da kyau yana kallonsu yana murmushi, da sauri Salima taciro wayarta tafara musu hotuna, ahankali yadaga hannayenshi ya rungume ta back, wani irin ajiyan zuciya ta sauke ta shige jikinshi sosai tana shakan kamshin dayakeyi, kaman ta jawo gobe takeji ayi a daura musu aure tayi ta dawo matar this ajebota handsome rich kid, "wai anan zamu kwana ne" Abdul yafada yana dariya, ahankali tasake shi cikeda jin kunya hakan yasa shima ya saketa, juyawa tayi suka hada ido da Arham da tundazu yake kallon bayanta Allah Allah yake yaga fuskarta, dan murmushi tayi sanan tajuya ta kalli Waleed din, dan lumshe ido yayi yabude kaman mai rada yace "my best friend, my brother, my blood, Arham" wani irin murmushi tayi ta juya ta kalli Arham tace "the great Arham nasha jin labarin ka tun abakin Ammi, my husband best friend childhood friend, so nice to meet you" dan murmushi Arham yayi yakasa daina kallonta yace "yes your husband is my blood we've been together since childhood, and he means the world to me, so ki kula min da abokina dakyau" dan dagakai tayi ta kalli Waleed kafin ahankali takama hannunshi tarike gam tana kallon face dinshi tace "I was born to do that, I love you so much Doctor na" ganin akwai mutane awajen yasa ahankali yace "thanks" wani iri Arham yaji he just feel inama shine yake da wanan soyayyan, Waleed is the definition of yaran da ake haifa da silver spoon abakin su, Waleed is just surrounded with love ne ta ko'ina, just look at yanda wanan hadaddiyar classic graduate lawyer yarinyar nan kesonshi tama mutu akanshi but yana yanga, infact baima sonta, baima son auren ko kadan, yarinya ga shegen kyau, itama yar masu kudi but yake yanga, he just wish zai sami yarinya haka dazata dinga mutunmai dinan, Salima ne ta katse silent din tace "I think we should go anfara event fa tundazu" fitowa sukayi duka atare, bayan an sanar da isowansu a hall aka kunna music suka shiga cikin kasa ita sai hotuna ake musu, sosai akai event kala kala duk in Ilham zata dagokai saita hada ido da Arham dake kallonta saidai ta sakanmai murmushi ta maida hankalinta kan Waleed, anso sai asuba za'a tashi 1 nayi Waleed kaman zaiyi kuka yakira Arham awaya bai dauka ba, ganin duk yay wani iri yasa Ilham tace "me kakeso baby?" batare daya kalleta ba murya chan kasa yace "nagaji i think atashi" ayanda yay maganan saida yasa har wani lumshe idanu tayi, Waleed is handsome gawasu mayun pink lips dayake dashi dake shinning kaman ka lashe, she can't wait to have a taste of them, kasa cemishi komi tayi sai binshi take da kallo, ganin kiss call dinshi yasa Arham yazo gayamai yayi atashi yagaji bacci yakeji, Arham baimai musu ba ya sanar da dj a kunne, yan abubuwa kadan akayi aka tashi, dudda yanda Waleed keso yaje gida Arham yace mai ba haka akeba shizai raka Amarya gida sanan saisu tafi, yanaji yana gani Arham yasa aka saka Amarya a bayan motansu yasa Waleed din kusada ita sanan yakoma gaba ya shiga ya tukasu, sun danyi nisa da tafiya Ilham ta matsa kusadashi ahankali tareda saka hannunta kan nashi ta kama gam, shiru yamata yana dan lumshe ido kafin daga baya bacci yay nasa ran kwasheshi ya daura kanshi kan kafadarta, wani irin dadine ya kasheta tai dan murmushi tace "haka abokinka keda saurin bacci?" ta glass din gaban motan ya kallesu yay dan murmushi yace "ai zakisha shagwaba, haka Allah ya yishi, mijinki shagwababbe ne" murmushi tayi ta shafa fuskarshi bata sake cewa komiba shima Arham haka har suka kai gaban gidansu, ahankali ta gyaramai kai tareda pecking nashi ta kalli Arham daya bude mata mota tace "good night our blood" murmushi yayi yace "good night our wife" gyadamai kai tayi tawuce yamaida kofan yarufe yana dan satan kallon bayanta, ta shiga gidan su, dakinta tawuce direct inda Salima da wata kawarta suke zaune harsun chanza kaya dansu tun dazu suka iso itakuma dayake ahankali Arham ke gudu saisa basu iso dawuri ba. [11/1, 11:44 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣ _*This novel is for free. Wanda mu Kungiyan FREE HAUSA NOVELS WATO BANZA *ASSOCIATIONS* muka dauki nauyin kawo maku. Page 6 *_MOHAMMED V INTERNATIONAL AIRPORT, MORROCO._* Karfe shida na safe daidai jirgin British Airways ya sauka a airport din Mohammed VI, sai kataniyar saukowa passinger suke daga cikin jirgin kana ganinsu kasan they're all stressed out sun gaji iya gajiya, saida kusan kowa yagama saukowa daga cikin jirgin sanan ahankali wata yar doguwan matashiya tasawo kanta tawajejen kofan zata fito tana goye da jakar makaranta abayanta tarike igiyoyin gefen jakan gam da hannunta, farace sol yarinyar tana sanye da wata bakar doguwan riga mara kwalliya ko daya ajiki jallabiya, sai gyalen ta datai rolling aka sai abin yay kaman hijabi dudda hakan bai hana bakin suman gaban goshinta bayyana ba sun mugun kwanta sunyi lublub kaman na yar jaririyan da aka haifo yau, tanada manyan idanuwa fararen fat da brown kwaiduwan ido dan ko kadan nata ba bakake bane brown nesu light brown, giran ta full da gashi baki mai shining kaman ta sakamai relaxer, gawani siririn dogon hanci daya ratsa tsakiyan fuskanta ya bala'in karamata kyau, lips dinta pink yirr yan fele fele kananu kaman na yaron da aka haifa yanzu yanzun nan. Sake rike igiyan jakan datake goyedashi tayi gam, ahankali ta lumshe ido iskan garinsu yawani kada mata fuska tasaki murmushi daya lotsar da dimples dinta na both sides, dama da haggu sun lume chan ciki sosai kaman rijiya tai wani irin kyau da ba'a iya misaltawa sanan tabude idanun ahankali kafin tadaga yar kafarta tafara saukowa daga kan matattakalan jirgin tana kallon ko'ina ganin bataga yan gidansu ba daidai da mutum dayaba yasa taji wasu hawaye sun taho mata masu dumi, ahankali takai hannunta kan fuskarta zata share hawayen kaman daga sama taji an kwalamata kira. "Widad! Widad!" wani irin juyawa tayi da saurinta, wata mata tagani ita kadai tadan manyan ta sosai dan akalla zatafi 70 yar tsohuwa ce tana sanye da doguwan riga itama da hijabi daya tsaya mata aciki tana tahowa da dan sandanta a hannu, wani irin tsalle yarinyan tayi hawayen suka karasa zubowa cikeda murna cikin harshen larabci tsohuwan tace "ahlan wa sahlan wa marhababik Widad" cikin wani irin muryan kuka yarinyar da tsohuwar takira da Widad tace "Assalamu Alaykum Amah" holding shoulders nata taohuwan tayi sanan tai kissing left cheek nata sanan tamata ana dama tana murmushi cikin tsantsan farin ciki da tsantsan so takara mata another peck a forehead tace "waallaykumus salam Widad, kaif? (how are you)" juyawa tayi tana kallon ko'ina na filin Airport din kaman mai neman wani abu tace "Alhamdulillah Amah" ganin yanda take kalle kalle yasa tsohuwar tai murmushi sosai batare datace mata komiba tabarta tacigaba da kalle kallenta, tana cikin kalle kallen kaman mai neman wani abu taji anrike mata hannu gam wani irin ajiyan zuciya ta sauke ta tsayar da kanta chak kafin ahankali lebbbenta suka furta "Ab.....Aby" dawani irin sauri ta juyo kaman amafarki, wani magidanci ne tsaye a bayanta yana rikeda hannunta yana sanye da jallabiya fari fat, kafanshi sanye da skos na maza, sai kanshi daure da rawanin larabawa sai farin gilas a idanunshi da daga gani kasan na kara karfin ganin idanune, kana ganinshi kaga tsantsan balaraben morroco kyakkyawa ajin farko, wani irin fashewa da kuka tayi haka Allah yayi ta tanada saurin kuka, very emotional mutum ce ita, sanan duk duniya batada wanda takeso kaman babanta saisa kodaga nesa takanji a jikinta yana kusada ita, fashewa da kuka sosai tayi tace "Abyyyy" anatse magidanci yasakin mata wani kyakkyawan murmushi yakai fararen hannunshi yadaura kan fuskarta ya share hawayen datake tass kafin yarungumeta ahankali yana bubbuga bayanta anatse irin na manya dinan cikin muryanshi na dattawa yace "marhababik, marhababik" sunkai kusan 5min tana jikinshi har lokacin tana sheshekan kuka sanan yadago ta, hannayenshi yasa akan fuskarshi yay cupping face dinta cikin tsantsan so yace "kidayra? (how are you)" ahankali tace "Alhamdulillah Aby" gyadamata kai yayi yace "masha Allah" yanuna mata mutanen dake tareda shi alamun ta gaidasu, ita sai a lokacin nema ta lurada su dazu mahaifinta kawai idanuwanta suka gane mata, yangidansu ne dan gidansu family house ne babban gaske, wata balarabiya dake kusada mahaifinta ta gaida ta hanyar cewa "Assalamu Alaykum Um" sanan ta kalli sauran tacemusu "Assalamu Alaykum" amsata sukayi ko wanne da murmushi kan fuskarshi banda matar dake kusada mahaifinta dako amsata batayiba, cikin harshen larabci mahaifin nata yace "mutafi gida" kasancewan ansan koshi waye agarin saisama aka bari suka shigo har filin jirgin yasa suna zuwa akaimata clearing komi suka shiga wasu manya manyan jeep farare sukai gida, itadai tana cikin na mahaifinta kusada shi sai matar data kirada Amah gefen ta, mahaifinta kuma na gaba da direba, sukabar airport din. Agaban wani babban tangamemen gida sukai parking, irin gidan nan da aka ginashi na usulin culture larabawa, an zagaye gaban gidan da flowers iri iri daban daban kalolinsu kaman kazo ka kwasa ka gudu, tun kafin tafito daga cikin mota takejin sautin ganga na mandiri ana bugawa ana wake, murmushi tayi ta kalli mahaifinta cikeda so duk lokacin dazata dawo daga school sai Aby yahada mata walima na kayatarwa daban mamaki dan tarbanta kadai, bude kofa tayi tafito sanan tamikama kakanta hannu tafito daga motan Aby yafito yana kallonsu, kowa ya sassauko daga cikin motar akai cikin gidan, babban compound ne da girman tsakar gidan zaiyi girman primary school ana raye raye ana wake ana, ana rawa, ganin Widad din da iyayen ta sun shigo yasa mawakin yataho gabansu da yan amshin shi suna buga mandiri suna rera wake yace "kaifa Anti? Wa kaifa ji'iti? Marbabiki Ya Widad binti Othman Benjalloun" wani irin murmushi tayi ta washe fararen hakoranta tana kallonsu tana kara rike igiyan jakan makarantan ta abubuwa like this nabata peace sosai yanasa tana tunawa da mahaifiyar ta, ahankali mahaifinta ya kalli fuskarta murmushin dayagani kwance kan fuskar yasa yaji hankalin shi ya kwanta sosai, flowers ya karba a hannun daya daga cikin ma'aikatan gidan sanan yazo ta gabanta yabude flower ya sanya mata flower a wuyanta cikin harshen turenci dakeda Arabic intonation yace "wercome bark homer Widad" rungume mahaifinta tayi tana murmushi sosai tama kasa magana, ganin abun nasu bamai karewa bane yasa Amah cikin harshen larabci tace "to mayyar mahaifinta tadawo fa yanzu mun shigesu, saki ubanki muje daki kiyi wanka kizo ki chanza kayan nan kizo kici abinci ki kwanta kiyi bacci" Amah tai maganan tanajan hannunta, binta tayi tajuyo tama mahaifinta waving hannu sukai cikin gida, dan murmushi mahaifinta yayi yajuyo ya kalli matarshi datai kini kini darai cikin harshen larabci yace "kawomin shayi dakina" yay maganan tareda wucewa yashiga wani wakacecen falo irin traditional falon larabawan nan namasu kudin gaske, babu kujeru adakin sai wasu irin filulluka hadaddu set set da ake kishigada akansu gawani wargajejen hadadden carpet daya zagaye ko'ina a falon sai uban laushi kaman da fatar jarirai akayi sai shisha pot asalin pot din na larabawa, dan daidaikun asalin gidan rikakkun balarabe ne zakaje da bazaka ga shisha pot a dakunan su ba. Othman Benjalloun dattijo ne dakeda shekaru 62 aduniya, bala'in mai kudine agarin morroco, agabaki dayan garin ance bayan Mohammed VI wanda yake number 1 mai kudin garin, Othman shine the second richest person in the whole morroco, yana harkan banking insurance, yanada bankuna yanada kasuwanci da dama, matayenshi uku aduniya, Mahaifiyar Widad itace ta farko wanda a yanzu ta rasu, sai matarshi da biyu wacce Widad takira da Umm, sai ta ukun wacce yasaka sabida cutar da Widad datasoyi Allah ya tona mata asiri, yarshi daya aduniyan nan tal Widad, Allah baitaba bashi haihuwaba sai akanta, itama din harya cire rai dan yaga yay mata uku duk shiru yace halan daga shine sai kwatsam ga mahaifiyar Widad da ciki, yakusan karaman hausa a lokacin daya gane tanada ciki saisa da aka haifamai mace saiya radamata suna WIDAD ma'ana love, yana bala'in son yarinyar so mai zafi, gashi kana ganin yarinyar kaganshi kaman yay kaki, ko office zashi da yarshi da mahaifiyar ta yake zuwa sabida yadinga sata a ido kodayaushe, indan tafiyan fitanshi daga gari ce ta taso saidai yadauki mahaifiyar ta da ita dan bazai iya nisa da itaba saisa itama yarinyar ta taso tana bala'in son mahaifinta, tanada shekaru 18 mahaifiyar ta tarasu daga ciwon kwana daya tal, Widad takusan hauka take mahaifin nata yafita da ita da kyar aka samu taji sauki aka dawo da ita gida tadinga kuka daga karshe taroki mahaifinta tunda tagama sakandire yakaita wata kasar tai University intana gida tunawa da mahaifiyar ta take sosai, da kyar da kyar saima dayaga ta kwanta tana ciwo sanan ya yarda yakaita Egypt yamata komi yasaman mata admission in datake karanta mass communication. Wani hadadden babban daki suka shiga itada Amah dake upstairs, dakin wakacece ne babba dayasha carpet tako ina mai bala'in kyau dan duk wanda yasan morroco yasansu da sana'ar kera carpet su sayar, gadaje biyune hadaddun gaske masu rumfa da aka zagaye da labulaye farare masu kyau acikin dakin babba da karamin gado, tun bayan mahaifiyarta ta rasu tadawo dakin kakanta da zama kakanta ne kadai takejin dadin zama da ita dan tana sonta kaman ne, jakanta tacire ta ijiye akasa sanan ta taka zuwa gaban wardrobe din dakin dan neman kayan dazata saka, Amah kuma ta ijiye sandarta agefe ta zauna ahankali kan gadonta tanabin bayan Widad din da kallo, shekara daya kacal dabata ganta ba amman saitaga ta chanza mata a ido sosai, dan murmushi tasaki tana tunanin Widad da aka haifa jiyane ta girma haka, batare da Widad tajuyo ta kalleta ba cikin harshen larabci tace "Amahh why are you smiling? Tunanin me kike?" tai maganan tareda juyowa hannunta rikeda wata jan kaftan dayasha ado kaman irin dogayen rigunan India, hararan ta Amah tayi tace "wuce kije kiyi wanka, favourite dinki nasa aka dafa tagine, rice da herbs saikuma flat bread" washe baki tayi ta yarda rigan hannunta kan gado da gudu tai bayi, kyalkyacewa da dariya Amah tayi tadauki sandarta tawuce tafita dan tabbatar da yan aikin sun jera komi a tsakiyan falon barinma wanda tasan yar jikallenta tafiso. Dan aikin datagani awurin yana ijiye plate dake dauke da dry fruits tacema "ina flat breads din danasa ku gasama Widad?" cikeda girmamawa yace "yanzun nan jibril zai karasa baking dinsu yafito dasu" zata sake magana taga Aby na saukowa daga sama shima da hannu tama dan aikin alamu daya wuce yabata wuri, da sauri yawuce bayan ya gaida Aby, saukowa daga benen Aby yayi yazo gabanta mahaifiyar tashi yace "Assalamu Alaykum Amah" "waallaikumus salam" ta amsashi tana zama, ahankali shima ya zauna gefenta yadau inibi daya yajefa abaki yanadan bin wakan da akeyi awaje cikin kwanciyan hankali, ganin yanda yake farin ciki yasa mahaifiyar shi takira sunan shi. "Othman" anatse yajuyo ya kalleta tareda ijiye inibin daya so jefawa cikin baki kan faranti, dan gyara zama Amah tayi da kyau kaman yanda shima ya natsu yana jiran yaji mezatace mai, cikin muryanta na tsofaffi tace "wace shawara ka yanke akan maganan damukai dakai jiya?" fuzar da iska yayi fuskarshi ya dan nuna damuwa yace "I don't know Amah, all I know for sure is bazata koma wanan makarantan babu aure akanta ba, ai nai mata kokari dana iya nabar y'ata wacce ita kadai ce Allah yabani aduniyan nan taje chan wani kasa tana karatu ba, banda hakama Amah bakiga yanda alamomin girma suka bayyana ajikinta sosai ba?" gyadamai kai Amah tayi cikeda gamsuwa da bayaninshi tace "nagani" yace "burin kowani mahaifin ya killace yarshi intana wanan matakin ya aurar da ita, na kashe all meetings danake dashi throughout this week, hutun sati biyu kacal gareta, nariga na sanar da iyayen Ahmad zasuzo anjima da daddare we are having engagement ceremony tonight, nikah zai biyo baya nanda sati in 7days time dudda a al'adance yakamata bayan engagement ceremony da shekara ne ake biki but I can't wait that long" ya karashe maganan ahankali saikuma yasaki dan murmushi mai kama data bakin ciki ya kalli Amah yace "Amah anya zan iya rayuwa kuwa in bana ganin y'ata?" yasakeyin murmushi hawaye na taruwaa idanunshi yace "Amah bantaba fadamiki wanan ba sabida nasan fada zakimin kice nabar yarinya tai concentrating a karatu kaza kaza kaza, kinkosan cewa ban taba kaiwa sati daya cur batare danaje Egypt ba dukko nisan shi?" ware ido Amah tayi cikeda mugun mamakin shi dan tasan dan danta business man ne yana yawan tafiye tafiye but bata taba sanin haka yake zuwa wajen Widad a makarantan ba frequently ba, one thing she knows for sure shine she always wondered ayanda Aby keson Widad kaman zaiyi hauka ya iya hakura hartai shekara a makaranta bai gantaba, maganan shi ne ya yanke mata dogon tunanin dataje yace "kinsan yanzu intai aure bazan iya dinga zuwa haka ina ganota bako" ya share hawayen dayadan zubomai da sauri yay murmushi yace "Amah banson ko kadan Widad ta wahala aduniyan nan, saisa nake aiki nake neman kudi sabida ita, dazaran na aurar da ita I believe lokacin tadawo cikakiyar mace, zanyi handing all over my properties, companies komi da komi nawa, all my assets to her ni zanyi retire na huta, shi will be managing everything, komi da komi dana mallaka nata ne Amah dan banda wani magaji aduniyan nan sai ita, I make sure nabata komi ranan da aka daura aurenta agaban mijinta da kowa, innai haka hankalina zai kwanta dan nasan tanada komi bazata taba wahala ba, yakika gani Amah?" kumatun shi Amah taja cikeda murmushi tace "brilliant thought, kasan I'm always proud of you Othman kai d'a ne nagari mai adalci, ina mai goyamaka baya dari bisa dari akan wanan hukuncin daka yanke, mu munriga munyi rayuwanmu aduniyan nan, munci duniyan mu da tsinke, mutuwa yauko gobe takan iya daukanmu, inhar bamu bama Widad da yanzu tafara girma komi damuka mallaka ba maimuka yi?" dan murmushi tayi tace "nima zinaruka na tunna lokacin aurena da mahaifinka, gabaki daya daman ita nakema ijiyansu ranan aurenta da izinin Allah zan bata, Allah yamaka albarka Othman Allah kuma yasanya ma auren albarka, na yarda da Ahmad sosai, nakuma san yanda yake sonta tun tana yar yarinya" dan dariya Aby yayi yace "kinsan mahaifinshi yacemin daya fadamai maganan engagement din danayi yakusan suma kinji fa yarinta" "ba yarinta bane tsabagen so ne da kauna ta gaskiya" suka kwashe da dariya irin ta manyan nan kafin tai hugging nashi su a dariya atare gwanin ban sha'awa. [11/1, 11:44 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣ _*This novel is For free. Wanda mu kungiyan *FREE HAUSA NOVELS WATO BANZA ASSOCIATIONS* MUKA DAUKI NAUYIN KAWO MAKU. AYI KARATU LAFIYAAAAAAA page 5 Bathroom tawuce dan shegen fitsari takeji, fitsari tayi sanan ta tube gown din jikinta tayo wanka gabaki daya tasaka bathrobe tafito tana kulle igiyan, zama kusada Salima tayi tana murmushi tace "I am so happy wlh, ina cikin tsananin farin ciki, am getting married to the man dat I love, wai kunga yanda Dr dina yay kyau kuwa" tai dan murmushi tana kallon lallen kafarta kaman mai tunanin wani abu tace "Dr na is so cute and duk mutanen dayake mu'amala dasu haka suke da kyau suma, just look at his best friend, shima yanada kyau wlh, so handsome saida baby na yafishi kyau nesa ba kusa ba" tai murmushi tareda danyin fari da idanu, dariya Salima da dayar kawarsu mai suna Nana sukayi dan is so obvious sonta yafi nashi yawa dat is inma yanason nata kenan, Nana tace "Ilham kinason Dr ki sosai wlh, har yanzu baki bamu labarin shi ba, waye shi a ina kuka hadu?" dagakai tayi tana kallon Pop dakin saikuma ahankali ta kwanta kan gado ta daura kanta ka hannayenta ta sauke ajiyan zuciya tace "Mummy na da Ammi (Maman) Waleed are gud friends very good friends, so su suka hadamu, parents dinmu suka hada auren maman shi na sona sosai, ita batason her only son ya auri any kind of girl saidai girl din da she trust sabida kar a cutar mata da yaro, tana sona sosai and taga nagama karatu na, inada good career ga kyau ga brains, gani yar aminiyarta saisa tace am the best choice for her son, that's that for that" tai dan murmushi taredayin tafi, Salima tace "to bamu labarin Dr" dan juya idanu Ilham tayi tareda gyara kwanciya tace "uhnnn Waleed baida wani much story to tell cus shiba loud person bane, baida hananiya, baida surutu sanan baya keeping friends, Arham shi kadaine abokin shi aduniyan nan" tasake yin shiru sanan tace "bayan su Mummy sun gama kulle kulle su kan zasu hadamu aure, sai wata rana Ammi ta aiko Waleed musamman danya kawo wasu kaya wajen Mummy na, itama Mummy na cus komi plan ne nita tura waje bayan ya iso tace na shigo dashi falo na karbi sakon, ina fita waje, Oh Allah" tai dan shiru sanan tace "wlh I've seen many men, many guys, yara masu kudi nayan gayuma, yaran baze da nile tun ina University but bantaba ganin one like Waleed ba, I saw a very tall full guy fari in complexion, ko kadan baida rama jikinshi acike, yana sanye da cooperate dress da alamu office zashi a ranan, wani farin riga ne ajikinshi da bakin wando yasa wani blue and white necktie, yanada full saje da gemu baki sidik, gemunshi a mugun gyare baida yawa sosai yana kyalli tsabagen gyaran dayaji, lips dinshi pink yirrr kaman zaka taba jini yafito look perfect a face dinshi and moist kaman ya shafa lip balm, gashi da dogon hanci idanunshi manya sosai yanada perfect black eyeballs, giran shi acike bakin kirin, gashin kanshi nada dan yawa ba chan chan ba gashin kanshi na kyalli kaman irin na larabawan nan, he don't really look Nigerian, dana ganshi kasama motsi nayi sai shi daya luradani yacemin cikin sassanyar muryan nan nashi Mummy na nan, Ammi sent me, yanda yake magana ko dole yatafi da imanin kine, yanada broadfull chest, that is it fa, bayan na karbi sakon da sauri mai dakin Mummy na nace Mummy waye wanan yaron, tacemin his name is Dr Waleed Warbai 28yrs of age, only son din Mrs Warbai kawata, yamin ina sonshi cus mamanshi naso tahadani aure dashi ne, wlh ko I was just blushing, I couldn't believe abinda naji bansan lokacin dana fada jikin Mummy ba ina murna dudda tsakanina dashi is just 2yrs ne cus 26 nake shikuma 28 ban damuba dan he looks older dan his age irin yaran yan gayun nanne dasuka ci dadi suka fashe, a hakan ma dan yana gym ne saisa kibanshi baiyi yawaba it looks perfect on him, shikenan aka bani number shi sanan yakanzo once in a while, this boy is rich, his late dad is multi billionaire, babanshi nada companies, yanada company building boat na ruwa, and his father was the first person dayakawo electronic car a Nigeria, baban shi mahaifin shi, that is his grandfather balarabe ne matanshi yar Nigeria saisa Waleed inji Ammi da babanshi yake kama, kanin babanshi daya a duniya yana Ukraine shima kudine dashi sosai but baida yara shima saisa Waleed keda gatan duniya, his uncle nasonshi kaman me, all kudaden da mahaifinshi yabarmai he use them yabude gidan marayu, akwai hospital agidan marayin da nakasassun, akwai school tundaga nursery har secondary kuma duk wanda wish to further yana kaisu University, insuka gama yabasu aiki in sunason suyi aiki gidan marayun yayi in a outside nema yabasu sanan yamusu aure, matan inhar sunada tsayaye yana aurar dasu tun kafin ma su shiga University, as small as Waleed but taimakon dayake ko mahaifina baya irinshi, na auri someone like Waleed na haifama family su magaji nida talauci har lahira saisa dazaran na shiga gwaranni zan dingayi ko Mummy ma haka tafadamin haka zan dinga yi, to shikenan labarin and I can't wait for tommorow muyi aure, can't wait to make luv to my Waleed, shagwabben mijina" dariya duk sukayi haka suka dinga hira har bacci yay awon gaba dasu. *** Ance rana bata karya saida uwar diya taji kunya, yau asabar dubbannin jama'a ciki harda gwamnoni da representative na shugaban kasa, dan ansan marigayi mahaifin Waleed, sanan har gobe suna business da companonin shi aka shaida daurin aure tsakanin Waleed Warbai da Khadija Ilham Maifanko akan sadaki 3million naira. Sosai idanunshi sukai jaa sosai, kasa amsa gaisuwan yan uwa da abokan arziki yayi, ga employees dinshi sun cika wurin sunamai Allah ya sanya alheri gyada musu kai kawai yake dan baijin zai iya bude baki yayi magana ba ayanda yakejin kanshi sai Arham dake tayashi karban gaisuwan cikeda fara'a kaman shine ango, ganin kanshi yasoma juyawa yasa kaman an tsikareshi ya mike tsaye hannunshi cikin aljihun Arham hakan yasa da sauri Arham dake magana dawani yajuyo ya kallai, Waleed bai damu da kallon da Arham kemai ba yazaro key mota yay gaba da saurinshi yana tafiya kaman zai tashi sama yakarasa wajen motan su yabude ya shiga mazahnin6direna da sauri rabon dayay tuki da kanshi harya manta, harya tada motan Arham yazo ta wajen glass din yana kallonshi yace "are you crazy x-man? Where do you think u are driving yourself too? Bazaka tsaya ka gama amsan gaisuwan mutane ba zaka gudu kana ango? Banda hakama kaine zaka tuka kanka katuna the last time you drive?" tsayawa yayi kallon Arham for few seconds inyace zai bude baki yamai magana he might cry hakan yasa ya dauke kanshi ya sauke ajiyan zuciya sanan yawani irin fizgan motan yay reverse da sauri Arham ya matsa baya, ganin yanda aka juyo ana kallonsu yasa yadan saki murmushin yake yace "ahhhhm mantuwa ango yayi gift din dazai bama amaryan shi na daurin aure" murmushi duk akayi banda uncle dinshi dayane nan fari fat kaman bature yana sanye da manyan kaya da farin glass a idanu, yataho inda Arham din yake, cike da girmamawa Arham yace "sannu Uncle" cikin fada yace "ya akayi kabarshi yay driving kanshi so kake ka kashemana d'a?" wani irin dukan zuciyan shi maganan Uncle Arham yayi hakan yasa yadago Kanshi ya kalli uncle din ahankali, cikin fushi uncle yace "if u can't take care of our son wats the point of being his friend eh? Wlh bansan shirme mtdww" yaja tsaki sanan yajuya ya kwalama direban bodyguard din Waleed dake chan suna cin abincin su da gudu yataho yace "Allah taimaki yallabai gani" cikin fushi Uncle yajuyo ya kalli Arham din yace "ina yaje?" ahankali kaman wanda yake rashin lpy yace "I think gida yaje" "you think! What an insolence" Uncle yafada cikin bacin rai sanan takalli direba yace "drive home in Waleed nagida call me ka sanar dani, be fast he just left" da sauri direban ya shiga mota yaja shikuma uncle yajuya yakoma wajen friends dinshi akabar Arham shikadai awajen a tsaye idanunshi sunyi jazur, ganin yanda yan wajen ajikinsu ke kallonshi yasa ya kakalo murmushi yamusu yataho inda suke yacigaba da hirada su. Cikin ikon ubangiji ya iso gida lpy, ta Gate din bayan layi yay parking tareda kashe motan, ahankali ya sauko yana ganin jiri yabude Gate din ya shigo ya shiga flat dinshi bedroom dinshi yawuce direct yawuce bathroom ya shiga kwara uban amai gwanin ban tausayi, saida aman ya tsaya sanan yay flushing aman yabude tap ya kuskure bakinshi tareda wanke fuskan shi yajawo dan gajeren towel dinshi ya shiga goge fuska yana sauke ajiyan zuciya yafito, rage kayan jikinshi yayi jikinshi yadau mugun zafi ahankali yakarasa ya kwanta kan gado sai bacci. Ahankali yaji ana kiran sunanshi sama sama ta cikin bacci, bude idanunshi yayi kadan ganin fuskar Arham yasa yabude idanun completely ya kallai, kafin ahankali yatashi ya zauna ya jingina bayanshi da bangon gado, zama Arham yayi agefenshi sanan ya fuzar da huci mai zafi kafin yadago kanshi ya kalle Waleed din yace "Waleed" Arham hardly call him da sunanshi saidai ya kirashi da Xman, yanda yakira sunanshi yasa ya kalleshi, anatse Arham yace "today is the last day dazan maka tambayan nan, wlh in bakaban amsaba bazan karabi ta kanka ba am telling you, bansan meke damunka ba, for god sake Waleed u weren't like this before, remember am your blood right, I know all ur worries, nasan anything that has to do with you, tun zancen auren nan naka ka chanza gabaki daya, I know magana dama namaka wahala but banda ni, amman this days harni din da kyar kake kulani, Waleed what is wrong? What's the matter with you? What is bothering you like this talk to me Waleed, talk! " Arham yadaka mai tsawa sosai, hannu yasa da sauri ya yatoshe kunnenshi saiga hawaye sun zubo, da sauri yasa hannu ya share, ganin hawaye akan idanun Waleed yasa jikin Arham yay sanyi ahankali ya matsa kusada shi yatsun shi biyu yakai kan fuskan shi ya dangwalo hawayen dayake kan fuskan shi ya kalli yatsunshi ganin hawaye ne da gaske yasa cikin wata irin muryan mamaki yace "t......tears X-man? Ar.....are you crying?" yay maganan da mugun mamaki dan zai iya cewa rabon dayaga kukan Waleed tun suna yara, cikin wata irin damuwa yace "Waleed wats making you cry like this? Baka rasa ci ba, sha ba, sutura ba, Waleed duk wata jin dadin zaman duniyan nan damuke ciki kanada shi, tari kadai zakayi sai sama da kasa ta kusan hadewa dan kawai asan dalilin dayasa kai tarin, look at your room" yabi ko ina da kallo adakin yace "dakinka ko dakunan 10star hotel albarka, everthing imported, designers kasa kaya mai tsada, kanada mesarati, ferrari, g wagon, brabus, benz, range rover wanan danake magana fa duk na 2020, kaci mai tsada, kahau mai tsada, ka taka mai tsada ka kwanta amai tsada, Waleed babu abinda kanema karasa aduniyan nan, kudi kaman zasu fasa account dinka, inda ace suna magana da naka harda fito zasu dingayi, banga abinda karasa awanan duniyan nan tamaliki yaumin deen ba u are loved banga wanda baya sonka ba, just look at how Ilham take sonka kaman zata mutu sometimes I use to wish inama nine kai dan banga wani abu dazai dinga damuna ba, koma abu nadamu na I can use my money na kauda duk wata matsala ta, money is problem solver and a joy buyer" cikin crying tone Waleed yace "you are wrong Arham! You are wrong! You are so wronggggg" ya karashe maganan muryanshi tai rauni sosai, hannu yasa ya share hawayen dasuka zubomai tass sanan yakalli Arham da jajayen idanunshi yace "dukiya komin yawanta bata iya siya maka farin ciki, kwanciyan hankali, money can't buy happiness Arham, and right now right here, at this current moment I am not happy, I am not happy, I am very sad, very sad, kasan menene?" yay maganan yana goge hawaye dasuka zubomai kafin ahankali yace "I am not happy with this arrange marriage ko kadan na Ammi, shekaru na is just 28 maisa akeso amin aure? Am too young for marriage, gajiya akayi dani? Why rushing to get me into marriage, Arham am not ready for anything marriage nor am I ready for anything family am too young, am not ready to settle down, inma aure ne baza abari na nemi wanda nikeso ba...." "to kanada wacce kakeson ne Waleed kaida baka kula mata? U don't even have their time, rayuwanka gabaki daya you've dedicated it to your orphanage, ina kake gidan marayu, ina zaka gidan marayu, daga ina kake gidan marayu, beside what is dere da bazaka iya son zabin Ammi ba? That girl is beautiful, she is gorgeous, bata nemi komi ta rasaba na y'a mace ba, gata she's educated, tai karatu abinta, karatun ma a kasan waje, lawyer fa, haba in baka godema Allah ba ai baka bijirema ni'iman daya maka ba Waleed, ur wife is too perfect" cikin zafin zuciya Waleed yace "tunda har kaga perfection dinta marry her now? Wait! Are you on my side or side din su Ammi? My parents did awful things to me and u are supporting them? Where is my Arham my blood that always support me through thick and thin?" dan fuzar da iska Arham yayi saikuma yamika hannunshi yakama hannun Waleed din yace "am right here Waleed, am right here and I will always support you, always, I will always be by your side kaji" shiru Waleed yayi baicemai komiba sai kallonshi dayake idanunshi jajir, ahankali Arham yace "am not saying su Ammi sun kyauta, kuma am not taking side dinsu all am saying is the gurl is okay guy, kasandai u are still a virgin ko" yay maganan yanadan cizan lips dinshi alamun neman tsokana yace "kai har yanzu bakasan kan dadin abinva trust me this gurl u will enjoy her, kobaka sonta kadinga biyan bukatun ka da ita make ur self a man jor dan har yanzu kai boy ne" dan yatsine fuska Waleed yayi irin na shagwababbun yaran yan gayun nan yace "I can't sleep with a woman I don't have feelings for" cikin takaici Arham yace "kai matsalan ka kenan andai daura muku aure hakkinta na kanka dolen kane wanan wlh, anyway mubar maganan tashi kaje kai salla, ni zanje gidan naje naji mai kawayen Amarya ke bukata kafin gobe mu rakakai daki wayaga su Waleed ango, am even picturing how u will be groaning kaman giw......" jefamai filo Waleed yayi Arham ya arce aguje yay wurin kofa yana dariya sanan . [11/1, 11:46 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_ ✍️ M SHAKUR 7️⃣ & 8️⃣ _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA, you can also send MTN card 500 idan bakida banki_ FREE PAGE Fitowa tayi daga wanka daure da blue towel ganin Amah bata daki yasa tawuce tadau doguwan rigan da taciro ta shirya tsaf cikin rigan takarasa gaban dressing mirror taja kujeran ta zauna hannunta tasaka ta warware farin karamin towel din dake kanta gashinta ne yazubo daya saukan mata har waist gashin baki sidik dashi so silky irin gashinsu, wani brush tadauka dake gaban madubin tai brushing gashin dakeda sanstsi gashin nakara tsayi sosai brush kawai yawo yake acikin gashin, murmushi tayi ta kalli kanta dudda babu kwalliya akan fuskarta amman tai shegen kyau ribbon tadauka ta daure gashinta ta dunkule jelan gashin sanan ta mike tai wajen jakanta budewa tayi taciro mac book dinta da wayanta kiran iPhone wajen socket tayi ta makalasu ajikin chaji sanan tafito daga dakin kanta babu dan kwali, karasawa wajen mahaifinta tayi da duk suko juyo suna kallonta jin tafiyan ta murmushi tayi takaraso wajen ta zauna kusada Aby tana dafamai kafa tace "Assalamu Alaykum" "waallaikumu sallam" Aby ya amsata yana ijiye kofin shayin hannunshi akan farintin kofin, ashagwabe tace "Aby nikazubamin abinci na naci kasan ko I miss abincin gidanmu, abincin school baikai na gidanmu dadi ba, and a Egypt koda yaushe nikadai nakecin abinci kaman mayya, I miss eating abinci cikin yan uwana da babana da Amah, Amah ina Sabeeha?" Amah zatai magana sukaji sahun tafiya hakan yasa duk suka dago kai matar Aby ce tasauko daga stairs rike da dan karamin tray dake dauke da dabino da olives, murmushi ta sakan musu tace "Assalamu Alaykum, ahlan bikum" tai maganan tana ijiye tray agaban Aby, ahankali Aby yace "ahlan bik" murmushi Umm tayi ta zauna kusada Aby tanadan satan kallon Widad data sunnar da kanta kasa tana wasada flowers din kayanta kaman ba itace mai uban surutun nan yanzun nan kafin tazo wajen ba, maganan Aby ne taji akanta yace "yauwa Hibba zoki zubama yarki abinci yunwa takeji dan rigima kuma wai ni zan zubamata" yar dariya Umm tayi tajuya ta kalli Widad din tace "mezan zuba miki yar gatan baban ta?" faduwa gaban Widad yayi hakan yasa ahankali batare data dagokanta ba tace "Umm kibarshi dama wasa nake" ganin yanda tai magana yasa da sauri Aby yace "yaushe za'ai haka, bari nazubamana sai muci tare ko yarinyar babanta" baijira cewanta ba yazuba musu yadebo yashiga bata, shiru duk akayi kowa ya shiga cin abincin, dayake ka'ida ne basa magana in anacin abinci saida suka gamaci tsaf sanan ta tashi zata shiga tattare kayan Aby yace "leave it mamanki da yan aiki zasuyi, Ke magana zanyi dake zoki zauna, Hibba tashi ki gyara wajen nan" ba karamin ciwo maganan yama Umm ba amman saitai kaman bataji su ba yan aiki ta kwalama kira suka shiga kwashe kayayyakin abinci tana ga yamusu inda zasukai saida suka gyara wurin tsaf sanan yadan numfasa yakalli Widad dinda hankalinta yay nisa tanachan tana kallon wayanda ke raye raye a tsakar gidansu yace "Widad" juyowa tayi da sauri ta kallai da dara daran idanunnan nata, ahankali Abby yace "family Ahmad sun zo last week, although nina hana Ahmad karya fadamiki sabida nafison nafada miki dakaina, iyayen Ahmad sunason dansu wato Ahmad yay settling down, yariga yagama karatu dadaddewa so suke amuku aure inyaso shi Ahmad din can follow you chan Egypt din kicigaba da rayuwan ku kina karatu, nima nafison haka Widad so nake kiyi aure hankalina ya kwanta yanzu you are 20 this is just the right time, sai mukai deciding on yau ranan dakika dawo tunda dasafe zaki sauka da daddare sai ai engagement ceremony din in one week time kuma ai biki yakika gani yar albarka?" wani irin kunya ne taji ya lullubeta batasan lokacin data boye fuskarta a bayan Aby ba tanadan murmushi, Amah tahau dariya tana tafi tace "wanan ayanda suke son juna itada Ahmad koyau kace zakai bikin su bazata taba cemaka a'a ba" akunyace ta tashi da gudu tai sama dakinsu ta fada tamaida kofar dakin ta rufe ta daura hannunta kan kirjinta dake bugawa da sauri da sauri, turo baki tayi saikuma ta harari system dinta tace "kojiya da daddare we did video call shine bai fadamin bako" tai kwafa saikuma tace "mun ma bata baran kiraka ba" ta daure fuska tabude kofa tawuce tafita chan rooftop din gidansu tahau babu kowa awajen sai gari dakeke gani ga iska na kadawa tako'ina, ahankali ta zauna tareda tan kwashe kafa ta lumshe ido tana feeling yanda breeze ke dibanta mamaki take dan she never thought of at this stage Aby zai mata aure, tazaci za'a bari tagama school kafin tai aure tunda duka duka saura mata shekara biyu, sosai tai nisa a tunani taji andafa mata kafada, da sauri ta dago kanta Aby ne, ahankali tace "Aby" zama yayi agefenta shima ya ta tankwashe kafa kaman yanda tayi yana kallon garin yanda mutane ke hayaniyan su cikin kwanciyan hankali yace "naje dakinku banganki ba nasan zan ganki anan saisa nabiyoki, Widad" Aby yakira sunanta anatse, dago kanta tayi ta kallai ahankali tace "na'am Aby" dan shiru yayi yana kallonta kafin yamika hannunshi ya shafa lallausan gashin kanta yace "inaso kifada min gaskiya karki ji kunya ta kinji, am your only friend right, inaso kifadamin kinason Ahmad?" shiru tayi tana kallon Aby kafin ahankali ta gyadamai kai, ahankali yace "mesa kike sonshi?" murmushi tadanyi ta dauke kai ta maida hankalinta kan kallon gari da sararin samaniya tace "Aby Ahmad is my best friend and only friend bayan kai, bayan Mama tarasu he was there for me giving me comfort, we use to play different games duddan kawai yaga bana tunani, anytime nafara kuka saiyaga nahakura nai shiru sanan hankalin shi zai kwanta, ko awayane saiya tabbatar daya lallasheni nahakura naidaina kukan sanan zai katse wayan, bayan nafada maka inaso naje karatu wani gari shima nafada mai he supported me, da ina Egypt kullum sai munyi video call, ya koyamin karatu, ya koyamin assignment, komi daya danganci na rayuwana he's there, he is just my everything my best best friend saisa nakeson shi Aby" tai dan murmushi saikuma ta daure fuska tace "but Aby yanzu fushi nikeda shi mun bata ma" da sauri Aby da tuntuni yake sauraronta yace "mesa?" murmushi tayi tace "Aby baifa fadamin his parents came over ba" dan dariya Aby yayi yakama kafadarta yasa hannunshi a aljihu yaciro wani dan karamin box yamika mata karba tayi tace "me aciki Aby?" cikeda jin dadi yace "open it" budewa tayi ahankali wani hadadden zobene na maza mai shegen kyau na gold tace "wow Aby, this is beautiful" tasa yatsanta tana taba ring din, anatse Aby yace "engagement ring dinki ne give it to your Ahmad kisamai a yatsan shi" dago kanta tayi ahankali ta kalli mahaifin nata kaman yanda yake kallonta hawaye ne suka zubo ahankali ta rungume shi bubbuga bayanta yayi yace "shiiii stop crying u are my everything Widad, am working hard in this life because of you if anything happen to you I will die, saisa nafison ayi aurenku ki koma Egypt tareda mijinki banson yanda kike zama a hostel ke kadai, I know Ahmad will always protect you he is a good loving boy" sun dade ahaka tana manne dashi jin ankira azahar yasa yasake ta tareda dagata yace "muje kiyi salla afara shirye shirye" gyadamai kai tayi yadagata suka tafi. Suna saukowa falo daidai shigowan wata yarinya fara itama tarr doguwa tana sanye da bakin doguwan riga tadaura gyalen rigan akanta batare datai rolling ba ana ganin blonde gashinta hannunta rike da jakan makaranta, Widad na ganin ta washe baki tai wajenta da gudu tai kissing checks dinta starting from the left one taima right din sanan ta rungume ta tace "marhaba Sabeeha" hada ido Sabeeha tayi da Aby daya tsaya yana kallonsu murmushi tayi ta dago Widad din daga jikinta itama tai kissing din kumatun ta sanan ta shafa fuskarta cikin harshen larabci tace "iyye Widad kin kara kyau abinki, kin kara girma kaman bakeba, ya makaranta?" gyadamata kai Widad tayi tana murmushi tace "kema kinyi kyau Sabeeha" "Sabeeha" sukaji muryan Umm daga sama ta kwaloma Sabeeha kira hakan yasa ahankali Widad tasaketa duk suka dagokai harda Aby suka kalli Umm din dake gaban bene, dan murmushi tayi tace "abu zatamin ne sorry na katse musu hira, bari taci abinci saita sauka afara shirye shiryen da ita" gyadakai Aby yayi cikeda gamsuwa yace "hakane, wuce kije kiyi salla Widad bari naje masallacin nima" juyawa Widad tayi kaman yanda mahaifin nata ya umarceta tai dakin Amah itakuma Sabeeha ta gaida Aby ya amsata cikeda fara'a yanai mata barka da zuwa sanan yawuce yafita dan zuwa gabatar da salla a masallaci. Har daki Sabeeha tabi mahaifiyarta jakan makarantan ta tacire ta ijiye ranta adan bace tace "Umm maisa baki gayamin yarinyar nan zata dawo ba yau?" kofi Umm tadauka ta tittila mata madara a cup din sanan tajuyo ta mikama Sabeeha tace "nima uban nata bai gayamin ba nadaiga anata saka flowers ana gyara gidan nazaci ko yauma iyayen yaron nan zasu sake dawowa ne ashe itace shine dazu dasafe wai na shirya zamuje mu tarbo yar gaban goshinshi daga Airport" cikin fushi Sabeeha tace "shine ke kikawani je, ni wlh Umm bazan yarda Aby nawani treating naki kaman wata nani ba, ke nani yarshi ce kema ai matarshi ce mai matsayin da daraja, ni wlh bazan yarda ana wulakanta min keb....." da sauri Umm tace "ke jinan inhar zai mallaka miki dukiyarshi all his property yakoma naki ai zan iya komi, kinga daga Widad sai ke ku kadaine y'a y'a agidan nan, banda haka ke accounting ma kika karanta kuma yanzu ma final exams dinki kikeyi ke kikafi chanchanta da zama in charge of dukiyoyin shi ba yarshiba" dan murmushi Sabeeha tayi ta mikama maman tata Cup din milk din data shanye tace "Umm inabadai yau Widad zata fadi ta mutuba ta ina Aby zai mallakamin dukiyarrshi nida ba yarshi ba" murmushi kawai Umm tayi ta ijiye cup din tace "leave everything to me, tashi kije kiyi wanka kici abinci saiki sauka kasa wajenta, so nike kiyi amfani da ita hakan zaisa Babanta yakara miki wata daraja na musamman a fadanshi" dan yatsine fuska Sabeeha tayi tace "I can't stand that gurl Umm am so jealous of her wlh, I wish nikeda mahaifin mai sona irin Aby, I wish nikeda all abubuwan data mallaka" tai maganan tana bude dakinta tana shiga ta maida kofar ta rufe cike da rashin jin dadi, yayinda Umm tabi bayanta da kallo, wasu hawaye ne taji sun tarun mata a ido, tarasa maisa Aby baison yarinyarta kaman yanda yakeson Widad, kome Sabeeha take bukata yana mata, shike biya mata kudin makaranta ya ijiye mota na musamman da ita kadai ake kaiwa duk inda zata dashi, babu abinda Sabeeha ta nema tarasa kawai dai wanan son da kaunar da affection dayakema Widad baima yarta shi dudda Sabeeha ce kullum agidan but baitaba jinta kaman Widad ba, baima janta jiki, daukan tray din madaran tayi tawuce ta shiga kitchen din dake falon ta dashi ta ijiye. Shirye shirye akahau yi sosan gaske abunku da babban gida, ma'aikata ne daban daban kowa na aikinshi, shidai Aby na zaune a falo kan tattausan kujeranshi yana kallon Widad yanda take murmushi dimples dinta na lotsawa duka biyun tana kallon hannayenta da ake mata hadaddun lalle akai, kowani hannu da wanda ke mata lalle akai, itakuma Sabeeha ganin idanun Abba na kansu yasa ta shiga gyara mata dogon gashinta tana applying hair treatment din da aka gama hadamata na gashinta tana shafawa tana bama Widad labarin yanda take fitsari ajiki datana yarinyar Widad sai dariya take kaman cikinta zai kulle. Sosai Abba ke murmushi yana kallonta deep down jiyake kaman karyama aurar da itan wlh baisan ya ai iya rayuwa ba itaba amman abu daya ke kwantarmao da hankali inya tuna shine yanda yaga tanason Ahmad din shima kuma Ahmad din na sonta, dafa kanshi dayaji anyi yasa yadago kanshi ganin Amah ce da sauri yatashi yazaunar da ita zama tayida kyau sanan ta kalli tsakar gidan dayake kallo tai murmushi tace "Widad kake kallo ko?" murmushi yayi yasake kallon inda Widad din take ya zubamata idanu yana murmushi yace "Amah she smiled just like her mother, Widad dina is so happy Amah" murmushi Amah tayi tana kallon Widad din da Saheeba ke saka mata gashinta cikin shower cap tace "nasan duk inda mahaifiyar ta take she's happy yarta is getting married" murmushi dukansu sukayi atare suka cigaba da kallonsu. Gama zana mata lallen akayi sanan ta mike tsaye tana murmushi tahau rawa irin na yan mata dinan su Sabeeha namata tafi tana juyawa blouse dinta nasake zama umbrella, sosai Aby ke kallonta suna murmushi mawakan nasake rera mata waka duk wanda zai ganta sai yaji kaman ya saceta ya gudu she looks so adorable and so sweet and happy, ta gefen ido Sabeeha ta lura har yanzu Aby kallonsu yake hakan yasa ta tashi itama ta shiga filin sukahau rawa itada Widad din sosai Aby da Amah nata dariya. Wuraren magrib aka gama raye raye aka wanke mata gashin ana wake akai drying gashin aka gyarashi tsaf bayan yasha maiyuka akamata parking sanan akasata taje tai wanka, wanka tayo sanan aka shiryata cikin wasu ubansu kaya long kaftan ne milk color dake dauke da stones da bids ta ko'ina masu shining kaman na diamond, djellaba (kaftan mai long lose robe) da aka daure mata igiyan ta wajen waist yay kaman belt, kayan kaman kayan yan India, aka yafamata gyalen kayan aka bayan an gyaramata gashi anyi parking ansaka mata wata sarka ta gaban gashin anmata makeup mai kyau lips dinan anshafa mata red janbaki dayasa tai kyau kaman ita takera kanta, gusan sarewa da wakoki dasukaji yana tashi na welcoming groom's family yasa Sabeeha tace "Ahmad and his family are here, iyye ta Ahmad kinyi kyau" akunyace ta lullube fuskarta tana kara daure fuska ita adole Sabeeha tadena tskonar ta, Sabeeha tai dariya tace "ina platan dake dauke da zoben sa ranan?" ahankali tace "yana wajen Amah" gyadamata kai Sabeeha tayi tace "tom bari naje naga ya ake ciki awajen" fita tayi daga dakin tai dankareren compound dinsu ta tsaya tana kallon kowa, iyayene aketa gaishe gaishe family su Ahmad ne da taasu tawagar yayinda wani kyakkyawan balaraben guy yana sanye da sherwani hadadden gaske milk color kaman kalan na Widad, sai fararen kafanshi sanye da Babouche (traditional morrocan shoes) hadadden gaske shima milk, fuskarshi na kyalli bakin sajenshi da gemunshi a kwance yana murmushi yana kallon kowa kanshi ya kafa wata yar karaman hula milk color dake dauke da bids design tsayamai a tsakiyan kanshi, dan tabe baki tayi ta tsaya daga inda take tana satan kallonshi kaman yaune tafara ganinshi. "Sabeeha" Aby ya kwalamata kira da sauri ta waigo Aby ne da Umm tareda iyayen Ahmad, cikeda fara'a kana ganinshi kasan yau cikin farin ciki yake yace "jeki kawo yar uwanki afara lokaci natafiya" gyadama Aby kai tayi tajuya takoma ciki, bude dakin tayi ta shiga ta tarar da Amah ma natare da Widad din tana kara gyaramata fuska, ganin yanda Amah ke kallonta yasa tace "Aby yace afito da itane Amah za'a fara" dago Widad din Amah tayi tana gyara mata zaman gyalen sanan ta kalli Sabeeha ta nuna mata farantin da jajayen flowers ke cike aciki sai akwatin zoben tace "biyomu da wanan, muje Widad" ahankali Widad ke tafiya idanuwanta akasa har suka fita tsakar gidan inda wakokin larabawa ke tashi taresu maman Ahmad tayi ta rungume Widad din da takasa daga ido ta kalleta tamata kiss akumata tace "masha Allah Widad kinyi kyau" mahaifin shi ma haka yamata kiss akumatu sanan Amah tawuce da ita har zuwa inda Ahmad yake azaune wanda nanne aka tanada dan zaman Amarya da ango Amah ta zaunar da ita akan kujeran gefen Ahmad sanan ta cupping face din Ahmad tace "dan saurayina kai kyau" dan dariya yayi yace "Amah nifa nagayamiki bani sonki jikanki nakeso" dariya tayi tamai kiss akumatu tace "ko kaki ko kaso yaro soyayyan mu ba fashi" tai dariya tareda wucewa tabarsu awajen shiru sukayi Widad taki juyowa ta kallai dudda takosa ta kallai dan tasan yay kyau jikinta na bata hakan. Yana kallon masuyin rawa kaman hankalin shi na wajen yace "tayaya zan fara bawa wacce zuciyata ke bugamawa hakuri?" yadanyi shiru yace "nasan Ahmad mai laifi ne amman da ace Widad zata dan juyo ta kalli Ahmad koda sau dayane da Ahmad yasami natsuwa dan zuciyarshi dab take data buga" dan juyowa tayi ahankali ta kallai saida kirjinshi yabuga baitaba ganin tamai kyau irin na yauba kasa daina kallonta yayi hakan yasa ta dauke kai abinta tanadan murmushi zaiyi magana yaji muryan Aby nabada izini akashe wakan dan zasu fara ceremony din, wani ne yazo yabude taron da addu'a sanan akasa Ahmad da Widad din sufito fili, dan wake aka fara yi ana zubamusu flower kafin abokin Ahmad din dake gefenshi yamika mai farantin zoben daukan akwatin zoben yayi yabude yaciro wani hadadden diamond ring ya kalli fuskar Widad din kaman yanda take kallonshi yace "inason ki Widad and I will love to spend the rest of my life with you, kin yarda muyi taking this relationship a step forward ta hanyar engagement?" ahankali ta gyadamai kai, hannunshi yasa yakamo hannunta ahankali yana kallon fuskarta ya zuramata zoben a yatsa ihu aka dauka da tafi ana jefamusu fulawowi, ahankali Widad ta juya tadau akwatin zoben ta daga farantin da Sabeeha tarike tabude ta ciro zoben sanan ta kalleshi cikin tattausan sweet muryanta tace "Ahmad you've been the source of my happiness and joy inhar ban aureka na zauna akarkashinka ba Menai achieving a rayuwan nan, yes I love you also and I don't have any greater wish daya wuce yin rayuwa dakai" ahankali ta ziramai zoben a yatsunshi hawaye ya cika idanunta saikuma tajuya ta rungume Aby da gudu dake gefen ta yana kallonta tahau kuka, watsa musu fulawowi akahau yi Aby na jijjigata dan tai shiru shikuma Ahmad na satan kallonta Widad is so soft, abu kadan kesata kuka, kaman ma a daura musu auren yau yakeji yahuta da wanan wutan son nata dake cinshi amman ya zaiyi nanda 7days ne tazama tashi halak malak, da kyar Aby yasamu tai shiru sanan yadagota tareda sharemata fuska duk yabi yadamu danshi ko inane ko agaban uban waye baida kunyan nunama yarshi so, cikeda lallashi dakuma damuwa yace "me haka kike kuka so kike kitadamin hankali? Eh" girgizamai kai tayi hakan yasa yace "to menene? Bakida lpy ne?" girgiza mai kai kawai tayi dan batason ta tadamai da hankali zai sake magana Ahmad dayakasa hakura yadan matsi kusadashi cikeda girmamawa yace "ahhh Aby please can I have a moment with her" gyadamai kai Abba yayi yana kara kallon fuskarta cikeda damuwa yace "kuje falona watakila tai shiru, please tafada maka meke damunta" gyadama Aby kai yayi ya kalli Widad din dake share fuska yace "muje" juyawa tayi ahankali sukai ciki yayinda iyayen su suka bisu da kallo cikeda so, instead of yaje falon Aby saiya kaita rooftop her fevorite place in the house, zaunar da ita yayi ahankali kafin ya zauna agabanta yana kallon yanda take share hawayen dasuka kasa daina tsayawa cikeda damuwa yace "why are you crying? I thought today suppose to be the most happiest day of our lives Widad we've come a long way, we are getting married in 7days" shiru yayi yana kallonta ganin takasa daina kukan, ahankali yace "are you missing your Mum?" dago jajayen idanunta tayi ta kalleshi duk duniyan nan banda Aby no one understands her like Ahmad, intai kuka yasan kukan me intai bakin ciki yasan name hakama intai murna, saisa take sonshi, ganin takasa bashi amsa sai kallonshi take wasu hawayen nasake fitowa yasa yadawo ta saitin inda take zaune ya zauna a gefenta tareda lankwashe kafa yay dan shiru sanan ya kalli sararin samaniya yana bin taurarin dake sama da kallo, cikin yar lallausan murya yakira sunanta. "Widad look up 👆" yanda yay maganan yasa ta dago kanta ta kallai ganin sama yake mata pointing yasa ta kalli saman itama yace "kinga wanchan taurarin dayafi kowanne cikinsu haske" shiru tayi tana kallon tauraron dayake nunama ta, yace "let's take your Mum to be that tauraron, trust me your Mum is up there tana kallonki, and believe me inna gayamiki abu daya datafi tsana aduniyan nan shine taga hawaye nafita daga precious eyes dinki, banda hakama ni she will be angry with me" da sauri ta kallai irin kallon tambayan nan, dan juyowa yayi ya kalleta shima yazubamata kyawawa fararen idanunshi yana kallon fuskarta cikin tsantsan begen so yace "I promise Mum tun kafin tarasu akan I will always make u happy, bazan taba barin yarta ta zubar da hawaye ba gashinan yau I couldn't keep my promise sai kuka kike, am a bad person I couldn't keep my word am a bad person" yafadi shima kaman zaiyi kukan yana kallon kwayar idanunta, ahankali ta girgizamai kai tace "you are not a bad person in fact you are the best human I've ever come across in this world" takai hannunta ta share hawayen tass tana kallonshi Kaman yanda shima ke kallonta kaman ya tsaga jikinshi yasata aciki yakeji kawai yahuta, tun yana University yanadan saurayi yake son Widad tun ranan da Abban shi yazo dashi gidan wajen Aby dan Aby da Abban shi na business tare sosai, lokacin Widad kaman 11yrs take tun lokacin yake sonta, kuma yana bala'in alfahari da ita dan yasan bata taba kallon wani namiji ba balle harta tsaya kula wasu samari dudda tanada mugun kyau da farin jini but shi kadai takeso, yazauna yayi zaman jiranta all this while dan alkawarinsu was sai tagama makaranta zai jiranta sanan sai suyi aure amman hakanan yan kwanakin nan yaji bazai iyaba saisa yadami Abba yazo yasami Aby akai maganan saka rana da biki, yau kuma daya ganta hakanan yakeji kaman ma bazai iya jira kwana bakwai dinan ba kaman a daura auren yanzun nan yakeji a ranshi jiyake kaman za'a kwace mai ita. "Ahmad" Widad takirashi ganin kaman yay nisa atunani, dan murmushi yayi yace "Widad" murmushi tayi tace "tunanin me kakeyi?" shiru yayi yana kallonta kaman bazai bata amsaba saikuma yace "tunanin ranan da am gonna make u mine, namiki ciki" "subhanallah" tafadi da sauri tareda tashi tsaye zata gudu dan kunya taji dan tunda suke tsawo shekaru 10 kenan yanzu baitaba mata maganan banza hakaba, karap taji yarike hannunta yatashi tsaye shima turo baki tayi batare data kalleshi ba tace "ka sakeni" batare dayasake taba yazo ta bayanta yace "kinsan in kika haifamin mace sunan Mum dinki zamu saka ko Widad" akunyace tajuyo ta runtse ido ita adole kunya take ta kalleshi tanaso ta fizge hannunta tace "ni naji to kasaken natafi kaga ana jiranmu ko" dan bakinta yake kallo yanda idanunta ke arufe tana mai shagwaba, ahankali yakai bakinshi saitin nata wani abu na pulling dinshi kaman zai mata kiss saikuma kawai ya rungumeta tsan tsam ahankali yace "I love you so much Widad, I love you" "Widad" Sabeeha ta kwalamata kira da aka turo takirasu a mugun tsorace tabude idanunta tareda fizge jikinta daga jikin Ahmad, Ahmad baitaba rungumeta ba sai yau bama tasan ya akayi hakan yafaru ba dan abin yafaru cikin few seconds ne, sakinta Ahmad yayi ya kalli Sabeeha da idanunta kyam akansu yace "baki iya sallama ba" juyawa tayi tareda watsamai harara tace "baka koyamin ba, dayake kana batama Aby y'a ai dole kace haka" ta juya tafice abinta, a mugun tsorace Widad ta juyo ta kallai zatai magana kuma takasa sai kuka tace "mesa ka rungume ni kaga zata fadima Aby ko" yana bala'in son yaga Widad ta rude bala'in bala'in kyau take, ganin murmushi yake yasa tafashe da kuka, ganin yanda take kuka tana bubbuga kafa akasa yasa yace "wlh in bakimin shiruba kamaki zanyi naita kissing inyaso su Aby sazosu ganmu ahaka kinga a daura auren mu ma yau ko dan ansan mun kosa" yay maganan bakodar atattare dashi shiru tayi takasa cigaba da kuka murmushi yayi yazaro handky ya mika mata yace "wipe those tears mutafi" karba tayi ta share tass sanan yakama hannunta yarike suka wuce suka sauka daga rooftop din. [11/1, 11:46 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 9️⃣ _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ _*NIGERIA*_ Abuja Washegarin ranan biki Misalin 9 na safe yafito yana sanye da fararen kaya, farin t-shirt sai farin wandon shadda ajikinshi da farin slippers din kafarshi, yana tafiyan nan tashi dai dai yana kallon yanda ma'aikatan gidansu ke aiki ana kara gyara gidan da aka gama biki jiya aciki kaman ba'ayiba, dan gajeren tsaki yaja yawuce ya shiga flat dinsu, babu kowa a falo sai wasu mata guda biyu dake sanye da uniform suna aiki daya na goge Centre table dayan na jera abinci dining, gaidashi duk sukayi amman ko kallonsu ma baiba yawuce yahau stairs dorect dakin dayasan zai sami Mom dinshi yawuce, bude kofan yayi bayan yay knocking akan dadduma yaga Mom hakan yasa yamaida kofar kawai yarufe ya shigo ciki hawa kan gado yayi yay kwanciyarshi tareda lumshe ido kaman mai jin bacci yay shiru kana gani kasan yaje dogon tunani. "Dan Yaro" Mom ta kirashi tana linke hijabin jikinta bayan ta tashi daga kan dadduman, dago kanshi yayi ya kalleta yace "morning Mom" "morning katashi lpy, daman yanzu nake shirin naje naduboka, kaci abinci?" yatsine fuska yayi yana tashi yana zama batare daya amsataba, daukan dadduma tayi ta linkeshi shima sanan ta ijiye ta taho ta zauna gefenshi abakin gadon takai hannunta ta daura akan kunnenshi tashafa tace "Dan Yaro how do you feel? Yau zaka koma gidan amaryan ka" yatsine fuska yayi batare dayace komiba murmushi tayi tace "muje dinning kai breakfast" tai maganan tana tashi tashi yayi shima yabita suka sauka kasa dinning sukayi tahadamai shayi yasha ba laifi dan yau yatashi feeling strong, ta zubamai Irish da source fork yadauka yafaraci duk sukai shiru. Ahankali take tattakala matattakalan benen, tun kafin ta sauko take kallonsu barinma Waleed, ko tari batayiba takarasa saukowa kamshin turarenta yasa Mom ta dago kanta ta kalleta, tai bala'in kyau tana sanye cikin wata dark brown atampa da milk color na English wax, tai kyau irin hajiyoyin matan nan, washe baki Mom tayi tareda ijiye spoon din datake cin abinci dashi tace "ina kwana Adda kin sauko" gyadamata kai Ammi tayi still looking at the Waleed, ahankali yadan dago kanshi ya kalleta hada ido sukayi saikuma ya dauke kai murya chan ciki yace "good morning Ammi" "morning" ta amsashi atakaice tawuce kan dogon kujera ta zauna tareda daukan remote ta chanza tashan zuwa African magic taga ko anfara series dinan the Johnson's badan komi takeson shirin ba saidan bada dariya da Nigerian series din keyi. Ajiye fork din Waleed yayi yadau tissue yana goge baki Mom tace "badai harka koshi ba Waleed ai bakaci komiba anan ga peppersoup ga yamballs you haven't touched any" ashagwabe yace "nina koshi, thanks Mom" yay maganan yana tashi daga dinning yamaida kujeran yafito zai fita batare daya kalli Ammi data bishi da kallo ba, har yakai kofa zai bude Ammi ta kirashi. "Waleed" juyowa yayi ahankali ya kalleta suka hada ido saikuma ya dauke kai, tun yana yaro haka yake in yana fushi da Ammi bai iya kallonta saidai kosunhada ido ya dauke kai kawai kuma bazai taba cemata komiba itakuma dazaran yafara mata haka tasan fushi yake da ita, ganin ya tsaya yasa tace "zonan" zuwa yayi ahankali ya tsaya agabanta yana kallon tiles yace "gani Ammi" gefen ta ta nunamai tace "zauna anan" murmushi Mom dake binsu da kallo tasaki tacigaba da breakfast dinta tana girgiza kai ita ya yarta har mamaki take bata, tanason Waleed fa kaman ranta amman rigimanta yafi karfinta. Binshi da kallo Ammi tayi daga sama har kasa babu alamun wasa tattare da ita fuskarnan ta daureshi tace "were you sick ne jiya?" juyowa yayi ya kalleta baki yabude zaiyi magana tace "karka sake kamin karya, I ask a question, where you sick yesterday? Maiya sameka jiya?" ta tambaye shi kai tsaye, shiru yayi kaman ba zaice komiba saikuma yace "zazzabi ne nai amai once but am fine now nasha magani" ji Ammi tayi ranta inyay dubu yabaci tace "and u don't think it was important to let me know ko, inda bantambayeka bama yanzu da bazaka fadamin ba eh?" shiru yamata baice komiba tsawa tadakamai cikin fushi tace "am talking to you kamin shiru Waleed, why didn't you tell me u were sick?" cikin fushi shima yace "wai Ammi for godsake when will you stop treating me like a child eh? Komine saina fadamiki? Yes I was sick yesterday, and I treated myself and I feel much better" yay maganan tareda tashi cikin fushi yay hanyar kofa, cikin fushi Ammi ta kwalamai kira. "Waleed, Waleed, Son, Son" ko juyowa Waleed baiyiba yabude kofa yafice abinshi, cikin fushi Ammi ta kalli Mom dake dinning tace "kina ganin abinda danki kemin ko?" ture plate Mom tayi tace "maiya miki? Ai gaskiya yafadi kinbi kin matsama yaro, kin hanashi sakewan rayuwa, kwaf kwaf kikebin lamuran yaron nan, ki maidashi ciki kamai kihuta haba, kin haba yaro sakewa, kina mai dashi kaman jariri, ki ciro nono ki dinga bashi mana karewanta" cikin fushi Ammi tace "ni kike gayawa haka?" itama cikin fushi dan dama tadade tana tike da Ammi tace "mene fadi? Ba gaskiya bace, kin kama kin aurar da yaro batare dakin shawarce shiba ko tambayan ra'ayinshi inda wasu yaran ne angayamiki zasu yarda ne, wlh dawasu ne da kinga tijara, ba dole yaro yadinga fushi dakeba" tai maganan tana ijiye tissue tai stairs da fushi, cikeda mamaki dakuma fada Ammi tadaga murya tace "nizaku hadewa kai kujuyawa baya, dani kuke fushi?" tai shiru saikuma tace "but I choose the best girl for him kema ai kinganta, I want jika, am so lonely I need jikoki dazaici sunan mahaifin Waleed, laifi nayi danna zabama Waleed mata shine kuka fushi dani daga ke har shi?" yanda tai maganan araunane yasa Mom taji wani tausayinta tasan yayarta sama da kowa and tasan Waleed is her weak point dazaran yaron nan yafara fushi da ita har ciwo kamata yake nan da nan BP ta zai tashi, dayake shi Waleed din danyan kai har yanzu bai sakeshi ba baitaba lurada shine weak point din mahaifiyar shiba hasalima kullum gani yake mamanshi is harsh dan Ammi is too strick dashi gata batada fara'a ko kadan Mom tafita fara'a nesa bakusa ba, saisa all abokanenshi sunfi sabawa da shakewa da mom kan Ammi. Ahankali Mom tajuyo ta kalleta tace "Adda baki gane abinda nake nufiba nasan kowani hukuncin kika yanke akan Waleed is for the best, but yayan yanzu bahaka suke ganiba, naga Ilham yarinya mai kyau, ga ilimi ga kunya, ko makaho ya ganta yasan kin zabo sanan kin dirzowa danki mata, but the question is does your son see it that way? No" ahankali Mom tace "ki sauke wanan harshness dinan kije ki lallabo yaron nan kinmai aure and he feels bai shiryama aure yanzu ba, just patch things up with him kinfini sanin yanda zaki hakan, Adda solve this problem once and for all please inba hakaba ke zaibama kunya inya fara wulakanta yar mutane" Mom na maganan tajuya tai sama abinta, bin bayanta da kallo Ammi tayi harta bacemata daga gani sanan takoma ahankali tazauna akan kujera tabuga uban tagumi takai kusan minti ashirin ahaka azaune saikuma ta mike kaman wacce aka tsikara tai waje. Flat din Waleed tayi bude kofa tayi ta shiga da sauri Waleed dake zaune yana kokarin kunna system dinshi yadago kanshi ganin Ammi ne yasa yamike tsaye ahankali, maida kofar Ammi tayi tarufe cikeda bala'in masifa tace "okay Waleed am now the villain in the story ko, dani kake fushi eh? Mena maka?" cikin kulewa irin exactly child and mother's fight dinan Waleed yace "ni nace kinmin wani abune? Akwai abinda kikace nayi dabanyi ba? U arrange marriage for me I didn't say a thing, kince I shouldn't go to office and am right here at home Ammi what else?" yay maganan idanunshi sunyi jajir kana ganinshi kasan yacika fam, yanda taga yanayinshi yasa hankalinta yawani irin mugun tashi, daura hannayenta akirji Ammi tayi cikin mugun mamaki tace "Waleed, Son!" juyawa yayi da sauri muryanshi narawa yace "ni bakimin komiba Ammi, I need a nap" yana maganan yay hanyar dazai sadashi da bedroom dinshi da sauri Ammi tabishi kafin yasa hannu yabude kofan ta fizgoshi tace "Waleed am talking to you" janyoshi tayi with so much love tai cupping face dinshi tana kallon fuskarshi duk yanda takaiga son su hada ido yaki bata daman hakan, cikin wata irin raunanniyan murya hankalinta inyay dubu yatashi ganin da gaske yaronta fushi yake da ita tace "Waleed dani kake fushi ni mahaifiyarka eh?" cikin muryanshi datahau rawa sosai kaman wanda ke shirin fashewa da kuka yace "Ammi nifa bance miki komiba I did exactly as you said please lea.......leav..." yakasa magana sai hawaye masu dumi, ji Ammi tayi kaman ta kurma ihu da sauri ta rungume shi tace "am sorry, am so sorry Waleed u are crying because me, ni mahaifiyar ka ke saka kuka, no no no, banda burin dayawuce insaka farin ciki aduniyan nan, I never knew my actions hurt this deep, Waleed, my Waleed kallen" tai maganan tana dago fuskarshi daga jikinta, fuskarshi harja tayi sabida hawaye, tsabagen rudewa dan kwalin English atampa dake jikinta hakan yasa gashinta dakenan da furfura anmata kitso shiku ya bayyana tadaura akan fuskarshi ta shiga sharemai hawayen tace "is okay, stop crying, stop crying Son, ya isa" bude bedroom dinshi tayi ta shiga tana rike da shi kan sitter gaban gadon ta zauna ta zaunar dashi tareda rike hannunshi kaman zatai kuka tace "Waleed I never meant to hurt you, kome nayi I did it for you dudda nasan my approach might seems wrong but that is me u know, Waleed kalli kaina" takamo jelar gashin kanta ta nunamai tace "Waleed furfura, am not getting younger anymore, tsufa nike kullum the same way yanda mahaifinka yarasu ya barmu haka nima zan rasu watarana" tadanyi shiru dan batason tai breaking down sanan tadanyi murmushi tai cupping face din Waleed din tace "Son you know about my hypersensitive situation, kaike monitoring minishi kana bani magani, masu irin condition dina can die any moment, na zauna nai tunani na kalleka nakuma karance ka Waleed matama basa gabanka sai aikin gidan marayu, and inaso kai aure inaso naga y'ayan ka my grandchildren kafin nima nabar duniyan nan, batun yau ko jiya nake nema maka mataba, nafara nemama matan aure tun kana 25yrs amman banga wacce tamin ba sai akan khadija, Khadija tayi sauka, tagama karatun ta lawyer ce mai zaman kanta, gata yar gidan mutunci, kuma ranan data fara ganinka na fahimci tana sonka so bakadan ba, inhar ban zabamaka irin matar nan ba wa zan baka maka? But I am sorry, na dauka na isa dakai but I guess I am w......" hannunshi yasa yarufe mata baki tareda girgiza mata kai yace "Ammi kin isa dani, I just didn't wanna get married now ne, Ammi am too young, just 28 fa, and ita yarinyar she is 26 da 2yrs fa na girmeta" dan murmushi Ammi tayi ganin ya sauko ta rungumoshi ta hanyar daura kanshi kan shoulder dinta tace "age is just a number Waleed, nasan tsoro kake kan baka wani girmeta sosai ba bazata girmamaka ba, and you being 28 itakuma 26 baya nufin hakan I know yarinyar dana aura maka tanada dattako she will respect you kaman her king son, are we good now kahakura kadena fushin?" gyadamata kai yayi ahankali yace "yes" dago kanshi tayi ta manna mai kiss agoshi tace "thank you, Allah yamaka albarka, yanda ka rufamin asiri baka kunyatani ba kaima Allah bazai taba kunya taka ba duniya walahira, Allah yakareka daga makiyanka, akwai kaya na mussamman dana maka ordersu daga Morocco 🇲🇦" "Sherwani masu kyau zakayi kaman wani dan India, dama yarona badai kyau ba ballema yasaka sherwani nan, dan murmushi kawai yayi, ahankali ta shafa kanshi tace "nagode kaji, ka rike amana kaji, ka kulada matarka, Uncle dinka ya shiga villa wai yanada meeting da president saisa baka ganshiba kafin anjima by 8 yatafi Airport dan jirgin su 10 zai tashi" gyadamata kai yayi kafin yatashi ahankali kan jikinta da sauri tace "ina zaka?" ahankali yace "waya zan dauko nakira blood" shiru tayi tareda binshi da kallo kaman yautafara ganinshi, wayan yadauko yadawo yay fillo da kafafunta ya kunna wayarshi yay dialing number Arham wayan yaji akashe hakan yasa ya ijiye wayan Ammi dake binshi da kallo tace "ya akayi? Baka sameshi bane?" dan tabe baki yayi yace "wayanshi akashe" gyadakai Ammi tayi tace "maybe yagaji ne ya kashe wayan dan ya kwanta yay bacci, yasha hidiman bikinka, tunda bikin ka yazo bawan Allah nan bai huta ba" murmushi yayi daya wani irin karama fuskarshi kyau ashagwabe yace "Ammi kinsan menene?" da sauri Ammi ta chusa hannunta agashin kanshi tahau shafawa tace "menene Waleed dina?" dagokai yayi ya kalleta yace "wlh am missing the orphanage so much, yau kawai dabanje be jinake kaman nai shekara I can't stop thinking about those helpless children I know kowa na kewana barinma the little ones" murmushi Ammi tayi sosai ta cigaba da sosamai kai tace "that is why am a proud mother of this hard-working young man, My doctor, I know you are missing dinsu saisa nima I got a surprise 4 you" da sauri yatashi ya zauna ya kalleta yace "suprise Ammi namene?" dan dariya tayi takamoshi ya kwanta tace "to sarkin azarbabi koma ka kwanta" gyara kanshi yayi akan cinyanta yana murmushi itakuma ta maida hannunta cikin gashinshi ta cigaba da massaging tace "kwanaki kafadi mini on the 8th ne zakuje excursion da yaran gidan marayunka a Yankari ko" gyadamata kai yayi tace "so I checked my date sai nagama ma next week ne 8th, so I called the Yankari game resort namuku booking gabaki dayanshi from on the 8th to 16th, kadauki matarka duka kutafi and have fun, if seeing those children da zama dasu makes u happy then am ready to give it to you all, kuje kaida matarka da Arham da yaran all Allah ya tsaremin ku but zakadau bodyguard dinku, kuna dawowa kuma u can resume office" tunda take maganan yake kallonta ta mugun mugun faranta mai rai zai iya cewa acikin plenty gift din databashi da bakin nan nashi this is just the best gift, hannunta yama peck yace "thank you Ammi na, I love you so so sooo much" murmushi tayi ta dagashi tace "ni barni naje nai breakfast kaiba abinda ka iya dafawa balle na zauna adakinka kaje kitchen kamin girki" dariya yayi yace "Ammi Allah ki zauna namiki sakkwara da miyan kubewa" hancinshi taja tana dariya tace "yakuri son ban shirya cin mara dadi yau ba" da sauri yace "Allah Ammi" fashewa tayi da Dariya tajuya tafita kaman ba itaba inkaga dariyan Ammi da danta take. [11/1, 11:46 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ 🔟 _Kai Ango Daki!_ Wuraren 9 pm na dare motarshi dasukayo convoy datasu Arham da kannenshi sukai parking akatafaren gidanshi wanda za'a iya kira da aljannan duniya, dan ajiyan zuciya ya sauke kafin yakaranto wasu yan addu'o''i na Allah ya bashi sa'a yana kallon kofar da zai sadashi da ciki, knocking glass din motarshi da akayi yasa ya waigo ganin Arham ne yana sanye da wata mahaukaciyar gizna yasa a hankali yacire lock din kofar tareda bude kofan gabaki daya yafito, binshi da kallo Arham yasakeyi daga sama har kasa kaman zai cinyeshi saikuma yay murmushi yace "wanan kayan yan India sun maka kyau Waleed, nawane ma?" juyawa yayi ya kalli su Abdul dasuka fito daga tasu motar, jin hayaniyan su as usual dan gardama suke kan kwallo yace "I don't know Ammi order for it" daidai lokacin su Abdul sun karaso rike da manya manyan ledoji a hannayensu, Arham ne yace "kumu tafi mukaima amarya kajin amarcinta da angonta kartai fushi damu munzo munkuma rike matashi anan" yay maganan yana satan kallon Waleed daya ballamai harara, dariya yayi sukai hanyar shashin kaman bazai biyosuba saikuma yabiyosu yana biyedasu abaya bude kofan sukayi wani hadadden kamshi yamusu sallama irin kamshin dakin amaren nan, falon babban falone dake dauke da kayan duniya bin haduwan dakin duk suke da kallo kafin Arham ya shiga su Waleed biyeda abaya zama duk sukayi Arham ya kalli Waleed dahar yaciro waya abinshi zai fara dannawa ko ajikinshi yace "kaje sama ka kira mana madam din" ballamai harara Waleed yayi irin kama rainamin wayau kafin ya kalli Abdul yace "go get her" yunkurawa Abdul yayi zai tashi Arham yace "ina za'ai haka, yanzu dai dama dare yayi, ganin amarya maganta next time, ga abubuwanta nan ka kaimata, ku Kuma kutashi mutafi gida good night X-man" yay maganan yana mikewa tsaye da sauri Waleed yamike tsaye Shima ya kallai kana ganin shi kaga tashin hankali ranshi yabaci yace "Arham" gwalo Arham yamai yawuce yafita abinshi kannenshi biyedashi suka maido kofan suka rufemai, saidai yaji karan motocinsu direba yabude musu gate dukji yayi badadi kaman yabisu zama yayi kan kujeran tareda dafe goshi yakaranto addu'a hasbunallahu wa niimal wakeel saida yaji yadan Sami natsuwa sanan yadena karantawa sai kallon agogo yake saida yaga kusan 10:30 sanan yamike tsaye ya kulle kofar ahankali tareda sa hannu ya kashe wutan dakin ya rike ledodin yawuce sama, ahankali yabude dakin daya zamto shine nashi yanabin koina da kallo dakin komi na ciki fari kaman wani dakin president, ijiye kayan yayi yawuce yaje ya rage kayan nan dasuka damai ya shiga bathroom, wanka yayo sanan yafito yabude wardrobe din bangon dakin yazaro wasu pyjamas na maza milk masu shegen taushi ya shirya tsaf cikinsu yafeshe kanshi da sababbin turarukanshi da Ammi tasa aka sayomai aka jeramai dann sawa tayi akazo akamai nashi jeren, Mom ta turo tun 2days dasuka wuce dan bataso yanemi komi yarasa, fararen indoors slippers din dake ijiyemai ya saka yadauki ledojin yabude kofa ahankali yafito yana kallon kofar dakin Ilham gabanshi nafaduwa shibaima San tayaya zai dinga mata magana ba, tsayawa yayi abakin kofan dakin yakai kusan 5min sanan yasauke ajiyan zuciya yatura kofan ahankali kaman wanda bayaso yabude sanan ahankali yadaga kafa ya shiga, akwance yaganta kan makeken hadadden gadonta tana bacci taja bargo ta lulluba danko face dinta ma baya gani, wani wawan ijiyan zuciya yasauke ya ijiye mata ledojin agefen gado sanan ya kara dagakai ya kalleta ganin ko motsi batayiba yasa yakara tantancewa yes bacci take yajuya yay wurin kofa ganin wutan dakin akunne yake yasa yasaka hannu ya kashe wuta yamaida kofan yarufe mata yakoma dakinshi har wata yar murmushi yake kaman ansauke mishi lodin kaya dagakai kwanciya yayi Akan gadonshi yajawo laptop dinshi dann baijin bacci kasancewan yau yawuni agida babu inda yaje saisa yasha bacci sosai abinshi. Yana fita ta yaye bargon tareda goge dan guntun hawayen dataji yana zuwan mata, tazaci fa zaizo yatadatane dantun dazu taji shigowansu, amman yaki zuwa yakirata, hawayen tasake sharewa tace "wlh saimun kwana tare, I've been longing for this day, I need good fuck, I wanna make my first night as a married woman memorable" wayanta dake gefen gado ta dauka ta kalli lokacin sanan ta mayar ta ijiye taredayin kwafa. Tashi tayi tasauka daga kan gadon, handbag dinta datai amfani dashi ayinin biki ta dauka tabude, wani turare taciro dake cikin kwalban duri gawata yar faran takarda acikin turaren da aka rubuta Dr Waleed aciki, dudda ta shafa turaren dazu amman sotake takara shafawa, shafawa tayi ko ina ajikinta har afuska sanan ta ijiye a karkashin filonta taredayin murmushi tanadan juya ido, almost 5min tadauka sanan ta rangada wani uban ihu da kuka atare "Wayyo Allah na Mummy kunamu agidan da macizai, wayyooo Dady zasu cijeni" Kaman daga sama yanacikin aiki da system dinshi yaji ihu da kukanta kaman adakinshi takeyi tsabagen daga murya, kalman kunamu da macizai data fadi yasa da sauri ya dirko daga kan gadon yabude kofar dakinshi yayi dakinta yana tafiyan nan kaman zakin daya fito farauta, bude kofanta yayi tareda saka hannu ya kunna wutar dakin dakin yay haske, sake kurma uban ihu tayi kaman batasan ya shigoba tana kankame jikinta dake rawa sosai tana kiran kunamu da macizai da sauri yy gadon yaja blanket din ya zazzage ya yar yana bin ko"ina na gadon da kallo da kasa kafin yamika hannu shi kaman wanda bayaso yatabata ganin ta birkice bama tasan da shigowanshi ba yakira sunanta cikin muryannan nashi mai kashe mata jiki. "Khadija, Ilham" afirgice tasaki jikinta tabude idanunta ta kallai ganin shine yasa tasake fashewa da kuka tawani irin fadawa jikinshi ta kankameshi tace "baby kunama da snake wlh dayawa kaga kasheni zasuyi please karsu kasheni na mutum Umma na zata kusan mutuwa da Dady, wayyo kunama wani nabin bayana dubamin" a rude tasakeshi tajuya tareda dagamai red rigan baccin dake jikinta dakenan close to nothing ana ganin duk wata hallita na jikinta, kaman matsoraci ya kalli bayan ganin yanda jikinta ke rawa yasa yay ta maza yaja rigan yarufe mata baya yajuyo da ita tareda riketa yace "listen to me babu kunama agidan nan ko kadan, inma akwai to maybe a kayan da aka kawoki dasune, so stop being scared and go back to sleep maybe u just had a bad dream ne is not real, now go back to sleep kiyo addu'a ki kwanta ta bangaren damanki" yay maganan yana kokarin kwantar da ita a gadon, wani razanannen ihu tayi da saida ya firgita itama tagani dan ta kusan sakin dariya daga gani kasan mutum ne dabai saba da ihuba so baiso, fadawa jikinshi tayi ta rungumeshi gam tana gogomai fuskarta ahanci danya shaki kamshin turaren da kyau dan Maman Hydar tafida mata inhar ya shaki turaren nan bazai taba iya barinta bane turare ne dake sama namiji yaji yana bukatar matarshi bukatar da baya iya jurewa barinma shi da musamman tabiya kudi mai kyau dan amata nata da sunanshi dan Sarai tasan baya sonta iyayensu suka hada auren itakuma wani irin mahaukacin sonshi Allah ya daura mata kaman tahadiyeshi, manna ma fuskan nata tayi ahancinshi tana dafa kafadarshi tace "Wayyo baby kaga suna cizona please mufita daganan" wani iri dayaji yanaji yasa yatureta da saurinshi cikin wata yar kasalalliyar murya yace "u had a dream just sleep Khadija bakomi anan" yay maganan yana sauka daga kan gadon yajuya da sauri yay kofa dan baison taga erection daya fara having wani irin abune haka kawai dantasan shiga jikinshi shikenan sai yay having erection gosh! This is so embarrassing wlh, yay maganan yana shiga dakinshi tareda kashe wutan dakin nashi yahau kan gado yadaga laptop dinshi yasa a side drawer yana tsaki yadaura hannu shi kan joystick din yarike gam maranshi na juyawa yace "wats this please? Mtsw......" bai ida jan tsakin ba yaji anbude kofanshi anshigoda gudu ana kuka kaman wacce akama mutuwa, maida kofar tayi tarufe tana kuka sosai tace "Baby wlh bazan iya kwana ba innalilllahi ni gobe zaka kaini wurin Mummy na da Umma Wayyo babanna" saikuma ta buga tsalle tace "Wayyo wani akafata" kafin kace me tabuga wani mahaukacin ihu tahau kan gadon before yay wani move ta dane kan jikinshi ta kankameshi gam gam kaman zata bulashi jikinta na rawa. "innalilllahi wa inna'ilaihi raji'un" kawai yake ambata aranshi yama rasa mezaiyi wata irin mahaukaciyar sha'awa yakeji da tunda yake arayuwanshi baitaba jin irintabba, wani irin farin cikine ya lullube Ilham dan sosai takejin erection dinshi na mikewa a daidai takan cikinta yana wani kara mikewa yana harbawa kaman zaici cikinta wani mahaukacin dadi ne yakasheta namiji duk shekarunshi baya nunama mace wayauba yaro kace baka sona amma bakaki sha'awaba yanzu, dole tama Maman Hydar kyauta gobe wlh Maman Hydar tabiyata, tamata komi aduniya, dan misilin turaren nan data rainane yay aiki haka, murmushi tayi tace time for my next move, wani irin ihu tayi ta zabura daga jikinshi ta tashi zaune tace "Waleed kaga snakes din sunbiyoni nan zoka ganshi" tana maganan tasa hannu ta damke manhood dinshi gamgam, Oh lord of heaven! Fantabulous! daman she always picture his dick to be big but bata taba kawowa it will be as big as this ba, thick huge and long, rikewa tayi gam ta matse kan tawajajen hujin tace "kaganshi" wata malalacin kara yasaki dan a woman has never hold this dick in his life before yace "auuuch stop that, let it go, is me Ilham" yanda yay maganan ashagwabe yasa yay wani irin melting heart dinta omg this guy is sexy, da gangan tai stroking manhood din ta wandon tawani karkadashi tace "no macijine gashinan naroketa gam zoka gani Waleed mukasheta" kaman zaiyi kuka jikinshi yahau rawa mika hannunshi yayi yature hannunta dagakai yace "stoooop, gabana kike rikewa not any kunama or whatever u call it" yay maganan kaman zaiyi kuka ya sake rike dick din tareda komawa ya kwanta cikin shi na ciwo, brain dinshi namai wani iri shi he can't have sex da macen da baiso baya iyawa gaskiya saisa koda yana school baiyi iskanci ba dan gaskiya bazai iya kwanciya da macen da he don't have feelings for ba. Ganin yanda yay wani irin yaushe yajuyamata baya yasa ahankali ta taho, zagayowa tayi ta gabanshi ta kwanta kaman zata shigeshi ahankali tace "sorry Dr bansan abinka narike ba I tot kunama ne, did I in anyway hurt you?" tai maganan cikin wata salo tana shafamai jiki ahankali tanamai susan katangare (waiwayi) , wani irin ajiyan zuciya ya sauke yakabar da hannunta yace "a.....m f.....ine" ahankali tamika hannunta ta karbe hannunshi wanda ta lura ya kama dick din dashi kaman batasaniba ta rike gam sanan ta matsoshi kaman zata shige jikinshi cikin wata seductive voice tace "ashe kadawo banma saniba nai bacci, how do you feel today Dr? Today is the happiest day of my whole life, I got married to the man I love, my parent choice, wlh ko Dr Ina sonka somai yawa" all this maganganun nan datayi baya jinta dan kanshi yafara juyawa sai uban jikewa dayakeyi sabida yanda take tabashi, kuma yaki koda kama hannunta, mannamai manyan boobs dinta tayi a kirji takai hannunta tana shafa face dinshi da gemunshi daya dade yana biyamata rai kafin ta saukar da hannunta kan lips dinshi, wani pos tayi tasaki ajiyan zuciya, wayannan lips din are the first thing data faraso a jikinshi lips dinshi pink sosai gasu taushin tsiya kaman katifan daya nikeda ruwa, a hankali ta daura fuskanta kan nashi cikin wata irin murya tace "I want to kiss my Dr, Dr this is our first kiss" Tai maganan tana daura bakinta kan nashi ta sakinmai wata irin light sharp kiss da saida yaji yanda yay ijiyan zuciya sanan tazare bakinshi tana kallon shi dudda ba haske amman tasan amugun bukace yake ganin yake nishi amman yaki tabata yasa tasake murmushi takai bakinta kan nashi tace "your lips taste good" ta shiga kissing dinshi kaman mayya tana tura harshenta cikin bakinshi tana laso ko"ina kafin in style ta turashi ya kwanta yana kallon sama ta yanda zata hau kanshi, Hawa kanshi tayi ta zauna kan cikinshi tana kissing dinshi tana shafshafa fuskanshi tana gogamai manyan boobs dinta akirji dan tanada manyan boobs, ganin yaki tabata gawani bala'in sha'awanshi na cinta yasa takai duwawunta kan joystick dinshi ta zauna akai da sauri kaman wacce zatai riding dinshi kasa daurewa yayi dudda bakinshi nacikin nata saida yasaki ihun shagwaba "ohhhhcchh" murmushi tayi tasaki bakinshi tace "sorry Dr" cigaba da kissing dinshi tayi kafin tasauko tafara kissing face dinshi zuwa wuyanshi wutan sonshi nacinta tasa hannu tafara bude boturan riganshi ta zare rigan ta yar gabaki daya yamata yaushe kaman wanda yasha giya yabugu sauka tayi taja wandon pj shima ta yar ko damuwa batayiba takama kafarshi tashiga kissing rawa jikinshi yafara dan wani irin sarrafa shi takeyi da ba'a taba yimai irinshiba, yar rigan jikinta tacire tayar sanan tahau kan jikinshi ta kwanta ta kankameshi, jin mace akan jikinshi yasa jikinshi yadau bari hannunshi takama ahankali tadan karkace tadauramai kan boobs dinta ta matsa chapke boobs din yayi gam gam murmushi tayi tareda kumshe ido hannun Dr dinta akan boobs dinta feels out of this world, likitaco dasunyi suna wajen son sex dan mayune amman wanan dudda turaren ma kaman tsoron tabata yake yana wani bata wahala, hannunta takai ta kama manhood dinshi daidai takan crowns din daya jike baisan lokacin daya chapke boobs din dakyau ba yasaka Kara. "aah hhhhh" bankarewa itama tayi dan taji dadi ganin joystick dinshi is his weakpoint yasa tawani irin kama kan ta murza baisan lokacin daya wani zabura yamike ba jikinshi na rawa, fizganta yayi kaman ya fizge tsumma ya jefata agadon wani irin murmushi tayi na jin dadi kafafu ta yakama yahade yarikesu ahannunshi yadagasu sama jikinshi narawa yakaranto addu'an saduwa da iyali kafin yakai manhood dinshi yakai zai shige, ihu tayi zata tashi ya danneta ko motsi takasa faduwa gabanta ya shiga yi, dawani irin karfi ya danna manhood din ciki she is tight dan tight amman bai wani sha wahala ba ya shige ciki fes, wani irin nishi tayi tasan maza biyu in her life samarinta ne datana University, daya sunyi dating which is a normal thing a kasan waje inma baki dating keyar kauyece shine yafara daukan pride dinta, bayan kuma tagama school kowa yakoma garinsu sai saurayinta na biyu anan Nigeria a law school suka hadu sukadanyi sau biyu saitazo ta hadu da Dr tana ganinshi kuma taji duk duniya saishi ta rabu da Wayan nan, all this men bata tabajin Wanda ya shiga ciki tajishi ya cike ko"ina a irin Dr dan yanada kauri kaman wani murtiki. Sarai yagane he wasn't her first but he didn't really pick offense dan to him is a normal thing in this generation, banda haka he is a Dr, and yaga yanda ake rayuwa now a day koshi da yana so daya ci different pussies by now, countless. Cinta yafara na fitina a yanda jaraba ke cinshi ahaka yake saukemata all he knows is he is having sex with who he don't wanna have kaman something is compelling him to, ihu tafara jikinta koina rawa yake kaman zata sume hannunshi takama takai kan boobs dinta matse matashi ya shigayi tana bankarewa, ahaukace yake hakkanta duk inta takai hannunshi tabamata yake takai kanshi kan boobs dinta gadinga Sha dan he really lost it, yadade ahaka sanan ya kawo bayan ta bala"in gaji ta rungumeshi tana sauke ijiyan zuciya. Within 2min da gamawa yakara chaji yatashi kifeta yayi doggy yafara sosai take farin ciki ashe dai Dr jarababe ne, he eat her pussy damn good dan har kukan dadi take ta tabbatar aurenshi was worth it, yakai almost 2hours sanan yay releasing. Kaman zata sume numfashinta har sama sama yake dan cinta yake kaman mahaukacin doki nishi tahauyi tace "Wayyo Dr nagaji, kacika girma kajijjimin ciwo wlh I can feel it" ko kala baice mataba yanajin yanda take murzamai nipple da hannu daya, dayan hannun tana shafa joystick dinshi dako alamun kwanciya bata yiba, tadan huta nakusa 10min danhar bacci yasoma Kwasheta tana cikin shafashi sanan yatashi, azabure ta bude ido janta yayi ya hau kanta ya shige zuruf yafara, at this time ruwan ta ya kare, sex din became so painful tafara kuka tana rokanshi amman baima saniba dan baima hayyacinshi. "Baby please kadena I am tired, nagaji, washhh, mama" tafashe da kuka sosai, saida ya kwakuleta tass kaman abinda aka turoshi duniya yayi kenan ganin ana kiran sallan asubahi yasa yasaketa yatashi rushewa da kuka sosai tayi, kunna wutan dakin yayi ya kalleta kaman yanda itama ta kallai tasa hannu tana share hawayen ta tanabin jikinshi da kallo, gabaki dayanshi fari ne amman manhood dinshi bakin kirin, dauke Kai yayi daga kallon datakemai yawuce tsirrara ya shiga bayi ko a jikinshi, kwanciya tayi da kyar tana Kara bude kafafunta dan kaman yaziba mata barkono takeji, gawani sabon azababben sonshi tana tunani at least wanan is a good thing tunda taga kaman bai ganeba saita dinga tafiya agwale gwale da hujja itama as first timer, fitowa daga bayin yayi ya kalleta ganin ta kumshe ido yakarasa cikin dakin yana tsallake kayanshi data cire mai ta jefar ya shafa cream yanemo wata jallabiya ya shirya tsaf sanan yay hanyar kofa harzai fita saikuma yajuyo ya kalleta yace "stand up jeki wanka kizo kiyi salla before u sleep" yasa hannu zai bude kofan saikuma yajuyo yace "use hot water for the place zafin zai r...agu" yay maganan ahankali dan yasan he fucked her dukda ba lubricant which normally women finds it painful don sex ba lubrication is disastrous, yajuya yabude kofa yafita tashi, tayi da sauri ta zauna tana wani irin murna tace "bai ganeba wlh". [11/1, 11:46 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣1️⃣ & 1️⃣2️⃣ _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ FREE PAGE Cikeda farin ciki Ilham tawani irin tashi zaune tace "bai ganeba wlh, nakoma sabuwa again, wanan rebranding na Maman Hydar yamin aiki, wayyo Allah na mezanma Maman Hydar na biya ta, wlh she is the best mai gyaran jiki in this whole Abuja, gashinan Dr baigane ba haryana cemin I should use hot water" wani kayataccen murmushi tasaki tasauka dagakan gadon ahankali tanabin gadon da kallo tana kara tuna jiya, bathroom tashiga tayo wanka aciki sanan tafito daure da towel tana dingishi ita adole anmata kacha kacha, kayan su ta tsugunna ta tattara ta shiga bathroom ta watsa a washing machine dinshi sanan tafita tai dakinta tana murmushi, she can't believe that yau this man da tasha gani a dreams shine yau tayi making love dashi in reality, he is so sweet wato mazama haka suke da dadi daban daban kaman mata, tunane tunanen abinda yawakana tsakaninta dashi tadingayi tana shiryawa harta shirya tsaf cikin wata hadaddiyar doguwan rigan atampanta super wax yellow daya amsheta sosai ta zira hijabi tai salla. Tana zaune kan dadduma taji shigowan shi, saikuma taji yabude dakinshi ya shige, kasancewan bataga yazo nemanta ba yasa duksai taji ba dadi, tashi tayi daga kan dadduman takoma kan gadonta tazauna, wayarta tadauka tai dailing number Maman Hydar amman saitajita akashe, dan tsaki taja ta ijiye wayan ta mike tsaye, gaban madubi taje ta zauna tashiga yima kanta makeup tai kyau sanan ta kashe dauri tareda feffeshe kanta da turare tanayi tana tunanin abinda yawakana jiya, omg bata taba ganin namiji dat can f**k like Waleed ba, and his groan omg is tentalizing and entertaining duk in yamata saitaji kaman zata suma, ita kadai tana gaban mirror tanabin jikinta da kallo tana tuna yanda ta babbama Waleed different wurare yasha kaman wata landlady dinshi, door bell din falo dayay ringing ne ya dawo da ita daga duniyan tunanin dataje da sauri ta daga kanta ta kalli agogon bango taga karfe tara da kusan rabi na safe, zamanta tayi acewanta zaije and get the door jin ansake yi yasa ta mike ahankali taidan murmushi at least tayi using opportunity dinan ta ganshi, bari taje ta kirashi, bude kofan tayi tafito tana wani shegen dingishi ita adole anmata kacha kacha, gaban dakin Waleed din taje tabude kofan ahankali ta shiga da dan gajeren sallama kaman batason tayi, akan gado ta ganshi dagashi saidan boxer yay baje baje yana bacci abinshi hankali kwance kana gani kasan biyan bashina na jiya yake dan baiba, maida kofan tayi tarufe jin ana sake danne door bell din ahankali tai stairs ta sauka tana tunani halan Ammin Waleed ta aiko musu da abinci ne, danko jiya saida ta aiko musu dashi, da sauri takara ware kafarta sabida yan aikin su fadima Ammi condition din dasuka ganta dan tasan dantafa yay aika aika, ahankali takarasa wajen kofan tabude ahankali, hada ido tayi da Arham dake rike dawata katuwan basket mai kyau yana sanye dawata soft yadi mai ruwan toka daya amsheshi sosai yana baza wani uban kamshi kaman wani sabon ango ya gyara gashin kanshi dabaikai na Waleed yawaba dan Waleed nadan barin gashi, wani irin binta yake da kallo dan saiyau yamata kallo mai kyau baitaba ganinta in broad day light ba, murmushi tayi tace "laaaa our blood kaine, sannu da zuwa, shigo ciki tuntuni na barka tsaye sorry about that" tai maganan tana juyawa tanadan dingisawan kaman yanda takeyi dazu, bin bayanta da kafafunta Arham yayi da kallo harya shigo bayan ya maida kofan yarufe ya tsaya kawai yana kallonta batare daya shigo ciki ba, waigowa tayi jin batajin sahun tafiyan shi hakan yasa da sauri yadauke kanshi kaman ba kallonta yakeba yashiga yi kaman yana neman abu, kujera ta nunamai tace "zoka zauna please, ko kayi mantuwa ne?" karasowa yayi ciki ya ijiye basket din kan centre table yace "no, na dauka dai nai mantuwan ne Amarya bata laifi ko takashe dan masu gida, ga breakfast Ammi tabani nakawo muku" murmushi Ilham tayi tace "Allah sarki Ammi dabata wahala ba, ai banma taba tsaraban daya kawo jiyaba daman nai niyyan na gasa a oven ne muyi breakfast dashi this morning" murmushi Arham yayi yanabin ko'ina najikinta da kallo yace "kawayen Amarya ai zasuzo anjima suci kazan amarcin bahaka akeyiba? Anyway that aside, dau basket din kikai dining" gyadamai kai tayi tace "tom don't mind me ga abinda yakamata nayi nacikaka da surutu" tai maganan tana daukan basket din tajuya tana dingishi yabita dawani irin kallo yace "ba laifin ki bane naturally haka lawyers keda surutu, surutun ai shine aikinku" yay maganan still idanunshi akan bayanta, hakanan yaji ranshi na baci yanamai suya, Waleed yaudaranshi yakene yanzu? But ai Waleed bayamai karya koyaya ne halinda yasan Waleed baidashi kenan karya, yana fadimai gaskiya kodako zaoja musu matsala, ya gayamai bayason yarinyar nan and he can't sleep with wacce bayaso menene menene, but ya akayi just yesterday dasuka kawoshi har yanakin zuwa yakirata shi adole baisonta shine har yay amfani da this beautiful young lady haka. "mezan kawo maka blood, blood mezan kawomaka?" kaman daga sama yaji maganan Ilham ya fargan dashi daga dogon tunanin dayaje dagokai yayi da sauri yaga ashema tana tsaye gabanshi tana tambayanshi, ajiyan zuciya yasauke hakan yasa tace "lpy tunanin me kake haka?" kallonta yayi kuri kaman bazaice komiba saikuma yace "tunanin kyakkyawan amaryan blood dina nike" dan dariya tayi jin ya yabeta hakan yasa tace "wlh you are so funny and sweet now I see the reason why Dr na ke sonka, gashinan nima am already loving you dudda this is the first long conversation dakuma taba having tare right" gyadamata kai yayi yana kallonta still kaman wani sabon maye, kallonshi tayi itama suka hada ido eye to eye saikuma ya basar yace "wai inama rascal dinan sabida ya kwanta da mace ne yake biyan bashin bac........" kasa karasa maganan yayi yadan zaro ido dan baisan maiya kaishi sakin magana haka agabanta ba but surprisingly saiyaga tafashe da dariya tazauna a kujeran dake gefenshi tace "kai blood kadenama baby na tsiya" takara kyalkyacewa da dariya kana ganin yanda take dariyan kasan maganan banzan yamata dadi bama kadan ba, binta da kallo Arham yayi saikuma yatabe baki yace "kawomin ruwa nasha natafi" da sauri tai kaman zatai kuka tace "kai dan Allah tun yanzu bayan kasa nafara enjoying company naka, please stay longer kajira yatashi ku gaisa kafin katafi, bari nakawoma ruwa muyi gist, tell me about everything I need to know akan baby na, my Dr, abinda zanmai yasashi farin ciki da wanda zanmai yabatamai rai da wanda zan kiyaye, everything I wanna know, kasan magana nama babyna wahala, ammadai tukunna bari nakawo ma ruwan" tajuya da saurinta tana dingishi tai kitchen yabitada da kallo, fitowa tayi daukeda tray da bottle water kekai da cup takawo mai ta ijiye sanan ta zauna tace "ina jinka" bottle water yadauka yay sipping sanan ya ijiye yace "Waleed Waleed do I even have much to say about him?" ya tambayi kanshi yanadan juya ido yace "well in kinason fushin Waleed ki tabamai gidan marayun nan, anan yake zama lion dankoni inkinga munyi fada kan gidan marayun ne, in munachan so kawai yake we should all concentrate on our work, and abinda nasan Waleed yafiso kan komai aduniyan nan shine dat orphanage and home of disabled din dayay establishing, bayan parents dinshi that house is his first love" yay shiru kaman mai tunani yace "your husband is a good man, he love helping people he sick pleasure in that, haka Allah yayishi, and I believe shine Purpose dinshi in this world" wani irin rungume filo tayi tace "awwwn my baby is the best, and whatever he does I know he does it wat too good, I love him with all my soul and everything dake jikina" sake kora ruwa Arham yayi yace "yayi miki kyau" zai kara magana sukaji alamun bude kofa hakan yasa duk suka dagakai Waleed ne yafito yana sanye da jallabiya dayake in kafito kana iya hango na falo, ganin Arham yasa yay murmushi yay stairs ya shiga saukowa yana saukowa da sauri Ilham ta tashi tafada jikinshi ta rungume shi tace "oyoyo baby, good morning babyna, kaga Ammi ta aikomana da breakfast" sanan tajuya ta kalli Arham while smiling tace "your blood nata fadamin about you abubuwan da kakeso da wanda bakaso" dan kallon Arham yayi, Arham yadagamai gira yadauke kai, tashi tayi daga jikinshi tace "nakawo maka breakfast?" gyadamata kai yayi hakan yasa tajuya tai dining shikuma yakarasa yazauna kan kujeran da Arham ke zaune, kafin ma yay magana Arham ya matso yamai whispering. "naga bakasonta Dan yaron mom wanan da a first night kai destroying pussy haka da magana kenan" dan hararanshi Waleed yayi yadauke kai yace "tun yaushe kazo shine baka hayo sama katadani ba?" da sauri Arham yace "kai bakasan kayi aure ba what if na shigo kana abun" dauke kai Waleed yasake yi hakan yasada sauri Arham cikeda isgilanci yace "how does it feel?" wani shegen kallo Waleed yamai yace "what feeling?" sake matsoshi Arham yayi yace "the feeling of you are officially a complete man today kaci mace, how does it taste?" tabe baki yayi yaciro wayanshi zai fara dannawa da sauri Arham ya fizge yana dariya yace "saika fadamin, how does it feel and taste like?" kaman Waleed zai dakai yace "is normal, see the whole sex thing is overrated, me aciki? It's just okay and just okay kawai to me" dariya Arham yayi saikuma ya kama baki yace "iyye sannu dan iska ka gama kwakule yar lawyer matarka kamaidata tafiya haka kana wani cewa sex is overrated saikace bakaji dadi ba" sake tabe baki Waleed yayi daidai takawo musu breakfast din, sukaci sunata hira kodan ganin fuskan Arham ne yadan sake da ita yayi dan hira da ita sai wajajen 12 suka fita tare shida Arham din ganin kawayen Amarya sun fara zuwa. Da magrib ya shigo gidan, alwala kawai ya dauro a bathroom dinshi sanan yafita masallaci tareda Arham suka shigo gidan, Arham yace "Waleed I think nima aure zanyi, I can't tayaya zan zauna dakai kadai as aboki gashi kayi aure banda wajen zuwa sainaita zuwa wajenka aisai matarka tafara jin haushina, inda a gidanku ne koda yaushe muna tare a flat dinka" murmushi yayi dan yaji dadin maganan yace "someone is missing me I can smell it like mmmm" hararanshi Arham yayi, kafadarshi Waleed yakama yace "look blood, wanan gidan" yamai pointing gidan gabaki daya yace "is as much as you own just as much as is mine, banda haka idan da yau zan fadi namutu kai zan barma yarana da iyalina ka kulamin dasu, you can come to my house anytime, any day, u are always welcome wlh kaji, so come as much as u want nidai kawai for now kadinga zuwa orphanage kullum and take care of everything kafin next week mutafi excursion" da sauri Arham yace "Allah yakaimu and trust me our orphanage is in safe hands" shiga ciki sukayi sukasha hiransu, sai wajajen eleven sanan yamusu sallama yatafi Waleed yarakashi. Bayan sallan isha'i Fitowa daga wanka tayi sai farin ciki take, wasu pitch arnayen kayan bacci ta dauko riga da short tasaka dasuka bayyana komi ajikinta, tadauko turaren Maman Hydar jikinta har rawa yake tana kokarin bude marfin ya salube daga hannunta dake rawa yafadi a tiles ihu tayi kafin takama yakai kasa yafashe ya tarwatse, kaman zatai kuka ta kalli kasan, wasu hawaye ne taji sun cikomata a ido tace "wanan wani irin abune mtsww" da sauri tafita daga dakin tadauko tsintsiya da paka ta share tafita taje ta zubar a shara, sosai taji wani irin bakin ciki bana wasaba saikuma tace "gobe da safe zan aiki yanmata taje ta dubomin Maman Hydar din tunda wayanta baya shiga" tana zaune tanaji ya shigo ya kulle ko'ina kaman zai wuce dakinshi saikuma yabude kofarta daga bakin kofan ya tsaya yace "zan kwanta, do you need anything?" girgixa mai kai tayi tace "bakomi" dan murmushi yasakin mata yace "alright saida safe, say your prayer before sleeping" gyadamai kai tayi kaman kuka zai kufcemata tadaure, juyawa yayi saikuma yajuyo sabida yanda yaga tai wani iri yace "baki bacci ke kadai agidan kune?" surprisingly taji tambayan hakan yasa da sauri ta gyadamai kai, dan tabe baki yayi yace "muje to" da sauri ta tashi murnanta ma yaki boyuwa, kawai sabida Ammi yamata hakan dan yaga tanason yarinyar sosai, dakinshi sukaje kwanciyan ta tayi shikuma yawuce ya shiga bathroom yay wanka yafito ya shirya sanan ya kwanta, dudda yadan taso wani abu ya shiga tsakaninsu amman babu abinda yamata har gari yawaye yatadata yay tafiyan shi masallaci. Tashi tayi tana zuwa dakinta abu nafarko data farayi shine kira aje mata gidan maman Hydar, tun agidan kanwarta takira ta sanarda ita maman Hydar itada mijinta da yaran sunyi tafiya sunje vacation inji makotansu, bakin ciki kaman zata mutu, ranta taji dukya dagule. Wasa wasa haryau Friday tun ranan daya shigo daki which is Sunday first night dinsu babu abinda yasake shiga tsakanin su, bala'in sha'awan Waleed take kaman me cus she can't stop thinking about that day, shikuma bata a gabanshi, this days ma he seems very busy aiki kawai yake a system masallaci ke dagashi. Tana zaune tana kallo a falo ya sauko kasa kallonshi tayi cikeda wata salo tace "ina kwana Babyna" "good morning Khadija" ya amsa mata atakaice karasowa falon yayi ya zauna kusada ita hakan yabata mamaki sai kawai tai murmushi tajuyo ta zubamai ido tana kallon lips dinshi datakeji kaman ta lashe, dan murmushi shima yayi yace "ki shirya kayanki gobe zamuyi tafiya" dawata irin murna tace "tafiya Dr? Ina ina zamu?" ahankali yace "yankari we are spending a week at yankari" wani irin murmushi tayi saikuma tafada jikinshi ta sakinmai kiss awuya tace "thank you Dr, I love you so much wlh" gyadamata kai yayi, yace "anjima zamuje muma Ammi sallama" gyadamai kai tayi batare data sakeshiba yace "yanzu zan fita zan danje orphanage but bazan dadeba" gyadamai kai tasakeyi sanan tasake shi ahankali tana kallon fuskarshi, tashi yayi daga kan kujeran yace "bye" yawuce yafita. Yanda yafadi hakan yafaru sukaje gidan Ammi da daddare, Ammi kaman zata hadiye ta tahuta, koda zasu tafi tamammata kyauta sanan, tahadasu da abinci suka tafi, washe gari da sassafe bodyguard dinshi yadaukesu a mota sai airport, anan ta tarar da yara almost 80children anyi queuing nasu, yaran duka duka bazasu wuce age 8 zuwa 18 ba, suna sanye da uniform din orphanage din all of them looking so neat kaman kasace, maza da mata da ma'aikatan gidan marayun da Arham ne duk suna sanye da suit, booking Arik Air gabaki dayanta yamusu sanan duk suka shiga plane din, a bangaren business class suka zauna tareda Arham jirginsu yadaga by 7 daidai, dayake 1hr flight ne to Bauchi, jirginsu na sauka suka fiffito saiga marcopolo buses dinsu wanda tun jiya Waleed yaturasu zuwa Bauchi, shiga motan sukayi aka jasu har zuwa yankari sai kalle kalle take saida ya tabbatar da ankai yaran masaukin su sanan yawuce indasu manya suka sauka room 15 da 16, room 15 dakin Arham sai room 16 dakinsu, shiga ciki yayi yaja jakanta zuwa ciki, dakin yahadu bana wasaba an gyara an saka musu banner welcome Mr and Mrs Warbai ajiki, ajiye jakanta yayi yace "hope u like the place ko Khadija?" ahankali tace "yes I love it Dr thanks" tai maganan tana kallon fuskarshi sosai takeji kaman ta tashi ta rungumeshi wani irin bala'in sha'awa ne ke damuna da maranta har ciwo ciwo yake, ganin tayi wani iri yasa yace "da daddare zan fitada ke, yanzu zamukai yaran on their first assignment here, we do this excursion thing every year, if you need anything let me know, kokuma call the reception ga number su chan a ijiye, bye, za'a kawomiki abinci" yay maganan yana ijiye mata kudi akan cinya, ahankali tace "bye baby" juyawa yayi yafice ya shiga dakin Arham yafito dashi suka wuce. Ahankali ta tashi ta tsaya ta jikin window dakin tana kallon yanda suke jera yaran a mota, Waleed sai murmushi yake yana wasa da yaran, gaskiyan Arham ne his heart is really in this his work, ganin sunja motar sun tafi yasa taji kuka yazomata da sauri takoma tafada gado sai kuka, tazaci fa honeymoon yakawo ta, ita yanzu kuka kawai zatai tayi wai tayi aure mijinta bazai iya kwanciya da itaba, baya bata hakkinta, yanzu dawa zata hadashi? Ammi? zuciyarta yace mata no da sauri tace "Arham, yes zaiji maganan Arham" tunanin hakan yasa da sauri tadauki wayanta ta tashi ta zauna daman tuni ta karbi number shi, sako ta shiga turamai. _slm Blood, please inada wata matsala da tadade tana damuna, please I seriously need your help, please kabarsu kazo yanzu, karka bari Baby yasani I don't want him to know nafada maka please_ Sun kai first stop dinsu joint din ice cream yana karban ice cream yana bama yaran dasukai layi yaji sako hakan yasa yamatsa ya kalli wani ma'aikacin su Isa yace "cigaba da basu Isa ina zuwa" bude sakon yayi ganin sako daga Ilham, jiyayi hankalin shi yatashi tome yafaru? Fada sukayi kome? juyawa yayi yaga baiga Waleed awajen ba, ganin kawai bashi awajen halan yazaga bayada wasu yarane yasa da sauri yabar wajen dudda da dan nesa da inda suka sauka amman trekking yayi zuwa wajen, agaban dakinsu ya tsaya yadan sauke ijiyan zuciya sanan yay knocking, share fuskanta Ilham tayi ta tashi tabudemai kofan, bin idanunta yayi da kallo yanda sukai ja da sauri ya shigo dakin yamaida kofan yarufe yace "lpy? Wat happen? Maiya sameki kikai kuka haka? Meya miki? Maiya hadaki da blood? Dukan ki yayine?" duk ajera yajefo mata tambayoyin sabida yanda hankalin shi yatashi, girgizamai kai tayi tajuya zama tayi akan doguwan kujeran 3sitter kwara daya dake dakin ta nunamai gefenta tace "ka zauna" zuwa yayi yazauna ahankali yace "menene khadija maisa ki kuka haka?" wasu hawaye taji sunzo mata da sauri ta share tace "Arham naga mijina ya daukeka dan uwanshi saisa zan gayamaka maganan nan, please karikemin amanan mijina dan sirrin mune" tai shiru tace "Waleed da ni kasan hadamu iyayenmu sukayi, nita bangarena inasonshi sosai amman shi har yanzu bai fara developing mini feeling ba cause baima taba bani time ba" tai shiru tace "tun bayan tarrayan mu na farko a first night babu abinda yakara hadamu and and......" tafashe da kuka sosai tace "bazan maka karyaba dis days ban iya bacci am so horny, but shi ko ajikinshi baima bani time ba balle yasan wani hali nike cikiba, nagaji am loosing my sanity, and tun bayan aurenmu bai karamin maganan aikina ba am sure da ina zuwa aiki nasan da bazan damuba sabi da aiki zai daukemin hankali, but kullum muna gida daya tare ina ganinshi ko hannuna bai rikewa saidai ni in rike nashi kuma bazaice komiba" tafashe dawani irin kuka tadaura hannayenta kan fuskanta, wani iri Arham yaji yanaji, wanan kyakkyawan yarinyar ne ta tsaya tana kuka sosai haka kan Waleed, yarinya mai aji haka, gaskiya Waleed yasami duniya dayawa, Allah yabashi komi saisa yake yanda yaga dama, ahankali yakai hannunshi dake rawa yarike mata hannu tareda janye hannun daga kan fuskanta hakan yasa da sauri tadago da rinannun idanunta ta kallai, kaman zaiyi kuka yajanyota zuuuu ta taho dab dashi harsunajin numfashin junansu, lips dintane suka fara rawa zatai magana ya girgiza mata kai yace "shiiii" sanan ya manna forehead dinshi da nata yakai hannunshi kan wuyan ta dan daman doguwan rigane ajikinta ta daura dankwali aka, kaman amafarki taji Arham yadaura bakinshi kan nata daya fara wani irin rawa yasaka cikin mouth nashi yashiga kissing dinta passionately kaman zai fasa bakinta yana kallon kwayar idanunta, hannunshi ya janye daga wuyanta ahankali yashiga saukar dashi kasa ya saukar da hannayen kan boobs dinta duka biyun dake cikin bra yakama ya matsa da karfi wani irin nishi tayi saikuma tabude idanunta da sauri tareda kabar da hannunshi ta fizge bakinta zatai magana yadaura yatsanshi kan lips dinta yace "I need you to trust me Ilham nasan minake yi, I am Waleed blood, Waleed yarone har yanzu baisan maiyake yiba sabida yatashi cikin gata, he is just 28 danyan kai jagab gareshi how do you expect daman yamiki yanda kikeso bayan baisan value dinkiba, saisa ya raina kowa, baiganin kowa da gashi, ganin mata yake kaman sabbin kaya yadauko duk wacce yakeso duk lokacin dayaga dama yay amfani da ita sanan yabarta yakoma wurin wata sabida yanada kudin, he don't love you not just that baimaso auren ba dan bai shirya ba, so yake yaci duniyan shi cus babu abinda yarasa, bai ganin darajan ki sabida yasameki tsaleliyar mace dake haka a araha, just look at matsalan daya sakaki, dakije kifada ga halaka ko wata bad hanya, gwara ni na taimaka miki, is just for today, sabida duk wani hornyness din yatafi kafin nasan yanda zan bulloma Waleed, I want you to relax kinji, I love you so much banso anything yadameki, bansanki tunda ba but the first day dana ganki naji I care for you, najiki kaman kanwan dabanda shi, naji I will love to have a beautiful, pretty educated young lady kaman ke dazanyi rayuwana da ita but nasan bazaki kallen ba sabida ni banda kudi kaman Waleed, and inhar inada maganin damuwanki zan baki waraka Khadija, relax no one is gonna know about this I give you my words, just between us, u are educated ke lawyer ce anytime that makes u happy go for it, am willing to give u myself freely namiki alkawarin nan sabida damuwarki tawace, any day dakikaji kinaso just call me kome nake zan barshi bazan taba barinki cikin damuwaba" wani irin fadawa jikinshi tayi tafashe da kuka sosai, yatsanshi yadaura kan kunnenta ya shiga mata waiwaiyi da sauri tawani irin hau kanshi tazauna kan kafafunshi, murmushi yayi yasake daura hannunshi kan boobs dinta ya matsa da karfi yace "kinada wayan nan abubuwan ne Waleed ya tsaya jan aji baya holewa dake" yay maganan yana sake cupping dinsu Yana matasawa, wani irin bankarewa tayi tace "wasssshhhh kashamin please blood help me" da sauri yadagata dogon riganta ya tattara yay sama dashi yacire ya cillar yadagata tsaye yabi farin jikinta dawani mayen kallo from head to toe, tana sanye da black bra da pant gata da manyan boobs, wani murmushi ya tsugunna yasa kanshi a tsakanin kafafuwanta yadaura bakinshi kan pant dinta tawajen yahau cizon gabanta yana wasa dashi ta saman pant, lumshe ido tayi kafafunta na rawa tadaura hannayenta kan saman kanshi tace "wayyo please karka dena, innalillahi" Jan pant din yayi kasa yadaura bakinshi kan gabanta yanakara ware kafarta yashiga zuko ruwan yanasha, kasa jure tsayuwan tayi tai baya zata fadi da sauri ya kwantar da ita akasa yahau kan maranta yazauna ya cisge bra yayi ya yar, yawani kwanto kan saman cikinta ya kafa mouth dinshi kan boobs din ihu tayi ta danne kanshi akai tana birgima akasa "wayyo Allah, blood zakaciremin kan nono, wayyooooo ni" kankame kanshi tayi kan nonon kaman zatai suffocating dinshi, jin wayan jikinshi na vibration yasa da sauri ya saketa itama tashi tayi zaune idanunta sunyi jajir, duba wayan yayi yace "Waleed ne" da sauri tafada jikinshi tace "innalillahi na shiga uku" murmushi yamata yace "relax I will handle it" sa wayan yayi a kunne yanadan gyara murya yace "Hello" cikin dan fushi Waleed dakechan yace "wai ina kajene u just disappear" dan juya ido yayi yace "nai mantuwa ne a dakina, yanzu zan dauka na juyo" cikin fushi Waleed yace "ni inka taho kasame mu a zoo bazamu tsaya jiranka ba" da sauri yace "ohh okay, will meet you guys there" katse wayan yayi ya ijiye, hannunta yakama yarike yace "ur secret is safe with you u can always count on me Ilham" ya shiga kissing dinta saikuma yasaketa yamike yana cire kaya yace "relax ba yanzu zai dawoba inhar bana wajen bazai taba iya barin wajen yaran nanba so bazai dawoba" tubewa yayi tsirara tabishi da kallo aranta tace "not bad but baikai Waleed dinta kayan aikiba, nashi siririne mai tsayi, na Waleed kuma murtiki ne mai tsayi" dukowa yayi ya dauketa kaman wata baby yajefata kan gado yace "lemme f**k you akan bed din da Waleed zai ciki" yahau kanta suka shiga kissing juna tana shafa bayanshi, boobs dinta yakama ya damke cikin wata irin shakakkiyar murya tace "dan Allah kacini, gabana na zugi" ware kafanta yayi yadaura kanshi wajen yafara bata head, haukacewa tayi dan saida ya taushe mata baki kar ajisu, saida takusan suma sanan yadage ya shigeta yana lumshe ido, yadade bai having sex ba, wani irin kankameshi tayi kaman zata koma cikinshi tace "wayyo Allah na dan Allah karka dena wlh kafishi iyawa, wayyo bugamin ita chan ciki, kashamin nono, Arham wlh zan mutu zan mutu wlh" sosai Arham yaji dadinta she is warm and sweet but not that tight dayay expecting to be honest, babu inda bai tababa yace "Waleed" sosai yay ramming dinta saida takawo da dan jimawa sanan yafara gurnani zai kawo zata tureshi gudun karya zuba aciki ya danneta yace "Waleed yazuba aciki nizaki kora waje" kaman zatai kuka tai shiru, dagata yayi yadau rigan datacire yashare joystick dinshi yadau boxer dinshi ya zura da kayanshi yamaida su tsaf sanan ya kalleta ganin tai lamo agado yace "kitashi kije kiyi wanka, bari natafi da sauri, zamu karasa maganan anjima" fita daga dakin yayi tai shiru tana tunani, me tayi yanzun nan? She just slept with her husband besty duka duka 1week da aurensu, she cheated on her husband wace irin mata ce ita akan kawai mijinta yay kwana 6 bai sadu da itaba bazata jureba kodai daman chan tana sha'awan Arham ne? Dan shima he's a cute guy wlh, Da sauri tace "no bana sha'awan shi" kasa koda motsi tayi takai kusan 2hrs ahaka sanan ta tashi tashiga bayi tai wanka tafito ta gyara gadon ta diddirje inda suka bata da dankwalinta tana tuna abinda Arham yamata. Da magrib ya shigo, yana rikeda wani katon jaka, itada dazaran ta ganshi zata rungumeshi kasawa tayi tana kwance tana kallonshi kawai, har gabanta yazo ya ijiye mata jakan yace "a gift for the lady of the house" murmushi tayi ta tashi ta zauna tadauka ta shiga budewa shikuma yay bayi, English wears yasayo mata sai wata yar karaman akwati data bude taga dan kunne ne aciki mai kyau, murmushi tayi sosai ta bala'in ji dadi ta ijiye, yafito yafice mosque sai wuraren 9 nadare suka shigo tareda Arham, hada ido sukayi da Arham dasauri ta sauke kanta kasa takasa kallonshi, koda sukaci abinci kasaci tayi da kyau, duk Waleed na lurada ita, wuraren 11 yatafi tai shirin kwanciya ta kwanta while Waleed was working da system ahaka bacci yay awon gabada ita. Cikin dare taji ana shafata hakan yasa tabude ido Waleed ne tagani, rungume ta yayi yace "jikinki zafi baki da lafiya ne you look somehow today, menene" kasa magana tayi tai shiru, sosai yaji he's feeling bad hakan yasa ya shiga yan wasanni da ita, rungume shi tayi tsam tsam tafashe da kuka tace "Waleed wlh I love you so much, please kasoni kaima" gyadamata kai yayi ta shiga kissing dinshi maida mata da martani yayi kafin tasakeshi tacire kayanta tayar ta taimakamai yacire nashi, yadanyi yan wasanni da ita kafin ya shigeta, ihu tayi danji tayi kaman zata barke, he fucked her damn rough, he felt she's a bit loose not tight kaman da, saisa yayi yanda yaga dama harda kukanta sanan ya kyaleta yasauka yaje yay wanka yafito yay sallan asuba adaki dan he missed it, tashi tayi itama taje tai wanka da kyar tafito tai salla, tana idarwa tahaye gado tagaji, ga mamakinta saitaga yakara zuwa kaman zatai kuka tace "Baby u just finish" shiga ciki yayi yace "am not okay" sosai yayi dan saida Arham yay knocking yace "Waleed where are you we are late?" da sauri yadagata muryanshi a shake yace "just go ahead zan sameku achan" Arham jiyayi ranshi yabaci sosai dan yasan me yakeyi hakanan jikinshi yabashi yawuce yatafi duk zuciyanshi ta lalace dagata yayi yay bayi ko kadan bai gamsuwa, that satisfaction da akace namiji yanaji bayan sex baiji, tsaki yayi ya shirya agurguje yamata bye yatafi. Bodyguard dinshi yadaukeshi a mota yakaishi chan wani fili mai kyau dakenan gabanshi akwai ruwa aka gyarama yaran and staff dan zasuyi painting competition, sauka yayi daga mota yaga already ana rabama yaran da staff din painting board, murmushi yayi ya kalli agogon shi yace "our judges are on their way coming to see your work and we choose our winner, yay taking all the prices so give it your best" atare sukahau tafi, shikuma yawuce wajen Arham dake rabamusu materials yace "hey blood sorry nai latti" tabe baki yayi yace "nidai muje musami waje muyi namu painting din" karban board dinshi yayi da abubuwan painting din sanan yajuya yay wajen wani bishiya da aka ijiyemai kujera, zama yayi ya kafa drawing board din, shikuma Arham yay wajen staff ya shiga cikinsu dan ayi shagalin dashi duk akai tsit kowa yafara painting. Waleed yadade yana kallon board din kafin yadau brush yalakato painting yafara zane, karan jirgin sama sukaji all of a sudden kaman akansu hakan yasa both yara da manya aka dagokai ana kallon sama daga yaran har staff, jirgin samane kasa kasa kaman wanda zaiyi landing, dagokai Waleed yayi ya kalli jirgin, kara jirgin kofan jirgin yabude yayi hakan yasa yara sukahau ihu suna gudu, wani akwati da Waleed yaga an jefo daga cikin jirgin yasa yay ihu. "take the children out of this place, evacuate something is going on" akwatin yafado cikin tsakiyan rafin ruwan wajen. Wanan kenan!!! [11/1, 11:46 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫_*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣3️⃣ _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ FREE PAGE _*MOROCCO 🇲🇦*_ _Hausawa sunce sannu sannu bata hana zuwa! Saidai......_ Yau babban ranace ga Ahmad, Widad da iyayensu dan babu wanda ya runtsa cikin dare dan ayau zasu aurar da yaransu da misalin karfe sha'adaya da rabi a katafaren mansion din gidan mahaifinta, inda Family mijin zasuzo ahadu ayi wasu shagulgula da wasanni naban mamaki kafin a daura auren sanan kuma a cigaba da daurin auren. Gidansu Widad duk inda kasaka kafarka mutane ne, ko bikin yar shugaban kasan morroco za'ayi albarka, mutane kaman kudaje sabida mahaifinta mutumne mai farin jini da taimako, Babanta yadauko mutane da dama, tun daga kan masu mata cultural gyaran jikinsu da wankin kafa da hannu, sanan gyaran kai, ga kayan dazata saka yau tai amfani dasu ancire matasu tsaf an ware masu hotuna nata dukansu, kayanta da komi dazatai amfani dasu designers ne da aka kashema zunzurutun kudi kaman baza'a mutuba, batai aureba ma mahaifinta yakashe mata dukiyanshi balle yanzu da dalili auranta, ai sai inda karfinshi yakare. Tun bayan tai sallan asuba tana sanye da plain dogayen rigunan nan nasu na bacci ta nannada gyale aka hannunta rikeda charbi tafito sadaf sadaf tahau rooftop din gidansu, zama tayi a spot dinta ta tankwashe kafa tana kallon sama, yan turarin nan dake fitowa da asuba hade da wata ta kalla, takai kusan minti 10 ahaka sanan cikin muryanta mai dadin sauraro tace "Mahaifiyata"! saikuma tai shiru ta saukar da kanta tadan dau lokaci ahaka sanan takara dagokai tace "Ummy I know duk inda kike kina janna ne da izinin Allah, and I am sure you've been watching over me, kafin kimutu I promised you da I will be a good hard-working young lady that follows her dream, a gurl who let her mind guides her not her heart, you always say this words to me that I called Ummy golden words _"Widad this heart is bias, don't let it rule you, let the mind rule your soul"_ tai shiru tareda dan share hawayen daya zubomata dan batason tai kuka yau ranan bikinta tace "Dearest Ummy, innace akwai ranan dabanyi tunanin ki ba nai karya, I think of you everyday, I miss abincin dakike min ki ijiyemin a kula inadawo daga makarantan sanawiyya, I miss kamshin ki, I miss komi naki saisa Ummy ban fadami ma Aby ba but I promise myself I will dress in your cloth ayau ranan bikina, Ummy I miss you so.....m..uch" muryanta yafara rawa tace "mutum bazai taba gane maraicin uwaba sai inhar kai rayuwa da ita, ka girma da ita, kasaba da ita thinking she will be with you har karshen rayuwanka rana daya kwatsam ta rasu! Kafara rayuwa bata aranan zakasan cewan rayuwanka tai gibin da babu hakorin dazai cikeshi, I miss you so much Ummy" tafashe da kuka nakaman 1min saikuma ta share fuskanta tass tai murmushi tace "sorry Ummy I promise bazan kara kuka ba but ina tayi ko kiyakuri" taidan shiru tanadan cizan lips dinta kafin ahankali tadaura hannunta kan kirji tace "anytime nahau kan rooftop dinan sabida kene dan yana tunamin dake, I remember lokacin tun ina yar karaman yarinya koda fita nayi nadawo nan zan hawo da gudu inbangan kiba ina kuma zuwa zan ganki kokina zaune kina kallon gari kokuma kina kwaba kullin flat bread dazaki mana, bayan kin rasu duk in nazo wajen nan hakanan I feel your presence anan hala sabida is your favourite place ne kema saisa nike jin hakan" tadan numfasa tace "Ummy today mark a day da I will embark on a new journey of life, jiya ko runtsawa idanuna basuyiba I am so restless, I am so so scared Ummy, banda sukuni tun jiya da daddare haryau" sama tasake kallo tace "Ummy haka kowace mace kejine ranan bikinta?" saukar da kanta tayi tareda dan murmushi tace "gabana nata faduwa Ummy but I know duk tension din bikin ne da rashin ki anan nasan inda kinanan dakinyi guiding dina, but kinsan wani abu Ummu?" taidan murmushi tace "karkiji komi cus am surrounded with so much love, Aby, Amah, Ahmad gakuma Sabeeha Ummy you need to see yanda take taimakamin da komida nikeso dudda mahaifiyarta batasonmu tare but bata damuba Sabeeha has been so so good to me lately" tai murmushi tace "and I am grateful for everything, Ummy I come to ask a favour from you" tai murmushin nan gwanin ban sha'awa tace "just watch over me kinji, always be with me nasan inhar u are with me babu abinda zai samen, I love you Ummy, Allah ubangiji ya jikanki ya gafarta miki, Allah yakai haske kabarinki Allah yasa kin huta yasa aljanna ce makomarki" da Ameen ta amsa ita kadai zata sake magana aka kwala mata kira. "Widad" da sauri ta juyo Sabeeha ce tacigayu cikin wata jada bakin blouse na mata, tace "wai me hadinki da rooftop ne kinsan karfe nawa kuwa? Kowa na gida ya shirya ke kinanan Amarya har yanzu sanye da kayan bacci, karfe sha daya fa za'a daura yanzu is 20min after 9" ware idanu Widad tayi sai yanzu ma ta lura gari yawaye sosai ita datake nan tun duhun asuba, da sauri ta mike Sabeeha tace "yi sauri zomuje ki shirya" gyadamata kai tayi tace "to, Sabeeha kinyi kyau" shafa kumatun ta Sabeeha tayi tace "kema haka kinyi kyau dudda ai bakiyi kwalliyan ba" dakin Amah suka karasa agurguje akasa tai bayi tai wanka tafito sanye da bathrub, Amah ta watsa mata harara tace "yarinya sai shegen nawa keda yakamata ki riga kowa shiryawa kece ta karshi jibi goma saura" turobaki tayi ashagwabe tace "Amah wai banace kiyakuri ba, aifa bansan lokaci yawuce hakabane fa ko Sabeeha?" da sauri Sabeeha tace "Amah bafa tasani bane kuma tabaki hakuri kinki kodai kishi kike zata kwacemiki Ahmad dinki" fashewa akai da dariya harda masuma Widad din makeup, sanda Amah ta shiga nema hakan yasa aguje Sabeeha tafita daga dakin tana dariya, Widad kuma ta gimtse dariyanta kafin Amah ta rafka mata sandar. Wuraren 11 aka gama shiryata tsaf cikin lebsa r'batia blue(sunan kayan), yanada mugun kyau kayan dogon rigan ne daya amsheta, kalan blue da fari, kunnenta yaji hadaddun yan kunnaye hannayenta da warwarori na zinare, farin gyalen amare Amah ta dauramata kan saman gashinta da aka gyara tsaf sanan tajuyo tamata kiss cikeda so tace "zauna anan dan Amarya bata fitowa akafa, bari naje chan tsakar gida wajen su babanki, yanzun nan neggafa asisitance zasuzo afitar dake, I love you" murmushi tasakin ma Amah tace "jazakillah Amah" gyadamata kai Amah tayi tana dogara sandarta tafita, babu kowa aciki kowa na waje dan nanne ake bikin, duk yan ciki sun fita sabida Aby na raba kyauta. Tana zaune shiru adaki tana kallon kanta a madubi ganin kyawun datayi yay yawa sai kewan Aby take sabida tun safe bataga Aby ba gashi aka'ida Amarya bata gani iyayen ta sai an fitar da ita acikin (amaria) a kaita wajen daurin auren dan Amarya bata tafiya da kafanta, tana cikin yan tunane tunane ta akai knocking kofar dakinsu faduwa taji gabanta yayi da sauri tajuyo tareda bada izinin shigowa wani ma'aikacin gidansu ne ya shigo yana sanye cikin wani uniform blue da purple, cikeda girmamawa yace "ga amaria ne abakin kofa anbamu izini mufito dake baya, Aby nason magana dake kafin mukaiki wajen daurin auren, motarshi na wajen" murmushi tayi tace "Aby" gyadamata kai yayi yace "bismillahi" mikewa tayi ahankali cikin blue embroidered dress din lebsa r'batia tasake kallon kanta amadubi sanan ahankali tafara tafiya, bude mata kofa ma'aikacin yayi tafita anan taga maza guda shida, dama a adaltance maza bakwai da ake kirada negaffa assistance ke daukan Amarya bayan ta shiga cikin amaria su daura hannayen abin akan kafadarsu sukaita chan wajen daurin auren, bude mata kofan sukayi ta tsugunna ahankali tashiga ciki ta zauna tare da tattare kasan gown dinta, cike da girmamawa yace "kin zauna da kyau? Are you comfortable?" gyadamai kai tayi tace "Alhamdulillah thank you" maida kofar yayi yarufe sanan yasauke labulen daya rufe kofan tabaya da akama ado ta yanda babu wanda zai iya hango amarya, daukan kafafuwan sukayi suka dagata sama suka daura akan kafadunsu instead of suyi tsakar gida sai sukai kitchen da ita, bude kofan bayan kitchen din sukayi suka fice babu kowa ata wurin, sanan suka cigaba da tafiya sukai gate din dake ta wurin bude gatedin sukayi suka fita, babu kowa ta wajen sabida daman Babanta yasai filin wajen babuma mutane sai wata katuwar bakar mota dake wajen, karasawa sukayi har gaban motan sanan suka sauketa, suka bude tafito ahankali, kallon wajen tayi sanan ta kalli daya daga cikin motar mahaifinta data gani awurin a pake murmushi tayi tace "Aby na ciki?" gyadamata kai sukayi, ahankali tasa hannunta tabude bayan motan daba kowa zata shiga taji saukan wani abu kaman tsumma a bakinta da hancinta within 3 good secs dip kanta yadauke, da sauri suka rirrike ta suka shigada ita cikin motan sanan wanda yazo yakirata yama direban da fuskarshi ke sanye da mask magana "yi sauri kutafi, yanzu mu zamuje daukota adaki as scheduled kumuje yara" da gudu suka dauki amaria suka tafi shikuma direban yaja motan dawani fitinannen gudu yabar anguwan. Wanan kenan!!! Ahankali take bude idanunta sabida kanta dataji yamata wani irin mahaukacin nauyi kaman an dauramata buhun simenti, jikinta namata nauyi, irin nauyin nan da jikinka kakeji yamaka bayan alluran kashe zafin ciwo ya saki, wani irin mahaukacin iska dataji yana kadata yasa tabude idanunta da kyau tangaran tana kallon inda take data kasa gane inane, hasken datake gani yasa tajuyar da kanta saitin hasken, kofa tagani abude wani wagagegen kofa saikuma fili haka datake hangowa na kasa bayan clean filin kuma bishiyoyi ne da shukoki take hangowa, cigaba dabin filin tayi da kallo taga jirage ne kaman irin jiragen airforce dinan amman wanan bana airforce bane guda uku, da duka karfinta ta daddage ta lallaba ta tashi zaune tana dafa fuskanta tana kara bude idanunta dakyau kafin da sauri tace "Aby, Aby" tai maganan tana mikewa tsaye tana tangal tangal sai a lokacina takalli inda take cikin jirgi take irin jirgin datake gani a TV da news jirgin airforce dake transporting weapons, ko troops gashi bataga kowa ciki ba, dafa bangon jirgin tayi ganin zata fadi dan batada karfi ko digi kafin tafara tafiya ahankali zatai wajen kofan. "ku kamota!" taji anfada agadarance da sauri ta juyo, Umm tagani tana sanye da dogon riganta hadadden daga gani tasa kayanne dan bikin ta, cikeda isa take tafiya tana fitowa daga cockpit din cikin jirgi wasu karfafan maza guda biyu biyeda ita, tsayawa Widad tayi chak tace "Umm! Assalamu Alaykum Umm, me mukeyi anan ina Aby na dakeson magana dani? Me wayan nan zasumin mesa zasu kawoni nan, su suka kawoni? Waya kawoni nan Umm?" tai maganan tadan daburce sabida mazan dasukayo kanta guda biyu, ko amsata Umm batayiba saidai tasami wata plastic kujera kaman dan ita aka ijiye ta zauna akai tareda crossing leg tana kallonsu, fashewa da kuka Widad tayi ganin gardawa sun rirrike ta sun dagata chak sun kawota gaban Umm sukasamata gwuiwa akasa tai kneeling right before Umm jikinta na shaking, da sauri cikin kuka ta daura hannayenta kan cinyan Umm tace "Umm dan Allah kiyakuri mukoma gida kinji me mukeyi anan dajin? Eh" murmushi Umm tayi tace "yau Widad ne agabana tana kuka tana rokona, naga in kikaga mahaifinki kinamin kallon farko kika gaidani baki sakemin nabiyu saidai in ubanki yasa nazo ma kwashe plate din dakika gama cin abinci dasu ki dagokai ki kallen koba hakaba? Yau ina ubanki yazo nan yabaki kariya mana? Bazai zona"? Cikin kuka Widad tace "wlh bahaka bane amman kiyakuri Umm, kinji bazan karaba kiyakuri dan Allah, karkisa sumin komi" gyadmatakai Umm tayi tana tabe baki tace "zaki gida?" da sauri Widad da jikinta har rawa yake tace "z......zani.....zani gida Umm" murmushi Umm tasakeyi takai hannu ta shafa fuskarta da kukan datayi dukyay ruining makeup din tace "you look beautiful, so beautiful da fuskarki kaman na mahaifiyar ki, daman gift nasa akawo ki nabaki but saina baki tsoro kafin nan, gift din bikin ki" tai maganan tana bin jirgin da kallo tace "jirgin nan jirginane, da kudaden dana tara iya zamana tareda mahaifinki nasayeta a black market, nasa aka gyarata tsaf, babu abinda bai aiki, anytime nakeson na shiga cikin wata kasa da wanan jirgin nike zuwa, babu wanda yasan inada ita sai y'ata Sabeeha, shine naga amatsayin ki na y'ata yakamata nakawoki kiga jirgin da idanunki kinaso? Shine gift din dazan baki kinaso"? Taima Widad tambayan tana karkada kafa tana murmushi tana kallonta, gigirza mata kai Widad tayi alamun a'a saikuma da sauri ta gyada ma yakai alamun eh ganin wani mugun kallo datamata, cije lips Umm tayi tasaki tace "good gurl tashi to kitafi da sauri, is official nabaki jirgin yazama naki tashi kitafi to, motanmu nawaje in mukakai gida kyayi signing papers din so that officially it becomes yours, tashi kitafi, clean your face kar Aby yace nasamai y'a kuka" tashi tayi jikinta har bari yake tajuya tafara tafiya batako waigen baya burinta kawai taganta agida wurin Ahmad dinta da Aby da Amah, daga zaunen Umm tamikama namiji dake kanta hannu, fire extinguisher cylinder yadaura mata a hannu ta karba ta ta tashi tana dagashi da kyar dan acike yake tana kallon Widad dake tafiya ta kusan kaiwa kofa, ahankali take tafiya without making a sound taku uku ta cinmata wani irin daga cylinder tayi ta daddage da duka karfinta da Allah yamata tasakinmata shi akai tawajen kaman bayan kai da keya daidai Widad tasa kafa zata fita daga jirgin taji saukan wani irin heavy abu akanta, sandarewa tayi tareda zaro ido kaman irin wacce aka harben nan, hannu Umm tasa takama bayan riganta ta fizgota cikin jirgin, janta kawai take kaman ta mutu saida tazo daidai tsakar jirgin sanan ta jefar da it tafadi warwas akasa idanunta na juyawa gawani mahaukacin jini dake bulbulowa daga kanta kaman an kunna pampo, bakinta na kokarin motsi amman yakasa idanunta sun juya sun birkice kaman ba idanun mutum ba tsabagen kanta da aka buga, komawa Umm tayi ta zauna tai crossing leg tace "next" da sauri gardawan suka shiga yaye wani abu dasuka lullube da bakin trampoline, coffin ⚰ ne, amma ba irin na Christian ba irin na musulmai, marfin saman anyi huji huji guda goma haka ko mesa oho, bude wa sukayi suka kalle Umm, Widad ta nuna musu da yatsa dat is lying on the floor kaman ba rai ajikinta tace "ku dagata kusata aciki" da sauri dayan yace "Hajiya ai zata mutu ta ina zata dinga numfashi?" kafin Umm tabashi amsan dayan yace "dakiki wanan hujin da akayi name to? Banda haka I've nake it clear ai no question, we don't question wacce tabamu aiki, kasan irin kudaden data biya kuwa, our lives have change, this woman is our live saver, ka kara tambaya I won't mind changing you yanzu yanzun nan" da sauri yace "tuba nike mai gidana" karasawa inda take sukayi suka dagata su kansu saida sukaji tsoron jinin dake zuba daga kanta amman basuda ikon tambaya kudi suke nema kuma shi aka biyasu, sakata sukai aciki yaraf kaman sun ijiye kayan wanki sanan suka rufe, suka juyo suka kalli Umm dake binsu da kallo, murmushi tayi tabude yar purse din hannunta maidan girma taciro kudaden garinsu rappa guda biyar tace "ga la'adan ku wanan kyauta ce sauran saikun dawo" karba sukayi jikinsu haryana bari, tace "inaso yarinyar nan itada gidan mahaifinta har abada, ban kisa sabida addinina yahana kuma duka zunubanta kaina zai dawo inhar na kasheta, wanan ma danayi na rabata da mahaifinta nasan Allah zai yafemin sabida laifi daya ne kadai zaka roki Allah da baya yafewa aduniyan nan shine shirk, hada Allah dawani, bantaba shirka ba kuma bazan tabayiba kuma ko wanan ma danayi Allah yaga dalilina, ku kaita danesa, kufitar da ita daga kasan nan gabaki daya, ku kaita chan wata kasan, cikin worse kasashen damukeda shi aduniyan nan gabaki daya, wulakantacciyan kasa zaku kaita wanda yan garin cikima neman hanyar fita daga ciki suke, kasar da weather ta is harsh, kasan da rayuwa acikinta zai zame mata annoba da ukuba, kasan da kisa ake kullum ana shayar da matsafa organs din dan Adam, kasan da al'adunsu ya banbanta da namu far far, kasan da Widad yar mai kudin nan bazata taba iya rayuwa ciki ba, kasan da mahaifinta bazai taba tunani tana wurin ba, sanan karku kaita kasar dake nan kusa dan nasan mahaifinta zai iya saka abinda ya mallaka na karshe danya nemota, ku kaita da nesa karku sake kuyi landing kar akamaku mahaifinta nada connections, daga sama zaku jefo akwatin chan takarata nasan koda tafarka bazata tuna damuba kafin namata wanan dukan a daidai wanan bangaren kan saida nai bincike dan haka zan tafi kuma kutafi ina tafiya, dan trust me nasan anjima akwai total lock down a morroco dan neman Widad" godiya suka mata ta tashi tafice motar dake pake awurin tashiga suka bar dajin. Wanan kenan!! [11/1, 11:46 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_ 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣4️⃣ _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ FREE PAGE *_NIGERIA_* 🇳🇬 Wani irin juyawa jirgin yayi kafin kace me jirgin yabace a hazo, kwashe yaran aka shigayi ana lodasu a mota yayinda wajen yacika security personnel da some marine forces dake wajen, wasu mutane guda uku ne sukayo wajen Waleed na tsaye inda yake suka shiga cikin ruwan kaman sune search force, sun duba ruwan basuga komiba saidai suka dawo tareda coffin din, Arham ne yakaraso inda Waleed yake tsaye bayan ya tabbatar da staff dinsu suntafi da yaran yace "meya faru just now blood? Jirgin sama right above our head? That's strange, bantaba ganin hakaba sanan ya jefar da akwatin gawa a ruwa is that even okay no wa.... " hannun da Waleed yadagamai yasa yay shiru ya kalli inda Waleed ke kallo da sauri, mutane biyun ne suka fito daga ruwan rikeda akwatin dayake abude suka ijiye bakin ruwan sanan suka fito da sauri Waleed yay wurin Arham biye dashi, tsayawa chak sukayi suna kallon akwatin da jini yabata sosai garuwa ciki, dayan dake cire kayan ruwan da yasaka ne kafin ya shiga cikin ruwan yace "I don't understand, jirgi kawai yazo yajefo mana akwatin gawa lafiyan su kalau ko bazugani da kyau sun zaci nan bolane" da sauri dayan yace "ni nama zaci gawa aka yardan mana ashema akwatin ce kawai, to Allah dai ya kyauta amman wanan abu haka, we will report to the police ashigar da karan susan inda zasu jefar da waste dinsu jibi yanda suka daga ma bakinmu hankal....." shiru yayi ganin Waleed ya tsugunna yanabin jikin akwatin da kallo yana shafa akwatin da hannu kaman maiso yagano wani abu, kafin idanunshi su sauka kan dan kunne kwaya daya dayake makale acikin hole din shan iskan nan da akayi kaman ramin yatokare dankunen dayakeda fadi dan dankunne yama ramin kadan abinda yanashi fita kenan da ruwa shima yay sweeping nashi away, ahankali Waleed yasa yatsanshi yaciro dankunen yamike tsaye yana kallo daya daga cikinsu yace "wow dan kunnen mai kyau halan yayimoshi yayi a ruwan, muje Bala mutafi da akwatin" daukan akwatin sukayi harzasu tafi da sauri Waleed yace "are you sure kunduba ruwan nan da kyau babu kowa ciki?" "yallabai babu inda bamu dubaba ai indai wanan rafin dakake ganine babu wani lungu da sako dabamu saniba cikinshi, bayau muka fara ceto rayukan mutane acikinshi ba" gyadamausu kai kawai yayi suka wuce suna zance, Waleed yajuya yana kallon ruwan da sauri Arham yace "don't tell me u want to go in da kanka" juyowa Waleed yayi ya kalleshi yace "of course yes, ga dankunne nagani a box din" da sauri Arham yace "this is river Waleed, ruwa ne, the coffin can pick the ear ring anyway aruwan, kagama wuce mutafi dan wlh kana kara making attempt din shiga ruwan nan zan danna ma Ammi kira" wani mugun kallo Waleed yamai yace "toka kira munafuki" yana maganan yafada ruwan da sauri Arham yace "Waleed" gabanshi nafaduwa yana kallon ruwan da Waleed ya nitse ciki, arude Arham yace "Waleed wai me haka sai wani abu yasameka acikin ruwan nan eh? Come out please" kusan 10min Waleed yadauka cikin ruwan sanan yafito ahankali, Arham yace "kagani kaima bakaga komin ba, kafi wayance iya aikinsu ne kawai kaje ka jika kayanka a banza" ballamai harara Waleed yayi yay gaba abinshi Waleed ya bishi da sauri yanadan dariya yace "wlh kacika rigiman banza, kawai daga ganin dan kunne shikenan" Waleed baice mai komiba har sukaje children section din, zai shiga ciki saikuma ya kalli Arham yace "lemme go and get Khadija and change" gyadamai kai Arham yayi Waleed yawuce. Knocking yayi tareda bude dakin yashiga, daidai lokacin Ilham tafito daga bayi tana sanye da hadadden jeans din daya kawomata as gift jiya da crop top din da hakanan yadauko let's just say he's use to seeing ladies yan gayu dress in them so practically he wants to see his wife dress like that, tana ganinshi ta taho da gudu zata fada jikinshi ta rungumeshi yakoma baya yace "am wet baki gani" binshi tayi da kallo cikeda mamaki zatamai tambaya yawuce bayi, fitowa yayi daure da towel yazo ya chanza kaya, tajowa wajenshi tayi da sauri saikuma tarike waist tamai wani irin juyi tace "bakace nayi kyauba, nayi kyau?" dan murmushi yayi kawai yakarasa bakin gado ya zauna bayan ya chanza kayan yace "is nice" wani irin blushing tayi ta taho da gudu ta zauna kan laps dinshi sanan ta manna mai kiss a lips dinshi tace "thank you" gyadamata kai yayi kawai sukia shiru, ganin yamata shiru yasa tace "Dr jirgin na landing awajen nanne dazu naji karan jirgi kaman akaina" ahankali yace "it just came and yakuma juya" gyadamai kai tayi tana kallon yanda yake maganan yace "get dress let's go out" cikeda wani irin murna ta dagashi wardrobe taje da sauri taciro gyale mai kyau dazai shiga da jeans din sanan takoma gaban mirror ta yaryada uban kwalliya tasa jan baki sanan ta yafa gyalen awuya tajuyo ta kallai yana danna waya tace "na shirya" dagokai yayi ya kalleta dauke kai yayi yace "change into something native" wani iri taji taso sufita ahaka ko Arham yaga shape dinta da kyau saikuma ta share tai gaban wardrobe din dakin wata pink atampa taciro da aka mata riga da skirt ta shirya tsaf ciki kayan sun mugun kamata suranta yafito sosai, tayafa gyalen daya shiga da kayan tasaka flat shoe sanan tazo gabanshi tace "Baby let's go" dagokai yayi ya kalleta sai kawai yamike tsaye yamaida wayan aljihu yay gaba, bude mata kofa yayi tafito sanan shima yafito yamaida kofan yafita, ahankali suke tafiya har zuwa children section atare suka shiga wajen, da Arham tafara hada ido da sauri ta dauke kai kujera yabata tazauna yace "am coming" gaishe da ita staff dinshi suka shigayi tana ansansu ayangance shikuma yawuce inda Arham yake yace "am taking her out blood she has been indoors tunda mukazo" batare da Arham yakalleshi ba yace "saikun dawo" juyawa Waleed yayi yaje wajen ta suka fice inda bodyguard dinshi ke tukasu, cikin Bauchi suka shiga shi bai wani surutu da ita amman kome takeso tana fadi zai siyamata daga bayama supermarket yakaita yasami waje ya zauna tadauki duk abinda takeso sai dadi takeji sanan suka dawo mota, da magrib sukaje wani eatry bayan ya tsaya sunyi salla a masallaci, sosai ranan taji dadi tasamu sunyi pics sosai dashi komi yasai mata saitai snapping asamu na nunama friends a status sai wajajen 10 nadare suka dawo, baje tsaraban ta tayi a kasan dakinsu tana dubawa tana snapping shikuma yatabe fuska ya shiga bathroom abinshi wanka yayi yazo ya shirya cikin pj yakoma kan gado yabude system dinshi yana aiki, harya gama yay bacci yabarta tana daddanna waya ana saka status ana amsa comment din kawaye. *** Ahankali motar data kwaso mutane kusan goma sha hudu ta God is good take tafiya sabida yanda motar ke over heating, passengers din cikin motar sai tsaki suke suna korafi daga Abuja da suke, yanzun nan suka baro Abuja Benin zasu amman shine tun yanzu sun tsaya yakai sau uku wanan wani irin abune, daidai sun shiga MURTALA MUHAMMADU BRIDGE dake nan hanyar lokoja gaban motan yafara hayaki hakan yasa dole direban yayi paki tareda tsaki yafito, bude kofa passengers sukayi dan sufito sudansha iska indamai fitsari yaje yayi, wata matace dake rikeda yarinyar da at least zatakai 7yrs ne tace "Mummy I want to ease myself" kallon Bridge din matan tayi duk titine ga maza kuma itama fitsarin takeji agaban su zasuyi tunanin hakan yasa takama hannun yarta tarike tareda rataya Jakarta akafada suka sauka daga Bridge din zuwa kasa, sauka sukayi suna tafiya, tanacikin tafiya taji ana tafiya da sauri matar ta juyo ganin wata yar matashiya yasa da sauri matashiyar tace "me to I want to piss madam, sorry if I scare you" juyawa matar tayi tace "no problem" sauka sosai sukayi suna dandarawa har zuwa gaban ruwan da ake cewa anan River Niger da river Benue suka hade, cirema yarta wando tayi tace "tsugunna kiyi, bari indan matsa ta chan is like na pupu dey worry me sef, since ba yanzu motar nan zatai cooling down ba gwara nai kayana our journey still fa, if u finish just stand here I dey come" gyadamata kai yarinya tayi itakuma Maman ta shiga cikin ciyayi sabida yadan kareta, yayinda itama dayan budurwa tashiga cikin ciyayi kowa yashiga biyan bukatun sa. Wani irin ihu da yarinyar ta kwala ba matan kadaiba har mutanen dake chan wajen mota saida yay calling attention nasu. "Mummmmmmyyyyy!" azabure uwar ta tashi ko kashin bata wanke ba tafito tanajan pant dinta sama same with dayar budurwan, da sauri Maman tai wajen yarta dake tsaye tana kallonta tace "wat is it Engozi?" daidai dayan budurwan itama tazo tace "wats the matter why are you shouting beautiful girl?" duk suka tsaya kan yarinyar suna tambayarta ganin yanda take shaking, ahankali tadaga hannunta tamusu pointing 👉 rafin duk suka juya suka kalli inda take pointing atare maman da budurwan suka hada baki suka kwala wani irin ihu. "ahhh hhhhhhhhhh hhhhhhhhhh!" within 1min suka hada mutane wajen ciki harda direban su dan ihun yay yawa sun zaci macijine ma ya sarezu, yanda yan tafiye tafiye sukaga direbobi na sauka kasa ana ihu yasa aka shiga parking mota ana sassakkowa dan anzaci hatsari ne kafin kace me mutane sunfi dari dayan kai awajen, matsar da mataye biyun akayi dake rangada uban ihu, daya daga cikin mazan da duk suka tsaya suna kallo yace "are you sure this one is alive" daya daga cikin mutanen wajen ne yace "acirota please wanchan bishiyan daya rike mata riga ne da yanzu ruwan yakara sweeping nata away" wani ne yace "waya iya ruwa dan Allah anan?" daidai lokacin wasu rundunan mutanen sun iso wajen daya daga cikinsu yace "na iya na iya" da sauri matan wajen sukahau cewa "oga pray o, this river they chop people wey no be from here" murmushi kawai mutamin yamata yace "this na my work in my state" kayanshi yatube agabansu yarage dagashi sai boxer yamikama wani dasuke tare dayake nan kaman kaninshi kawai yay iyo cikin ruwan, mutane akahau salati masu kiran jesus nakira masu ciro waya na video nayi, cikin hukuncin ubangiji mutumin yakai inda take sanan yafito da kanshi hamdala akahau yi, karasawa yayi wajen ichen daya rike riganta sanan ya damke rigan kafin yazare daga jikin icen, yakarasa wajen yarike ta gangan ajikinshi yashiga iyo da ita yana zuwa baki bakin rafin maza kusan shida suka saka hannu suka karbeta aka cirota ana ihu mutane fam awajen wasu na cewa she don die, this one don die, wasu na cewa na Mamy water, kwantar da ita akai akasa aka danne cikinta amman batai aman ruwa ba, babu wani abu da ba'a mataba, wani direba ne da yanadaga cikin wayanda ke kanta yace "please waye likita anan ko nurse koda na gargajiya ne? Yakamata asan ko tana raye kota mace gashi kanta a fashe yake gabaki daya ta baya please in akwai Dr yazo" yay maganan yana ihu sabida aji hakan yasa aka shiga passing information din har zuwa kan titi inda tulin mutane suke tsaye dan basu samu wurin shigowa ba sabida acike, ciki ikon Allah aka samu wata mota da Dr keciki da sauri aka sauko dashi akai making mishi way har zuwa kan wacce aka tsinta a ruwan tsugunnawa yayi akanta gabanshi na faduwa yace "kai anya wanan bil adama ce?" yay maganan shikadai saikuma yace "ta zubar da any ruwa" atare duks samarin sukace "mum mata komi amman bata fito da ruwaba" soyake ya daga dogon gashinta dat is lying akasa dayaga yakai har cinya ta amman harga Allah tsoro yake baison abinda zai hanashi bacci, tunda yake a Nigeria baitaba ganin mace mai gashi hakaba, hannunta yakama yarike danyay feeling pulse dinta, almost 3min yana saurara amman baiji komiba yana shirin zare hannunshi yaji pulse dinta but very slow and weak a dimauce yace "sh.....she's alive" wani irin kabbarta wajen yadauka. "Allahu Akbar" kiristocin sukahau cewa. "thank you jesus" tashi yayi yace "amman a kaita any nearby hospital this girl or whatever she is need to be saves quick inba hakaba za'a iya loosing nata, machine za'a sata dazai zuko ruwan" da sauri wani yace "wayasan any nearby asibiti?" shiru duk akayi duk asibitin da za'a fadi nacikin garine saikuma wani tsoho yace "ku kaita WARBAI ORPHANAGE HOME AND HOME OF THE DISABLED ko tsintuwa fa akayi gwamnati ta halatta mana kai abinda aka tsinta awajen, akwai asibiti da kwararrun likitoci a gidan, kana zuwa za'a karbeta, banda haka asibitin ne kadai zaku kaita ko sisi baza'a chajeku ba sanan kubarta awajen baruwan ku sune zasu dauka daga wajen, in nemo iyayenta ne inma menene duk su zasuyi, kuma ma ai babu wani nisa yana nan hanyar fita daga Abuja zakuga dankareren gini wane University ga sunan baro baro ajiki ga sojoji" addu'a akahauma tsohon maza suka dauketa wani bawan Allah dazaiyi Abuja yay volunteer motarshi mutane uku suka bishi sabida zamanin nan ba'a yarda da kowa tafiya kusan minti hamsin yakaisu gaban WARBAI ORPHANAGE HOME AND HOME OF THE DISABLES, sojoji suka taresu saida aka duba motan tsaf bayan sun nuna abinda suka tsinta sanan sukai ciki har asibitin aka kaita soja biyedasu. Suna shiga sukai parking gaban dankareren asibitin dako wani asibitin cikin gari albarka, already nurses harsun gunguro gado dan sojoji sun riga sun sanar dasu, daura ta mazan sukayi akan gado nurses din na kallonta suka gungurata ciki, Sojan daya biyosu ciki yace "we will take it from here thank you" yanuna musu motarsu, komawa cikin motar sukayi sukabar orphanage din. Wanan kenan!!! Assignment din dazasuje yau shine hiking with benefit, sunan dasuka bashi kenan, chan wani mouthain zasu da tun jiya Waleed yatura maaiktan shi akaje dan dubawa dacire duk wani abu dazai cutar mai da yara sanan akai planting various gift awajaje daban daban dan za'ayi treasure hunt duk wanda yasamu wani abu yazama nashi halak malak saisa aka sama hiking din suna _Hiking with benefits_, yaran sai jin dadi suke, they're super excited, gabaki dayansu yau sun saka sport wears da p-cap harda yan matan cikinsu, bayan kowani t-shirt anrubata sunan gidan marayun koda yaro zai bata za'a iya dawo dashi, ko tracing daga inda yake, kasancewan Ilham tacemai zata bishi yasa sune last to arrive venue din, bodyguard dinshi ya tukosu, tunda taga harda yan mata da sun isa aure a marayun yasa taji tama tsani aikin, sanye take da jeans da riga da sneakers amman saida yasa tadaura after dress akai, shikuma yana sanye da jeans da riga sai canvas da p cap akai, yay bala'in kyau idanunshi sanye cikin bakin glasses dan rana tafara fitowa takwas ne na safe dayan mintuna, Arham kawai suka samu akasa bai riga yafara hawa ba gabanshi da manya manyan jaka guda biyu wanda bottles water ke ciki da glucose incase wani yaro yagaji, kallo daya Ilham tamai tadauke kai tace "Barka da asuba" Barka yacemata yana kallonta saikuma yay murmushi ganin bata iya kallonshi tun bayan abinda yawakana tsakaninsu yace "blood your wife tayi kyau sosai cikin english wears dinan da sneakers menawani sa tasaka after dress akai?" jaka daya Waleed yadauka yagoya abaya sanan yace "she is married ba kyau ana ganin jikin matan aure, let's go" yay maganan yanayin gaba yafara hawa kan dutsen, dan kallonta Arham yayi suka hada baki, lashe lips yayi irin kinyi kyau dinan u look yummy sanan yabi bayan Waleed, murmushi tayi ganin yanda ya mutu akan gayun shiko Waleed koya cemata tai kyau baiyyiba, ajere suke tafiya Waleed nagaba Arham atsakiya sai ita abaya, ahaka har sukakai saman mountain din kafanta kaman zai katse ta gaji, sauke jakan Waleed yayi yana murmushi ya kalli yanda yaran suka zuzzube akasa suna haki sai zufa suke nanko dazu sunfi kowa kosawa a tafi yace "are you tired children tun yanzu?" atare sukace eh, dariya yayi yashiga ciro rowan yana raba musu suna karba sauran ma'aikatan ma nabasu ruwawwakin dan kowa saida ya goyo jakan ruwan cikin maaikatan, wayanshi dayashiga kara yasa yamikama wani staff dinshi yamai alamu yacigaba da raba musu sanan ya matsa gefe yaciro wayan, ganin daga orphanage dinshi ake kiranshi Dr Kemi yasa da sauri yay picking yakai kunnenshi yace "talk to me Dr Kemi" anatse matan tace "Sir we have an emergency case, we need you here ASAP" bayan shi Dr Kemi is the second best Dr yakedashi a hospital dinshi, ganin ita da kanta tana fadomai akwai emergency ana bukatan shi yasa yace "what happen? Who is sick?" anatse tace "Sir a patient was brought into the hospital few minutes ago...." da sauri yace "is it a BID (brought in death) case"? Da sauri tace "no no sir, is not a BID case amman close to BID" "kaman ya close to BID? Dr Kemi skip the talk and cut to the chase" ajiyan zuciya tasauke tace "Dr Warbai 4 men suka kawo yarinyar nan cewan an tsinceta acikin ruwa, karkashin gadan murtala Muhammad Bridge in zaka lokoja, I believe them cause the evidence was obvious" anatse yace "did she sustain any injury?" "yes sir, yes, akwai bruises ajikinta ko'ina, sanan kanta yafashe" "what is kanta yafashe? Da kanta yafashe da BID za'a shigo da ita, tell me the exact lobe a head dinta daya fashe, is it the temporal lobe, frontal lobe, parietal lobe, ko occipital lobe, wanne ne yafashe?" anatse tace "occipital lobe dinta ne tasami injury, wajajen keya, wajen yatsage yafashe, the problem now is I believe water yay finding his way to her cerebellum, naduba eyes dinta sun karkace, I think her vision sight has been distorted" cikeda damuwa yace "that's metamorphopsia, yawanci head injury nasaka hakan" ajiyan zuciya Dr kemi tasauke tace "she is unconscious, pulse dinta kadan ne sir" wani irin ajiyan zuciya yasauke yama kasa magana saikuma yace "I will be on my way just stabilise her condition" da sauri tace "ejo, mabinu Sir, listen sir" ahankali yace "yes! Kince"? anatse tace "Sir am the only Dr on duty am sorry bazan iya duba yarinyar nan ba trust ne indai yarinyar nan bayar ruwa bace to mami water ce, I just got married, I don't want my husband to loose me" wani mugun tsaki yayi ya katse wayan yajuya ya kalli Arham daketa rabo itama Ilham na rabon, karasawa wajen yayi ya kirashi "blood" da sauri Arham yadago ganin yakira shi yasa ya ijiyema yaran snacks din yataho wajenshi yana kallon idanunshi yace "yanaga idanunka sun chanza? Menene?" ahankali Waleed yace "akwai emergency a orphanage a clinic, Dr Kemi isn't helping matters, I need to be there now, but once nashawo kan case din zan dawo koda gobe ne, please don't tell Ammi nakoma Abuja koda takirata, I don't want her to know, zanbar Ilham ma anan, dankoda nace zanje da ita zata mayarmin aiki bayane ko?" da sauri Arham yace "yes kabarta anan aiduk muna tare she will be fine, but tell her first kafin katafi sabida karta damu kasan tana sonka dayawa, don't worry I will take care of her, go and save life Allah sa muji alkhairi" side hug Waleed yabashi yace "thanks blood" sanan yakira Ilham dake wajen yara. "Khadija" da sauri Ilham tadago kanta saikuma ta tashi tazo inda yake tana kallon fuskarshi ganin kaman yanayinshi ya chanza tace "baby menene"? For the first time yakai hannunshi kan fuskarta kaman mai son lallashinta yace "I need to go to Abuja yanzun nan Ilham, ga Blood na he will take care of you, anything you need just let him know, zan dawo once nai stabilising case din, take care of yourself okay" gyadamai kai tayi kaman zatai kuka tace "Allah ya kiyaye" fuskanta yadan shafa yace "Ameen bye" gyadamai kai tayi, bye yama Arham yawuce, bodyguard dinshi yabishi mota ya shiga already akwai wallet dinshi ajikinshi daman, Airport yakaishi direct yabi available flight to Abuja baima sami business class ba haka yay managi da economy, yana kaiwa yadau drop direct to his orphanage, sojojinsu zasu taresu yasaukar da glass suna ganin shine aka bude gate da sauri ana gaidashi motan yawuce ya shiga, har gaban clinic dinshi yafito yabama direban kudaden dabaisan iya adadinsu ba. Shiga cikin clinic din yayi da Dr kemi yafara haduwa a reception baibi takanta ba yawuce washhand basin dake reception dinshi ya wanke hanunshi da hand-wash sanan yatare senitizer yay amfani dashi yajuyo lab-coat dinshi Dr Kemi ta mikamai cikeda girmamawa tace "welcome Sir" gyadamata kai yayi yakarbi lab coat din yasaka daidai lokacin wata nurse takawo mai faranti da handglove kekai, dauka yayi yasaka sanan yace "where is the patient Dr Kemi" adan daburce Dr Kemi tace "ICU Dr" tafiya yafara yay hanyar ICU tana biyeda shi da nurse guda daya, Dr Kemi tace "Sir ko nurses dinmu sunce karmu tabata, kaganta wlh she is the definition of ba mutum bace" tsaki yayi baice musu komiba tsabagen takaici har sukakai gaban ICU din, ahankali yadaura hannunshi kan handle din kofan ya murda kafin ahankali yatura kofan. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫_*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣5️⃣ Ahankali yatura kofan ICU kaman wanda bayaso yatura, wasu fararen kafa yagani farare tass wane kafar jaririya, tafin kafan so so pinkish kaman andiga mishi pink tiri ajiki da dogayen fararen yatsunta dakenan amike tsaye, ahankali yadaga kafanshi ya shiga dakin yanabin tundaga kafan zuwa wani blue jikakken hadadden doguwan riga dake jikinta da ruwan kayan ke diddiga akasa in drops, bakin silk gashinta daya fara tundaga kan cinyarta yake kallo har zuwa fuskarta da gashin yarufe gabaki daya ya mammanne awuyanta, faduwa gabanshi yayi shima dum! Hakan yasa ya tsaya chak dan dazaran yay motsi na bayanshi daman sun riga sun tsorata in shima ya tsorata ai mutuwa kawai yarinyar zatayi dan bazasu iya bata taimakon daya kamata ba, addu'o'i ya karanto a zuciyan shi daidai Dr Kemi da tuntuni suna wajen kofan dakin basu shigoba itama ta shigo dakin ta tsaya kusada shi tace "kaga abinda nagayama ko Dr Warbai, this gurl is not a human, look at her hair saikace bishiyan gashi" juyowa yayi ya kalli Dr Kemi irin kallon nan na in bazakiyi shiruba to kifita hakan yasa taja bakinta ta tsuke, karasawa gaban gadon yayi ya tsaya chak saikuma yadago kanshi ya kalli nurse din dake bakin kofar dakin yace "kawomin rubber band" da sauri nurse din tajuya ko minti daya bai dauketa ba tadawo rikeda robali guda biyu ta tashigo ta mikamai, karba yayi sanan yamika ma Dr Kemi yace "karba kwashe mata wanan gashin ki daure" wani irin matsawa baya da gudu Dr Kemi tayi ta rungume jikinta tace "Oga Waleed, haba now, please me no go touch this girl abeg, no vex Doctor" wani irin tsaki Waleed yaja idan har yace abin nan baikaishi wuyaba yay karya shiru yamata yajuya yay ta maza, hannunshi yasa na haggu yadagota zaune ahankali tareda saka mata filo abaya yatareta hakan yasa tai kaman ta zauna dakanta sanan yasa duka hannayenshi biyu ya tattare gashin nata ya kama da robalin da kyar, har ijiyan zuciya yake dan bai iyaba ya maida ita ya kwantar sai a lokacin idanunshi suka saukar kan fuskarta, dauke idanunshi yayi da sauri kaman wanda baiso ya kalleta sanan yasake juyowa ya kalli Dr Kemi cikin fushi yace "you have two options Dr, either you change this girl wet cloth to hospital cloth or you pack your things and leave my hospital har abada you are fired" da sauri Dr Kemi ta zuba kafafunta akasa tace "Doctor!" cikin fushi yace "what sort of unprofessional attitude are you displaying today? Da ace nasan this part of you tuntuni da bazan taba dauko ki harna baki aiki ina biyanki salary every month ba, for God sake yarinya daga cikin ruwa aka daukota ko kunya bakuji ba kunma kasa ciremata wanan jikakken kayan ajiki so kuke sanyi yakai har bone marrow dinta? Where is the hope, yarda da amincewa da al'umma suka daura akan wanan gidan marayun where is it? Where is that trust that the people and all this hopeless people bestow on us? Kunsan yanda yarinyar nan zataji lokacin data farka taganta alive bayan tariga ta dauka tata takare she is dead already, just look at this helpless child dakukai abandoning nata da sunan aljanna ne koma mayya ce whatever u guys named her ku kukasani, inkuka taimake ta, dame yarage ku ko angayamuku kuka taimaki aljani mutuwa ake? Listen ko aljanna ne, ko mayya ce koma wata halittan ce daban da bamusaniba all we know now is she needs help and Warbai orphanage and home of disables hospital is gonna offer that help to her, now my friend stand up change this girl or leave my hospital immediately" yafadi aziciye yana nuna mata tareda dakamata tsawa batare daya damu datama girmeshi ba, tashi tayi da sauri tace "zanyi, wlh zanyi? I Dr Kemi Ayobami will do it Sir, I am sorry Dr Warbai for my unprofessional code of conduct, or lemme say malpractice" matsawa baya yayi ya kalli Nurse din, da sauri ta shiga itama kafin yabata nata, dauke kai yayi yana kallon agogo har suka gama chanza mata kayan bai kallesu ba sanan suka cireta daga gadon da aka gungurota dazu akai suka maidata asalin gadon ICU nurse din tafitar da gadon sanan Dr Kemi tace "all set Dr kazo" karasowa ciki Waleed yayi ya tsaya akan Widad din dayaki kallon fuskarta yace "kunna the machine" wasu machina Dr Kemi ta kunna ta mikomai wasu igiyoyin dat are connected to the machines da bakinsu allura ne, yakarba tareda bude buturon gaban rigan Widad ya makala mata ta wajajen kirji guda uku, biyu kuma a goshinta ta both side, sanan ya kalli Computer wajen dan yaga heart beat rate dinta, daukekai yayi sanan yay placing two hands dinshi kan cikinta ya danna tareda wani irin matse flat cikin amman ko motsi batayiba ganin taki motsi balle sa ran zata amayar da ruwan yasa Dr Kemi tace "Dr I think you should go for CPR" dan jimm yayi kaman mai tunani saikuma yazo ta kanta ya tsaya yakalli fuskarta, ajiyan zuciya yasauke sanan ahankali yakai hannunshi yabude dan karamin bakinta, sosai gabanshi ke faduwa amman yasake irin dakewan nan na maza yakai kanshi ahankali saitin fuskarta, kasa jure kallonta yayi ya runtse idanunshi gam sanan yadaura lips dinshi kirjinshi na bugawa sosai kan nata, kaman an sashi dole ya hura mata iskan bakinshi cikin bakinta sosai sanan ya dago ya kalli Dr Kemi, matse cikinta Dr Kemi tayi amman ba ruwa, sake maida bakin nashi yayi ya hura iska wanan karan fin nada sanan yadago matse cikin Dr Kemi tayi cikin ikon Allah sai gashi tafara amayar da ruwa idanunta a kulle ya tsaya akanta yana kallonta saida tagama sanan ta cigaba da baccin, kallon Nurse din wajen yayi yace "get the scan room ready, I want to run magnetic resonance imaging (MRI) da computerised temograpy (CT) scan, duka biyun zan mata I want to be sure inga in hydrocephalus case (water in the brain) ne koba hakaba, inma akwai any other thing this two scan can detect " fita Nurse din tayi bayan yagama mata bayani, shikuma yadau wata yar karaman touch mai kama da byro ya bude idanunta ya haska yaga har lokacin idanun ajuye suke, sakin idanun yayi suka koma suka kulle yay dan huci ya kashe torch din ya ijiye daidai nurse din ta shigo tace "all set Dr" gadon ya nuna musu yace "ku gungurata" gungurata sukayi bayan an ciccire mata abinda ya makale dazu yana biyeda su abaya, scanning din yamata kana ganin yanda yake kasan likita ne shi kwararre yanayi yana rubutu a wata yar karaman jutter yanama Dr Kemi bayani yace "akwai ruwa a brain din but we are lucky is not much, the water is not even the problem the problem is the injury she sustain, banda this outer one dakika gani akwai na ciki dan har jini yadan zuba but kadan aciki, but if she is still a lucky person I might be able to get it all out, idan kuma bahaka ba zan iya fito da wanda zan iya sauran with time dakuma medication zai koreshi zai tafi sabida inhar yana wurin this girl might likely behave abnormal inta farka dan dameji ne babba a brain din" girgixa kai Dr Kemi tace "ko ya akayi yarinya karama taji irin wanan ciwon akai haka yanzu gashi sai an mata aski ko"? Dan shiru yayi yana kallon computer saikuma yace "no only wajen daya tsage akan zanbi nama horizontal layi small aski haka, sabida nasamu nai mata stitches" gyadamai kai Dr Kemi tayi, ya kalli nurse yace "get the theater ready the earlier the better for her" fita nurse din tayi taje ta shirya komi, sukai theater da ita. Wasa wasa tunda suka shiga theater basu fitoba sai wajajen bakwai da rabi na dare, dan aikin yaso yabashi matsala saida yay facetime the asalin Dr dinshi dayay training dinshi a hospital a Norway 🇳🇴 , Dr Trump Abraham Ali, da taimakonshi yay successful operation yagama yazuko fluid din dudda wani yarage da baifi a drop of water ba, Dr yacemai karya damu da wanan zai bace inhar tanashan magani sanan tana hutawa, sanan Dr yasa yaduba idanunta, dubawa yayi yaga karkacewan ya gyaru amman ba tas tas ba Dr yacemai shima wanan zai bace yanzu a kaita ICU a lullubeta da bargo in AC na a kunne a kashe asa hitter, kasusuwanta na bukatan suji dumi dan sanyi yariga ya shigeta, gyadamai kai yayi sukai yanda yace sanan yafito bayan yabarta under nurses care. Ahankali yake tafiya ya bala'in gaji, gashi daman dazu sunyi hiking a Bauchi, office dinshi yawuce yabude ya shiga, laptop dinshi yacire yarataye sanan yabude dakinshi ya shige wayanshi yacire daga aljihun wandonshi da tun dazu yasa a silent, sanan yawuce ya shiga bathroom wanka yayi da ruwan dumi sanan yafito daure da towel yabude wardrobe din wajen yadauko wasu riga da wando ya saka, dadduma ya shimfida sanan yahau kai yafara salla, biyan sallan yayi sanan yafito yawuce masallaci dan sallan isha'i sai gaidashi ma'aikatan shi suke yana amsawa. Tun bayan Waleed yatafi, Arham ke satan kallonta amman dauke kai Ilham take kaman batasan yanayi ba, 1na rana aka gama komi student da suka tsince treasures din sai murna suke, dan akwai wacce ta tsince Ipad na yara, wasu ball, wasa game na ludo, wasu yar baby, toys, mp3 and many more, it was so fun, ana gamawa aka tafi, Ilham na cikin tafiyanta ahankali dayake daman itane na karshe a duka mutanen wurin Arham kuma abayanta kaman yanda dazuma sune na karshe zuwa, tafiyansu suke har lokacin basu cema juna komiba, ganin Arham yaki kulata yasa da gangan ta turgude tai baya zata fadi, dan ihu tayi da sauri Arham yatareta ta hanyar kama waist dinta yahada bayanshi da jikinshi yace "hey lawyer watch inda kike saka kafa" buge hannunshi tayi dake kafadarta tace "me haka so kake aganmu"? Kashe mata ido yayi yace "suda sukai gaba we are the last people anan fa, ya akayi ne are you not horny? Please mukoma hotel dinmu let's screw saimuyi wanka and come out for next activity kinga mijinki yabani amanan ki yace nakulan mai dake kibari nafara kulan tun daga yanzu" ballamai harara tayi tace "stop all this ko wanda nayima ada nai nadama am not gonna do it again" tai gaba tafara tafiya da sauri, da sauri yasha gabanta yace "tell me you are not interested in me," yanuna mata kanshi yace "just tell me u are not interested in this fine hausa fulani boy, kallan fa" tsaki tayi zata wuceshi ya fizgota taredakai hannunshi ya matsa butt dinta yana kallon idanunta yace "angaya miki banga dazu har chanza tafiya kikayi da kika ganni ba kina murgudamin wanan naughty ass din naki, tell me I don't turn u on lawyer" yay maganan yanakai harshen shi kan wuyan ta yadan laso kadan yanasake squeezing ass dinta yace "tell me seeing Arham doesn't turn u on Lawyer" kasa koda motsi tayi yana kallon yanda take breathing fast fast, murmushi yayi yasake shigewa jikinta yace "I fucking turn you on kaman yanda u fucking turn me on, I give you heat, heat irin wanda Waleed dinki dakike so baitaba bakiba, fadamin da bakinki in Waleed nacinki da kyau kaman yanda naciki ranan, naci wanan ramin" yakai hannunshi wuraren gabanta ta saman jeans dinta rawa jikinta yafara dan she totally lost it, kasa magana tayi saima wani shegen shaukin datakeji abinda yakamata Waleed yadinga mata shi Arham yake mata nan da nan yagama da ita, babu alkawari da ranan nan batayiba akan bazata sake irin kuskure nan datayi da Arham ranan ba amman takasa, lips dinta ne suka fara motsi tadan lashe lips din yana mata wani shegen kallo yace "what? Kimusa mana? Tell me Waleed fucks you better than how I fucked you that day tell me" jikinta nawani irin rawa tace "Wa......umm....Wale...ed" ahankali while squeezing har butt yace "uhun talk" lashe lips dinta tasakeyi tace "I can't get yanda kai sexing dina ranan daga kaina" wani irin murmushi yayi yace "sabida am better than Waleed your husband ko?" gyadamai kai tayi tace "uhn u are" bakinshi yakai kan nata ya tsotsa yace "good Lawyer inason yanda you choose pleasure dinki kan komi, now let's go and have fun, nafara kulan dake da mijinki yasani let's go, zaki iya tafiya kona dauke ki?" ahankali tace "zan iya" sakin ta yayi suka fara tafiya saikuma yarike mata hannu suka sauko har kasa babu motar student sai tasu inda bodyguard din da yakai Waleed Airport ke jiransu, ganin bodyguard din na kallonsu sabida ganin dayayi Arham yarike mata hannu yasa yay murmushi yace "faduwa tayi, kasan the mountain is kinda sloppy dole mutum na kula in yana tafiya" cikeda girmamawa bodyguard din yace "sorry madam" gyadamai kai tayi suka shiga motar yajasu har zuwa hotel din, sauka sukayi suka shiga, dakinsu ta shiga yana biyeda ita abaya, maida kofar yayi yarufe yana saka sakata, sanan ya juyo ya kalleta, jallabiyar jikinta tacire ta yar akasa sanan tabude boturin jeans din jikinta taja jeans din kasa Arham na jikin kofa yana wani irin kallonta, riganta tacire tayar akasa sanan ta juyamai baya ahankali in a seductive way tacire pant jin jikinta tayar sanan takai hannunta bayanta tacire bra tayar tai wani irin mika tace "auuuccchh nagaji" dan waigo da fuskarta tayi ta kallai hada ido sukayi tawani irin kashemai idanu daya sanan tai hanyar bayi tana wani irin tafiya ass dinta na kadawa, binta yayi dawani irin kallo yace "matar Waleed" bude bayin tayi ta shiga sanan tadan juyo ta kallai da yatsar ta sabbaba tamai alamun yazo sanan tace "inka shirya kula dani da aka cema ka saman aciki" ta shige cikin bayin tabar kofan abude. Ja idanun Arham yayi tsabagen jaraban sha'awa Ilham badai boobs ba, tanada ass ma amman ba sosai ba, kayanshi ya kwabe ya yar sanan yay bathroom din kaman wani mahaukaci, atsaye ya ganta karkashin shower ruwa na dukanta tundaga kai har kafa, dan juyowa tayi jin alamun mutum, ganin Arham ne tsirara ga joystick dinshi amike sambal yasa tai murmushi ta tara ruwa da hannunta ta watsamai, murmushi yayi yace "ni kike watsama ruwa lawyer" daga gira tayi tace "an watsama din" dawani irin gudu ya shigo shower yadagata sama ya jinginata da bango ya matse tareda kama nipples dinta ya matse da karfi harsaita tai kara tace "wayyo Allah zafi fa Arham" sake nipples din yayi yay kissing lips dinta yana ware kafafuwan ta ruwa na dukansu yakama joystick dinta yakai bakin wajen yatura ciki da karfi yana nishi yace "that is your punishment matar Waleed" hannunta takai kan gefen cikinshi tarikeshi gamgam tana gyara tsayuwa tace "wash Arham I miss you, wlh tun ranan nan bansan ko wani abu kamin ba bana iya daina tunanin sex din da mukayi" turawa ciki yayi da karfi yana lashe wuyan ta kaman maye yace "bakijin dadin Waleed ko yanzu" kankameshi tayi tace "inaji amman dai...." shiru tayi idanunta na juyawa, tsayawa yayi chak yace "koki karasa maganan kona ciro na barki" da sauri ta kankameshi tace "no please karka ciro, amma dai kawai nakasa daina tunanin yanda muka sadu ne ranan" ciro wa yayi ahankali sanan yay wani irin mahaukacin shiga da karfi da saida yasa ta buga uban ihu. "na shiga uku na lalace Mummy" dannewa yayi sosai kaman zai tabo mahaifan ta yace "so nake kidena jin dadin Waleed ko kadan, so nake kidena mutuwa akan Waleed kina nunamai shi wani ne har kina sha'awan shi saisa yake wulakanta ki baidamu ba, sonake ki share shi kinuna koyay shekara bai sex dakeba ba matsala ko oho, kodama yazo sex din kidena bashi kanki ko hanashi kijamai aji hakan zaisa yafara sonki yana mutum miki, karki sake kibashi koda kwana nawane ke bakida matsala kinada ni, koda mun koma Abuja dazaran yazo gidan marayu nizan fito nazo har gidan muyi sex son ranmu na kawar miki da kwadayin shi kinji, banson hadaddiyar mace ajin farko irinki na zubar ma da Waleed darajan ki dagayau u are a change Ilham, u are a change khadija kinajina" gyadamai kai tayi duk wani magana nashi na shiga ranta chass yana zama, wani irin juyar da ita yayi ya kifarda ita a bango ya shigeta ta haka yana ramming nata sanan yawani irin danneta zai kawo rawa jikinta yafara tace "Arham please kadena kawowa ciki hakama ranan kayi karnai ciki" danneta yayi yajuye tass ciki yace "inma kinyi Waleed zaki manna mawa kici gado, bakiga family su basa haihuwa ba Allah sa ma Waleed din na haihuwa am your only option" bata sake cewa komiba wanka sukayo suka fito suka dawo daki suka cigaba da having fun abinsu. Misalin karfe tara tana kanshi tana riding dinshi dan tun rana dasuka dawo abu daya sukeyi kaman wayanda akama baki suyi suyi bacci sutashi suhuta acigaba, sunyi order abinci da magrib dinan suna gamaci suka cigaba, wayan Arham ne dake gurnani sabida yanda Ilham ke riding dinshi yashiga kuka har wayan takatse kasa picking yayi akaro nabiyu ne yamika hannunshi yadauka batare daya kalli screen dinba, cikin muryanshi data shake yace "Hello" dan dariya Waleed yayi yace "don't tell me harka kwanta" ture Ilham yayi da sauri yatashi ya zauna itama natsuwa yayi dan tagane Waleed ne, ahankali Arham yace "x-man that hiking is not easy dole nai bacci da wuri am tired my feet are killing me" murmushi Waleed yayi yace "sorry nima nagaji, dudda kokari nagama komi nadawo ba dade daga a operation ba yanzu ma daga masallaci nake nai isha'i nace bari nakiraku kafin nai bacci am so tired, I've been calling Khadija wayanta akashe I've been wondering why wayanta zai zama akashe bayan akwai 247 light a yankari, da naso nai magana da ita gashi kafara bacci" dan murmushi yayi yace "no no that's not a problem blood, bari nakai mata wayan, just give me some minutes na chanza and put on something decent sai naje" "thanks Man" Waleed yafara tareda katse wayan, kallon Ilham Arham yayi yawani irin bushe da dariya yace "ke mijinki na nemanki fa, lemme call him" gyadamai kai Ilham tayi yay dialing number Waleed ringing daya Waleed ya dauka Arham yace "yauwa gatanan" yamika ma Ilham wayan yace "gashi madam karki damu kokun gama wayan kawai ki barta a wajenki ta kwana inada wata, gobe na karba saida safe" ahankali kaman da gaske Ilham tace "saida safe blood thank you" tana riding dinshi sanan tadaura wayan a kunnenta, ahankali tace "hello" ahankali yace "what happen to your phone Khadija"? Dan shiru tayi tana kallon fuskan Arham dake kallonta tace "ahhh...." Kasa magana tayi sabida jan boobs dinta da Arham yayi wani irin bankarewa tayi tace "wayyo Allah na Ab..ba" da sauri Waleed yace "menene? Are you sick" kanne mata ido Arham yayi tama rasa natsuwa tace "kafafuna ke zugi bazan kara binku hiking ba" dan dariya Waleed yayi dan abin yabashi dariya yace "sorry" zai kara magana ta tareshi tace "bacci nakeji, zan kwanta halan kafan yadena zugi gud night" dan jimm yayi yana mamakin kota tambaye shi ya hanya saikuma yace "okay gud night ki kunna wayanki" katse wayan tayi ta jefar batare data bashi amsaba, wani irin jefata gado Arham yayi yabita da sauri ya shiga bata doggy yanda ranshi keso kaman ba Allah. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣6️⃣ _sorry guys my screen broke yesterday, I couldn't press or even answer call, na gyaro will give you more updates anjima_ Da asuba ya farka wuraren karfe biyar na yamma, dawata shegen yunwa yafara cikin shi har wani hunger contraction yake having, sai yanzu yake tuna rabonshi da abinci tun breakfast din dayayi jiya at yankari kafin ma sufito hiking, shi mutun ne dabai yawancin abinci baima damu da abinci ba amman tunda yaji yunwar nan yunwan takai ne cikin shi so empty, tashi yayi ahankali ya sauka daga kan gadon yay bathroom brush yayi yadauro alwala yafito, cire pyjamas dinshi yayi ya shirya cikin wasu riga da wando nasoft yadi yafito, masallaci yaje yay sallan asubahi sanan yadawo, wayarshi yadauka ya lallubo number Mom, dailing number yayi ringing daya Mom dinshi ta dauka tace "su Dan Yaro mutan yankari yau antuna dani" yatsine fuska yayi kaman zaiyi kuka yace "Mom am hungry please ki aikomin da abinci" da sauri Mom tace "kana Yankarin ne zan aikoma da abinci Dan Yaro"? Girgiza kai yayi yace "nadawo jiya ina orphanage, ki aikomin da abinci am damn hungry bazan iya magana ba yanzu, please Mom don't tell Ammi nadawo kinji" dan jimm Mom tayi kanajin muryanshi kasan yunwan yakeji dan da kyar yakema maganan hakan yasa tace "shikenan, bari namaka simple abu na aiko maka dashi in bama su Abdul ko direba yakawo ma?" da sauri yace "direba su Abdul da bakinsu bai shiru suje su tonani wajen Ammi" dan dariya tayi tace "shikenan matsoraci, sannu kaji nan da 30min abinci zai isoka in sha Allah" "thanks Mom" yafadi ahankali yana fadawa gado soyake yaje yaduba patient din nan but yunwa bazai barshi ba, security yakira ya sanar dasu wani zai kawomai breakfast abari ya shigo suka amsa mai da to cikeda girmamawa, ijiye wayan yayi yadan lumshe ido, ko 1hr cikakke ba'a dauka ba yaji ana kwankwasamai office hakan yasa yamike da kyar yafita kofa yabude ahankali cikeda girmamawa direban Mom dake rikeda wani hadadden basket yace "Barka da safiya yallabai" murmushi yamai yace "Adamu yau baka bata ba" dariya direban Mom Adamu yayi yace "yallabai ai yanzu na gane office din naka sosai ban bata, gidan marayun ne masha Allah da kwai girma Allah dai ya faranta ma kaman yanda kake faranta ma yaran nan marasa shi" murmushi yayi yasa hannu ya karbi basket din yazaro kudi masu yawa ya mikamai, karba Adamu yayi ya shigama Waleed godiya, batare da yadamu ba dan to him is nothing much yace "ka gaidamin da Mom, sai anjima" ya maida kofan yarufe yay ciki zama yayi kasa yana ciro komi na basket din katon flask ne dake cikeda coffee murmushi yayi ya tsiyaya coffee da kamshin shi ke tashi dan harya cika dakin da kamshi a cup, sanan yabude flax yadebi soyayyan Irish da plantain saiya debo pepper soup din fish yazuba agefe yafara ci, abinci ma rahama ne sosai wlh, duk sanda Allah yabaka ka godema dan yunwa bala'i ce, yaci abincin sosai dudda bawani cin azo agani bane but ya koshi, yay Hamdala sanan yature yatashi yakoma kan gado yakarasa shan coffee dinshi, saida ya shanye tass sanan yawuce bathroom wanka yayi yafito daure da towel a waist dinshi gashin kirjinshi sun kwanta gwanin ban sha'awa, ganin wayanshi na ruri yasa yakarasa wajen wayan ya dauka, ganin Mom ne yasa yay murmushi ya dauka yakarasa gaban dressing mirror yasa wayan a speaker ya ijiye yadau cream yabude zai fara shafawa, daga tachan bangaren Mom tace "oya start explaining nasan ai kagama cin abincin yanzu, maiya dawo dakai Abuja bayan duka duka kwanan ku biyu yanzu da tafiya Yankarin? Wani emergency ne yadawo dakai? Bayan nasan 7 days excursion kukeyi every year" dan ajiyan zuciya yasauke yace "Mom now ina miki karyane wai"? "no bakamin karya but ai I need to know abinda yadawo dakai kaida nasan baka wasa da wanan excursion din naku, yanzu dai ina matar naka kuna orphanage dinne tare?" girgiza mata kai yayi yace "a'a na barta achan" cikin daga murya Mom tace "kabarta achan Dan Yaro! Wai lafiyan ka kalau kuwa"? Ahankali yana shafa mai yace "Mom! Arham na wajen fa" dan shiru Mom tayi kaman mai tunani tace "dudda hakan bai kamata kabar yarinya achan ita kadai ba duka duka kwanan ku nawa da auren eh? Abinda zaka mata Arham zai mata ne? Kokuma angayama zata iya tunkaran Arham akan kome takeso ne kaman yanda zata tunkareka kai tsaye ta gayamaka, bama wanan ba maiya kawoka Abuja"? Dan shiru yayi kaman ba zaiyi magana ba saikuma yabata labarin komi, ahankali ta nisa tace "okay okay nagane, yanzu dai inhar kaga case din zai karasa ka kwana yauma toka kira Arham yakaita Airport tadawo nan kajini"? Murya chan kasa yace "tom" cikeda gamsuwa tace "bari na barka ka shirya kaje kaduba patient dinka, sai nakira anjima zan aiko maka da lunch" murmushi yayi yace "you are the best Mom" hararanshi tayi kaman yana wurin ta katse wayanta abinta, shiryawa yay tsaf cikin wata sky blue long sleeve shirt da dark blue wando, neck tie yadauka yasaka sanan yadauko agogonshi rolex ya saka, feshe kanshi yayi da turare sanan yazauna yasaka cover shoe yamike tsaye, wani drawer yabude yadauko wani clean ironed lab coat yarike a hannu yadau wayanshi yachusa a aljihu yabude kofa yafito yana takun nan dai dai duk wanda zai ganshi saiya kara juyowa ya kallai danyay mugun kyau sai baza uban kamshi yake. Agogon hannunshi ya kalla 8 tayi na safe harda yan mintoci, masu shara da watering plant sai gaidashi suke yana amsawa atakaice dan baida son yawan magana ko dogon zance da ma'aikatanshi inbadai takama ba, karasawa clinic din yayi ya shiga da sauri nurses biyu dake wajen suka karaso inda yake. "good morning Dr" "morning" ya amsa atakaice yana tafiya, daya daga cikinsu dake rike da nursing chat sheet ne a hannunta tace "Dr the patient a ICU yanzun nan nadawo daga daukan vitals dinta everything seems normal" gyadakai yayi yana tafiya, sanan tace "jinin daka samata yakare, nacire waiting for you ka shigo tukunna" tai maganan daidai suna karasowa gaban ICU din, ahankali yace "good job Ramlat" murmushi nurse din tayi, dayan nurse din tace "Dr baby Mustafa, that sickle cell from pediatric ward da aka tsinta" gyadamata kai yayi alamun yagane wanne Mustapha take magana tacigaba da magana tace "we lost him last night" chak ya tsaya yajuyo ya kalleta, saikuma yace "wani irin we lost him? Ba Dr Kemi ke handling case dinshi ba amatsayin ta na pediatrician?" gyadamai kai tayi tace "Sir yaron yaji sauki sosai, toys din daka sayomai harya fara amfani dasu yana wasa playing sosai, ko jiya operation din da kayi net nasan bai baka daman dubashi ba, jiya kawai middle of the night temperature shi yay rising saikuma yafara convulsing, Dr Kemi did all she could amman we eventually lost him, actually Dr Kemi ma just left yanzun nan tana tafiya kana shigowa" shiru yayi saikuma ahankali yasaki handle din kofar ICU yajuya direct pediatric ward yaje single room section ya shiga nurses din biyedashi, ahankali yake kallon wani dan karamin jariri da duka duka bazai wuce 5month ba an lullube shi da farin zani dakin an gyara tsaf, dakin hadadden gaske, toys ta saman gadon da aka kwantar dashi dake juyawa wanda zai dinga sa yaron murna yana daukemai hankali, karasawa gaban gadon yayi yaja plastic chair ahankali ya zauna yay shiru yana kallon gawan yaron batare daya budeta ba, sanan yajuyo ya kalli nurses din biyu yace "kuje boys section, akiramin Baba Mani" gyadamai kai sukayi suka fita tareda rufo mai kofan, maida kanshi yayi ya kalli gawan kafin ahankali yasa hannu yabude fuskan yaron tahanyar yaye lullubin ya kallai, yaron baida wani kiba sosai fari ne kaman yaran fulani ga gashi akanshi sak irin gashin agwai yay wani irin haske yadan soma chanza kala dan tun around biyun dare ya rasu, hawaye ne yaji sun taho mai da sauri ya sharesu sanan yatashi yakai lips dinshi ya sumbaci yaron a goshi yana kallon fuskarshi kaman zaimai magana yamai gwarancin yara, ahankali yay murmushi yace "I remember ranan da aka kawo ka gidan marayun nan 5month ago" yay dan shiru yace "wasu manoma guda uku suka kawomin kai, suka cemin sunje gona zasu shuka iri sukaga abu a kwali ga kukan jariri suna budewa aka ganka ba kaya a jikinka jini duk yabata ka daga gani daga haifoka aka yardakai, aka kawomin kai gidan nan, I collected you and held you in my arms ina kallon fuskarka ina wondering wace mahaifiya ce zata haifo wanan kyakkyawan halittan ta yardashi awulakance haka, I whispered to your eyes Mustapha don't cry again domin kuwan Allah yakawo ka idan bazan taba bari daidai da sauro daya ya cijeka ba, mahaifiyarka ta wulakanta ka amman Allah daya hallito ka yace bazaka wulakanta ba yakawo ka inda za'a baka kulawa, allura dakai, abaka duk wata aba dakake so" yay dan shiru ya share hawaye again sanan yace "na aika aka kira Mama Iyami nabata kai nace amai wanka asamai kaya akawomin shi clinic naduba Mustapha, nabaka Mustapha sunan prophet manzon mu da Allah ya aiko mana dashi, after series of tests nagano sikla ne kai, ban karaya ba nace I will do everything in my power naga karayu amman dayake Allah shine ubangijin mu yace baxaka rayuba harka kai matsayin danike tunani ba yau karasu Mustapha, Allah ubangiji ya jikanka, Allah ya gafarta maka, I so much wish dabaka rasu ba but Allah yafini sonka, till we meet again Mustapha" yay maganan ahankali yana kara sumbatar goshin shi daidai lokacin an bude kofan dakin, tashi yayi ahankali batare daya juyoba yasa hannu ya share hawayen shi tass sanan yajuyo ya kalli Baba Mani wani dan tsoho ne daya manyanta cikin shigan arziki ya shigo, hannu Baba Mani yamikamai yace "ina kwana likita, Allah ya gafarta mai kaji, Allah yasa yahuta" Baba Mami yamai gaisuwa dan yasan inhar akai rasuwa a gidan marayun nan yana mugun taba Waleed bakadan ba dudda yana daurewa baya nunawa, dan murmushi Waleed yayi yace "Baba Mani a dauke shi aje amai wanka amai sitira, in angama komi a kirani muyi jana'iza sai akaishi" gyadamai kai Baba Mani yayi yace "shikenan likita kayakuri, tafi ka cigaba da aikin ka, ladanka naga ubangiji ne abinda kake mana mu marasa karfi da wayan nan marayun ubangiji Allah ne kadai zai iya biyan ka, katafi" gyadamai kai yayi yajuya yafita daga dakin nurses din suka bishi, ICU yayi ahankali yabude kofar idanunshi suka sauka kan fararen kafar nan nata tafin kafan so pinkish suna facing kofa, ajiyan zuciya ya sauke ya shiga ciki yakarasa gaban gadon ya tsaya tareda folding hannunshi akirji yana kallon fuskarta da idanunta kenan a lumshe, dauke idanunshi yayi daga kanta yadau torchlight mai kama da byro yadan duko yabude idanunta tareda haskawa yaga idanun sun gyaru dan bakin sun sauko ba kaman jiyaba da ba'a ganin bakin,, sakin idanun yayi yakai yatsunshi biyu ahankali yadaura kan wuyanta, wani irin firgita tayi cikin bacci da saida shima ya firgitan ya janye hannunshi da sauri yakoma baya, ajiyan zuciya ta sauke tacigaba da baccin ta tayi kaman ba itane ta firgita yanzun nan ba, vitals dinta yaduba yaga komi nata is stable sanan ya kalli nurse yace "by 1 zan dawo na dubata" fita yayi daga dakin ya zaga through all wards din yaduba all patients dinshi dat are on admission sanan ya sallami wanda sukaji sauki sosai aka maidasu hostels dinsu, wuraren 10 yagama komi yafito sabida kiran da Baba Mani yamai, alwala yayi yaje akama Mustapha salla suka wuce suka kaishi shibai bisu ba sabida zai koma hospital. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_ ✍️ M SHAKUR 1️⃣ 7️⃣ FREE PAGE Hospital din ya shiga yawuce consulting room dinshi ya zauna, wata nurse ce ta shigo cikeda girmamawa ta gaidashi tace "Sir nafara aiko maka marasa lafiyan for consultation?" dan Jim yayi yana kallon wayanshi sanan yace "in 10mins time lemme make call" wayarshi yadauka yay dialing number Ilham amman har lokacin akashe hakan yasa yaja dan gajeren tsaki yay dialing number Arham, ringing biyu Arham da fitowansu daga wanka kenan tareda Ilham yadaga wayan yana kallon Ilham yana mata signal da cewan Waleed ne yace "Hey X-man ya akayi ne, katashi lpy?" anatse Waleed yace "lpy lau, how are you and how is everything going on around there?" murmushi yayi yace "gamunan duka muna sport yard ne nama fitone dan noise din yaran is too much, alot is going on, above all is super fun" dan murmushi Waleed yayi yace "to Alhamdulillah, I've been calling Ilham wayanta akashe, please blood take her to the airport inaso tadawo Abuja cause I don't think I can come back, har yanzu yarinyar nan bata farka ba banda haka I have alot to do a asibitin nan, please kasa ta a jirgi tazo" wani irin bacin rai Arham yaji ya diran mishi amman yadanne da sauri yace "haba Waleed mesa kake hakane?" dan shiru Waleed yayi dan baigane ina zancen Arham din yayiba yace "what do you mean?" cikin dan fushi Arham yace "what I mean is banga dalilin da dankai bazaka dawoba kacema matarka da already tasaba da yaran nan tadawo ba, karka zama miji mai takura, kaga yanda Ilham ke kulada yaran nan kuwa, kasan bamu taho da any female staff ba, so now anything da yara matan ke bukata wajenta suke zuwa, and she's so happy doing the work, trust me halan ma aikin ya mantar da ita bata kunna wayanta ba, please blood ko for the sake of those children dakeson matarka kayakuri kabarta kawai nanda 4days ne mun dawo yanzu kwanan mu 3 awajen fa, mekace?" dan shiru Waleed yayi kaman mai tunanin maganan Arham din saikuma yace "alright, shikenan to" wani irin hamdala Arham yay a zuciyanshi yace "idan nakoma ciki zan fada mata kana nemanta ta kunna wayanta, bye bari nakoma ciki" ahankali Waleed yace "alright bye, saina kira anjima" katse wayan yayi ya ijiye daidai lokacin nurse din tasake dawowa tabude kofa tace "Sir are you done sufara zuwa?" gyadamata kai yayi tawuce tafita tafara sendo yaransu, yawanci yan matan gidan marayun ne ciwon mara ne most complain dinsu sai masu toilet infection, kasan cewan baya wasa dasu babu wata sabo a tsakanin su yasa kowacce tana zuwa kai tsaye take gayamai matsalanta yana rubuta musu maganin sanan yana kudiran aniyan anjima da yamma da kanshi zaije yay inspecting bayin hostel din matan dan baigane infection din dasuke dama dashiba, one daidai yatashi dan yagaji yatafi mosque sallan azahar yayi sanan yadawo yawuce hospital din yana kallon agogon hannunshi karfe daya harda kusan rabi, direct ICU yayi, ahankali yabude kofan ya shiga har lokacin tana nan yanda yabarta tun safe, samin kanshi yayi da daukan plastic chair yazauna agaban gadon tareda folding hannunshi a kirji batare dayamata komiba yana kallonta kaman irin yanzun ne yasami courage din kallonta tunda yaganta jiya batare da gabanshi yafadi ba, tundaga kan tulin gashinta dayake a daure da lobari yake kallo har zuwa kan fuskarta kafin ya sauka kan hannayenta dayaga akwai yan zanen jan lalli ajiki, kaman ance yakoma baya dan hakanan saiyaga kaman idanunshi sunga wani abu, komar da idanunshi baya yayi yafara kallonta daya kan cikinta xuea fuskarta ya saukar da idanunshi kan kunnenta na dama, chak ya tsayar da idanunshi kan dankunen ta dake makale a idanunshi na dama hakanan yaji ajikinshi yataba ganin this exact dan kunnen, kaman jira mind dinshi yace haka kawai kanshi yay refreshing yatuna shine exact dan kunen dayagani da coffin a yankari, mikewa tsaye yayi da sauri yamika hannunshi yakai kan kunen nata yadaura hannunshi kan dan kunnen yadan daga jikin kunnenta ya kalla, wani irin bin dan kunnen da kallo yayi ganin har yanzu yakasa gasgata cewan dan kunnen ne yasa yakai hannunshi tabayan kunnen yabude hook din ahankali yabudu sanan yamaida hannunshi tagaban kunen zai zare dan kunen mistakenly hannunshi ya sauka kan fatar jikinta yana cire dankunnen wani irin firgita tasake yi da saida yasa yasaki dan kunnen akasa yakoma baya da sauri ya tsaya chak asandare yana kallonta, ware fararen idanunta tayi tarr tabude su duka biyun da har yanzu idanun sun karkace kaman harara garke tana kallon cilin din dakin, wani irin ajiyan zuciya ne ta kufce mai mai kara dayasa tajuyo da kanta ahankali kaman wata robot ta dauramai dara daran fararen idanunta wane madara sukai ido da ido da ita, wani irin kallonshi take kaman yanda shima yake kallonta gabanshi nafaduwa sosai, kasa jure kallon datakemai yayi hakan yasa ya runtse idanunshi da sauri yana karanto addu'o'i aranshi, an tsinci yara manya da kanana da dama agidan marayun nan wasu ma har amasai aka tsince su amman baitaba jin tsoronsu kojin wani abuba sai akan yarinyar nan shi yana rasa takamaimam miyakeji, ko tsoron dasu Dr Kemi suka haddasamai natane a zuciyanshi oho all he knows is yana shakkan ta. "aaaahhsshh, aashh, auuuccchh, a hhhhh....." yaji wata irin siriruwan murya, sassanya maidan gardi dake ratsa zukata na furta kalaman nan irin kalaman nan da ake furtawa idan kana jin zafi ko wani abu namaka zafi, ahankali yashiga bude idanunshi kaman wani mara gaskiya kafin yabude su tarr, zaune yaganta kan gadon tadaura hannunta akan saman kanta tana shafa inda ya aske mata a keya yamata stitches tana bata fuska tana making those sounds alamun zafi hawaye yacika idanunta gam, ahankali yake daga kafa yafara tafiya yana binta da kallo harya zagayo ta inda kafafuwanta suke ya tsaya awajen sanan yakama karfen gadon da duka hannayenshi guda biyu ya tsaya chak yana kallonta kaman ba zaiyi magana ba saikuma yace "sannu zafi yakemiki?" ko kallonshi batayiba sai cigaba da tatttaba wajen datayi daidai hawaye ya zararo zirr daga idon haggunta takai bayan hannunta tashare idanunta, tasake maida hannunta wajen tana tattabawa, ganin yanda take tabawan yay yawa zata iya warware dinkin dayay jiyan nan yasa yazagayo ta bangaren datake hannunshi yakai ahankali yakama hannunta dake kan wajen dinkin da sauri, dago idanunta dasuke akarkace tayi ta kallai, sakon hannun nata yayi da sauri yace "kul kidena tabawa, hannunki zai iya yuwa da germs ko bacteria akai bai kamata kina kai hannun kina taba fresh stitches dashi ba, so kidena" zaro ido tayi kaman irin wacce tadan haukacen nan saikuma tadan duko da kanta tana leka bakinshi kaman irin tanaso taga yay magana kuma, ganin yay shiru yana kallonta kaman yanda take kallonshi yasa ahankali takai yatsanta zata daura kan lips dinshi da sauri yakoma baya, komawa baya itama tayi da sauri saikuma tadaga hannayenta tana kallo, shiru yayi yana kallonta ganin da gaske ne lallai wanan blood yay affecting brain nata, ajiyan zuciya yasauke yana tunanin what exactly ma yakamata yamata yanzu, kujeran plastic yajawo yazauna yace "kalleni kina jina inaso nadam miki tambayoyi duk wani abu dakike ji yanzu ki gayamin" yay maganan yana kallonta still ganin har yanzu ba shi take kallo ba hannunta take kallo, ahankali yace "meke miki ciwo yanzu?" kaman ma batasan Allah yayo mutum awajen ba, wani irin kallon hannunta take tana kallon yan zane zanen lallen hannunta dasuka fara fading, jim yayi yana kallonta ganin kaman ma batasan magana yakeba yasa yakai hannunshi kusada kafarta ya bubbuga katifan yace "ke kallen dawo da hankalin ki nan" tsayar da kallon hannunta take ta kalli hannunshi da sauri daya buga akan katifa kaman irin Abun ya mugun jan hankalinta dinan, hannunta tasada sauri takai kusada tashi hannun itama ta bubbuga tana kallon nashi kaman taga wani irin film, safe gaban goshin shi yayi irin na yadamu dinan, ganin mouth conversion bazai musu aikiba dan bamata gane maiyake cewa yasanya yatashi daga kan kujeran kawai da zumin yafita sai yakira mata nurses azo a mata brush amata wanka ashiryata inyaso bayan sun gama sai akirashi yazo yay mata proper check up, tunanin hakan yasa yajuya ahankali yay wurin kofa wani irin wawan kuka yaji tasaki cikin yar muryanta dayaji har gangan jikinshi ta ratsa tashiga kiciniyar saukowa daga gadon, da sauri yajuyo ya tsaya chak yana kallonta, bare baki tayi tana kuka tana nunashi da hannu tana shirin saukowa yarinyar da tun dazu tai kaman bamatasan yana wajenba shine yanzu danya juya zai fita take wani dan iskan kuka hawaye sun wanke mata ido kaman sune abu mafi saukin fitowa ajikinta, ganin takasa saukowa kaman ma kafarta daya tarike ne dan takasa motsi dashi yasa da sauri yadawo dakin, komawa tayi ta zauna tajuyo tana kallonshi ahankali yabi kafar haggun nata da kallo sanan yamika hannunshi yazaro handglove cikin kwalin shi dake jikin windon dakin ya zura sanan yace "muga kafar" yakai hannunshi ahankali kan kafar yadaura duka hannunshi kai, mugun firgita tayi kaman irin firgita nan nacikin mafarki da sauri yasaki kafan yakoma baya yana kallon fuskarta yama kasa magana, dago kanta itama tayi ta kallai tana turo baki kaman mai shirin yin kuka kaman ba ita bace ta firgita yanzun nan ba, shiru yayi jim yama kasa cemata komi kawai saiya kara jawo kujera ya zauna ya rungume hannayenshi akirji, ganin har lokacin kallonshi take yasa yace "kalla baki magana ne ke kuma ce"? Yay maganan kaman yanda akema kurma magana yana hadawa da yatsa, yanda yay da yatsa tamai itama batare datai magana ba, ijiyan zuciya ya sauke ganin da gaske bata gane maganan shi ne, dagokai yayi ya kalleta ido cikin ido yace "what is your name"? Da sauri tanuna mai kanta cikin yar muryanta tace "name"? Abun ya mugun bashi mamaki ganin tagane turenci rass harda nuna kanta alamun da gaske tagane sunanta ya tambaya, samun kanshi yayi da murmushi dan he call this nasara dan tunda yafara magana da ita sai yanzu yaji tace wani abu, gyadamata kai yayi yace "yes, your name, tell me what is your name" kaman yanda taga ya sakin mata murmushi itama tasakin mai murmushin daya lobar da dimples dinta duka biyun tana leka fuskarshi tace "my name is" tai shiru kaman maison tuno wani abu kaman irin da gaske tanason ta tuno sunanta dinan, saikuma tace "my name issss......name" tai maganan tana lumshe mai idanu, shiru yayi kawai yana kallonta ganin ita karan kanta batasan wacece itaba yasa yace "listen to me, as from today, your name is......" yay shiru yana kallon yanda take kallon bakinshi kaman takosa yafadi mata sunan, dan ijiyan zuciya ya sauke yace "your name is Saheeba" da mugun sauri ta nuna kanta tace "ana Saheeba?" ta tambaye shi, wani irin mugun mamaki ne ya kasheshi jin tamai larabci ahankali ya gyadamata kai yace "anti Saheeba" sanan yace "Saheeba I want you to make my work easy for me, allow me to examine your leg, eye and head, my name is Dr Waleed Warbai, your Dr" yay maganan yana tashi tsaye daga kan kujera, binshi tayi da kallo kaman mai koyon magana tace "a Doctor, injection" tai maganan tana kallon alluran dake ijiye kan table din dakin, kallon alluran yayi kafin yasami kanshi dayin murmushi yace "no injection I promise, now lemme see the leg" yay maganan yana mikamata hannu alamun yabashi kafar, ahankali tadan matsomai da kafar, matsowa yayi shima yakai hannunshi ahankali yadaura kan kafar, firgita tayi sosai da saida yasa yarike kafan gam, ajiyan zuciya ta sauke yace "relax am not gonna hurt you, kidena firgita Inna tabaki" duba kafan yayi ta hanyar mamkatsawa take yagano buge kafan tai dawani abu, probably acikin ruwan nema halan ta buge, sanan yadau torchlight yazo tagaban ta Ahankali yakai hannunshi zai taduba idanunta, firgita tyi takai hannunta da sauri tarike hannun nashi tana kallonshi kaman yanda shima yake kallonta kirjinsu na bugawa atare.[11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣6️⃣ _sorry guys my screen broke yesterday, I couldn't press or even answer call, na gyaro will give you more updates anjima_ Da asuba ya farka wuraren karfe biyar na yamma, dawata shegen yunwa yafara cikin shi har wani hunger contraction yake having, sai yanzu yake tuna rabonshi da abinci tun breakfast din dayayi jiya at yankari kafin ma sufito hiking, shi mutun ne dabai yawancin abinci baima damu da abinci ba amman tunda yaji yunwar nan yunwan takai ne cikin shi so empty, tashi yayi ahankali ya sauka daga kan gadon yay bathroom brush yayi yadauro alwala yafito, cire pyjamas dinshi yayi ya shirya cikin wasu riga da wando nasoft yadi yafito, masallaci yaje yay sallan asubahi sanan yadawo, wayarshi yadauka ya lallubo number Mom, dailing number yayi ringing daya Mom dinshi ta dauka tace "su Dan Yaro mutan yankari yau antuna dani" yatsine fuska yayi kaman zaiyi kuka yace "Mom am hungry please ki aikomin da abinci" da sauri Mom tace "kana Yankarin ne zan aikoma da abinci Dan Yaro"? Girgiza kai yayi yace "nadawo jiya ina orphanage, ki aikomin da abinci am damn hungry bazan iya magana ba yanzu, please Mom don't tell Ammi nadawo kinji" dan jimm Mom tayi kanajin muryanshi kasan yunwan yakeji dan da kyar yakema maganan hakan yasa tace "shikenan, bari namaka simple abu na aiko maka dashi in bama su Abdul ko direba yakawo ma?" da sauri yace "direba su Abdul da bakinsu bai shiru suje su tonani wajen Ammi" dan dariya tayi tace "shikenan matsoraci, sannu kaji nan da 30min abinci zai isoka in sha Allah" "thanks Mom" yafadi ahankali yana fadawa gado soyake yaje yaduba patient din nan but yunwa bazai barshi ba, security yakira ya sanar dasu wani zai kawomai breakfast abari ya shigo suka amsa mai da to cikeda girmamawa, ijiye wayan yayi yadan lumshe ido, ko 1hr cikakke ba'a dauka ba yaji ana kwankwasamai office hakan yasa yamike da kyar yafita kofa yabude ahankali cikeda girmamawa direban Mom dake rikeda wani hadadden basket yace "Barka da safiya yallabai" murmushi yamai yace "Adamu yau baka bata ba" dariya direban Mom Adamu yayi yace "yallabai ai yanzu na gane office din naka sosai ban bata, gidan marayun ne masha Allah da kwai girma Allah dai ya faranta ma kaman yanda kake faranta ma yaran nan marasa shi" murmushi yayi yasa hannu ya karbi basket din yazaro kudi masu yawa ya mikamai, karba Adamu yayi ya shigama Waleed godiya, batare da yadamu ba dan to him is nothing much yace "ka gaidamin da Mom, sai anjima" ya maida kofan yarufe yay ciki zama yayi kasa yana ciro komi na basket din katon flask ne dake cikeda coffee murmushi yayi ya tsiyaya coffee da kamshin shi ke tashi dan harya cika dakin da kamshi a cup, sanan yabude flax yadebi soyayyan Irish da plantain saiya debo pepper soup din fish yazuba agefe yafara ci, abinci ma rahama ne sosai wlh, duk sanda Allah yabaka ka godema dan yunwa bala'i ce, yaci abincin sosai dudda bawani cin azo agani bane but ya koshi, yay Hamdala sanan yature yatashi yakoma kan gado yakarasa shan coffee dinshi, saida ya shanye tass sanan yawuce bathroom wanka yayi yafito daure da towel a waist dinshi gashin kirjinshi sun kwanta gwanin ban sha'awa, ganin wayanshi na ruri yasa yakarasa wajen wayan ya dauka, ganin Mom ne yasa yay murmushi ya dauka yakarasa gaban dressing mirror yasa wayan a speaker ya ijiye yadau cream yabude zai fara shafawa, daga tachan bangaren Mom tace "oya start explaining nasan ai kagama cin abincin yanzu, maiya dawo dakai Abuja bayan duka duka kwanan ku biyu yanzu da tafiya Yankarin? Wani emergency ne yadawo dakai? Bayan nasan 7 days excursion kukeyi every year" dan ajiyan zuciya yasauke yace "Mom now ina miki karyane wai"? "no bakamin karya but ai I need to know abinda yadawo dakai kaida nasan baka wasa da wanan excursion din naku, yanzu dai ina matar naka kuna orphanage dinne tare?" girgiza mata kai yayi yace "a'a na barta achan" cikin daga murya Mom tace "kabarta achan Dan Yaro! Wai lafiyan ka kalau kuwa"? Ahankali yana shafa mai yace "Mom! Arham na wajen fa" dan shiru Mom tayi kaman mai tunani tace "dudda hakan bai kamata kabar yarinya achan ita kadai ba duka duka kwanan ku nawa da auren eh? Abinda zaka mata Arham zai mata ne? Kokuma angayama zata iya tunkaran Arham akan kome takeso ne kaman yanda zata tunkareka kai tsaye ta gayamaka, bama wanan ba maiya kawoka Abuja"? Dan shiru yayi kaman ba zaiyi magana ba saikuma yabata labarin komi, ahankali ta nisa tace "okay okay nagane, yanzu dai inhar kaga case din zai karasa ka kwana yauma toka kira Arham yakaita Airport tadawo nan kajini"? Murya chan kasa yace "tom" cikeda gamsuwa tace "bari na barka ka shirya kaje kaduba patient dinka, sai nakira anjima zan aiko maka da lunch" murmushi yayi yace "you are the best Mom" hararanshi tayi kaman yana wurin ta katse wayanta abinta, shiryawa yay tsaf cikin wata sky blue long sleeve shirt da dark blue wando, neck tie yadauka yasaka sanan yadauko agogonshi rolex ya saka, feshe kanshi yayi da turare sanan yazauna yasaka cover shoe yamike tsaye, wani drawer yabude yadauko wani clean ironed lab coat yarike a hannu yadau wayanshi yachusa a aljihu yabude kofa yafito yana takun nan dai dai duk wanda zai ganshi saiya kara juyowa ya kallai danyay mugun kyau sai baza uban kamshi yake. Agogon hannunshi ya kalla 8 tayi na safe harda yan mintoci, masu shara da watering plant sai gaidashi suke yana amsawa atakaice dan baida son yawan magana ko dogon zance da ma'aikatanshi inbadai takama ba, karasawa clinic din yayi ya shiga da sauri nurses biyu dake wajen suka karaso inda yake. "good morning Dr" "morning" ya amsa atakaice yana tafiya, daya daga cikinsu dake rike da nursing chat sheet ne a hannunta tace "Dr the patient a ICU yanzun nan nadawo daga daukan vitals dinta everything seems normal" gyadakai yayi yana tafiya, sanan tace "jinin daka samata yakare, nacire waiting for you ka shigo tukunna" tai maganan daidai suna karasowa gaban ICU din, ahankali yace "good job Ramlat" murmushi nurse din tayi, dayan nurse din tace "Dr baby Mustafa, that sickle cell from pediatric ward da aka tsinta" gyadamata kai yayi alamun yagane wanne Mustapha take magana tacigaba da magana tace "we lost him last night" chak ya tsaya yajuyo ya kalleta, saikuma yace "wani irin we lost him? Ba Dr Kemi ke handling case dinshi ba amatsayin ta na pediatrician?" gyadamai kai tayi tace "Sir yaron yaji sauki sosai, toys din daka sayomai harya fara amfani dasu yana wasa playing sosai, ko jiya operation din da kayi net nasan bai baka daman dubashi ba, jiya kawai middle of the night temperature shi yay rising saikuma yafara convulsing, Dr Kemi did all she could amman we eventually lost him, actually Dr Kemi ma just left yanzun nan tana tafiya kana shigowa" shiru yayi saikuma ahankali yasaki handle din kofar ICU yajuya direct pediatric ward yaje single room section ya shiga nurses din biyedashi, ahankali yake kallon wani dan karamin jariri da duka duka bazai wuce 5month ba an lullube shi da farin zani dakin an gyara tsaf, dakin hadadden gaske, toys ta saman gadon da aka kwantar dashi dake juyawa wanda zai dinga sa yaron murna yana daukemai hankali, karasawa gaban gadon yayi yaja plastic chair ahankali ya zauna yay shiru yana kallon gawan yaron batare daya budeta ba, sanan yajuyo ya kalli nurses din biyu yace "kuje boys section, akiramin Baba Mani" gyadamai kai sukayi suka fita tareda rufo mai kofan, maida kanshi yayi ya kalli gawan kafin ahankali yasa hannu yabude fuskan yaron tahanyar yaye lullubin ya kallai, yaron baida wani kiba sosai fari ne kaman yaran fulani ga gashi akanshi sak irin gashin agwai yay wani irin haske yadan soma chanza kala dan tun around biyun dare ya rasu, hawaye ne yaji sun taho mai da sauri ya sharesu sanan yatashi yakai lips dinshi ya sumbaci yaron a goshi yana kallon fuskarshi kaman zaimai magana yamai gwarancin yara, ahankali yay murmushi yace "I remember ranan da aka kawo ka gidan marayun nan 5month ago" yay dan shiru yace "wasu manoma guda uku suka kawomin kai, suka cemin sunje gona zasu shuka iri sukaga abu a kwali ga kukan jariri suna budewa aka ganka ba kaya a jikinka jini duk yabata ka daga gani daga haifoka aka yardakai, aka kawomin kai gidan nan, I collected you and held you in my arms ina kallon fuskarka ina wondering wace mahaifiya ce zata haifo wanan kyakkyawan halittan ta yardashi awulakance haka, I whispered to your eyes Mustapha don't cry again domin kuwan Allah yakawo ka idan bazan taba bari daidai da sauro daya ya cijeka ba, mahaifiyarka ta wulakanta ka amman Allah daya hallito ka yace bazaka wulakanta ba yakawo ka inda za'a baka kulawa, allura dakai, abaka duk wata aba dakake so" yay dan shiru ya share hawaye again sanan yace "na aika aka kira Mama Iyami nabata kai nace amai wanka asamai kaya akawomin shi clinic naduba Mustapha, nabaka Mustapha sunan prophet manzon mu da Allah ya aiko mana dashi, after series of tests nagano sikla ne kai, ban karaya ba nace I will do everything in my power naga karayu amman dayake Allah shine ubangijin mu yace baxaka rayuba harka kai matsayin danike tunani ba yau karasu Mustapha, Allah ubangiji ya jikanka, Allah ya gafarta maka, I so much wish dabaka rasu ba but Allah yafini sonka, till we meet again Mustapha" yay maganan ahankali yana kara sumbatar goshin shi daidai lokacin an bude kofan dakin, tashi yayi ahankali batare daya juyoba yasa hannu ya share hawayen shi tass sanan yajuyo ya kalli Baba Mani wani dan tsoho ne daya manyanta cikin shigan arziki ya shigo, hannu Baba Mani yamikamai yace "ina kwana likita, Allah ya gafarta mai kaji, Allah yasa yahuta" Baba Mami yamai gaisuwa dan yasan inhar akai rasuwa a gidan marayun nan yana mugun taba Waleed bakadan ba dudda yana daurewa baya nunawa, dan murmushi Waleed yayi yace "Baba Mani a dauke shi aje amai wanka amai sitira, in angama komi a kirani muyi jana'iza sai akaishi" gyadamai kai Baba Mani yayi yace "shikenan likita kayakuri, tafi ka cigaba da aikin ka, ladanka naga ubangiji ne abinda kake mana mu marasa karfi da wayan nan marayun ubangiji Allah ne kadai zai iya biyan ka, katafi" gyadamai kai yayi yajuya yafita daga dakin nurses din suka bishi, ICU yayi ahankali yabude kofar idanunshi suka sauka kan fararen kafar nan nata tafin kafan so pinkish suna facing kofa, ajiyan zuciya ya sauke ya shiga ciki yakarasa gaban gadon ya tsaya tareda folding hannunshi akirji yana kallon fuskarta da idanunta kenan a lumshe, dauke idanunshi yayi daga kanta yadau torchlight mai kama da byro yadan duko yabude idanunta tareda haskawa yaga idanun sun gyaru dan bakin sun sauko ba kaman jiyaba da ba'a ganin bakin,, sakin idanun yayi yakai yatsunshi biyu ahankali yadaura kan wuyanta, wani irin firgita tayi cikin bacci da saida shima ya firgitan ya janye hannunshi da sauri yakoma baya, ajiyan zuciya ta sauke tacigaba da baccin ta tayi kaman ba itane ta firgita yanzun nan ba, vitals dinta yaduba yaga komi nata is stable sanan ya kalli nurse yace "by 1 zan dawo na dubata" fita yayi daga dakin ya zaga through all wards din yaduba all patients dinshi dat are on admission sanan ya sallami wanda sukaji sauki sosai aka maidasu hostels dinsu, wuraren 10 yagama komi yafito sabida kiran da Baba Mani yamai, alwala yayi yaje akama Mustapha salla suka wuce suka kaishi shibai bisu ba sabida zai koma hospital. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_ ✍️ M SHAKUR 1️⃣ 7️⃣ FREE PAGE Hospital din ya shiga yawuce consulting room dinshi ya zauna, wata nurse ce ta shigo cikeda girmamawa ta gaidashi tace "Sir nafara aiko maka marasa lafiyan for consultation?" dan Jim yayi yana kallon wayanshi sanan yace "in 10mins time lemme make call" wayarshi yadauka yay dialing number Ilham amman har lokacin akashe hakan yasa yaja dan gajeren tsaki yay dialing number Arham, ringing biyu Arham da fitowansu daga wanka kenan tareda Ilham yadaga wayan yana kallon Ilham yana mata signal da cewan Waleed ne yace "Hey X-man ya akayi ne, katashi lpy?" anatse Waleed yace "lpy lau, how are you and how is everything going on around there?" murmushi yayi yace "gamunan duka muna sport yard ne nama fitone dan noise din yaran is too much, alot is going on, above all is super fun" dan murmushi Waleed yayi yace "to Alhamdulillah, I've been calling Ilham wayanta akashe, please blood take her to the airport inaso tadawo Abuja cause I don't think I can come back, har yanzu yarinyar nan bata farka ba banda haka I have alot to do a asibitin nan, please kasa ta a jirgi tazo" wani irin bacin rai Arham yaji ya diran mishi amman yadanne da sauri yace "haba Waleed mesa kake hakane?" dan shiru Waleed yayi dan baigane ina zancen Arham din yayiba yace "what do you mean?" cikin dan fushi Arham yace "what I mean is banga dalilin da dankai bazaka dawoba kacema matarka da already tasaba da yaran nan tadawo ba, karka zama miji mai takura, kaga yanda Ilham ke kulada yaran nan kuwa, kasan bamu taho da any female staff ba, so now anything da yara matan ke bukata wajenta suke zuwa, and she's so happy doing the work, trust me halan ma aikin ya mantar da ita bata kunna wayanta ba, please blood ko for the sake of those children dakeson matarka kayakuri kabarta kawai nanda 4days ne mun dawo yanzu kwanan mu 3 awajen fa, mekace?" dan shiru Waleed yayi kaman mai tunanin maganan Arham din saikuma yace "alright, shikenan to" wani irin hamdala Arham yay a zuciyanshi yace "idan nakoma ciki zan fada mata kana nemanta ta kunna wayanta, bye bari nakoma ciki" ahankali Waleed yace "alright bye, saina kira anjima" katse wayan yayi ya ijiye daidai lokacin nurse din tasake dawowa tabude kofa tace "Sir are you done sufara zuwa?" gyadamata kai yayi tawuce tafita tafara sendo yaransu, yawanci yan matan gidan marayun ne ciwon mara ne most complain dinsu sai masu toilet infection, kasan cewan baya wasa dasu babu wata sabo a tsakanin su yasa kowacce tana zuwa kai tsaye take gayamai matsalanta yana rubuta musu maganin sanan yana kudiran aniyan anjima da yamma da kanshi zaije yay inspecting bayin hostel din matan dan baigane infection din dasuke dama dashiba, one daidai yatashi dan yagaji yatafi mosque sallan azahar yayi sanan yadawo yawuce hospital din yana kallon agogon hannunshi karfe daya harda kusan rabi, direct ICU yayi, ahankali yabude kofan ya shiga har lokacin tana nan yanda yabarta tun safe, samin kanshi yayi da daukan plastic chair yazauna agaban gadon tareda folding hannunshi a kirji batare dayamata komiba yana kallonta kaman irin yanzun ne yasami courage din kallonta tunda yaganta jiya batare da gabanshi yafadi ba, tundaga kan tulin gashinta dayake a daure da lobari yake kallo har zuwa kan fuskarta kafin ya sauka kan hannayenta dayaga akwai yan zanen jan lalli ajiki, kaman ance yakoma baya dan hakanan saiyaga kaman idanunshi sunga wani abu, komar da idanunshi baya yayi yafara kallonta daya kan cikinta xuea fuskarta ya saukar da idanunshi kan kunnenta na dama, chak ya tsayar da idanunshi kan dankunen ta dake makale a idanunshi na dama hakanan yaji ajikinshi yataba ganin this exact dan kunnen, kaman jira mind dinshi yace haka kawai kanshi yay refreshing yatuna shine exact dan kunen dayagani da coffin a yankari, mikewa tsaye yayi da sauri yamika hannunshi yakai kan kunen nata yadaura hannunshi kan dan kunnen yadan daga jikin kunnenta ya kalla, wani irin bin dan kunnen da kallo yayi ganin har yanzu yakasa gasgata cewan dan kunnen ne yasa yakai hannunshi tabayan kunnen yabude hook din ahankali yabudu sanan yamaida hannunshi tagaban kunen zai zare dan kunen mistakenly hannunshi ya sauka kan fatar jikinta yana cire dankunnen wani irin firgita tasake yi da saida yasa yasaki dan kunnen akasa yakoma baya da sauri ya tsaya chak asandare yana kallonta, ware fararen idanunta tayi tarr tabude su duka biyun da har yanzu idanun sun karkace kaman harara garke tana kallon cilin din dakin, wani irin ajiyan zuciya ne ta kufce mai mai kara dayasa tajuyo da kanta ahankali kaman wata robot ta dauramai dara daran fararen idanunta wane madara sukai ido da ido da ita, wani irin kallonshi take kaman yanda shima yake kallonta gabanshi nafaduwa sosai, kasa jure kallon datakemai yayi hakan yasa ya runtse idanunshi da sauri yana karanto addu'o'i aranshi, an tsinci yara manya da kanana da dama agidan marayun nan wasu ma har amasai aka tsince su amman baitaba jin tsoronsu kojin wani abuba sai akan yarinyar nan shi yana rasa takamaimam miyakeji, ko tsoron dasu Dr Kemi suka haddasamai natane a zuciyanshi oho all he knows is yana shakkan ta. "aaaahhsshh, aashh, auuuccchh, a hhhhh....." yaji wata irin siriruwan murya, sassanya maidan gardi dake ratsa zukata na furta kalaman nan irin kalaman nan da ake furtawa idan kana jin zafi ko wani abu namaka zafi, ahankali yashiga bude idanunshi kaman wani mara gaskiya kafin yabude su tarr, zaune yaganta kan gadon tadaura hannunta akan saman kanta tana shafa inda ya aske mata a keya yamata stitches tana bata fuska tana making those sounds alamun zafi hawaye yacika idanunta gam, ahankali yake daga kafa yafara tafiya yana binta da kallo harya zagayo ta inda kafafuwanta suke ya tsaya awajen sanan yakama karfen gadon da duka hannayenshi guda biyu ya tsaya chak yana kallonta kaman ba zaiyi magana ba saikuma yace "sannu zafi yakemiki?" ko kallonshi batayiba sai cigaba da tatttaba wajen datayi daidai hawaye ya zararo zirr daga idon haggunta takai bayan hannunta tashare idanunta, tasake maida hannunta wajen tana tattabawa, ganin yanda take tabawan yay yawa zata iya warware dinkin dayay jiyan nan yasa yazagayo ta bangaren datake hannunshi yakai ahankali yakama hannunta dake kan wajen dinkin da sauri, dago idanunta dasuke akarkace tayi ta kallai, sakon hannun nata yayi da sauri yace "kul kidena tabawa, hannunki zai iya yuwa da germs ko bacteria akai bai kamata kina kai hannun kina taba fresh stitches dashi ba, so kidena" zaro ido tayi kaman irin wacce tadan haukacen nan saikuma tadan duko da kanta tana leka bakinshi kaman irin tanaso taga yay magana kuma, ganin yay shiru yana kallonta kaman yanda take kallonshi yasa ahankali takai yatsanta zata daura kan lips dinshi da sauri yakoma baya, komawa baya itama tayi da sauri saikuma tadaga hannayenta tana kallo, shiru yayi yana kallonta ganin da gaske ne lallai wanan blood yay affecting brain nata, ajiyan zuciya yasauke yana tunanin what exactly ma yakamata yamata yanzu, kujeran plastic yajawo yazauna yace "kalleni kina jina inaso nadam miki tambayoyi duk wani abu dakike ji yanzu ki gayamin" yay maganan yana kallonta still ganin har yanzu ba shi take kallo ba hannunta take kallo, ahankali yace "meke miki ciwo yanzu?" kaman ma batasan Allah yayo mutum awajen ba, wani irin kallon hannunta take tana kallon yan zane zanen lallen hannunta dasuka fara fading, jim yayi yana kallonta ganin kaman ma batasan magana yakeba yasa yakai hannunshi kusada kafarta ya bubbuga katifan yace "ke kallen dawo da hankalin ki nan" tsayar da kallon hannunta take ta kalli hannunshi da sauri daya buga akan katifa kaman irin Abun ya mugun jan hankalinta dinan, hannunta tasada sauri takai kusada tashi hannun itama ta bubbuga tana kallon nashi kaman taga wani irin film, safe gaban goshin shi yayi irin na yadamu dinan, ganin mouth conversion bazai musu aikiba dan bamata gane maiyake cewa yasanya yatashi daga kan kujeran kawai da zumin yafita sai yakira mata nurses azo a mata brush amata wanka ashiryata inyaso bayan sun gama sai akirashi yazo yay mata proper check up, tunanin hakan yasa yajuya ahankali yay wurin kofa wani irin wawan kuka yaji tasaki cikin yar muryanta dayaji har gangan jikinshi ta ratsa tashiga kiciniyar saukowa daga gadon, da sauri yajuyo ya tsaya chak yana kallonta, bare baki tayi tana kuka tana nunashi da hannu tana shirin saukowa yarinyar da tun dazu tai kaman bamatasan yana wajenba shine yanzu danya juya zai fita take wani dan iskan kuka hawaye sun wanke mata ido kaman sune abu mafi saukin fitowa ajikinta, ganin takasa saukowa kaman ma kafarta daya tarike ne dan takasa motsi dashi yasa da sauri yadawo dakin, komawa tayi ta zauna tajuyo tana kallonshi ahankali yabi kafar haggun nata da kallo sanan yamika hannunshi yazaro handglove cikin kwalin shi dake jikin windon dakin ya zura sanan yace "muga kafar" yakai hannunshi ahankali kan kafar yadaura duka hannunshi kai, mugun firgita tayi kaman irin firgita nan nacikin mafarki da sauri yasaki kafan yakoma baya yana kallon fuskarta yama kasa magana, dago kanta itama tayi ta kallai tana turo baki kaman mai shirin yin kuka kaman ba ita bace ta firgita yanzun nan ba, shiru yayi jim yama kasa cemata komi kawai saiya kara jawo kujera ya zauna ya rungume hannayenshi akirji, ganin har lokacin kallonshi take yasa yace "kalla baki magana ne ke kuma ce"? Yay maganan kaman yanda akema kurma magana yana hadawa da yatsa, yanda yay da yatsa tamai itama batare datai magana ba, ijiyan zuciya ya sauke ganin da gaske bata gane maganan shi ne, dagokai yayi ya kalleta ido cikin ido yace "what is your name"? Da sauri tanuna mai kanta cikin yar muryanta tace "name"? Abun ya mugun bashi mamaki ganin tagane turenci rass harda nuna kanta alamun da gaske tagane sunanta ya tambaya, samun kanshi yayi da murmushi dan he call this nasara dan tunda yafara magana da ita sai yanzu yaji tace wani abu, gyadamata kai yayi yace "yes, your name, tell me what is your name" kaman yanda taga ya sakin mata murmushi itama tasakin mai murmushin daya lobar da dimples dinta duka biyun tana leka fuskarshi tace "my name is" tai shiru kaman maison tuno wani abu kaman irin da gaske tanason ta tuno sunanta dinan, saikuma tace "my name issss......name" tai maganan tana lumshe mai idanu, shiru yayi kawai yana kallonta ganin ita karan kanta batasan wacece itaba yasa yace "listen to me, as from today, your name is......" yay shiru yana kallon yanda take kallon bakinshi kaman takosa yafadi mata sunan, dan ijiyan zuciya ya sauke yace "your name is Saheeba" da mugun sauri ta nuna kanta tace "ana Saheeba?" ta tambaye shi, wani irin mugun mamaki ne ya kasheshi jin tamai larabci ahankali ya gyadamata kai yace "anti Saheeba" sanan yace "Saheeba I want you to make my work easy for me, allow me to examine your leg, eye and head, my name is Dr Waleed Warbai, your Dr" yay maganan yana tashi tsaye daga kan kujera, binshi tayi da kallo kaman mai koyon magana tace "a Doctor, injection" tai maganan tana kallon alluran dake ijiye kan table din dakin, kallon alluran yayi kafin yasami kanshi dayin murmushi yace "no injection I promise, now lemme see the leg" yay maganan yana mikamata hannu alamun yabashi kafar, ahankali tadan matsomai da kafar, matsowa yayi shima yakai hannunshi ahankali yadaura kan kafar, firgita tayi sosai da saida yasa yarike kafan gam, ajiyan zuciya ta sauke yace "relax am not gonna hurt you, kidena firgita Inna tabaki" duba kafan yayi ta hanyar mamkatsawa take yagano buge kafan tai dawani abu, probably acikin ruwan nema halan ta buge, sanan yadau torchlight yazo tagaban ta Ahankali yakai hannunshi zai taduba idanunta, firgita tyi takai hannunta da sauri tarike hannun nashi tana kallonshi kaman yanda shima yake kallonta kirjinsu na bugawa atare. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣8️⃣ FREE PAGE Tasowa tayi ahankali taleka fuskarshi tana kallon soft gemunshi da sajenshi har lokacin tana rikeda yatsunshi ta matso da fuskarta daidai saitin fuskarshi takai dayan hannunta ahankali tadaura kan soft gemunshi takama tana zaro ido kabarda hannunta yayi da sauri yakoma baya yana kwalama nurse kira. "Nurse! Nurse, Ramlat" ya kwalama nurse kira da sauri nurse ta taho dakin, cikeda girmamawa tace "gani Dr" anatse ya nuna mata Widad yace "ki kira wata nurse kuzo brush her teeth sanan anata wanka a chanza mata kayan nan be careful kar ruwa yaje kanta in anyway" gyadamai kai tayi tace "to sir" juyawa yayi zai fita Widad takwara wani uban ihu da saida yasa yajuyo da sauri kokarin saukowa take daga gado kota damke shi amman kafanta yahanata sabida ciwon dayike mata, sosai yaji tabashi tausayi saikuma yadawo yace "listen babu abinda zata miki I will be back soon okay" sanan ya kalli nurse din yace "make sure an bata abinci taci, go to the orphanage kitche......" saikuma yay shiru bai karasa maganan ba yace "just tafida ita bayin kimata all abubuwan danace, zan aiko da abinci dazaki bata da drugs kuma, zan fita yanzu zanje wani hospital acikin gadi nataho mata da glasses dazai gyara eye balls dinan nata in tana kallon ka" gyadamai kai nurse din tayi tace "saika dawo Sir" tsugunnawa yayi yadauki dan kunen ta daya cire dazu tai ihun dayasa yasaki dan kunen akasa, juyawa yayi yafita yana jiyota tana rangada shegen ihu da kuka, fita yayi daga asibitin yana dannama Mom dinshi kira ringing daya ta dauka yace "Mom ki aikomin da mota yanzu please" kaman zata tambayeshi saikuma tace "to bari na aiko direba" dan tare take da mai gidan ta, wucewa yayi ya shiga office dinshi basket din abincin rana da Mom ta aiko mai dashi yasa aka karba aka ijiyemai a office yadauka yafito, wani staff dinshi yakira yabashi basket din yace "kai this basket ICU kabama nurse din dake wurin" gyadamai kai staff din yayi yajuya yatafi shikuma yashiga cikin office, wanka yayi ya shirya cikin wasu fararen yadi yafeshe turare yay shegen kyau zama yayi abakin gado yabude wayanshi yay dialing number Ilham but har lokacin akashe tabe baki yayi yamike tsaye jin dayayi ana knocking kofar office dinshi, fitowa yayi direban Mom ne yace "barka da fitowa yallabai" gyadamai kai yayi direban ya mikamai key mota yace "Hajiya tace nakawoma mota gatanan nai parking dinta awaje" karban key yayi da murmushi yace "nagode" murmushi shima direban yayi yace "bari ni nakoma" da sauri Waleed yace "no muje na rage maka hanya ai fita zanyi nima" gyadamai kai Direban yayi ba karamin dadin hakan yajiba, fitowa Waleed yay daga office din yamaida kofan yarufe sanan yay wurin motan shiga sukayi ciki yaja motan sukabar gidan marayun, cikin gari suka shigo akan wata babban Junction ya sauke shi yazaro kudade masu yawa yamikamai yace "gashinan sai kahau abin hawa ni zan dauki wanan hanyar ne" sauka yayi yace "nagode, nagode Allah ikara taimakawa" murmushi kawai Waleed yamai yadauki wata titi daban, agaban wata babban super market yayi parking ya shiga siyayyan abubuwa yayi tundaga kan kayan abinci su buhun shinkafa, semi, wake jarkan manja da man gyada dasu madara da ovaltine sanan yakoma wajen supplement yasai irin supplements dinan na 30+ matan dasuka wuce shekaru talatin above yakamata suna sha, yawuce yabiya kudi ma'aikatan wajen sukamai packaging kayan sanan suka fitomai dashi, bude boot yayi suka zubamai kayan suka rufe yakoma cikin mota abinci yatayar yawuce yafita daga premises din, wata hanyar ya dauka kafin yay parking agaban wani dan madaidaicin gida mai kyau, kashe motar yayi yafito ya tsaya yana addu'an Allah ya jefo wasu yaran ko almajirai bai gama tunanin ba saiga yaran layin sun keto dagudu daga gani dana kwallo suke, dayake sun sanshi sosai kodan duk randa zaizo saiya musu kyautane yasa suka kwaso da gudu kafin ma yakirasu. "Yaya Waleed, Yaya Waleed, ina wuni, ina wuni, ina wuni" haka duk suka shiga gaidashi ajejjere harya rasa nawane zai fara amsawa murmushi kawai ya sakan musu da sauri kafinma yay magana sukace "me za'a shigan maka dashi cikin gidan Ya Waleed?" remote din motan ya danna hakan yasa boot din motar ya bude, kafinma yay magana suka shiga sunkutan kayan suna cikin gidansu Arham dashi saida suka gama shiga dashi tatas sanan suka dawo wajenshi sukace "munkai Yaya Waleed" kudi yaciro daga aljihunshi yakirga 20k yabasu karba sukayi suna ihu sunamai godiya murmushi kawai yayi yawuce ya shige cikin gidan daidai Maman su Arham nafitowa daga dakin tana tafi da hannu cikeda mamaki, ganin Arham yasa takama habanta tace "ai tunda naga kaya niki niki nasan sai Waleed, waikai Waleed baka gajiya da kashemana kudi dagakai har mahaifiyarka baku gajiya, ai yakamata yanzu duk kubar abubuwan nan tunda kunbama Arham aiki ana biyanshi, eh Waleed" ta karashe maganan da mugun mamaki, murmushi kawai Waleed yayi adan kunyace ya tsugunna yace "ina yini Mama, ya karin karfin jiki" dan dariyan farin ciki tayi takai hannu ta dagoshi a rayuwa tanason Waleed, so dashi kanshi Waleed baisan iyakan son datakemai ba, bala'in sonshi take sabida yama danta komi a rayuwa sanan yaso danta tsakani ga Allah, sanan ya fifita shi sama da kowa nashi aduniyan nan, shafa kanshi tayi tace "Waleed ai jiki kam Alhamdulillah, wayan nan magungunan daka bawa Arham yakawo min tunda nasha yanda kasan tsafi shikenan, muje ciki kaji nacika da surutu kahuta" tai maganan tana janshi ciki, ciki suka shiga, zama yayi akan kujera itama tazauna kujeran dake kallonshi tana washe baki bala'in dadi takeji tace "sannu dazuwa kaji Waleed ubangiji Allah yamaka albarka, Allah kuma yabarka da matarka lafiya" ahankali yace "Ameen Mama nagode" "madallah, madallah, yanzu me za'a kawo maka kaci? Dambu mukai da ranan nan bama adade da sauke ta ba, akawo maka da soyayyan naman talo talo" gyada mata kai yayi yace "Mama kin yanka tala talon kine" "uhmm" ta sauke ajiyan zuciya tana tabe baki tace "ai tunda dan uwanka yatasa yan tala talolina agaba waishi ihunsu na hanashi bacci zai yankasu nace a'a karya sake yatabamin kayana nasan wani abu zai samesu, kasan Arham da shegen bakin hali, ingayama shine fa jiya suka fara zazzabi fa nako gille kayana, nida Salma saici muke, ai bangayamaka ba dayake shekaran jiya tazo ko Arham ma ban gayamishi ba yar wajen kanwata Salma tazo daga kauye, kawai na karbeta koya kagani Waleed, kaga abokin ka bawani zama yakeba kullum ni kadai awanan tangamemen gida daka siyamin Waleed wlh nagaji bansaba rayuwa ni kadaiba, ko kanwar tawama dan mijinta yaki yardane da sonayi su dawo nan kawai tunda gidan gawuri koba komi ai nasami masu debemin kewa" gyadamata kai yayi yace "hakane Mama" tabe baki tayi saikuma ta nisa ta kwalama Salma kira. "Salameme, Salameme, ke Ummu Salama" amsawa yarinyar tayi daga kitchen tace "na'am gani nan zuwa Mama" maida kanta tayi ta kalli Waleed tace "danan bari yarinyar nan tazo kaganta" ki 2min ba'a dauka ba wata doguwan yarinya da tamafi Widad tsayi tana sanye da doguwan rigan atampa ja yarinyar kyakkyawa gata Black beauty, karasowa gaban Mama tayi da sauri tace "Mama gani" baki Mama ta kama tace "nifa dadi na dake haka kike abu kaman makauniya Salma, bakiga yayanki bane Yaya Waleed" tamata pointing Waleed dake zaune a kujeran data juyama baya, juyowa tayi ahankali ta kalli Waleed, jitayi kunya yakamata batasan lokacin data kara duka hannayenta biyuba tarufe fuskarta cikeda kunyan yaran kauyen nan tana washe baki tace "ina kwana" da sauri Mama tace "kwana kuma Salma, oh ni Bilkisu wanga yarinyar wanga yarinya dai to, Allah nagode maka" dan murmushi Waleed yayi yanabin yarinyar dakeda kunyan bala'i da kallo, Mama tace "tashi kije ki zuboma yayanki abinci kihado komi a tray kaman yanda nakoyamiki jiya ki kawomai" tashi tayi tawuce kitchen Mama tabita da kallo tana girgiza kai sanan ta kalli Waleed tace "Waleed kaga Salman ko ya kaganta, yar kanwata ce a kauye suke, ta taba aure sau daya amman ko sati hudu ba'ayi da bakin ba mijin yarasu maciji ya sareshi a gona, ingayamaka shikenan yarasu, yabarta da cikin sati biyu, cikin shima watanshi biyu jikinta yafice da kanshi, na daukota ne musamman sabida nahada aurenta dana dan uwanka" wani irin mahaukacin dariya ne Waleed yaji yazomai da kyar yarike dariyan yadan zaro ido yana kallon Mama, zata sake magana daidai lokacin Salma ta shigo. Shigowa tayi rikeda tray mai kyau da flask ke kai da plate da serving spoon da cup dakuma juice da ruwa, tun kafin takaraso gaban falon Mama kebinta da kallo sabida taga kotai shirme ganin takawo komi daidai kaman yanda ta koyanata yasa ta sauke ijiyan zuciya, karasowa gaban Waleed yayi daya saukar da kanshi kasa dariya na neman kwasheshi shiba yarinyar kebashi dariya ba Arham kebashi dariya danhar yafara hango bura'uban da Arham zeyi idan Mama tagabatar mai da maganan, harta ijiye ta juya takoma ciki baima saniba sai maganan Mama yaji tace "ya kaganta fisabilillahi Waleed batayi ba"? Gyadama Mama kai yayi yakai kololuwa wajen damke dariyan shi amman saida yar murmushi ta subuce mai yace "tayi Mama" washe baki Mama tayi tace "Allah sarki Waleed wlh kai dan Albarka ne, yaro maijin maganan iyayenshi, jibi fa kai Ammi ka tacemin tana gabatar maka da zancen auren kai na'am inama ace haka dan uwan naka Arham yake, amman ina Arham baida wanan kawaicin" dan shiru tayi tana kallonshi sosai take farin cikin ganinshi ko Allah yasan tanajin Waleed har ranta sosai, ajiyan zuciya ta sauke tace "Waleed daman inaso nakawo maka karan dan uwanka" shidai kanshi nakasa baice komiba tace "kasan menene dan Albarka abokin ka baya kyautamin, tunda yay tafiyan nan bai kirani ba sai jiya, kasan bani iya fito da sunanshi awayan nan daka siyamin, amman ai shi yanada number ta, saida nafita na shiga nan gidan makotan nawa na nemo danta Aliyu inma karike maka zance har jiran Aliyun nayi yadawo daga gantalinshi dan kawai na ganshi na bashi wayan nace yanemo min Arham shinefa yaciro number yakira nasamu nai magana dashi, wai ina mishi korafin bayi wani kirani shine yahau cewa waini nacika fada abu kadan fada kome yayi fada, wai naje naga yanda akema ba'a maka fada kome zakayi agidan ku" ta karashe maganan ahankali alamun kalman yamata ciwo, bata cika kawomai karan Arham ba amman tunda yaga wanan karan takawo mai karan abun yay mata ciwone, ahankali yadago kanshi ya kalleta yace "Mama kiyakuri, ba lallai yanda kikadau zancen haka yake nufiba, kinsan aiki yake sosai achan ko hayaniyan yara zai iyasa yaji baya hayyacinshi, kimai uzuri aiba haka yakeba...." da sauri tace "wlh haka yake, kai bazaka gane Arham bane, nasan abokin kane ka tsani kaji laifinshi wanan halinka ne tun kana yaro amman saina fada saidai ku hadakai kuita fushi dani, kaga wanan Arham din dakake gani" tai maganan tana karkada kafafu tace "Waleed bawai banda godiyan Allah ba, kokuma inafa takura ba wlh Waleed bancin kudin Arham, nasan inada komi kamin komi Waleed amman wani zubin kowace uwa zataso ko biyar ne danta yadauka yabata yace ungo Mama asamana albarka, Waleed kaine chefanena duk wata, kaine motata kudin man da ake xubamin ciki, kaine magunguna na sanan kaine mai bani kudin kashewa tun kana dan kankanin ka kakemin wanan hidiman har gobe, bawai korafi nakema ba kokuma naga gazawar ka a'a yakamata ayanzu Arham kemin irin abubuwan nan sabida yagama makaranta yanada aikin yi, amman bayi komi, haryakai ga nace Arham ban kaza saida yace ai Waleed yayi miki kaza kokuma kinada kudi Waleed yabaki, kaga ai badadi" hakanan Waleed yaji baiji dadin abinda Arham yayi ba anatse yace "kiyakuri Mama zai gyara in sha Allah" tabe baki tayi tace "Allah yasa ci abincin ka na tsareka da surutu dan Albarka" spoon yadauka ahankali yashiga cin dambun yaci sosai dan yakusan cinye plate din sanan yature, sosai sukasha hira da Mama dudda kusan rabinta karan Arham take kawomai, sai wuraren la'asar yabar gidan, wani eye clinic yaje kai tsaye yafadi irin glasses din dayake so a keramai akamai yabiya kudi ya shiga mota yakoma orphanage. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 1️⃣9️⃣ & 2️⃣0️⃣ FREE PAGE Tsayawa yayi yay sallan magrib sanan yawuce clinic, yana shiga daidai Dr Kemi data shigo aiki da yamman nan dan night take tace "good evening Dr Warbai" gyada mata yayi tace "naduba patient ta ICU ai shi lost memory completely babu abinda tasani yanzu, zan chanza mata daki na maida ita normal ward tunda babu wani huge issue muna fitowa zamu wuceda ita idanunta suka sauka acikin pediatric ward kaga kuka kuwa" tadanyi shiru da mugun mamaki tace "she almost turned this hospital up side down, hakan yasa dan asami lpy babu kuma kyau tana kuka tana bare baki kodan aikin dake kanta yasa kawai na kaita pediatric ward din, Dr kaga murna kuwa" tadanyi dariya tace "tamafi yara wasa da kayan cikin ward din the thing is damn funny go see for yourself" sanan Dr Kemi tace "I think using medical lens zaiyi correcting those eye balls dinta dasuka karkace" ahankali Waleed yace "I've already got 1" yajuya yay pediatric ward din, ahankali yabude kofan dakin ya tsaya chak abakin kofa gadaje uku ne adakin, dakin cike yake da kayan wasa, kowani gado nada nashi kayan wasan asama dake juyawa kaman fa ka, tana zaune kan gadon tsakiyan ukun, tajuyama kofa baya, an saka mata wani pink gown na hospital mai kyau, kanan nata adaure yanda ya daure natashi saikuma gadan inda yama aski yay dinki, wani irin kallon kayan wasan take takai dan yatsanta tana tabawa take wasu yare da baima gane takamaiman metake cewa, dudda baya ganin fuskarta but he could see and feel how happy she was, dan murmushi yasaki yana kallonta still danbama tasan da zuwan mutum ba. Daidai takai hannunta zata kama toy din jirgin saman ta tsaya chak kaman ance ta tsaya sanan tajuyo ahankali ta hanyar waiga kanta ido da ido dasukayi da Waleed yasa da sauri ta juyo da duka jikinta ta fuskance shi da kyau, ta washe fararen hakoranta tareda wani irin daga hannu ta shiga tafi tana dan diddirke azaunsn ita adole murna take yadawo, murmushi yayi yasan one thing dashi ko staff dinshi basa ganin murmushin shi kaman yaran gidan marayun shi, haka yake sonsu ne is a natural thing in him, daga kafanshi yayi ya shigo dakin yasa hannu ya janyo kofan yana tafiya ahankali yana dumfaro ta, kasa daurewa tayi dan kaman duk taku dayan dayayi kara samata farin ciki yake yasa tama dena tafin tafara yarfe hannu bakinta na babar babar tanason tai magana amman maganan yaki fita karasowa gaban gadon yayi yace "someone is happy to see me" kyalkyacewa da dariya tayi irin na yaran nan bai Ankara ba yana kokarin ciro glasses din daya kawo mata kawai yaji ta rungume shi daga zaunen tsam tsam kanta nakan cikinshi, sakin glass din hannunshi yayi da sauri glasses din yafada kan gado da ace hannunshi na saitin kasan da sai glass din yafashe, sunkai kusan 3min ahaka tana rungume dashi tana dariya sanan yadan tureta ta hanyar kwace kanshi yadan koma baya yace "sit Saheeba" komawa tayi ta zauna hakan yasa yadan matso kusada gadon, glasses din yadauka cikin harshen turenci yace "this will help with your sight, zoki sa nagani" fuskarshi takawo mai da sauri ahankali ya zura mata glass din sanan ya kalleta ba karamin kyau glass din yamata ba sanan ya maida idanunta daidai, inta tana sanye da glasses din ka kalleta zaka ga kaman idanun are normal inta cirene zakaga idanun sun karkace. "are you hungry?" yamata tambayan yana dauke kanshi daga kallonta sabida wani irin faduwa gaba yake inhar tana kallonshi suna having eyes contact, hamma tayi ganin bata rufe bakiba yasa yakai hannunshi yarufe mata yadan kalli idonta yace "always do dis okay" gyadamai kai tayi tana kwanciya ahankali tamika hannunta takama hannunshi, sake dagokai yayi ya kalleta amman saiyaga ta lumshe ido kafin kace me bacci yay awon gaba da ita yana tsaye akanta tana rikeda hannunshi, bude kofan ward din akayi aka shigo hakan yasa ya waiga yana daura hannunshi kan nata yana kokarin zare hannunshi daga rikon datamai, Dr Kemi ce ta shigo tana kallon yanda tarike hannun Waleed, ahankali Waleed yazare hannunshi sanan yakama hannunta ya ijiye kusada ita ahankali yaja bargo ya lullube ta yace "just look at her tagaji sosai which is abinda bai kamata ba, ko kadan ba'ason wanda keda brain damage yay stressing kanshi out" ahankali Dr Kemi tace "to Dr Warbai ba dole ba, I came in this evening I met this gurl crying, kukanta ko'ina shi akaeji awanan clinic din gatada shegen zakin murya, to ninefa namata yan dabaru tai shiru, da nakawo ta nan kuma saitai kaman ba ita tagama kuka ba she was so happy" dan ajiyan zuciya ya sauke yamaida kanshi ya kalleta yace "ko kadan bai kamata tana kuka da ihu hakaba, daman I was waiting for ta farka naga yanda take, normally someone dakeda brain damage that is caused by fluid in the brain yakamata the amount of sleep dayake having each day yay doubling lokacin datake staying up, her brain needs to relax, batason pressure damuwa da koma wani kalan abune, akwai wasu magunguna we don't have them in our clinic but yanzu ina fita zan aika akawo, zata dinga shansu zata dinga bacci kaman wacce ke coma, this girl needs sleep from now till few months, the more tana bacci tana relaxing the more jinin na tsinkewa yana draining kanshi with the help of magungunan" gyadamai kai Dr Kemi tayi sanan tace "Dr what about broadcasting din tsintuwarta, naga haka kakeyi ma duk wanda aka tsinta aka kawo idan ankawoshi da any rashin lafiya kowani abu zakai treating nashi dazaran ya warke u send his picture da labarin yanda ya iso gidan marayun ka to government, sukama government zasu yada labaran akafafan yada labari, idan yanada family they come for him idan kuma ba'a samu family shiba yacigaba da zama damu" shiru yayi yana kallon fuskar Widad, she is the first person da tunda yabude gidan marayun nan aka kawota yaji baison yay wanan, hakanan jikinshi ke bashi yarinyar is in danger, serious danger, banda haka yaga bruises na alamun an damke mutum a hannayenta, this injury kanta he also belive ba faduwa bane ko accident this is an intentional Well planned incident, he just wanna take his time yasamu yarinyar ta sami lafiya, first now is fluid din kanta ya tsotse inhar ya tsotse zata dena wanan abnormal behavior, daga nan he concentrate on gaining her memory back, akwai wani workshop daya tabayi a 🇨🇺 Cuba kan memory lost, but dole sai fluid din kanta ya tsane sanan zai iya daurata kan medication na memory lost, yanaso harsaitaji sauki tafadi mai she is in danger ko she is not before yay announcing tsintuwarta, for now her safety and her wellbeing first. "Dr Warbai" dago idanu Waleed yayi ya kalleta tace "tunanin me kakeyi ne?" dan yatsine fuska yayi yace "alot! Anyway I will see about abinda kika fadi, bari tadanji sauki tukunna, bari naje na aika magungunan da allurai zaki mata some this night" gyadamai kai tayi yawuce yafita daga dakin, rubuta sunan all abinda yake bukata yake sanan yabama wani ma'aikacin shi da kudi yaje yasayo yakaima Dr Kemi shikuma yawuce office dinshi. ****** _Bauchi_ "wash Allah na blood zaka kasheni, wai kai wani irin jarababbe ne, yaufa sau daya kafita kaje wajen yaran nan ko 20min bakayiba kadawo, baka tsoron wani yafadi ma Waleed ba'a ganinka awajen" murmushi yayi yana cillar da towel din datake daure dashi yadauketa chak yakaita gaban mirror yazaunar da ita yana ware kafafunta yana shigewa yace "bazasu fadaba, Waleed communicate with me only, bayan gani maisa zai kira wasu? Dan kome nafada yazauna awajen shi Lawyer, I need that sweet pus, zansa chaji" yay maganan yana jawo kanta yana kama bakinta yakai hannunshi duka biyun kan boobs dinta yana matsa nipple din, bankaromai kirji tayi tace "Arhammmmm wlh nagaji......." yatsanshi yadaura kan lips dinta yace "kinajin dick dina ciki zakiji baki gajiba" yay maganan yana tura joystick dinshi ciki. "wassshhhh Arham waida magani kake amfani ne?" harshen shi yadaura kan kunnenta yace "tsabagen dadin wanan hausa fulani boy dinne ke driving naki nuts" zarowa yayi ahankali yana wani gwale kafa sanan yasake zuba matashi ciki, rawa kafanta yafara tace "innalillahi wayyo Allah na, wlh abokin ka bayamin haka bai iyaba" wani irin janyo cinyoyinta yayi yasake zuba mata rawa jikinta yafara yawani irin danna ciki tana ihu ringing da wayarta yafara yasa duk suka juyo, tsaki tadanja tace "cigaba dayi" girgiza matakai yayi yace "is Waleed jeki dauki wayar karyay tunanin wani abu" yay maganan yana zaro erected joystick dinshi daga cikinta ya sauke ta daga gaban madubin, ahankali take tafiya takarasa gaban gadon tadau wayan tai picking tasa a speaker tace "hello" "Khadija" yakirata ahankali as usual, wani irin bakinciki Arham yaji yatasomai hakan yasa yawani mike yace "lemme f**k your wife right to your ears" yay gaban gadon daidai tana cewa "Ya aiki?" wani irin dagata Arham yayi da bala'in fushi, tana kokarin fizge kanta yahanata, daura hannayenta yayi kan gadon yasa wayan a tsakiyan hannayenta sanan yasa tai ruku'u daidai Waleed na tambayanta. "Ya Bauchi? Am sorry nabarki ke kadai" girgixa mai kai tayi tana murmushi ko Allah yasan son datakema Waleed is natural, ahankali tace "wlh I miss you so much baby" cikin wani irin fushi Arham ya shigeta jin abinda tafadima Waleed, saida tarafka uban ihu. "wayyo Allah na shiga uku ahhhhh" arude Waleed yace "what's the matter? Meya sameki"? Cikin wata mahaukacin fushi Arham yasake bugamata gwatso batasan lokacin data daura hannunta kan bakinta ba tana ihun dabaya fita, Waleed nata hello hello amman shiru, zuba mata duka Arham yayi a ass yawani irin danneta ya shiga fucking nata rough, yakama nipples dinta yaja kaman zai cire yana ramming nata, zare hannunta tayi daga bakin tacigaba da kurma ihu tana kokarin tureshi. "wayyo Allah zan mutu, na shiga uku wayyo" katse wayan Waleed yayi da sauri ya shiga kiran Arham, sosai tashiga kokawa da Arham tace "ka saken banso tunda zalinta ta kake" ta daddage ta fizge kanta tafada kan gado, tana masifa sunma mata hotel suke, azuciye yahau gadon idanunshi sun mugun kada da ita kanta saida taji tsoro ya fizgota yakifar da ita akan gadon yace "agabana kike cema wani kina sonshi you miss him, what about me?" da daka mata tsaya yana Jan kanta kaman zai ciremata gashi, buge hannunshi tayi tace "dalla kadena jamin gashi dannace mai I miss him kazaci i meant it ne, you've lost it" ta tureshi zata tashi fizgota yayi baiyi wata wataba ya dauketa da lafiyayyan mari akunci yakai hannunshi wuyanta ya shaketa sosai idanunshi na ciccika da hawaye yace "I love you Khadija, tun ranan dana fara ganinki a day to your wedding nafara sonki, na nuna miki ta hanyoyi da dama but baki gani, you think am sexing you making you happy sabida iskanci ne, no sonki nike, I love you much more than you could think, but baki ganin sonda nike miki sabida am not Waleed, banda kudi, nima yaron Waleed ne his slave dake mishi aiki dat he boss around ya aikeni duk inda yaga dama, Waleed, Waleed, Waleed, komi Waleed everything Waleed, the whole world is against me kowa Waleed yake so banda ni, hatta Mahaifiyata Waleed takeso banda ni sabida yanada kudi? Sabida he's rich? He was born with a silver spoon nikuma a'a I wss born spoon less ko robber spoon ba'a haifan dashi ba balle silver one, saisa duk kuke sonshi, the amount of love he's receiving niko kwatanshi banda shi, I am tired, nagaji, nagaj......." tarin data fara tana kakarin mutuwa ne yasa yasaketa tazube akasan dakin tana tari tana sosa wuya, juyawa yayi yakama kanshi dayakeji kaman ya tarwatse ayanda yakejin kanshi yanzu dazaiga Waleed dazai iya chakamai wuka koya huta, ko kowa zai fara ganinshi instead of a ganshi, juyowa yayi ya kalleta tana sosa wuya tana tari yace "Waleed ko, you miss him" binta yay kasan, yawani irin turata tai flat akasa har kanta na kumewa yakama kafafunta yadaga asama, azuciye ya shigeta yana danneta ko motsi bata iyayi yafara trusting in kaman wanda yazare yace "Waleed come and see yes me Arham, am fucking your wife's pussy, ina saduwa da ita, inacin matarka exactly the same way dakayi, najuye sperm dina kaima kazo kazuba, kome kaci sainaci aduniyan nan, kome kaso sainaso, kome kahau sainahau, kome kasa sainasa, ko'ina ka tsaya saina tsaya amukamin nima, do you know why? Cus am jealous of you, am fucking jealous of you, yess everything turns in your favor not me, babu wanda ke noticing nawa saidai ayi noticing naka, u have the full attention a ko'ina mukaje while am the slave the messenger, the PA the meeting organiser, okay now come and see kwanciya da matarka nake and I cum inside, yes aciki nake kawowa and wanan cikin nata mark my word kafin yay bearing yaranka yarana zata fara kawowa duniyan nan dan na nuna maka nima nafi karfinka" yanda yakeyi kaman zai kasheta yasa da muryanta dabata fita sosai tace "Ar......ham, am sor......ry" "quite! Yadaka mata shegiyan tsawa yanayi, fashewa da kuka tayi sosai tana begging nashi da muryanta dabata fita sosai amman baiko saurareta ba sai a ranan ta yarda is true maza na punishing mace da this same joystick dasuke baki pleasure dashi, Arham ya wahalar da ita da saida taji tai dana sanin cema Waleed I miss you datayi, sai wuraren four yatashi akanta yaja kayanshi cikin fushi yasaka sanan yabude kofan dakinta yafita yashiga nashi duk tana kuka, tun bayan Waleed yatafi tare suke kwana he has been super sweet romantic towards her bai taba bata matarai ba amman yau ita tabata mai but is not her fault batasan yana sonta ba she thought fling kawai suke abinsu, da rarrafe tawuce ta shiga bayi tayo wanka tafito tahau kan gado tana kallon Waleed nasake kiranta takasa amsawa haka tabar wayan har bacci yay gaba da ita. Da safe ta farka, tagumi tayi kalaman Waleed namata yawo akai. _komi Waleed komi Waleed, you think iam making you happy sexing you for fun ne, is because I love you, ina mugun sonki daga ranan dana fara ganinki a day to your wedding_ wani cute murmushi ne ya subuce mata bata taba having hot and crazy lover in her life kaman Arham ba, ace soyayyan datake gani a Hollywood movies is real namiji nason budurwan shi but yazaneta yana sexing nata at the same time she always wanted that gashi jiya Arham yamata dudda taci bakar wuya. Wayarta dataji tai ringing yasa tajuya ganin Waleed ne yasa taja tsaki jitayi ranta yabaci, gudun karyay tunanin wani abu yasa takarasa tadauki wayan kafin tai magana yace "maiya sameki jiya kiketa ihu?" rasa mezatace mai tayi da kyar tahado yar kalaman bakinta tace "marana naji yadaure and am not on mp fa" shiru yayi saikuma yatabe bakinshi as usual yace "kisha lip tea mai zafi" "tom" ta amsamai karya kawo mata maganan komawa yasa da sauri tace "Baby inajin dadin activities naku wlh, kaga yanda yaranka kesona kaman ka kara mana kwanaki instead of 7days muyi 2weeks mana" dan dariya yayi yace "ahhh kinji dadin jibi zaku dawo anyway, bamayi for morethan a week" tabe baki tayi tadan harari wayan tace "shikenan zan koma bacci natashi saina tafi bye" ahankali shima yacemata bye ya katse wayan, Kwanciya tayi ahankali tana tunanin Arham addu'a take Allah yasa yazo, amman shiru shiru har yamma ko leko dakin baiyiba, takasa zaune takasa tsaye, ko abincin datai order takasa ci sosai, wuraren 10 patient dinta yakare, hijabi tasaka har kasa, tabude kofan dakinta ahankali kaman wani zai ganta yafito tazo gaban dakin Arham din, batare datai Knocking ba tamurza handle din jitayi kofan yabudu tura kofan tayi ta shiga da sauri yana kallon Arham daya kife akan gado yana wasa da bedside lamp ya kashe ya kunna yakashe ya kunna yamai dagokai ya kalleta, ahankali ta maida kofar tarufe tasaka sakata, sanan takaraso gaban gadon ahankali tazauna takai hannunta kan saman kanshi ta shafa murya chan kasa tace "I am so sorry Arham" kojuyowa baiyiba balle tasaran dazai kalleta ba saima cigaba da kashewa da kunna wuta dayake yi, hannunta takai yakama hannu dayake kashe wutan dashi tace "Arham" ganin yaki kallonta still dudda tarike hannunshi yasa tace "I am so sorry for my actions, Arham kafahimce ni bantaba sanin sona kakeba sai jiya daka fadimin, and now that you've told me you also made me realise that dan zaman nan danayi dakai nima nakamu da sonka, banta kallonka dawai bakada kudi kai yaron Waleed ne yana saka aiki bossing u around ba saisa bana sonka ba, a'a wlh is not like that, Arham am willing to do anything for you dazai sakaka farin ciki sabida maganganun ka na jiya yasa nagane you've been through alot, kasan mene inada 7M a account din kudade nane hakan malak nabaka duka kyauta, kaima u will be reach, and I promise zan dinga karban kudi a hannun Waleed ina baka, zan koma aiki I know all my salary I will be giving you, I will make you rich koda baikai na Waleed ba but u will be reach da kaima sai ansan yes kanada kudi karka sake looking down on yourself, kagama karatun ka kanada kwali inhar yana bossing naka around mesa bakaje ka nemi aiki wani wuri ka barmai gidan marayun shiba eh? Ban account number ka" tashi yayi ahankali yarungumeta itama rungume shi back tayi sun dade ahaka sanan tadago shi tace "is okay, bani account number ka" ahankali yashiga karanto mata baki kunya ya yaye hijabinta ya shiga ciki yana kallonta daga ita sai pant and bra, kwanciya yayi kan cinyanta yaciro boobs dinta yakai bakinshi ya shiga tsotsa, ashagwabe tace "transfer fa nake zaka hanani yanzu" dakatar da shan nonon yayi tai maza ta turamai all the 7m sanan tayaye hijabin ta, tana kallon fuskarshi taga idanunshi sun kode, ahankali tace "kuka kayi?" kaman bazai ce komiba saikuma ya gyada matakai alamun eh, wani irin mugun tausayi yabata, ganin haka yasa yagane ya chapke ta a hannu tatas ahankali cikin murya kaman zaiyi kuka yace "i was very small da babana ya rasu ya barni da Mama agidan haya, so Mama na dauramin ayaba naje talla" dan nisawa yayi yace "I was an ayaba seller" dan shiru yayi yana kallon yanda hawaye suka cika mata ido yace "na girmi Waleed so he saw me yana sona yazo yafara bina muna tallan tare, ranan da Ammi tagano danta tallan ayaba yakeyi har Mama na saida ta mara tasa aka kulle Mama wai tana aika yaronta talla dani" Waleed cry cry yagayama mahaifinshi ganin haka babanshi yazo ya sakemu sanan yabamu hakuri, daga baya Waleed yasa babanshi yasani a school dinsu, Waleed na sona but as a person da yanamai aiki I remember nike bashi abinci abaki a lokacin inba hakaba bazai ciba tun muna yara nake ma Waleed bauta sabida yaga shine gatana yamin komi na kaini University, yasaima Mama gida da mota yana kaimata kayan abinci da komi saisa Mama tafison shi akaina danshi kan Waleed matar nan zata iya tsinemin" ya karshe maganan da tone din kuka da sauri yajuya ya chapke boobs dinta ya shiga sha, da goshi Ilham tayi tai cupping face dinshi tana kallonshi tace "babu wanda zai kara mayar dakai slave ina raye, I will give u anything u want, kome kakeso just tell me zan maka, I love you Arham" fashewa da kuka yayi daya wani irin tafida imaninta, rungumeshi tayi ya mugun narke mata duk hankalinta yatashi he was so happy yanda yaga yay winning nata sau daya, cikeda damuwa tace "Arham dan Allah kadena kuka ya isa haka, am here for you, kalle tell me makake so, kome kakeso zan maka shi aduniyan nan" cikin wani irin sheshekan kuka yace "inason ko cikina ya shiga jikinki karki zubar, ki haifomin yara, bazan taba tonaki ba zamu bama Waleed but I want yazamto cikina na my sperm" murmushi tayi ta sharemai fuska tace "angama yallabai now will u stand up and fuck me kaman yanda kamin jiyaba, like your slave, fast and crazy" [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣1️⃣ & 2️⃣2️⃣ FREE PAGE Yau tun karfe biyar tamai a airport sabida karfe biyar na yamma jirginsu zai sauka anan Abuja, Ammi tun safe take dannamai kira takirashi yafi sau biyar dan kwana bakwai dinan tai kewanshi kaman me, tace mai su sauka agidan ta tamusu girki. 5:05pm jirjinsu yay landing a nmandi azikiwe airport, yana zaune acikin Airport yana kallon gaban Airport din suka fito, tana sanye dawata matsassen doguwan rigan lace sky blue ta yafa dan mininin gyale da handbag dinta da wani Hill, sai shikuma Arham yana sanye dawata soft yard shima sky blue ka kagansu zaka dauka mata da mijine ma'aikatan Airport na turo musu luggage dinsu a cart, saikuma yaran dasukayo layi sunyi tsaf tsaf loking neat staff dinshi na jerasu suna dumfaro marcopolo bus din dake pake gaban motarshi, karasowa gaban motar Arham da Ilham sukayi hakan yasa ahankali yabude motar yafito murmushi dauke kan fuskarshi ya bala'in kewan Arham dan yasaba duk inda zashi aduniyan nan da Arham suke zuwa inba wanan emergency daya rabasu ba, cikedajin dadi yace "hey rascal welcome" sukadan kashe kafin suyi hugging juna Waleed na murmushi saikuma yasake shi yace "look yanda kai fresh abinka da nine da yanzu nai zuru zuru yaran nan sunsa na fita hayyacina" dariya Arham yayi yace "sabida kai stress ne baka saba da wahala ba saisa, niko nasaba saisa har wata kyau nayi" dan hararanshi yayi yace "dalla yanzun aikin dazanyi kokai bazaka iya yinshi ba" yay maganan yana dan juyawa ya kalli Ilham dayaga itama tai shegen kyau ta kara haske kaman mai shafamai, folding hannunshi yayi akirji yana kallonta, yanda yake kallonta kaman mai son gano wani abu yasa taji she's feeling uncomfortable, rasa mezatayi yasa tai gabanshi ahankali zata rungumeshi dan tsayawa tayi gabanta nafaduwa sanin Arham na wurin saikuma ta daure ganin yanda Waleed ke kallonta tace "oyoyo baby" "mesa kika saka gyale a irin wanan kayan, please this should be the last time" gyadakai kai tayi ahankali tana sakinshi, Waleed ya kalli Arham yace "ku shiga mota, bari na gaisa da yarana Ammi na jiranmu tamana girki" yay maganan batare daya jira amsan suba yay wajen yaran da sai a lokacin suka lura dashi ai motar dabasu shigaba kenan sukayo kanshi. "oyoyo teacher, oyoyo teacher" daga wayanda zai iya sama yayi cikin jin dadi sanan yace "ku wuce ku shiga mota, kuje kuhuta nasan amuku special treat" sakin su yayi sanan yaje suka gaggaisa da ma'aikatan shi sanan suka shige motar tsaf, yadan bubbugi motar alamun direban yaja su tafi sanan yawuce yakoma mota inda har Arham ya shiga gaba, Ilham abaya, zagayawa yayi yashiga gaba yaja motar, sosai suketa hira da Arham amotan har sukakai gidan Ammi, parking sukayi suka fito, tun kafin sukai gaban flat din Ammi ma Ammi tafito tana sanye cikin shigan alfarma wata atampa exclusive dake numfashi tayi ado da zinare akunne da yatsunta duka biyar, washe baki tayi tana fitowa tawani irin rungume Waleed, itafa Ammi danta shine nafarko kawai a komi nata kuma bata kunyan nunama danta so agaban uban kowa, tanason Ilham sosai amma son Ilham baitaba ketare na Waleed ba kaman yanda wasu surukan sukeyi sai kaga sunso matan y'ay'ansu sama da dansu ita ina danta ne number one. Tadade rungume dashi shima yay mugun kewanta inyaga Ammi ko Mom shagwaban shi tashi take, dagoshi tayi ta mannamai kiss a goshi sanan tace "sannu da zuwa Son, ya hanya? Hope bakagaji ba ko?" gyadamata kai yayi yana yatsine fuska yace "I miss you Ammi" murmushi tayi kaman ta hadiyeshi take tasake shi tace "ina zuwa" sanan takalli Ilham dake tsaye tana kallonsu tace "daughter na" guwiwa Ilham takai kasa zata tsugunna ta gaidata da sauri Ammi ta dagata ta rungumeta tace "sannu dazuwa diyar kirki, my son is looking masha Allah, Allah yamiki albarka kinji" akunyace ta gyadama Ammi kai, sakinta Ammi tayi tace "wuce kishiga ciki, nasa an gyara muku daki a upstairs yau awajena zaku kwana jeki wanka kufito aci abinci" gyadama Ammi kai tayi tawuce, sai alokacin ma Ammi ta lurada Arham dake tsaye kanshi akasa, dan murmushi tasaki ba yabo ba fallasa tace "Arham mutanen yankari" dago kanshi yayi fuskarnan cikeda murmushi saiyadan rage tsawo yace "Ammi ina yini, mun sameku lpy" "lpy lau Arham" Ammi ta amsa tace "shigo mana" tai maganan tana juyawa takama hannun Waleed dayabi ya langabe mata kaman wani dan jariri sukai ciki Arham biyeda su abaya, hakanan yaji wani iri, Ammi ta rungume kowa harda musu peck amman shi ko kanshi bata shafaba kaman ba bataji dadin ganinshi ba, shine abokin danta tun yana yaro amman haryau bata wani sakemai ingaka murmushi da fara'an Ammi toda danta Waleed ne, bude kofa Ammi tayi suka shige ciki itada Waleed Arham biyedasu, ahankali Ammi tace "to go and freshen up saika sakko aci abinci" kaman zaiyi kuka yace "wlh ni yunwa nikeji Ammi I will do dat after eating, blood ai kaima yanzu zakaci ko"? Dan murmushi Arham yayi sanan ya gyadakai, Ammi tace "to ai saiku taso kattin banza ko Khadija bazaku iya jiraba" dining din sukayi taja kujera Waleed yazauna Arham ma yazauna Ammi tace "Arham feel free zuba abinci kaci wanan abokin naka shirme zaitayi" kaman Waleed zaiyi kuka yace "nine mai shirme Ammi to bazan ciba ma" ya yunkura zai tashi da sauri Ammi tarike shi, zaunar dashi back tayi tana dariya. Tai maza tadau serving ta shiga zubamai rice datamai dawani ubansun vegetable soup da ita da kanta tamaishi yaji kayan ciki, ta debo da hadadden nama takai bakinshi tace "yauwa bude bakin Dan Yaron Mom" bude bakinshi yayi ahankali Ammi takai spoon din bakinshi shima yakawo bakinshi yana shirin ya karba ta kauda spoon din takai bakinta zataci wani irin malalacin ihun shagwaba yasaki. "aaaammmm Am..." kyalkyacewa da dariya Ammi tayi tai maza takai spoon din bakinshi daman wasa takemai tace "ihakuri, oya amshi" saida yadan mata kumbure kumbure sanna yabude bakin tasakamai ciki, ko motsi Arham bayayi bayau yasaba ganin ana bama Waleed abinci abaki ba dan inhar Mom ko Ammi na gida to Waleed bayataba saka hannu a abinci yace shida kanshi zaici, dudda yasaba dagani amman baya taba daina kallonsu in sunayin har karshen ranshi jiyake inama ace shine, yaso ace Mamanshi is educated kaman Ammi, Mama na sonshi shima amman ba kaman yanda Ammi keson Waleed ba kaman zata hidiyeshi ba, ahankali Ilham ke saukowa daga stairs tana sanye da wata doguwar rigan atampa super, free gown ne babu komi jikinshi, tundaga stairs take kallo yanda Arham ke kallonsu Ammi, dauke kai tayi kar alura shi take kallo takaraso dinning din tana murmushi tana kallon Ammi data waigo tace "zo daughter zauna kici abincin ki" tai maganan tana kai abinci bakin Waleed, kujera taja tazauna sanan tadau plate ahankali ta shiga zubama Arham masa dudda batasan koshi zaici ba tazuba mai miya da uban namomi ta turamai gabanshi tace "bismillah Yaya Arham" dan juyowa Ammi tayi ta kallesu sanan tadauke kai tacigaba dabama Waleed abinci itama Ilham ta debi masa duk akai shiru ana cin abinci dariyan Waleed da Ammi kawai kakeji sai wasa suke sunacin abincin gwanin ban sha'awa dan shima Waleed bayan yagamaci zubama Ammi tayi yashiga bata kasacin wani abincin kirki Arham yayi yature abincin yadau tissue yana goge bakinshi, sanan yamatsar da kujeran baya yamike tsaye da sauri Waleed ya kallai yace "badai harka koshiba kaidake son masa" dan yatsine fuska yayi yace "nagaji ne blood inaso naci but taki shiga nasan innaje gida na huta zan iyacin abincin" da sauri Ammi tace "ina za'ai haka, bari nakira a deba maka a kula kaje gida saikaci ka gaidamin da Maman ka please, jiya ta aikomin da kwamdon tumatir da buhun albasa daga gona, haba ita bata gajiya, kace nace tadena daurama kanta dawainiya please kaji, niya kamata nabata ba itaba kaji" gyadamata kai yayi kanshi akasa maganan karshe ta mugun mai ciwo wanan kasancewan har ina wai ita yakamata tabata wato ga Mamanshi fatararriya matsiyaciya ko, sukuma masu kudi, hmmm wata rana dagake har danki saina saku kuka wlh, saina muku abinda kudinku bazai taba gyara abinba, tsayar da maganan zucin yayi daidai yar aikin Ammi takawo wani hadadden kula da masa da miya keciki tabashi, karba yayi yace "thank you Ammi" sanan yajuya, tashi Waleed zaiyi Ammi tace "kanacin abinci baka gama bane zakawani tashi" kaman zaiyi kuka yace "nifa Ammi nakoshi, kuma I want to see blood off" "to ai saikaje su mai blood" Ammi tai maganan da zuciyanta daya dariya Waleed yayi yawuce yabi bayan Arham dahar yajuya da sauri yay kofa itakuma Ilham tai kaman ba satan kallon Arham din dataga ko bye baimata ba, yarage dinning din daga ita sai Ammi. Concentrating Ammi tayi tana cin abinci saikuma chan tadan dago daidai itama Ilham ta dago hada ido sukayi da Ammi, Ammi tai murmushi sanan ta mayarda hankalinta kan abinci cikin seriousness dinan nata da halinta na bawasa tace "Khadija kinyi kyau, you look so fresh Masha Allah, am expecting good news kwanan nan fa daga wurinki" kasa dagokai Ilham tayi tama kasakai abincin baki tana wasada spoon din ahannunta, Ammi ta cigaba. "nasan ku yaran zamani bakusan dazaran kunyi aure ayi aciki a haihu kunfison sai anci soyayya, bakuson ace daga shigowa kunyi tuntube dashi, wasunkuma ma har planning suke, please daughter banda planning take note, I need an heir, inason magaji, inason naji good news daga gareki kwanan nan kinji" gyadama Ammi kai Ilham tayi akunyace tace "in sha Allah Ammi zakiji kwanan nan" murmushi Ammi tayi cikeda gamsuwa tace "sai magana tabiyu, bazaki yi aikiba, am sorry about that I know bazaki so hakan ba, banson kina dauke da jikana a jikinki kije kinama wasu aiki, this magana is between me and you bazakiyi aikiba but every month zan dinga biyanki salary is that okay with you?" gyadama Ammi kai tayi ahankali tace eh, juyowa Ammi tayi ta fuskance ta da kyau tace "sai magana ta karshe ki kulamin da yarona da kyau, Alhamdulillah kinga Waleed yanzu kinyi zama dashi kinsan yanda yake, Waleed is a very sweet calm boy, baida hayaniya ko kadan kuma baidau duniya da zafiba, nasan abinda na haifa nasan, nasan waye shi, nasan Waleed zai kuladake da kyau dan haka kema ki kulada shi da kyau, kome yamiki ki kirani ki fadamin bawai kihau yima d'ana fadaba, ni kadai nakeda wanan ikon na dagama yarona murya da sunan fada duk duniyan nan, ba'a haifi wanda zai ma innocent yarona ihu aka ba koyaci mutuncin shi saidai in ban raye, inko daraina sai inda karfina yakare so ki kula kinji" gyadama Ammi kai tayi gabanta nafaduwa daman tun kafin ayi auren mahaifiyarta ta riga tafadi mata Ammi nada zafi gata kuma da zaki but inhar kanason kaji zakinta kaso danta, akan danta zata iya komi, muryan Ammi ne yadawo da ita daga dogon tunanin dataje kwalama yar aikinta kira tayi. "Huwaile, Huwaile" dagudu yar aikin tazo tarage tsawo agabanta tace "gani Hajiya yakuri banjiki da wuri ba ina baya ina aikin dakika sanine" tabe baki Ammi tayi tace "wuce kije fridge kidauko min magungunan dana bakiyau ki samin a fridge nace miki na matar d'ana ne" da sauri yarinyar ta tashi taje fridge, wasu goruka guda uku ta dauko a basket mai kyau takawo ta ijiye gaban Ammi, daukan gora daya tayi ta jijjiga tareda budewa tamikama Ilham tace "gashi kisha" karba tayi cikeda girmamawa ta kwankwada zata ijiye Ammi tace "shanye duka" kwalkwalewa tayi ta ijiye tana lashe baki dan maganin da dadi, Ammi tace "wanan maganin dakika gani yana wanke ciki tass da mahaifa, inma yarinya tai planning ne kan kartadauki ciki tass saiya wankosu su fito ta fitsari, sanan ya wanke mahaifa koda ya cushe zata wanke tsaf ta yanda once yay releasing zai tafi mahaifarki direct, inhar mace tasha maganin nan akayi batai ciki ba to tanada wata natural condition ne dake hanata haihuwan" faduwa gaban Ilham yahauyi wanan son yara da Ammi kedashi haka na lafiya ne, mika mata sauran gorunan Ammi tayi tace "wayan nan tsumi ne kishanye su" karba tayi tasake gyadamata kai daidai Waleed ya shigo tashi Ammi tayi tace "zonan yallabai" dariya yayi yabita stairs tahau yana biyeda ita abaya, Ammi tace "bakabani labarin excursion dinba, how was it" labari ya shiga bata sunayin sama Ilham tabisu da kallo har suka bace mata wanan wata irin matace, wayarta tadauka data ijiye agefenta tabude da sauri daidai sako na shigo mata, ganin Arham ne yasa tabude dagudu. _"you are mine, ban yarda wani yatabaki ba, karki yarda ki kwanta da yaron nan, is a warning ⚠"_ Murmushi tayi tamai reply da. _" to sarkin kishi, babu wanda zai taba maka ni yallabai, I miss you, sainaji inama bamu dawoba, please kazo da daddare nadan ganka"_ Maido mata da reply yayi da. _"I don't wanna come, bazan zoba, cus I hate that old witch, she don't like me is obvious babu dai yanda zatai danine sabida tasan danta bazai iya rayuba bani ba, I will see you tommorow"_ Wani iri taji kaman tai kuka, hakan yasa tai reply dinshi da. _"promise"?_ Dawo mata da reply shima yayi da _"I promise Lawyer"_ Da sauri ta turamai da. _"but tayaya bayan gobe kuna orphanage kuna aiki"?_ Sake aiko matada sakon yayi yace. _"just trust your Arham, ki kawai tabbatar ya maidake gida dasafe kafin yatafi orphanage, you will see me, cus if I didn't have you I might die, I can't go a day without that yummy pus"_ Wani malalacin murmushi tayi tace. _"I trust you my dirty nigga, gat to go bye_ Tai maza ta tura sakon tareda deleting messages din duka ganin Waleed na saukowa daga stairs daure da alwala zashi masallaci, karasowa yay dinning din ya tsaya daga dan nesada ita yace "har yanzu baki gamacin abincin ba?" murmushi tayi ta kalli plate din gabanta sanan ta kalli fuskarshi saitai shiru kawai ta tsaya tana kallonshi barinma ruwan daya jika pink lips dinshi, bazata iya karyaba tanason Waleed soma mahaukacin so, kodan baimata yanda takeso ne yasa takejin Arham dake yimata yanda takeso oho, sanan tana tausayin Arham sosai saisa take sonshi ko menene oho ita tama rasa, all she knows is takasa tsanan Waleed, and duk in zata kalleshi saitaji wutar sonshi nakara ruruwa aranta to kodai kyanshi da kudinshi ke dibanta ne? Or is it possible kaso MAZA BIYU KUMA ABOKANAN JUNA? Ta tambayi kanta. "Tunanin5 me kike"? Waleed yamata tambayan yana karasowa gabanta a dinning din ya rungume hannayenshi akirji. "wai ni?" ta tambayi kanta tana kallonshi, daga mata gira yayi alamun yes you, murmushi tasake mai tace "kawai tunanin gidan mu nike inaso naje zaka barni?" yana kallonta eyes to eyes ya girgixa mata kai, sanan yace "matar Waleed bata zuwa ganin gida sai bayan ta shekara da aure, I am a well cultured man you know" yasake daga mata gira, samun kanta tayi da kasacemai kala saima wata shegiyar kasala da sha'awan shi dataji ya diran mata all of a sudden, he was so close to her yana mata magana ciki ciki sanan yana wani kashe mata sexy idanun nan nashi yana daga mata gira, ganin ta shagala da kallonshi yasa yajuya kawai yafice daga dakin yace "tashi kije kiyi salla, ankira magrib". Sai wuraren 9 bayan anyi isha'i yamayi magana da wasu naroka yan anguwanni haka dasukazo neman taimako ya sallame su sanan ya shigo cikin gidan, maida kofar falo yayi yarufe yana kallon Ammi data zauna kan kujera tana aiki da laptop dinta duba sales din da aka mata a campanonin ta take, is a normal thing kullum around that time zata saka fararen glasses sanan ta zauna tana aikin sai wajen 11 na dare sanan zata gama taje ta kwanta, zama kusada ita yayi ahankali yace "sannu da aiki Ammi" kanshi ta shafa tace "kadawo son" gyada mata kai yayi ya jingina da kujera yana zaro wayanshi daga aljihu yarike wayan yana kallo saikuma ya shiga daddanna wayan yanemo number Dr Kemi yay dialing, ringing daya kaman wayan na hannunta ne daman ta dauka. "Hello Dr Warbai, good evening" kafin ma yay magana yaji karan kuka sosai a background din wayan, ahankali yace "who is crying?" "your patient" tabashi amsa da sauri, tashi yayi yazauna dukya damu, ahankali yace "what about medication dinta danace a dinga bata dakesata bacci" cikeda damuwa tace "Sir wlh na bata tun bayan ta farka da magrib dinan but taki bacci, daidai da ruwa takisha, inta ganmu ma ihu take, taki yarda damu kwata kwata jikinta ma yadau zafi, tun dazu ina kanta sai yanzu nafito daman nazo nakira kane saigashi kiranka ya shigo kaman kaji ajikinta tana kuka" shiru yayi yana rasa mezaiyi saikuma ya kalli Ammi dake aikinta hankali kwance gabanshi nafaduwa yasan yanzu yana fadimata orphanage zashi saita balbaleshi da bala'i, katse wayan yayi yamaida wayan aljihu ya ijiye yay shiru gabaki daya jin karan kukanta yasa yakasa natsuwa mikewa yayi zumbur kaman an dagashi yazuri key motar Ammi dake Centre table da sauri Ammi ta kallai tace "ina zaka?" "orphanage Ammi, emergency case gareni, I have to go" shiru Ammi tayi tana kallonshi kaman zaiyi kuka yace "please Ammi dazaran nagama zan dawo" yanda yayi yasa tace "saika dawo" da sauri yafita daga gidan, motar Ammi ya shiga yay horn gateman yabudemai gate yawuce yafita ya shiga titi yaba sharara gudu, wani super market yawuce akan hanya hakanan saiya sami kanshi dayin reverse back yadawo parking yayi agaban super market din ya shiga, yau kusan 3days kenan bata sakashi a ido ba, wata Teddy babba yasaya, saikuma yasai su snacks da chocolate da ice-cream yabiya kudi yafito ya shiga motar yaja, ko minti 15 baidauka ahanya yakai orphanage din, parking motarshi yayi agaban clinic din yafito lokacin 10 harda kusan minti 15 but yana iyajin ihunta daga wajen, daukan Teddy din yayi da sauri yama manta da sauran abubuwan saya sayo tsabagen yanda kukanta ke rudeshi ya shige cikin, ward din datake ciki yayi agaban dakin datake yaga Dr Kemi da nurses dukansu tsaye sunyi charko charko, babu wanda kukanta the bai dagawa hankali ba, Dr Kemi na ganinshi ta sauke ajiyan zuciya tace "thank God you are here, bari naje nahuta ba'a taba kawo mana patient data taba bamu wuyaba irin wanan yarinyar" wucewa suma nurses din sukayi suka tafi bayan sun gaidashi, ahankali yake daga kafanshi haryakai gaban dakin, kukanta dake tsuma zuciya nakara tashi yana kururuwa, daura hannunshi yayi kan door handle din kafin ya murda yatura kofan ahankali yana kallon dakin, tana zaune akasa kusada kofan ta tankwashe kafa kanta sauke tana rusa uban kuka dakowani gaba na jikinta ke amsawa, bama tadago kaiba balle tasan waye yashigo ba, maida kofan yayi yarufe ahankali, sanan yadago kafanshi yazo har gabanta, ijiye mata Teddy yayi akasa agabanta sanan ya zaga ta gefenta ya tsugunna ahankali yana kallon yanda tsabagen bala'in kuka kandaya kulle mata ta wargajeshi yama rufe mata fuska da baya, cikin wata irin karaman tattausan murya yace "Sabeeha" har kasan kwakwalwanta taji kiran sunanta dayayi dawani irin sauri ta dago kanta takai hannayenta ta gyara gashin gaban fuskarta ta hanyar waresu kyakkyawar fuskarta ya bayyana ta kallai suka hada ido, wani irin fashewa da kuka tayi saikuma tasa hannayenta biyu ta tureshi tana ihu da kuka. "ahhhhh ammmm" saikuma tajuya da sauri ganin Teddy daya ijiye mata awurin yasa tai grabbing nashi da sauri ta daga ta shiga kwadamai tana mugun kuka jikinta na rawa ranta ya bala'in baci, saida ta kwalamai Teddy iya son ranta sanan ta jefar dashi akasa ta tattaka tana kuka saikuma ta dauka ta mike tsaye tana tafiya tana dingishi tai wajen gadonta tahau ahankali ta kwanta ta rungume Teddy tana sauke ijiyan zuciya. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣3️⃣ FREE PAGE Yadade atsugunne yanda ta barshi, zai iya cewa tunda Allah ya halltoshi duniya da dai wayanshi aka bai taba ganin mutumin daya daga hannu da sunan zai dakeshi ba aduniyan nan ballema har ya dakan sai akan yarinyar nan, bude idanunshi da tuntuni suke alumshe yayi yadan juya ya kalleta, sai ajiyan zuciya take irin na wanda yay kuka dinan ta kankame Teddy tana jikinta har bari bari yake, ahankali ya furta zuciya! Mikewa tsaye yayi ahankali yafara tafiya batare daya waigo ya kalleta ba yay kofa, hannunshi yadaura zai bude kofan yaji tawani irin fasheda kuka da sauri yajuyo, ganin yayi ta tashi daga kan gadon tana kokarin saukowa daga gadon, saukowa tayi tana kuka ta taho har gabanshi tana dingishi, rungume hannayenshi yayi yanabin gashinta dake lilo da kallo yace "you just finshi beating me, why are you crying again? Ba bakison ganina ba?" yay maganan gabaki dayanta cikin harshen turenci, cigaba da kukan tayi batare data cemai kalaba, sosai yaje yanason yay training nata yabata tarbiya mai kyau, ahankali yace "you don't beat your elder koma mesuka miki, is wrong, now say sorry" dago jajayen kumburarrun rinannun idanunta tayi ta kallai kaman yanda shima ya tsare mata ido, ahankali cikin dishashiyar muryanta dabata fita sosai tace "so...rry" yanda tafadi sorry was so cute da saida yasashi murmushi, handky aljihunshi yaciro yazo har gabanta ya tsaya sanan ahankali yadaura left hand dinshi kanta sanan yakai right hand dinshi dake rike da hanky din kan fuskarta wani irin wawan ajiyan zuciya ta sauke da saida yasa ya kalli fuskarta kafin ahankali yashiga goge mata hawayen dayay chaba chaba a fuskarta, sanan ya share mata hancin daya baci da majina, sanan yawuce cikin dakin zuwa gaban gadonta, pink bathroom slippers din da aka bata na sawanta yadauko ya ijiye agabanta yace "put on the slippers" sakawa tayi da sauri tana kallonshi shikuma ya tsaya yana kallon cute yatsun kafarta fararen da zai iya cewa baitaba ganin yatsun kafan mace kai kyau hakaba kodan baya kallon yatsun ne oho, dago kanshi yayi ya kalleta yace "let's go" yay maganan yana bude kofa yafito yajuyo ya kalleta, da sauri itama tafito tana kara rungume Teddy dinta ta tsaya kusadashi, hannunshi yasa yajawo kofar yarufe sanan yafara tafiya ahankali sabida ita, kallonsu nurses din suka tsaya sunayi da mamaki yarinyar daketa uban kuka, tana ganinsu tadaga Teddy ta sama tai gaban counter dinsu da gudu zata rafka musu da sauri Waleed ya daka mata tsawa. "Saheeba" tsayawa chak tayi bata rafka musu ba tajuyo kaman zatai kuka ta kallai, daure fuska yayi tamau yace "come here" tahowa tayi ahankali sukuma nurses din na dariya kasa kasa, hannunta yakama yarike sanan yay wajen kofar fita daga clinic din da ita, security yabude musu kofan suka fito, tunda aka kawota bata taba fitowa ga wuta ko ina a premises din kaman ba dare ba, ga hadaddun flowers ga few cars dake pake a filin, tsalle tahau yi tana kara kankame Teddy ta kana ganinta kasan she's very very happy, tai wajen flowers tana tattabawa saikuma ta daura Teddy ta akan flower tana tsalle, murmushi yayi yawuce ta yace "lets go" daga Teddy ta tayi ta dauka tabishi da sauri tana dingishi har zuwa inda yay parking motarshi, bude mata gidan gaba yayi yace "seat" shiga tayi ta zauna ahankali sanan yazaga mazaunin direba tana binshi da kallo kaman zai gudu saida yabude motan ya shigo sanan ta sauke ajiyan zuciya ta shiga tattaba motan tana yan surutai kaman yanda yara keyi in sukaga kayan barna, wajen radio mota ta shiga tattabawa da sauri yace "stop" denawa tayi ta hade hannayen takai dukansu baki tana kallonshi da kwala kwalan idanunta, dan ajiyan zuciya yayi yahanata wanan takoma wanan, ahankali yamika hannunshi baya yadauko jakan desert da snacks din daya siyo mata ya daura kan jikinshi ice cream yaciro yabude yasaka spoon yamika mata yace "ice cream" tsayawa tayi tana kallon ice cream din dabai wani narkeba da kallo dan da kankaramshi aka bashi, kwanto da kanta tayi tana leka ice cream din kaman wata matsoraciya spoon din yazaro ya lakato ice cream din yakai bakinshi yasha ya lumshe ido yace "is sweet, ice cream" karban duka ice cream din tayi daga hannunshi zata sha saikuma ta dago takai hannunta ta fizge spoon dinta shiga shan ice cream din kaman zata hada da roban cikin 2min ta shanye tass tamikamai spoon da roban ice cream din, murmushi yayi yaciro muffin daga ledan yabata kaiwa baki tayi taci taci ye tasake mikamai hannu alamun yakara mata saida tacinye duka guda biyar din dayasa yo sanan yabata ruwan sanyi ba sosai ba tasha tai gyatsa da karfi dayasa yatabe fuska yana kallonta yace "yanyanyaa, don't do that again" gyadamai kai tayi hankalinta yakoma kan yan littatafai data gani kan saman motan, da sauri tamika hannu zata dauka kafin ta dauka ya dauke yace "stop is not mine na Ammi ne" ahankali tana kallon fuskarshi tace "Am....mi?" gyadamata kai yayi yace "yes Ammi Saheeba" saita shiru ta tsaya kallonshi, murya chan kasa yace "now listen kinsan me yasa nakawo kinsan nabaki kayan dadi"? Yay maganan da turenci dan turenci kadai ya lura tanaji inya mata hausa bata ganewa, turencin ma yawanci bata cikamai reply ba, badaita wani maganan kirki dan baitabajin tamai full sentence da turenci ba, ahankali yace "you see am a very busy person, I work in this orphanage, and I am a Dr, bakoda yaushe zaki dinga ganina ba, kinsan menene banso inhar kinayi zanyi fushi dake?" da sauri ta girgiza mai kai yace "banso kina kuka, kobaki ganni ba karki kara kuka do you know why? Because am going to make you a promise now" yay dan shiru yana kallonta ganin gabaki daya ta natsu shi take kallo yace "duk ranan duniya zaki ganni in sha Allah, zanzo naduba ki dan nine Dr ki, but ba lallai ki ganni dawuri ba sabida ina aiki dayawa, bawai dan baki ganni ba kiyita kuka, no banso kina kuka sabida in kina kuka bazaki warke ba, kidena kuka, be a good girl kome kikeso za'amiki, kidinga shan maganin ki in anbaki kinji" gyadamai kai tayi yay murmushi yace "muje nabaki wasu magani saikiyi bacci saikuma gobe u will see me okay, zan sayo miki ribbon and other hair stuff kidinga kama gashin nan" gyadamai kai tayi yabude kofa yafito yazaga yabude mata side dinta tafito ahankali rikeda Teddy dinta yamaida kofan yarufe sanan yamaida ita dakinta, wasu magani yabata sanan yasa ta kwanta, kwanciya tayi rikeda Teddy tana kallonshi shima yana kallonta kaman wayanda fuskokinsu ke magana da juna harta fara lumlumshe ido, saida bacci ya Kwasheta sanan yatashi bargo yaja yarufa mata sanan yatofa mata addu'an bacci yajuya yafita daga dakin, Dr Kemi yama sallama yawuce yatafi, koda ya isa gida wuraren 12, kulle kofa yay yay upstairs, Ilham yasamu tai bacci abinta bayi yashiga yay wanka yafito saida yay sha'fa'i da wuturi sanan yazo ya kwanta sai bacci. ******* Da asuba yatashi as usual yatafi masallaci, itama yana fita ta shiga bayi dan maganan Arham ne aranta dayace mata ta tabbatar yakaita gida, salla tayi bayan tafito sanan tai kwalliya cikin doguwan riga baki mai kyau. Wuraren 7 tafito jin muryan Ammi akasa, ahankali take sauka daga stairs daidai Waleed shima ya shigo gidan, a stairs suka hadu, murya chan ciki tace "good morning baby" "morning" ya amsata yay gaba saikuma ya tsaya yace "kinyi arranging kayan ki ko am dropping you off at home kafin na wuce aiki" gyadamai kai tayi tace "to yallabai bari na gaida Ammi nadawo nayi" gyadamata kai yayi yawuce itakuma ta sauka, a kitchen tasami Ammi dayan aikinta suna breakfast, har kasa ta tsugunna ta gaitada, dda murmushi Ammi tace "Khadija harkin tashi, to barkanmu da asuba Mike tsaye kidena tsugunnawa kina gaidani dan Allah" tashi tayi ahankali tace "Ammi bari nai breakfast din kije kihuta" da sauri Ammi tace "kul, matar d'ana bata wahala, wuce kikoma wajen mijinki ki taimakamai ya shirya aiki, saiku sauko kuyi breakfast kan kuwuce, wuce wuce" Ammi tai maganan tana cigaba da aikinta wucewa tayi tafice tanajin dadi inhar haka Ammi take ai tafita masifan ta ko ajikinta, duk masifar matarnan jibi yanda takeji da ita, sama ta koma Waleed na bayi hada kayanta tayi tsaf sanan tai kwanciyan ta kan gado tadau wayanta ta shiga message ta turama Arham sako. " _barka da asuba mijin Khadija, dafatan katashi lpy_ " Kaman wayan na hannunshi da sakon yashiga yamata reply. _"hey lawyer, couldn't sleep wlh, kin hana wanan fine Hausa Fulanin yaron bacci, wai me kikamin ne_? Dan dariya tayi tashiga typamai sako " _nidai karka manta da alkawarin dakamin, kace nakoma gida yanzu kuma zan koma gidan, Waleed zai ijiyeni kafin yatafi aiki_" _"you will definitely see me, worry not"_ Murmushi tayi zata sakemai reply taji muryan Waleed akanta. "who is making you smile like that"? Awani irin birkice tadago kai ta kalli saman kanta taga bashi akanta yanama gaban wardrobe din dakin yana kokarin ciro kaya, juyowa yayi rikeda hanger da suit kejiki ya kalleta saikuma yay murmushi yace "I guess is that your friend ko, yana sunanta" yay shiru kaman mai tunani da sauri tace "Salima, eh Salima ce tamace na gaisheka" murmushi yayi baice mata komiba ya shiga shiryawa idanunta akanshi kaman zata cinyeshi, tsaf ya shirya sanan suka sauka kasa breakfast sukayi mairai da lpy Ammi tasa aka sauko musu da akwatinan su aka loda a mota sanan tarakasu har wajen mota suka tafi. Acikin gidansu Waleed yay parking, suka fito akwatin su yaja musu Ilham biyedashi sukai cikin gidan, ga mamakinta taga ko'ina agyare tsaf yana kamshi ba kura hakan yasa tace "naga dakin ba datti" tabe baki yayi yahau stairs yace "Ammi ta aika aka gyara ko'ina" murmushi tayi dan dama tanata tunanin aikin gyaran gidan dazata yi inta dawo har dakinta ya shiga ya ijiye mata akwatin ta sanan yawuce nashi dakin ya ijiye nashi bude akwatin yayi yaciro wandon ranan nan dayake jikinshi daya shiga rafin nan bayan an jefo coffin ciki, zura hannunshi yayi acikin aljihun wandon nan exactly irin dan kunnen Widad yafito, faduwa gabanshi yayi yace "so is true, this girl is in danger, serious danger, someone is trying to kill her I need to protect her" maida dan kunnen yayi yasa a aljihun wandon jikinshi sanan yafito dan dayan dan kunnen na office dinshi a orphanage, sallama yama Ilham yawjce compound ya shiga mota gateman yabudemai Gate yawuce yabar gidan. A parking lot din gidan marayun yayi parking yabude motan ahankali yafito, as usual Arham yafito daga office dinshi yana sanyeda suit da pad a hannunshi yasauka daga matattakalan yataho yace "welcome boss" hararanshi Waleed yayi yace "yau yan mutuncin na kusa, tell me wat we've got yau?" shiga to do list dinshi Arham yayi yace "the first thing dakace zakayi bayan kadawo daga excursion is meeting da Nora, by 9, already ma he's around, yana jiranka, sai the second thing is meeting da staff dakai shifting, sai na uku, clinic round, hostels round dats all" gyadamai kai Waleed yayi daidai yabude kofar office dinshi ya shiga Arham biyeda shi, jacket dinshi yacire yay hanging a mahanga sanan yazauna akan kujera, yadaga hannunshi ya kalli agogon rolex dake daure a wrist dinshi yaga 1min after 9 hakan yasa, yace "kira Nora din" fita Arham yayi daga office din baiwani jimaba ya shigo tareda wani guy da zaiyi 25yrs, maraya ne tun 14yrs aka kawoshi wajen Waleed, yacigaba da rayuwa gidan marayun harya gama secondary school, Waleed yatambaye shi yanason yacigaba dan wasu basuso yace ceh yasashi a University, yanzu haka yana final year Waleed ke biyamai everything, daman normally insun gama University in aiki zasuyi sun samu Waleed zai barsu sune suyi wasu kuma suna nunamai sunfiso suyi aiki gidan marayun dan sunyi rayuwan maraita suma sunaso su taimakama wasu marayun, haka zasu fara aikin kuma duk watan duniya saiya biyasu albashi mai kyau, shigowa cikin office din yaron yayi cikeda murmushi Waleed yace "Nora" ya mikamai hannu zagawa Nora yayi harta gaban inda Waleed din ke zaune ya tsugunna har kasa yace "ina kwana Mai gida" ko kadan Waleed baijin dadin abinda bama Nora kadai ba yawancin yaran gidan marayun suke hakan yasa yace "stand up Nora" tashi Nora yayi ahankali Waleed yace "nahanaka bakaji kadena tsugunnawa in zaka gaidani please now sit down let's talk" zama yayi kaman yanda Waleed din ya umurce shi shima Arham ya zauna a kujeran gefen Nora, dan nisawa Nora yayi ya saukar da kanshi kasa sanan yafara magana. "banda uwa, banda uba, banda yan uba banda kowa, kai kadai gareni, kaine gatana kaine kuma uban gidana" yay dan shiru ya nisa kaman abinda yakeso yafadi namai nauyi sanan yace "daman maganan danike so nafada maka shine aure nakeso maigida" daga Waleed har Arham tsayawa duk sukayi suna kallonshi, Arham ne ya katse shirun yace "me kake cewane Nora, wani irin aure kakeso bayan baka karasa makaranta ba sauranka shekara daya, final year fa kake yanzu, wani irin zance ne wan......" hannu Waleed yadagama Arham alamun yay shiru hakan yasa Arham yay shiru, Waleed ya kalli Nora dahar lokacin kanshi akasa yakasa dagowa ya kallesu, anatse yace "aure kakeso Nura?" gyadamai kai Nora yayi yace "eh, aure nakeso" shiru Waleed yasake yi yace "kanada wacce kakeso? Wacece wacce kakeson ka auran?" kanshi akasa yace "inada wacce nakeso amman bantaba mata magana ba, tana daya daga cikin dalibai na anan islamiyya classes" dan ajiyan zuciya Waleed yasauke yadanyi murmushi yace "wakake so Nura?" wata kunyace yaji yakamashi saikuma yadaure yace "Shafa'atu Auwal" yana fadin sunanta Waleed yaganeta dan yasan yaran gidan marayun, yarinyar nakashahshiya ce, tanada shanyayyen hannu guda, 18yrs, sune yan SS3 a makaranta, yarinyar akwai kokari both boko da islamiyya" dan dariya Waleed yayi saikuma yace "tashi katafi, zanga Iyami, zansa akiramin Shafa'atu, inhar tai na'am tace eh tana sonka then we have a wedding to plan in this orphanage" ya karashe maganan yana dariya sosai, kasa tashi Nura yayi cikeda kunya Waleed yace "ko saina daura auren yanzu ne zaka bar office din" akunyace yatashi yafita harda dan gudunshi, Arham yatabe baki yace "ustazu da jaraba" kyalkyacewa da dariya Waleed yayi yace "hey common blood, he's a grown-up man mana, Nura nada natsuwa ga ilimi, so u trust the boy, fatana Allah sa yarinyar tasoshi itama" sake tabe baki Arham yayi yatashi yace "bari nakoma office dina" da sauri Waleed yace "no karka tafi yanzu dawo kazauna akwai maganan dazan makane, I need your advice" ji Arham yayi ranshi yabaci kaman zaiyi kuka yace "let's talk later please blood akwai abinda zanyi is very important, Mama tasani, ina zuwa" yafita saga office din da sauri batare daya jira me Waleed zai karacewa ba, sanin bazai fito yanzu ba yasa direct yay wajen motarshi shiga yayi yaja motar yabar gidan marayun yana zuba wani mahaukacin gudu. Akofar gidan Waleed ya danna horn, Ilham najin horn ta sauka daga kan gado da gudu ta leka window, gateman dinsu ne yafita ya leka yana ganin Arham ne yadawo ciki dagudu yabude gatedin Arham ya shigo, parking yayi yafito ya gaisada gateman din yabashi kudi sanan yay cikin gida, bude kofar falo yayi ya shiga da gudu Ilham ta shiga saukowa daga stairs tana. "oyoyo, oyoyo, oyoyo Kafi Zabo na" dawani irin gudu tai tsalle ya chapketa suka shiga kissing juna yana shafata kafin su zube akasa suna yan shafe shafe, saikuma yadagata ta hanyar daukanta chak yace "am going to fuck you akan gadon mijinki let's go" yahau stairs yakarasa har gaban dakin Waleed yabude kofan, kamshin Waleed ne ya Hugo hancin su Arham ya yatsine fuska ya shige da ita ya maida kofan ya rufe sanan ya jefata kan gadon ya tsaya yatube kaya yayar yace "I miss you gurl" yawani fada gadon kanta sukahau iskancin su suna moaning. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣4️⃣ FREE PAGE Saida yayi yanda yakeso da ita akan gadon Waleed yabata zanin da fluid sai wuraren 11 yadagata shima sabida kiranshi awaya dayaji anata yi kuma yasan ba kowa bane illa Waleed, sauka yayi daga kan gadon yace "lemme shower Lawyer nasan Waleed ke kirana" gyadamai kai tayi tana daga kwancen tana kara sauke ijiyan zuciya, wanka yayi a hadadden bayin Waleed yanabin ko'ina da kallo komi kar kar sanan yafito daure da towel dinshi, kayanshi yadauka ya mayar yana kallonta ganin ko motsi bata iyawa, gira daya yadaga mata yace "ya akayi you need more"? Lashe lips dinta tayi tadan tashi zaune ta jingina da bango tace "kawai nagaji ne yaushe zakai resigning daga gidan marayun nan eh? I will find a job for you I promise, kuma zan dinga baka salary, nawa Waleed ke biyana every month as salary"? Batare daya kalleta ba yana kokarin saka links din kayanshi yace "500k" "wow 500k" dagokanshi yayi ya kalleta yace "is too small ko, kowani watan duniya gwamnati nabama gidan marayun tallafin kudi, dudda nasan Waleed baya jiransu da kudin kampanin babanshi dakuma gadonshi yake running komi, yakamata idan gwamnati takawo tallafin saiya dinga bani kaso mai kyau koda 2min ne duk wata" da sauri tace "let's be Frank, 500k is a very good amount trust me Waleed kawai kyautansu yakema wani aikine zaka samu da zasuna biyanka 500k duk wata ko as an engineer dakake adai Nigeria nan babu saidai in a abroad" shiru yayi yana kallonta sai kawai ya kada kai yace "you will not understand, am his partner, I run the place kaman yanda shima yakeyi namafishi aiki tunda dai shi kike supporting is fine" da sauri yace "wlh bashi nike supporting ba" "bye" yamata yana bude kofa yafita daga dakin ya sauka kasa yabude kofa yafito daidai direba na bude gate wani irin wawan faduwa gabanshi yayi amman yadake yacigaba da tafiya yakasa dagokai ya kalli motar da shigo, hayaniya da surutun mata dayaji yasa yadago kanshi, wasu manyan matane guda biyu da kananun yara a hannunshi mataye suna bala'in kama da Ilham kaman yayyinta binshi sukai da kallo baice musu kala ba yabude mota ya shiga sukuma sukai ciki. Suna bude kofa suka shiga falon suke kwala mata kira. "Ilham, Ilham" da sauri Ilham tashiga saukowa daga stairs da hijabi ajikinta har kasa ciki tana daure da zani tana washe baki. "oyoyo Anty Hassu da Anty Husai" takarasa tadau yaransu da gudu tace "ke Aiman da Ameera ba magana kuna wani shan alawa" batare da Anty Hussaina dasuke cema Hasai tazauna ba babu alamun wasa akan fuskarta tace "waye wanan daya fito daga flat dinki yanzun nan? Naga ba Waleed mijinki bane wayeshi" ijiye yaran tayi tadago ta kallesu ganin duksun tsareta da idanu yasa tace "Arham nefa Anty, best friend din Waleed, ya aikoshi nabashi wani kati ne dazai kaima chan orphanage, inama bacci nima yay knocking banmaji ba saida Waleed yakirani wai ya turo nabada sako nafito nabude kofa, shine fa nabashi yatafi" atare sukace ayyo kafin Anty Hussaina tace "amman baida mutunci ya kare mana kallo tsaf sanan ya zubar kaman yaga kashi bako gaisuwa, kinga kawo mana ruwa musha, ya honeymoon a Yankari" hanyar kitchen tayi gabanta nafaduwa. Nafaduwa har lokacin ganin tawuce da kyar, drinks takawo musu da ruwa sanan tai sama tace "bari na watsa ruwa sai nazo namuku girki" sama tayi tana zuwa dakin Waleed ta shiga direct ta yaye zanin gadonshi tasaka wani sabo ta shiga bayinshi ta jefa zanin a washing machine ta feshe dakin da turare sanan tafita ta shiga dakinta wanka tayi ta shirya cikin wasu kananun kaya sanan tafito ta shiga kitchen ta daura musu girki suna hira. Wuraren 12 ya shigo orphanage din yayi parking motarshi daidai Waleed nafitowa daga office dinshi tareda Iyami, mai kula da girl section da yara ke kira da Mama Iyami, bude motar Arham yayi yafito Waleed ya daukekai kaman baiganshi ba dan ranshi yadan baci tayaya za'ayi yafita batare dayasanar dashiba bayan sunada uban aiki aka saidai kawai ya nemishi yarasa daga cemai dayayi bari yaje office dinshi yana Mama abu yadawo, shikenan saiya fice, girl section suka wuce shida Iyami, gate dinsu tabude yana biyeda ita abaya yara mata ne manya da kanana wasu na wasa wasu na wanki different activities all the girls looks happy and so undisturbed, stiars sukayi shida Mama Iyami sukai sama suka shiga room one, bunk bunk din gadaje yagani dasuka sami matsala tace "to kaga wayanda nagayamaka da sai an gyara yanzu haka nahana ai amfani dasu harsai an gyara" gyada mata kai yayi yace "zan aiko azo a fita dasu za'a saka sababbi yanzu dai kima Shafa'atu magana kome tace saiki fadi mini" gyadamai kai tayi suka fito suna sauka kasa har gate tarakashi yawuce yafita sanan takoma ciki, office dinshi yakoma yana shiga Arham nabude kofa ya shigo, dan juyowa yayi ya kalleshi saikuma yakoma kan kujera shi ya zauna batare daya nunamai wani abuba yace "ya akayi Mr P.A" yanda yake maganana shi adole fushi yake yasa Arham yay dariya yace "common baka iya fushi ba baima maka kyau shatwababben yaron Ammi, am sorry wlh Mama takira ni guess what?" ahankali Waleed yace "what?" dan dariya Arham yayi sanna ya nuna kanshi yace "waini Mama ke cema na auri wanan yarinyar yar kauyen nan niyama sunanta? Mtswwwww wlh nama manta, but just imagine wai nine zan aureta" tsareshi da ido Waleed yayi yace "to me aciki danka aureta I did see anything" dukan table din Arham yayi yace "na farko bazawara ce tafa taba aure a kauyen su, that aside gata yar kauye, kauyen ma kauyen kayayau, how can someone like me get married to yar kauye haba now" girgiza mai kai Waleed yayi yace "bahaka bane u are getting it all wrong Arham, yarinyar nan yar uwarka ce, idan ma aureta still kanka kataimaka, ko anje an dawo she will still be called your cousin, and kanacewa yar kauye ne, once you brush dat girl kanata kulawa ko shekara baza a dauka ba zata kile tadawo kaman kowa, your Mom likes her she spoke to me about it, kodakai bakaso do it for the sake of your Mom kaman yanda nima nayi" "bura'uba Allah ya kyauta, am not like you Waleed bazan taba iya auren abinda banso ba, ni inaso na auri mace yar gayu yarinya mai ilimi da aji kaman Ilham dinka" yay maganan yana kallon kwayan idon Waleed kaman yanda Waleed ke kallonshi Waleed yace "kaikuma abinda kakeso kenan?" gyadamai kai Arham yayi, dan tabe baki Waleed yayi saikawai ya girgixa kai yace "kawai kai addu'a Allah ya zaba maka mata tagari , but gaskiya you are due for marriage ka isa aure but ka kiyi" dan dariya Arham yayi yace "dudda banyi ba but trust me nafi wani mai auren ma morewa, I dey dive and scatter pussy" tsareshi da idanu Waleed yayi yace "I thought we've spoke about this thing tun muna school kacemin bazaka kara all this pre marital sex ba, ka komane kuma yanzu blood"? Waleed ya tambayai ahankali kuma ranshi adan bace idan akwai abinda ya tsana shine yaga Arham na aikin zunubi da suna school a kasan waje lokacin yabi wasu bad friends yan department dinshi dasuka sa yafara bin mata sosai, lokacin ne shida Waleed sukai having their first ever serious fight ganin Waleed yay fushi dashi sosai yasa yamai alkawari bazai jarayiba kuma yarabu da abokanen da yan matan yazo ya natsu kaman bashiba saikuma yau dayakeji yanamai magana haka, ganin yanda Waleed yay nisa yana tunani yasa ahankali Arham yatashi yazo ta wajen kujeranshi yace "hey tunanin me kake?" yadanyi dariya yace "wasafa kawai namaka, I was just joking bada gaske nakeba, ya za'ayi nakoma ma aikata zina bayan nasan haramun ne trust me ko lokacin danayi friends suka sani, yanzu ma kawai nafadi ne naga reaction dinka, but kasan wani abu"? Yay maganan yana kallon fuskar Waleed kaman zaiyi kuka yace "I use to wish inama nine nai auren nan da akama na auri Ilham sabida ko ni har yanzu banga wata mace datamin ba, Mama kuma fisabilillahi haka ake nomoma ma mutum mata, just take u now for example Ammi tanemoma mace daidai kai your standard ni kawai ta kama takawomin wata bazawara yar kauye" yaja tsaki kafin yadaura hannunshi akan forehead dinshi, hannunshi Waleed yakama yarike yace "Hey listen, aure lokaci ne don't pressure yourself, idan lokaci yayi zakayi, idan bakason yarinyar is fine talk to Mom kamata explaining politely sanan kadinga kyautata mata kama faranta mata hakan zaisa you will prosper and excel in this life, iyayenmu dakake gani are the gateway to our success abinda yakamata shine mu gyara zamanmu dasu" Waleed yashiga mai wa'azi yanamai fada batare daya nunamai cewan Mama takawo mai karanshi ba sun dade ahaka saida aka kira salla sanan suka wuce suka fita salla. Suna dawowa Waleed yace "I've been wanting to talk to you about something, ka tuna dan kunen dana tsinta a Coffin dinan a Yankari"? Da sauri Arham yace "eh natuna, what's with the earring"? Shiru Waleed yayi yabude office dinshi ya shiga yabude dakinshi ya shiga yaciro dan kunnen daya cire daga kunen Widad sanan yatura hannunshi a aljihu yaciro wanda ya tsinta daga yankari ya ijiyema Arham duka biyun agabanshi akan table, dawani irin sauri Arham yadago kanshi ya kalli Waleed yace "how did you get the second earring"? Zama Waleed yayi yace "now listen, ba ankirani ina yankari nazo emergency ba, so apparently dana iso na tarar wata aka tsinta achan hanyar lokoja a Murtala Muhammadu Bridge dinan, she was unconscious, sanan kanta ya barke ta wajen keya to the extend saida namata aiki namata stitches, now the thing is this girl yasami brain damage ruwa yashiga kanta, da jini, I was able to get some out saura dan kadan wanda with time tana taking magani zasuzo sui draining kansu da kansu su fice, dazaran sun fita zata dena abnormal behaviour datake yi, sai the second problem is tasami memory lost, wanda for now bazan iya mata komi akaiba harsai fluid din kanta ya fice tatas, I saw this particular earring a kunnenta guda daya, now do you know my problem"? Da sauri Arham ya girgiza kai, dan ajiyan zuciya Waleed yasauke yace "inhar jirgi zai dauko yarinyar nan, jirgin da dudda yasauko kasa kasa but maguna sunanshi ba basuna jikin jirgin, sanan abude kofa a yarda yarinyar nan a akwatin gawa cikin ruwa sanan jirgin yabace, koda muka bude akwatin ai munga jini sosai this clearly means this girl is in serious danger, all the bruises na bugewa da kurjewa ajikinta, da wanan fashewan kan I believe duk yimata shi akayi, my biggest problem ko dazai iya jamin matsala anan shine, one of the policy da akai establishing gidan marayu akai shine, inhar aka tsinci abu aka kawoma kanada right ku ijiye yaron with you, kubashi shelter inbaida lafiya a lura dashi, but dole ne ka sanar da gwamnati cewan an tsinci wane an kawoshi gidan marayu ne, kabada any information akan yaron harda hoton yaron, kamai file ka aikadashi ya zamto gwamnati sunada copy na information din yaron, bayan nan za'a bada sanarwa dan zai iya yuwa yaron nada family yanada yan uwa he's not homeless kuma ana chan ana nemanshi, da sanarwan nan yan uwanshi zasuzo a dauke shi su tafi da kayansu, koba gidan marayu ba ko gidan mai anguwan aka tsinci yaro haka akeyi, but in the case of this girl my heart and mind is strongly telling me not to do it, najira harta sami lafiya tafadiman dakanta suwaye iyayebta saina kaita har gidansu dakaina, gidan nan ba gidan marayu bane kadaiba this house is also gidan kariya, we have to protect kowaye damuka lura is in danger and helpless ayanzu koma waye keson kashe yarinyar nan suma sameta ahaka ai bazata musu wuyan kashewa ba, hala koda suka yarda ita sun zaci tamutu neyanzu suna gano she's alive zasuzo har nan su dauketa ne su kasheta, I've never ever done this before but this time am willing to do it to protect the helpless girl, what do you think blood"? Gyadamai kai Arham yayi cikeda gamsuwa da bayanin shi yace "I support you Waleed, inhar kan abinda is right ne ina bayanka dari visa dari, abari harta warke tafadi mana da bakinta su waye iyayenta sanan waye ke kokarin kasheta kafin muyi taking next step for now let's keep her living her a secret" gyadamai kai Waleed yayi yana sauke ajiyan zuciya sai yanzu yaji ya natsu, tashi yayi yace "muje na dubata saika ganta" tashi Arham din yayi suka fita daga office tare sukai clinic, shiga clinic din sukayi yau Dr Kemi na off, Dr Ayo ne a duty, gaisawa dasu Waleed sukayi sanan suka wuce ward din da Widad ke akwance hannu Waleed yasa yabude kofar ahankali ya shiga Arham biyeda shi abaya yana kallon gadon, Widad na kwance kan gado tana bacci an lullubeta dawani bargo tana baccin ta looking so peaceful, gashinta yadan rufe mata fuska amman ba sosai ba, Arham dake bayan Waleed ne ya matsa gefe shima ya kafe Widad din da ido tamai bala'in kyau, ahankali Waleed yakarasa gaban gadon yana kallon fuskarta yakai yatsunshi biyu wuyanta yadaura danyaji temperature dinta wani irin firgita tayi da sauri yazare hannunshi yakoma baya. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣5️⃣ FREE PAGE Ganin yanda Waleed ya matsa baya yasa Arham yazo wajen da sauri yana kallon fuskarta da kyau yace "blood wanan mutum ce ko aljana? Omg I've never in my life see mutum mai kyau hakaba, wai itace"? Yatambayi Waleed yana matsawa gaban gadon yana kallon yanda ta kankame Teddy, hannunshi yamika ahankali zai daura kan gashinta danya matsar ya kalli fuskarta Waleed dake bayanshi ne yace "don't touch her" da sauri Arham yajuyo ya kalleshi gyadamai kai Waleed yayi yace "mutafi, ba'a tashin ta in tana bacci she needs this sleep" yajuya yay kofa hakan yasa Arham yabishi abaya haryakai kofa zai fita yakara juyowa ya kalleta. "Arham" Waleed da yafita ya kwalamai kira hakan yasa da sauri yajuyo yafito yabishi abaya suka fita daga clinic din. Kwanaki sunja, tafiya tasoma nisa, amman haryau wanan so dinan Waleed baitaba jima Ilham shiba, banda haka she is so lazy, gyara gida wahala yake mata, Ammi ta turo mata da yar aiki ya nuna mata shi kar yar aiki ta gyaramai daki in bazata iya gyarawaba tabarshi danshi baida takura, bata gyaraba hakan yasa kullum dasafe saiya gyara yake wanka yatafi aiki. Kwanan nan koya nemeta bata bashi saita dinga nunamai bataso ta gaji hakan yasa ya tattare lamarinta shima ya jingine waje daya, daman yana neman ta ne sabida karya shiga hakkinta tunda ya lura bataso ya share ta shima bai kara neman ta ba saidai yana kulada ita danya lura tana fama da laulayin ciki sosai bana wasaba yana kulada ita bana wasaba. Yau ta tashi da sassafe dan tunda tasami ciki bata iya tashi da wuri saidai ta tashi taga Waleed yadade da tafiyanshi aiki, ahankali ta daura hannunta kan katon cikinta dayay girma yana motsi ta lumshe ido tana yan tunani, Ammi tafi kowa murna da wanan cikin, kaman tahadiyeta takeji ta kwallafa ranta akan cikin, dan ajiyan zuciya tasake saukewa tabude idanunta ta kalli saman dakin tana tunani tana shafa cikin, idan za'a kasheta yanzu bazata iya cewa takamaiman cikin wayeba cikin Waleed da Arham, all she knows is yanda take having frequent sex da Arham bata having that sex da Waleed, tunda Waleed ya aureta batai MP ba, dan asatin da za'ai bikinta daman tai MP, kuma tun bayan sun fara sex da Arham bataga ranan duniya da Arham bazai zo yay sexing dinta ba saidai intaje gidansu kokuma intaje gidan maman mijinta shine kawai bazatazo ba, gashi wani irin so yanzu takema Arham kaman me dan son na neman fin yanda ma yake sonta ko cikin jikinta ne yasa haka oho, duk randa bata ganshi ba adaddafe takekai ranan, cikin yasa gabaki daya Waleed yafita kanta, bamataso yazo kusada ita dan kamshin turarenshi daga mata hankali yake, bata iya komi, ko girki bata iyayi saidai yar aikinta tamata akawo taci shi daman Waleed baruwanshi da abincin gidan yanada inda zaici abinci dayawa, gidan Mom, gidan Ammi, da gidansu Maman Arham. Duk wata da zaran Ammi ta tura mata 300k salary zatama Arham transfer dinsu sabida kawai she want to see him happy shima yabude business ko company kanshi yadena aiki karkashin Waleed. Mika hannu tayi ta dauki wayanta ta, number Arham tai dialing saida wayan yakusa katsewa sanan yadauka, cikin wani irin kashe murya tace "Kafi Zabo zaka shigo dawuri ko?" dan yatsine fuska yayi yace "babe kinga kin kusan haihuwa cikinki yay girma dayawa bai kamata kina sex yanzu ba, banda hakama kindan soma budewan haihuwa I don't enjoy it down there is a bit wide" yafadi in I don't care attitude, wani irin dukan zuciyanta maganan tayi amman saita danne batace komiba, saikuma chan tace "shikenan abari saina haihun, bye" takatse wayan da sauri hawaye ya cicciko idanunta, maganan ya mugun sosa mata rai, batason tai fada dashine danko taso tayi bazata iyaba, kwanan nan yanga yanga yake mata tarasa mesa yake mata haka, she don't know, gashi mugun son taganshi take kamshin jikinshi samata kwanciyan hankali yake, tana kwance taji kara alamun Waleed yafito da sauri tajuya baya taja bargo alamun bacci take dan tasan zai leko, bude dakin yayi ya leko ganin tana bacci yasa yamaida kofan yafice, ya sauka ya shiga motarshi yabar gidan, saida taji karan maida gate aka rufe sanan ta tashi da katon cikinta tabude kofan bayi ta shiga wanka tayi tafito tasaka wata yar short gown tadauko kasa kan dinning ta zauna tana kallon abinci amman duk taji ta tsani ci gashi tariga tace ma yar aikinta tana mata breakfast ta tafi sabida tasaran da Arham zaizo yau dan kullum in zaizo sata take ta tafi gidansu dan bata kwana daman, tana zaune gaban dining tana kallon abincin har karfe shadaya taji anbude Gate, zabura tayi ta tashi tsaye tai wajen window da sauri ta tsaya ganin motar Arham ne yasa tashiga tsallen murna, parking yayi yagaisa da mai gadin da tun yana mamakin zuwan shi gidan harya dena, yawuto wanshi cikin flat din, bude kofan yayi ya shiga yay kyau sosai yana kallonta, ahankali yamaida kofan yarufe sanan yay murmushi yabude mata hannu alamun tazo dawani irin gudu tai wajenshi tafada jikinshi ta rungume shi tsam tsam, shafa bayanta yashiga yi yace "sorry nasan joke dina got you angry, I love you matata uwar d'ana" yay maganan yana dagota ya shafa cikin jikinta, hararan shi tayi tace "tayaya kasan danka ne?" shiru yayi kaman bazai amsata ba sanan yace "sabida ni nasan nafi karfin mijinki Waleed, sperm dina ya shiga jikinki nashima ya shiga jikinki but am sure nawa yafi karfin nashi, and u will see bayan kin haihu ko danwa kika haifa" yay maganan yana tsugunnawa ya sakinma cikin kiss sanan yace "muje indan ciki sabida fita zanyi akwai very important place din dazani da kyar nasamu mijinki ya barni nafito" ahankali duk jikinta yay sanyi ganin baya wanan rawan jikin dayakeyi mata da idan zasuyi sex, yanzu yi yake kaman yana mata favor dan yaga she's addicted to him, da ace zata iya data cemai bataso, sama sukaje yabude dakin Waleed ya shiga da ita yashiga yan wasanni da ita dake haukatata dayasa tafara mai minshari sanan yay sexing nata, tabude dayawa yasa he don't enjoy her at all now yawani irin gaji da ita, ko 30min baiyiba yakawo sanan yasauka daga kanta, kana ganin idanunta kasan bata koshiba zaiyi bayi tarikeshi kaman zatai kuka tace "please Arham second round cikin nan yasa ban koshi dan Allah zan baka wasu kudaden da babanmu ya raba mana na end of the year" daure fuska yayi yace "kinma maidani mayen kudi" hawaye ne ya gangaro mata hakan yasa cikin fushi tace "wai Arham where is our love, nabar mijina ban damu dashi ba, babu abinda ke shiga tsakanina dashi, I hate him now sabida kai, and yanzu kana kokarin kadinga wulakanta ni after all that aI've done for you, kafadamin mena maka wani laifin namaka ne eh?" tamai tambayan tana kuka, mikewa yayi yay bayi batare daya damuba yace "is like yau baki tashi in good mood ba, is not your fault ciki kesaki ganin abu ba'a yanda yakeba, nidai ban dena sonki ba". Dan nisawa yayi yace "I will always love my lawyer, kinsan ciki babu hormone din dabaya tabawa ajiki, to harda na brain dinki yake tabawa saisa kike ganin abu ba'a yanda yakeba, akwai inda very Important zan lallasheki inna dawo" ya shige bayi yafara wanka, yana cikin wanka taji anbude gate, dawani irin sauri ta zabura ta tashi ta yaye labulen dakin Waleed taga motar yayarta Anty Hussaina ya danno cikin gidan, gefenta kanwar Maman su ne dasuke kira da Yakolo, sai back seat dabata gane wayeba tadai tabbatar Anty Hassana ce, salati ta buga. "Innalillahi wa innailaihi raji'un" da sauri tai wajen bayin ta bubbuga tace "Arham please kafito da sauri kasaka kaya su Anties dina sunzo" da sauri Arham yadauraye jikinshi yafito daure da towel, kayanshi Ilham ta tattara ta mika mishi daidai yayinta na kwarara sallama a falo, Anty Husai tace "karkuyi mamaki tanachan sama tana bacci abunku damai ciki kumuje saman mutadota" da sauri Yakolo tace "nifa banison shirme in mijinta na nanfa" "miji, ai mijinta Anty Yakolo tun safe yake tafiya aiki, daman tun bayan jere baki kara ganin gidaba kumuje sama" sukai stairs rawa jikin Ilham yadauka tace "na shiga uku na lalace, nabani Arham mezanyi yanzu sunzo sama" daidai lokacin yakarasa saka riganshi yace "calm down I will handle it" yay wardrobe din Waleed yabude wani jallabiyan Waleed yadauko yamika mata dan tsirara take yace "saka wanan kiga" sakawa tayi ya agurguje ya saukan mata har kasa sanan murya chan kasa yace "calm down" ijiyan zuciya tasauke ahankali sanan yashiga kalle kalle adakin, wani file din Waleed yagani akan side drawer dinshi yadauka da sauri yay hanyar kofa yace "muje" bude kofa sukayi daidai su Anty Hussaina sun hayo saman turus dukansu sukayi suna kallon Arham da Ilham dasuka fito daga dakin yay kaman bai gansu ba yace "mijinki ya isheni da aike, kidinga dubawa kina tabbatar da baiyi mantuwa kafin yatafi ba" dan dariya tayi tace "ai baby sai......" daidai ta juyo tahada ido dasu Anty Hussaina wani irin tsalle ta daka da ihu tai wurinsu. "oyoyo Anty Yakolo" tafada jikin kanwar Maman su datai turus tana kallonta, ganin haka yasa yataho shima ahankali yace "sannunku da zuwa" sanan yawuce yaraba ta gefensu yasauka kasa abinshi boldly and majestically yabude kofan falo yafice, yana fita Anty Yakolo ta fizge ta daga jikinta tace "dan ubanki wanan wani kato ne yafito daga dakin mijinki, sabida ke dakikiya mahaukaciya ce jibi gashinki bako dan kwali ya hargitse kaman na mahaukaciya, dan ubanki waye shi?" kaman zatai kuka tajuya ta kalli Anty Husai, Anty Husai ranta abace tace "badake ake magana ba, dakina Amarya ma haka mukazo gidan muka ganshi, kifada mana uban meyake kawo shi nan gidan, tuntuni muna sallama ba amsa" kaman zata fashe da kuka tace "me kuka nufi da wanan irin tambayan dakuke min? Wani tunani ne aranku? Sabida kun ganni busu busu ahaka? Nima tashina daga bacci kenan, shine ma yatadani daga bacci Waleed ya aikoshi ya daukomai wani abu adakin, shine fa nabude mai dakin ya dauka, banmasan kaina ba dankwali ba" tafashe da kuka sosai dayasa dukansu jikinsu yay sanyi, Anty Yakolo ne ta katse shirun tace "nidai tashi bar kukan ba kyau me ciki na kuka, je dauko dan kwali kisaka, kukuma mu koma kasa kawai" juyawa sukayi itakuma ta tashi tana kuka kaman gaske ta shige dakinta har lokacin gabanta faduwa yake tana godema Allah datasha da kyar. [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣8️⃣ FREE PAGE Direba ne yace "Waleed kikeson gani Hajiya"? Gyadamai kai tayi hakan yasa yarike ma Ammi hannu yar aikin ma tarike ta suka dagata da kyar ta iya tsayuwa a feet dinta, mai gadi yacema yar aikin. "kawo mata mayafinta da jaka da takalmi" da gudu yar aikin tai sama dakinta ta shiga tadauko mata hadadden mayafinta da takalmin ta da jaka ta sauko kasa yafama Ammi mayafin tayi akan tsadadden lace din dake jikinta sanan tasa takalmin, ta karbi jakan dan tasoma dawowa daidai sukai waje da ita motar ta direba yabude ta shiga baya ta zauna suka rufe ta sanan ya shiga gaba yatada motar gateman yabude gate suka fice, suna ficewa motar Mom na sawo kai tabi motar Ammi da kallo daya wuceta da gudu yar aikin tafita waje taje wajen motar Mom cikeda girmamawa tace "sannu da zuwa Mom, Mom please jibi Hajiya, ankirata awaya bansan me aka fadi mataba amman saida ta sume kuma yayyafa mata ruwa ta farfado tace a kaita wajen Waleed agidan marayu yanzu sun tafi, please kibata I don't want wani abu ya saman mini Hajiya" cikeda tashi hankali Mom tace "karki damu bari na bita" kwana tayi da sauri tabi bayan Ammi itama. Motar Ammi na zuwa gate kasancewan security sun santa suka fara ihu. "Hajiya Don come Hajiya Don come, open the gate" sukahau jin dadi dan bata cika zuwa gidan marayun ba but duk randa zatazo ruwan kudi take musu, dan yake ta musu ta saka hannunta cikin jakan da yar aikinta tabata rapas din yan dubu sababbi ta dauko guda biyu ta mikama babban su, ihu sukahau yi suna mata godiya direba yaja motar ciki, kafin su rufe gate saiga second Mom, dadi kaman yau ana baki itama kyautan tamusu mai tsoka sanan ta shiga ciki, har gaban office din Waleed inda yake parking motarshi direba yay parking, tsabagen yanda jikin Ammi ke rawa kasa bude kofan tayi saida direba yafito yabude mata tasa kafafunta tafito tana fitowa motar Mom na sawo kai wajen, parking tayo tafito da sauri tai wajen yayanta data tsaya chak tana kallonta tace "Adda meya faru?" kasa magana Ammi tayi tajuya kawai Mom biyeda ita, itama Mom ganin yanda mutane suka taru a tsakar wajen yasa taji gabanta yafara faduwa, ana ganinsu aka fara gaishe dasu. "Barka da zuwa Hajiya, barka da zuwa Hajiya" kasa amsa kowa sukayi Ammi tai gaban asibitin daidai Mama Iyami dake kuka sosai tafito tawani irin zube agaban Ammi tace "Hajiya ku shiga yana ciki, wayyo Allah na mun shiga uku, gatanmu na kwance a asibiti raga raga, rai na hannun Allah" tsallaketa Ammi tayi tasa hannu tabude kofan ta shiga ciki Mom biyeda ita, Nurses din data gani charko charko tsaye agaban reception din tawani irin dakama tsawa. "kuna kallo na bazaku gayamin inda d'ana yakeba" arude duka nurses din suka mata pointing dakin da aka rubuta emergency asama, yanda Ammi ke ihu yasa Mom takama mata kafadar Ammi alamun tai calming down, kabar da hannunta Ammi tayi tai hanyar dakin, tana zuwa batai watawataba tabude kofan tasa kanta ciki, Dr Kemi da Dr Ayo ne akan Waleed din dahar lokacin bai farfado ba, ancire mai riga da singlet, dagashi sai dogon wandon jikinshi da belt anmai dauri akafada ta wajen hammata an hade da hannunshi kaman wanda ya karye, fuskarshi tai jajajir, gefen idon damanshi dama idanun duk sun kumbura, gefen bakinshi ya tsage yanadan jini tsabagen marin dayasha na Arham, wuyan shi tsabagen matsan da riga da necktie din wuyanshi sukamai har ciwo suka jinmai jini nafita wuyan yay jajir kaman an zaneshi da bulalan inji. Hawaye ne suka cika idanun Ammi takasa rikesu suka shiga zubowa har zafin dukan takeji ajikinta tsabagen tashin hankali, tunda ta haifi danta incident makamancin hakama baitaba samun dantaba, daidai Dr Ayo yagama gyara jinin wuyan yajuyo ganin Maman Waleed yanda jikinta ke rawa tana kuka yasa yace "calm down ma, bawani abu babba bane kashin kafadarshi tadan goce ta sanadiyan buga bayanshi da akayi da bango, saikuma bruises din wuyan nan dakuma na ido, dan jini yataru acikin idanunshi but with time zai washe, calm down Hajiya, nan da dan anjima kadan danki zai farfado" da sauri Dr Kemi data karaso wurinsu itama ta gyada kai tace "yes ma calm down please Ma" sukabi ta gefensu suka fita daga dakin, wani irin juyowa Ammi tayi cikeda wutan bala'i, da kunan rai da tsantsan bakin ciki ta kalli Mom sanan tanuna mata Waleed dake kwance kan gado da hannu tace "kinga abinda Arham yama d'ana ko? Kinga abinda Arham yama d'ana ko, kina gani daiko, yaron da dama kece tun day one kikai approving friendship dinshi da yaron, left to me yarona ya rayu ahaka baida aboki I his mother can be his best friend and his everthing aman kika nace saina barsu sunyi abota, dan haka karma naji kinhanani dauka hukunci dan wlh wlh bazan yarda ba" tai maganan tana dauko wayanta daga cikin jaka da sauri Mom tace "Adda kinga calm down yanda kike tafarfasan nan bai kamata kidau hukunci ba, dan Allah kiyakuri Adda" da wayan hannunta tanuna Mom tace "Zainab ki shiga taitayin ki, na rantse miki da Allah yanda Arham ya jima d'ana rauni ko kwana baza'ai ba shima sai anjimai, wlh saiyasan ya buganmini d'a, shidan ubanshi ubanwa yataba dukanshi haka? Waleed dakoni bantaba daga hannu na daka bane wani kato zai dokanmin wlh wlh saina ramamai, wlh kuwa kinji na rantse miki" Ammi tai maganan tana bude kofa tafita daga dakin tana dailing number Maman Arham. Ringing daya Mama tai picking call din ganin kira daga Ammin Waleed, kafin ma Ammi tai magana cikeda fara'a tace "Assalamu Alaykum, barka da yamma Hajiya" ko amsa sallamarta Ammi batayi ba cikeda bacin rai tace " please kome kikeyi kibarshi kisamemu a orphanage na Waleed yanzun nan kizo, ina jiranki yanzun nan" tana kaiwa nan ta katse wayan jikinta na vibrating, Mom ma takasa cewa komi tazama yar kallo matsalan yayarta kenan intai fushi batada hankali, kuma bataji bata gani barin ma when it comes to Waleed matter. Gaban Mama ne ya yanke lokaci guda ya fadi, tunda tasan Ammi tsawon shekaru kenan bata taba tamata irin wanan kiran ba saiyau, tomeya faru? Allah yasa alkhairi ne, ahankali tafara karanto innalillahi wa innailaihi raji'un kota samu natsuwa cikin zuciyarta, dan batada natsuwa ko kadan sabida zuciyarta wani irin mummunan faduwa kawai yake. Hijabi kawai ta dauka ta zira akan kayan dake jikinta, ta kwalama diyar kanwanta kira tace "nafita yar albarka saina dawo, ki daura abincin dare" daga ciki yarinyar ta amsa da "saikin dawo Mama" fita tayi daga dakin ta kwalama driban ta kira yafito, mota ta shiga tace yakaita orphanage dinsu Waleed ya amsa mata da to, yatada motar yafita daga gidan. Ko cikakken 15min direban bai daukaba yakaita orphanage din, tana fadin mahaifiyar Arham ce ita aka barta ta shiga dan ta taba zuwa sau daya suka shiga ciki, kirjinta bai kara faduwaba sai dataga ma'aikatan orphanage din carko carko a tsaitsaye ana tattaunawa agaban clinic, parking direba yayi tabude kofa tafito daga motar kirjinta na bugawa, wayarta dake hannunta taciro tanemo layin Arham ta hau kiranshi danta tambayeshi maiya faru, wani abu yafaru ne amman har wayan ya katse bai dauka ba, hakan yasa tai dialing number Ammi, ringing daya Ammi ta dauka, ahankali Mama tace "Hajiya na iso" cikin muryan Ammi dabata fita sosai tace "kishigo asibitin muna emergency" shine kawai abunda Ammi tafadi mata ta katse wayan, sosai Mama taji kirjinta na bugawa yanda Ammi kemata magana, hakan yasa ta daga kafarta tana kallon mutane ta shiga tafiya harta karasa gaban asibitin tasa hannu ta bude kofar ta shiga ciki, kasan cewan emergency din asibiti bata boyuwa yasa tana ganin dakin tagane batare datama tambayi nurses din dake wurin ba tai wajen kofan, ahankali ta murza hannun kofan dakin tashiga ciki, Ammi da Mom tagani zazzaune, Mom kan kujera Ammi kuma kan gado gefen kafar Waleed, Waleed kuma kwance kan gadon asibiti, ansa mishi drip, fuskarshi tai jajir ta kumbura wuyanshi ma haka, hannunshi adaure daurewan irin na karaya dinan, wani irin mummunan faduwa gabanta yayi karfin hali tayi tadaga kafarta ta karaso cikin dakin ta tsaya gefen Waleed, bakinta har rawa yake tace "Ha....Hajiya meya sami Waleed? Meya faru? Meyasame shi"? muryanta na breaking sosai tayi maganar hankalinta a mugun tashe, dagokai Ammi tayi tazuba mata jajayen idanunta sanan ta tashi daga kan gadon tace "biyoni" da sauri Mom ta tashi tana girgiza ma yayarta kai amman Ammi ta dauke kai kaman bata ganta ba tabude kofa tafita Mama biyeda ita, itama Mom tabisu wajen, tsayawa sukayi a reception premises din cikin fushi Ammi tamata pointing dakin da Waleed yake ciki tace "wlh mutuncin ki danake ganine yasa nakiraki dan kizo kiga abinda yafaru da idanun ki, kinga Waleed dina, kinga yanda yake akwance agadon asibiti, kinga yanda yadawo, dan iskan danki ne ya mishi haka, Arham ne yama Waleed dina haka, jibi yanda yama d'ana dukan dakoni dana tsugunna na haifeshi bantaba mai irinshi ba, kitayani tambayan Arham da ina labo yazo yatayani nakudar d'ana ne dazai kamamin shi ya daddaka haka"? mamaki ne ya mugun cika Mama kaman wacce ke koyan magana tadafa kirjinta tace "Arham! " tana kwalalo idanunta waje tsabagen mamaki, cikeda masifa Ammi tace "duk abunda Waleed yama Arham da abunda zai saka mishi kenan, Waleed ko agogo nasaimai bayi karba saina sayo biyu nashi dana Arham, komi shida Arham, amman yau Arham ne zai kamashi yama wanan shegen dukan toh wallahi bazan yarda ba, wlh, bazanji kunyarki na cuci kaina ba, wlh wlh bazan yarda ba yanda yama yaron nan shegen dukan nan sai shima anmai irin ta, mai rabani da Arham sai Allah don saina yagashi, saina sa anmishi x10 abunda yama Waleed wallahi wallahi bazan yarda ba" Mom dai batace komai ba kuma batayi yunkurin hana Ammi fadan ba saboda zata iya komawa kanta, ita kanta abin ya daure mata kai har lokacin yanda Arham yakama Waleed ya daka haka. Numfasawa Mama tayi ta goge hawayen daya zubo mata tace "Hajiya kima Arham kome kikaga dama, karki barshi kisa shima amishi fin haka, fin dukan dayama Waleed ma dan abinda yayi bai daceba nabaki goyon bayan nan dan inbama kisa amai hukunci ba ni wlh sainasa" wayan dake hannun Ammi tabude takira inspector general of police na tafada mishi komai sannan tace mishi atabbatar ankarya ma Arham hannu da kafa kafin dare da toture na police, tana katse wayan ta shiga turama inspector address din gidansu Arham. ❤❤❤ [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣6️⃣ & 2️⃣7️⃣ FREE PAGE Komawa falo sukayi duk suka zauna Anty Hussai da Yakolo sukahau hira banda Anty Hassu datai shiru tana tunani ko kadan bata yarda da Ilham ba, but still batason tama Ilham tunanin datake yi, duka duka yaushe Ilham ta girma hartai wayon da da aurenta zata dingabin wasu mazan, ta tambayi kanta saikuma tai shiru, duka duka yaushe akai auren Ilham dake mugun son Waleed kaman zatai haukane zatabi wani namijin? Ajiyan zuciya ta sauke tana kokarin kawar da tunanin daga zuciyanta dan bamata fatan abinda take tunani shike faruwa. Wuraren 4 na yamma ya shigo gidan marayun yay parking motarshi yana tattaro wasu uban takardu daya ijiyesu a kujeran gefen direba ya kwasa dayawa yarike sanan yabude motan yafito daidai Waleed yakaraso wajen dan daga masallaci yake, wani iri Arham yaji dayaga Waleed kaman zai maida takardun cikin motarshi saikuma yarike hannunshi, karasawa wurin shi Waleed yayi hannunshi zube cikin aljihu yace "kadawo blood" gyadamai kai Arham yayi yace "yes nadawo blood, Mama ta iya saka mutum aiki, iyaye sai ahankali" zaro hannu Waleed yayi daga aljihu yamika Arham din yana kallon uban papers din hannunshi yace "what are those blood mugani" Da sauri Arham ya kalli papers din gabanshi nafaduwa Saikuma yakara linkesu yana lankwdhesu da kyau gudun karyaga mainene su yace "they're not mine, nawani dan anguwan mu" saikuma yabude mota da sauri ya zubasu ciki sanan yamaida kofar motar yarufe yajuyo ya kalli Waleed dahar lokacin kallonshi yake, sanan yace "muje daman akwai maganan danake so namaka" juyawa Waleed yayi yace "am going to the clinic now to check my patient nafito mayi maganan" ganin kaman ran Waleed din yabaci yasa yace "muje to naraka ka clinic din" yabi bayan Waleed din, clinic din suka shiga da basuda much patient that are on admission saidai out patient wayanda kawai zasuzo suyi complain kazakaza na damunsu adubasu abasu magani sutafi, dakin da Widad take direct Waleed yayi Arham biyeda shi suka ya shiga, tana kwance akan gadon an lullubeta da bargo fuskarta ne kawai awaje da gashinta da akai parking tana bacci, idanunta har wani nama nama sukayi tsabagen bacci, karasawa gaban gadon yayi Arham biyeda shi, Arham yace "for the past 3month now kullum yarinyar nan nazo dakin nan bacci take saikace wacce take a coma" stethoscope yadauka yana makalawa a kunne yace "she's not in a coma, babu ranan duniyan dabata tashi, yawanci sau daya take tashi, amata brush abata abinci suma duk tanaci tana gyangyadi tasha magungunan ta, I was the one that increase her dose, duk wanda yakeda damage a brain need absolute rest, yesterday nakara mata MRI da CT scan I was happy with the result, fluid din yaragu sosai wanda yarage baifi an atom size ba, yanzu shi nabashi 4days, dazaran kwanakin sun cika zan sake running test din inhar babu saina godema Allah, tagama da magungunan zan mata transfer zatabar hospital takoma hostel, dudda haka I will be monitoring her ina bata magungunan that help with the memory lost" yay maganan yana zare, stethoscope din daya daura kan kirjinta duk Arham na kallonshi, dan tabe baki yayi yace "tamayi kokari kusan watan ta 9 akan gadon asibiti, sai yanzu ma nake dana sani daban karanci medicine ba nima nadawo likita kaman kai nawani kama ina karanta engineering, kumako kasan inda na karanta medicine dafa nafika kwarewa" yay maganan ahankali hankalin shi nakan wayanshi dayake dannawa yana kokarin turawa Ilham message kartace baikara nemanta ba, dan juyowa Waleed yayi ya kallai jin maganan yamai wani iri aka, ganin wayama Arham din ke dannawa yasa yagyara mata bargon yace "let's go" yay gaba shikuma Arham yamaida wayan aljihunshi da sauri yabishi suka fita, office din Waleed suka shiga, Arham yaja kujera ya zauna Waleed ma yazauna yana gyara zaman takardun kan table dinshi sanan yace "yes ina jinka kace akwai maganan da kakeso kamin blood" Ahankali Arham yasake jawo kujeranshi gaban table din sosai yasauke ijiyan zuciya ahankali sanan yace "I need a favour blood, kaima kasan you've been my ride, my backbone my everything, u are my only friend I come to you in every situation" yadanyi shiru sanan yace "I need money blood, I need money sosai" ahankali Waleed yace "for what?" ahankali yace "kaga na farko, Maman su yarinyar nan da Mama tace na aura, kanwar Mama gidansu ya rushe, ruwa yamusu gyara, sanan inaso nasaya ma mijinta shanu da gona su dinga sana'a, sanan inaso nakaisu Umara harda Mama and many other thing, please kabani 10m blood" yakarshe maganan ahankali shiru Waleed yayi yana kallonshi, arayuwanshi baida mutum daya keso kaman Arham, saisa kome zaimai baya taba sa ido koyaga mezaiyi da kudin kowani abu baruwan shi, in yabashi kudi yabashi ne so badamuwarshi bane abinda zaiyi da itaba, baitaba cire kudinshi yasai kaya ma shi kadaiba bazaima iyabane inhar shi zai cire kudi yasai sitira to nashi dana Arham zaisaya, duk wani abu dazaisa ajikinshi inhar Arham baidashi to iyayen shi ne ko uncle dinshi suka siyamai, yana bama Arham kudi sosai excluding kudin albashin shi, lokacin bikinshi yabashi dollars da Ammi tabashi baimasan yawansu ba, ko last 2weeks saida yamai kyautan 3M cikin kudaden sa gwamnati takawo ma gidan marayu tallafi dan he don't really needs government money kafin su kawo yay amfani da kudinshi yayi abinda ya kamata, abincin Mama da supplement dinta yana kanshi kowani wata saiya saya yakaimata yabata kudin kashewa amatsayinta na maman abokinshi, yabada kudin man motan ta dakudin man generator na gida, banda inverter dayasa aka saka agida saisa 247 duk lokacin dazaka gidan Mama nada wuta, Arham baya komi danta ko'ina ya tare mai wata dawainiyar shi to'ina yake kai kudin shi? Abin yadade yana damunshi bawai dan sa ido kowani abuba just amatsayin shi na abokinshi na gaskiya zaiso yasan inda yake kai kudaden shi karyazo yana wulakanta kudinshi koyana saka kudinshi awani abu na haram ne, yariga yasaimai dankareren gida a anguwan da gidanshi yake da Ilham keciki, incase inya tashi aure yasa matanshi ciki ballema yace gini yake da kudin ina Arham yake kai kudi, kowani bad abu yake da kudi? No hakkinshi ne amatsayin shi na abokinshi na gaskiya ya tambayeshi yaji. "X-man kayi shiru kobaza kabani bane?" Arham yatambaye shi, dan nisawa Waleed yayi yace "no bahaka bane, actually I've been wanting to ask you this question also, I think today is the right day, Arham" Waleed yakirashi anatse, zubamai idanu Arham yayi irin ina jinka dinan batare daya amsaba, ahankali Waleed yace "Arham banso kamin karya, tell me please mekake yi da kudi"? Dawani irin sauri har yana neman taran numfashin shi yace "kaman ya menake yi da kudi" dan jim Waleed yayi yana kallonshi saikuma yace "okay lemme do it like this kafahimce ni, blood duk wata dawainiya dazata sa ka kashe kudinka na dauke makashi yet kullum bakada kudi, me kakeyi da kudi"? Wani irin zabura Arham yayi yamike tsaye daga kan kujeran dayake kai yana kallon Waleed din yace "mekake nufi da duk wata dawainiyar dazata sa na kashe kudi ka daukemin ita yet kullum banida kudi, Waleed gori kakemin sabida kana siyama mahaifiyata yar buhun shinkafa duk wata kana kaimata"? Waleed was still seated akan kujeran shi ya girgiza kai yace "uhm'uhn that's not wat I meant Arham, calm down and sit let's talk please, banga abin zafin nanb......" wani irin buga table dinshi Arham yayi da hannu yay kara yace "don't fucking tell me to calm down, on what account zaka dinga tambayana menake da kudi sabida ka daukemin dawainiyar kaina kana saima mamana yar buhun shinkafa da wake, Waleed ni kakema gori sabida kaga Allah bai horemana kaman kuba eh? Ni kake ma gori Waleed, am talking to you kamin shiru are you stupid"? Arham yadakama Waleed tsawa dayasa Waleed yaji ranshi yabaci dan ba'amai tsawa koda yana yaro baima sababa, tashi kawai yayi dan baiso yabiye mai suyi fada yay wajen hanger dayake makala suit dinshi yaja yadauka zai saka, wani irin shan gabanshi Arham yayi da jajayen idanunshi ya kalli Waleed yanuna kanshi da hannu yace "ni kakema gori Waleed, sanan inamaka magana kamin banza ni kake ma gori"? Kasa saka jacket dinma Waleed yayi sabida ihun Arham dayake mai a kunne kaman zai fasamai dodon kunne yamaida jacket din yarike a hannu sanan ya kalli Arham yace "since you are too dumb to understand a simple question dana tambayeka then take it anyhow you wish to take it" yana gama maganan yadau wayanshi daga kan table zai juya yay kofan fita Arham yasha gabanshi yace "ni kakema gori"? cikeda mugun bacin rai da kulewa da maganar Waleed yace "nayi, kai duk abinda kaga dama" kaman amafarki Arham bai wata wata ba ya daurama Waleed wata lafiyayyen mari ata gefen ido dan marin har yadan taba idanunshi na side din dama jikake kau! Idan Waleed yace he was expecting a slap from Arham he is lying, jin saukan mari yayi kawai daga sama baisan lokacin daya saki wayanshi da jacket din dake hannunshi akasa ba suka fadi, wani irin fincikanshi Arham yayi ya bugada bango bayanshi yabada bam, Arham ya shakemai wuya, cikin kunfan baki da mugun tsana yace "sabida rashi da talauci yasa am working under you, yaro dakai u are just 28 inada 35yrs na girmeka da shekaru shidda zaka tsaya kana gayamin magana yanda kaso, daman hausawa sunce yaro da kudi babba yake dawowa, this can not work with me, yau saina koyama hankali, I will teach you a lesson, fight me back now, fight me back" har alokacin Waleed was shocked yama kasa yarda Arham dinshi ke fada dashi haka, ya shakeshi yana neman kashe shi idanunshi sunyi jajir jijiyoyin kanshi sun fito, fuakanshi tai jajir abunku da farin mutum, ahankali ya iya yataba hannun Arham dake wuyanshi muryanshi bata fita sosai yace "u.....are....hurt.....ing me blood.....am....am.....my....my.....breath" yay maganan about to die amman Arham baida alamun sakinshi saima kara shakeshi dayayi yace "I said fight me, fight me mana, I want you to fight me dan Allah inka isa, kai fada dani kaga yanda zan baka kashi, na farfashe maka wanan bakin dakake min gori dashi kan kasayama Mahaifiyata wanan shegen tsukukun gidan kaman gidan kiwon kyankyasai, da shegiyar akurkan motar nan, inda don Allah kakeyi da tikeken gida zaka saya mata irin naku mansion, mota mai numfashi bata manoma ba, yau saina nuna maka kudin ka bazai iya taimakonka a hannunna ba, I will deal with you yau Waleed, wlh saikai fada dani zan kyaleka na rantse maka" daidai lokacin akai knocking kofar office dinshi, sake shakeshi yayi to the extend this time idanunshi sun soma juyawa gashi yakimai komi dan he can't raise his hand on his friend or hurt him in anyway ba, da kyar hannunshi ya iya komawa baya dashi yatataba flower verse din dake kan table dinshi ya kabar dashi kasa yay kara akasa sabida wanda ke waje ke knocking kofarshi yaji ya shigo, jin karan flower verse yasa Mama Iyami tace "subhallahi karan menene wanan" ta murza handle din kofan kawai ta shigo ciki, ganin yanda Arham ya shake Waleed yasa da sauri tai kansu yace "Mr Arham innalillahi wa innailaihi raji'un, wats happening here? Meke faruwa haka? Kaida abokin ka, let him go, sakkashi kaga" ta shiga kokarin fincike hannun Arham daga wuyan Waleed, cikin fushi Arham yace "wlh bazan sakeshi ba saiyay fada dani, sainaga uban karfin dayike dashi dayake juyani yanda yakeso sabida yaga yanada kudi dan ubanshi" ganin yanda Arham ya harzuka Waleed na neman mutuwa a hannunshi yasa tafita daga office din da gudu ta kurma uban ihu. "jama'a kuzo kutaima keni, Dr Waleed Warbai and Mr Arham are fighting, please helppppp" ihunta gabaki daya yadauki gidan marayun, da gudu wasu staff din Waleed da yaran gidan marayun damasu shara, gardeners da waye da waye aka shigo office dinshi da gudu, Nura dawasu maza hudune suka fizge Arham, suka jashi baya Waleed kuma yay baya zai zube wasu ma'aikatan suka tareshi, da gudu Iyami tafashe da kuka tace "innalillahi is sir alive jama'a?" wani ma'aikaci ne mai suna Auwal yace "he's alive but sai ankaishi asibiti" da sauri suka fita dashi daga office din, Mama Iyami tajuya ta kalli Arham dake huci yana tsaye ya fizge kanshi daga rikon da akamai tace "Mr Arham meya hadaka fada da abokin ka eh, dan uwanka fa, blood naji kuna kiran junanku, Mr Arham meya hadaku dashi" cikin wani irin fushi Arham yace "kije ki tambaye shi mana, dayake shi ogan kine bazaki iyaba shine yabaki aiki, yana baki na abinci bazaki iya tambayanshi ba, amman dayake ni kin rainani dole kitasani agaba kina tambaya, matsiyatan mutane, masuyin boyi boyi dan abasu kudi, fatararru kawai" yay maganan fuuu yafita daga office din ma'aikatan kowa yabishi da kallo ana mamakin tome yahada su tsawon shekaru nawa ba'a tabajin kansu ba saiyau, motarshi ya shige yaja motar yawuce yabar orphanage din. Staff, ma'aikata, yaran gidan marayun aka fiffito aka taru awaje, daman ance bad news yafi yanda wuri nanda nan aka cika ko'ina, aka cika gaban clinic da saida Dr Kemi da Dr Ayo suka kira security gate biyu sukazo, akasa kowa yakoma various places dinsu, Baba Mani ne kawai da Mama Iyami aka bari suka shiga asibitin har zuwa dakin da aka kwantar dashi likitoci akanshi ba'a bari sun shiga ciki ba, fuskarshi tai mugun jan da saita baka tsoro, gefen idanunshi na dama ya kumbura dan hardan tsagewa yayi jini yadan fito, kasa daurewa Mama Iyami tayi ta fashe da kuka a rayuwa tanason Waleed, bata taba haihuwa ba, mijinta yarasu, an koreta gidan haya yazo batada inda take kwana, abakin titi takoma tana bara tana tara kudin datake samu danta kama haya, wata rana tana cikin baranta taga anyi parking, Waleed yafito kai tsaye yace mata mesa kike bara Mama, tace banda kowa, mijina yarasu, banda y'aya Allah baitaba bani haihuwa ba, ankoreni agidan haya, bara nake natara kudi nasami matsugunni, budan bakinshi bazaki kara baraba, sanan yajuya yay wajen motarshi yace zomuje, gabanta nafaduwa amman hakanan taji zuciyarta nacemata tabishi, motar ta shiga, yana zaune agefenta ga basket da alamun abinci ne aka dafamai agida, dauka yayi duka basket din yabata yace kici, budewa tayi ta shigaci kaman bata tabacin abinci, yakaita gidan marayun shi, yakaita asibitin shi yasa tai wanka, aka kawo mata kayan asibiti tasaka yadubata tsaf bata dawani ciwo sai maleria yay treating nata, sanan dakanshi yakaita girls hostel yabata daki na musamman dake dauke da komi sanan yace "aikinta kawai ta dinga kulamai da activities din yaran nan, she's in charge anan section din, zai dinga biyanta duk wata, sanan yasa akayo mata dinkunan kaya masu kyau aka kawo mata, tundaga ranan kulada ita yake to the extend har Ammi tasani tanada number ta, Ammi data ambata aranta yasa taciro wayarta ta shiga neman number Ammi tana kuka sosai, kaman wayan zata katse sanan Ammi ta dauki wayan, cikin kuka Mama Iyami tace "Allah yataimaki Hajiya amin afuwa hala ban kira alokacin daya kamata ba, amman dolece tasa nakira" takara wani irin rushewa da kuka dayasa gaban Ammi ya shiga dukan uku uku tama kasa magana tsabagen faduwan gaba dan tanada hawan jini, Mama Iyami cikin kuka tace "Hajiya kome kikeyi kibarshi kizo ba'asan ko karshen ne yazo ba, wayyo Allah na Hajiya" takara kecewa da kuka dayasa Ammi bakinta yafara motsi tana kokarin furta magana takasa dakyar tana wani irin nishi tace "k.....kar.....shen wane.... Iya.....mi"? Cikin wani irin mahaukacin kuka kaman wacce akama mutuwa Mama Iyami tace "karshen Dr Waleed Hajiya, Mr Arham yama Dr Waleed shegen duka, yanzu haka Dr Waleed baisan inda kanshi yakeba, likitocin mu gabaki daya na kanshi baisan inda kanshi yakeba ana kokarin ceto rayuwanshi, saisa nace kizo idan ma cikanwan ce yacika agaban ki, ai Mr Arham bai kyauta ba da kyar muka kwaci Dr Waleed a hannunshi Hajiya, dan Allah kizo yanzu koda karshen ce yayi ta a hannunki, wayyo Allah na Dr Waleed" tarushe dawani rikitaccen kuka tana katse wayan, majina shabe shabe. Wani irin baya Ammi tayi zata zube akasa daidai lokacin mai aikinta tafito daga kitchen dauke da katuwan kulan abinci, wani irin sakin kulan tayi akasa tai kan Ammi da gudu kafin Ammi ta zube ta tareta tareda ihu tace "Hajiyaaa!" duk masifar Ammi tana bala'in sonta dan tayi aiki a gidaje da dama bata tabayin aiki agidan dataji dadi irin na Ammi ba, ganin Ammi ta sume yasa ta kuma ihu. "Mai gadi, direba, duk wanda yake awaje ya shigo ku taimake ni, Hajiya ta suma" da gudu ma'aikatan gidan suka shigo, su mai gadi naganin Hajiya assume sukai kitchen suka fitoda ruwa agora yayyafa mata ruwa sukayi tawani irin sauke ajiyan zuciya tare da bude idanunta, ahankali take kallonsu one by one, kafin ahankali tace "ku kaini wurin Waleed gida a orphanage, dan Allah ku kaini wurin Waleed dina a orphanage". [11/1, 11:47 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 2️⃣9️⃣ FREE PAGE Hayaniya da zata iya cewa tunda take a asibitin bata tabajin irinshi ba, hayaniyan ya mugun cika mata kunne yasa tabude idanunta ahankali tana kallon dakin, idanunta sunmata shegen nauyi sabida bacci bai isheta ba, sosai kirjinta taji yana wani irin faduwa, ward din datake gabaki daya ta kalla babu kowa cikin ward din sai ita kadai dake kwance akan gadon an lullubeta da bargo sanan anmata parking gashinta gabaki daya anyi mata parking na ponytail, ihu dawani irin masifa dataji yana sauka akan kunnenta yasa ta yaye bargon jikinta ta tashi zaune dagakan gadon tana kalle kallen dakin, ihu da hayaniya da masifan da akeyi jitake kaman a brain dinta akeyi, sakkowa tayi dagakan gadon tazira pink slippers dinta dake wajen sanan tadau Teddy dinta ta kankameshi akirjinta ta shiga tafiya ahankali kaman ana kiranta, hannu tasa tabude kofar dakin datake tafito tana tafiya dogon jelar gashinta na lilo tana kankame da Teddy ta kaganta kaman kasace ta kagudu, tai bala'in kyau doguwan yarinya da ita, batada wani kiba tana sanye da gown din asibiti daya wuce guiwanta da kadan, batada wani cikan kirji sosai, kirjinta moderate yan daidai irin na yaran larabawan nan, kanta an mata parking an daure da ribbon gashin na lilo, tundaga nesa take hango su Ammi, Mama da Mom na hayaniya dayasa ta tsorata tasake kankame Teddy gam gam idanunta na kawo kwalla dan tsoro taji sun bata hakan yasa ta shiga waige waige tana neman Waleed, fitowa tayi daga corridor ta shiga tafiyanta kaman bana mutum ba a reception din su Mom ko kadan basu lurada itaba, tunawa da ranan Waleed yayi kofa da ita yafita da ita yasa tai wajen kofan da sauri tana cikin tafiya kaman ance ta kalli glass din kofar emergency ta hango Waleed kwance kan gado fuskarshi a kumbure yasa tai dakin da sauri, hannu tasa tabude kofan ta shiga duksu Ammi basu lurada itaba, maida kofar tayi tarufe, ganin ciwo ajikinshi yasa tawani irin saki Teddy ta akasa tai kanshi da sauri, hannayenta tadaura kan cikinshi tabude bakinta tana kokarin ma magana takasa sai kawai tasaki kuka sosai tahau jijjigashi, amman bai motsa ba, kai hannunta tayi ta daura kan gefen idanunshi daya kumbura suntum ta taba tana kuka sosai tanaso tai magana tama kasa, bama tasan sunanshi ba amman sotake yabude ya kalleta, girgiza shi tayi tace "ahhhh, Umm mm" kafadarshi mai lafiya ta bubbuga tana kuka da kyar bakinta ya iya furta. "you, youuuuuuu, yo.....u" tasaki kuka sosai kaman zata mutu saikuma tadaura kanta kan kirjinshi tahau kuka tana jijjigashi tace "youuuu" sosai take kuka, takai kusan 5min ahaka tana kuka tana jijjigashi sanan tadago kanta ahankali ta kalli fuskarshi saikuma tajuya ta kalli TV dakin dake aiki da babu kara ko kadan dan anyi muting television din, tashar AIT ke aiki suna wani series na Korean film. Daidai wata yarinya tashigo dakin wani namiji mara lafiya tana kuka tana zuwa kawai ta duka ta daura bakinta kan nashi sai saurayin ya farka, tana ganin haka da sauri tana kuka ta kallai, kafin ahankali tana kuka sosai takai fuskarta saitin nashi tana kallon fuskarshi yana mata wani irin kwarjini ta kafe pink lips dinshi da ido kafin ahankali ta saukar da bakinta kan nashi, tasaka all his lips inside her tiny mouth tai shiru tana kallon idanunshi ita adole tana jira yabude ido shima kaman na film hawaye na zuba daga idanunshi. Kaman acikin mafarki yaji saukar wani tattausan lips kan nashi, bude bakinshi kadan yayi yay grabbing those soft tender lips yashiga kissing dinsu kaman zai cinye bakin, yatura tongue dinshi cikin bakinta yana lasowa kasa daurewa yayi yamika hannunshi trying to grab something yaji yakama mutum, ahankali yashiga bude idanunshi dasukamai nauyi kaman banashi ba, dishi dishi yake gani saikuma idanun suka washe tarr, ido da ido yayi da Widad da bakinta ke cikin nashi har lokacin bai dena kissing dinta ba idanunta sunyi jajir tsabagen kuka tana kallon idanunshi kuri kaman wata mayya, wani irin sakin lips dinta yayi da sauri yacire lafiyayyen hannunshi daga bayanta yaja jikinshi yakoma baya da sauri yana kokarin tashi zaune yana kallonta still, mikewa tayi itama tsaye takai hannunta kan idanunta tana share hawayen daya kasa dena zubowa sanan ta taho da sauri tazauna kan gadon tafada jikinshi ta rungume ta hanyar daura kanta kan kirjinshi tana kuka sosai, rasama mezai mata yayi hakan yasa yakai hannunshi mai lafiya yadaura akan bayanta yadan bubbuga alamun tai shiru sanan yatureta daga jikinshi ta tashi, hannunta ahankali takai ta daura kan wuyanshi dayaji ciwo tana turo baki kafin ahankali bama tasan tayaya maganan yafito daga bakinta ba tace "so....ry" gyadamata kai yayi cikeda dauriya, sanan ya tsareta da idanu, saikuma yace "who thought you how to do that"? Yanuna mata bakinshi, juyawa tayi kaman wata yar yarinya ta nunamai TV da yatsan ta hakan yasa ya kalli TV, Korean film yaga anayi yasan tunda ta nunamai wajen yasan anan tagani, shiru yayi yana kallonta, muryan Ammin shi dayaji yasa ya kalli kofa da sauri, faduwa gabanshi yayi, hakan yasa ya kalleta, dagata yayi tamike tsaye, anatse sabida tagane cikin harshen turenci yace "inaso kidauki Teddy ki ki koma dakinki kinji Saheeba, anjima kadan zanzo wajenki, now be a good girl and listen to me and go" makemai kafada tayi tafashe da kuka, girgiza mata kai yayi kaman zaiyi kuka yace "please Saheeba kitafi, yanzun nan zanzo kinji" sake makemai kafada tayi tana kuka, ahankali yasanya hannunshi ya jawota jikinshi rungumeta yayi tareda bubbuga bayanta a kunnenta yamata whispering yace "listen to me, please Pretty go, I don't want Ammi to see you here, please pretty go" yay maganan tareda dagota ahankali, fuskarshi ta kalla ya gyadamata kai hakan yasa ta sauka ahankali daga kan gadon, daukar Teddy dinta tayi sanan tajuyo ta kallai shima kallonta yake kaman yau yafara ganinta, ahankali tasa hannu tabude kofar dakin tafita tamaido kofar tarufe yana kallonta, ta glass din kofar yacigaba da kallonta ahankali take tafiya ta kankame Teddy ta, tai corridor dazai sadata da ward din da aka kwantar da ita. Ajiyan zuciya ya sauke tareda lumshe ido yadaura hannunshi kan fuskarshi kafin yasauke hannun kan bakinshi yay shiru yana tunanin what just happened. ******* Within 30min IGP yayi deploying police zuwa address da Ammi ta tura mai. Knocking Gate din gidansu Arham one of the police men yayi, fitowa daga daki maigadi yayi yaleko, ganin police ne yasa yace "bayin Allah wakuke nema"? Wani daga cikinsu ne yace "Goodday please we are looking for Mr Arham" mai gadi da tuni jikinshi yahau bari ganin yan sanda yasa yace " yes gidan nan ne gidan Mr Arham" daya daga cikinsu policeman dinne yace "is he in"? Ware ido mai gadin yayi dan baigane turencin ba hakan yasa daya daga cikinsu yace "yana nan? Da sauri yace "yes.....eh,yana nan, yanzun nanma ya shigo gidan" "kaimu wurin shi" da sauri yajuya yay gaba suna biyedashi abaya har flat dinsu yabude kofa yashiga suma haka, a palour suka sameshi ya daura kafa daya kan daya yayi resting head dinshi a kam one seater kujeran dayake zaune akai hannunshi rikeda chilled maltina, jin mutane akanshi yasa yadago yana kallonshi, babban su ne yace "good-day Mr Arham we are here to invite you to our office for some questioning" yana gama maganan yafito mishi da ID card dinshi ya nunamai, bin ID card din yayi da kallo sanan yatabe baki yamaida kanshi kan kujeran yana girgiza kafa, kara maimaita mishi maganar sukayi but no response still saima maltina shi daya cigaba dasha, mai gadi ne saya gama tsurewa yace "Alhaji dakai fa suke" dago kanshi yayi ya musu wani irin kallon banza yace "what questioning"? Cije lips policeman din yayi yace "when you reach our office you will find out" "and where is your office located at"? Shiru police din yanasa baicemai komiba dakin ya tsit, maigadi dake shirin sakin fitsari yace "Alhaji kabisu kar su maka wani mara kyau, kagan sunata binka ahankali tun dazun, kawa Allah kamike kabisu" y policeman dinne ya juya ya kalli wasu manyan officers guda biyu da sauri sukai heading directing to kujerar da Arham yake zaune. "Sir you are under arrest" fisgoshi daya daga cikinsu yayi ya tayar dashi tsaye Arham bayyi wata wata ba ya dauke policeman din da mari mai kyau, bai ijiye hannun kasa ba yaji saukan mari to ko'ina akan fuskarshi dayaji yaji kwakwalar warshi tajuya abaibai. ❤❤❤ [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 3️⃣0️⃣ Kamar jira suke suka haushi da duka kaman an aikosu suna bugamishi gindin bindiga all over his body, jin duka tako'ina yasa Sadiya tafito daga ciki dagudu tana ganin Arham ya sanda ke duka tahau ihu, mai gadi shima jikinshi narawa yashiga rokonsu su yakuri subarshi amman ko jinshi basayi saida suka tabbatar da sunmai lilis, he is totally weak baima iya motsi jini nafita daga hancin shi da bakinshi sanan suka barshi suka sakamai ankwa handcuff sanan suka jashi kamar ragon layya suka fita dashi daga dakin zuwa cikin motarsu. Binsu har waje Mai gadi yayi shida Sadiya suna rokonsu akan susakeshi amma basubi takanshi ba, suna jefashi ciikin motarsu suka shiga direba yatada motar sukai gaba dashi. Koda suka Isa police station fuskar Arham yay subu subu tsabagen mari kan dayasha, janshi suka karayi zuwa cikin station din suka bada report that lead them har suka mishi dukkan nan sanan aka jefashi cikin cell, babban su ya shigo cikin cell din rikeda wata zungurariyan takarda ya fara karanto mai offense dinshi na trying to murder Dr Waleed warbai. Janshi akayi zuwa toture room aka Fara tambayarshi why he strangulated Mr Waleed Warbai. Dago jajayen idonshi Amma baice musu komai ba. Fara dukkanshi sukayi tako Ina Yana ihu Yana " Don Allah kuyi hakuri, it was a mistake" kuka yafara yi Amma still basu barshi ba. Sai dasuka tabbatar da sun mushi lis har kasa daga lafanshi guda dayayi sannan Suka kawo mishi ruwan zafi suka bashi yasha. Bayan sallan magrib Ammi da Mom da Mama suka shigo dakin dan sunje masallaci sunyi salla, ganin Waleed azaune yasa da sauri Ammi ta saki jakanta kasa tazo gadon tazauna gefen kafafunshi takai hannayenta kan fuskar Waleed, kaman zata fashe da kuka tace "My baby katashi, tell me meke maka ciwo eh? A ina kakejin ciwo ajikinka, tell me Waleed dina meka maka ciwo"? Tai maganan hawaye nata ruwa a idanunta tana shashafashi kaman zata cinyeshi, dan murmushi yamata ganin yanda tadamu yace "am fine Ammi karki damu, meya kawoku orphanage haka? Mama" yakira sunan Maman Arham ahankali yana murmushi, karasowa Mama tayi wajen zuciyarta tamata mugun nauyi, wani irin kunyan Waleed dinma taji tanaji jibi yanda danta yamai, yaron dake sonshi dake nufinshi da alkhairi ne yama wanan jina jinan, tsayawa tayi ahankali agabanshi, dan murmushi tayi mai kama da murmushin dole sanan ahankali tahada hannayenta biyu tace "Waleed dan girman Allah kayakuri abinda Arham yamaka, wlh naji kunyan halin......" da sauri Waleed yamika hannunshi mai lafiya yakama hannun Mama yace "Mama me haka kike cewa dan Allah? Please kidena bani hakuri, ninace miki Blood yamin wani abune"? Wani wawan harara Ammi ta watsa mishi, Mama tace "Arham yamaka abinda ba daidai ba, Arham bai kyauta ba, kalli halin dayasaka ciki, wlh naji kunyan abinda yamaka, kunyan kallonku dukama nike, Arham bai kyauta ba wlh, saisa nabama Ammi goyon baya takiramai yan sada amai lilis akaryashi kaman yanda shima yamak......" kafinma takarasa maganan Waleed yatareta yace "waya kirama Arham police"? Cikin fushi Ammi tana ballamai harara tace "nice nasa aje akamashi akaishi police amishi shima dukan dayamaka, ko angayamai banison kane dazai kama yamaka wanan dukan eh? Karfinku dayane yasan da shekara nawa ya girmeka dazai kamaka ya bubbuga haka saisa nasa inspector yasa aka kamashi akaishi Station amai wanan shegen dukan dayamaka" sosai idanun Waleed sukai wani irin ja ranshi yawani irin baci, cikin fushi yace "Ammi wai mesa in everything saikin shiga rayuwana ne eh? Friends fight don't they? Sabida munsami miss understanding da blood saiki shiga fadanmu har kisa akulleshi, ninace miki ki kullemin dan uwane eh"? Wani irin kallonshi Ammi take kaman ta rufeshi da duka amman bazata iyaba, wani irin kunci da haushin abinda Ammi tasa akama Arham yaji hakan yasa yace "Ammi call that inspector right away kicemai yasaki Arham" cikin fushi Ammi itama tace "bazanyi ba dan ubanka" Waleed zaiyi magana da sauri Mama datake ganin duk laifin ta ne komi tace "kaga Waleed abinda mahaifiyar ka tayi tayi gaskiya, daidai tayi wlh ko ansakoshi nida kaina saina sassaba mishi, dan haka kamabar maganan nan" gyada musu kai Waleed yayi cikin kunan rai yace "ok" wani irin yunkurawa yayi daga gadon yana cije baki sabida yanda bayanshi da kafadarshi da aka daure ke mugun ciwo, da sauri Ammi ta tareshi tace "kai ina zaka Waleed" ture hannunta yayi cikin karfin hali irin na maza ya shiga kokarin sauka daga kan gadon, rikeshi daga Mama har Ammi da Mom sukayi, fashewa da kuka Ammi tayi tace "Waleed wai mesa bakajin magana ne kacika taurin kai eh? Ina zaka, sokake daurin da aka maka ya turgude, Waleed kasheni kakeso kayi kahuta eh Waleed, mena maka? Mena maka nace da zaka tashi zakabar gadon da kake kwance kana ganin bamaka da karfin tashi" tureta yayi a haukace ya kabar da hannunta daga jikinshi yace "leave me alone Ammi, kurabu dani, I can't fight with my friend again, friends can't fight again? Eh dole saikun shiga, dole sai kin shiga komi nawa? Ko kasheni Arham yayi he's my friend, Ammi you have no right to interfere in my affairs, sabida Arham ya dakan saiki aikamai police su kamashi a kulle shi adaka haba Ammi, haba Mom" yay maganan yana kallon Mom itama yace "bakuji kunyan Mama datake nan tsaye dakuba kuna saka a chaza danta eh?" da sauri Mama zatai magana Waleed yadaga mata lafiyayyen hannunshi yace "Mama please kiyi shiru" sanan ya kalli Ammi yace "Ammi baki kyautamin ba, and inhar you feel wanan abun dakikeyi akaina shine son dakike min then guess what am not proud of the love you have for me am not, cus kinsa inajin kunyan abokina, my childhood friend, my only friend my blood Ammi, Ammi you hurt me today" yay maganan yana kwanciya a gadon ahankali tareda lumshe ido, shiru Ammi tayi tana kallonshi kalaman shi sun mugun sosamata rai, zatai magana Mom ta girgiza mata kai, dauke kai tayi tace "Waleed nikake ma magana haka akan nace a hukunta Arham ko" tai shiru tana kallonshi ko bude idanunshi Waleed baiyiba, ciro wayarta tayi takira Inspector agaban su tace asaki Arham din sanan ta katse wayan, sanan ta kalli Mom tace "stay with him nizan tafi gida" tana maganan tadau jakanta cikeda fushi tafita daga dakin zuciyarta kaman zai tsage yafashe, Mom zata bita Mama tace "bari nina bita ki zauna dashi" juyawa Mama tayi tafita daga dakin, Mom kuma ta zauna kan kujera takifa kanta kan gado tai shiru tana tunani. Koda Mama tafito har motar Ammi direba yajata sunyi gaba, awani irin hankali Mama takarasa motarsu, baya tabude ta shiga direba ma baya cikin motar da alamu masallaci yaje, fashewa da kuka tayi sosai, intace dukan da Arham yama Waleed bai mata ciwo ga wlh tai karya, ta bala'in jin ciwon dukan nan kaman me, Waleed d'a ne wlh, dan halas d'a na kwarai, tasan harga Allah tanaso aramamai amman da Waleed yafarka yayma Ammin shi maganganun nan saida ranta ya sosu, bala'in sosuwa ma, Waleed d'ane da kowace uwa zatai alfahari dashi aduniyan nan, taji kunyan abinda danta yamai wlh taji kunya, tasan Ammi tagaya mata maganganu amman ko kadan bataji zafinsu ba dan tasan ciwon dakake ji in wani yakama maka d'a yadaka ba gaira ba dalili, Arham bakin halinshi da bakin zuciyanshi tamai yawa, kuka tayi mai suna kuka amotar nan hakanan ma taji bazata iya komawa cikin asibitin tahada ido da Waleed ba, tana zaune direban ta ya shigo yace "Hajiya yakuri ina masallaci ne mutafi?" gyadamai kai tayi tace "eh mutafi", tada motar direban yayi suka fita daga gidan marayun. Direban Ammi nakaiwa gidan bamata jira yabude mataba tabude tafito, ahankali take tafiya dan bamata gani sosai, kanta wani irin bugawa yake kaman ana dukanshi da gatari, falo tabude ta shiga, yar aikinta da gudu tafito tana mata sannu da zuwa ko iya amsata bata iya tayiba tawuce stairs tai sama ahankali tabude dakinta ta shiga, yarda jakanta tayi anan tsakiyar dakin tawuce kan gadonta da kyar ta zauna tamika hannunta ta shiga tattaba saman kan side drawer dinta wani goran magani ta dauka da sauri, sanan ta bude taciro wasu kwayoyin magani na masu hawan jini guda biyu ta jefa abaki ta hadiye sanan tadauko bottle water ta kurbi ruwa kadan tasha, kanta na bala'in ciwo, tadafe kan da duka hannayenta ba'awani dauki lokaci ba bacci yay awon gabada ita. *** Wuraren karfe biyun dare cikinta yawani irin murda mata da sauri tabude idanunta rass ta tashi zaune tznabin dakin da kallo, fuskarta ta taba taji tahada wani uban zufa kaman wacce tai dambe dudda uban AC dake dakin, tashi tayi ahankali ta dauki wayarta ta lalubo number Waleed tana yatsine fuska sabida ciwon maran datakeji, dailing number shi tayi amman bai shigaba, hartai bacci taga bai dawo ba gashi number ta bayi shiga hakan yasa tamike tsaye ahankali da kyar tana daga kafarta tabude kofa tafito daga dakinta, dakin Waleed tabude taga baya ciki hakan yasa tai stairs tafara tafiya ahankali zata sauko, wani irin ciwo dataji ya tokare mata mara yasa ta kurma wani mahaukacin ihu. "Mai gadiiiiii" zama tayi awurin tana wani irin nishi kafin tasake kwalama mai gadi kira, akaro na uku ne yaji yafito daga dakinshi yana share idanunshi dake cikeda bacci, ganin daga flat ake kiranshi yasa yay flat din yabude kofa ya shige hango Ilham daga ita sai doguwan rigan bacci yasa yay wurinta da sauri yace "Hajiya sannu haihuwan ce bari nakira miki dakta awaya" zai ciro wayarshi tace "kabarshi bayi shiga, kiramin duk wanda zaka iya kira azo a kaini asibiti azaba nikeji mai gadi" takurma wani uban ihu da saida ya firgita yace "Hajiya salati zakiyi, salati ake" juyawa yayi ganin bamatasan inda kanta yakeba ihunta kawai take, saida ciwon yadan sarara sanan ta nemi number Arham amman harya gama ringing bai dagaba, sau biyar takirashi amman shiru, dialing number Ammi tayi shima bayi shiga, ganin haka yasa tai dailing number Mummy ta, ringing daya Mummy ta tadauka fashewa da kuka tayi tace "Mummy mutuwa zanyi, Waleed bai dawo gidaba number shi bayi shiga, ina kiran number Maman shi itama bata shiga, dagani sai mai gadi agidan, kuma bai iya tuki ba balle yakaini asibiti, Mummy mutuwa zanyi" tafashe da kuka sosa daya ruda mahaifiyarta, anatse tace "kinga ba'a kuka in ana nakusa, be strong kinji yar albarka, ga Babanku nan yanzu zai kawoni wurinki just stay where u are kinji am coming" ta katse wayan, daidai mai gadi na shigowa yace "Hajiya wlh duk basa bude gate kinsan anguwan manya ne nan" ko jinshi batayi tahau ihu tana kuka sosai mai gadi yama rasa maizai mata sai dialing number Waleed yake amman bata shiga. Wani ruwane yafashe mata dayasa tahau ihu. "mai gadi zan mutu kataimaka min wayyo Allah na kataimaka min dan Allah, daidai lokacin akai knocking kofar gidansu, da gudu mai gadi yafita yana zuwa yabude gate iyayen Ilham dinne mamanta da Babanta} da mota, Mmummy ce ta shigo tai ciki tafito da ita aka sata a motar Baba sanan takoma ciki taje ta nemo akwatin haihuwan ta adaki sanan tawuce takai motar ta shiga baban su yaja motar sai hospital. Bakaramin wahala tasha ba sai wuraren karfe 8nasafe ta haihu, ta haifo danta namiji katoto mai bala'in kamada Arham kaman yay kaki ya tofar. [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 3️⃣1️⃣ Shirya yaron akayi aka fito da fitoda shi aka kawoma Mummy shi, ahankali Mummy ta karbe shi tana murmushi tace "miji nasamu ko kishiya"? Dariya nurse din tayi tace "miji ne Hajiya" karbanshi Mummy tayi tana kallonshi yaron kato dashi Masha Allah. Daidai mijinta yakaraso tace "Alhaji kaga mijina masha Allah dawa yay kama"? Dan dariya Alhaji yayi yace "ai kamanshi daban da uwar da baban, hala sai nan gaba zai dauki kamanni, sake gwada namban mijinta dana mahaifiyar shi kiji ko zasu samu yakamata" number Waleed tafara dialing amman bai shiga har lokacin hakan yasa tai dialing number Ammi, lucky wayar ta shiga, wayar na gab da katsewa Ammi ta dauka, kafin ma Ammi tai magana Mummy tace "kawata lpy kuwa? Tun jiya da daddare muke kiranki dagake har Waleed baya shiga wlh hankalina yatashi" dan murmushi Ammi tayi tace "Waleed ne yadan sami hatsari wlh yana asibiti agidan marayun shi har karyewa yayi akafada, ban fadima Ilham bane kinsan mai ciki ba'a daga musu hankali haka, nikuma ina dawowa gida magani nasha na kwanta sabida hawan jinina yatashi, Mom ce awurin shi amman yanzu nai wanka shiryawa ma nike nakaimusu breakfast" da sauri Mummy tace "innalillahi wa innailaihi raji'un, ashe abinda yafaru kenan Ilham takira takira mijinta bayi shiga daga karshe saidai takira mu mukazo gamunan a asibiti wlh tasami karuwa yanzun nan amman tun cikin dare mukazo, anmiki miji fa, baki ganshi ba dan lukuti dashi" Mummy tafada cikeda farin ciki sabida tasan yanda Aminiyarta keson jika, Ammi mutuwan zaune tayi tama kasa magana, hakan yasa Mummy ta kyalkyace da dariya ta kalli mijinta tace "Alhaji tayi mutuwar zaune fa" sukahau dariya sanan tace "ki shirya saiki biyo kiga jikanki kafin ki kaima su Waleed abinci, Allah yabashi lpy, anjima dazaran an sallameta zamuje mu gaidashi" Ammi kasa yarda da abinda aka gayamata tayi hannunta har wani irin rawa yake tai dialing number Mom dake zaune dakin tana kallon Waleed da tun jiya daya lumshe ido yaki budesu bacci mai nauyi ya kwasheshi yanzu muka yatashi dan tasan yana jinta sarai wlh, kaman bazata dauki wayan Ammi ba saikuma ta dauka takai wayar kunnenta, wani irin zabura tayi tace "Ilham ta haihu?" rass Waleed yabude idanunshi jin ance Ilham ta haihu, katse wayan Mom tayi tana murmushi sanan ta kalli Waleed dake kallonta ta tabe baki tace "mara kunya aika bude ido dakaji matarka ta haihu, suna asibiti ta haihu ansami namiji" ahankali yadan saki wata yar kyakkyawan murmushi sanan ya yunkura zai tashi, kafadarshi kawai da akai dauri kehanashi motsi yanda yakeso, da taimakon Mom ya iya tashi, Mom tace "me kakeso?" ahankali yace "office dina zani, I want to shower na chanza kaya naje nagansu" taimaka mai Mom tayi yamike tsaye ahankali suka fito waje, nurses sai gaidashi suke gyadamusu kai kawai yake, haryakai kofa yatuna alkawarin dayama Widad, Mom ya kalla yace "am coming Mom" sanan yay hanyar dakin datake, hannunshi yasa yabude kofar ahankali yashiga yana kallonta ganin tana bacci, ahankali yakarasa gaban gadon ya tsaya akanta yana kallon fuskarta kaman yatasheta dan taganshi saikuma yafasa yajuya kawai yafito tareda kullo mata dakin sanan yafito yay office dinshi shida Mom suka shiga ciki, dakin shi ya shiga yay bayi, brush yayi sanan yay wanka da ruwan zafi, jikinshi ciwo yakemai bana wasaba bai taba fada a rayuwanshi ba ko saisa Arham yay galaba akanshi oho, fitowa yayi yadauko wani jean yasaka da kyar sanan yadauko wata riga sai saka yakasa sawa, kwalama Mom kira yayi hakan yasa ta shigo, wani scissors yanuna mata, saida suka yanke hannun rigan daman sabida hannunshi yay balance sanan tasamai rigan ta shinfidamai dadduma yay sallolin da ake binshi sanan suka fito, Mom kejan motar suka dauki hanyar asibitin da Ilham take, parking sukayi suka fito sanan suka fara tafiya har zuwa dakin datake akwance. Bude kofan Mom tayi ta shiga, Ilham na kwance kan gado, fuskarta ya kumbura suntum tsabagen kuka, sai Mummy dake zaune kan kujera rikeda jaririn da aka shirya yay kyau, Mummy na ganinshi tace "subhallahi, innalillahi wa innailaihi raji'un, Waleed wanan wani irin hatsari ne kaga yanda jini yataru a idanunka kuwa, jibi wuyanka da fuskarka sannu Waleed" kanshi akasa duk take maganganun nan ahankali yace "ina kwana Mummy" "ina kwana Waleed, ya karfin jiki? Allah yabaka lpy kaji, Allah yasa kaffara ne sannu" gyada matakai yayi suka shiga gaisawa da Mom sunama juna barka, karasawa gaban gadon yayi yana kallon Ilham data tsareshi da ido itama tana kallonshi tana mamakin abinda yasame shi haka, dan murmushi yamata ya shafa goshinta da hannunshi saida ta lumshe ido tabude su ahankali ta kalleshi, murya chan kasa yace "thanks for giving me a baby khadija, Allah yamiki albarka" gyadamai kai tayi tareda mika hannunta takama lafiyayyen hannunshi tarike gam, cikin muryanta da baya fita sosai tace "what happen to you Babyna"? Baki yabude zaiyi magana Mom ta taho rikeda jaririn tace "wato agaban mu ake nuna mana sonkai ko kana nuna kafi damuwa da matarka kan yaronka dayazo duniya yauko" murmushi Mummy tayi ranta fess ganin Waleed naji da yarta. Mom tamikamai yaron tace "ga danka nan dauki abinka kaga yanda yay kama da abokin ka kuwa kaman yay kaki ya tofar" wani irin mummunan faduwa gaban Ilham yayi saikuma ta daure ta lumshe idanunta da sauri kaman wacce bacci ya sace, ahankali Waleed yasa hannunshi ya karbi yaron yana kallon fuskarshi sanan yazauna abakin gadon yana rikeda shi yana kallon fuskar jaririn dake bacci yana murmushi, ko Allah yasan cewan yanason Arham, so na domin Allah, Allah ya azurtashi da d'a amman sai yaron bai biyoshi ba bai biyo mahaifiyar shi ba saiya dauko kamannin amininshi hakan yasa yaji bazaima iya sakama yaron sunan mahaifinshi ba, dan da yace in namiji yahaifa zai sakamai sunan mahaifinshi but wanan da yaron ke kama da Arham dole Arham zai bama yaron kodan Arham yagane shibai rikeshi da komiba sanan har gobe har jibi shi dan uwanshi ne no matter what. Bakinshi ya daura kan goshin yaron ya sumbaci yaron yana murmushi sanan yama yaron huduba ya karbi dabinon dasuka sayo da zasuzo yatauna yabama yaron yabashi ruwan zamzam, yadago kanshi ya kalli Mom yace "Mom sunan d'ana Arham Waleed Warbai" shiru Mom tayi tana kallon Waleed din for few seconds itama Ilham saida tabude ido gabanta nafaduwa ko Waleed yagane ne saisa yabama yaron sunan Arham sosai ta birkice saikuma cikeda siyasa tace "d'ana yawani kama yayi kama da abokin ka saikuma kawani bashi sunan shi" karban yaron Mom tayi tace "Allah ya rayaka Arham, daidai nan aka bude kofa Ammi ce ta shigo yar aikinta abayanta da direba rikeda basket din abinci, tace "ku yakuri ai danaji ya'ta ta haihu kitchen na koma da kaina namata abincin da maijego yakamata taci, sassanunku now ina Dr da nurses din dasuka karbi haihuwan jikana kuga" tawuce tafita waje tana kwalama nurses da Dr kira, duk wanda yazo bashi bandir din yan dari biyar guda take zukuga yanda aka cika Mummy sai murmushi take, saida ta rabar da kudin tass sanan ta shigo dakin ta kalli Mummy Ilham tace "bakin ciki kikemin ne aminiyata bazaki tashi akan kujera na zauna na dauki jikana ba"? Kwashewa da dariya akayi, Mummy ta tashi daga kujeran tace "maida wukan dadin abin nidai kafin nayi wanan jikan naki nayi wasu balle amin yanga" zama Ammi tayi tace "yanga yanzu kika fara gani" all this maganganun ko Waleed dake zaune bata kalla ba, saisa ma bataje gadon ta duba Ilham ba sabida yana wurin, ahankali Mom ta taho rikeda Arham junior sanan tamikama Ammi shi ahankali tace "ga Arham Waleed Warbai, Arham karami" Mom tai maganan tana kallon fuskarta kaman yanda itama Ammi tadago tana kallon fuskar Mom kafin ahankali tadaura fuskarta kan yaron, shiru tayi ganin yaron kaman Arham yay kaki, dudda yaron jariri ne but kamannin was so obvious da kana gani zaka gane da Arham yake kama, gabaki daya Ammi jitayi duk wanan farin cikin da murnan nan da rawan jikin datake yi na zatazo taga jikanta yakoma ciki, abinda ma yafi bata abin shine sunan dataji Waleed yasamai, kuma tai alkawari bazata sake shiga rayuwan shiba kaman yanda yafadi, so yasaka sunan abokinshi ma danshi danyaci mata mutunci itakuma bazata cemai komiba ya kyauta, murmushi kawai tayi tace "Allah rayaka Ar.....an jikalle" tafadi ahankali danta kasa kiran sunan Arham din, bude kofa akayi Baban Ilham ya shigo ciki yana ganin Waleed yace "assha, sannu son wanan daurin asibiti ai saikafi shekara baka warkewa tashi muje nakaika wajen wani mai dauri yana maka zaka warke cikin sati tashi muje" yay maganan yana kallon Waleed tashi yayi ahankali yabita gaban Ammi da kanta kekan jaririn, suka wuce suka fita, a mota baban Ilham ya daukeshi sai janshi yake da hira amman baya wani iya amsawa da kyau dan nauyin mutumin yakeji, agaban wani gida yaga sunyi parkin, fitowa sukayi baban Ilham yace "muje" shiga sukayi har wani dankareren falo inda wani mutumi ke zaune, Baban Ilham yace "Barka da rana malam, ga dana nan ya karye akafada munzo agyaramai" tashi baban yayi yazo yadaura hannunshi kan wajen saida Waleed ya yatsine fuska sabida zafi, Baban yace "ba karaya bace kashi ce ta goce ina gyarawa yanzu shikenan" da sauri Baban Ilham yace "kagani ko babu abinda asibiti suka iya indai kan dauri ne, yace Baba ayi mun gode" kwalama wasu maza kira Baba yayi, Waleed yaga wasu karfafan maza su kusan shidda sun shigo, hannu Baba yasa ya warware daurin sanan aka rike Waleed din, addu'a Baba yayi yatofa kan kafadar sanan yakai hannunshi kan wajen yafar kokarin saita kashin sosai Waleed yaso yadaure dayaga azaban ba nan bane yafara kokarin kwace kanshi amman ko motsi baya iyayi, da azaba yay azaba kuka yafara kaman zai mutu Baban Ilham sai sannu yakemai kusan awa daya aka dauka a hannun sanan baban ya gyara tsaf aka sakeshi da sauri yasa hannu yana share hawayen Baban Ilham sai sannu yakemai, magani Baba ya shafamai akafadar yace "ka warke baka bukatan wani dauri kuma angama" kudi Baban Ilham yaciro mai yawa yabiya mai sanan suka tafi. Duk suna zaune adakin Dr ta shigo ta duba Ilham sanan tabasu sallama tawuce tafita, ahankali Mummy tace "aminiya natafi da ita gida tai jego ne?" ada Ammi tai alkawari bazata je jegon gidaba amman sai kawai taji gwara sun tafi, gyama Mummy kai tayi tace "eh kuwuce kuma a kulamin da matan d'a da jika da kyau, suna arba'in zanzo na kwashi abuna wlh" duk akai dariya Mummy tace "nina nafi kowa sanin bala'in ki ai bazanyi wasa ba yallabiya" tai maganan tana kallon kofa ganin anbude Baba ne da Waleed da idanunshi sukai jajir da sauri Mom tai wajen Waleed din tace "sannu Dan Yaro an gyara" gyadamata kai yayi, Baba yace "bama karaya bace ashe gocewar kashi ne yanzu an gyara an shafamai magani, Allah yabashi lpy" ahankali Mom tace "angode Alhaji" Mummy tace "Allah baka lpy" itadai Ammi tai kaman bataji su ba, Mummy ne tace "Alhaji an sallamemu mutafi dasu gida, agida zatai jego" da sauri Baba yace "to bari nakai kayan mota" daukan kaya yashiga yi Waleed yaje zai tayashi da sauri Baba yace "kaga jeka zauna kaida hannu ba lafiya ne zakadau abu jeka huta" yay maganan yana fita, ganin haka yasa Mom ta shiga tayashi suka kwashe komi sukakai mota, sanan Waleed yadau hijab yabama Ilham tasaka ahankali yace "test me all that you need zan aiko miki dashi" murmushi tayi ya gyadamai kai ganin yana wani ji da ita kodan ta haifamai d'a ne, kofa yabude mata tafita suka jera atare tana tafiya ahankali har motar Baba ta shiga ta zauna sanan ya matsa ganin Ammi tazo baby ta shiga ta bama Mummy sanan suka rufe musu motar suka tafi Ammi tajuya tai motar ta ta shige direba yajata banda Waleed daya tsaya chak awajen, ahankali Mom tace "mutafi" daga kafa yayi yawuce ya shiga motar ta suka tafi, gida sukaje yana fitowa flat dinshi yaje kwanciya kawai yayi, yaciro wayarshi number Arham yakira amman harta gama ringing bai dauka ba, 3 miss calls yamai ganin bai dauka ba yasa yamai message. _"Hey blood, I called no answer I guess you are still angry with me, I called nafada maka Khadija ta haihu, an sami baby boy, yaron yay kama dakai sosai blood, and do you know what's even} great? Yaci sunanka, sunanshi Arham Waleed Warbai, blood you mean alot to me, u make my life colourful, I am sorry idan maganan dana maka jiya kajita somehow I was just trying to know what you've been up to lately, and I am also sorry akan abinda Ammi na tamaka please forgive us, take care, anjima zan shigo_" Yaturamai sakon tareda lumshe ido bacci na saceshi kafin baccin yay nasaran daukeshi. [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 💫💫_*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 ✍️ M SHAKUR 3️⃣2️⃣ & 3️⃣3️⃣ END OF FREE PAGE Wuraren karfe biyun rana ya farka, sosai yaji karfin jikinshi kawai gajiya yakeji bawani abuba, tashi yayi dagakan gadon yaje gaban madubi ya tsaya ya kalli kwayar idanunshi na dama ganin har yanzu akwai jini aciki yasa yabar gaban madubin yana tunanin inya fita anjima zai tsaya a pharmacy yasai maganin dazai saka jinin idanun ya washe, bathroom ya shiga, wanka yayi yasake yin brush sanan yafito, wardrobe dinshi yaje yadauko wasu native, farin yadi ne mai taushi da akamai jumper yasaka sanan yadau turare yafeshe kanshi dashi, dadduma yahau yay sallan azahar sanan ya zira takalmi bayan yadauki wallet dinshi yafito, side din Ammi yayi gabanshi nafaduwa, ahankali yabude kofar ya shiga hada ido yayi da Ammi dake zaune kan dogon kujera hannunta rikeda remote ko taji zai shigo ajikinta ne oho dayasa take kallon kofar oho, suna hada ido ta ijiye remote din ta tashi daga kan kujeran da sauri ya shigo dakin yamaida kofan yarufe yace "Ammi, Ammi please wait" sama Ammi tayi da sauri yabita kafin yakai harta shige dakinta tarufe da key dan bamata son ya shigo, tsayawa jikin kofar yayi yay shiru, yakai kusan 5min ahaka sanan yace "Ammi please listen to me, kiyakuri kinji please Ammi na" yay maganan ahankali yana knocking kofarta yakai kusan 10min ahaka awurn ganin bamata da niyyan bude kofan yasa yawuce ya sauka kasa, dinning yaje yazauna sabida shegen yunwa yakeji, warmer yabubbude, tuwon shinkafa yagani da vegetable soup, zubawa yayi baima wani iyaci da yawaba yasha ruwa yamike tsaye key motar Ammi dake kan centre table yadauka yawuce yafita, motar ta ya shiga ya zauna sanan yaciro wayarshi ganin har lokacin Arham baimai reply din message dinshi ba yasa yatada motar direba yabude mai yawuce yafita daga gidan. Agaban gidansu Arham yay parking motarshi yabude yafito yatura gate ya shiga gidan, babu kowa a tsakar gidan, sallama yayi yabude kofa ya shiga falon Mama ce ta amsa mai ahankali, saikuma tasaki murmushi tace "Waleed kaida bakaji sauki bane ba kafito? Ya karfin jikin? Maman ka takirani ta sanar dani abin farin cikin daya samemu ubangiji Allah ya raya, ya dayyaba, ya sunan yaron ne"? Murmushi yayi yace "sunanshi Arham Mama" wani iri Mama taji jikinta yay sanyi, sanyin ma karara hakan yasa tama kasa magana, lurada yanayin ta yasa Waleed yace "Mama ina Arham yana nan"? Cikin dan fushi tace "ohon mai rabona dasa Arham a idanuna kwana uku kenan yau" mikewa da sauri Waleed yayi yay corridor falon shiga yayi direct yay gaban dakin Arham, knocking kofar yayi yakirashi. "blood" jin shiru yasa yatura kofar ahankali ya shiga cikin dakin, dakin babu haske sai uban duhu, ahankali yamika hannunshi ya kunna switch hakan yasa dakin yya haske, Arham ya hango kwance kan gado bai lulluba ba dagashi sai gajeren wando fuskarshi ta kumbura suntum tsabagen dukan dayaci, jikinshi duk tabon ciwo dawani irin sauri Waleed yay gadon yace "subhallahi blood who did this to you eh? Waya maka haka"? Yay maganan yana dago Arham zaune, tashi zaune Arham yayi yana wani irin kallon Waleed din da sauri Waleed ya sauka yay bayinshi, ruwan zafi ya dauko yajefa towel ciki yazo yazauna akan gadon cikeda tausayi ya matso towel din kaman zaiyi kuka yakai kan fuskarshi yana dannamai yace "blood am so sorry, am ashamed of abinda Ammi na tasa aka maka, look what they did to you, this people are heartless, sorry blood" yay maganan yana gaggasamai, ijiye ruwan akasa Waleed yayi bayan yagama yasauka daga kan gadon yanabin dakin dayay kacha kacha da kallo yace "kasha any medication, kaci abinci?" dudduba dakin yayi ganin baiga maganin anything ba yasa yadau ruwan yakai bayi yafito sanan yadawo kan gadon, hannunshi yadaura kan kafadar Arham yana kallonshi kaman yanda Arham din ke kallonshi, ahankali yace "talk to me blood meke maka ciwo eh? Sanan wani abinci zakaci let me go out and get it for you, kafada min please ina da ina ke maka ciwo mow"? Wani irin kallo Arham kemai kafin ahankali yakai hannunshi ya kabar da hannun Waleed daga kan kafadarshi yace "wato halinka Waleed naban mamaki" ahankali Waleed na kallonshi yace "halina blood kaman ya"? Dan murmushi Arham yayi yakai hannunshi ya share fuskarshi dahar lokacin lema leman ruwan da Waleed u gasamai jiki kekai yace "kaida uwarka kunsan polisawa sunzo sun kamani sunmin bugun mahangurba shine yanzu zakaso kana wani rawan jiki kana bani kulawa kaman bakasan hakan yafaru ba" sassauta murya Waleed yayi ahankali yace "blood listen to me, I have no reasons to lie to you koda chan banmaka karyaba yanzu ne zan maka karya, believe me bansan Ammi tasa amaka abu makamancin hakaba, a lokacin danasani saida nasa aka janye aka sakeka, blood you are my only friend danai basing life dina dashi in this world, bazan taba hurting nakaba no matter what, besides you are morethan a friend to me, you are my blood Arham" tabe baki Arham yayi sanan ya nunashi da yatsa yace "ku masu kudin nan feels zaku iya duk yanda kukaga dama aduk lokacin dakuka so, zaku iya duk yanda kuka so aduk lokacin dakukaga dama, listen to me Waleed wlh zan gwadama aduniyan nan dudda uban kudinga, kadaiga mahaifinka nada kampany akasan waje dake gina boat dawasu kampanoni, mahaifiyarka nada kampany da business da dama ko, amman wlh zan nuna maka duk wayan nan kudin da dukiyan dakuka tara bazai taimakeka da komiba saika gane kurinka Waleed" shiru Waleed yayi yana kallon idanun Arham, all he could see was hatred, tsantsan tsana kawai yake gani a kwayar idanun Arham, wani iri yaji yanaji kaman zaiyi kuka saikuma yahana kanshi, ahankali yana kallon Arham din yace "Arham all wanan fadan da maganganun is it akan kawai natambayeka ina kake kai kudin ka? But why do I feel kaman there's more to this case, blood na kalli idanunka abu daya kawai nake gani shine tsantsan tsana ta, blood mena maka? Menataba maka? What have I done to you please kafadi mini watakila bansani ba please tell me kaji my friend" da sauri Arham yanuna kanshi yace "friend? Nine friend dinka Waleed? I can never be a friend to rich kids sabida all they know is sumaka ihu, suyi controlling naka, suyi matching naka and step your your neck aduk lokacin dasukaga dama, Waleed zaka iya tuna how many times kakemin ihu kakemin tsawa in your office kanamin fada"? Wani irin hawaye ne Waleed yaji sun gangaromai shaaarr, hannu Arham yanunamai yace "ba kuka nace kamin ba tambayanka nayi, kasan how many times kakemin ihu aka a office"? Girgiza mai kai Waleed yayi ahankali kafin yafuzar da iska yasa hannu ya share idanunshi tass sanan yanisa yace "I never meant all those shout, badan cin mutunci kowani abubane yasa nayi hakaba, Blood kasanni sama da kowa, and you know how passionate I am towards my work at the orphanage, idan yazo takan orphanage dina ne banson wasa kawai strictly work saisa I do all those to you sabida kai aikin da yakamata kayi, but tunda har ahaka kadauki abun ka fassara am sorry for that too I didn't do it because am rich or whatever I do it cus I feel is my own way of motivating my staff to do more, to perform better, idan akazo kan human resources management akwai two ways of motivating a staff, akwai positive motivation and negative motivation, I guess mine was the negative one but kayakuri" ya karashe maganan ahankali muryanshi tayi sanyi sosai, tabe baki Arham yayi yace "orphanage orphanage orphanage, staff, staff, staff, Mr, Dr. Waleed Warbai the chief CEO of Warbai orphanage home and home of the disables how does the name sound"? Yatambayi Waleed dake kallonshi cikin yanayi na isgilanci sanan yaydan murmushi yace "I will make you a promise yau dinan akuma gabanka, Waleed kome kaci sai Arham yaci! Waleed kome kasaka sai Arham yasaka! Waleed kome kahau sai Arham yahau! Waleed kowani matsayi ka taka sai Arham yataka shima! Sai last thing dazan fada maka is over between us" da sauri Waleed ya kallai, gyadamai kai Arham yayi yace "yes is over tsakanina dakai Dr Waleed Warbai, we should go our separate ways, yanzun haka danake maka magana my resignation letter na gidan marayun ka duk lokacin dakaje za'a baka, ka kama gabanka nakama gabana, daidai da silebiyar dinka karka sake bama Mahaifiyata, Arham bai sanka ba bai san dazaman kaba kaima do me a favour ka kwatanta hakan, is over we are not friends we are not friends, please katashi kafitar min daga daki kabar min gida and yau yakasance rana ta karshe dazaka kara zuwa gidanmu" kasa koda motsi Waleed yayi daga inda yake, hannu Arham yadaga yanuna mai kofar dakinshi yace "out, I said out" yadaka mai tsawa irin na cin mutuncin nan yace "indai kai ba maye bane katashi kafitar min daga daki mara zuciya kawai dolo" sosai Waleed ke kallonshi kafin ahankali yasauka daga kan gadon idanunshi sunyi ja mugun ja yabude kofa ahankali Mama yagani gaban kofan, murmushin dole ya kakalo yace "sai anjima Mama" baima jira amsanta ba yawuce yafita da sauri yya wajen gate yafita yabar gidan ya shiga motarshi yaja dawani irin gudu sanan yabar anguwan. Bin bayan Waleed Mama tayi da kallo taji gabaki dayan maganan su sabida ita kanta tadamu tun ranan batada Arham a idoba sabida fushin datake yi dashi yasa taki zuwa tadubashi, hakan yasa Waleed na shiga dakin tabiyo bayanshi. Tura kofan dakin tayi ta shiga, hada ido tayi da Arham da yana ganinta ya saukar da kanshi kasa, ahankali dawata irin murya dake rawa sosai Mama tace "Arham Waleed kama wanan cin mutuncin, Arham anya nina haifeka kuwa? Anya nonon nan nawa kasha"? Takama nonon ta tanunamai, saikuma tafashe da kuka sosai dan her heart is so heavy tace "wlh wlh da'ace a asibiti na haifeka Arham da na rantse maka da Allah dayau dinnan sainace bakaine danda nahaifa ba, anchanza mini kai a asibiti, amman agida na haifeka dagani sai unguwar zoma" tafashe da kuka sosai, sanan ta share idanunta tass da bakin zaninta tace "wlh albasa batai halin ruwa ba, babu ta inda ka gado malam mahaifinka, baban ka malami ne, wayan nan manya manyan malaman da ayau a Abuja dasu akeji duk ubanka ya koyarda su Arham, Arham ubanka malami ne, kakanka malami ne, amman kaiko Arham shaidanin yaro ne" tafadi haka tsabagen yanda zuciyarta ke tafarfasa, cikin ihu da fada da kunan rai tace "Arham wai shinko katuna waye Waleed koko kamanta ne?" tamai tambayan tana kallonshi sanan tace "Arham kanajin tsoron Allah kuwa? Arham kana kokarin ka tabbatar da cewan mutane kadau mutum daga rana ka maidashi inuwa shi saiya maida kai rana, Arham kai butulu ne eh? Yanzu inda ace zaka tashi kaje sip dinan naka zan rantse da Allah nakuma kara idan akwai kayanka daka saya da kudinka basu wuce kala biyu, Arham gabaki dayan sitiranka Waleed kisiya maka, Arham yaron nan nasonka har kuka naji yana maka kanamai ihu kana cewa ba kuka kace yamaka ba, matarshi ta haihu yarada ma danshi sunanka Arham duk baka ganin abubuwan nan? Da ace Waleed bai tsamoka daga talauci dahar yau ayaba kake saidawa, Arham Arham Arham" Mama tama rasa maizata cemai saikuma tafashe da kuka tace "kaga yanda idanun yaron nan suka taru da jini dukan dakamai? Amman bai rikeka ba ya tattako yazo wajenka, bari kaji bazan taba bari ka wulakanta mai sonka ba wlh, bazan taba bari ka wulakanta wanda ya chanza mana nidakai rayuwa ba, Arham bazan taba bari ka wulakanta Waleed ba domin ka wulakanta yaron nan kadauka nika wulakanta aduniyan nan, dan haka dau wayar ka ka kirashi agabana kasa handsfree dan naji, kabashi hakuri sanan kafadimai duk abubuwan daka fadamishi wasa kake kanajina "! Mama ta dakamai tsawa, dago idanunshi Arham yayi ya kalli Mama yace "Mama kiyakuri amman wlh ni bazan kirashi ba, kuma kidena cewa ya taimake mu babu abinda Waleed yamana Allah ne yataimake mu kuma shine yamana komi wlh, daman shi Allah haka yake abinshi inya tashi taimaka maka saiya nemo wani ya taimaka maka ya hanyar shi, tunda ai shi Allah bazai sakko kasa yamika maka kudi da hannunshi ba yace gashi Arham saidai yay amfani dawani, dan haka wlh Mama ni Allah ne yamin komi babu wani mahaluki daya isa yataimaken, Shidin banzan shi, kudin shi na banza meyake dashi, shi idan ma yaga asalin masu kudi guduwa zaiyi yaboye wlh irinsu Otedola, Zuckerberg da sauransu, shidin me shidin banzan shi, dan ubanshi nada kampani a kasan waje yake mana kapapa yana daga mana kafada wlh bazan kirashi ba" yay maganan ranshi duk abace, rungume hannu Mama tai aciki tana kallon Arham kaman tasami TV, ahankali Mama tace "Arham Annabi yace a kullum mudinga kallon nakasa damu bana sama damu ba hakan zaisa mungode ma Allah da kyau, Arham batun yau nake karantan wani abu tattare dakaiba amman yau Allah ya bayyanamjn abin gabaki dayanta Hassada kakema Waleed" da sauri Arham yana daga murya yace "shi awa zan tsaya inamai hassada Mama? Ubanme yakeda shi? Allah ya kyauta kafin na ganshi naga masu kudi dubu ni mama kima dena min maganan wani Waleed banson jinta, dashi da wanan matsiyaciyar uwarnan nas...." bai karasa maganan ba Mama taxuba ma bakinshi mari, sanan tacire slippas din kafarta tahau dukanshi ta ko'ina tace "Arham kaci uwaka, bani na haifeka ba, wanan bakin halin naka da bakar zuciya uwarka da ubanka basu dashi, wayanda suka taimake ka kake zagi eh, kai wani irin butulu ne, Arham ni kake so kabama kunya aduniyan nan" dudda dukanshi take bakinshi kin mutuwa yayi yace "ki kasheni Mama, dama batun yau nasan kinfison Waleed kan danda kika haifa ba, Waleed nada kudi, yasai miki gida da mota, gaki da generator ga solar, ga kayan abinci ga kudin kashe wa ba dole ba, Mama ki kasheni sabida Waleed, badai danni banda kudiba banda gidan marayu ba saisa bakisona nima ba zakiga abinda zai faru Mama kicigaba da dukana har saina daina numfashi, badai kowa dukana yake akan Waleed dan gata ba, ajebota kucigaba nikuma namuku alkawarin sainaima Waleed abinda dukanku bazaku iya taimakon shiba wlh, wlh kuwan, kiyita dukan" yakara mika mata kanshi dantaji dadin duka, dukanshi Mama tayi har saida Sadiya taji ta shigo da gudu taja Mama baya dake haki kaman zata mutu tace "sadiya kibarni na kashe yaron nan nahuta dan ba da'na bane, Sadiya kibarni, Arham nason yacimin mutunci, Sadiya Arham nason ya kunyatani aduniya, dawani idanu yakeson na kalli mutanen nan dasuka mana komi a rayuwa eh" tafashe da kuka, rungumeta sadiya tayi itama tahau kuka tace "Mama yakuri kidena kuka dan Allah" cikin wani irin fushi Arham ya tashi ya finciki key motarshi yafita daga dakin ya barsu awajen idanunshi sunyi jajir. Waleed rasa inda zashima yaji dadi aranshi yayi kirjinshi sai wani irin mugun tafarfasa yake, baisan ya akayi ba yadaiga yazo gidan marayun shi, parking motarshi yayi yafito sai gaisheshi ake yama kasa amsasu da sauri da sauri yake tafiya har zuwa cikin asibitin shi, direct ward din da Widad ke kwance yake, bude kofar ahankali Ya shiga maida kofar yayi yarufe yana kallonta ganin bacci take, direct yawuce gadon da sauri zama yayi kan plastic chair gaban gadon kawai yakifa kanshi kan gadon kukan dake cinshi tun adakin Arham ya shiga sakinshi awajen ahankali yana sheshek, maganganun Arham gets to him sosai, sun shigeshi was he that bad kaman yanda Arham ya suffanta shi? Was he?. Kaman amafarki taji kaman ana kuka ahankali wanda sautinshi ke kaiwa har kokon kirjinta, bude idanunta tayi kaman wacce ta firgita ta kalli ko'ina kafin ta kalli gefenta, kan mutum tagani kife kan gadon, gashin kan nawani irin shining sunyi sili sili tsabagen gyara dasuka ji, dudda bataga fuskarshi ba amman tagane mutumin nanne bargon jikinta tayaye da sauri taja jikinta ahankali ta tashi tazauna tana kallonshi tai raurau da ido, ahankali tadaga hannunta ahankali tadaura akanshi, jin soft hannu dake dauke da dan danshi danshin zufa akan sumanshi yasa yadago kanshi ya kalleta da jajayen idanunshi da hawaye yacikasu sosai, wani irin kallonshi take hankalinta yatashi sosai ganin yana kuka ahankali yakai hannunta kan fuskarshi sharemai hawayen tayi da sauri tana girgizamai kai, jiyayi zuciyarsshi tawani irin tsinke baisan lokacin daya tashi daga kan kujeran yazauna abakin gadon ya rungume cikinta tsam ba, fuskarshi nakan cikinta yasaki kuka ahankali cikin harshen turenci yace "Saheeba baki sanni ba, dudda duka yanzu 10month kikayi da sanina, dan zaman dakikayi tareda ni please ki gayamin am I a bad person? I know I makes different decisions, but kowani decision zan dauka abune dazai kawo cigaba dakuma raya wanan gidan marayun, you know ana yawan cewa breakup masoya ne kawai irin couples haka ke breakup ba'asan cewa akwai friendship breakup ba and the shit hurts badly" yasaki kuka sosai akan cikinta dayasa tahau girgiza mai kai tana bubbuga kanshi alamun yay shiru tana kokarin magana takasa but kana ganinta kasan ta mugun damu, ahankali yace "I am so saddd, I don't know who to talk to, banma san mesa nazo wajenki ba bayan bazama kingane menake cewaba, but crying ajikinshi anyway makes me feel better, am sorry natashe ki kinji" yay maganan yana dagowa daga jikinta tareda tashi daga kan gadon yana juyawa da sauri batare dayabari sun hada idoba, hannunshi yaji anrike gam hakan yasa ya tsaya chak, dirkowa tayi dagakan gadon tana rikeda hannunshi ta zagayo tagaban shi ahankali ta tsaya tana kallonshi, gani yayi itama idanunta sunyi ja, ahankali tabude bakinta tana kallonshi takai almost 20sec tana kokarin iya maganan dazatayi sanan cikin yar siriruwan muryanta tace "you aren't a bad person" tai maganan tana kara kai hannunta yakama dayan hannunshi tarike gam, sanan ta kallai tace "you are a goodman" tai murmushi dayasa hawayen idanunta suka zubo, saikuma ta washemai baki tace "and I love you" tasakin mai wani heart melting murmushi dayasa all her dimples suka lotsa, wani irin ajiyan zuciya yasauke yasan bamatasan metake cewaba, sanan this is not the first time ake cemai I love you besides Ilham tasha fadimai kalman nan countless time but yau da Saheeba tafadi saida heart dinshi yakusan skipping out, like he felt the words har cikin diddigan kashin jikinshi sosai yay nisa yana tunani yaji an fizge hannunshi, firgigit ya farka yaga ita ke janshi, zaunar dashi tayi akan gado ga mamakin shi daiyaga tasa hannayenta akan kafadarshi ta turashi ya kwanta tana murmushi, samun kanshi yayi da kwanciya yana wani iri kallon yanda takemai murmushi kaman yau yafara ganinta, stethoscope din dayake dauka kullum dake kan bed drawer dinta inya shigo dubata ta dauka ta makala a kunnenta tsaf tana murmushi sanan tazo bakin gadon tana ware Big lulu eyes dinta ta daura hannu kan lips dinta tana kallonshi alamun yamata shiru sanan takai bakin stethoscope din ta daura kan saman kirjinshi ta saman riga lumshe ido yayi da sauri yana sauke wata nauyayyan ijiyan zuciya jin hannunta kan jikinshi, ita kawai she is doing it jokingly ne but jin beat din kirjinshi acikin kunnuwan ta yasa tawani irin kwalalo ido a tsorace ta fizgo daga kunnenta ya yar, dan dariya yayi yatashi yazauna ahankali itama dariya tayi saikuma ta makemai kafada ta taho dagudu tawani fada jikinshi ta daure hannayenta tabayanshi tana murmushi, wani irin natsuwa ne yaji ya shige shi, lumshe ido yayi tareda manna hancin shi cikin gashinta, murya chan kasan makoshi yace "I love you Saheeba". _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ _Zaku cigaba da ganin update , cikin satin dazamu shiga in shaa Allah, ONE LOVE FANMILY_ [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 3️⃣4️⃣ *This novel na kudi ne, idan kika karanta baki biya ba banyafe ba🤷🏻‍♀️* _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ Dagokanta tayi da sauri ta kalli fuskarshi tana kwalalomai idanunta irin meyace dinan dan batasan meyace ba, taji yay magana but bataji meyace ba dan ahankali yay maganan, har lokacin hannayenta kulle abayanshi tana kara kallonshi, manyan kwayoyin idanunta farare tass ya kalla dayaji sunsa jikinshi ya soma mutuwa, ahankali yakai yatsanshi yadan dungure matakai yace "bazan maimaita abinda nace dinba kina kallona da manyan idanunki da basu dade da dawowa daidai ba" washe mai baki tayi kaman tasan maiyace dan hausa yamata, tsayawa yayi yana kallon set din white hakoranta yace "lemme go" yay maganan yana kwance hannunta dake bayanshi yadawo dasu gaba, yamike tsaye da sauri, kaman zatai kuka ta rikemai hannu karbe hannunshi yayi da sauri ahankali kaman mai shirin bata tsoro yace "stop touching me anyhow Saheeba ba kyau" Tashi yayi ahankali kawai jitayi yadagata da duka hannunshi ya dauketa kaman yanda ake daukan kananun yara da sauri ta zaro idanunta waje tana kyalkyata dariya, murmushi shima yayi anytime ta kyalkyace dariya sound din dariyan yafito fito fili abin na burgeshi, zaunar da ita kan gadon yayi yace "mara kiba kawai, bari naje naduba maiya kamata kiyi having for lunch zansa akawo miki okay" gyadamai kai tayi tace "okay" tai maganan kaman yanda yamata, juyawa yayi ahankali yafara tafiya itakuma tabishi da kallo, har wajen kofa yakai sanan yasa hannunshi yabude kofan yajuyo ya zuba mata idanu she really makes his day, he was so sad da abinda yahada shi da Arham but yana zuwa wurinta kaman tasaka spoon ta kankaromai fushin, shegen murmushin datakemai yasa da sauri yasakai yafice dan murmushin ta nasa yaji zuciyarshi kaman zata tarwatse Sosai yan gidan marayu shi keta gaidashi amsasu yakeyi ahankali haryakai wajen motarshi budewa yayi ya shige yana shirin tada motar wani security yazo da gudu ta window yabudemai envelope din yace "Dr an aikoma da sakon nan dazu" mika hannu yayi ya karba yace "thank you" juyawa yayi yakoma shikuma ya yage envelope din yabude takardan yaga resignation later Arham ne hakan yasa yama ajiye batare daya karanta content din cikiba dan baiso yanda yaji Allah ya yayemai bakin cikin nan wani abu yakara tunamai dashi.❤**** _*Washe gari*_ Zaune yake a office dinshi ga mac book dinshi a gabanshi, ayyuka ne dashi dayawa dan rabonshi da aiki tun fadansu da Arham a office ga system din a gabanshi but he couldn't do a thing, yakasa daina tunanin Arham, tunda ya shigo yafita waje yakai sau 8 yana duba inda Arham ke parking motarshi da kofar office dinshi yaga in abude alamun yazo amman saiyaga bai zoba. Yana zaune akan kujeran shi yayi nisa atunanin from afar yaji karan sardine, jin karan yay yawa yasa ya tashi daga kan kujeran dayake kai yajeta wajen window office din ya tsaya, hannunshi yasa ya bude hadadden curtain din jikin window dan so yake yaga bakin dasuka shigo orphanage din da wanan serene din dako government officials basa shigomai da ita, kara yacika ko'ina saikace zasuje kama barawo. Mota biyune bakake dasukayo comboy jeeps, sai marcopolo guda 5 suka biyo titin gidan marayun ajere, parking sukayi a inda yakamata suyi parking, aka bude bayan motar da gaba government officials guda hudu suka fito sun sha bakaken suit suka wuce straight to office na MD Waleed's office. He was still standing on the window trying to figure out what those marcapolo are meant for danba na gidan marayun shi bane because it was literally the first time inma government officials ne suke zuwa da marcapolo, faduwa yaji gabanshi yayi hakanan, yana cikin yan tunane tunanen yaji ana knocking office dinshi❤️. Kafin ma ya amsa Baba Mani yabude kofa ya shigo cikeda girmamawa yace "likita kayi baki ace masu su shigo? Sunce wai daga ministry suke wai wajenka sukazo" anatse ya karaso yazauna akan kujeranshi yana gyara zama sanan yace " Let them in Baba Mani" fita Baba Mani yayi da sauri within a blink of an eye suka shigo dukansu, mikewa Waleed yayi from his sit ya basu hannu wearing a smile. Bayan sungama exchanging pleasantries, daya daga cikinsu wanda shine Babban su yace "Mr. Dr. Waleed Warbai, nasan bakasan fuskokin muba, we are from the ministry, Ministry of Women Affairs and Social Development, the ministry sent us here to shut down your orphanage based on some facts not yet clear to us untill investigation is fully done" wani irin faduwa gaban Waleed yayi amman yadake yacigaba da sauraronsu mutumin ya cigaba. "sanan anbamu order akan to move all the orphans and disables, duka yaran gidan nan tatas to a safer orphanage, Better still, you are given 30mint to move any important personal document you will like to go with naka not anything related to this orphanage before relocation and shutting down commence." mutumin yay maganan yana kara gyara zaman agogon hannunshi yana duba daganan zuwa 30min lokaci nawa yaragema Waleed din, Waleed wani mutuwar zaune yayi because he don't know where all this is coming from kaman ya shutting down orphanage dinshi dat he dedicate all his life to, moving yaranshi zuwa another orphanage ana bashi 30min, what's all this? Is he dreaming ne kome, no notice nothing nothing kawai yaga mutane kaman daga sama, he was speechless that he was just starring at them like a moron yadau kyakkyawan mintina goma ahaka sanan ya sauke ijiyan zuciya sanan azuxiyarshi yafurta. "Innalillahi wa innailaihi raji'un" wani karfi ne yaji yazomai hakan yasa yace "On what basis, or on what account zakuyi shutting down gidan marayu na and moving the orphans out again, why all this, please sir mai kake cewa ne seriously nakasa fahimtan ka" dan gyaran murya mutumin yayi yace "Well Mr Waleed akwai basis dayawa dayasa kaji wanan hukuncin daga sama haka, you have been accused of RAPE(FYADE)" wani irin zabura Waleed yayi yamike tsaye yana kallon mutumin, mutumin yacigaba. "kayi raping yara mata har guda takwas agidan nan is it because kagansu helpless kaine komi nasu saisa make taking advantage of kananun yaran nan, you've accused of CHILDREN TRAFFICKING, kana saida yara ana fitar dasu daga kasa, saikuma kadena fada mana bamu account of any new member da aka samu agidan marayun, MALTREATMENT, yaran gidan nan ana basu bakar wuya an many more, this are just the core ones, saisa gwamnati tabada order immediate evacuation of duka yaran gidan marayun nan to a safer orphanage sanan ayi shutting orphanage naka down till further notice for proper investigation".❤[11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 3️⃣5️⃣ & 3️⃣6️⃣ *This novel na kudi ne, idan kika karanta baki biya ba banyafe ba🤷🏻‍♀️* _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ ya kasa kallon mutumin kawai yake, yakasa yarda cewan he just heard cewan za'a rufe gidan marayun shi da he work so hard for, he dedicated his life for this humanity work, this is the only thing yakema mahaifinshi dan ladan yakai gareshi kabari how could they just shut his orphanage down kan wanan baseless accusation din sanan suyi moving all yaran gidan marayun to another orphanage, no no no please this is not happening to him dan Allah, wani irin rawa kirjinshi yafara da kyar ya daure ya natsar da kanshi yace "you can't just come to my orphanage kuyi accusing dina akan abubuwan I have no knowledge for with no evidence, dan on that basis your case is noll and void" yafadi ahankali yana komawa kan kujeran shi dan kafafunshi sun soma rawa sun kasa daukanshi, murmushi kawai sukayi dukkansu atare lokaci daya suna kallon Waleed din. Mika hannu babban su yayi ya karbi wani file from the other person nakusa dashi sanan yamika ma Waleed file din tare da cewa "you can go through it please, ciki zakaga hoton ka da baturai on several occasion tareda yaran gidan marayun which clearly shows yaran saida musu su kake dan yaran yanzu haka basa gidan marayun nan" da sauri Waleed ya kalli hotunan da baimasan lokacin da aka daukesu ba, hawaye ne suka xomai da sauri ya shanye hawayen yace "wayan nan baturan daka gani are my friends munyi makaranta tare a UK anytime dasuka zo Nigeria for vacation or business sukanzo wajena and pay a visit to my orphanage, wanan yaron dakake gani is called Hamis, he is dead, sikla ne, inada file dinshi and everthing I will never sell my children, is a lie" murmushi mutumin yayi yaciro wayanshi daga aljihun cikin rigan suit dinshi yadanyi yan danne danne sanan yamai playing voice note inda Waleed ke cema Arham ranan akan bazai fadima government zancen zuwan Widad ba, daidai iyanan maganan ya tsaya sanan mutumin yace "wanan shine evidence daya tabbatar mana da cewa ana kawo yara nan gidan baka sanar mana da zuwan su, kai kanka kasan u cannot deny cewa wanan muryanka ne dan muryanka ne Dr, let's go to the next" mutumin yasakemai playing wani voice note inda yara ke kuka sosai suna cewa Waleed yay raping nasu bayan yamusu dukun bala'i, wata harda cewa allura yamata sanan yacire kayanshi yahau kanta, at this point saida hawaye yazuboma Waleed da sauri ya ijiye hannayenshi kan table, shivering hannayenshi suka shiga yi sabida tashin hankali, ahankali yamika hannayenshi dake shivering yadauki file din dake rawa sosai a hannunshi kaman zai fado kasa tsabagen yanda hannunshi ke rawa, kufcewa file din yayima daga hannunshi yafadi kan table hakan yasa officials din suka mimmike tsaye babban su yace "we don't have all day, I advice you to cooperate inba hakaba akwai consequences, we are going outside zaka kira security all yaran gidan nan needs to come out cus we are moving them out to a safer home" yay maganan suka bude kofan office din suka fito, ganin sun fito basu ganshi ba yasa daya daga cikinsu yadawo cikin office din ya tarar dashi azaune kaman yanda suka fita suka barshi hakan yasa yace "Mr Waleed kaifa muke jira, stand up and accompany us to the hostel we need to comfirm the case of rape da'ake accusing dinka with da maltreatment and many more" mutuwar zaune Waleed yayi because lokaci daya kanshi became so dump that he could not even think straight anymore yakuma kasa tashi dagakan kujeran saida mutumin ya maimaita mishi maganan sanan ya iya tashi ya bisu. Kai tsaye hostel din mata sukayi suka tsaya agaban gate din hostel din, Mama Iyami ce tafito idanun Waleed kadai ta kalla tagane da matsala sabida yanda sukai jajir, ahankali Waleed da da kyar yake magana yace "call everybody Mama Iyami, kowa yafito waje" gyadamai kai kawai Mama Iyami tayi ta shige hostel dinsu, Baba Mani ne yazo Waleed yafadimai shima afito da kowa, kafin kaceme ancika filin gidan marayun makil da yara da manya ana hayaniya ga staff masu kulada yaran suma duk sun fito kowa dai yafito banda security dake gate danacikin asibiti. Gyaran murya babban cikinsu yayi yace "Good morning beautiful ladies, young children, and the gentlemen, as you all know we are the officials daga ministry muke, Ministry of Women Affairs and Social Development, turomu akayi, we are sent in here by the government to carry on some investigation on this orphanage inaso kubamu hadin kai karkuji tsoro sabida u all are safe hakkin mune mukula daku, munsami information from avery good source, labari yasami ministry dinmu akan you girls, yaran matan orphanage dinan, wato yan matan gidan marayun nan are being molested by Mr Waleed wato mai gidan marayun ku wanan!" yanuna musu Waleed in disgust, jikake wajen tsit kaman ruwa ya cinye kowa, mutumin yacigaba. "ku saurara there's absolutely no need to panic as we are here to save you girls, munzo mu ceci rayuwan kune, but bazamu wato we can't save you unless you help us to ease our work by raising your head so that we can identify who and who were molested by Mr Waleed, karkuji tsoro ko kiunyan kowa, inkun boye bazaku boyema Allah ba, ku kaddara mu dinan dauki ne Allah yaturo muku dan mu ceci rayukan ku, so ladies please raise your hands if you've ever been molested by Mr Waleed, inhar Dr Waleed yataba miki fyade, yay amfani dake koaina ne kawai kidaga hannu dan musan dake, I assure you all u are safe dan zama mu maida kowa wani gidan marayu ne so babu abinda zai iya muku kawai kudaga hannu" mutumin yay maganan cikin kwanciyar murya, ahankali wata yarinya ta daga hannunta nai suna Hassana sama saikuma tafashe da kuka ta duka kasa tarufe fuskarta da hijabi tace "Dr yasha min fyade har office dinshi ke kirana" tafashe da kuka da sauri watama ta daga hannu, a take yan mata takwas duk sukahau kuka kan cewa Waleed yamusu fyade kowacce da kalan labarinta Waleed nemar waje yayi ya zauna as his legs could no longer hold him yanda yagan student sun daga hannu, yaran da yakula dasu baijin sunma taba zuwa office dinshi ba amman yau suke daga hannu suna cewa yamusu fyade, daman haka shairi yake ajiki abinda bakasan hawaba bakasan sauka ba ace kayi tunda yaje in his life banda Ilham baitaba kwanciya da wata mace ba amman yau yaran dayamusu komi, da yake aiki morning and night tirelessly just to give him happiness and a proper life harsu takwas ke cewa ya musu fyade, daurewa yayi iya dariya yahana kanshi hawaye yahana kanshi kuka yadago kai yana kallon yan matan d'a har lokacin sunki hada ido dashi kuka suke kansu akasa. Mama Iyami datakasa hakuri ne maganan na cinta tawani irin daga murya tace "na rantse da Allah, na rantse da zatin ubangiji na, wlh wlh Waleed bazai taba iyama mace fyade ba, yarone Waleed natsasse da zan shaida ko a ina" da sauri Baba Mani yace "kuji tsoron Allah, wanda yamuku alkhairi bakwa mai shairi ba, sanan kutuna akwai ranan gobe kiyama, hakkin bawan Allah nan zai kamaku wlh, kuma Allah baya yafe hakkin wani saidai idan shine yace ya yafemaka, mesa zakumai shairi eh"? Kafin suyi magana wasu staff guda uku sukace. "komu nan mun taba kamashi da wasu dalibai a motarshi" juyowa Waleed yayi ya kallesu da sauri Baba Mani da Mama Iyami sukace karyane! Hayaniya ne ya kachame awurin Mama Iyami ta zubama staff din da yama Waleed shairi ta chakume shi tace "me yaron nan yamuku da zakumai shairi eh? Maiya muku maiya muku kukemai wanan kazafin?" chaaa wajen yadauki surutu, cikin fushi babban mutum din cikin officials din yace "silent!" shiru akayi duk aka juyo ana kallonshi sanan yace "direbans on the car" kunna motoci direban yayi, mutumin yace "yaran nan gabaki dayan ku kuwuce ku shiga mota, ministry yabada order akaiku a safer orphanage, staff duk wanda yabisu job offer dinku is intact, wayanda kuma are not interested can go, amman dai yaran kuwuce, kaikuma kuje kutaho da all yaran hospital, the whole orphanage should be evacuate, ko mahaluki daya baza'a bari ba, zamu kulle gidan we are shutting it down" ahankali Baba Mani da Mama Iyami suka tsaya abayan Waleed, Baba Mani yace "muba butulu bane, likita kadauki wanan amatsayin kaddara" Ahankali Nura shima yazo ya tsaya bayan Waleed yace "nayi imani da Allah sanan na yarda cewa ubangida bazai taba iya aikata wanan mummunan halin ba da abu akasa, na wuce 18yrs ko ayance inada yancin kaina inada ikon nace bazan bikuba kuma baku da yanda zakuyi dani so I stand with ubangida na dayamin komi" yay maganan yana dafa kafadar Waleed takowa shamsiyan dayakeso tazo ahankali tace "Allah zai sakama Teacher, na zauna gidan marayun nan ko bangaren mata baka taba shigowa kai kadai ba saida izinin Mama Iyami, sanan saita sanar damu cewa Dakta zai shigo mu gyara sanan zasu shigo tare yay kome yazoyi yagama duk tana tsaye tareda shi, Hassana, Rukayya, Farida, Hauwee, Bushira, Laila, Adama, Kabira, Razika kuji tsoron Allah, flat dinmu daya, daidai dasau daya bantaba ganin yanayinku ya chanza ba balle har adanganta shi da anmuku fyade, inkun gaji da gidan saiku tafi amman basaikun ma bawan Allah nan shairi b..... " "shut up there" babban cikinsu ya daka mata tsawa daidai lokacin antaho dasu Widad da kowa nacikin asibitin harda su nurses da Dr, mutumin yace "listen inhar kawuce ko kakai 18yrs you have the right to choose, ko kubimu akaiku safer orphanage kokuma kuyi gate kufita kuyi duk duniyan dakuka ga daman, as for this young folks dabasu kai matakin kansu ba they're all coming with us, now move to the car" yay maganan yana nuna musu marcopolo da aka bubbude, ahankali ake tafiya yara na shiga manya na shiga staff ma na shiga, mutumin ya juya ya kalli wayanda suka kawo daga asibiti yace "ku shiga mota, Dr kukai patient dinku mota" da sauri Dr yace "what's happening here" tsaki mutumin yaja ya kalli wanda ke kusadashi yace "sa yan asibiti cikin motan" kama yan asibitin ya shigayi yana kaisu mota Widad na tsaye tana zaro ido tana kallon kowa dan bata taba ganin mutane da yawa hakaba, kuka tasaki ahankali, mutumin nadawowa yazo zai kama hannunta wani irin wawan ihu ta kwara da saida Waleed yajishi har cikin kirjinshi mutanen wajen suka taushe kunnuwansu dan Widad akwai murya, tsaki mutumin yaja yace "are you stupid zaki fasamin dodon kunne ne let's go" makemai kafada tayi tana kuka sosai tana komawa baya tana kalle kalle, cikin fushi Mama Iyami tace "itama bazata biku ba ai tawuce 18yrz wanan so akyaleta" wani irin kallonta officials din sukayi ta daure fuska tawuce tai wurin Widad data makale abango tana kuka sosai, anatse Mama Iyami tace "ke baturiya ishuru nan ga oga chan je wajenshi tunda kema bakiso kibisu ki tsaya abayanshi, tai maganan tana mata pointing Waleed" bin hannun Mama Iyami tayi da kallo tana kuka, Waleed datagani zaune kanshi akasa yasa dawani irin gudu tai wajenshi tana zuwa batai wata wataba tafada kan jikinshi tasaki kuka tana nunamai officials din da hannu, tunda ya zauna akasa dazu yakasa dago kanshi sai akanta, yanayin idanunshi data gani yasa ta sauka daga jikinshi da sauri tana leka fuskarshi, saikuma takara fashewa da kuka duwatsun wajen ta kwasa dan yanayin shi data gani tasa tagane wayanda sukai harassing nata ne sukai mai shima, da sauri ta mike zata wurga musu dutse chak taji an kama hannunta da sauri tajuyo, da Waleed suka hada ido girgixa mata kai yayi hakan yasa ta zubar da duwatsun tasake fashewa da kuka tana wani irin kallonshi. Loda yan gidan marayun akayi suka cika marcopolo fam, wayanda suka tsaya da Waleed are just mutane 8, Baba Mani, Mama Iyami, Nura, Shamsiya, sai staff dinshi guda biyu sai Widad, shi Dr Ayo bacin rai yasa ya shige motarshi yabar gidan marayun, cikeda rashin mutunci baban su yazo gaban Waleed yace "all set you have lessthan a minute kabar gidan nan kaida fadawan ka, and mind you Mr Waleed you are advised not to leave the country or the state dan zamu iya nemanka at anytime" ganin ko motsi yakasa har lokacin Baba Mani da Nura suka kama hannunshi suka mikar dashi ahankali, da kyar Waleed ya iya standing on his feet Widad sai kallonshi take tana kuka gani take kaman anmishi wani abune ko mugayen nan sunmai duka ne, ahankali ya kalli Nura yace "je office dina ka daukomin car keys, da keys din wani mota a garage dazaku dauka" gyadamai kai yayi da gudu yatafi hawaye na zuban mai bashi akama shairi ba but he wanna cry for Waleed, dan dariya mutumin yayi yana kallon Waleed yace "ahaka kaman bazaka iya abinda akace kayi ba, da farko da aka kawomana case din ni kaina na musa halinka ne not u till lokacin da aka kawo evidence nagani" dan murmushi da za'a kira murmushin ciwo Waleed ya sakinmai, ahankali yace "I have just 1 request please, badanni ba ku kaisu good orphanage da za'a lurada su da kyau dan most of kananun yaran nan have medical condition" tabe baki mutumin yayi yace "you don't have to worry about that, sabon orphanage fill zamu kaisu, infact sune first set of yara da zasu fara shiga orphanage din, jiya jiyan nan akai commissioning orphanage din, sunan gidan marayun ARHAM DAN MALAMAI ORPHANAGE HOME AND HOME OF THE DISABLES wanda wani matashin arziki yabude mai suna ARHAM ABDALLAH!!! ba Waleed kadaiba hatta su Nura da zuwanshi kenan wajen dasu Baba Mani saida sukaji wani iri, murmushi Waleed yayi yace "inhar Arham ne mai gidan marayun then I can relax hankalina ya kwanta dan nasan waye Arham yaran nan zasu samu kulawa daya dace" "Allah ka sakama Waleed, Arham bamu yafe makaba! Cewan Mama Iyami da baya iya shiru, murmushi Waleed yasake yi da clearly za'a kira data dariya ya karbi key mota daya daga hannun Nura sanan yace "je garaj ka dauko mota ka kwashi dukanku zan tura maka address din inda zaku tawaya" da sauri Nura yatafi ya dauko mota ya yadawo sienna ce motar dayake ya iya tuki dan Waleed na yawan basu mota, ahankali yakalli su Baba Mani da Mama Iyami data jona Widad suna kuka sosai da wani irin tausayi Waleed din taji yana bata yace "ku shiga mota kutafi zan biyoku" Baba Mani ne yafara shiga gaba itakuma Iyami ta shiga baya Shafa ma haka, ahankali yajuya ya kalli Widad dake kuka sosai yawani irin daure dan baiso tasashi kuka yace "enter d car Saheeba" makemai kafada tayi tana kallonshi tana kuka, lumshe ido yayi da karfi sanna ahankali yace "please get in karki sani surutu" ganin yanda yake yasa Shafa tafito hannun Widad dake tutturje mata takama ta shigar da ita mota tana kwala uban ihu tana kallon Waleed suka zazzauna, sanan staff din suka shiga seat din tsakiyan motan, ahankali Waleed yarufe musu kofan yace "kutafi" Nura yaja motar sukabar wajen sanan batare daya kalli security ba yadaga kafanshi ahankali yafara tafiya yaje har inda motarshi yake pake ya shiga, "oya oya you are wasting our time " cewan official din, ahankali yadaukey motar yasaka ya kunna motar ahankali yaja motar yana kallon marcopolo da yaranshi ke ciki suna kallonshi kananun namai bye bye, da sauri ya dauke kai, gate yayi yafito yanaso yama security magana kan ya sallamesu amman yakasa dan kuka zaiyi yawuce kawai yay hanyar gida baima gadi da kyau dan duhu duhu yake gani. Ikon Allah ne kawai ya kaishi gida lafiya, parking yayi yafito daga motar yay flat din Ammi da sauri zuciyarshi namai nauyi tana wani irin rawa da hayaki, bude kofar falon yayi ya shiga baima tsaya maida kofan ya kulle ba yay stairs da sauri ganin Ammi bata falo, ahankali yabude kofar dakin Ammi ya shiga, Ammi na zaune kan doguwan kujeran dakin tana duba wata takarda tana sanye da shiga irin ta alfarma, jin an shigo dakinta ba sallama yasa ta dago kanta, hada ido sukayi da Waleed, ganin yanayin idanunshi yasa ta tsareshi da ido, baki Waleed ya bude cikeda zuciyanshi datamai wani irin nannauyan nauyi cikin irin sigan nan da yaro keyi idan zaikawoma mahaifiyar shi kara idan an cuceshi awaje yace "Am.......m...." kasa maganan yayi tsabagen yanda zuciyanshi ya kumbura kawai yataho dagudu yawani irin fada jikinshi Ammi yadaura kanshi kan kirjinshi yafashe da kukan da bata tabajin Waleed yay irinshi ba, cikin kuka sosai yace "Ammi mutuwa zanyi, Ammi daman haka akeji in aka maka shairi and bakada wata hanya dazaka nuna shairi aka maka ba gaske bane? Ammi na dan Allah nataba raping any yarinya tunda kika haifeni? Ammi tayaya zanyi raping mata ba daya ba, ba biyu ba, har guda takwas, Ammi sunce I rape 8girls" yawani irin fashe da kuka Ammi could feel yanda jikinshi ke bari tanajin yanda zuciyanshi ke bugu, cikin kuka sosai yace "Ammi please don't let them take my orphanage from me, this is what I dedicated my life to, Ammi inason gidan marayu na with every part of my life, Ammi kinga king....." yakasa magana sai kuka, kasa jurewa Ammi tayi dudda tana fushi dashi sosai, dagoshi tayi daga jikinta takai hannunta kan fuskarshi ta sharemai fuskan shi tace" Waleed menene? Calm down kamin magana da kyau, suwa suka maka shairin rape"? Hannun Ammi dakekan fuskarshi ya rike gam yace "Ammi please tell me the truth am I a bad person, kinga kin sanni sama da kowa, menama Arham? Ammi what have I done to Arham? Menamai? Arham yabude gidan marayun shi yasa an rufemin nawa, sanan ya kwashemin yaran gidan marayuna duka, yasa akamin shairi da kazafi, Ammi my heart is bleeding" kasa jure yanda Waleed ke kuka Ammi tayi duk juriyanta saitahau kuka dan her heart was shrinking dudda bataji labarin nashi in details ba but she clearly understands abinda Waleed keso yafada mata, cikin wani irin muryan so da tsantsan tausayi tace "Waleed Arham ne yay hurting naka to this extend"? [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR *This novel na kudi ne, idan kika karanta baki biya ba banyafe ba🤷🏻‍♀️* _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ 3️⃣7️⃣ Gyadama Ammi kai yayi yana wani irin kuka, yace "Ammi wai nai raping mata guda takwas, Ammi nataba ma any mace fyade eh Ammi?" girgiza mai kai Ammi tayi tanajan majina trying tahana kanta kuka ta girgixa mai kai takai hannayenta kan fuskarshi tana sharemai hawayen sanan tai cupping face nashi tace "Waleed nina haifeka nakuma raineka I know who is my son, nasan what you can do and wat u cannot do, Waleed nasan cewa bazaka taba yima yara mata fyade ba, bazaka tababa, Arham ne yamaka shairin nan kuma yama kanshi, zakaran da Allah ya nufa da chara ko ana ha maza ha mata saitayi, kadena zubar mai da hawaye come here Waleed dina" Ammi takama kanshi ta daura akan kirjinta tana bubbuga bayanshi tana wani irin kuka mara sauti hawaye, tamafi Waleed jin ciwon abinda ya samai, but yanzu he should calm down first yay shiru tukunna kafin taji full labarin abinda yafaru, takai almost 20min lallashin shi take, jinshi shiru yana sauke ijiyan zuciya ahankali yasa tagane bacci yayi ahankali taja cinyarta ta tashi tsaye tana rikeda kanshi a kirjinta kaman dan jariri sanan ta kwantar da kanshi ahankali kan kujeran tana kallonshi idanunshi sun kumbura sosai sabida kuka fuskarshi yay ja, same da lips dinshi dayay jajir sabida tsabagen kuka, tashi tayi ahankali tadauko bargon saman gadonta tadawo ta lullube shi da bargon sanan tadau wayarta tabude kofar dakinta tafita daga dakin kirjinta na tafarfasa, sauka tayi kasa tazauna kan dogon kujeran ta shiga contact dinta number Mama Iyami ta nemo tai dialing number, ringing daya Mama Iyami ta dauka, Mama Iyami zata fara surutunta Ammi ta tsareta tace "please Mama Iyami, abinda nakeso kawai shine ki sanar dani maiya faru banson surutu kaina ciwo yake sosai, ina jinki" ahankali Mama Iyami ta shiga mata bayanin duka abubuwan dasuka faru har zuwa kan address din da Waleed yatura musu cewa yanzu hakama suna gidan, shiru Ammi tayi duk tana jinta sanan ta sauke ijiyan zuciya tace "ok nagode zansa akawo muku kayan abinci sabida kudinga girki" "to Hajiya mun gode Allah saka da Alkhairi, sanan Allah ya fitar da Waleed ya wanke shi daga wanan shairin" katse wayan Ammi tayi ranta na boiling takira Mom, tana daukan wayan tace "kizo gida yanzun nan" katse wayan tayi direct takira number vice president din Nigeria Osijoban. Ringing daya, biyu ya dauka yace "Hello Hajiya" "don't call me Hajiya Osijoban" Ammi tafada da fushi sosai dan zuciyarta tafarfasa yake sosai tace "after all that I've done for you, banji kyashin baka all kudaden dakake bukata ba for you campaign, because my late husband kafin yarasu consider you his close one nima haka na dauka shine da ranka da lafiyan ka har alakama d'ana shairi sanan a kulle mai gidan marayu kayi shiru, no no no am disappointed and heart broken Osijoban" Ammi tafada kaman zatai kuka, cikin wani irin calm voice vice president yace "listen to me Hajiya, wlh ina shirin kiranki kenan kiranki ya shigo wayana, as am talking to you now yanzun nan case dinan ya shigo office dina, Ministry of Women suke incharge of orphanage sunada wanan ikon su kulle duk wani gidan marayu dake harka mara kyau, danaga gidan marayun d'ana ne Waleed raina saida yabaci, namasa acema Minister inason ganinta yau yau dinan bama gobe ba, and I will promise you one thing, kibani lokaci kalilan sabida dole ayi bincike bazan iya kawai nace baza'ayi binciken ba, amman kibani nan da 30days namiki alkawarin zan budemai gidan marayun shi, da ace nasan kan case din kafin su yanke hukuncin nan dana hana amman sai yanzu nake sani, I will do everything in my power nabude mai gidan marayun nan for now ki kulada shi kinji Hajiya, take care okay, sai gobe" ahankali Ammi tacire wayan daga kunnenta ta katse sanan ta ijiye tanaso takira Maman Arham amman saitaga enough sunma kansu but wlh tayi alkawarin zatai maganin Arham, tana cikin tunanin Mom tabude kofa 5a shigo tana rikeda hadaddiyan jaka tayi kyau sosai tana ganin idanun Ammi tagane da wani abu da sauri ta ijiye jakanta kan centre table takaraso kan kujeran da Ammi ke zaune da sauri ta zauna takai hannunta kan wuyan Ammi tace "Adda bakida lafiya ne eh? Maisa idanunki sukai ja haka kaman kinyi kuka"? Ajiyan zuciya Ammi ta sauke tace "idan da zanga Arham yanzu zan iya shakeshi sainaga yana gab da shurawa zan sakeshi, an rufema Waleed gidan marayunshi! Da sauri Mom tace "what" gyadamata kai Ammi tayi tana cijan lips tace "not just that yahada ma d'ana shairi kala kala, ciki harda yay raping yan mata guda 8, can you believe yaran sun fito sunyi confessing wai Waleed yay raping dinsu da gaske agaban kowa harda kuka" ahankali Mom tace "innalillahi wa innailaihi raji'un" ahankali Ammi tana wani irin kallon Mom tace "ance Waleed na saida yara, yana trafficking yaran gidan marayun and maltreatment, Waleed told me an kwashe yaran an maida su gidan marayun Arham shima wai yabude gidan marayunshi" kasa magana Mom tayi wanan lokacin sai Kallon Ammi take jikinta yay morethan sanyi, cikin wani irin yanayi Ammi tace "ban taba son abotan shi da yaron nan ba daidai da sau daya, kullum sani kike nadinga ma Arham dariya tunda d'ana nason shi amman ban iyawa, kaman Allah ya nunamin nan gaba zai yaudari d'ana ne, Arham ya yaudari Waleed bakadan ba, he uses my child weakness against him, he cheated my son, ya yaudari yarona" tai maganan tana girgiza kai, ahankali Mom tamika hannunta takama hannun Ammi tace "Ammi listen to me, nasan halinki sosai, I know yanzu haka zuciyanki na kitsa miki abubuwa da dama, I want you to calm down Ammi, ba'a rama mugunta da mugunta, ba'a rama cuta da cuta, nasan yanzu haka duk inda Arham yake yana tunanin bama hakaba yana expecting zuwanmu for revenge ko rashin mutunci, Ammi kinajina please wanan karan ki sauraran, tunda dai Allah ya nuna mana wayeshi, sanan Allah yabude mana ido harda da Waleed munsan waye Arham din mubarshi da Allah, kome yama Waleed yama kanshi, ni to me da Waleed ma yahakura da gidan marayun dudda passion dinshi ne yana ma mahaifinshi ne but kawai yakoma normal hospital yafara aikinshi still lada zaikai ga Abba, yabar Arham da halinshi, yana kanshi yaci amanar kanshi, ya manta dashi da abinda yamai and move on, ga yaron shi chan, jibi suna yakamata yaje yagansu kiyakuri Adda na" shiru Ammi tayi tana kallon Mom ko kadan batason ta hakura tanason ta gwadama Arham ba'a taba mata yaro a zauna lpy amman kuma tana tunanin maganganun Mom, wani irin ajiyan zuciya ta sauke ya jingina da kujera ta lumshe ido takasa daina tunanin abinda Arham yama Waleed, takasa daina tunanin yanzu Waleed baida gidan marayu yanzu Arham ne mai gidan marayu da yaran gidan marayunshi. Ajiyan zuciyan takara saukewa hakan yasa ahankali Mon ta rungumeta tace "ya isa Adda I know what you are going through is okay, kiyakuri Allah natare da masu hakuri duk wanda ya cuceka kanshi ya cuta Adda so kibarshi da halinshi" haka Mkm ta dinga bama Ammi baki harta saukko sosai, suna zaune nan akasa sukaji anbude kofar dakinta daga sama da sauri Ammi da Mom suka daga kansu, Waleed ne yafito idanunshi sun kumbura suntum da sauri Ammi tai hanyar stairs din tace "Son katashi" tai maganan tana mika hannunta tarikeshi ahankali tace "katashi Waleed" gyadamata kai Waleed yayi yana kallon Mom dayagani biyeda Ammi tana kallonshi murmushi ya sakin mata yace "Mom kinzo" gyadamata kai tayi ahankali tace "nazo Dan Yaro na" ahankali yake saukowa daga stairs din tareda Ammi, murya chan kasa yace "Mom yunwa nakeji" Ammi jitayi kuka yazo mata tuntuni fushi take dashi tasan baya wani cin abinci yan kwanakin nan tunda yafadi da bakinshi cewa yunwa yakeji dat means yaji yunwa sosai dan Waleed bayacin abinci sosai, muryan Ammi na rawa sosai tace "sh.....shiga kitchen ki dafamai abin.....abin....d....yakes....." kasa karasa maganan tayi saikuma tafashe dawani irin kuka Ammi tayi da sauri tasaki hannun Waleed zata koma sama dan batason yaga tana kuka rike mata hannu yayi gam ahankali yace "Ammi" fadawa jikinshi tayi tasaki kuka tace "Waleed I am sorry, nima I abandon you jibi yanda kakejin yunwa eh, you have been going through alot Waleed wlh ban kula dakai yanda yakamata ba inda nayi da non of this would have happen to you" girgizama Ammi kai yayi yadagota share mata fuska yayi yace "shiiii Ammi don't cry, idan kina kuka I will break down Ammi, you are my strength, please kidena kuka if anything happen to you bazan yafema kaina ba, stop crying kinji Ammi na" gyadamai kai tayi tana kara share fuskarta, ahankali tace "Arham hurt you Waleed" hannun Ammi yarike yace "Ammi kidena maganan Arham, abinda yamin hurt me deep but such is life nayi imani da kaddara mai kyau da mara kyau, please ku manta da komi kima dena kiramin sunan shi, I want to forget everything and move on Ammi, kinji" gyadama Waleed kai tayi, Waleed yakama hannunta sukai dinning, Mom kuma ta share gajeren hawayen daya zubo mata tai kitchen, spaghetti kawai ta dafa musu hadadden gaske, sosai Waleed yaci yanuna ma Ammi babu abinda ke damunshi duddan karsu damu itada Mom, saida yaci ya koshi sanan yatashi yace "bari naje nai wanka" murmushi Ammi tayi tace "ka shirya gabaki daya kawai sai muje muga Ilham da Baby mukai musu kayan suna ko" gyadamata kai yayi kawai yawuce yafita, duk suka bishi da kallo. Flat dinshi ya shiga ya maida kofan yarufe bedroom dinshi ya shiga ya zauna akan gado yanzu ne komi yake kara dawomai fresh, kaman zai fashe da kuka yakeji, wani irin ciwo yakeji da bazai iya misiltawa ba, baison yana tunanin Arham ne yay mishi all this abubuwan saiya kawar da tunanin kawai dai yasan yarabu dashi, tashi yayi da kyar ya shiga bayi wanka yayi yafito ya shirya cikin wata Ash color shadda gizna datamai bala'in kyau kaman bashine ke cikin matsala ba, turare ya feshe kanshi dashi sanan yadau dark shade yasaka dan idanunshi sunyi ja, yadau wallet dinshi yafito, bude kofa yayi yafito ahankali yake tafiya haryay wajen da motarshi take a pake ya kwalama Ammi kira da Mom. "Ammi, Mom kufito am outside" yay maganan yana juyawa ya kalli gate jin anyi horn gateman yafito da gudu yana bude gate din, wata brand new ferrari ne yaga ta shigo compound din da baima iya hango na cikin motar glass din motar is tinted, dawani irin gudu mahaukacin motar ta taho harsaida gateman yace "kai" saura kiris motar ta buge Waleed a inda yake tsaye amman ko matsawa baiyiba sabida hakanan ranshi ya fadimai Arham ne, daga kofar akayi Waleed na kallon kofar daga inda yake, kashe motar akayi aka sawo kafa akasa, kafanshi na sanye da wani tomford mai bala'in tsada sanan yafito daga cikin motar, Arham ne yana sanye dawasu hadaddun suit ajikinshi baki idanunshi sanye da bakin glasses yana kallon Waleed yana wani irin murmushi sanan yafara taku daidai yana tahowa gaban Waleed din daya tsareshi da ido yazo har gabanshi ya tsaya yace "call me Mr Arham Abdallah CEO of Arham jikan Malamai orphanage home and home of the disables, Mr Waleed I heard what happen to your orphanage saisa nazo nan, I come to offer you a job agidan marayuna". [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR *This novel na kudi ne, idan kika karanta baki biya ba banyafe ba🤷🏻‍♀️* _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ 3️⃣8️⃣ Dan murmushi yasake yi yakai hannunshi ya zare bakin glass din kan idanunshi ya kalli Waleed din yace "am willing to offer you a Nani job a boys section dina, idan irin kananun yaran nan dabasu iya magana ba sunyi kashi ko fitsari ajiki saika wanke musu, am ready to pay you 100k monthly for just that Waleed" daidai lokacin Mom da Ammi dasukaci gayu sosai sun fito yar aikin Mom biyedasu takwaso wasu hadaddun kaya dazasu kaima Ilham, hango Arham yasa da sauri Ammi tace "Arham!" juyowa Arham yayi yazuba mata idanu da sauri Ammi tayi wurin Mom biyeda ita tana zuwa ta tsaya kusada Waleed sanan ta kalli Arham din cikin fushi tace "how dare you step into my house with those your filty legs, ubanme kazoyimin agidana" wani irin kallon Ammi yayi sanan ya kalli Mom kafin yatabe baki ya nuna mata Waleed da hannu yace "nazo nabama danki aikin Nani ne idan yanaso agidan marayu na" wani irin sake handbag Ammi tayi akasa ta chakumo rigan Arham tace "how dare you Arham? Kasa an rufemai gidan marayu har kanada gut din shigowa gidan nan eh? How dare you waye kai? Kai dinan waye? Uban waye ubanka waye ya tsaya maka, kasan waye Waleed kuwa? Dan kasa anrufe gidan marayun shi sai me? Bari kaji yanzu haka Waleed nada kudin dazai iya gina gidan marayu dari inyaso, d'ana baida lokacin ka, baka gabanshi yanzu, yabarka har, so I expect you to do dsame stay out of my sons way inba hakaba Arham zan koyamaka hankali wlh" tai maganan tana sakinshi ta tureshi dan murmushi Arham yayi yasa hannu ya kakkabe kwalan shi yace "my expensive suit, anyway is fine" ya kalli Waleed yace "katuna abinda nataba fada maka kwanakin baya Waleed?" wani irin murmushi yayi batare daya kalli Ammi ba yace "nasan ka manta, lemme remind you, Waleed nafadi maka cewa duk abinda kaci sainaci, duk abinda kasaka saina saka" yanuna mai suit din jikinshi dan irin wanda Waleed yake sakawane masu tsada, yace "duk abinda kahau sainahau Waleed" yanuna mai motar sanan yace "duk matakin daka tsaya wlh saina tsaya, meet Arham the newest CEO of orphanage home how does that sound a kunnuwan ku" gate Mom tanuna mihsi tace "munji Arham kayi gidan marayu and muna maka fatan alkhairi the gate is over there kawuce kabar mana gida" girgixa mata kai yayi yace "a'a Hajiya bangama da danku ba tukunna" ya kalli Waleed yace "not all those orphanage student are in my orphanage, kasan kuma wanake cewa nabaka awa uku kasa wanan specific one din dakasan akanta nake magana kasa amaidata gidan marayu na dan ina bukatan ta if not things will get dirty yaro". "get out butulu kawai, leave my house kafin ka kirga uku matsiyaci dan gidan talakawa," kallon Ammi yayi saikuma ya kyalkyace da dariya yadaga hannu sama cikeda isgilanci yace "I come in peace, you seems angry menene wai? Bari nabar miki gidanki kinsan they can't arrest newest CEO" wajen motarshi yayi ya shiga sanan yasake leko da kanshi ta window mota ya kalli Waleed yace "don't forget my offer and maganan dana maka Waleed I need that girl in my orphanage nabaka 3hrs" yatada motarshi yay reverse yawuce yabar gidan, juyowa Ammi tayi zata rufe Waleed da fada dataga baicema Arham uppan ba Mom ta girgixa mata kai alamun kartayi sanan tace "mutafi Waleed" juyawa kawai yayi yabude gaban motar ya shiga sukuma suka shiga baya suka zauna Waleed yatada motar, Ammi ta shiga masifa tace "wanan irin yaron ne Waleed zai kama danshi ya radamai sunanshi tirrr wlh, tier, I hate Arham with passion my heart is burning with rage, I want to deal with this boy dabazai kara tunanin crossing anylane with my son ba amman kin hanani kina cemin nabarshi da halinshi sabida yaga d'ana karami baida shekaru kamanshi sanan baida fada he is calm shine zai dinga gayamai maganan just look at the gut har gidana zai tako yama d'ana rashin mutunci wlh Arham yaci ganye, yaci ganye sosai, and zai gamu dani" tai kwafa Mom ta shiga bata hakuri, Waleed duk yana jinsu yay kaman baya jinsu at this point ya shafe zancen Arham a ranshi gabaki dayan hankalinshi ya karkata zuwa kan Saheeba, yasan tanachan gidan nan tana musu kuka dan batasan dukansu ba, and maganan da Arham yamai yasan kan itane yamai maganan, and koda zai bada komi daya mallaka ne bazai taba bari Arham ya karbi yarinyar nan ba, sabida yarinyar nan nabukatan kulawa da medication shikuma baidashi dazai bata koma bawanan ba bazai taba bama Arham itaba. Horn yayi agaban gidansu Ilham mai gadinsu yafito yabude musu suka shiga ciki, yarane atsakar gidan sunata wasa saiga Mummy tafito tana murmushi tana musu sannu tazuwa tace "oyoyo oyoyo" parking Waleed yayi su Ammi suka sauko daga motar sukai wajen ta, sanan Waleed ma yafito yabi bayansu, cikeda girmamawa dakuma kunya yace "ina yini Mummy" "ina yini Waleed, sannunku da zuwa ku shigo dan Allah kunga yara duk sun cika gidan wlh yaran yan biyu ne, sunyi tafiya suna dubai fa bama suga baby ba har yanzu, amman yau mukesa ran zasu dawo in sha Allahu" Mom ce tace "Allah yadawo dasu lpy" hadadden falon su suka shiga Waleed yasami kujera ya zauna su Ammi zasu zauna Mummy tace "kawa bazamu bar yara su zanta ba, muje sama, Waleed bari aturo ta" tai maganan tana kwalama Ilham kira. "Ilham, Ilham kifito ga mijinki" wani daki Mummy tabude musu suka shiga, basu dade da zama ba saiga Ilham ta shigo tana sanye cikin wata atampa riga da zani, tai wani irin kiba nonon ta sun ciko sunyi suntum sabida shayarwa, tai duhu sosai kaman ba itaba sabida zafin ruwan zafin jego, har kasa ta tsugunna agaban Ammi da Mom tace "sannunku da zuwa Ammi ina yini" kanta Ammi ta shafa tace "daughter na sannu kinji ya jego? Nonon ki naciwo ne" gyadama Ammi kai tayi tace "eh yanamin barin ma inzaisha nono" cikeda tausayawa Ammi tace "kije yana falo ki fadamai inyaso yasamo miki abinda zakisha sannu kinji" gyadama Ammi kai tayi ta kalli Mom tace "ina yini Mom sannu da zuwa" "sannu Ilham ya jego kinji yanda mukeji ko yanzu damuka haifoku" dariya Mummy tayi tace "ai ingaya muku yaron nan inyafara kuka itama farawa takeyi kullum bamu baccin dare, kai jikan Kawata badai kuka ba" tai maganan cikeda zolaya, Ammi tace "inkin gajine bani kayana na tattara natafi dasu mufa ba'a mana wulakanci" dariya duk sukayi adakin, Ammi tasake kallonta ganin tana inda take tace "jeki gaida mijinki" tashi tayi Mummy tace "ko dauko yaron nan daga bacci kikaimai" gyadamata kai tayi tafita, dakinta ta shiga ta dauko Arham karami tarikeshi a hannu sanan ta sauka kasa tundaga sama Waleed kebinta da kallo harta karaso gabanshi tana murmushi ta zauna kusadashi ahankali tace "Baby oyoyo, sai yau zakazo kaganni nai fushi" dan murmushi yamata yasa hannunshi ya karbi danshi yarike ahannu yace "sorry I've been busy" sanan yazuba ma yaron ido yana kallonshi yaron dako sunanshi ba'a yiba amman yay kato yay kyau sosai sai kallon yanda yaron yag kamada Arham yake, yanda taga yana kallon yaron saida gabanta yafadi akullum gani take kaman dazaran ya kalli yaron zai gane dan Arham ne, ganin kallon dayake mishi yasa tace "Baby kakosan Arham ko zuwa duba takwaran shi baiyiba, ko kiranmu ma awaya baiyiba wlh baby abin yaban mamaki" murmushi yayi yakai Arham kafadarshi dayake son yafara ihu danhar yatashi yace "zaizo he's busy" ahankali yace "yimin list din abubuwan dakuke bukata na suna" murmushi tayi cikedajin dadi tace "Baby ni nafison kaban kudin zan aika ayomin siyayyan" gyadamata kai yayi yace "nawa kike so"? Wani irin dadi taji danso take tahada kudaden data samu da wanda zai bata tabama Arham tamai transfer halan zaisa yafara daukan wayanta dan gabaki daya bai daukan wayanta bai mata reply na message gashi batada halin fita tana jego saisa har Allah Allah take tai arba'in, ahankali kaman wata marainiya tace "5m ma zai isa" gyada mata kai yayi yace "ok zan miki transfer to your account anjima" rungume shi tayi tace "thank you Baby na Allah barmu tare" haka suka zauna afalon sukai shiru sai kallonshi take dan yamata kyau yan kwana biyun nan dabata ganshi ba gani take kaman tai shekara bata ganshi ba saitaga ya kara kyau, ga Arham ko kadan yaki kuka ajikinshi da normal ne yaron nan natashi zaisha nono ya koshi fa saiya fara uban kuka harsai yayi bacci amman yanzu yana jikin Waleed dakemai wasa yay shiru, cikin zuciyanta tace "danda bama nakaba jibi yanda yay bonding dakai I wonder yanda yaranka zasuyi bonding dakai" hannunshi takama ahankali tadaura kan boobs dinta tana kallon fuskarshi tace "ciwo yakemin Dr" sauke hannunshi yayi da sauri yana kallon boobs din yace "zan aiko miki da magani, sorry" yay maganan ahankali, gyadamai kai tayi yajuya yacigaba da wasa da Arham itakuma na kusadashi tana kallonshi, suna zaune ahaka har su Ammi suka fito, tashi duk sukayi aka shiga sallama sanan suka rakosu har mota, Waleed yabude booth yakira mai gadi suka shiga shigar da kayan dasuka kawo musu ciki sanan suka shiga mota suka musu sallama suka tafi, suna fita motar daya dauko su Anty Hassu suka shigo gidan, da sauri Ilham tafara murna tace "oyoyo yan dubai Anty hope kunyomin tsaraba" fitowa sukayi daga motar rungume su Ilham tayi sanan aka dunguma akai cikin gida, duk bajewa sukayi afalo da yaransu Mummy takawo musu Arham karami, Anty Hassu ce tafara karban yaron hadiye murmushin datake yi tayi ganin yaron gabaki daya sai tunanin ta yakoma kan fuskar Arham dasuka tabagani agidan har sau biyu, kaman Arham da yaron harya baci, dan murmushi ta kakalo tayi tamika ma Anty Hussai yaron, karbanshi tayi ta shiga murna dan ita mutum ce da batada lura haka, itakuma Hassu a kawai lura gata da kaf kaf da abu banbancin su kenan, sakewa Anty Hassu tayi gudun kar Ilham ta zargi wani abu suka cigaba da hira har magrib sanan aka tashi dan aje ai salla Mummy tabama Ilham yaron, tace "kije ki kwantar dashi ki zauna tareda shi mangariba tayi Ilham zama kake kusada yaran ka ka natsar dasu" karbanshi Ilham tayi tana murmushi dan dadi sosai takeji tana expecting kudi tai sama, bude dakinta tayi ta shiga tana shiga kafin ma ta kwantar da Arham aka bude kofa aka shigo dakin da sauri tajuyo Anty Hassu ce, maida kofar tayi ta rufe sanan tasaka sakata, tashi tsaye Ilham tayi rikeda Arham dake bacci akafadar ta tace "Anty Hassu" karasowa Anty Hassu tayi tamika hannu tace "bani shi na kwantar miki dashi" karbanshi Anty Hassu tayi sanan ta kwantar dashi ahankali cikin gadonshi ta gyaramai net sanan tajuyo ta zauna abakin gadon takamo hannun Ilham ta zauanr da ita tace "zauna nazo muyi magana ne saisa ma na kulle kofa dan banso aji maganan mu" zama ahankali Ilham tayi tana kallonta, hannayenta Anty Hassu takama tarike tace "Ilham, agidan nan bayan yayyin mu maza guda biyu, saini da Husai, sai wata data rasu kafin ke, saisu Farida, Ilham kinga kome zai faru we are family and we will always be, sanan babu wanda zai rufa maka asiri aduniyan nan kaman dan uwanka najini, kingani nan niba yarinya bace ke kanki kinada shekaru 26 sanan akwai wata data girmeki data basu kafin mu kinsan ko mun kwana biyu, kalleni da kyau Ilham niba yarinya bace, sanan duk gidan nan a duka yaran da Baba yahaifa shi kanshi Baba yafadi bai taba ganin d'a mai fikra da lura da abu cikin dukanmu kamani ni ba, ko rashin lafiya ake agidan nan kafin a fada ina ganin mara lafiyan nasan baida lafiya, so Ilham bansan kwana kwana, sabida inason na taimaka mikine tun kafin lokaci yakure miki" Anty Hassu tai maganan babu wasa tattare da ita sanan ta tsare Ilham din da idanun rass batako kyaftasu sanan ta nuna mata Arham dake cikin gadonshi da yatsa tace "dan chan yaron waye? Na mijinki ne kona abokin mijinki"? Wani irin faduwa gaban Ilham yayi da ita kanta Anty Hassu saida taga faduwar gabanta. Kasa magana tayi saiji datayi bakinta ya bushe sosai ta shiga lashe lips dinta, Anty Hassu tace "bayan wanan bazan sake miki tambayan nan ba, yaron nan dan wayeshi na mijinki ne kona abokin mijinki"? Kasa magana still Ilham tayi tabude bakin ma komi takasa fitowa, gyadakai Anty Hassu tayi tace "yayi miki kyau Ilham, magana daya tal zan gayamiki, kwana chassain da tara na barawo ne kwana dayane tal na maishi, kibi duniya asannu sanan kidinga sara kina kallon bakin gatari dan karyazo daga baya yadauki wuyanki, bari naje nai salla" Anty Hassu tamike kaman ba ita tai maganan ba tai kofa tasa hannu tabude sakatar tabude kofan tafita daga dakin, dawani irin sauri Ilham ta tashi tai gadon Arham karami, yaye net din tayida sauri sanan ta kalli fuskarshi muryanta na rawa cikeda tashin hankali tace "wai daman ana gane kaiba dan Waleed bane? Tokodai Waleed yagane shiru kawai yamin yana kallona? Innalillahi wa innailaihi raji'un, ya Allah karufamin asiri" [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 3️⃣9️⃣ _duk wacce bata karanta DUNIYA BIYU MABANBANTA ba ansha dake, littafi ne da dan Nigeria 🇳🇬 Bahaushe yahadu da balarabiyan kasan Morocco🇲🇦, a Two Different world ne zakuji asalin bayanin miye tsantsan cin amana da hassada, wat are you waiting for? Biya kiji abinda wayanda suka biya keji, kika karanta kuma na Allah ya isa kin kaskantar da kanki_ _I don't like much surutu please, M Shakur bansan littafin Allah ya isa bane, yanzu dai kinji nakudi ne_ How to subscribe _Pay 500 into my account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461_ Hawayen daya zubomatane ta share tana sharce majina sanan tadau wayarta dagakan gadon daidai alert na shigowa tabude da sauri instead of 5m data tambayay saitaga alert na 7m wani irin dadi taji ya lullubeta da sauri tai dailing number Arham amman harya gama ringing bai da gaba, takirashi yafi sau goma still bai dagaba cillar da wayan tayi cikin fushi tafashe da kuka, ace ta haihu yau yaro kwanan shi biyar amman har yanzu baizo ya duba dandan shiba, tamai text, tamai text, takirashi, takirashi harta gaji amman bai daukaba, baimayi acknowledging anyone of them ba, to wai yanzu baya sonta ne kome? Ina sonta dayace yake mata yake eh? Yanzu when she need Arham the most suhadu su kula da dansu yanzu ne zai juyamata baya baima damu da itaba, wlh tai nadaman budema Arham kafa harya shigeta yamata ciki ta haifan mishi d'a. * Koda sukakai gida yaso yafita dan ranshi sai kawomai Saheeba yake he could not stop thinking about her amman Ammi tahanashi fita tace yazauna agida, hakanan ya zauna agida sai nan nan dashi take dan batason yay tunani kowani abu. Wanan kenan _kizo zuciya kibiya and say bye bye to karatun Allah ya isa, pay 500 into 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to M Shakur 07012181461_ ****** Tunda suka kai gidan nan kuka Saheeba take, kuka take kaman an yankata, gidane mai kyan gaske flat biyu ne aciki da compound mai dan girma, Baba Mani da Nura da maza biyun staff din Waleed ne sukadau flat daya sai Mama Iyami da Saheeba da Shamsiyaa sukadau dayan flat din, tun da suka shigo Saheeba bata barsu sun huta ba, gidan nan babu wanda bai lallashi teba amman kaman ba ita ake lallashi ba har kudi Baba Mani ya aika asayo mata abinci amman takici, da kyar suka samu anayin isha'i bacci yay awon gabada ita shima barawo danko ruwa bata saka a bakinta ba, kome suka bata saita barar taki basu. Wanka duk sukayi sukaci abinci dan Ammi ta aiko musu da abinci da kayan girki, da gas pots da komi dai harda sabulan wanka, gangariyan girki Mama Iyami tamusu itada Shamsiyaa sanan takira Nura ya shigo yana satan kallon yar budurwan shi ya dauki na maza yafita, Mama Iyami taje tai wanka tai salla ta shirya bacci, Shamsiyaa ma haka, duk saida suka leka Widad dan adaki daban take sanan sukaje suka kwanta. Marazuciya, ace Allah ya isa ki kasa bari sabida ke mayya ce, kika karanta baki biyaba Allah ya isa. Wuraren 1:20 na dare motar Arham yay parking, bude motar yayi yafito yana ganin hasken wuta yace "yes! Nasan daman dole yazamto kuna daya daga cikin gidajen Waleed" wajen gate din yayi yataba jin gate din a kulle yasa yay knocking gate din da karfi, cikin bacci Baba Mani yaji ana knocking kofa tashi yayi yazauna dan daman baida nauyin bacci, jallabiyar shi ya nema yasaka dan shima daki daban yake yafito, yana fitowa yaga Nura ma yafito yana saka t-shirt, da sauri yace "Baba Mani oga ne yazo yake knocking"? Anatse Baba Mani yace "wlh bansani ba Nura, mujedai mugani" bude kofar falon sukayi suka fita compound din sukai gate, suna zuwa gate Baba Mani ya tsaya yace "waye awurin likita kaine"? "nine" Arham yafadi ranshi abace, jin muryan Arham yasa Baba Mani yasa hannu yabude saka Arham yaturo gate din ya shigo da sauri ranshi abace, anatse Baba Mani yace "Malam Arham lafiya da daddaren nan me kakeyi anan"? Kai tsaye yace "ministry suka fadi mani nazo na dauki Sabeeha, tanada matsalan brain dudda tawuce 18yrs she cannot make any decision for her self, zan tafi da ita na ayi admitting nata a hospital dina ana dubata, wlh cikinku duk wanda yahanani saina sa police sun kamashi dan I have the order, tana inane"? Yay maganan yana dakamusu tsawa babu alamun wasa ko tsoro irin adole da gaske yake dinan, ahankali Baba Mani yace "bari na tadasu nasa Iyami takawo maka ita amman suna mata ai baka kutsa bangaren su hakanan ba" da sauri Arham yace "inna shiga ka fizgoni" yay dayan shashin dayaga Baba Mani na kallo alamun nanne inda suke, kai tsaye yabude kofar luckily yaji kofar abude shiga ciki yayi yana kallon falon da babu kowa yay corridor daya gani, dakin farko a corridor yabude aiko yaga Widad akwance tana bacci tana sanye da rigan asibiti da silifas a kafarta kanta babu dan kwali, ga cinyoyinta har wasu irin sheki suke yabisu da kallo wani irin kwadayinta natasomai, hannu kawai yasa ya fincikota tamike tsaye chak a firgice ta shiga sosa ido janta yayi yafara tafiya har suka fito waje daidai idanunta sun washe tadaga kai ta kalleshi ta kalli su Baba Mani dake tsaitsaye suna kallonsu ga Arham nawani irin janta yana gate kaman zai tsinka mata hannu, kwarara wani irin uban ihu tayi. "ahhhhhhhhhh" da saida Arham yasa hannu yataushe kunnenshi daya sanan yadaka mata tsawa. "are you crazy zaki fasamin kunne ne stupid girl"? Fashewa tayi dawani irin kuka tana tirjewa amman janta yake yabude gate yafice abinshi bayan mota yabude ya jefata ciki yamaida kofar yarufe yace "mahaukaciya dake amman sai shegen gardama da turjiya" gaba yabude yashiga yaja motar sukabar anguwan daidai Mama Iyami nafitowa daga flat dinsu tai wajen Baba Mani tace "Baba Mani ina mara lafiyan nan take? Fitowa tayi wlh bacci ya Kwasheni mai nauyi sama sama naji kukanta ina take"? Ahankali Baba Mani yace "Arham yatafi da ita, wai hukuma tacemai yazo yadauke ta ai batada hankali balle ta tantance metake so ba, yace muka hanashi zai hadamu da yan sanda" zubewa Mama Iyami tayi akasa tace "innalillahi wa innailaihi raji'un, shikenan" tabuga uban tagumi saikuma kaman an tsunguleta tace "Waleed, Waleed" da sauri tamike tsaye ya kalli Nura dake tsaye sunyi charko charko akanta tace "ki......kiramin likita Nura I sauri" waya Nura yaciro daga aljihun shi yay dialing number Waleed, harya gama ringing bai dagaba, yasake kira akaro nabiyu yana gabda ya katse Waleed yabude idanunshi dake cikeda bacci, ya mika hannunshi ya kunna bedside lamp, yadau wayarshi ya bude ganin har 2miss calls daga Nura yasa yaji gabanshi ya buga hakanan ranshi yabashi Saheeba, dan ita kadaine zatai abinda har zaisa akirashi this night halan taki bacci kuka take musu, kokarin calling Nura back yayi kiran Nura ya shigo da sauri yay picking muryan Mama Iyami yaji cikin tashin hankali tace "likita yanzun nan ko minti biyar ba'ayiba Arham yazo yadauki yarinyar nan mara lafiya dake sanye da kayan asibiti" jumping Waleed yayi ya sauko daga kan gado, wata irin zuciya ne yaji yazomai yace "whatttt!" tsawan dayayi ita kanta saida Iyami taji tsoro bakinta na rawa tace "un......ungo Baba Mani yana wurina akai komi" karba Mani yayi yace "Barka da dare likita, yanzun nan fa cikin bacci mukaji ana knocking nama zaci kaine nafita nida Nura......" Yabashi labarin komi tatas, Waya na kunnen Waleed ya zuri key motarshi dake kan side drawer yafita daga shi sai pj ajikinshi dogon wando mai gidan siga fari da blue dawata faran riga, kafafunshi sanye da farin bathroom slippers, yanda ranshi yay kolokuwan baci har dishewa muryanshi yayi, da kyar yace "kasan inda yakaita yanzu Baba Mani"? Ahankali Baba Mani yace "wlh bansani ba, amman dai cewa yayi zai tafi da ita gidan marayunshi tunda tanada tabin hankali bazata iya zaban abinda yafi mata kyau ba" katse wayan Waleed yayi yabude kofan falonshi yafita compound dinsu, da sauri sauri gudu gudu yake tafiya yay gate, gaban dakin gateman dinsu ya tsaya ya bubbugamai kofa yafito yace "budemin gate nafita Adamu" yakoma wurin motarshi yabude ya shiga ya tada motar saikuma ya daki kujeran motar cikeda cinrai yana tunanin Saheeba, wayarshi yadauka ya shiga goggle da sauri yay searching address din gidan marayun Arham nan location din yafito, jan motar yayi yafita daga gidan da gudun mahangurba. Wanan kenan Baki cika isasshiyar mace ba inhar kina karanta littafin Allah ya isa, danhaka kika karanta baki biyaba Allah ya isa. Da gudu Arham ke tuki kukanta na ratsa doduwan kunnenshi sabida akwai ta da shegen murya, tsaki yadinga ja yana sharara uban gudu akan hanya, kukan da Widad keyi har tausayi saita baka babu inda bata waigawa Waleed dahar yau batasan sunanshi ba shitake nema, ahaka haryakai gidan marayun shi. Inkika karanta batare dakin biyaba baki isa bane, fatararriya. Babban gidane shima saidai bakaman na Waleed ba, ginine har gini saidai babu plasta da penti, ga wani mai gadi guda daya dake gate din waje yana zaune kan wata plastic chair hannunshi rikeda radio dan shine keyin night, yana ganin motar Arham yabude gate din, Arham yashigo yana kallon ko'ina agidan marayun da akwai wuta ko'ina shiru yara da kowa na bacci, administrative block yayi inda office dinshi yake yay parking awajen ya kashe motan yajuyo yana kallon Widad dake kuka ahankali tana gyangyadin bacci alamun bacci na gab da awon gaba da ita, bin jikinta yayi da kallo tundaga tulin gashinta da akaimata parking aka tupke har zuwa kan doguwan rigan asibitin dake jikinta sanan ya saukar da idanunshi kan boobs dinta dayagansu atsaitsaye da alamun babu bra ajikinta, boobs din basuda wani girma dan ko rabin na Ilham ba sukai ba, lips dinshi ya lashe yace "irin wayan nan ne ka kamasu ka matse su na kwana biyu saigaka sun cika kirji kaman ka zuba musu yeast" yay maganan yana saukar da idanunshi kan fuskarta danta lumshe ido tafara bacci, gashin idanunta zara zara gwanin kyan gani ga lips dinta yay jajir ahankali yace "gosh this girl is beautiful wlh kodanai karatu a kasan waje naga yaran turawa bantaba ganin mai kyau irin yarinyar nan ba, gata yar charas, nasamu yarinyar nan na aura I will so enjoy her wlh" shiru yayi yasaukar da idanunshi kan cinyarta da rigan yadan kwaye sama kadan fararen cinyanta sol suka bayyana, tashi tsigan jikinshi yayi yace "I want to rock life with this girl, gani yanzu the latest CEO, gani da kudi, banda wata matsala, bari na more wanan yar karaman mahaukaciyan yarinyar nan Ilham tariga tabude I will not enjoy her kaman wanan yarinyar fresh blood" bude kofar motar yayi a hankali yay office dinshi yaciro wasu keys daga aljihunshi yabude kofar office din, yabar kofan abude sanan yadawo motar yabude baya ahankali, cikin dabara yakai hannunshi zai dauketa firgigit ta farka tareda bude baki zata sandara ihu da sauri yakai hannunshi yataushe bakinta gum sanan yadauketa tana kokarin kwace kanta yay office dinshi da ita, maida kofar yayi yarufe sanan yakaita gaban table dinshi har lokacin yarufe mata baki da hannunshi, dayan hannunshi dakeda lafiya yamika yadau salatef dake kan table dinshi mai ruwan toka, dauka yayi yasaki bakinta tafashe da kuka sosai, tsawa ya daka mata tace "shegiyar yarinya sai shegen kuka, mahaukaciya kawai yanzun nan zan dinke bakin naki tass" ya yanko salatep din yakai kan bakinta ya like tass yafashe da dariya yana kallon yanda take kuka tanason ta kwace hannayenta daya rike takasa, yace "stop crying yar mahaukaciya, muje kibiya min bukata ta, abukace nake this night, babu wacce zan amfani da ita asirina arufe agidan marayun nan irin ki, muje ciki baby" yay maganan yana daukanta yabude wani kofa ya shiga cikin bedroom din office dinshi da ita, akan gado ya kwantar da ita da sauri ta tashi zaune tana kuka sosai tana kallonshi da sauri yace "relax yarinya karfa kisa na daddaure ki, just relax" yay maganan yana warware belt din jikin wandonshi yazare riganshi ya yarda akasa, sanan yaja wandon yay kasa, wani irin jumping tayi daga kan gadon da hannu kawai yabugeta takara fadawa cikin gadon, yarda dogon wandon yayi yafado kanta yadauketa yadaurata kan jikinshi tana wani irin kankame jikinta yakai hannunshi yadaura kan soft bombom dinta dakeda hips da tudu yace "gosh, wlh ko jikin jariri bazai nunama naki taushi ba, freaky ass" yay maganan yana wani irin jan gown din jikinta sama yadaura hannayenshi kan bombom dinta dake sanye da white pant yasaki wani kara. "arhhhhh". Duk wacce takaranta min littafi batare data biyaba ban yafeba Allah ya isa. [11/1, 11:48 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 4️⃣0️⃣ & 4️⃣1️⃣ _*Duk wacce bata karanta DUNIYA BIYU MABANBANTA ba ansha da ita, littafi ne da dan Nigeria 🇳🇬 Bahaushe yahadu da balarabiyan Morroco, a Two Different world ne zakuji asalin bayanin akan miye tsantsan cin amana da hassada, what are you waiting for? Wait oo are you even doubting M Shakur's write-up? Biya biya kiji abinda yan GGM dina keji_ _How to Subscribe_ _pay 500 into my account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting_ _duk wacce ke karanta littafin Allah ya isa bata isa bane🤣 ba ishashiyar mace bace, sanan kin ragema kanki daraja wlh, vex and prove me wrong kibiya_ Widad was completely traumatised, shocked and scared, gashi batada bakin ihu, kanta wani irin saramata yake kaman zai tarwatse, ihu Arham yayi yace "what!!! this your body is real mahaukaciya, kinji taushin jikinki kuwa, tashi tashi na duba yan kananun nonuwan nan naki naga" yay maganan yana dagata, samu tayi ta fizge hannunta batai wata wataba ta zubamai mari akan hanci da baki daman tun farkon rashin lafiyanta she was violent Waleed ne yake hanata in zata daki mutane yace mata ba kyau tadena, ganin marin ya shigeshi yasa tasake daga dayan hannunta zata zubamai ya chapke hannun yana kallonta yace "nikika mara, ni Arham Abdallah kika mara, kinsan yan mata nawa naci dasuka fiki aji suka fiki komi, naci turawa daban daban, sanan nazo Nigeria nai daga daga da gaban yaran masu kudin garin nan da Nigeria keji dasu, yarinyar alhazawa yanzu inda kinga yanda take kirana dasaikinyi mamaki sotake nazo nacita amman naki, Ke bama kici sa'a ba inama kulaki matsiyaciya irinki mahaukaciya dabama kisan me kikeyi ba" yay maganan yana wani irin murder hannun data mareshi dashi cikeda zalunci, wani irin bankarewa tayi tana nishi kaman zata shide tunda take ba'a taba mata mugunta hakaba, ganin yanda kirjinta ke fitar da numfashi kaman wacce ke shirin mutuwa yasa yasaki hannun nata yajefata kan gadon yace "wlh idan baki natsuba zakisha azaba a hannuna" yahau kanta yakai hannunshi kan wuyan rigan asibitin ta da sauri ta rike tana kuka sosai, tsawa yadaka mata yace "sake wuyan rigan nan nacire boturin, sakeshi nace" bamatasan maiyake cewa ba kawai dai tarike wuyan riganta gamgam jikinta ko'ina yana bari da ace tasan sunan Waleed da Allah kadai yasan sau nawa zata kirashi, ganin yanda yarinyar keda kafiya tarike gaban rigan gamgam tamaki barinshi yabude boturin yasa azuciye ya fizge chajanshi dake bangon gadon ajikin socket ya tsige USB charger ya daddage ya shiga shaula mata batasan lokacin data saki wuyan riganba sabida zafin dataji tana ihun da ba'aji tana soshe soshe kaman zata zare, mercilessly ya zaneta da igiyan nan ko tausayinta baijiba sanan ya yarda wayan ganin jikinta ya mutu lilis yasa yace "kisake min gardama kiga mahaukaciyan banza kawai" yakai hannunshi wuyanta baiyi wata wataba ya barka rigan gabaki daya farin jikinta sol ya bayyana tana sanye da half bes white daya rufe mata boobs kadai, dudda batada lafiya batasankanta ba amman saida takai hannayenta ta kare kirjinta tana kokarin tashi, wani irin washe baki Arham yayi yanabin suranta yana kallo boobs da shape dinsu yafito ta half bes din da kyau, gasu they're so perky gasu a mugun tsaye kaman zasuyi tsalle basuda wanan girman nan irindai nonon larabawa batasaka bra ba, hannunshi yakai kan hannunta datake kare kirjinta dashi ya fizgo hannun da karfi, kafafunta tasa ta shure kirjinshi takoma bangon chan karshen gado, ranshi baci yay cikin gadon yya kanta wani irin jawota yayi yazuba mata mari yace "sai wahala kike bani shegiyar yarinya" yay maganan yana kara kaimata wani marin yaja boxer jikinshi kasa ya kwanta akanta yana kokarin jan pant dinta tanamai shure shure taki tsayawa waje data dan bala'in tsoro fuskarshi yake bata. To sannu makwadadda, stingy koko da biyama kanki bukata ke miki ciwo, gadai novel kinaso amman kin kasa siyama kanki saidai ki karanta na Allah ya isa, anyway nobe your fault bakikai wajen bane. Wani irin bugo kofar dakin akayi da kafa da saida Arham yawani irin firgita yasaketa da sauri yadago kanshi yajuyo, Waleed yagani tsaye abakin kofar dakin jijiyoyin kanshi sun fito rau kaman zasu fasa goshinshi su fito waje yana wani irin kallonshi, Widad na hango Waleed tawani irin ture Arham cikin kuka sosai ta mirgina takifo kasa danko kadan batada karfi jikinta yay rudu rudu, ahankali Waleed yadauke idanunshi dagakan Arham ya zubasu akanta tana kasa tana struggling ta tashi takasa sabida tsabagen yanda jikinta kemata ciwo bakinta manne da salatef tana tattaba kasa tana dago kanshi tana kallonshi tana kokarin mikewa tazo wurinshi, k Shigowa cikin dakin yayi yataho yayo kanta, tsugunnawa yayi agabanta yakai hannunshi yadagata ahankali, wani irin fadawa jikinshi tayi ta kankameshi kaman zata koma cikin cikinshi jikinta ko'ina na rawa, he could feel yanda kirjinta ke bugawa, heart dinta na racing tsabagen tsorata da kuka datayi, rungumeta yayi back ahankali idanunshi sunyi ja ya bubbuga bayanta yana kokarin sa ta natsu sanan yazare ta daga jikinshi, farin rigan pj dinshi ya cire ya sanye mata batare daya kalleta ba, ya wawwaiga baiga komi adakin ba dazai bata tasaka tarufe cinyoyinta ba, kawai dukawa yayi ya zare wandon pj jikinshi yadaga mata kafa batare daya kalli cinyoyinta ba ya sanya mata shi yarage dagashi saidan short din cikin jikinshi baima tsaya cire mata salatef din bakinta ba yadauketa chak a hannunshi yay hanyar kofa da ita, wani irin dirkowa Arham yayi daga kan gadon yana maida joystick dinshi cikin wando yace "where the hell do you think u are taking that girl to? Bring her back to this bed inba hakaba saina maka dan bura'uban duka da tsakar daren nan, wlh dukan danamaka ranan nan harka kwanta a asibiti kadanne compare to wanda zan maka now" chak Waleed ya tsaya saikuma yajuyo yana rikeda ita ya kalleshi, ahankali ya saukar da ita yazaunar da ita nan gaban kofan fita daga dakin cupping fuskarta yayi kafin yasakin mata peck ahankali agoshinta yace "am coming, stop crying okay" gyadamai kai tayi tana sauke ijiyan zuciyan kuka, shafa fuskarta yayi yawani irin mike yajuyo ya kalli Arham, cikeda isgilanci Arham yace "ohohoho don't tell me wanan mahaukaciyar yarinyar kakeso"? takawa har gabanshi Waleed yayi yana tafiyan nan daidai a kasaitacce ya tsaya agab dashi dan har sunajin hucin juna afuska, cikin wani irin yanayin bacin rai yace "karka sake kiranta mahaukaciya" Waleed yay maganan cikin wata kakkausan murya da Arham baitaba jinta da irinshi ba, tsayawa chak Arham yayi yana kallon kwayan idanun Waleed din kaman maison karanto wani abu daga ciki, ahankali yace "Waleed son yarinyar nan da aka tsinta a ruwa bakasan asalinta ba kake"? Sake matsawa gabanshi Waleed yayi kaman zai manne dashi yana kallon kwayar idanunshi yace "yes! Sonta nake! And if u ever raised a finger on her kokuma ka kalleta zan nunamaka wayeni, you are lucky babu abinda kamata da ace kamata wani abu da wlh saina kasheka har lahira you low life bastard" ya kalli gefen Arham din ya tofar da yawu sanan ya kalli kwayar idanunshi yace "I spit on the day dana sanka Arham" yana maganan tareda juyawa, sosai kalamanshi sukama Arham bala'in zafi dan bakaken maganganu yamai harda cewan yatofa ma ranan daya fara saninshi yawu jiyayi zuciya tazomai ya waiga wata flower verse dake kan side drawer gado ya dauka yay bayan Waleed dagudu yakirashi. "Waleed" yadaga zai bugamai, juyowa Waleed yayi da sauri ya kama hannunshi azuciye, wani irin murda hannun Arham din yayi yana kallon kwayar idanunshi dasukai jajir tsabagen azaban dayaji, murda hannun Waleed yayi duk karfin Arham kasa kwatan hannun yayi yana mamaki dan baitaba sanin Waleed nada karfi hakaba ya bala'in rainashi, sakin verse din yayi akasa ya tarwatse sanan Waleed yawani irin kaima gefen wuyan shi wani wawan duka dako kwakkwaran motsi Arham bai sakeyiba yazube akasa asume cikin kwalaben, tsallakeshi Waleed yayi idanunshi sunyi jajir yayi kan Widad datama kasa zama tazube awajen akwance tana kuka ko numfashi da kyau bata iyayi, tsugunnawa yayi ahankali akanta yasa hannayenshi ya dauketa yabude kofa yafito office din sanan yabude kofa yafita waje da ita yay wajen motarshi, bude gaba yayi ya zaunar da ita yace "sorry Pretty" hannunshi yakai kan salatef din ya daye tawani irin fashe da kuka da bama'a iya ji tsabagen kukan datasha dan da zafi sosai, kwantar da kujeran yayi sanan ya maida kofan yarufe yay booth yabude lucky yasami wandonshi da riga take awajen yasaka sanan yawuce yadawo motar ya kunna yaja yabar gidan marayun ko kallon mai gadin gate din baiyiba, tunani yadinga yi ina zai kaita, bazai maidata gidan nanba ko any of his houses bama dan Arham yasan duka gidajen shi saisa yay locating nasu ma esily, da tsakar daren nan kuma bazai iya kaima Mom itaba dan yasan Mom kadai ce zata iya karbanta, to yanzu ina zai kaita and treat her kallonta yasakeyi yaga har numfashi sama sama take, hannunshi yamika ahankali yadaura kan saman cikinta yanda yaji cikinta yagane hardama yunwa babu abinci acikinta, wani hadadden hotel da garin Abuja keji dashi yaje parking yayi ganin kaman tama soma bacci yasa yafita bayan yadau kudaden dayake dashi na cikin motar wanda 300k ne kawai yan rapas din dubu dubu guda uku, reception yaje yamusu booking one room sanan yasai mata kayan sawa na mata awani boutique dakenan reception din, yabama waiter yarike mai sanan yafito yaje mota yabude side dinta, ahankali yakai hannunshi kan jikinta wani irin firgita tayi zata kwala ihu yasa hannunshi ya taushe bakinta yace "hey is me" bude idanunta tayi da kyau ganin shine yasa tadaura kanta kan kirjinshi ta kankameshi tana sauke ajiyan zuciya kaman wata karaman baby, ajiyan zuciya yasauke shima yama rasa mezai mata kaman zaiyi kuka ta bala'in bashi tausayi jikinta harya dau zafi sabida tsabagen wahala. In bakida kudi kiwuce mana kibarshi inda kika ganshi ance dole saikin karanta Allah ya isa ne? Allah yaja zamanin ku matan GGM dina, alkhairin Allah yakai gareku domin kuwa baku kyashin biyan kudin novel din M Shakur koda kam miliyan ne. Daukanta yayi ahankali yay reception din da ita kanta lamo akirjinshi kaman wata babyshi, they look so cute together bai damu da yanda ma'aikatan ke kallonsu ba yay wajen lift ya shiga wanda yarikemai kayan daya saimata kuma biyedashi har zuwa dakin da aka basu room 315, abakin kofa ya karbi ledan ma'aikacin yajuya yatafi shikuma ya shige ciki ya maida kofan yarufe tareda saka key sanan yakaita kan gado, kwantar da ita yayi ahankali yana kallonta ganin yanda fuskarta yatashi sabida marukan daya daura mata, daidai lokacin akai knocking, tashi yayi da sauri yay kofa budewa yayi dayake yamata order cold yogurt shi aka kawomai a tray da glass cup mai kyau, karba yayi yamaida kofar yarufe yadawo cikin dakin yana kallonta, sauke tray yayi akasa yabude yogurt din ya cika mata glass cup din cikeda yogurt yadau cup din yamika mata yace "drink u are hungry" ahankali tamika hannunta dake bala'in mata ciwo zata karba hannun ya shiga rawa sosai, ganin haka kawai yasa yatashi yazauna kusada ita akan gadon yakai yogurt din bakinta da sauri ta shiga sha tass ta shanye yakara mata ta shanye shima, zai sake zuba mata na uku ta girgiza mai kai alamun takoshi saikuma tafashe da kuka tana neman shigewa jikinshi tana sossosa hannunta da jikinta dake mugun yimata ciwo ta mikamai hannunta alamun yaduba, karban hannun yayi yaga shati shatin bulala jiyayi ranshi yasake baci baisan harda zaneta yayi ba, tundaga hannun yake kallo har cikin wuyanta yanabin shaidun dukan da kallo, ijiye hannun yayi ahankali yatashi yabude kofar dayagani adakin wanda yasan cewa kofar bathroom ne, shiga yayi ya bude shower dayay mixing yana fito dana zafi da sanyi, normal hot water da mutum zai iya wanka a karkashi, fitowa yayi daga bayin yazo gabanta cikin harshen turenci yace "zomuje kiyi wanka da ruwan zafi, kafin kifito zanje nasamo miki man zafi na shafa miki aciwukanki, u will be fine" tabe baki tayi cikin kuka ta mikamai hannunta alamun yadauketa, daukanta yayi tasake yin lamo ajikinshi ya shiga bathroom din da ita, ahankali ya ijiyeta akarkashin shower yajuya da sauri zaitafi yana magana yace "bath, inkin gama zan dawo na daukeki" karaf yaji takama hannunshi tarike tareda sakinmai kuka, juyowa yayi ahankali yazuba mata shanyayyun idanunshi da har yanzu xaka gane da bacin rai acikin su yana kallonta yanda ruwan shower ke sauka akan gashinta daya jike sharkab yana zuba kan fuskarta zuwa kan jikinta, farar riganshi dake jikinta na pj ta dameta sosai sabida ruwan har kana iya hango half bes dinta tana kallonshi tana kuka mara sauti idanunta sun kode sosai tsabagen kukan datasha ga gajiya gakuma zazzabi, ahankali yatako kafarshi yashigo karkashin shower shima, hannayenshi biyu yakai kan kuncinta ya tallabosu yana kallonta, cikin harshen hausa yace "Saheeba please kidena min abubuwan nan, what do you want from me" yay maganan ahankali yana kallon fuskarta kaman yanda take kallonshi yakai hannunshi kan ribbon din da akasa aka kulle gashinta ya zare gashin yabaje ya manne ajikinta ruwa nabinsu, shigewa jikinshi tayi ta daura kanta akan kirjinshi ta kulle hannayenta abayanshi tana sauke ijiyan zuciya, yanda yakejin komi nata akirjinshi na bala'in tadamishi da hankali yana kuma kashemai jiki, rungumeta yayi back shima murya chan kasa yace "I love you pretty" ya lumshe tareda daura kanshi kan gashinta ruwa na sauka akan jikinsu atare yana gangarawa kasa, cikin wata irin murya dashi kanshi baisan yanada itaba yace "I want to marry you Saheeba, will you marry your Dr?" Gyadamai kai tayi tana kara chusa kanta cikin kirjinshi tana shakan kamshin dayakeyi da batada abinda takeso irin kamshin, kankameta sosai yayi jin ta gyadamai kai, cikeda wani irin sassanyar so yace "I am the only one that can keep you safe because I love you, I will keep you safe har ranan da Allah zai dawo miki da memory ki muje wajen iyayenki maybe then with our kids" yakarasa maganan yana dan murmushi he really don't know when he start falling for this girl, sun dade ahaka sanan yadagota daga jikinshi yana kallon fuskarta yace "please Pretty take off your clothes shower saiki fito okay" gyadamai kai tayi tana turomai baki ko kadan batason ya barta, sakinta yayi yaja towel yawuce yafita daga dakin da jikakken kayan jikinshi yamaida mata kofan yarufe, cire kayan yayi yadaura towel a waist, tsaki yadanja dan baida kayan dazaisa dole yazauna da towel ahaka a waist, zubar da kayan yayi anan yawuce kan gado ya zauna yana dudduba wayanshi, ganin baiga wayan ba yasa yagane wayan na mota, ya har wayan amota. _please GGM dina sakarya ce kadai ke karanta abin Allah ya isa kobahaka bane?_ nifa abin Allah ya isa ko kallo bai isheni ba🤷🏿‍♀️ Tadade abayi danta iya wanka dudda dai bata tabayi da kanta, ba kullum nurses ke mata wanka, da farko saidai su goge mata jiki da towel daga baya kuma aka fara mata wanka da soso da sabulu, kasa wankan da kyau tayi dan jikinta zafin bulala, tana gamawa dayan towel din data gani arataye ta dauka ta kulla a waist gashinta na diddiga da ruwa tabar kayan data cire anan kasan shower batare data kashe shower ba tabude kofar bayi tafito, ahankali yadaga kai ya kalleta wani irin bugawa kirjinshi yayi da sauri yasake dauke kai yamaida kanshi kan tray da yogurt din datasha ke kai, she's so pretty, towel din da kadan yawuce mata cinya, ga gashinta ya mammanne da wuyanta sunyi lema lema looking so hot, ahankali ta tako har gadon ta zauna kusada shi har jikinshi na gogan nata, da sauri yatashi yakasa kallonta yashiga waige waige saikuma yaga ledan kayan daya siya mata da sauri yadau ledan ya ijiye agabanta yace "wear cloth and wrap your head with the towel am coming" ya kwashe kayanshi daya ijiye gaban bayin yawuce cikin bayin, kashe shower yayi ya kwashe kayanta duka data bari akasa harda half bes da cute pant dinta ya sassagalasu abayin harda nashi koya samu su bushe dan inhar kayanshi basu busheba bashi ba fita gobe, yadan dade zaune abayin sanan yafito, zaune yaganta kan gado ta kwanta tana lumlumshe ido tasaka wani cotton singlet mai kyau na mata wuyan shi anmai ado da lace, tasa wandonshi wanda yake dan short daya tsaya mata acinya ahaka kayan shine mai mutunci daya samu a shagon yasaya. _Ai macen datasan ta isa, takuma kai matsayin, sanan tasan ansan dazamanta ita kadai ke biya biyan kudin novel, saisa nifa babu sakararrun mata a groups dina_ Jin sahun tafiyanshi yasa tabude idanunta da kyau, zama yayi abakin gadon da sauri ta mirgino tarike shi murya chan kasa tace "I want to sleep" kallonta yayi duk in tayi magana saiyaji dadi, ahankali yace "sleep am here to watch you" raurau da ido tayi zatai kuka takara rikeshi gamgam tana nunamai gefen gadon tace "sleep" shiru yayi yana kallonta, ganin yaki kwanciya yasa tashiga rera mishi kuka, kwanciya yayi ahankali saikuma yamika hannu ya kashe bedside lamp din dakin yay duhu, hannunta takai tadaura kan kirjinshi sanan ahankali ta matso kusada shi tasa fuskarta kan power hannunshi ta sauke ijiyan zuciya tareda lumshe ido, soft hair din kirjinshi dataji hannunta ya dilmiye ciki yasa tafara shafawa ahankali, charaf taji an rike hannunta, cikin wata dishahhiyar murya yace "stop pretty" makemai kafada tayi ita kawai sotake tajita cikin jikinshi kota iya bacci, ahankali tahau kan jinikinshi tai lamo kan kirjinshi tana sauke ijiyan zuciya, wata yar malalacin kara Waleed yasaki. "Umm" all her boobs da babu komi akansu were on his chest and abun ya mugun arousing nashi, da sauri yasa hannu yadan yureta yace "stop, lay down on the bed" makemai kafada tayi tana kara gyara kwanciya akan jikinshi, murya chan kasa yace "Saheeba ki sauka you don't know anything, but you are making me horny please" makemai kafada tayi tadaura kanta kan kirjinshi tana shafawa, fizgo hannunta yayi itama ya fizgeta harsaida ta firgita ya kwantar da ita kan gadon tareda hawa kanta, ahankali yadaura kanshi kan fuskarta yana goga hancin shi kan kumatun ta yana numfashi da sauri sauri kaman yanda itama ke bacci da sauri sauri, dan bude bakinta tayi sabida yanda yake goga mata hancinshi nasa tanajin wani iri, hancinshi yakai kan lips dinta yana gogawa wani irin abu na fizganshi, ahankali tafito da tongue dinta waje ta laso hancin wani irin vibration yaji baisan lokacin daya daura bakinshi kan nata ba ya shiga kissing nata yana numfashi da sauri da sauri kaman mai asma yana having wani irin strong erection, tasan ranan nan tamai irin wanan abun but ranan bataji komiba but yau dashi yake mata yasa taji jikinta namata wani yammm yammm, hannayenta takai ta bayanshi ta rungumeshi tareda kankameshi jikinta narawa sosai, yanda tamai yakara hada fatarshi da jikinta, dumjn da jikinta kedashi yasa yaji yana neman zaucewa, hannunshi yakai duka biyun yatura cikin wet gashinta yana wani irin cukurkudawa yana kissing dinta, kafin yasoma saukar da hannun yakai kan wuyanta yashiga saukar da hannun kasa tuntube yayi da boobs dinta baisan lokacin daya saki ijiyan zuciya ba while kissing her, saida yakai hannunshi har kasan rigan saman yatura hannunshi cikin rigan, sosai yake kokarin hana kanshi abinda yakeso yayi amman yakasa her skin is too soft baitaba jin skin hakaba, ko jaririnshi Arham daya dauka taushin jikinshi baikai na Saheeba ba, ahankali yake gangarawa da hannunshi sama hannunshi har wani irin rawa da bari yake saikuma dawani irin gudu kaman first timer ya damke boobs dinshi dasuka cika hannunshi daidai, wani irin nishi dagashi har ita suka saki itakuma tasaki yar kara. "ahhhh" dan taji zafi da karfi yakama mata ya damke su kaman mahaukaci, sakin bakinta yayi muryanshi na rawa yace "pl.....please Saheeba kisaken, push me away I can't control myself, I need you pretty but I don't wanna take advantage of you bakisan me kikeyi ba, push me away please, cry" makemai kafada tayi takara kankame shi, maida bakinshi cikin nata yayi yana kissing dinta saikuma yadagata shiya kwanta akan gado ya daurata kan jikinshi rigan jikinta ya cire mata hannunshi har rawa yake ya yar sanan yakara jefata kan gadon ya warware towel dinshi ya yar gabaki daya ya zauce wani irin mugun bukata da sha'awa yataso mai wanda bai jinta akan Ilham, all his hands yakai kan boobs dinta ya matse zafi taji dawani iri kuma hakan yasa tace "ummm it's hurt" danneta yayi yaja wandon ta kasa yama cire gabaki daya ya yar, yakama erected joystick yakai gabanta. [11/1, 11:49 PM] Re@l🖤 K@usy 🔐: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 4️⃣2️⃣ Yanda yake kissing dinta and the taste of her mouth was driving him crazy, tasakin mai kanshi she is so relax tanajin wani irin dadin dabata tabaji ba, ta rikeshi Gam har lokacin, cire pant din nata yayi yar akasa sanan yakama huge joystick dinshi yakai gabanta cikin wata irin murya kaman wanda zai fashe da kuka yace "omg I don't wanna do this, Baby am so horny, I need you badly, I've never felt like this towards any woman before, ahhh I wanna f**k you soo good until I feel your pussy clinching round my cock" yay maganan yana danna joystick din a tiny gabanta da hole din baida bambanci dana yar jaririya, dawani irin karfi yatura hakan yasa Widad ta kwala wani irin uban ihun dayasa yaji hankakinshi yadawo jikinshi da sauri yasaketa yatashi zaune yana salati saikuma da sauri yatashi yayi bathroom, maida kofan bathroom din yayi yarufe ya jingina da jikin bango yadaura hannunshi kan ma ranshi dayawani irin murdamai dan bala'in sha'awa yaji ta tasomai yahau istigifari yanajin kukanta sama sama, runtse idonshi yayi ahankali yace "what were you doing Waleed, inhar kaman yarinyar nan haka menene banbancin ka da Arham? Subhanallah, astahafurullah" yahau tuba yama manta bayi yake, yakai kusan awa daya kafin yadawo daidai wankan tsarki yayi tsaf sanan yafito daga bayin yabude kofa ahankali gudun karya tadata danya tabbatar tana bacci, kan gadon ya ganta ta lulluba tana bacci tana sauke ijiyan zuciya ahankali, tsugunnawa yayi yadau towel dinshi ya daura da ace yanada kaya da salla zaiyi amman baidashi, filo kawai yadauka yajefa akasa ya kwanta a kasan dakin yana cizan lips dinshi dan maranshi namai ciwo sosai wanda bai sabamai ba gabaki daya maran ya haukace mai soyake yasamu nace ya sadu da ita koyasamu yay releasing yarage ma kanshi ciwon maran amman bahali. Birgima yadingayi akasan kaman zai fashe da kuka da ace Ilham nakusa kuna bata jego dasaiyaje ya sauke bukatan nan amman baida yanda zaiyi ahaka har bacci yay nasaran sace shi akasan nan. Wuraren 8 nasafe yake bude idanunshi ahankali, akan kyakkyawan fuskarta yasauke ido baccin ta take fuskarta na facing nashi akasa har lokacin tana lullube da bargo tai wani fayau, lumshe ido yayi yana kokarin hana kanshi tunanin jiya sanan yatashi zaune ahankali ya kalli agogon dakin ganin 8 nazafe yasa da sauri yay jumping yatashi yay bathroom brush yayi da sababbin brush da toothpaste dake bayin sanan yadauro alwala yana kallon kayanshi dayagani har yanzu ajike dan babu wani iskan kirki, tunani ya shiga yi yanda zaiyi da sauri laundry yafado mai arai, dakin yakoma yakira reception ta landlines kan aturomai lubdry services, sanan ya ijiye ya koma bayi ya kwaso duka kayan harda pj shi daya bata tasaka jiya sanan yafito daidai ana knocking budewa yayi yabasu yace "ayi drying a kawomai yanzu" karba sukayi suka tafi ko minti 30 basu bataba suka kawomai karba yayi sanan yamaida kofar yarufe, riga da wandonshi ya saka sanan yay salla ya idar yana azkar ya jingina da bango yana kallonta kaman yau yafara ganinta, he just wish inama halaliyar shice dayaje ya kwanta akan gadon nan and have her to his content, yana cikin yan tunane tunanen tabude fararen idanunta kaman wayanda aka wanke su da madara ta daura akanshi kaman dachan idanunta biyu, ganin kyakkyawan fuskar Waleed zaune jikin bango yana kallonta yasa tasakin mai wani cute smile she is so fund of him, tana bala'in sonshi, ganin tana shirin tashi zaune yasa da sauri yadauke kanshi dan baison yaga anything dazai tadamai da hankali, bakinshi na dan rawa yace "g......go to the bathroom and shower kizo kiyi salla" yay shiru yana mugunjin nauyin yacemata tai wankan tsarki dan yasan gabanshi yataba gabanta but yanzu ma zai iya koyamata ne yakaita gidan Mom, Mom takoya mata, yansan then idan yakaita gidan tahadu da yaran Mom dan Mom nada mace daya dake ss3 yanzu kuma yadawo gida hutu dan boarding school take zata iya magana zai mata kawa da Asma'u, Ma'un Mom, jin karan kofa yasa yagane tabude bayin shiga bayi tayi dan fitsari takeji sosai, tashi yayi da sauri ya shiga tattare kayanta dayacire ya yarda mata akasa sanan yadau jakan yabude yaciro mata wani gown da pant mai kyau sanan yay wajen kofar bathroom din dan yasan zata iya tafito daga bayi tahau kuka in bataga shi ba, dan knocking kofar yayi yace "Saheeba am coming wanna go get you some things outside" yajuya da sauri yafita daga dakin, kasa yasauka yay waje wajen motarshi yasan Ammi takulirashi sama da sau dari, shiga motar yayi yazauna yadau wayarshi 28miss calls yagani all daga Ammi, dan ajiyan zuciya ya sauke sanan ya shiga number Mom yay dialing, ringing daya Mom ta dauka tace "Dan Yaro haba kaiko yanzun nan Adda takirani akan kafita tsakar dare batasan inda kaje ba tana kira kuma baka dauka" dan murmushi yayi yace "wayan na mota ne, I will call her now, Mom are you at home"? "eh ina gida, da zama muzo gidanku ne nida Asma'u sunyi hutun makaranta daganan saimuje gidan suna" dan yatsine fuska yayi shiyama manta yaune suna, anatse yace "Mom karku fita please kijirani yanzun nan zanzo" yana maganan ya katse wayan yakira Ammi, ringing daya ta dauka kafin tai magana yace "Ammi am fine, gidan danakai su Mama Iyami Arham yaje tsakar dare suka kirani shine natafi" Ammi zata fara magana yace "nan bada jimawa bama zanzo bye Ammi, love you" yay maganan tareda katse wayan, tada motar yayi yafita cikin gari ya shiga ya nemo mata wani hijab dark blue yadi uku da aka dinka sanan yadawo yay cikin hotel din. Kofar dakin yabude hada ido yayi da ita tana zaune kan gado tadauki wani littafi tana kallo, tana ganinshi ta washe baki sanan ta tashi da gudu tai kanshi zata rungume shi, hannunshi yadaura kan kafadarta ya tsayar da ita yace "wait Pretty, come and wear this hijab lemme see you" yay maganan yana warware hijabin hannunshi yasaka mata, wani irin bala'in kyau hijabin yamata da saida ta tsaya yay shiru yana kallonta saikuma yaciro wayanshi daga aljihu yace "smile lemme snap u" murmushi tamai daya mugun lobar da dimple dinta ya dauketa hoto tai wani irin kyau, sanan yamaida wayan aljihu, silipas ya tsugunna ya ijiye mata kafarta ta zura tana dafamai kafada sanan yatashi ya kwashe kayansu tass da ba yawa ajakan boutique din kayan daya siyo mata sanan suka tafi, a reception ya tsaya yana rikeda hannunta kafin ta gudu wani wajen yay clearing all bill dinsu sanan suka fito, gaban motarshi yabude ya sata ciki yamaida kofar yarufe sanan yakoma mazaunin direba ya shiga tareda wurha kayansu baya yaja motar yamusu playing soft music a motar, juyarda kai tayi sai kallon hanya take tana kallon motoci kaman bata taba gani ba, shi abinma har mamaki yabashi yanda taketa kallon motoci da gari sai kuma yatuna all this while yaune rana na farko datake ganin cikin gari, ahaka har suka shigo anguwan su Mom, horn yayi agaban gidan aka budemai gate yaja motar cikin gidan yay parking ya kashe yafito. Zagayowa yayi yabude mata motar tafito ahankali tana kokarin rikemai hannu ta daure fuska yace "don't touch me" turomai baki tayi kaman zatai kuka yadauke kai da sauri ganin nema take tasa ya daburce tana wani turomai small pink lips dinta da har yanzu ganin yanda ya tsotsesu jiya yake. Gaba yayi da sauri yace "let's go" ahankali take biyoshi tana turo baki, kofa yabude ya shiga falon yajuyo yana kallonta har lokacin turomai baki take ta shigo dakin kaman zata burgeshi dan murmushi yayi yanajin wani shegen sonta a ranshi yabiye mata kwarkwancewa zaiyi kaman ita, kawai yasa hannu yamaida kofan yarufe ya shigo falon daidai Asma'u tafito daga dakin Ya Abdul asama data kaima coffee tana sanye da wata doguwan rigan atampa yellow itama batada kiba siriruwa ce kaman Widad saidai Wudad tafita tsaye dan ita doguwar mace ce , tana hango Waleed tawani irin kwala ihu. "Ya Waleed!" dagokai Waleed yayi ya kalli sama, dawani irin gudu Asma'u ta shiga saukowa daga stairs dan arayuwanta tanason Waleed yafiji da ita a family su gabaki daya. "oyoyo Ya Waleed" tana zuwa gabanshi tawani daka tsalle ta rungume shi tana murna sosai kaman anmata kyauta, Widad da tun lokacin datai ihu take binta da kallo ta tsaya chak tana kallon yanda ta rungume Waleed tana murna, ranta ne yabaci tazo gaban Waleed din hannu tasa ta fizgo bayan riganta da sauri Asma'u ta sauko daga jikin Waleed tana waigowa dan taga waye ya fizgota, da sauri Widad ta shiga gaban Waleed takama waist dinta tarike tana turoma Asma'u baki tana zaro mata idanu, mutuwan tsaye Waleed yayi yana kallon Widad din yama kasamagana, sai Asma'u data bita da kallo ne kaman zata cinyeta tana kallon Widad still tace "Ya Waleed wacece wanan kyakkyawan yarinyar? Sorry matan? Ko itane matan da Mom tacemin ka aura kasan har yau bantaba ganinta ba duk innazo hutu bansamu naje gidanka saidai wajen Ammi na, itane Ya matarka Ya Waleed"? Ganin yanda Widad tai tsayin daka a gabanshi har lokacin rikeda kugu tana hararan Asma'u yasa da sauri yaja hannunta yazaunar da ita akan kujera yace "sit down, she's my sister, her name is Asma'u but we call her Moxi, she is your friend kinji" makemai kafada tayi tana kallonshi idanunta sun ciccika da hawaye sosai kaman anbude pampoo, wani iri yaji saikuma yaji badadi yajuyo ya kalli Asma'u dake tsaye kansu yace "common kin isheni da tambaya aku, go call Mom kice mata nazo" gyadamai kai tayi tajuya da sauri ta tafi shikuma yajuya yamaida hankalinshi kan Widad dahar hawayen sun zubo da sauri yakai hannunshi kan idanunta yashare mata hawayen cikeda damuwa yace "don't cry please, she is just my sis, don't cry okay come here" yajawo kanta yasa a kirjinshi ahankali tasaki kuka harda tarin kuka abin ya mugun bashi mamaki sai duk yaji ba dadi, yashiga jijjigata, murya chan kasa ta yanda dagashi sai ita zasu dinga ji cikin harshen turencin wanda daman dashi kadai yake mata magana danshi kadai yaga tana fahimta yace "stop crying Pretty, I love you so much and you are the only one in my heart, I will never do anything that will hurt you, now clean your tears banso mutane suga kina kuka" yadagota daga jikinshi yasa hannu yagoge mata fuskar idanunta har sunyi jajir, daidai lokacin Mom tafito daga daki itada Asma'u dake bata labarin kyakkyawan yarinyar data gani tareda Ya Waleed, saukowa Mom tayi tazauna akan kujera tana kallon Widad tace "Dan Yaro harka iso" gyadamata kai yayi yace "good morning Mom" sanan ya kalli Widad yace "greet my Mom" ahankali tadago kanta murya chan kasa tace "good morning Mom" murmushi Mom tasaki tace "morning yarinya, yaya sunan ki"? Ahankali Waleed yace "batajin hausa, Mom please sata dakanki tabi Asma'u suje sama" sanan ya kalli Moxi yace "ki kaita dakinki, help her out tai wanka kibata kayanki zasu mata tasaka sai kizo kihada mata breakfast, mostly fruits tafisha sai yogurt batacin all this heavy food for now, Mom talk to her" yay maganan ahankali, tasowa Mom tayi tazo har wajensu ganin Waleed yadamu da ita tasan yarinyar must be very special, anatse takai hannunta ta shafa kan Widad cikin turenci tace "kibi Asma'u takaiki kije kiyi wanka kinji" juyawa tayi da sauri ta kalli Waleed gyadamata kai yayi ahankali sanan ta tashi, da sauri Asma'u tamika mata hannu tana murmushi tace "ke baki sona niko wlh bakiga yanda nake sonki ba, muje dakina kiga dakina kiga, inada abubuwa da yawa, kinga Ammi na tamin sababbin dinki jiya ta aikomin dasu nabaki daya cikinsu kisaka kema?" gyadamata kai Widad tayi dan tagane metace sabida da turenci tai maganan sukai sama binsu Waleed yayi da kallo harsaida suka bace sanan yajuyo ya kalli Mom da tuntuni kallonshi take, kafin ma yay magana tace "who is she?". 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 4️⃣3️⃣ & 4️⃣4️⃣ Shiru yayi yana kallon Mom kaman bazaiyi magana ba sanan yadan nisa yace "Mom I don't know" ahankali Mom tace "kaman ya you don't know who she is" shiru yasake yi kaman wanda ke tunani saikuma yace "Mom wlh da gaske I don't know who she is but Mom I love beyond much and I wanna marry her" kyar Mom kebinshi da ido ko kyaftawa batayi ganin maganar nashi da girma take, ganin yanda Mom ta tsareshi da ido yasa yace "an kawota gidan marayu ne about 10months ago, all this while tana admission bed ne sai kwanan nan tasami lafiya, before bata iya wani tafiyan kirki idanunta sun sami matsala and many more but yanzu tasami lafiya, kawai memory lost dinne shima due to cases din danaketa shiga kwanan nanne yasa ban daurata kan treatment dinba da tuni nafara" shiru Mom tayi tana sauraronshi tace "Waleed kasan mekake cewa kuwa? Yarinyar dabakasan waye itaba, bakasan daga ina takeba, yarinyar da bamata hayyacinta ne zakace kanaso? Kasan mekake fadi kuwa"? Shiru yayi shima yana kallon Mom din kafin ahankali yace "Mom you know me morethan Ammi, u were the one data rainen, you know me idan inason abu, Mom I love this girl and all I could think of right is moment is spending the rest of my life with her all other things are secondary, we can all handle it" yay dan shiru saikuma yabata labarin komi har zuwa abinda yafaru jiya da Arham yadauke ta yace "gwara na aureta na kilkace ta, na kula da ita duk tana karkashina, cus Mom inkinyi tunanin abin what if memory ta bai dawo ba? Haka zata cigaba da rayuwa batada kowa? Or babu wanda zai aureta harsai randa memory ta yadawo tafadi mana waye family ta, Mom I seriously love this girl saisa nafara tunkaran ki da maganan first inaso na aureta banma so idan kunsa rana yadauki tsawon month please kinji Mom" shiru Mom tayi danta itane batada matsala wlh, tasan ba'a bari ya auri ra'ayinshi da farko ba yanzu kuma yakawo she will support after all shi namijin mace hudu ne but Ammi zata yarda? Bayan ta aurama dan nata yar kawanta abundai da kamar wuya, maganan Waleed ne yadawo da ita daga dogon tunanin dataje. "Mom" dagokai ta kalleshi, murya chan kasa yana kama hannunta cikeda lallashi danta yarda yace "Mom please inaso yanzu ta zauna anan tareda ke cause I know Arham zai cigaba da neman ta, please Mom let her stay here har zuwa nan da nai magana da Ammi hopefully yau zan mata maganan kinji Mom" yay maganan ahankali akuma ashagwabe, ahankali Mom tace "naji zan rike maka ita, but Waleed dududu aurenka ko shekara daya chur ba acika da yiba karewanta ma yaune ake sunan danka shine zaka tado da maganan aure you are just 28 Waleed harzakai mata biyu karfa kazama namiji mai aure aure" murmushi yayi yace "Mom ni ko mace daya kacal ce zan iya rayuwana da ita inhar ina sonta sanan tanamin abin......" kasa karasa maganan yayi ganin Widad da Asma'u na saukowa daga stairs, Widad na sanye da wata atampa riga da skirt ash color da dark brown daya mata wani mahaukacin kyau, kayan sunbi jikinta tsaf kaman an aunata kafin adinga sun mugun fito mata da shape, Asma'u tamata daurin kallabi mai kyau daya bayyanar da gashin goshinta da gashin farko farkon kanta dasuka kwanta suna shinning, wani irin faduwa gabanshi yayi yaune rana da farko tun bayan randa aka kawota ajike dayake ganinta da kaya samadana asibiti, tai kyau ansaka mata dan kunne kaman wacce zatace gasan kyau, ko kallon Waleed dinma batayi ba sabida labarin da Moxi kebata da turenci datake ganewa sosai this is the first time datake fira dawata haka other than Waleed, ganin gabaki dayan hankali shi yayi akansu yasa Mom takara tabbatar wa cewan Waleed nason yarinyar kam sosai, ahankali tace "tashi muje kayi breakfast saika tafi wajen Ammi ka" tashi yayi Mom ma ta tashi duk sukai dinning, zama yayi kusada Mom yana satan kallon Widad din dahar lokacin hankalinta kekan Asma'u, gake deban mata fruit a bowl zata hada mata fruit juice mai madara. Bai wani iyacin abincin ba yature yatashi daga dinning, jiyayi duk ranshi yabaci ganin yanda gabaki daya hankalinta kekan Asma'u, tana wani kallon Asma'u kaman tasami TV, cikeda daga murya yace "am going Mom" da gangan yay maganan kota juyo, jin maganan shi yace he's going yasa da sauri tajuyo ta kalleshi ganin yamike yasa da sauri itama tamike tana kallonshi, daure fuska yayi yace "u are staying with your new friend" girgixa mai kai tayi da sauri tana shirin kuka ta zagayo ta inda yake da sauri tazo wurin shi zata rikeshi yadan zare mata ido alamun karta tabashi hakan yasa taki yakalli Mom yace "Mom bye" gyadamai kai Mom tayi tace "sai andawo" sanan yajuya ya kalleta yace "stay here don't go anywhere" yay maganan yay waje, duk abinta bata iya ketare abinda yace fashewa tayi da kuka takoma ta zauna akan dinning Mom dai murmushi tayi tacigaba dacin abincin ta Asma'u kuma tacigaba da lallashinta. Gida yakai yay parking motarshi, fitowa yayi sanin inya shiga bangaren Ammi bazai fitoda wuriba yasa yawuce direct flat dinshi zama yayi akan bed dinshi yadauki wayanshi yana kallo gabanshi nafaduwa, yasan Ammi zata iya bashi matsala a zancen auren nan, shikuma baison haka but ya tabbatar da inhar yafadima Uncle bazai taba jin kunyaba, ko mata dari yakeso Uncle is ready ya auro mishi, ciro number uncle yayi daga contact dinshi sanan yay dialing number, yana ringing aka kashe, murmushi yayi ko kadan Uncle bai daukan wayanshi wai International call ne za'a cinyema Waleed kudi saidai ya katse ya kirashi, yana cikin tunanin wayan ya shiga ruri, murmushi yayi yadau wayan yakai kunnenshi, cikeda wani irin shegen shagwaba yace "Uncle" Cikin wata irin murna dake nuna tsantsan kewa Uncle yace "My not so little son, how are you Boy"? Ahankali Waleed yace "Uncle I need something" Gyara zama Uncle yayi ya kalli mutumin baturen dake cikin office dinshi yace "excuse me please my son need me" tashi baturen yayi cikeda girmamawa yafita daga office din yarufomai kofa, hakan yasa Uncle yace "yes Son, talk to me" Dan jim Waleed yayi yana tunanin ta yanda zaifara gabatar ma da Uncle maganan daga farko sanan yace "Uncle there's this girl in my orphanage......." yabashi labari tatas sanan yakarake da "I really love her Uncle, but am afraid nai approaching Ammi, zata iya cewa bazan auri yarinyar da bamusan daga ina takeba" Cikin muryan Uncle data riga takoma na turawa yace "no, no, no Son, Ammi bazata iya cewa hakaba, love doesn't have anything to do with who you are or who are your parents, love has to do with two different souls da heart dinsu are connected, koma daga family mayu take ko family aljanu inhar kana sonta go for her, kai d'ana ne, my blood runs through your vein, family ba babu wanda bazasu iya aure aduniyan nan ba kodaga ina yarinyar take, kanadai sonta ko"? Murya chan kasa akuma kunyace yace "eh" Murmushi Uncle yayi jin kunya a voice dinshi yace "alright, yaushe kakeson wedding din should take place" Murya chan kasa kaman wani na kirki yace "banma so yakai up to 1month" Murmushi Uncle yayi yace "shikenan Waleed dina, once nabar office zan kira mahaifiyarka, take care of yourself okay, if you need anything just call me, koma menene, I've sent you gift din jikana Arham, ehen that brings me there, ya friend dinka Arham"? Faduwa gaban Waleed yayi ko kadan baiso yafadi ma Uncle abinda yafaru tsakanin su hakan yasa yace "he is fine Uncle" Gyadakai Uncle yayi yace "how do you want the wedding big wedding kakeso ko simple one"? Ahankali yace "I want it so simple banson any event ko taro, kawai daurin aure kadai nakeso" Anatse Uncle yace "is fine, bayan haka saikuyi signing marriage certificate" Gyadakai Waleed yayi cikeda gamsuwa. Uncle yace "will talk to you later son, bye I love you" Ahankali Waleed yace "I love you second Dad" Murmushi Uncle yayi ya katse wayan, Waleed yawani fada gado tareda daura wayan akan kirjinshi zuciyanshi tai fari kal, dan yasan tunda uncle yay na'am to kaman ya auri Widad ne yagama, tashi yayi yacire kaya ya shiga bathroom yayi wanka, fitowa yayi ya shirya cikin wani 3-quarter yasaka farin singlet ya feshe kanshi da turare sanan yazura silipas yafito yay flat din Ammi. Babu kowa a falo sai TV dake aiki hakan yasa yay sama, bude kofar dakin Ammi yayi cikeda farin ciki yana kallon Ammi dake kallonshi tana zaune kan kujera rikeda system, murmushi yayi yamaida kofan yarufe yakaraso inda take zaune, hannu yasa yadauke system din ya ijiye akan gado yace "Ammi system dinan baisan nan cinyanki wurina bane" murmushi Ammi tayi ganin yana cikin nishadi ya zauna kusada ita tareda rungumeta ta side yace "oyoyo Ammi na good morning" "morning Son, yau sunan danka, kako kirasu" girgiza mata kai yayi yace "no sai anjima da yamma" gyadamai kai tayi tana kallonshi kaman maison karanto abu a fuskarshi, dauke kai yayi da sauri yatashi yadauko system dinta yadaura kan cinya shi yace "aikin me kikeyi Ammi natayaki" hannu Ammi tasa ta karbe system din ta ijiye gefenta tace "talk to me Waleed, there's something strange about you today? Why this sudden happiness kaida kake cikin kunci, menene ke faruwa dakai eh Waleed dina?" shiru yayi yana kallon fuskarta ba abin yafada mata bane tahau mai bala'i gwara Uncle yafadi mata saitamai bala'in inzata iya, kuma once uncle yace sai danshi yay auren sai yayi. "Son" Ammi takirashi ahankali tace "menene?" dan jim yayi saikuma yace "aure nakeson nakara Ammi zaki yarda"? Wani irin kallo Ammi tamai irin kallon mehaka kake cewa kaman wani mara hankali, dauke kai yayi yamaida kanshi kan TV dakin yace "daman nasan bazaki taba yarda ba, bazaki taba barina ba, saisa nakira Babana nafadamai" wani irin kallo Ammi tamai tace "Waleed in the middle of crisis, kana cikin matsalolin nan an kwace ma gidan marayu shine all you could think of shine kara aure, are you even okay" cikin wata irin cool voice yace "Ammi aure nakeson nakara, please" yay dan shiru sanan yace "Ammi I don't wanna go into details dake but please Ammi aure nakeson nakara ki barni, at least my first marriage namiki abinda kikeso yanzu ki barni na auri wacce nakeso kinji" cikin dan kakkausan murya Ammi tace "Waleed do you even realise you are just 28 ko 29yrz bakakai ba dahar zaka ijiye mata biyu, angayamaka kanada karfin ijiye mata biyune" cikin yanayin dan fushi yace "Ammi nifa namiji ne shine kuma banda karfin managing two wives, Ammi I love her kinji, kina hanani wlh zan iya mutuwa" wani irin kallo tamai irin na yaronan lafiyanka kalau kuwa, hannunshi yamika ahankali yakama hannunta sanan ya shiga bata labarin komi na Widad har zuwa abinda yasameta jiya da daddare, sosai jikin Ammi yay sanyi, Waleed yace "Ammi what if kece kika haifeta, can you imaging me in this life datake ai zakizo ataimaken ko, Ammi that girl needs care, banda haka ina sonta Ammi so sosai, please Ammi inhar kinasona dagaske ki yarda kika yarda ni kinmin komi dan girman Allah Ammi" yay maganan yana rokonta, ganin seriousness din dake idanunshi da tsantsan sonta, dakuma tausayin yarinyar dataji tanaji yasa ta sauke ijiyan zuciya, ahankali tace "Waleed inhar bantayaka son abinda ka kawo kace kana soba menayi, kawai kaga ukuba da dama ne ciki harda Arham, karyazo Arham yaturo yarinyar tama wani abu, but tunda kana sonta shikenan zan kira Mom takawo yarinyar nan itada Ma'u duk saisu zauna anan inyaso saita dinga zuwa islamiyyan su Ma'u, Wata daya za'a saka shima sainai magana da Baffan ka kome yace haka za'ayi" wani irin fadawa jikin Ammi yayi sanan ya manna mata kiss a goshi yace "I love you Ammi thank you" ahankali Ammi tace "but da sharadi" da sauri ya gyara zama, Ammi tace "banson kana zaman gida, zakaje kadinga min managing company na for now harsai an maidamaka da gidan marayun ka, sanan zaka koma chan gidanka, kaje ka gyara inda zaka gyara amaryanka, inhar Amaryanka na nan bazaka dinga zuwamin gida anyhow ba, kaida ka kara ganinta dagayau sai in ankaita gidanka" da sauri yace "na yarda Ammi" dan acewanshi ganinta inhar tazo gidan Ammi abu mai sauki ne, murmushi Ammi tayi tace "kasami lokaci kaje kasami Ilham kafadi mata sanan kamata kayan fitar kishiya, kazama mai adalci" dan shiru yayi yana tunani sanan yace "Ammi is a simple wedding, banson any taro, zan mata kayanta na ijiye mata inta dawo daga wanka I will te her Ammi" shiru Ammi tayi tace "tadaiji daga bakinka, ina zuwa bari naduba yan aikina nasasu min aiki" tai maganan tana tashi daga kan kujera tafita daga dakin, wani irin tsalle yayi kaman dan yaro yafada gadon Ammi, he never knew haka akeji idan zaka auri love of your life, all this excitement baijisu ba dazai auri Ilham ba sai yanzu, da Ammi ta yarda kaman an bashi kyautan kujeran makka. Washe garin ranan Mom da Asma'u da Widad sukazo Waleed baya gida dan tun safe Ammi takadashi company ta, sosai Ammi tadinga kallo Widad da saida Mom tasata ta gaida Ammi ta gaidata sanan takoma wajen Asma'u dake zubamata uban surutu kaman gidan radio, sun dade zaune afalon sanan Ammi ta tashi tai sama Mom tabita, dakin Ammi suka shiga Mom biyeda ita, zama Ammi tayi kan gadon Mom ma tazauna tace "kinga yarinyar ko? Batada matsala Adda, komi sai wanda ka koyamata zatayi and nalura she is very sharp, yau Asma'u na koya mata karatun Al'qur'ani tacigaba dayi da kyau, wlh dadin muryanta saida yasa nafito daga dakina da asuban nan na shigo dakinsu, kinga abubuwan data iya kuwa, magana ne kawai bata waniyi saida Asma'u, but she is good Adda" ajiyan zuciya Ammi ta sauke tace "indai Waleed na sonta shikenan, yarinyar namin yanayi da...." Ammi tai shiru bata karasa maganan ba da sauri Mom tace "dawa take miki yanayi?" dan yatsine fuska Ammi tayi tace "never mind kawai raina ke kirfamin hakan, but basa yanayi, zan baki kwangilan akwatin ta kinji afara shirye shirye, kima mai gyaran jikin nan magana" gyadamata kai Mom tayi tace "angama Adda" sosai suka dade sai plan suke, sai wuraren magrib ta tafi sukuma Ammi tabasu hadadden daki. Wasa Wasa lokaci ke tafiya, time to time Waleed ke zuwa yaduba Ilham da little Arham dudda har yanzu bai gayamata cewan zaiyi aureba, yayinda rabonshi da Widad tun ranan dayabar gidan Mom, babu yan dabarun dabaiyiba akan zai ganta amman Ammi tahana, Widad sai gyara takesha, yanzu tana dan hira sosai, ta mugun sabawa da Asma'u, akwai randa Asma'u taje gida tadawo batajeda Widad ba sabida shegen ciwon maran datake yi dahar saida Ammi tasa aka kawo mata maganin ciwon mara tasha, Asma'u nafita tadinga rusa uban kuka Ammi nata kallonta, kaman ranan tafara ganin yarinyar, charisma din yarinyar na nuna kaman yar baBban gidace sanan tanada shagwaba, da kyar ta samu ta lallasheta ajikin Ammi tai bacci. Sannu sannu ance bata hana zuwa, yau dududu bikin Waleed da Widad saura 5days yau, dudda wedding din low-key wedding ne bai hana family fara shirye shirye ba, Ilham itama anata bangaren tanata shirye shiryen fitan arba'in. Wanan kenan 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 4️⃣5️⃣ & 4️⃣6️⃣ Tana zuwa gaban gate din gidan marayun Arham aka bude mata gate kaman ansan dazuwanta, shiga ciki tayi tana kallon gidan marayun tana mamakin yaushe Arham yabude gidan marayun shi, tana shiga taganshi tsaye akan hanya yana sanye da wani dan 3quater na common flag light blue da dark blue sai wata light blue t-shirt ajikinshi, yay wani irin kyau har haske yayi kana ganinshi kasan kudi sun soma zauna mai, rage gudun motar tayi shikuma yanuna mata inda zatai parking sanan yabiyo ta abaya, karasawa tayi tai parking daidai yakaraso yabude ta side din da yaron yake yadauki baby sitter da yaron ke ciki yana bacci ya tsaya kuri yana kallon yaron, harta rufe motar ta zagayo ta bangarenshi kallon little Arham yake, wani irin kayataccen murmushi yasaki sanan yadago ya kalli Ilham din, dan yatsine fuska yayi cikeda yanga yace "let's go" yay gaba yana rikeda yaron itakuma tana biyedashi abaya, bude kofar office dinshi yayi ya shiga itama ta shigo sanan yabude uwar dakan office din ya shiga yakarasa kan gado ya ijiye baby sitter sanan yajuyo daidai lokacin Ilham tashigo office din wani irin fizgota yayi ya maida kofan yarufe sanan yabugata ajikin kofan, wani irin murmushi tayi tace "wanan ne oyoyon" hancin shi ya goga kan kuncinta yace "I am horny" yay maganan yanakai hannunshi zip din bayan riganta ya zage sanan yacire rigan ya yar yarage daga ita sai bra, boobs dinta ya kafe da ido dasukayi tima tima, ahankali takai hannunta saman wandonshi tai grabbing manhood dinshi dahar yatashi tace "I miss you badly Arham" bakinshi yakai kan nata yashiga kissing dinta ahaukace ta shiga maidamai da martani sukama kansu tsirara, sanan ya dukar da ita ya shiga zuruf yaji ya shige shi kawai ko kadan baijinta kaman da lokacin tana Amarya harji yake kaman bazai iya fitowa ba sabida yanda take amatsaye, he fucked her dirty kaman wata slave dinshi tasha maruka jin zai kawo yasa ta hankadashi tace "please Arham ban riga nakoma asibiti six weeks check up ba asakamin implant na family planning, dan girman Allah karka suna ciki" wani irin fizgota yayi yana kama wuya ya danneta yatura ciki yace "ina mijinki kike gayamin karna juye sperm dina acikin ki menayi kenan" yay maganan yana wani dannawa ciki sperm din nazuwa yay amanshi acikinta sanan yadagata ganin Arham na mutsu mutsu yatashi yaje gadon daukan yaron yayi sanan ya kalleta ganin ko motsi bata iyawa yace "xonan kibama d'ana nono" kasa ko motsi yayi hakan yasa yadaka mata tsawa yace "bakiji ba" da sauri ta tashi yabi jikinta da kallo da katon cikinta dabai riga yakoma ba ranshi nabaci tazo ta zauna gefenshi karban Arham din tayi tashiga bashi nono yana kallonta yaja wani tsaki, dago idanunta tayi tace "wai menene baby?" cikin fushi yace "my god just look at you, duk kinbi kin dawo tsohuwa, fat belly, stretch mark ko ina ajikinki, wide pussy kinyi baki kaman bakeba" kuka ne yazo mata tadaure tace "Arham kataba ganin mace ta haihu tadawo yanda take ada? Stretch mark dole nasame su sabida ciki na dauka na wata tara yasa nai kiba, baki kuma ruwan zafin jego ne, kace am wide anfa yimin dinki babu wani wide ai da kyar ka shiga" tai maganan tana share gutun hawayen dayazubo mata, cikin fushi yace "look is one thing, koki gyara kanki kidawo min yanda kike da kona samo alternative, ga matanan birjik gidan marayun nan, nonuwan su da jikinsu daidai, pussy su tsukakke kenifa I hate wide pussy bayida dadi bazaki gane bane" at this point kasa daurewa tayi tafashe da kuka tace "Arham wai mesa kakemin wulakanci ne, daba haka kakeba, kasoni d'a, sai yanzu ne zaka faramin wulakanci bayan nariga na haihun maka eh" ganin yanda take kuka yasa yatashi yace "my friend sa yaron nan bacci kizonan and ride me, ban kiraki dan kizo kinamin kuka akai ba" yay maganan irin ko ajikinshi dinan, gama ba Arham nono tayi luckily for her yakoma bacci ta ijiye shi duk Arham na tsaye yanashan madara yana kallonta, tashi tayi ta dauki riganta cikin fushi ta shiga sawa sanan tadau skirt zata saka yawani irin fizge skirt din yace "where do you think you are going?" cikin fushi tace "baruwan ka but I must tell you this Arham nai nadaman saninka harna biyemaka wlh, nai nadama cus u are nothing but a cheat" da sauri yanuna kanshi yace "ni kika kira da cheat?" gyadamai kai tayi tace "ankira din" ta fizge skirt dinta daga hannunshi takarasa saka skirt din tana yafa mayafinta zata dauki Arham karami dake kan gadon yace "you can go amman ki ijiyemin d'ana tunda badaga buran ubanki yafito ba" wani irin juyowa tayi ta kalleshi idanunta sunyi jajir, gyadamata kai yayi yace "kitafi bazan taba hanaki tafiya ba wlh but kibarmin d'ana tunda bake kikama kanki cikin ba, after all nan gidan marayu ne akwai thousands dazasu kulamin dashi, so leave him akan gadon ubanshi kifitan min daga office" wani irin rushewa da kuka tayi ta zube akasan wajen tace "Arham ni, ni Ilham dinka kakeson katonawa asiri, nakoma gida ba yaron nan kasan irin tambayoyin dazansha kuwa? Arham is it a crime to love you? Ni ni Arham dake sonka ne kakemin wanan wulakancin ni eh" tasake rushewa da kuka tsaki yaji irin ko ajikinshi dinan yakara tittila yogurt akofi yakai bakinshi zakisha yace "ki gama kuka kifitan mini daga office, wawiya" rushewa dawani irin kuka tayi kaman ranta zai fita, ganin kukan bazai fusheta ba tai kneeling agabanshi tahade hannayenta tace "Arham in kanama Allah kabarni natafi da yaron nan karka sani a matsala, Arham nine fa Ilham dinka, wacce kafara gani ranan bikin ta kadinga kallona, Arham nine fa Babyka dakake ji da ita, kana kishina, katuna yanda mukai making crazy love a Yankari? Do you remember yankari Arham? Dan Allah kayakuri kaji Arham wlh kome kakeso zan maka" gabanshi ya nuna mata dake amike har lokacin sanan yadaga cup din yogurt din dake hannunshi yajuye akai yanabin siririyan joystick din yace "come and leak yogurt dinan tass and ride me afterwards, satisfy me dawanan wagegen gaban naki saiki daukeshi kubarmin office" yay maganan yana dada kwarara yogurt din kan gabanshi gabaki daya harda uban gashi dake wajen dabai aske ba, amai taji yana taso mata amman ta daure zata taho yanuna jikinta yace "tashi kicire kaya first" tashi tayi tacire kayan yana binta da kallo ganin yanda nonuwanta suka fara kwantawa sanan ta taho ahankali tai kneeling agabanshi tafara lasan yogurt din gabanshi yana wani jin dadi yana bankarewa, saida ta lashe tass sanan yasa tahau kanshi ta shiga riding dinshi yana zaune akan kujeran ya babbaje hannu kaman wani sarki yana jujjuya idanu, har kafanta yay tsami da riding dinshi datake bai tausaya mataba saida at a point takasa lifting kanta up sanan yawani bugata akasa yabita yamata kacha kacha yakawo sanan yabarta, sai kuka take dan tun tanajin dadi harta fara jin zafi at a point saitaji kaman yanason ya barka inda aka dinkamata ya warke ne, saida yagama tass sanan yatashi yabude bayi zai rufo kofa yajuyo ya kalleta yace "dau yaronki ki tattara kibarmin office dina, zan fita" yay maganan yana maida kofa yarufe tashi tayi da kyar idanunta har kumbura sukayi sperm dinshi nabin cinyoyinta bata damuba ta nemi pant dinta tasaka ta saka kayanta tass tayafa lullubi tadan jawoshi gaba sanan tadauki Arham karami daga baby sitter tadau car key dinta tafita daga dakin, tafita daga office dinshi, cikin sa'a bata sami kowa a premises dinba tawuce ta shige mota taja tabar gidan. Fitowa daga bayi Arham yayi yanajan tsaki har lokacin abunshi bai kwanta ba, ko kadan Ilham bata gamsar dashi ba dan tabude dayawa kuma wlh koma menene saiyaci tsukakkiyar mace yau dinan, yana tunanin haka yazura kayanshi yakama abin da boxer yawuce yafita daga office din direct hostel din mata da bai ijiye wata babba dazatana kula dasuba, bude gate yayi ya shiga ga yan mata yara da manya birjik a tsakar gidan ana wasa ana hayaniya ana ganinshi akai shiru tsit kaman ruwa yacisu. Daga Gate yabisu da kallo yace "ina Farida Hassan" da sauri aka shiga kwalama Farida Hassan kira dake chan sama a dakinsu, fitowa tayi da sauri tana daure da zani akirji dan daga wanka take, tana ganin Arham kunya yakamata maida kanta tayi kasa shima ya dauke kai tareda daure fuska yace "kizo office dina inkin shirya wasu nason suyi adopting budurwa kiyi sauri" yana magana yafita da sauri itakuma takoma ciki ta shirya tsaf tasa hijabin gidan marayunta tafito sanye da silipas, tai hanyar office din Arham din da saurinta tana zuwa tai knocking daga ciki Arham yace "come in" bude kofa tayi ta shiga ta maida kofar tarufe tana kallon office din ganin bataga kowaba, binshi da kallo tayi harta tsaya gaban table din ta Ahankali tace "ina wuni" murmushi yamata yace "an Farida na, kinga kudadenku da kayan danasayo miki naki daban ko" gyadamai kai tayi tana murmushi, shima murmushi yayi yace "an Farida na kenan duk godiya ce na abinda kukamin kuka fito kuka nuna Waleed yamuku fyaden, karki damu kome kikeso kizo direct kifadi mini zan miki" murmushi tasakeyi adan kunya ce arayuwanta tanason Arham dan duk inda yaganta yadinga mata wasa kenan yanace mata an Farida saisa ma ta yarda tama Waleed shairi daya kirata awaya yafadi mata tayi zai bata kudi itada kawayenta, murmushi yayi yace "zauna mana an Farida" zama Farida tayi tana murmushi akunyace, tashi shikuma yayi yana murmushi kaman wani bawan Allah yabude fridge yadauko wani maltina mai sanyi yamaida fridge din yarufe yadawo ta inda take yawani irin ijiyemata malt din tareda bude mata yace "sha maltina mai sanyi An Faridan Arham" wani irin lullube fuskarta taida hijabi cikeda kunya, zama yayi akan kujera yace "sha mana An Farida na, I said sha, banson wanan kunyan nan fa, saki hijabin ki dauka kisha yauwa" sakin hijabin tayi tana murmushi tamika hannunta tadauki maltinan takai baki tashiga sha dan rabonta da drink tun agidan marayun Waleed, binta yayi da kallo yana tabe baki aranshi yace da ace badan gidan marayu ba irin yaran nanne ke sauda dafaffiyar masara akasuwa, saida tashanye tass ta dire, murmushi yayi yace "in karo miki ne" girgixa mai kai tayi tana share bakinta da hannu, dan murmushi yayi sanan ya gyara murya yace "kinsan mesa nakiraki" girgixa mai kai tayi yace "nakiraki ne sabida banga wata natsassiyar yarinya mai hankali da aji ba agidan marayun nan irinki Farida, saisa naji zuciyata ta aminta dake, nasan kawayenki zasu dinga kishi dake amman kin riga kin wuce su kinfi karfinsu, inaso naji daga bakinki ne zaki aure ni An Farida na?" wani irin zaro idanu tayi takai hannayenta kirji dan faduwa gabanta yayi sosai bata taba zatan abinda zai gayamata kenan ba, yanzu wanan hadadden Mr Waleed dinne zai aureta yar bakan nan da ita mummuna, wai mafarki takeyi ne, kara gyara murya Arham yayi yace "bakice komiba matas sonake ki amince, kina amincewa zan fita sallan magriba ana idarwa za'a daura mana aure anjima bayan isha'i ki shigo turakan mijinki nan office zakizo eh matas, ko ba'aso nane"? Hijabinta tasa tarufe fuskarta cikeda kunya tana girgiza mai kai, wani irin murmushi yayi yana hararanta yace "tokin yarda" gyadamai kai tayi da sauri tana murmushi, Murmushi shima yasakeyi yatashi yaje fridge tunda ya lura mayya ce, saiya dauko babban exotic mai sanyi yabata yace "to tashi kitafi amaryata, karfa kifadima kowa dan kawayenki kishi zasu dingayi dake, dagani saike saikuma mutanen masallaci, dauki juice dinki kitafi matas" cikeda wani irin dadi tadau juice din tafita hartana rangwada, binta yayi da kallo sanan yatabe baki yace "yama akayi banyi tunanin abunba na tsaya inata tunanin baturiyan nan, amman dai ina mugun sonta ita, yanzu dai haka duk zanbi yaran nan na moresu son raina" yanacikin magana yaga wayarshi na ringing ya kalli wayan ganin Mama ne yasa yadanja tsaki metake damunshi, tun ranan data haushi da duka yabar gidan bai karabi ta kansu ba, tanata kiranshi baya dauka abin duniya yataru yamata yawa, akaro na uku yadauki wayan yakai kunne kafin ma tai magana yace "Mama wai menene kin gama dukana kan Waleed yanzu ma kin kirani ki dakenne ta waya ne, ni sai anjima kije ki kira danki Waleed wanda yake baki kudi" Mama nakokarin mai magana ya katse wayan abinshi yatashi yafito yana kara duba gidan marayun baida ma'aikata enough he need them, haka yadinga yawace yawacen shi har aka kira magrib yawuce ya shiga yana murmushi dan yasan for Farida mind an daura mai aurefa da ita ko, saida akai sallan isha'i sanan ya aika wani ma'aikacin shi yaje yakiramai Farida sanan yawuce office dinshi, yana zaune a office dinshi tabude kofar ta shigo tana sanye dawani jan hijabi mai kyau, jikinta sanye da atampa riga da zani sabo fil cikin kayan dayasiya mata, fuskarnan tadau hoda dajan janbaki, murmushi yayi yatashi da sauri yace "Amarya na barka da zuwa" yay maganan tareda kaimata wata kyakkyawan rungumo saida ta sauke ijiyan zuciyan dashi kanshi saida yaji, yatsine hanci yayi aranshi yace "wawiya" sakinta yayi ya kullo kofar office din sanan ta shigo yakama hannunta yarike yace "muje turakan mijinki kiga" yay maganan yana bude uwardakan shi daya gyara suka shiga ciki, zaunar da ita yayi akan gado sanan yakai hannunshi yakama goshinta kaman da gaske yace "ubangiji Allah ya sanya miki albarka, Allah ya albarkaci auren mu yabamu zuri'a dayyaba Farida ina sonki dayawa kinji, kina sona matata"? Gyadamai kai tayi akunyace yasakin mata murmushi, sanan yace "bazaki tube hijabin mijinki yaga kwaliyar kiba" akunyace takai hannunta ta cire hijabin, ga dinkin nan yafito da ita rass kaman wata yar budurwan kauye, kirjinta acike ba laifi, tashi yayi ranshi fess da dadi ya kashe wutan dakin babu maganan bama sabuwar Amarya kaza sanan yadawo kan gadon yatsaya agaban gadon yatube kayanshi tsaf burinshi kawai ya kwakuleta sanan yazauna akan gadon yakama hannunta ahankali yace "Farida na, inaso ki gayamin menene hukuncin matar da mijinta yakirata shimfida taki yarda da aka ga yamuku a islamiyya" ahankali tace "mala'iku na tsine mata hargari yawaye" gyara murya yayi kaman wani mutumin arziki yace "Farida yau zamu hada shimfida daya, ma'ana zan sadu dake matata kuma halaliyata, kituna babu kyau bayyana sirrin mijinki ga kawaye dan haka kar wani yasan mun kwana tare harma mun sadu kinji Matata ta sunna" gyadamai kai tayi, ahankali ya juyar da ita yaja zip din riganta yacire rigan ya yar sanan yadagata ya kwance kullin zanin da kyar ya jefar shima, yakai hannunshi bayan bra dinta ya kwance sanan yajuyo da ita yakai hannunshi kan kirjinta jinsu acike yasa yace "masha Allah, Allah yayima matata baiwar dukiyar fulani, tsugunna kiga" tsugunnawa tayi ahankali ware kafanshi yayi yakama kanta yakai joystick dinshi bakinta yace "tsotse ta" rawa jikinta yadauka amman ko ajikinshi burinshi kawai yasha dadi tadinga sha saida yaji yana neman kawowa sanan yadagata yajefata kan gadon batare dayabi takan wasa da ita ba ya barka pant dinta, haike mata yayi kaman yasami wata jaka bako tausayi tun tana daurewa harta fara kuka dan bata taba sanin namiji ba sai ranan, jaga jaga Arham yamata dan yajita amugun tsuke abunku da virgin, saida yaga tana neman suma sanan yabarta ya kwanta ranshi fess ko damuwa da kukanta baiyi ba araina nace Allah yakara, Alhakin Waleed yakamaki Farida, saura su bakwai din dasuka rage. Wuraren asuban fari ya farka yatabata jin tana numfashi yasa ya bubbugata tabude ido rass sanan yasake koma mata shifa bai damuba koda ace zata mutu yanzu batada uban kowa dazaiyi kuka akan mutuwanta to shine gatansu, hakanan zai dinga kashe musu kudine bazai mori gabansu ba, yau da daddare ma wani auren zaiyi, Hassana zai auro dan yaga yarinyar akwai botsareren duwaiwai, saida garin Allah yawaye tass sanan yasaketa ya sauka zai shiga bayi yace "tashi kitafi hostel dinku kiyi wanka Amarya ta, nabaki kwana uku ki warke arana nahudu zaki shigo turakata kinji, kuma ki gyara tafiyan ki inkin fita" gyadamai kai tayi ahankali shikuma yawuce yashiga bayi aranshi yace "fool" Tashi tayi tadau kayanta tasaka da kyar tasaka hijabin ta sanan tawuce tafita idanunta har kumbura sukayi sabida tsabagen kuka tai hostel dinsu sai kallonta aake amman ko kallon wata batayiba, ruwan zafi tadeba taahiga bayi tai wanka tsaf tai tsarki da ruwan zafi sanan tafito adaddafe tai sallan safe ta kwanta sai bacci. A ranan haka da daddare exact abinda yama Farida yama Hassana yace andaura musu aure, yabi yay ragaraga da Hassana dan ita har suma saida tai ahannunshi, kuma duk wacce tadawo bata fadin abinda yafaru kowacce najin kanta as matar Mr Arham. ***** Ilham nakomawa gida a falo taci karo da Mummy, Mummy na ganinta tace "ke lafiya meya sameki kikasha kuka haka kinga idanunki kuwa?" murmushi ta kakalo zatai magana saiga wani kukan dan abinda Arham yamata ya tsaya mata arai tafashe da kuka sosau, salati Mummy tasaki ta karbi little Arham tana dubawa tace "wani abune yasami Arham baida lafiya ne kike kuka haka"? Mummy tai maganan tana duba Arham ganin lafiyan shi kalau yaroma bacci yake abinshi yasa tace "lafiyan Arham kalau, ke Ilham maiya sameki haka kodai Salima ce ba lafiya innalillahi" da kyar ta iya tahana kanta kuka ta shiga share fuskarta sanan tace "Mummy hatsari akai agabana matar da aka buge tarasu" kaman Mummy zatai kuka tace "Haba shine duk zakibi ki tayarmin da hankali? kinga wuce kije kiyi wanka bari narine miki Arham, tafi kidena kuka, Allah ya jikan matan" gyadama Mummy kai tayi tawuce dakinta tana shiga, tai kuka tai kuka tai kuka harta godema Allah, tai dana sanin 17m din data turamai, da tara kudaden datake bama Arham take daya isheta gina company, gashi yaci kudinta ya cuceta ya maida ita banza, yasa tadauki cikinshi tahaihun mai sanan yabarta, jibidai yanda yau yamata kaman yasami akuya, wulakantaccsn sex yay da ita, wlh tai dana sani, ga mijinta Waleed yaro karami nagari, ga kudi ga komi amman shaidan yarude ta tabi Arham da baida komi, iya sex dinma wlh bakai Waleed ba, girman joystick dinma baikai Waleed ba, tasan Waleed doesn't fuck her frequently but at least duk randa zaiyi saita jita ta koshi but tabiyema Arham dayakaita yabaro ya cuceta, kuka tayi yafi na awa, saida taji Mummy zata kawo Arham dake kuka sanan ta tashi da gudu tawuce ta shiga bayi. ****** Wani irin mahaukacin kewan Widad Waleed yake kaman zai zauce, he thought abune da zai iya jurewa but at this point yaji patient dinshi yakare, yau duka duka bikinsu saura kwana biyu haka kuma yaune ranan da Ilham zata dawo gidanta dan tagama wankan jego. Daga company Ammi yafito around 10AM nasafe dan wani mahaukacin wutan son Widad ne ketaso mai yau koma mezai faru saidai yafaru wlh saiyaga his wife to be koma me Ammi zatamai, shiga motarshi yayi yaja wani soft music natashi daga cikin motar harya shigo anguwan su. Tun kafin yakaraso gaban gate din gidansu idanunshi ke kyam gaban gate din, hango Widad dayayi tana tsaye gaban gate din sanye dawani pitch lace dayabi jikinta an mata dinkin riga da skirt sai wani dan mininin mayafi akanta da ake ganin duka gashinta dan babu dan kwali akanta tana tsaye dawani saurayi dake jigine dawani hadaddiyar faran mota yana mata magana yana wani irin kallonta itakuma tana wani mishi cool smile daya lobar da all dimples dinta, wani irin bugawa da kirjinshi yayi saida yasa yataka wani mahaukacin burki nesa dasu, tunda yake baitaba jin irin abinda yaji dayaga Widad dawani ba aranshi akan wata y'a mace ba aduniyan nan saiyau, wani irin@ mahaukacin zuciyane yadebeshi baisan lokacin daya dirko daga motan ba yay kansu, yanda yake tafiya ma kadai abin tsoro ne yay kansu. 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 4️⃣8️⃣ Ko minti biyar baiyi da fita ba saiga yan aikin da Ammi ta aiko mata dashi, murmushi tayi taji hawaye nazuwan mata mema take tunani tanada mother in law maisonta haka taje tawani biyema Arham dat use her to make money yagina gidan marayun shi, fita tayi tabama mai rainon Arham tace "achanza mai kaya agoyashi, inya tashi saiki kawomin shi yasha nono, muje kiga dakinshi" tai maganan tanayin stairs mai rainon biyeda ita itakuma yar aiki ta zauna akasa afalon tana jiran fitowarta abata nata aikin. Fitowa yayi da motarshi gateman yarufe kofar gidan, wayarshi yaciro daga aljihun shi dayaji tai karan notification, duba notification din yayi yaga notification ne na Mama food stuff drugs and what have you, wanan notification din tuntuni yake wayanshi duk karshen watan duniya yake mata cefane, ko tunanin Arham bai kawoba dan koda Arham koba Arham Mama yadauketa amatsayin mahaifiyarshi ce kuma har abada he will always see her that way nomatter what Arham did to him, tada motar yayi yana fasa zuwa office din wani pharmacy yaje yasayo mata yan magungunan ta sanan yawuce wani supermarket, ya lodo mata kayan abinci aka jeramai a boot sanan yawuce har anguwan su, yana zuwa yasami yaran anguwan as usual suka 000 shiganmai da kayan ciki suna murna suna fitowa yamusu kyaututtuka sanan yawuce ya shiga cikin gidan yana tafiya ahankali, sallama yayi ya shiga falon daidai Sadiya tafito daga corridor idanunta sunyi jajir sun kumbura suntum tana zuwa takarasa gabanshi harda dan gudunshi ta tsugunna agabanshi sai kuka abunku dayar kauye, anatse yace "Sadiya menene lafiya kike kuka haka? Maiya faru" kafin ya amsata yaji muryan wata mata dabai wayetaba tace "au zuwa kikayi kinamai kuka ko Sadiya keda akace ki shigo dashi" dagokai Waleed yayi ya kalli matar yanda yaga kamannin matar da Mama yasa yagane kanwar Umma ce itace mahaifiyar Sadiya, cikeda girmamawa yace "ina yini Umma" murmushi Maman Sadiya tayi tace "Waleed shigo kaji kekuma ki tashi ki kawomai abinsha" bin gefe Waleed yayi yashiga ciki har zuwa gaban dakin Mama, Maman Sadiya tabude kofa ta shiga Waleed yabiyota ciki, Mama yagani kwance kan gado kafar damanta ya kumbura yay suntum tundaga kan dan yatsa har zuwa cinya wando daya da rabine ajikinta kafar hagu ne dogon wandon shikuma na dama aka yake kafar, daidai gwuiwar kafar daman ta baya yafashe ruwa na fita, gabaki dayan Mama tafice hayyacinta ta rame tana kallon Waleed din dayama kasa motsi tsabagen shock tana murmushi, hannu tamikamai alamun yazo sanan tace "zo Waleed dina, zo karkaji komi kaji karkaji tsoro, bayamin wani ciwo kumburi ne kawai" cikin wani irin kuka Sadiya data kawo lemu a tray tana bayan Waleed tace "wlh karyane, Ya Waleed kafar Mama ciwo take na fitan hankali, kafan yafara mata zugi har suma takeyi tafice hayyacinta, taki bari akaita asibiti waisai Arham yazo inbaizo ba haka zata mutu adakin nan, takishan magani, abinci ma wani zubin sai Umma tamata dure takeci, mun kira Arham amman baya dauka koyama dauka baya sauraran mu yake kashe wayan, tun ranan dayamaka wulakanci Mama tamai fada yabar gidan bai kara dawowa ba amman Mama nason kashe kanta kanshi bayan tasan baidamu da itaba bazai dawoba" Sadiya takara rushewa da kuka itama Maman Sadiya kasa daurewa tayi saikawai tabi ta gefen Waleed tafita tana kuka dan batason tai kuka agaban yayar tata. Ahankali Mama tace "zo Waleed, taho" ahankali Waleed ke daga kafarshi da bayajin shike iya motsata ba haryakai gaban gadon wani irin zubar da guwiwan shi yayi agaban gadon cikin wani irin muryan fada dake rawa sosai yace "Mama bakida......d....da....lafiya maisa baki kirani nazo ba, kinada number na namiki saving ta yanda kika gane kina kirana dashi, maisa bakisa ankirani ba Mama kika zauna da ciwo look at your leg, maisa baki kirani ba, eh......eh Mama"? Hannunshi Mama takama tarike gam takara kakalo murmushi tace "Waleed bayan duk abubuwan da d'ana yamaka na yaudara da cin amana kunya bazai taba iya barina nakiraka ba Waleed kayakuri" girgiza matakai Waleed yayi hawaye yazubo daga idanunshi haka Allah yayishi yanada mugun tausayi ko mace bazata nunamai tausayi ba, yamayi kuka amutuwan yaran gidan marayunshi balle wani nashi, fuskarshi yadaura kan hannunta yafashe da kuka sosai yace "Mama koda Arham koba Arham ke Mahaifiyata ce, amatasayin Mahaifiyata na daukeki and I will always yimiki abinda kowani d'a kema mahaifiyar shi Mama" yanda yake kuka akan hannunta yasa takai dayan hannunta tadaura kan saman kanshi tana shafawa alamun lallashi tace "Waleed kayakuri, inamai dada baka hakuri akan abinda Arham yamaka, wlh daidai da rana daya bantaba rainon Arham yazama abinda yazama ba, Arham kaga koni mahaifiyarshi baidamu daniba, yaron dako uwarshi bai kulawa da ita kagako zai iya komi aduniya amman bakomi, duniya nada mugun fadi da babu wanda yasan a ina karshen ta yake, yaje zaiga......." da sauri Waleed yadago rinanun idanunshi yakai hannunshi kan bakinta yarufe yana girgiza matakai yace "karkimai baki Mama, karkimai baki" ture hannunshi tayi zatai magana saikuma tafashe da kuka tamaida idanuwanta kan silin tana wani irin kuka tana nuna kirjinta tace "ni Arham zai wulakanta, Arham dan Adam ne, butulu kacireshi daga rana kakaishi Inuwa yamaka dare, nakira Arham banda lafiya amman yaron nan yanuna mini banda amfani, Waleed na tsugunna ni dinan na tsugunna na haiho Arham, da ina nakudan shi har barkono aka zubamin a garwashi aka lullubeni da bargo na shaka ina tari inajin azaban yaji dukan yaron nan nafito, nasha azaban duniya kafin na haiho Arham amman shine zai wulakantani aduniya, Waleed wlh bazan yahewa Arham ba, bazan yafemai ba" tafashe dawani irin kuka dayasa Waleed yaji shima kukan yazomai, juyowa tayi ta kalleshi, murmushi tamai ta share hawayenta sanan tace "bani fuskarka" matso da fuskarshi yayi yakai mata, hannunta tasa ta sharemai hawayen tastas tana murmushi, sanan takama keyanshi tamai kiss agoshi abinda bata tabamai ba kenan tace "naji dadi daka ganni kafin Allah yakirani gidan gaskiya Waleed" kasa daurewa Waleed yayi sai kuka, sake gogemai hawayen tayi tace "Waleed kai bawan Allah ne sanan yaro nagari wanda kudin iyayenshi baisa kana isgilanci ba ko raina nakasa dakaiba, inaso karage kukan nan kaji, saurin kukanka da tausassan zuciyan da Arham yagama karanta yaga kanadashi yasa yacutar dakai dashi, karage kuka kaji sabida kaga nabar duniya babu mai kula dakai, kaga wanan kafar tawa Waleed" taidan shiru sanan tasakemai murmushi tace "bata tashi bace, saisa nasa Sadiya takira mahaifiyarta tazo duk narasu a hannun yar uwata da yarta tunda ni yanzu banda d'a" Waleed jiyayi heart dinshi yay breaking tasake fashewa da kuka, murmushi tamai tace "kadena kuka Waleed sabida inaso inna rasu ka tsaya ka tabbatar an suturtani da kyau ammin duk abinda yakamata dan nasa d'anda nahaifa bazaizoba yamin wayan nan abubuwan ba" fashewa da mugun kuka yayi yasake taushe mata baki yace "Mama babu abinda zai sameki ciwo ba mutuwa bane, kuma Arham zaizo namiki alkawari zan kirashi zakiga zaizo, amman yanzu bari nafara kaikai Zenith abaki kulawa tukunna kinji Mamana" wani irin ijiyan zuciya tasauke sanan tace "Waleed harnakoma ga ubangiji bazan taba manta abinda kama d'ana daniba, yau kuma zan roka maka Allah agabanka, ubangiji Allah ya sakamaka da sakkayya ta aljanna Firdaus, Waleed Allah ya kareka ya nisanta ka daga dukkannin shairuka sanan ya Sadaka da alkhairi, Allah yabaka mata tagari dakuma zuri'a dayyaba, Waleed irinku bakuda yawa aduniyan nan kai kyauta ne Allah yama iyayenka, ina rokon Allah daya biyaka duniya walahira, Waleed bissalam kaji d'ana danakeso" takarashe maganan ahankali tana murmushi wani irin kuka da Waleed yakeyi jikinshi har bari yake da kyar yay controlling kanshi yay shiru yatashi wardrobe dinta yabude hijabin dayagani yazaro yazo bakin gadon yadaga kanta yasa mata sanan ya ciccibeta bai damu da ruwan dake fitaba yana bata kayanshi yay wajen dakin da ita yanacema Maman Sadiya da Sadiya yace "kurufo gidan mu tafi asibiti" yay waje da ita, yana tafiya tana kan jikinshi tana kallon fuskarshi tana murmushi, bayan mota yabude ya kwantar da ita ya gyara mata riga da zaman wandon sanan ya maida kofan yarufe daidai su Mama sun fito, gaban motan shi ya nunamusu suka shiga su biyun shikuma yazauna mazaunin direba yaja motar dawani mahaukacin gudu, suna zuwa zenith dayake an sanshi sosai a asibitin yay housemanship dinshi yana zuwa suka karbeta akai wani daki dasu yabisu shima da gudu, yarike mata hannu gam yace "Mama na" murmushi tamai saikuma yaga hawaye ya ziraro ta gefen idanunta but still murmushi takemai kasa daurewa yayi yashiga kuka cikin rawan murya sosai yace "lemme call Arham Mama kinji, yanzun nan zaizo, yanzun nan I promise" yay maganan yana sakinta likitoci suka dukufa akanta yawuce yafita daga dakin, staff room dinsu yawuce ya shiga yawuce bayida sauri tap yabude ya wanke fuskarshi dataija sosai sanan ya jingina da bango, kafin ahankali yazura hannunshi cikin aljihu yaciro wayarshi, mantawa daduk wani fadanshi da Arham yayi yay dailing number Arham har wayan takatse bai dauka ba, saida yamai good 7miss calls ana 8th one dinne ya dauka, cikin wata irin dashshiyar murya dan yanacikin sex da Murja ne yakira yakai wayan kunnenshi awulakance yace "wai ya akayi ne? Idanma ka kirane danka sanar dani ka karbi offer dana baka na matsayin nani kazo office in person kafadi min" Waleed bai damu da maganganun shi ba yace "Arham something serious is going on yanzu is not time for our fight, Mama batada lpy sosai she's even admitted, please kazo kaganta kaji" wani mugun tsaki yaja yace "inzo in mata ubanme? Ai tuntuni Mama tai taking side dinta, she choose you and your money over ni danda ta haifa, so kuyi abuku gaka likita tana nemana namata me nidai tagama dukana kanka, kace nace bazan zoba gaka likita kamata abinda yakamata, please don't call me again am eating virgin pussy kasan ba pussy dayakai virgin one dadi" ya katse wayan, da sauri Waleed yasake dailing number dan ayanzu he doesn't mind har guwiwa zai iya samishi akasa dandai kawai yazo yaga mahaifiyar shi dan is obvious Mama na kewan danta, kira yayi harsau uku but yaji wayan akashe hakan yasa yasake wanke fuskarshi yafito daga bayin sanan yabude dakin yafito cikin asibitin, ganin wasu nurses da Dr na gudu suna shiga dakin da aka kwantar da Mama yasa da gudu yay dakin ya shiga shima, gani yayi likitoci almost 7 sun zagayeta ga nurses kafanta dake ruwa yanzu yafara jini irin jinin nan kaman na maruru yafashe jikinta nawani irin rawa tana kokarin magana but hakoranta sun datse, dawani irin gudu yay kanta yace "Mama!" hannu Mama tadaga tana mikamai jikinta na bari da sauri Waleed yay kanta yakama hannunta yarike, ahankali consultant din dake kanta yadago kanshi ya kalli sauran likitocin tareda girgiza musukai, damke hannunta gam Waleed yayi yana kuka mai sosarai yace "Mama tsaya kiji karki tafi ga Arham nan zuwa, gashinan zuwa go slow ne yarike shi yace kijirashi kinji Mama" hannunta tasake mikawa tadaura akan na Waleed, Waleed dayagama fita hayyacinshi yace "Mama me haka ki kallen dan Allah kinji, Mama" wani Dr ne yakama mai kafada kallon Dr yayi hakan yasa yagane sakon Dr, kallon Mama yayi saiya fashe kuma da kuka ahankali cikin wani low tone yace "La'ilaha illallah Muhammadur rasulullah" haka yadinga maimaita mata kafin bakinta yabude kadan ta iya furtawa sanan Allah ya karbi ranta hannayen Waleed nacikin nata, wani irin kuka Waleed yadingayi he can't believe Mama tarasu right infront of his eyes, yakai kusan 10min kuka yake sanan ya iya yay shiru ya share fuskarshi tass dan yatuna kalamanta nadazu _kadena kuka Waleed sabida inaso inna rasu ka tsaya ka tabbatar an suturtani da kyau ammin duk abinda yakamata dan nasa d'anda nahaifa bazaizoba yamin wayan nan abubuwan ba_ Ahankali yakai bakinshi kan goshinta ya sumbaceta yace "Allah ya gafarta miki Mama, Allah ya jikanki" sanan yaja zani ya lullubeta yay shiru yana kallonta, gabaki dayan jikinshi yamutu, gani yake suma tayi saisa ya tsaya yana jiran tabude idanu yamata magana.barayi Allah ya isa banyafeba inkika karanta batare dakin biyaba 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 4️⃣9️⃣ *This novel na kudi ne, idan kika karanta baki biya ba banyafe ba🤷🏻‍♀️* _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ Kalaman Mama da yatuna yasa yaji yadake sai zuciyarshi dake kuka kamar ranshi zai fita, daurewa yayi sanan yadake ganin kuka won't help him yasa ya bude kofan dakin ya fito ahankali, kaman jira suke suma yana fitowa su sadiya da mamanta suka nufoshi arude. "Waleed ya jikin natane yanzu"? Maman Sadiya tamai tambayan hankalinta atashe, baii iya amsata ba sai ma wani sabon hawaye dayayi rolling down his chick da sauri yasa yatsa ya goge cikeda natsuwa yace "sai dai muyi hakuri Umma, Allah daya hallitota sanan yakuma fimu sonta ya amshi abunshi, Mama ta riga mu gidan gaskiya Umma". Wani irin kuka mai sosa rai Sadiya tafashe dashi, ita kuma Maman Sadiya tayi karfin hali ta share fuskarta tass ta dake dan dama tuntuni takawo ma Mama mutuwa sabida yanda take mata magana kullum dare bayan Sadiya tai bacci kaman tana mata wasiyya, ahankali ta furta. "Innalillahi wa innailaihi raji'un, Allah ya miki rahama Yayata, Allah yasa kin huta, Allah yasa iyakar wahalarki kenan, Allah ya yafemiki kurkuran ki, mungode sosai Waleed Allah ya maka da Albarka, su fito mana da gawarta aje a kimtsa ta akaita gidan gaskiya." Gyadamata kai yayi ya wuce office na doctor ya fada mishi sunaso su tafi ya fada mishi bills dinshi sanan amai arranging ambulance din dazai dauketa. Takardan bill din komi aka bashi yaje Yabiya a account, yafito daga office din yana tafiya yana dialing number Arham, wayanshi na ringing baya dauka,. Wajen cashier yaje account din asibitin, yayi settling bills dinshi suka bashi receipt ya karba yatafi. Jingina yayi da bango ya na jiran afito musu da gawar mama fito da phone dinshi ya sakeyi daga aljihu, akaro nabiyu yasake dailing number din Arham y amma har ya tsinke bai dauka ba, kara dailing yayi still no answer. Haka yaci gaba da dailing number dinshi har kusan sau 6 still no answer daya baya ya mishi droping message. _“you should come home Arham, Allah ya ma Mama rasuwa yanzun nan a Zenith, but yanzu zamu koma da ita gidane dan anbamu gawarta”_ Daidai Yana tura mishi message din ana fitowa da gawar mama z'aa sakata a ambulance dazai kaisu gida. Shiga motarshi yayi su sadiya da maman sadiya suka shiga baya yayi gaba amblance din na binshi abaya with high speed. Suna shiga gida aka fito da gawar Mama aka shigar da ita palour suna ajiyeta suka juya suka tafi, kafin kaceme makota sun soma cika gidan dan duk kusan kowa yasan da rashin lafiyan Mama, saisa sunajin kukan ambulance sukasan ba lafiya ba, kuka wiwi Maigadi ya dunga rusawa . Maman sadiya ne tayi karfin hali ta tashi tafito daga dakin tasami Waleed tsaye atsakar gida da waya akan kunnenshi yana kiran Arham har lokacin tace "Waleed Arham yaji kuwa Mamanshi ta rasu?" gyadamata kai yayi yace "Yes na fada mishi yace gayinan zuwa" hmmm shine abinda Maman Sadiya ta furta dan ko kadan bata yarda da maganan Waleed dinba tai kwafa tajuya takoma ciki. Ganin Arham ba dauka zaiyiba yasa yayi dailing number Mom da Ammi ya fada masu Allah ya ma mama rasuwa, salati both suka dauka all suka shiga shock, they can't believe Mama tarasu, Mama akwai kirki da dattako danko ita Ammi ta yabama Mama a dattakon ta, danta yay laifi bata taba siding nashi ba wani haline da bakowace uwa zata iyaba. Koh 30min bai daukesu ba suka karaso kafin su iso ma makota duk ancika gidan makil ga Maza dake waje suna jiran akawota don su mata salla sai tambayan danta Arham ake amman babushi, shiga ciki mom da Ammi sukayi suka hango Waleed idanunshi yayi ja alamun yasha kuka ya koshi kusa dashi Ammi ta tsaya tana tama Matan wajen gaisuwa sanan suka wuce suka shiga dakin. Ammi, mom da maman sadiya sune suka ma mama wanka aka suturceta, Maza sun shigo don daukarta Waleed yace adan bari kadan ga Arham nan zuwa. Wani irin kallo maman sadiya ta mishi kafin tace "bayin Allah don Allah ku tafi da ita amata sallah a sadata da ubangijin ta, yanada kyau agaggauta kai mamaci makwancinsa" kasa cewa komai Waleed yayi kawai ya tsugunna daukarta sukayi akayi waje da ita dan asallaceta. ******** _Bangaren Arham_ Sai wajajen magrib ya kyale Murja yamata jaga jaga gwanin ban tausayi, yace "tashi kitafi Amarya ta nabaki 2days hutu, karkuna kifadiwa kowa abinda ya shiga tsakanin ki da mijinki" gyadamai kai tayi tadau kayanta ta saka da kyar yana hararan shegun nonuwanta masu suffan maruran dabasuyi ruwa ba, sanan yawuce ya shiga bayi yafara wanka yana kirga cikin su 8 biyune kawai yarage baiyi disvirgin ba, wani irin murmushi yake wato d more kanacin mata the more kana kara experience, dadin mata daban daban ne, tundaga kan Ilham baitaba cin wacce tamai dadi kaman Hassana ba, wayyo Allah yarinyar nada madara, jiya yay amfani da ita wayyo Allah kaman karya dena, tunani ya shiga yi yanzu da daddaren nan wazai kira cikin biyun dasuka rage, fitowa daga wankan yayi yafita zuwa office dinshi ya zauna yaci lafiyayyen abincin da yabada asayomai sanan yakora da juice yatashi yay salla la'asar magriba dakuma isha'i sanan yafita wani mai Shara ya aika yace "jeka kiramin razika daga female hostel" yakoma office dinshi ba'a wani dauki lokaci ba saiga razikan tasaka hijabi ta shigo, same trick dayama sauran yamata sai murmushi take tanajin dadi Mr Arham ya aureta, sanan yarufe office sukai uwar daka yafara da ita, shi ko kuka suke baya sauraransu saida yagama da ita fess ya tabbatar da mitsitsike nonuwan nan kaman zasuyi ruwa sanan yafara destroying nata tai kuka harta gode Allah hartaci sa'a yabarta. Wuraren 6nasafiya ya farka kadata yayi ta tafi bangaren su sanan shikuma ya shiga bayi wanka yayi yafito yay salla, sanan yazauna akan gado, wayarshi daya daura kan side drawer yadauka yanason yakira a kawomai breakfast yaga miss calls din Waleed wane 40, wani mugun tsaki yaja yace "wai wats my problem with this dude" message dayaga yanadashi ya shiga yaga message from Waleed kaman bazai budeba saikuma yabude, yana budewa yaga sakon da Waleed yamai. _“you should come home Arham, Allah yayima Mama rasuwa yanzun nan a zenith, but yanzu zamu koma da ita gidane dan anbamu gawarta“_ Wani irin zabura yayi yamike tsaye yasaki wayan akasa jikinshi na rawa yana kallon wayan dake kasa yace "M.....a....ma" yama kasa believing abinda yagama karantawa, hannunshi yasa akan idanunshi ya share idanun sanan ya duka ya dauki wayar yaga still test message din na nan dayake tunanin mafarki yake yaji kirjinshi na dukan uku uku, ance duk iskanci yaro saiyaji mutuwar uwarshi har tsakiyan kashin jikinshi da hanji same thing dake faruwa da Arham kenan, yaki yarda Mama tarasu gani yake kawai Waleed yay hakanne danyasa yazo gida, key motarshi yazura yawuce ya shiga mota yaja motar da mugun gudu sai gida, tundaga kofar anguwan su yahango Waleed yafito da babban botikin fenti yana zubama Samari da manyan dattawan yan anguwa shayi akofi, ga bread birjik slice one, sanan ga uban takeaways na abinci dayay order su daga wani hadadden eatry duk maiso yadauka yaci, ahankali yakarasa yay parking motar nashi yafito, kallo daya Waleed da idanunshi suka kode yamai yadauke kai yacigaba daba jama'u shayi, ahankali Arham ketakowa yana zuwa wajen mutanen dayagani akai akofar gidan yasa yakara yarda dacewan Mama fa tarasu inba hakaba babu abinda zai tara yan aguwansu da makota haka akofar gidan anacin abincin Sadaka, karasowa wajen yayi da kyar ya iyacewa "Assalamu Alaykum" atare jama'un wajen suka amsa da "yakarin hakuri Arham? Allah ya gafarta ma mahaifiyarka, kayakuri haka mutuwa yake, kaga daya tashi zuwa baice bari yajiraka daga tafiyan dakayiba a'a, amma dai abokin ka ya tsaya amadaddin ka yama mahaifiyarka komi dakaine zakamata, Allah ya jikan ta da rahama" gyadamusu kai yayi idanunshi sunyi jajir ya lankwashe kafa yana kallon gate din gidansu yana ganin kaman zaiga Mama tafito ta kwalamai kira Arham, yakai kusan minti talatin awajen zaune, saida jama'an suka watse bayan sun gama kari sanan yamike tsaye ahankali batare daya kalli Waleed ba yay cikin gidansu, wani irin tafiya yake harya karasa falonsu da babu wasu mata dayawa ya tsaya chak yanabin fuskan kowada kallo, Ammi ne datake kallonshi in disgust, sai Mom, sai Sadiya da takife kanta kan kafafunta har lokacin takasa daina kuka sai Maman Sadiya take wani irin kallonshi irin kallon nan na Yayata tai asaran haihuwanka, Mom ce ta danne zuciyanta tace "yahakuri Arham" ahankali yace "dagodiya" Maman Sadiya ne taso ta daure iya daurewa but takasa, dan gani take shine sanadiyan mutuwan yayarta, cikin wani irin yanayi na kunan rai tace "mekazo yimana agida eh Arham? Meya kawoka? Ba kace bazaka kara zuwaba, tana rashin lafiya tana nemanka kaki zuwa yanzu me amfanin zuwanka bayan ta rasu?" wani irin murmushi tayi tace "Arham duniyan nan nada girma kuma wlh duk wanda uwarshi tamutu tana fushi dashi toya tabe, kaje zakagani" wani irin ja idanunshi sukayi jin jiri jiri nakamashi yasa yazauna atsakar dakin kaman wani almajiri dayazo bara, tabe baki Ammi tayi ta mike tsaye ta kalli Mom tace "tashi mutafi we have wedding" sanan ta kalli Maman Sadiya tace "yar uwa bari mutafi gida, kinsan gobe bikin Waleed, kome kikeso kisa Sadiya takirani a wayar dana bata tasanar dani in sha Allah zan aiko muku dashi" tsugunnawa tayi tashafa kan sadiya dake kuka har lokacin tace "ya isa yarinyar kirki, kidena kuka kinji, kozaki bini" dagokai Sadiya tayi da jajayen idanunta ta kakaloma Ammi murmushi, murmushi itama Ammi tayi tace "inkun gama zaman makoki zanzo sai asan yanda za'ayi bazadai ku kara komawa kauyeba, in kinason karatu zan maidake school Sadiya, inkuma aurene saikiyi auren ki kinji" gyadamata kai Sadiya tayi sanan tace "to sai anjiman ku" cikeda so Maman Sadiya tace "angode Hajiya Allah yasaka da alkhairi, Allah kuma ya sanya albarka abiki" suka wuce suka fita har waje, awaje suka sami Waleed attending to some guest, kiranshi Ammi tayi. "Waleed" ahankali yadago kanshi, wani mugun kallo da Ammi tamai dan tasan halinshi sarai zaice mata bazai tafi gidaba yasa yamusu sallama yataho, motansu ya shiga sukuma suka shiga baya yaja motar Ammi tace "you've done your best wanda ko danta baiyiba, yanzu tunda Allah ya kadoshi yadawo gida, kabarshi da aikinshi go and concentrate aurenka gobe, use today to tell your wife zakai aure kanajina ko, ranan bakwai dukma dawo gabaki daya mu sakeyin gaisuwa"" gyadama Ammi kai kawai yayi dan bayason surutu, agida ya ijiyesu sanan yawuce gidanshi. _sorry guys, I've been at the station jiyan nan all through, i will be fully stable gobe, and normal posting continues_ 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣0️⃣ Tundaga gate yakejin kukan Arham parking yayi yashiga cikin gidan, a falo ya tarar da mai rainon yaron da Arham matan tagaji sai jinjigashi take ga zanin gayo a hannunta alamun daga bayama ta sauke shi, maida kofa yayi yarufe yakarasa wajen yamika hannun ya karbai da sauri yace "why is he crying like this ina maman shi?" anatse mai rainon tace "takoma baccin safiya yallabai tace kar atadata harsai ta tashi zata fito ta amsheshi" ji Waleed yayi ranshi ya baci, baicema mai rainon komiba sanan yawuce yay sama dashi, dakin Ilham din yabude ya shiga dakin duhu, hannu yasa ya kunna wutan dakin dakin yay haske hakan yasa tabude idanunta ta waigo hada ido sukayi da Waleed daya dauki Arham dake kuka, cikin muryan bacci tace "Baby maisa ka dauko shi saina tashi zan bashi nono, please ka mayar mata dashi" wani mugun kallo yamata yace "kirashi and breastfeed this boy" jitayi ranta yabaci dan da daddare Arham baya bari tai bacci shan nono yake, ta tsani ana shamata nono, tashi zaune tayi ahankali sanan tamika hannu batashi yayi tana karbanshi cikeda fushi takaimai shegen duka abaki yaron yawani irin kwala mugun ihu dan daduka karfinta ta mari bakinshi tace "shegen fitinannen yaro babu abinda yasani sai nono" tsawa Waleed yadaka mata yace "are you mad Ilham" itama cikin fushi tace "ga yaron dazaka tambaya nan ko he is mad, yaro yahanani sukuni yahanani sakat, nono nono nono wani irin abune haka, kasheni zaiyi wlh nagaji" tai maganan tana ciro nono takai bakinshi amman ina yamaki karba sabida tsabagen zuciya da yanda yake ihu, cikin fushi ta kalli Waleed daya tsaya yana kallonta tace "kaga halin ja'irin yaron ko, kangararre kaman ubanshi, matsiyacin d......." wanketa da lafiyayyen mari Waleed yayi yace "karki kara zaginmin yaro, karki kuma kara kiranshi da kangararre, come Arham" yadauki yaron yajuya yafita daga dakin yaron sai kwala ihu yake yasauka kasa ya sami mai rainon shi yace "anmai wankan safe"? Girgixa kai tayi yace "hadomin ruwan shi" ruwa tawuce tahado Waleed yaciremai kaya tun yana school aka koyamusu yima jariri wanka dan suna amsan haihuwa, Arham na kuka yama yaron wanka tsaff sanan ya shirya shi cikin kayan da takawo mai sanan yadauki madaran dayasa aka damamai yabashi da kyar yasamu yaron yasha, shegen zuciya yanasha sai bacci, bama mai rainon shi shi yayi ta goyashi sanan ya wuce sama dakinshi yabude ya shiga yay wanka sanan yabi lafiyan gado, wuraren 1 yafarka wanka yasakeyi ya shirya yafito Ilham yagani a falo yar aiki na matsa mata kafa ko kallonta baiyi yawuce yafita mosque, yana dawowa yawuce dakinshi ya zauna kan gado yana kallon setin akwatinan ta daya mata guda 12, sanan ya kwalamata kira. "Khadija, Khadija" daga kasa ta amsa da na'am sanan ta taso tayo sama, dakinshi da tunda tadawo yaune take shiga ciki tabude ta shiga tanabin dakin da kallo da hadaddun akwatunan dake jere akasa, karasawa tayi ta zauna kusada shi tana kallon akwatin tace "gani baby, wayan nan akwatunan masu kyau fa" ahankali yace "nakine" washe baki tayi ta kallai tace "nawa"? Gyadamata kai yayi yace "yes nakine, am getting married tommorow kimin addu'a" wani irin kallo tamai gabanta ya yanke yafadi tace "aure zakayi Waleed, ni xakama kishiya"? Hannunshi yamika yadauki laptop dinshi yabude tareda gyara zama ya jingina da bango yana kunnawa yace "am getting married tommorow Khadija, sunan yar uwanki Saheeba" "tufiakwa! Kishiyata can never be yar uwata, wai Waleed are you for real nizaka karawa kishiya eh Waleed? Duka duka auren namu wata nawa eh, nizaka cuta? Ni zaka ciwa amana? Nizaka ha'inta ta hanyar yomin kishiya kumama sai ana gobe aure sanan zaka sanar dani eh Waleed" sosai ihunta ke cikama kunne hakan yasa yanuna mata kofa yace "get out please aiki nakeso nama Mummy a laptop, excuse me" yanuna mata kofa, fashewa da kuka tayi tace "wlh wlh indai hakane bazan zauna dakaiba saidai ka zaba koni ko ita wlh bazan yardaba" ganin har lokacin kofa yake nuna mata babu alamun wasa yasa tawuce tafita tana masifa. Dakinta ta shiga tadauki waya takira Mummy, Mummy na dauka tafashe da kuka tace "Mummy kinji ni Waleed zai ciwa amana wai kishiya zaimin, Mummy duka duka shekaran mu nawa da aure dazaimin kishiya eh Mummy, saisa wlh akashe duk namiji badan goy......" tareta Mummy tayi ta hanyar "ina zuwa yarinya, yimin shiru" shiru tayi kirjinta na tafarfasa, Mummy tace "kiketa wani bala'i ni banda kishiya ne" cikin wata yar kankanuwar murya tace "kinada shi" Mummy tace "good, inada shi but har yanzu kina gidana, har yanzu nikeda fadan baban ku, kowace kishiya da halina take zama, sanan ba akanki za'a daurataba, inaso ki natsu ki kwantar da hankalinki kinada karamin yaro a hannu ki kulada yaronki sanan kibawa mijinki kula da komi dayakamata, kishiya is just a normal thing, maza ne they're naturally polygamous in nature, so I advice you to calm down kinajina, banson in karaji kina hayaniya ko wani abu kinjini " gyadama Mummy kai tayi wasu hawaye masu dumi na sauko mata tace "uhm" sanan ta katse wayanta, wani irin fashewa tayi da kuka kaman ranta zai fita why is Allah testing her like this, Arham ya dauramata ciki ta haihu yanzu yaci amanan ta bayan ya cinyemata kudade duka, saikuma ga Waleed yanzu kishiya zai mata ubanwa zai aura ma, yaushe ma Waleed yafara kallon mata dahar zai mata kishiya, kuka tasha tai ma'ishi koda aka kawo mata Arham ko kallonshi batayi ba yaron sai tsala ihu yake saidai Waleed yafito ya amsheshi yasa amai madara a kawomai yabashi, har dare Ilham kuka take hakanan ya shareta danshi baison rashin kunya yakuma lura abinda tafiso kenan. ********* Yau babban rana ce ga Waleed da Widad, gabaki daya dagashi har ita babu wanda ya runtsa, shi kawai Allah Allah yake gari yawaye yaga ya auri Saheeba tadawo mallakinshi, shi karan kanshi yarasa wani irin so yake mata, kawai son yarinyar yake bana wasaba, dayake karfe shadaya ne bikin hakan yasa yay wanka yafito shiru yayi yazauna akan gado yana tunani shikenan yanzu baida aboki he is on his own, da ace yanada aboki da yanzu yama fitomai da kayan dazai saka, girgiza kai kawai yayi yatashi dan bayason yafara tuna Arham kuma yazaro kayan dazai saka daga wardrobe, wasu fararen shadda ne masu mahaukacin kyau, hasken su zai iya kashema ido, shiryawa yayi tsaf kamshi natashi daga jikinshi kaman yay barin turare, takalmi ya sanya yadau wayarshi yarike yana kallon agogon hannunshi sanan yabude kofa yafito yana taku daidai, ahankali yabude dakin Ilham ganinta yayi zaune kan gado baijinma tai wanka ba tai busubusu riganta dukya jike da ruwan nono, wani mugun kallo tamai hakan yasa ahankali yace "yallabiya nazo namiki sallama ne, amin addu'a" wani mugun harara ta sakinmai tace "ubangiji Allah karya kaika lafiya, Allah ya tarwatsa auren" shiru yayi yana kallonta ganin yanda takejin wani masifa kaman zata tashi ta dakai, baison yabiye mata hakan yasa yajuya kawai ya sauka kasa, bude mota yayi ya shiga yaja har anguwan su dayaga an cika dudda fa simple wedding ne amman mutane sun cika gidansu, yana zuwa ya shiga rumfar da aka tanada dan daura aure, wasu manya manyan limamai ne guda biyu daya ya wakilce shi dan Uncle baisamu daman zuwaba daya kuma ya wakilci Widad dan anmusu bayani ba'asan kowa nataba tsintarta akayi ya wikilce ta aka daura aurensu da akan sadaki dubu dari uku, sanan suka bashi marriage certificate dazai shiga yaje suyi signing shida ita. Godiya yamusu sosai sanan aka shiga Walima ana fitomusu da kayataccen abinci aka shiga yi, cikin gidansu yayi yana mamakin mutanen dasuka cika gidan aranshi yana Ammi, Ammi she will never change, tagama cewa babu wanda zata gayyata but see people, shashin shi yayi sai guda akeyi da aka ganshi, shiga bangaren nashi yayi yazauna afalo sanan yadauki wayarshi yakira number Asma'u, ringing uku ta dauka tace "hello Ya Waleed Ango" murmushi yayi yace "Hello Ma'u kanwar Ango" kyalkyacewa da dariya tayi dan maganan yabata dariya, dan gajeren tsaki yayi yace "Common, bakira nayi dan kiyitamin dariya ba, ki kawomin matata bangarena" da sauri tace "Ya Waleed wlh Ammi tahana tace sai anjima idan ankaita gidan ka" akumbure yace "ke ina wasa dakene, cewa Mom certificate zatai signing nabaki 5min idan baki kawota ba kin shiga uku" ya katse wayan dib. Widad dake zaune akan kujera makeup artist namata applying wani new makeup na white gown din data saka tace "what is it Moxi"? Hararanta Asma'u tayi cikin harshen turenci tace "dalla mayyar miji, tuntuni kike tambaya na shi, gashinan shima yace nakaiki kiyi signing marriage certificate" wani irin cool smile tasaki she really miss him, tadade bata ganshi ba, fita Asma'u tayi daga dakin tai dakin Ammi dake magana da Mom, tace "Ammi Ya Waleed yace naraka Saheeba bangaren shi tayi signing marriage certificate" tsaki Ammi tayi tace "yaci gidansu bazata ba, ko yaushe ne ai ina zata iya signing certificate din zai wani ishi mutane to bazata zoba" da sauri Mom tace "wai Adda mai matsalan ki da yarona ne eh?" ta kalli Asma'u tace "wuce ki rakata kinji" cikeda jin dadi Asma'u tafita daga dakin tana rawa, Ammi tai murmushi tana kallon Mom tace "yayi kyau ni akewa yan ubanci ko" dariya Mom tayi sosai tace "anyi kema ai kinamin fin haka kikaga su Abdul, ni natafi" tawuce tafita daga dakin murmushi Ammi tayi tabi bayan kanwar nata da kallo ita kadan tasan she is so lucky da Allah yabata Mom amatsayin kanwa, Mom is everthing with triple plus. Gyarata akayi tsaf aka lullubeta da net tana wani irin mahaukacin kamshi, ita kanta Asma'u tsayawa tayi tana kallon Widad din dan wlh tunda take bata taba ganin mace mai kyawunta ba, ana yawan cewa farare fari ne kawai ya cecesu amman munana ne, but in the case of Saheeba kyakkyawan yarinya ce ta karshe, ita ko kadan batama yarinyar ma kallon bahaushiya ko fulani haka, tanama Saheeba kallon baturiya ne wacce ma badaga Nigeria takeba, dan duksu Ammi sunfi mata kallon yar fulani dan akwai asalin yan fulani dako zo basuji da hausa but ita batamata kallon yan fulani. Ganin ta tsaya tana kallonta yasa Widad kaman zatai kuka tace "let's go" baki takama tace "waike banace miki kidinga jin kunya ba" murmushi tayi daya lobar da dimples dinta batace komiba, Asma'u tabude kofa suka fito yan falo suka fara buda, Mom na tsakar gida but jin ana guda yasa saida tajuyo dantaga meakeyi, subhanallah tsarki ya tabbata ga Allahu subhanahu wata'ala daya hallice wanan hallita, Widad nada kyau batada kiba hakan yasa akai gown din yabi daidai jikinta saiya wani irin fito da dirinta da shape dinta, anmata applying simply makeup dan yarinya ce dat is already beautiful she don't need heavy makeup, sanan akabi pink dan karamin lips dinta, dawani sexy pinkish lipstick dayasa tai kaman wata hurun ini, tasaka hill ba chancjan ba dan tanada tsayi sai abin yabada wani classic look, ajiyan Zuciya Mom ta sauke tana kallonsu yanda Widad ke tafiya daidai dakuma yanda tai kyau yasa ahankali tace "Waleed Allah yasa baka auri abinda yafi karfin muba, anytime I look at this girl I feel kaman yar wanice dan is written all over her, Allah yabaku zaman lafiya Allah yakade fitina" fitowa waje sukayi Mom ta zaro kudi tana murmushi ta watsa musu akahau ihu sanan sukai flat din Ya Waleed da ita. ALLAH ISA IDAN KIKA KARANTA MIN BOOK BAKI BIYABA 07012181461 CHAT ME UP 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣1️⃣ Waleed dake zaune kan kujera jin yanda ake guda ana ihu sabida ganin Amarya da akayi yasa yakasa daurewa yatashi ta window shi yaleko ahankali yana kallonsu, wani irin ijiyan zuciya yasauke daya hango Widad, kasa daukanshi kafafun shi sukayi hakan yasa yakoma da sauri yazauna jikinshi ko ina bari yake har wani dan sanyi sanyi yaji, daman haka akeji idan ka auri wanda kakeso, he is feeling anxious and eager gawani irin snayi danaji yanaji kaman ana cikin pik of hammatan, jin har yanzu basu isoba wanda yaci ace sun iso bangaren shi yasa yakara tashi da sauri yay window yaye labulen yayi kadan ya kalli tsakar gidan saikuma bai gansu ba daidai anbude kofar falonshi, da sauri yasaki labulen yajuyo suka hada ido da Asma'u datake kallon inda yake tace "laaaaa Ya Waleed lekomu kakeyi" wani irin mugun kallo yamata hakan yasa ta taushe bakinta dan mugun dariya ke cinta, dauke kai Waleed yayi shi adole ba kallonsu yakeba yadan sosa kanshi sanan yakoma kan dogon kujeran dayake kai ya zauna yadagokai ya kalli Asma'u dahar lokacin dariya take gimtsewa yace "excuse us madam tunda kin kawota" kafada ta makemai tajadiye dariyan tace "ai Ammi tace na tsaya na jira tai signing nakomar da ita" at this point kasa daurewa yayi yacire takalmin kafarshi guda yamike yayi kanta dawani irin gudu ta kwasa tana "wayyo Ammi Ya Waleed zai dokan" ita kanta Widad saida tai dariya dudda batajin mesuke cewa dan hausa sukeyi sanan ya tsaya chak daidai wajen kofan inda Widad take atsaye, ahankali yajawo kofan ya kulle tareda saka jamlock sanan yatsaya shi yana kallon kofa ita kuma tana facing cikin dakin tana murmushi, murya chan kasa batare daya kalleta ba yace "what can I say? What can I do? I never knew that one behaves like this anytime he is getting married to love of his life, Saheeba kinsan yanda nakeji kuwa? I feel kaman nafita this compound inta ihu ina jumping telling everyone that this girl is now mine, she is my wife, and...." yay dan shiru kafin yajuyo ahankali ya tsaya adaidai bayanta yabude hannunshi murya chan kasa yakira sunanta kaman mai whispering yace "Saheeba turn around" ahankali tajuyo tai facing nashi tasakin mai wani irin alluring smile, hannunshi yamika ahankali yakai kan net din da aka lullube mata fuska dashi sosai hannayenshi suka shiga rawa innailaihi the whole thing is so new to him baitaba sanin haka akeji ba in ka auri wacce kakeso jikinshi wani irin rawa da bari yake, ganin yanda hannayenshi ke rawa sosai yasa awani irin hankali ta daura soft hannayenta dasuka sha hadadden first class lalle akan nashi takama hannun tarike gam tana kallon fuskarshi tacikin net din suka rike net din tare, cikin wata irin murya tace "this signifies that together we can overcome anything that come our way not alone Ya Waleed" yanda tai maganan tafurta kalaman har cikin ranshi saisa yaji this is the first time take kiranshi kuma yasan sabida taji Asma'u na kiranshi da sunan ne yasa itama ta koya but still at that saiyaji kaman duk duniyan nan babu wanda ya iya kiran sunanshi kaman ita, ahankali hannunsu har lokacin ahade yakara takowa yazo gabanta da kyau ya tsaya sanan gently sukai lifting net din tare zuwa kan head dinta, ahankali yakarbe hannunshi daga nata sanan yadaura hannayenshi kan kuncinta kafin slowly yakai bakinshi ya manna kan goshinta, murya chan ciki yace "I love you Saheeba" murmushi tayi sai kawai ta shige jikinshi ta rungume shi sosai kaman yanda shima ya rungumeta tsam tsam duk suka lumshe ido sunkai kusan 10min ahaka kaman wayanda suka tafi wani duniya sukaji ana knocking kofar falon. "Dan Yaro har yanzu baku gama signing dinba ana neman Amarya kawayan mamanka sunzo" da sauri yasaketa yakama hannunta sukai wajen table din yace "Mom am coming" pen yadauka yya signing sanan yabata pen din yace "is our marriage certificate you sign her Pretty" karba tayi tai signing yana kallon signature dinta saiyaga kaman larabci saikuma bai ganewa dan baiga lokacin data fara signature dinba dan yana chan yana kallon kofar da Mom ke knocking, tashi sukayi tare sanan sukai wajen kofan sake hugging dinta yayi yana kallon lips dinta kasa hakura yayi ya manna mata kiss a lips yace "I can't wait akawomin ke gidana" sanan yabude kofan tareda daure fuska, Mom na ganinshi ta dunguremai keya tace "dalla bani wuri mara kunya, kekuma wuce mutafi" takama hanun Widad suka tafi kaman zaiyi kuka, komawa kan kujera yayi yazauna saikuma ya kwanta yadau filo ya rungume yana kallon sama he's so eager to have this girl in his court, dayaye rabonshi da having any affair with a woman fa tunane tunane yadinga yi daga baya su Abdul suka shigo su suka daukemai hankali dan sun isheshi kaman zai kurma ihu haka yadinga ji, daga bayama suka jashi suka fita. Bayan sallan isha'i aka kai Amarya hadadden gidanta dake GRA phase 2, dan gidan Ilham na Phase 1 ne, lokacin da Ammi kefadamai za'a kwana kuka ne kawai baiyiba hakan yasa duk sai Ammi taji badadi, but dole akawana akwai wani magani da za'amata daren yau taci, shine zai kama jikinta dolenshi yahakura, saisa kawai ta shareshi dan tasan he moment she press him a little longer zai iya yafashe mata da kuka hakan yasa ta katse wayanta kawai yamai saida safe, komawa gidanshi yayi dakinshi kawai ya shige baima nemi Ilham ba dan yasan fushi yake tanamai any magana mara dadi zai iya yahuce akanta. Tun bata iyashan abubuwa da magungunan da ake bata tanasha hartazo tafara sha dan dolenta wani zubin zuciyanta tashi yake bayan tagama sha sai andan bata lemun tsami tasha tukunna sanan zataji tadainajin yanda takejin, fitowa sukayi da bayin itada wata matar da Mom tadauko mata an wanke mata tulin gashinta dawasu garukan turare matar tace "Hajiya angama gashinta da jikinta gabaki daya zai dauki kamshin nan har tsawon shekara daya" murmushi Mom tayi tace "an gode abusar da gashin ne"? Da sauri matan tace "no a barshi yabushe dan kanshi saiya bushe sanan sai a gyara gashin, turarukan dazata dinga amfani dashi na shafawa dana fesawa duk ma jera matasu agaban madubi yanzu sai wanchan farfesun dazata sha dazaran ya warke" murmushi Mom tayi tace "masha Allah" murmushi matan tayi cikin harshen hausa tace "amman Hajiya wanan abubuwan ai iyayenta yakamata su mata bakuba" murmushi Mom tayi tanaba Widad din hijabi tasaka ganin tanajin bacci tace "ai mune iyayen nata dole mu mata abinda zamuma Asma'u" gyadamata kai matar tayi bata kara cewa komiba saida akasa ta shanye farfesun sanan aka sata itada Asma'u suje su kwanta sukuma su Mom suka cigaba da gyara jeren gidan yanda sukeso. Washe gari wuraren magrib aka waste agidan bayan sunma Widad ado cikin wata hadaddiyar atampa yellow da lafaya ma yellow daya amshi jikinta naban mamaki gabaki daya duktai wani iri kaman mara lafiya ganinta ita kadai gashi babu Asma'u data mugun shaku da ita ayanzu, gajiya tayi da zama tabi lafiyar gado ahankali kanta namata ciwo sosai. Wuraren 9:30 ya shigo gidan, bude kofar falon yayi yashigo wani kamshi mai bala'in dadi ya daki hancinshi, maida kofar yayi yarufe yasaka key sanan yashigo falo hannunshi rikeda babban leda, kitchen ya shiga ya dauke roasted kajin awani hadadden tray sanan yadauko yay stairs, ahankali yabude dakinta ya shiga yana kallonta ganinta kwance kan gado bacci ya Kwasheta, murmushi yayi ya ijiye sanan yakoma yashigo da drinks yadawo ya ijiye a kasan carpet, yadawo ahankali yazauna abakin gadon dan baiso yatadata ya zauna kawai yana kallon fuskarta, wayarshi yaciro daga aljihu ya turama uncle dinshi text. _"thank you Uncle for giving me the upper hand to get married to love of my life, Uncle inason yarinyar nan sosai wlh, you made my dream come true second Papa I love you Oldie but goodie"_ Ya turama Uncle messege din yana murmushi sanan yatashi ko kadan baiso yatasheta he just wanna watch her sleep knowing fully she is his yanzu, and haka zasu dinga sleeping under the same roof till eternity, yakai almost 2hrs zaune kawai yana kallonta sanan yatashi ganin she is sound asleep, bathroom ya shiga yayo wanka yafito daure da towel a waist dinshi, ya tsaya agaban mirror yana tsane ruwan kanshi da karamin towel sabida yanada dan cikan gashi nai aske gashin shi duka sanan baya barin gashin shi yay tsayi kaman namata he always tream, yanacikin goge jiki yana kallon fuskarta ta madubi yaga tadanyi motsi, da sauri yajuyo ya kalleta, yatsine fuska tayi hakan yasa da sauri yakai hannunshi kan fuskarta jiyayi jikinta zafi hakan yasa da sauri yadagata yasata ajikinshi yace "pretty u are burning up, menene are u sick shine duk basu fadamin ba" bude idanunta tayi ahankali kaman wacce bata dagani sanan tadaura shi kan kyakkyawan fuskarshi ta kallai wani irin ijiyan zuciya tasauke sanan takara shigewa jikinshi ta kankameshi kafin takara lumshe ido wani baccin yasake kwasanta, shiru yayi kawai yana kallonta kaman yasami film sanan ya manna kanshi cikin gashinta yana shakan kamshin ta ahaka shima bacci yay gaba dashi, kiran sallan asubahi ya farkan dashi daga nauyayyan baccin daya tafi yabude ido ahankali, kwance yagansu akan gado yana manne da ita, itama tawani kanannade ajikinshi kaman mage, da sauri yatashi yafada bayi dan sunada tafiya yau ko Ammi bai fadamawa ba Ilham kawai yasanar takomai hauka jiyan nan, wanka yayo yafito ya shirya cikin jallabiya sanan yahau kan gadon, taba jikinta yayi jin yanzu ba zafi yasa yakai bakinshi ya manna mata kiss a lips yace "wake up Pretty" ahankali take bude ido, hada idanu tayi dashi wani irin genuine smile tasaki sanan ta yunkuro zata shige jikinshi da sauri yasauka dagakan gadon yace "please karki batamin alwala, banda control akan ki, bye am off to mosque, go and shower we are going somewhere" yawuce yafita da sauri tabishi da kallo kafin ahankali tasauka dagakan gadon tawuce ta shiga bayi wanka tayi tafito daure da towel tabude wardrobe din da Mom tanuna mata tajera kayanta, hakanan idanunta suka sauka akan wani black doguwan riga, ita taciro ta shirya cikinshi tana murmushi sanan ta tsaya agaban madubi ta nannada gyalen abin har mamaki yabata yanda ta iya nannada gyale bayan bata tabayi ba yay kaman hijabi sanan tawuce tahau kan dadduma tai salla, tana zaune akan dadduma taga Waleed ya shigo yana kallonta dudda baice mata komiba ya ijiye passport guda biyu kan gadon yadau tray din kajin jiya yafita dashi yakaima gateman dinshi yabashi komi harda drinks din sanan yadawo dakin yamaida kofan yarufe still baice mata komiba yacire jallabiyan jikinshi yafara kokarin neman kayan dazai saka, ahankali tazo tabayanshi ta tsaya sanan tarungume shi tabaya ta kulle hannunta kan cikinshi murya chan ciki tana shakan mayan kamshin shi datake bala'in so tace "good morning Ya Waleed" rigan daya ciro ahanger yasaki yafadi akasa sanan yadaura hannayenshi kan nata data daura acikinshi, sirintaccen kamshin datake yi na fizganshi jikinshi nawani irin daukan chaji cikin wata irin naked voice yace "oh this gurl u are driving me crazy, I don't have plans of having you this morning stop tempting me ahhhh" yakarasa maganan ahankali yana wani irin juyowa hancinshi na nata na gogan juna kawai ya chapke bakinta yashiga kissing dinta yana shafa bayanta kafin ya zagayo da hannunshi tagabanta ya damke boobs dinta dayaji ba bra but he could feel half vest, hannunshi yakara kaiwa zai damke boobs din ta kabar da hannun tana tureshi dan zafi taji, sakinta shima yayi ahankali yakama strong erection dinshi yajuya yadau riganshi daya yar yasaka yaciro wando yasaka ya shirya tsaf yasaka takalmi, bagpack kawai yadauka na system dinshi amman ko kaya kala daya basu daukaba komi yariga yay order achan, sanan yajuyo ya kalleta yanda tai shiru tana kallonshi, hannu yamika mata yarike ta yace "let's go zaki bini"? Gyadamai kai tayi suka wuce suka fita, already akwai bodyguard dinshi daya dena fita dashi for a while suka shiga motan yajasu sai Airport, suna zuwa Airport, yadauki wayar nashi yaturama Ammi text. _"my one and only Ammi na, Mama ta takaina, Ammi am on three weeks honeymoon vacation, zamuje Umara sai mukoma dubai, Ammi thank you for getting me married to this girl, Ammi I love Saheeba wlh morethan anything you have no idea yanda nakeji, saimun dawo Ammi kimin addu'a and take care of yourself for me, Bye Mommy na 😘"_ Yatura mata sakon sanan yakashe wayan yabama bodyguard din yace "ka kaima Ammi" sabida so yake yasoye dagashi sai Widad babu mai damunsu, soyayyan dabaiyi ba abaya shi zaiyi this time around and enjoy his self yasan ya ijitema Ilham morethan enough money, ga Dr Ayoka yace mai yadinga zuwa dUk week yana duba yaronshi damatarshi incase, kudi yabama bodyguard din sosai sanan suka wuce suka tafi. 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣2️⃣ Jirgi suka shiga business class yabiya musu, hannunshi takama tarike gam jirgin yatashi kankameshi tayi tanaso tai kuka kanta na juyawa sosai, murmushi yayi yace "Pretty look at me" kallonshi tayi atsorace idanunta nakawo hawaye, ahankali yakama hannunta yakai bakinshi yace "anytime we are together don't ever be afraid do you know why"? Girgiza mai kai tayi da sauri tanajin yanda jirgin ke tafiya kaman a cikinta yace "because no harm can befall on you, am always here to protect my wife" yatsine fuska tayi tana dan lumshe ido ahankali tace "am feeling somehow and am having headache" dayake bangaren su kadaine arufe yasa yace "say no more I gat u" yasa kanta ahankali a kirjinshi rirrike shi tayi gam ahaka har bacci ya kwasheta. Karfe hudun yamma suka sauka akasa mai tsarki, tashinta yayi tabude idanunta tana kallonshi dan hararan ta yayi yace "lazy girl you've been sleeping all through, oya mun iso" kwance mata seat belt yayi sanan shima ya kwance nashi yatashi yaciro jakarshi sanan yamika mata hannu yana kallonta, kama hannunshi tayi yabi lallin hannunta da kallo yatashi suka fita aka kwashesu amota zuwa Airport din suka sauka kasan cewa basuda luggage yasa suka tafi clearance, suna fita ya hango Muhsin direban Uncle dinshi ne duk insunzo makka, gidan da Uncle yasaimai a makkan Muhsin ya kwashe su a lafiyayyen motarshi suka tafi, sai kallo hanya suke yana nunama Widad wuraren tana murmushi har suka kai gidan, gidane hadadden gaske ga swimming pool gakomi najin dadin rayuwa agidan dako gateman babu tai ciki shikuma ya tsaya yana magana da Muhsin yana tambayan shi ko yasai komi daya turo musu na list ya tabbatar mai yasaya, godiya yamai ya mishi kyauta, Muhsin ya karba yace "duk lokacin dakuke bukatata just call me ta landline, na ijiye muku katin restaurant din Uncle dinka dazaka dinga kira for abincin su dama komi, nabarku lafiya" gyadamai kai yayi yajuya yatafi, shikuma yarufe gidan yay ciki yana kallon swimming pool din yana murmushi kaman irin yanada plans plans dinan sanan yay daki, babu kowa a simple sitting room din hakan yasa yay the only daki dakenan cikin corridor wanda shine bedroom din, dakin agayre tsaf an zuba flowers kan gadon ansa happy married life Saheeba and Dr Waleed, gadon irin gadon larabawan nan na katoko an zagayeshi da labule dudda labulayen an daure su ba'a saki ba, an kukkunna candles masu kyau dakesa kamshin daki, doguwan riganta dayagani akasa yasa yay yabi kofar bayinda kallo alamun ta shiga wanka kenan, ijiye jakan system dinshi yayi akasa ya shiga cire kayan jikinshi yana kallon bayin, anan kasa shima yabar kayan daya cire tass sanan yay bathroom din dakin, ahankali yabude kofar bayin batare dayabari yay kara daidai da kwara dayaba ya shiga bayin sanan yamaida yarufe yajuyo ya kalleta tana tsaye karkashin shower ruwa na sauka kan saman kanta, gashinta ya barbaje ya manne da bayanta, kara bude idanu yayi yana sake kallon ass din nata sosai tunda yake bai taba ganin mace mai farin ass irin na Saheeba ba, Ilham farace but ass dinta baki, Saheeba kuwan farin ass dinta an it looks so soft and innocent kana gani kaga ass din da ba'a saba tabawa ba, jiyayi yasami wani irin strong erection da sauri yadaura hannunshi kan erection din yarike but yakasa, ahankali yaga ta daga hannayenta tadaura akan gashin nata ruwa na sauka kan gashin kanta da fuskarta hakan yakara bashi side view na boobs dinta dabasu dawani girman kirki da ampit dinta dakenan so white and smooth kaman gashi bai taba fitowa tacikin shiba, kasa daurewa yayi yafara tafiya sadaf sadaf harya shiga wurin shower sanan gently kuma unexpectedly yabata back hug yakai bakinshi gefen wuyanta yana tsotsan wuyanta yanashan ruwan dake zuwa wajen, wani irin ijiyan zuciya tasauke, cikin wata murya yara tace "y....ya W....." takara kiran sunan nashi sabida jin hannunshi datayi kan navel dinta yana tura hannunshi cikin hole dinta, wani iri daji batasan lokacin datai baya zata fadiba yay maza yatarota tareda juyota tai facing nashi yana facing nata akarkashin shower din, bude idanunshi rass yayi yanabama jikinta wani dirty look, itakuma tana kokarin bude idanunta takasa sabida ruwan dake sauka akanta sai murmurza lips dinta take feshin ruwan na sauka kan fuskarshi, tana kokarin bude idanunta taji saukan hannayenshi kan kunnuwan ta yana tura hannun zuwa a gashinta yana yamtsuwa kafin gently yay grabbing lips dinta while she gave him free access to, yanda yake kissing dinshi yasa taji kaman tana fitsari ajikinta she is feeling soo so somehow, sundade ahaka sanan yazare hannayenshi daga cikin gashinta yay grabbing both boobs dinta yawani irin squeezing fizge kanta tayi da sauri tana yatmutse fuska tana turomai baki ashagwabe, kaman zaiyi kuka yakara matsawa kusada ita idanunshi sunyi jajir cikin harshen turenci yace "mesawai bakison ina kama boobs dinki"? Kaman zata fashemai da kuka tace "because is small and that makes it painful" murmushi yayi cikeda iskanci yace "nafison irin su kibarni dasu kibamu sati daya kiga yanda zasu koma, all bra dinki saisun miki kadan" murmushi tayi saikuma tasake turomai baki tanabin kirjinshi da kallo hakan yasa yakara shigeta yace "I love how small your nono looks kaman tangerine" daga hannu tayi zata dakai da sauri yafashe da dariya yace "please give me the chance na mayar miki dasu gwanda wlh inason nonon ki this small girl" murguda mai baki tayi itama cikin turenci tace "kaima you are a small boy" wani irin fizgota yayi yace "says who" ahankali kaman mai tsoron yin maganan tace "A.....mmi" murmushi yayi yace "metace"? Ahankali tana shafa gashin kirjinshi dake burgeta sosai tace "that u are just 28yrs" murmushi yamata yace "irinmu munfi dadi dan abunmu bai dade da gama developing fa, jijiyoyina are stronger than rod, bala'in dadi ne dani" tana kallon hair din chest dinshi har lokacin cikeda zuciya daya tace "wani irin dadi kakeda shi"? Ahankali yakama hannunta dake kan kirjinshi yace "na nuna miki?" gyadamai kai tayi da sauri tace "eh ka nunamin" wani irin daukanta yayi kaman yar jaririya yasa hannu ya kashe shower yafito da ita bedroom din yadaurata kan gado shima yahau kan gado da jikakken jikinsu. Tashi yayi zaune yakama kafarta yadaura kan kirjinshi yakai babban yatsanta bakinshi ya shiga tsotsa yana kallon gabanta dayaga yawani irin ciko kaman kumburarren buredi yanashan yatsun kaman maye, wani iri gasping tayi tana kokarin fizge kafar dan she can't endure this feeling dayake sakataji, ahankali yadaukar da bakinshi down to writs din leg dinta yanabin ko'ina da kiss har zuwa cinyarta kafin dawani irin gudu yakai bakinshi kan gabanta da kafin ma yay locating saida yaci wuya dan naman wajen yaciko sosai, ihu ta kwala tana kokarin tashi dan wani irin shocking da zugi dataji all at the same time jikinta nawani irin rawa takama zanin gadon tarike gam tana kokarin cirewa. "St.....op it, is somehow" yanasha yana ragargaza wajen da hancinshi yace "is somehow what"? Ihu tayi tana daura hannunta saman kanshi tana daga kafafunta sama tace "somehow........uhmmm sweet" murmushi yayi yace "I told you inada ni'ima, ni mai dadi ne wlh, lemme suck all yoUr juice little girl and show you am not that little boy Ammi kecewa dan am getting you pregnant today". 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣3️⃣ Yanda yakezuko juice dinta yasa taji kaman zata shide ware hannayenta tayi takama asalin katakwayen ta rikegam jikinta namata wani ruwa she don't really know meyake mata but she finds whatever this is fantabulous, ganin yanda bamatasan inda kanta yakeba yasa da sauri hannayenshi har bari suke tsabagen kosawa dayayi yadaura su kan boobs dinta both kafin ya shiga matsawa yana bata head, wani irin turomai kirjin tayi dudda tanajin zafi dan gaman zai ciresu daga reshensu yakeyi but dadin head yasa bamatasan me akeba. "Mmmmm don't stop, I love it, is sweet" tai ihu sosai wani ruwa nasake bubbulowa da Waleed ke zukowa yana sha yana kara murza boobs din feeling kaman yamutu, baitaba samun ta ya murje hakaba sai yau, yana murzawa yanaji kaman zaibar duniya erection dinshi har yaji yaji yakemai tsabagen yanda yakosa yajishi yafara ramming nata, wani irin rawa jikinta yadauka bai aune ba tawani irin kawo da yawa jikinta yamutu, dagata yayi ahankali yahau saman kanta kafin ya kwanta agefenta yana jawota yasa jikinshi idanunta yashafa dasukai yan fici fici yana kallonta sanan ahankali yay grabbing lips dinta yafara sucking itama tana mayarmai da martani yasauke hannunshi kan nononta yana matsawa yanajan nipples din, kokarin ta shige jikinshi take yahanata yacigaba da murza boobs din tana turomai su Sunday lokaci ahaka sanan ahankali yakama joystick dinshi dake dripping yana karanto addu'an saduwa da iyali sanan yakai wajen Wall din, gabaki dayan kan joystick dinshima yafi gabaki dayan gabanta girma, ganin bazai iya ahakaba yasa yasake tashi yahau kan jikinta har lokacin baisaki lips dintaba jikinshi narawa yakosa ya sadu da ita, hannunshi dake kan boobs dinta yacire yakai gabanta bude gaban yayi ta yanda zaiga da ficicin V dinta, ahankali yakai joystick din gaban marin daidai ya ijiye ta hanyar saita ta, bai turaba dan yasan zataji mahaukacin zafi saiya maida hannunshi kan boobs dinta yacigaba da matsawa, wani sangartattacen kuka tasaki na moaning, ganin haka yasa yatura ahankali in style, rikeshi tawani irin yi gam tana yatsine fuska tana sake kissing dinshi da sauri da sauri irin kotadaina jin zafin nan, slowly yakara turawa but still bai shigaba, rawa jikinshi yafara dan sosai yay kokarin yay mata ahankali but it seems impossible and is like the more yana kokarin penetrating the more yanajan his patient nasoma karewa, wani irin ijiyan zuciya ya sauke go for the third time ahankali ko alamun budewa ma wajen baiyiba rawa jikinshi yafara wane anjonashi da shocking kaman wani mazari yadage da duka karfin shi yatura, wani irin ihu zata saki sanin yasan halin ihunta yasa yarike bakinta gam tareda matseta da kyau ajikinshi amahaukace yakoma kan yadan shiga kadan kaman irin ka leka abu dinan, tip of his head kadai dayaji awurin ji yayi his life is about to end, innalillahi, mantawa ma yayi he's having sex with Saheeba, dawani mahaukacin karfi yay shifting ciki yana sakin ihu da shine yasaki bakinta. "wayyo Allah fire!" fashewa dawani mahaukacin kuka Widad tayi tana kokarin kwace kanta ya daddage ya sake shiga kan yadan sake shiga ciki. "zan mutu omg, what is this Ya Allah daka hallita anan" yay maganan yana zaro dan kadan din daya shige ciki waje gabaki daya sanan dawani wawan gudu yakoma ciki kan yacige tass amman banzan shiga, wani mahaukacin ihu Widad ta saki ko motsi bata sakeba ta sume warwas, bata tabajin anything as strong as this agabanta ba, Ya Waleed kaman zai baremata gaba haka taji. Jin crowns dinshi aciki duka yasa yaji kaman zai mutu, bura'uba bawai cin fuska ba ko wani abu but he never felt this way inside Ilham saisa yacema Arham sex is overrated cus there's really nothing to talk about, but yau dayaji abinda ke cikin gaban Widad jiyayi kaman ma bazaiyi lasting ba wani wawan mahaukacin sperm yazomai kawai yay releasing batare dayay knacking nataba, jikinshi na bari hawaye yataru a idanunshi sosai jiyake kaman yayta having dinta non stop, when it comes to Ilham the truth is he never fancy sex baimaso yanayi da ita tunda ya lura he wasn't her first, but this small girl here he just pray Allah yasa karya kashema masu y'a yarsu dan he will so eat dis girl ko wlh harsai tanemi wajen guduwa, he just pray zata zama mace mai yawan bukata wlh koma batada shi saiya maidata with drugs and other stuff. Ahankali yakoma gefenta dan baiso ya sakeyi da ita yanzu, he will save all this sha'awa dake damunshi zuwa night tunda yanzu yadanyi creating hanya kadan, yanzu suyi wanka suci abinci suyi sallolin sanan suhuta, ahankali yakai hannunshi kan fuskarta murmushi yayi yay kissing dinta sanan yakai tongue dinshi kan saman idanunta ya shiga wasa dasu, ahankali idanunta ke motsi, ganin haka yasa ya kyaleta yakoma gefe yakai hannunshi kan boobs dinta yana murzawa yana kallon idanunta, bude idanu tayi da kyar dasukai jajir ta kallai zata fashe da kuka yace "listen if you cry I will sex you now lazy girl" hana kanta kukan tayi ta hadiye tana ware kafafunta dataji kaman anzuba yaji, murmushi yayi danya lurada abinda tayi yakai hannunshi kan gaban yadan shafa kadan yace "sorry, tonight I will take all the pain away, do you still love me"? Gyadamai kai tayi ahankali kaman wata marainiya, kiss yamata a kumatu yace "and I love you more my little wife" sauka yayi daga kan gadon tabishi da kallo juyowa yayi ya kalleta ganin inda take kallo yasa yakama joystick dinshi yace "kinga is still erected ko, bankoshi dake bane wlh daurewa kawai nayi, kidena kallonmin working tools" yay murmushi tareda shigewa bayi, hada ruwan zafi yayi acikin bathtub din dake separate place acikin bayin sanan yafito yana kallon fuskarta ganin ko motsin kirki bata iyayi kuka ma take, murmushi yamata yakai hannunshi zai dauketa bugemishi hannu tayi hakan yasa yace "haba my small nono queen" yay maganan yana sunkutar ta yay bayin da ita, wani shegen kuka takemai amman bai biyemata ba saida ya wanketa tass yamata wankan tsarki sanan yafito da ita sharemata jiki yayi yaje wardrobe din dakin yadauko mata wani white gown mai kyau da hijab yakawo yasamata sanan yasakamata su ya shimfida mata dadduma yace "pray nima bari naje nai wanka" yawuce bathroom ko kallonshi batayiba tafara sallan azaune dan zafi takeji sosai akasanta, tana kan dadduma yafito shima shiryawa yayi tsaf cikin wata farar jallabiya sanan yazo kan dadduman yahau gefenta ya kabbarta salla, ahankali tadaga kanta tana kallonshi ta jingina da gadon, Waleed nada kyau wlh kaman wani balarabe saidai kawai banbancin shi da balaraben shine sun fishi haske sosai, gashi dawani irin mahaukacin saje kwantacce mai shegen kyau yana sheki, gashi murdadden namiji ga natsuwa da tausayi, very very softman da mata kan kira maza irinshi da burin mace danko wace mace nason tasami irin Waleed. Kiss dataji an sakin mata yasa tai firgigit tadawo daga long tunanin dataje ta kallai saikuma tai raurau da ido zata kuka, ahankali yace "shagwababbiya kina kallona kina admiring dina, yanzu kuma just because I kissed you kinason kimin kuka" turomai baki tayi amugun shagwabance tace "is it not you" jawota yayi in a very caring way yasata a kirjinshi yace "ni mijin Saheeba menayi"? Kaman zatai kuka tace "that thing ahhhh, the place hurts" dan dariya yayi yace "gobe dasafe zan samiki magani" da sauri tana kan kirjinshi tanawani kara narkewa tace "why not now"? Cikin kwaikwayon muryanta yace "because the main course takes place later, now bari nakira abaki abinci mezakici"? Shiru tayi tana kallon lips dinshi kafin ta lumshe ido ahankali tace "aubergine dip, tangine, rice with herbs, beans in garlic, flat bread and zucchini marinade" shiru yayi yana kallonta, jinyay shiru yasa tabude idanunta ahankali ta kallai, hada ido sukayi ahankali yace "how did you know all this foods? Koni I know Tangine sabida nataba zuwa morroco lokacin ina yaro tareda Abba na kafin yarasu munje vacation, I know tangine very well sabida shine Morocco's most popular dish, but how did you know all this meals dan ba abincin yan Nigeria bane" yasake shiru yana kallonta kaman maison gano game da ita sanan murya chan kasa yace "who are you Saheeba"? Washemai baki tayi dimples dinta suka lotsa kafin ahankali tace "I am Saheeba, Dr Waleed Warbai's Wife" ta murgudamai baki dayaji abin yamugun burgeshi ya dungure mata hancinta yadagata yadaurata kan gado sanan yatafi wajen landline din gidan yakira restaurant din Uncle yasanar dasu all abincin data fadi akawo musu sanan ya ijiye wayan yadawo kan gadon yazauna kusada ita, shigewa jikinshi kawai tayi tai lamo tana shafa kirjinshi ta saman riga tana sauke ijiyan zuciya yana jinta har bacci yasoma debanta, knocking kofar gidansu da akayi yasa yadagata ya kwantar da ita yawuce yafita ya karbo abincin da aka jejjera musu a wasu hadaddun jakunkuna ya fiffito dashi sanan yataso yadauketa yace "zokici" zaunar da ita kusadashi yayi tana runtse ido sabida zafin dayakeji idan zata zauna, yana kallonta yanajin dariya amman yarike dariyan suka faracin abinci sosai yaga taci abincin abin har mamaki yabashi sai yama kasaci ya tsaya yana kallonta, sosai taci sanan ta ture daidai anfara kiran magrib tashi yayi yace "natafi mosque, sai anyi isha'i zan dawo, do you need anything"? Girgizamai kai tayi alamun a'a, daukowa yayi yamata peck a goshi sanan yawuce yatafi wani irin farin ciki yakeji sabida yasan yau shi angone. Saida aka kira isha'i tai sallan isha'i sanan ta tashi tana dingishi idan akwai abinda tasan Mom ta koyamata shine tacemata duk in taji gabanta namata zafi tadinga deban ruwan zafi tana tsarki dashi, kayanta ma tacire gabaki daya tawuce bayi tana dingishi tana turo baki kaman zata fasheda kuka, wanka tayi sai bayan tagama sanan tai tsarki da ruwan zafin tafito daure da towel, tadau ribonta kulle gashin kanta daya bushe dan tun dazu ajike yake, gaban wardrobe din dataga yaje dazu taje tabude taga kayane nasu da yawa, wani white kayan bacci datagani yar figigiyar riga tadauko ta zura sanan tafeshe kanta da sababbin turaren mata datagani anjera mata ata bangaren kayanta tadau pant fari shima tasaka, kamshin hadaddun turaren yabi yacika dakin sanan tajuya ahankali tai kan gado tana kallon kofa, duksai taji tagaji ganin itakadai ne agidan, kaman tabude kofa tafita tabishi haka takeji, kwanciya tayi ahankali kan gadon taja bargo ta lullube kanta tana kallon kofa Allah Allah kawai take ya shigo. Yana fitowa daga masallaci yatafi wani shago dasuke yin business din kira, biyan kudi yayi ya karbi wayan yasaka number Ilham yay dialing, kaman bazata daukaba wayar na gab da katsewa tadauka, anatse cikin tattausan murya yace "kin sauko Mom Arham" muryan Waleed dataji yasa tace "wlh nizaka ciwa amana ko, nizaka karoma kishiya ce, Waleed niko, harma kadau amaryan ka kutafi honeymoon wlh you are a cheat cheater kawai" duk murmushi yayi yana jinta hartakai aya sanan yace "where is my boy" wani irin ihu tamai tace "ni zaka maida mahaukaciya eh, nizaka maida mahaukaciya ina maka magana kana tambayana Arham, Waleed wai is it a crime to love you sabida kaga ina sonka shine kakemin haka eh" ganin bala'in takeji yasa yace "I think this is not the right time will call you tomorrow" kafin ya katse wayan tace "dats wat u always say dazaran nafara magana ai, shege matsiyaci, maciyin amana jarababbe, yaro dakai ko 29 baka kaiba har kasan kaci mata biyu, banza kawai shege" sosai Ilham tashiga duramai uban asahr sabida shegen kishin dayahau kanta, katse wayan kawai yayi sabida bayason matsalan ta yamika mUsu wayansu yabar shagon ranshi ba dadi. Wuraren 10 nadare ya shigo gidan yamaida kofan yarufe, kamshin turaren jikinta kadai dayaji tundaga falon dakin ya mantar dashi bacin ran da Ilham tasaka shi ciki. 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣4️⃣ Wani irin sassanyar ijiyan zuciya ya sauke yamika hannunshi ya kashe wutan falon bayan ya maida kofan yarufe da key sanan yay hanyar bedroom, bude kofar dakin yayi ahankali wani hadadden sassanyar kamshi yama hancinshi oyoyo, saukar da idanunshi yayi akanta yaga hartai bacci har lokacin kafafunta awawware, dan murmushi yayi tareda cije lips dinshi a iskace irin zaki sani dinan ne, cire jallabiyar jikinshi yayi yatafi wajen wardrobe yabude ya rataye sanan ya mayar yarufe yajuyo yawuce bathroom, bude kofa yayi yashiga ciki yay wanka da ruwa mai dumi sanan yadauro alwala yafito daure da towel yana kallon fuskarta, if there's one thing daya lura akanta shine tanada nauyin bacci, gaban wardrobe din yakoma ya tsaya yabude, wasu mugayen turaruka yaciro daga side dinshi yadaga ampit dinshi ya fesa, da kasan gemunshi, sanan daidai maranshi yasake fesawa dakin yadauki kamshi da ake kira da nabar duniya, gyara kanshi yayi tsaf sanan yadauko wani sabon pant na maza fari looking super sexy kaman wani male stripper. Juyowa yayi yana tafiya ahankali yabude kofar bedroom din yafita, baiwani dade ba yadawo ciki rikeda wani cute goran honey, hannunshi yadaura kan switch din wutan dakin ya chanza wutan zuwa wani dim blue light dake sanyaka feeling cozy, ahankali yatashi daga wajen sanan yataho yahau gadon anatse da bismillahi dan bayison yatadata yana kallon fuskarta yanabin fitinannen rigan baccinta da kallo, bude marif goran zuman hannunshi yayi dayake she is lying on her back yasa ya matsa honey asaman kirjinta tawajajen cleavage dinta sanan yarufe goran ya ijiye agefen shi, ahankali yakai kanshi kan kirjinta daura hancinshi yayi kan wuyanta yana shakan wani magical kamshin dake fita daga jikinta dayake neman yasashi yajike all of a sudden, ahankali yadaura hannunshi kan rigan bacin yadanja rigan baccin kasa hakan ya bayyanar da white boobs dinta, hannunshi yakai yadaura kan boobs din duka biyun batare daya matsa ba sanan yafara sakin mata wasu irin pecks masu shegen kara dake tada tsigan jiki awuyanta, wani irin motsi tayi dan dudda tana bacci saida tsigan jikinta yatashi ahankali yakai bakinshi kan honey yafara leaking kaman irin sabon mayen nan da maita bai dade da kamashi ba, wani wawan ajiyan zuciya tasauke tareda bude idanunta ahankali tana kallon ko'ina, dago kanshi yayi yakai fuskarshi saitin nata yadan fito da harshen shi ya lashe tundaga gemunta har zuwa kan goshinta da sauri takai hannunta tarikemai waist gam tana numfashi da sauri da sauri, cikin wata deep voice yace "Hey pretty girl" yasake lasan lips dinta yace "I wanna do you some freaky freaky things" yay maganan yana tura harshen shi da karfi cikin bakinta da sauri ta chapke harshen kaman wacce ta tashi da yunwa suka shiga kissing juna, dagota yayi zaune yana daurata kan cinyarshi yana wani bankare mata yana tura mata kirjinshi yakama hannayenta yakai kan kirjinshi bakinshi nacikin nata kaman zai fashe mata da kuka yace "romance me please, touch me anyhow, kiyi duk yanda kikaga dama dani, am all your baby" itadai batasan mesaba Allah yazuba mata son taba kirjinshi sabida chest dinshi abude gawasu kwantaccen suma ga nipples dinshi bakake, ahankali take shafa kirjinshi shima yashiga shafa kirjinta kaman yanda takeji yanajin wani mahaukacin dadi, matsa boobs din yayi ahankali hakan yasa tai making wani malalacin moarn irin na yaron dake shirin sakin kuka dinan. "urhhh" ta turomai kirjinshi itama tana kama nipples dinshi ta murza, mugun haukacewa yayi he never knew cewan nonon maza is an erogenous area saida ta tabamai, cikin wata yar malalacin murya yace "squeeze it like that pretty, oh my god it feels damn gooood" yay maganan yana sakin right boobs dinta yakai hannunshi kan joystick dinshi dake cikin pant din daya saka tanamai wani mugun ciwo dan pant din bai bari yamike ba, ta gefen pant din yafito da joystick din, har wani nishi take kaman kumurci tsabagen yanda jaraba kecinta, ayanda take duk gaban data kama da daddaren nan saitai banna, hannunshi yamika yadauki honey daya taho dashi yabude yazuba akan joystick din yay wanka dashi kan joystick dinshi sanan ya ijiye goran, ahankali yaraba bakinsu cikin muryanshi dabata fita sosai yace "suck me, blowjob, I terribly need it" yatashi tsaye kan gadon itakuma yabarta azaune ayanda take jikinta yamutu tatas yakama kanta da hannu daya yakai kanta kan joystick din daya wanke da zuwa, ahankali takai bakinta tadan lashi kan, dadin dataji yasada sauri yakai duka bakinta danji tayi kaman tasami alewa mai tsinke tafara shan joystick din kaman wata wacce ta kware tanabin zuman dayakai har kan shaft dinshi tanayi kaman zata hadiye duka joystick din dayafi karfin bakinta dan yanada mugun kiba ga tsayi. "wayyooo Allah na, my dick mehnnn, oh lord of heavens pretty ahhhhh! Your mouth feels good, wayyooo wayyooo ta cijan" yay maganan yana danna kanta kan joystick din yanaji tana kakarin amai, but the feeling of zatai amai da yanda tiny makogoronta kerawa akan joystick din wants to make him drop every inch of his cum in her mouth, ganin bakinta nason yamata illa yana neman yakawo yasa yazaro joystick din da sauri yay kanta yahau kissing dinta yana nishi da sauri da sauri kaman wanda ke shirin suma itama tana kissing nashi back, pants din jikinshi yacire ya yar sanan yakama rigan jikinta yacire ya yar tareda cire pant din shima yayar, goran honey yadauka yasaki bakinta ya shiga diddiga mata tundaga kan boobs dinta daya wankesu da honey down to her stomach, her navel, abdomen kafin yasauka kan kumburarren cikakken gabanta kaman gaban mai kiba nanko batada kiba ko daya, daga honey yayi yazuba mai bala'in yawa agaban, wani irin nishi Widad tasaki tana kara ware mai kafafun tareda kama bedshit zuman namata wani irin sanyi ea damshi agaban, ahankali yasa hannunshi yanayin facha facha da zuman agabaki dayan wall din tundaga inda gashi ke fitowa down to wajajen an*s, ahankali yasaukar da kanshi ta daidai kasan mara inda gashi ke fitowa da nata kenan so smooth kaman gashi baitaba fitomata ba ya lashi zuma wajen inya vertical way, wani irin nishi tayi ta kankame zanin gadon gam da hannayenta, sake laahe zuman Waleed yayi down to her vulva, cikin wata irin murya tace "ahhhhh Ya Waleed" ahankali yana tura nose dinshi daidai wajen vulva yana separating nasu dan yasamu daman chapke clit dinta yace "yes pretty" yay maganan yakai tip of his tongue ya laso clits dinta da asalin Jan bangon wajen, wani shegen ihu tayi he could see yanda wani ruwa yafito daga hole dinta da gudu tace "uhmmmmm Ya Waleed ouuuch" yanda take moaning da her little voice is freaky turning him more into a beast, is making him wanna have her super rough that kind master and slave sexs dinan dazaka nuna mata you fucking own her, gabaki daya taburkita shi hakan yasa yashiga sucking nata so rough yana laso every bit of honey daya zuba awajen, ihu take da farko saikuma tafara kuka takankame bedshit idanunta na juyawa kaman tana shirin shidewa sunanshi kawai take kira saida yaga tana neman ta sumemai dan saida ya zuko gabanta tass sanan yaciro kanshi still ihu take dan batasan yama dena ba, yakai bakinshi kan boobs dinta daya zuba honey yashiga sucking yana kara bude kafarta yana karanto addu'a a zuciyanshi at this point yariga yay making up his mind he must sex her and saiya shiga ciki fully yau he want to feel himself kaman all other married men in the whole world, tana cikin ihu taji abu na kokarin shiga wajen by voice at a spot tadawo hayyacinta, zatai magana yadaura hannunshi kan bakinta ya rufe gam sanan yawani matseta ta yanda koda wasa bazata iya guduwa ba nor ta iya mishi gardama ijiye tausayi yayi ya ijiyeshi agefe inya biyema tausayi bazai taba saduwa da Saheeba ba dan she is way to tiny and too small kafinma kai locating hole dinta is a work, dagewa yayi ya shigeta yana kara danne bakinta da kyau takasa ihu, ga hannayenta yahade ya matse ballema tabuge hannunshi nakan bakinta dashi, tanaji tana gani Waleed kemata wani irin mugunta dayasha taji kwakwalwanta namata kaman zai fashe, tana ganin wasu fuskokin mutane aduhu dabata gane waye, dawasu irin abubuwa, saikuma taga kanta tana gudu tareda wata mata awani hadadden wakacecen compound, saikuma fess tasume daidai lokacin daya shiga cikinta da karfi dayaji gabaki dayanshi, fashewa da kuka yayi baitaba jin pussy hakama, gaban Saheeba jiyayi kaman an matseshi irin matsewan nan dakakema kayan daka wanke in kanason ruwa yafita, ganin tasume which dama he already knew hakan zai faru yasaki bakinta chapke boobs dinta yayi dan su zamemai comfort inba hakaba irin ihu da kukan dazaiyi sai makota sunzo, ahankali yazaro waje sanan da karfi da yaji yasake tusawa ciki hawaye shi nabin nononta, kaman zaibar duniya, baison abinda zai yankemai wanan jin dadin, knacking dinta yafara da kyau he screw her so well sabida wajen yasaba da abunshi dan wlh ayanda yajita he don't think daga rana tayau akwai randa zai iya dagama yarinyar nan kafa bai having nataba saidai in tana MP, ajiye tausayi yayi yay sex mai kyau sabida baiso gobe tawahala inzai sake gwara yau taji zafin gabaki daya a wuce wajen, good 4round yayi da ita sanan yajishi ya gamsu sosai gamsuwan dabai tabaji yayi irinshi ba tunda yay aure, sanan yazaro sperm dinshi nabiyo shi dan Allah yahoremai yawan sperm kodan sabida lafiyayyun abincin dayakeci ne oho, sanan yatashi ahankali yazauna yanabin gaban nata da kallo thinking of abinda zai mata da bazataji wani zafi sosai ba nanda nan zafin zai tafi, hannunshi yadaura kan wajen yaji har wani zafi yayi tsabagen wahala murmushi yayi yace "am sorry, it wasn't my fault, you are too sweet I couldn't hold myself back" dubata yayi ganin ba tear sai lot of bruises which daman yasan yamata yasa yay hamdala, yana kallon gadon babu wani jini saidai sperm dinshi dake fitowa daga jikinta gauraye yake with stain of blood, murmushi yayi yaja bargo ya rufa mata baimason yatadata yanzu yasauka daga kan gadon yay bathroom yana kallon agogo ganin hudu saura na asuba, bayi ya shiga yay wanka mai kyau yana wani wanke gabanshi yana murmushi yace "God thank you daka bani wanan gaban dat I can use and satisfy any woman, the best kyauta shine Allah yamaka bura da mace zata jita yasata sanan ya gamsar da ita, wayanda basUda ita saisu koma ga Allah su roka dan dabarunka baya baka". 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣5️⃣ & 5️⃣6️⃣ Wanka ya gamayi tass ya tsaftace kanshi yafito daure da towel a waist dinshi babu komi a kasan towel din, Kallonta yayi yaga tana barci tana sauke numfashi loudly, murmushi yayi yace "kin farfado kenan" Daga kafa yayi sadaf sadaf ya taka zuwa godon, zama yayi ta baki bakin gadon tareda yaye blanket din daya rufe ta dashi yanabin jikinta da kallo still dai bata bude idanunta ba. Sunkutar da kanshi yayi yafara ruining mata wasu matsiyatan kiss all over her face, jin saukar cold abu dats a lil bit wet akan face dinta yasa tafara bude idonta dasuka kankace suka kumbura tsabar kukan data sha cikin dare, bare baki tayi zata saki wani kukan sighting him datayi akanta yana kallonta kyalkyacewa da dariya yayi ganin duktabi ta tsorata dashi yanzu ya sunkuceta yayi bathroom da ita ya sakata acikin bathtub dake dauke da ruwa cike mai zafi nagashi. Kuka tafarayi sosai tana yarfe hannu alamun zafi. "Sshhhhhh, sorry Pretty, it hurts right?? " Daga mishi Kai tayi still tana kuka bata ce komai ba, cikeda lallashi dakuma tsantsan so da tausayi yace " Okey stop crying kinji, after this bath you will feel relieved" still dai kuka tacigaba dayi kamar ba da ida yayi magana ba, ganin bazatayi shuru ba yasa ya dauko sponge yayi da shower bath ya fara mata wanka tanata kuka tama kasa tsayuwa da kyau, yana gama mata wankan sabulu ya tara hot water tare da surkashi da ruwan sanyi acikin wani bowl. Daukarta yayi ya sakata cikin hot/warm water din. Ihu tasaki tare da mikewa tsaye da gudu tace "Ya Waleed, it hurts" tausayi tabashi but baiso ya nuna mata tabashi sosai dan bazata bari yayi the right thing ba. Kara mayar da ita yayi cikin hot water din da kyar ta yarda ta zauna acikin ruwan har ya huce. Yana gamawa ya mata wankan tsarki ya nannadota cikin towel suka fito, zaunar da ita yayi akan kujerar yaje yacire zanin gadon yasa wani sabo dan sun bata wanan da juicec dinsu yasa wanda yacire kuma yasa acikin washing machine. Yana Gama laying bed din yataho kusada ita akan kujera yana kallon yanda she look damn sexy da daurin towel dake kanta, zuwa kusa da ita yayi yagan har ta fara barci fuskarta duk yayi jaa abunku da farar fata, picking dinta up yayi ya kaita kan gado tare da lullebeta da blanket. Clock din bango ya duba ya gan 5:35 am lokacin subhi yayi, wardrobe dinsu yaje ya shirya kanshi tsaf cikin farar jallabiya itama yadauko mata wata farar jallabiya ta mata shara shara da dogon hijabi yazo yasanya mata, dadduma ya dauko tare da gabatar da sallan nafila sanan yatashi yadukarta yayi dagakan gadon yadaurata kan dadduman, kiss ya mata a forehead hakan yasa ta bude ido. " Pretty, it's time for prayers kinji, zan tafi mosque, will get you drugs idan zan dawo, do you need anything kafin natafi"? gyada mishi kai kawai da sauri yace "me kikeso" murya chan kasa hawaye na bulbulowa daga idanunta tace "yogurt" da tashi yafita daga bedroom din baiwani dauke time ba yadawo dakin rikeda wani hadadden youghrt da glass cup ya ijiye kusada ita yace "shikenan"? Gyadamai kai tayi yasake mata peck a goshi yace "natafi" yawuce yatafi masallaci dukya damu ganin yanda takejin jiki but deep down zai iya buga chest yace "he's the most happiest man on earth today, saiyau ya yarda sex is not overrated actually sex nada dadin da ake yawan cewa yanada shi, and disvirgining a virgin feels awesome, kaman yaje yasake yakeji. Wuraren 7 ya shigo gidan hannunshi rikeda leda na magunguna nawani pharmacy, shigowa bedroom din yayi yamaida kofa yarufe yana binta da kallo ganin bacci take hankali kwance kan gado, karasawa yayi yadauki roban yogurt din ganin tasha sosai tama kusa shanyewa yasa yaji dadi sosai, ya ijiye sanan yaciro magungunan daya sayo, wasu allurai kala biyu yahada, sanan yakai hannunshi ahankali ya yaye riganta sama, gentle yamata alluran, dayake bacci ya shigeta ko motsi batayiba dan hannunshi baida zafin allura ko kadan, fita yayi da syringe din yakaishi waste ya yar, sanan yadauko mata bottle water yadawo dakin, ballo magungunan dazata sha yayi yadawo kusada ita yazauna, dagota yayi ahankali yace "zokisha magani saiki koma bacci kinga jikinki yasoma zafi" yay maganan yana bata maganin, karba tayi ta sha yabata ruwa takora sanan ya kwantar da ita ganin sosai takejin baccin, tashi yayi ya ijiye komi sanan yacire jallabiyan jikinshi yamaida hanger yadawo ya kashe wutan dakin sanan yazo yahau kan gadon, hannunshi yadaura kan jikinta yana shafata ahankali sanan yakama boobs dinta ya shiga matsawa, fashewa tayi da kuka, kasa hakura yayi ya yaye rigan sama kaman wani yaronta yakai bakinshi kan boobs din yashiga sha yana matsa dayan, tun tana kuka hartai shiru ganin baya wani abu kuma, wani irin dadi takeji yana yake sucking sanan yana murza nipple din dayan, ahaka tun tana jinshi har bacci yay awon gaba da ita shima haka bakinshi nakan nono. Kiraye kirayen sallan azahar dayajine ya farkar dashi daga daddaddan baccin daya kwashesu, bude idanunshi yayi ahankali yaga har lokacin bakinshi nakan boobs dinta, murmushi yayi yasaki boobs din yana kallon yanda kan yay jajir, daga kanshi yayi yagan har lokacin barci Widad take tana sauke ijiyan zuciya ahankali ahankali, hannunshi ya daura kan kumatunta yaji jikinta bazafi yanzu ko kadan, tashi yayi ya shiga bathroom yasakeyo wanka yaje closet ya dauko wani farin jallabiya da wando ya saka, yafeshe kanshi da turare yay kan gado gefenta yaje ya sunkuya ya sakin mata kiss a forehead dinta still bata tashi ba, ko motsawama batayibaa, murmushi kawai yayi yafita daga dakin batare daya tadataba. *One hour later* Shigowa gidan yayi hannunshi rike da jakunkunan abinci daya karbo daga eatry bude kofan yayi ya shiga bedroom dinsu, kwance ya ganta yanda ya barta tana shekan bacci kasancewan bata sami najiyaba, ijiye kayan dayariko yayi ya zauna akan gadon ya fara shafa fuskarta. Bude Ido tayi, tana kallonshi kafin ta dauke fuske tana bitting lower lips dinta alamun something is paining her, dagota yayi ya daura kanta kan chest dinshi yana shafa bayanta. "How are you feeling my babygirl, Pretty lady" turo mai baki tayi kamar zata mishi kuka saikuma ga hawaye sharr suka zubo, da sauri yakai hannayenshi ya share hawayen yace "no baby don't cry okey, I just make you a full woman yesterday, what we had yesterday is normal thing dat a husband and a wife those" yay dan shiru yana kallonta ganin kuka take sake shirin mai yasa yace "if you cry again I will sex your sweet pusss wlh, dan I will not mind nakara wani now" yanagama maganar ya fara dariya ganin yanda dukta tsure tahadiye kukan tsaf, matsar da ita yayi kadan sannan ya bude takeway daya shigo dashi budewa yayi fara bata chips dake ciki. Gamtse baki tayi alamar baza taci ba... "Idan Baki bude bakinki kinci ba I will screw you again" da sauri tabude baki tafara ci . Saidataci ta koshi sannan tafara girgiza mishi kai alamun ta koshi. Tashi yayi ya dauko mata maganin daya siyo mata ya bata na rana tasha sannan yakaita bayi tadauro alwala yazo yadaurata kan dadduma tafara salla, ya kwashe takeaway din ya kai kitchen bayan yadanci shima. Zuwa yamma ta dan fara samun sauki sosai kaman ba itaba sabidaa maganin da Waleed ya baata tasha, gabaki daya tadaina jin ciwon jikin, zafin datakeji awurin ma tadaina ko pain killers yabata oho, kokuma sabida gasatan dayake every minute ne oho, amman dai tadainajin any zafi kaman anzareshi daga jikinta. ******** _Washegari_ Yau kaman kullum garin was so quiet and serene, ta tashi yau ta samu sauki sosai sabida kulawan da Waleed yabata na musamman, wajen ya daina mata zafi ko kadan unlike jiya datakeji kaman an daddaka barkono da kayan kamshi an watsa awurin, dakanta ma tai wanka ta shirya cikin wata yar singlet fari na mata da farin boxer singlet din na mata, shimin yamata shegen kyau kana ganin yan kananun nonuwanta gwanin ban sha'awa tacikinsu babu bra akai, ta daure kanta dawani yellow ribbon gashin na lilo wani dan sili agaban goshinta yabi gefen fuskarta, kana ganinta she look like a little angel. Zama tayi akan gadon bayan tai salla tadau system dinshi datagani akan bedside drawer alamun yay amfani dashine datana bacci ta shiga tattabawa tana mamakin ya akayi ta iya. Bude kofar bedroom din da akayi yasa ta dago kanta, ganin Waleed ne ya shigo rikeda jakunkunan breakfast dinsu yasa ta tashi dagudu tai wajenshi hakanan taji wani irin farin ciki takeji data ganshi, wani irin tsalle tayi ta dane jikinshi. "oyoyo Ya Waleed" sakin duka jakunkunan hannayenshi yayi suka zube anan bakin kofa, yadaga hannuwanshi ya rungumeta back yana shafa bayanta kafin finally yay landing hannunshi kan ass dinta yace "please go gently on Ammi's only Boy fa, karki kashe mata d'a" wani irin murmushi ta sakinmai tana bala'in sonshi whenever yamata wanan barkwancin, hannayenta ta kulle a bayan wuyanshi tana kallon fuskarshi kaman yau tafara ganinshi, daga mata gira daya yayi cikeda iskanci yace "Ya akayi ne yan mata"? Washemai baki tayi saikawai ta manna mai wani irin kiss mai gunna akumatu sanan tadago kanta ta kallai tana lankwasamai kai tana murmushi, cikin sweet voice dinta tace "you are so Cute Ya Waleed" shiru yayi yana kallonta kiss din datamai was still a shock to him, sosai muryanshi ya shake, murya chan kasa yana kallonta yace "if I am cute that makes me what"? Washemai baki tayi da sauri tace "Cutest", dan dariya yayi ya rungumeta tareda manna mata kiss shima akumatu yace "you are so brilliant Pretty, am happy a woman if your calibre become my wife, its an honour, nothing beat ka auri mace natsassiya data kawomaka mutuncinta gidanka, Allah yamiki albarka kinji" lips dinshi dataketa kallo tama peck, hakan yasa yakai hannayenshi kan boobs dinta daketa tsolemai ido ya matsa, dirkowa tayi daga jikinshi tana turomai baki tace "ammmm, stop ittttttt" murmushi kawai yayi sai binta yake da kallo. Breakfast sukayi tare sukaci sosai yasake bata magungunan tasha, ganin tanata zufa yasa ta tashi tashiga bathroom zataje tasakeyin wanka, saida ta shiga bayan yagama bin tempting ass dinta da kallo dayasa yaji yana wani irin mugun shaa'wanta ya kwala mata kira. "Pretty wanka zakije kiyi without me, ahhh that's not fair bayan kullum nike miki sanan nama kaina" ya karashe maganar da fuskar tausayi kamar zaiyi kuka voice dinshi na cracking, sanan ahankali yace "have you forgotten the promise we made to each other yesterday that we will always bath together so fast"? Bude kofar bathroom din tayi rikeda singlet dinta a hannu tana kare kirjinta ta kallai shikuma yabita dawani mayen kallo kaman yaune yafara ganin tsiraicinta, murgudamai baki tayi tace "I'm scared, I don't want you to put that inside me, it hurts badly" ta karishe maganar kamar zatayi kuka tana yatsine mai fuska. Tashi yayi da sauri hakan yasa ta kwasa ihu kafinma tagudu yazo bayanta ya rungumeta ta baya yamanna mata kiss abayan kunnenta mai kara, wani irin goosebumps ne suka fito mata ajiki lokaci guda sabida yanda taji, rike hannunta yayi yana shafawa tare da jan hannunta yana kallon fuskanta kaman yanda take kallonshi yadaura kan kirjinshi yanajan hannun kasa har zuwa kan joystick dinshi data mike dake cikin wando ya daura akai, cikeda rashin kunya irin na maza yace "can you feel how hard you get me"? Yay maganan yana lashe lips dinshi in a very naughty way, dariya tayi ta fizge kanta da sauri tashiga wurin shower dan batason wankan bathtub da saurinta, tsayawa yayi yay stripping kanshi naked sanan yabita shima da saurinshi yana murmushi irin yasami tsuntsun daga sama gasashe dinan.. Bude kofar wajen shower yayi da sauri tajuyo ganin shine yasa da sauri ta fizgo kan shower daga jikin bango ta juyoshi ta fesamai ihu yayi sabida ruwan sanyi ne yace "ahhhhh Ammmmmii" kyalkyacewa zuwa yayi ya fizge shower yajuya shi kanta, kwakusa ihu tayi tafada jikinshi ta manne yanajin saukan bare nononta kan kirjinshi, hannunshi yakaita bayanta ya taimaka mata yaja boxer daya rage shikadaine ajikinta kasa yafita daga jikinta. Bin white jikinta yayi da kallo sabida daman babu komai aciki ba apart from boxer daya cire mata. Sakinshi tayi tajuya in a very sexy way tafara tafiya tafito daga wajen shower tai wajen bathtub ruwa tahada ta shiga cikin bathtub din bombom dinta yana wani irin shaking tai relaxing kanta a inda ake ijiyekai. Tana shiga tajuya ta kalleshi tachan wajen shower inda ta barshi yana kallonta kaman wani solobiyo, kashe mata ido daya yayi ganin tajuyo tana kallonshi yace "baby you are so sexy I swear, damn! Kai na auri mace awajen nan" yay dan shiru yana lashe lips dinshi, murmushi tamai ahankali tace "and you are sexy too Cutest" dariya yayi yace "really" yay maganan yana fitowa daga shower yazo wajen bathtub kusa da ita, gyada mishi kai kawai tayi ta wani watsa mishi ruwa a fuska tana dariya, one thing daya lura is tanada neman tsokana, hakan yasa yace "kika jikani? Don haka tare zamuyi wankan nan" yay maganan yana wani irin kallonta yana tsaye a gabanta itako sai kallon gaban Waleed take ganinshi amike har wani rawa rawa yake kaman yana numfashi, she just don't know why but she fancy looking at his joystick kodan bata taba gani bane oho tanadai balain son kallon dakuma taba gabanshi, it gives her wani irin unexplainable goosebumps. Ganin inda take kallo yasa ya tsaya agabanta tare da mayar da hannunshi bayan head dinshi ta baya ya wani bankaro mata gabanshi haryana dan gogan fuskarta abunka da katon gaba yace "stop admiring it from afar, touch it, it's all yours, Inshort ai shine yajin miki ciwo koh, purnish ittttt Baby" yakai hannunshi yawani irin jaa joystick din sanadiyar hannunta dayaji kan calves dinshi tana wani mishi waiwayi. Chakpe hannunta yayi yarike ganin tana neman kasheshi sanan ya shige cikin bathtub din, ya shiga cukurkudata sun dade abayi sanan suka samu sukai wanka suka fito palo, share mata jiki da towel yayi shima ya goge nashi sanan yawuce ya shiga bayi ya mayar da towel din yadawo kashe wutan dakin yayi dakin yay duhu kaman dare sabida thick dark curtains ne ajiki sannan yakama hannunta yarike yace "let's go to bed am so sleepy jiya baki barni nai baccin dareba da rigiman ki" Kwanciya both sukayi akan gadon yaja bargo ya lullube su, itakuma ta kwanta akan kafadarshi tana shafa mishi gashin kirjinshi dasuka kwanta lubluba sabida wankan dayayi, shiru yayi yana jinta cikin wata yar kankamuwan murya yace "If you continue robbing my chest like that I won't be responsible for what will happen next" turo mishi baki tayi kamar wata baby, Kissimg bakinta yayi yana murmushi sosai yakejin sonta aranshi kaman zai zare. Itama kissing dinshi back tayi hade da lashe mishi bakinshi da tougue dinta da sauri ya capko bakinta ya shiga bata wani irin mugun kiss jan bargon daya lullubesu dashi yayi yayi ya wurgar chan kasan daki, daukarta yayi ya daurata akanshi yana cigaba da kissing dinta kaman zasu cinye bakinsu, hannunshi daya na shafa mata boobs dayan hannun kuma na caressing bombom dinta dashi, sai moaning sukeyi da numfarfashin su kadai ketashi adakin, jan abunshi yayi ya tsayar dashi kafin yadan dagata sama yasa manhood dinshi daidai gabanta. Yace "Pretty sit on it" zama kadan tayi akai duk suka saki ihu tare, shi na dadi ita kuma nazafin dataji, yarfe hannu tafarayi tana shirin kuka tace "Cutest it still hurts Allah like the other day" shikuma dayagama rudewa burinshi kawai yacita yace "please do it again Pretty, it will not hurts koma it hurts zan baki magana I am a Dr remember? Please eat me Pretty, sit on it ahankali" yakai hannunshi kasan hips dinta yana kara gwlae fatar wajen sanan yakai bobom din kan mikakkiyar joystick din tadan kara zama kadan ya shiga kan da kyar sabida yanda yakama kafafunta ta zauna akai by force, ihu tayi still tana yarfa hannu tanason tai kuka, ahankali ahankali yadinga mata wayau harta gama zama akai dukka yatura gabaki dayanshi cikinta yana rike kafafuwanta gam. Waleed wani irin nishi yake saki kaman zai shide tsabagen dadin dayake ji yana sama da kasa da ita daga baya kifoda ita gado yayi yafara sex mai kyau da ita, tun tana daurewa tanajin dadi tafara kuka danta gaji, ita kuka shi kuka haka yay 2round yakyaleta da kyar. Na yauma yamata zafi amma yana hade da pleasure dakuma dadi, daukarta yayi ya shiga bathroom ya mata wanka suka fito suka kwanta sai bacci. Hakka suka dunga barci sai dai su tashi su ci abinci, ko fitada ita waje baiyiba ya ijiye ta agida yabata abinci taci shima yaci nashi, gashi bata iya resisting nashi dan he is so charming ko Allah ma yasan yanda yake sonta itama haka take sonshi, wani shakuwa, tsantsan soyayya, tausayi da kaunar juna nakara kulluwa tsakanin su. _Bayan kwana 5_ Sosai sukai building wani unimaginable love that only them can define it, saidai one thing is babu randa baya sakata kuka, bawai sex ne bataso ba, tanaso dan tana bala'in jin dadi kawai dai baya gamawa da wuri, gashi baya aikin fari bare nabaki masallaci kawai ke fitarda shi, inba masallaci ba yana makale da ita yana kwakusarta kaman tazamemai abinci, kusan duk sallan da zashi saiyay wankan tsarki, dan yana dawowa daga masallaci zai dasa daga inda ya tsaya, yazame mata kaman cingum, ya nace na linke yakuma manne mata danhar tasoma sabawa da halin Waleed na maitan saduwa. Shirye shirye suka farayi na barin Dubai dan tafiya aikin umransu, washe garin ranan suka bar kasan sai Jidda, daganan suka wuce makka aka fara Umara, they were so serious, taji dadi sosai dan tahuta da bukatun shi, kusan addu'an umaran shi yawanci was Allah yadawo mata da memory ta, sanan Allah yakade fitina a rayuwan auren su sanan Allah yama aurensu albarka da sauran su. Har suka gama Umara bai nemeta ba, dayayi niyyan dazaran bayan Uamar Nigeria zasu koma sai kawai yaji he need to pay a surprise visit to Uncle, yanunama Uncle the love of his life, komi yamusu kawai suka wuce Russia 🇷🇺. Kasan cewa asabar ne yasan definitely zai sami Uncle dinshi agida, dan ranan hutawanshi ne yasama sukabi jirgin, karfe 4 na yamma jirginsu ya sauka a airport, komi sukayi suka fito yadauki hadadden taxi sukai gidan Uncle bayan ya rungume Widad datai laga laga tagaji dan bata hutawa all this while aikin Umara gakuma tafiya wanan shegen long flight dinan dasuka bi, har kofar gidan uncle dinshi aka kaisu wani hadadden gida wane aljanna duniya, baturen security dake gadin gidan yana ganin Waleed nagane shi da gudu yatashi yatayasu ciro jakunkunan su daga mota dan sunyi siyayya yace "welcome Sir" sanan yay ciki da akwatunan Waleed biyedashi yana rikeda hannun Widad dake tafiya ahankali, falo aka bude Uncle na zaune kan dogon kujeranshi akan hadadden falon shi da za'a kirada aljannan duniya security shi yabude kofa ya shigo rikeda jakunkuna, gyara zaman glass din idanunshi yayi yana kallon mutumin kafin yay magana yana Waleed yadawo kanshi cikin dakin rikeda wata kyakkyawan balarabiyan yarinya dake sanye da doguwan riga, wani irin mikewa tsaye uncle yayi yay pointing Waleed da yatsu, saikuma yacire glasses dinshi da sauri ya goge yasake maidawa, ganin Waleed ne still yana tsaye yana murmUshi yasa ya buga wani ihu kaman yaro. "My son, my son is here, Waleed". 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣7️⃣ & 5️⃣8️⃣ Dawani irin gudu Waleed yasaki Widad ya rungume Uncle dinshi cikeda murna, a rayuwanshi bayan mahaifinshi this is the second man he love the most in this world cus uncle always got his back, sun dade a rungume sanan yasaki Uncle din Uncle nashafa fuskarshi yana farin ciki yace "what a pleasant surprise so dama bayan Umara zakuzo wajena shine ka boyemin ko, am so happy you guys are here" yay maganan yana tafiya wurin Widad dake tsaye tana kallonsu yana kwalama matar shi kira. "Wife, Wife" daidai yakarasa wajen Widad hannu yabude mata murmushi tayi ahankali tace "Uncle oyoyo" "oyoyi daughter" murmushi tayi ta rungume shi saitakeji kaman ta rungume mahaifinta dan she could feel his happiness naganin su ajikinshi sakinshi tayi yarike mata hannu yace "muje ki zauna" daidai wata kyakkyawan baturiya tafito kana ganinta kaga Christian, tana ganin Waleed tabuga ihu. "oh my God, I can't believe this, Baby is it our son am seeing" tai maganan tana kara Zagayowa daga bayan kujera tana kallon Waleed dake murmushi tana kallon mijinta, gyadamata kai Uncle yayi tawani irin rungume Waleed sanan ta rungume Widad dataji tanaso kafin tace "kuzo nakaiku bangaren ku and freshen up then come down for dinner" binta sukayi takaisu wani hadadden side dakenan close to nasu, babu abinda babu aciki na kayan yan gayu sanan tace "feel at home please" tai maganan tana mintsilin kumatun Waleed tana kashemai ido tana kallon Widad datamata kyau, dariya Waleed yayi tawuce tafita daga dakin, itakuma Widad tawuce ta shiga bayi danta mugun gaji kaman taita kurma ihu takeji, maida kofan yayi yarufe yacire kayan jikinshi sanan yawuce yabude kofa ahankali ya shiga bathroom din yana bin bayanta da kallo ya bala'in kewanta, baima taba sani zai iya wanan hakurin dayayi mataba, ko kadan bataji motsinshiba tadaiji anrungumota tabaya tsamtsam yadaura kanshi kan gefen wuyanta, atare dukansu biyun suka sauke ijiyan zuciya, kiss yama wuyanta ahankali yace "I miss you Babyna" murmushi tamai ahankali murya chan kasa tace "me too" daga kanshi yayi yasake kissing kunnuwanta yarrr tsigan jikinta yatashi tasauke wani irin nauyayyan ijiyan zuciya, matseta yayi yashigayi yakai hannunshi ya fizge sponge daga hannunta yashiga wanke ta Ahankali ta baya kafin yawani irin juyoda ita, hada ido sukayi yakai bakinshi kan bakinta yana mikamata sponge din alamun shima tamai wankan, karba tayi takai sponge din kan kirjinshi ajiyan zuciya yasauke yay grabbing lips dinta to his mouth yashiga kissing nata ahankali itama tana biyemishi, deep down she misses him also, she miss his touches and everything, yanda yake kissing dinta yana matseta kadai ya nuna how much he misses her, janye ta daga kasan shower yayi yajingineta da glass din wajen shower yajuyata dasauri yanakai manhood dinshi to her hole yay thrusting in, ihu tayi tafashe da kuka danji tayi kaman baitabayi ba da sauri tace "please karkayi zafi wlh" jikinshi narawa yamake mata kafada yama kasa magana kaman wani angry lion yatura ciki da mugun karfi saida tai ihu da kyau, he fucked her kaman baya tausayinta, dudda bai wanijishi dam ba amman ya kyaleta ganin magrib ya gabato yamusu wanka suka fito tamaki kallonshi sabida fushi dashi datakeyi, wasu fine kaya masu kyau daya siyo musu daga makka yaciro musu ankone itadashi suka saka sanan yajasu salla kafin sufita dinner, anan sukai isha'i, sun dade suna hira har tafara jin bacci, gani haka yasa Uncle yace "rakata taje tai bacci tahuta" rakata yayi dan hiranshi da uncle baya karewa sanan yadawo, itama matar Uncle dake tayasu hiran gajiya tayi ta mike tace "saida safen ku bazan iyaba baku gajiya da hira" tawuce wanta, suka cigaba da hiransu sai wuraren 1 sanan Uncle yasashi yaje ya kwanta yatafi. Bude flat dinsu yayi yashiga ya tarar tai nisa a baccin ta, bayi yashiga yayo wanka yafito baima saka kayaba turare ya feffeshe kanshi dashi sanan yazo ya kwanta kan gadon, tana cikin bacci taji ana ciremata kaya, bude ido tayi rass saikuma tafashe da kuka tace "Ya Waleed please kabarni inyi bacci kaji" kaman zaiyi kuka yace "please Pretty I need you, banda wata matan saike abukace nake please my luv" yana maganan yana kissing boobs dinta, as much as she hate it and she wanna sleep kasa resisting nashi tayi hakan yay night party da ita shikadai yake haukanshi kaman zai sume akanta harta samu yabarta gab da asubahi tai bacci. Haka suka cigaba da rayuwa gidan Uncle, kiri kiri Uncle yahana su tafiya yace rabon Waleed da gidanshi how many years tunda Allah kuma yakawo shi yanzu sai randa yaga dama zai sallameshi, sai kaisu yawo garin yake har Widad tagaji da yawon tana zama gida tareda matar shi datake so sosai tana koyamata girke girken su, ya zamto kullum dashi da Waleed ke fita amman Waleed nadawowa saiya fanshe nafitan shi, kotana wajen Mom baya kunya saiya kirata har Mom ma tagane saisa dazaran biyar na yamma yakusa lokacin dawowan su zata tura Widad din ta tafi shashin su, daga Shi har Widad din sunyi mugun kyau kaman zaka tabasu jini yafito. _*NIGERIA*_ _BAYAN ONE MONTH TEN DAYS_ Tun bayan tafiyan Waleed karamin haukane kawai Ilham batayiba, bata taba sanin tana kishin Waleed hakaba, gashi tunda ta zageshi yama daina kiranta saidai yamata text ya tambayi Arham junior, kokuma yace yatura mata kudi for anything dasuke bukata, kudi yake turamata regularly baya wasa da wanan, yan aikinta sunsha masifanta da zagin ta harsun saba, Arham junior kuwa yanzu harya saba da ihunta da makanshi datake, yaron sai kiba yake yana bulbul dashi, kamaninshi da mahaifinshi nakara fitowa bana wasaba. Yauma kaman kullum tana zaune a garden dan hakanan kwanan nan batason kamshin dakinta tada mata da zuciya yakega shegen zazzabin datakeyi tsakar dare data rasa name tadaifi dangantashi da tunanin Waleed da kishiyarta aranta halan abubuwan daya taru yamata yawane yasa take zazzabin daren, yanzu babu inda takeso agidan kaman garden dinta, kamshin fresh grases da flowers din wajen na mugun kwantar mata da hankali, tana zaune wayarta yadauki ruri ta kalli wayar ganin number wajene yasa tadauka dagudu. "Hello Maci amana, wlhy Allah ya isa ban yafe ba, yau kagaji dayan text messages dinka ne and decide to call me, kaci amana na, ka cuceni Waleed wlh kuwa" kuka ne yaci karfinta maganar ma ya daina fita dakyau kaman daman jira take yakira, shiriu yayi yana sausaranta, saidata tsagaita kukanta sanan taci gaba tace "ka barni da yaronka tsawon wata daya da rabi, almost two month now kaje honeymoon da wacce kakeso nika barni anan, koh ta kanmu baka karabi ba, Waleed what have I done to deserve this inhumane treatment from you ehmm, is it a crime to love you? Dan kaga ina mutuwar sonka Waleed"? kuka takara fashewa dashi harda pyace majina dukyana ji, he hates yanda take zaginshi dan baison raini abinda kuma yake hanashi kiranta kenan daya kirata tamai rashin tarbiya gwara yahakura yamata text instead amman dudda haka tabashi tausayi sosai, ahankali yace " I'm so sorry kinji Khadija, yanzun haka ina Russia wajen Uncle dina, akwai abubuwan danake yimai ne, wani dan mini project muke working akanshi nidashi, but am sure nan da two weeks or so zamu gama saina fara shirya dawowa, but very soon I promise you zan dawo am sorry kinji" yay maganan sounding so soft and tender, murmushi tamai ta turo baki jin cool voice na Waleed dinta daya wani irin sanyaya mata zuciya, idan mijinka ya lallasheka it feels good, ahankali tace "toh amma kasan dai ba Amaryanka kadai bace matar ka ba koh, tunda abun haka ne nima zan shiryo kayana dana danmu mutaho Russia din kawai saboda nima inzo inkarbi hakkina, I miss you" dan shiru yayi kafin yadan nisa yace "I said I will be coming back soonest, saboda haka there is no need kizo okay, just stay over there take care of my son and yourself" yana gama maganan in other not to allow her to keep ranting yayi sauri yatambayeta "how is my little boy?" " He is fine, gashi yayi kiba da kyar nake daukarshi, koh madara bayason sha idan ba nono ba, zai iya yini da nono abaki baya gajiya hakama kwana, gashi kuma both of us bama jin dadi duk zazzabi mukeyi dagani harshi although shi yama warke ninedai naki warkewa" ahankali yace "It's okay, Allah ya kara muku lafiya zan kira Dr Ayo yazo ya dubaku agida gobe, kokuma yau, take care of yourself da son dina, I will see you soon, Allah ya kara sauki" sallama sukayi ya kashe wayanshi. Tashi tayi ahankali tana yatsine fuska jin wani irin ciwon kai tawuce ta shiga ciki tai bedroom dinta tafada kan gado ta kwanta gefen Arham Little daketa tikan bari abinshi, da sauri taja blanket ta rufe kanta tanaso itama tasamu tayi bari gashi tahaujin sanyi kuma tunda itama bata cika barcin dare ba sabida shegen zazzabin dake nukurkusanta. 45mints barci tasamu tayi duka duka phone dinta yahau kara, farkawa tayi kanta na mugun sarawa tamika hannu ta dauka takara akunne, chan kuma tace "kice please ya bani 10mint ganinan fitowa, make him comfortable pls abokin aiki Dr ne" tana gama maganar ta ajiye wayarta tashiga toilet da gudu jin fitsari kaman zai fasa mata mara, yitayi tafito. Gyale tayafa hade da daukar Arham daketa faman barci abinshi tafice daga dakin dan Dr Ayo yadubasu duka. Fitowa tayi suka gaisa da Dr Ayo, sannan ta faffada mishi abunda yake damunta da Arham little. Bayan ya gama jin complain dinta ya fada mata cewa zai dauki jininta yaje yayi test a hospital agan exactly what is wrong it might be maleria kokuma wata cutar zuwa anjima da yamma ko gobe zai kawo mata result din da magunguna it depend on lokacin da test din yafito. Godiya ta mishi yaduba Arham little sanan yadauki briefcase dinshi ya fita. Karfe 7:05pm na yamma yar aikinta takirata tace Dr Ayo na nemarta a palour. Koh minti biyar batayi batayi ba tafito rike da Arham dake kuka, tabama mai rainon shi shi sukabar musu falon sukai sama dakin little. Gaisawa sukayi again kafin yamika mata envelope da Kuma magungunan daya kawo musu yace "nayi prescribing yanda zakisha maganin dana small baby, sannan that envelop result na test na kine, anyway congratulations, am happy for you and Dr Warbai saida safe" yatashi yafita daga dakin yana murmushi itakuma tabi bayanshi da kallo hannunta rikeda envelope na test din, haka kawai taji kirjinta nabugawa ama ta daure. Hannunta takai tacire gyalen data yafo ta ajiye kan kujeran sanan tadauki Envelope din tayage saman tasaka hannunta tazaro farin paper ciki tafara budewa still kirjinta na bugawa kaman zai bare ta warware takardan tafara karanta abinda keciki. "Innalillahi wa innailaihi raji'un, Hashunallahu waniimal wakeel, lahaula walakuwata ilabillahi aliyul Azeem, na shiga uku na lalace, jama'a nabani, wayyo Allah na nashiga uku" abinda da ta dunga maimaita kenan bayan ta bude test result din takaranta abinda keciki daya fito _*Pregnant positive, pt positive*_ "nashiga uku na lallace, 6weeks fah" salati ta kara rangadawa idan tasan tanada ciki Allah ya konata, hawaye masu zafi suna biyo kuncinta, hankalinta yatashi ainun, jawo phone dinta tayi tafara nemar number din Arham still tana hawaye tama taushe bakinta da hannu dan batason tafashe da kuka sosai yan aikinta sujita. Takirashi yakai sau bakwai bai dauka ba ana takwas yadauka murya chan kasa dakenan adishsshe yace "Hel....lo" cikin muryan kuka sosai dake breaking tace "wlh wlh Arham I regret knowing you in my life, nayi dana saninka arayuwana, I hate you and hate anything that has to do with you, sabida u are nothing but a manipulative bastard, devil, you lured me into sleeping with you duka kudadena da ko Gina masallaci nayi dashi danasam nai abin alkahiri dashi na tattara nabaka shine yanzu zaka karamin ciki Arham is just 3month old inada cikin kusan wata biyu, dagayin arba'in kamin wani cikin? So kake Arham nada wata goma kacal zai haiho wani, wlh wlh nagama haifa maka yara, wlh wlh bazan zauna da cikin nan daka duramin ba saina zubar dashi, kuma Allah ya isa tsakanina dakai, wlh saina zubar dashi" wani irin mahaukacin tsawa Arham yadaka mata yace "ko kalman zubarmin daciki kika kara furtawa wlh saikinga my other side, yaro da ubanshi gani raye da lafiyata ne zaki kwashemin d'a, wlh baki isaba wait and see" yay maganan tareda katse wayan, tsugunnawa tayi a kasan falon tadaura hannu aka ta rushe da kuka, wlh badadan dare yayiba anriga anyi magrib da koma ina zata shiga yau da saita shiga tagano inda za'a zubar mata da cikin nan. Kuka tashiga yi sosai ta mike tsaye ta tashi tai sama da kyar tafada dakinta tana wani irin kuka, zata iyacewa tunda take arayuwanta bata taba shiga tashin hankali irin na yauba. Maganganun da Ilham tafadi mai yasa yature Hassana dake kan jikinshi tana sama da kasa akanshi ya hankadeta yatashi tsaye yamugun rame yay duhu tun bayan rasuwan Mama sex dayaran nanne kawai guda takwas keragemai yawan tunani da damuwa, kaya yadauka yashiga sawa ranshi abace yakalli Hassana dake kallonshi yace "kitashi kibar nan zan fita" tashi tayi da sauri ta maida kayanta tasaka tasaka hijabi tafita shima yafita yarufo office din yawuce ya shiga mota yaja motar da mugun gudu zuwa gidan Waleed, yana horn mai gadi yabude mai kofa kasancewan yasanshi ya shiga yay parking yafito yay cikin gidan yana shiga falo yaga yar aikin da ai rainon sun dauki Arham dayay bacci suna kallo, fuska a daure yace "suwaye ku? Me kukayi da yaron nan"? Yay maganan yana mika hannu ya karbi Arham din daga hannunsu, yarinyar tace "nine mai rainon shi itakuma itace yar aikin" tabe baki yayi yazaro kudi daga aljihun shi yan dubu dubu ya jefe musu guda biyu yace "Kubar gidan inji Mai gida, yana hanyan shigowa harsaita nemeku kutashi" dayake kowacce na sanye da hijabinta yasa duk suka fita sadaf sadaf, rufe kofar falon yayi da key yana kallon Arham dake bacci sosai a hannunshi yana kara kallon yanda yaron yay kama dashi, murmushi yayi ya rungume shi ajikinshi yay stairs, Dakin Ilham kai tsaye yabude ya shiga da sauri Ilham data kife kanta akan gado tadago kanta da idanunta dasukai jajir ta kalleshi, mikewa tsaye tayi cikin mugun fushi tace "uban me kakemin agidana"? Baice mata komiba yay wajen gadon Arham dake dakin ya kwantar da yaron sanan yajuyo ya kalleta wani irin kallon wulakanci, cikin fushi tace "ubanme kakemin agidana, kawuce kafita kona maka ihu yanzu" wani irin murmushi yasaki tareda tabe baki yace "how humans forget easily, yanzu har kin manta lokacin dakike kirana to sex you, Khadija the lonely woman Arham dick lover" wani irin runtse idanu tayi yana soso mata abinda ta tsani ta tuna yayi tace "if I tell you am not regretting those acts am lying, nai nadaman every time I remember abinda na tsaya nayi da richard bastard irinka" wani irin smirking yayi jin zagin da tamai ya lashe baki yace "anyway I come to tell you one thing Khadija, wlh inhar kikai gigin kashemin d'a saina tona miki asiri sanan saina kwace d'ana, I have a clip of you dakike fadamin kinaso naciki, so be careful dani cus I can make your world black wlh, be very very careful, kina ciremin ciki wlh saina fallasaki aduniya da internate asan me yaryan Alhaji Hassan takeyi agidan aurenta, as for me I got nothing to loose Mahaifiyata na kwance akabari, karki gigin ciremin d'a ki haifamin kayana inaso, inkuma kince kin shirya bala'i dani dahar kimutu bamu gamaba harkan jikokin mu toki gwada cire cikin jikinki kigani" wani irin kallonshi take yana maganan hawaye suka shiga zubomata, ayanda yanzu tasoma ganin true colors dinshi tasan Arham can do morethan this self, zubewa kasa tayi ahankali takama kafarshi tarike tana wani irin kuka mai tsuma rai tace "Arham ninefa, all I did was to love you Arham, na tausayamaka akan yanda kace Waleed na treating naka, nabaka kaina batare danai tunanin a day like this is coming ba da zaka juyamin bayaba, kamin ciki na haifa maka beautiful Babyboy, Arham koba komi naci darajan yaron dana haifa maka yaushe nafita arba'in dahar zanyi wani cikin? Yaushe system dina ya warke dahar zan kara daukan wani nauyin cikin? So kake Arham little yasha ciki? So kake Arham little na 10month harna mai wani kani? Haba Arham please katausayamin kaji karka tonamin asiri, wlh tunda na haihu Waleed bai kwanta daniba tayaya zan likamai wanan cikin? Wanan karan zai ganomu "? Tabe baki yayi yace "at this point ban tsoron uban kowa, koma yagano banashi bane ai yanada dai uba ko? So wanan chan ta matse muku, yanda kika likamai wanchan wanan ma ki likamai, karki sake ki zubar min da ciki, ba nonon da Little zaisha yana kara girma zai faracin abinci, so spare me this trash u are saying you little woman, tasonan lemme even sleep with you" wani irin kuka take tana kallonshi amman ko ajikinshi, dagota yayi ya shiga kissing neck dinta, yabita bayanta yaja zip din riganta kasa ya kwance mata zani, tareda tuge pant din yasa tai ruku'u jan wandonshi yayi kasa yakamo abinda harta mike yatura ciki, lumshe ido tayi yana kuka, ko ajikinshi zane ass dinta yayi yana fucking nata like his goat yana gamawa yajata kan gadon ya matse sukai bacci cikin bacci taji yana neman ta barinshi tayi bata hanaba deep down she is enjoying it haka yamata yanda yaga dama, saida gari Arham yatashi daukanshi tayi tana bashi nono shikuma Arham yazauna yana kallonsu, juyowa ahankali tayi ta kalleshi hada ido sukayi sukai shiru, ahankali tace "mesa karame kai duhu?" dauke kai yayi yace "is non of your business, sa yaron nan bacci kizo nan" ahankali tace "kai sex, sex,, sex kawai" "yes it takes my pain away, and is obvious you enjoyed it stupid woman mayyar bura, wlh bakida class, kince kin tsaneni but kin kasa tsanan burana, nikuma I promise you haka zanta dirkamiki ciki kina likama mijinki sai kin haifomin 12kids jaka!" ya dankara mata zagi yana mata wani disgusting look dan ya tsaneta shima hakanan ganin tagama fadimai ta tsaneshi waye waye, da uban zagunan but gashinan he just sleep with her harta manta tana tambayanshi mesa yarame, tsaki yaja yatashi yace "loose woman" bin gabanshi tayida kallo gaidata batakai ta Waleed ba but dadin Arham dakeji sosai dan he fucks her special. Ijiye Arham dayay bacci tayi ta tashi tafada jikinshi tana fizgan nipple dinshi da teeth tace "nine loose woman, kai wat are you aboki mai cin matan aboki ko bad boy" nipple dinta yaja ruwan nono yafesomai afuska da sauri yasaki daga ita harshi suka fashe da dariya saikuma ya fizgota kaman mahaukata ya shiga fucking nata crazy both of them having the best time of their life, sun manta da komi saijin dadinsu ba wanda yay sallan asuba cikinsu, Ilham tama manta da battun zudda ciki. Saida suka gama sanan sukai bayi wanka suka shiga yi yana kallonta yana wanke jikinshi yay tsaki ganin gabanshi yaji kwanciya yace "wlh you don't satisfy me Ilham sabida kin bude, gabanki ba dadi, ina cinki har tusan gabafa kike shit, mtswww" yaja tsaki tacigaba da wanka, yace "mtswww ni wlh sabida ma sperm abincin dan ciki ne kuma nasan mijinki ba cinki yakeba da babu abinda zaisa naciki bayan inada fresh 8 pussies, wlh so tight and yummy, nina baresu sanan nikadai nake amfani da kayana aduk duniyan nan, Ke kinjisu kuwa" yay maganan yana kallon fuskarta ganin yanda idanunta sukai jajir yasa yace "gaskiya fa nafadi, I need to go na saduda Farida wlh °gabana zakiga ya kwanta dan tsukeni gabansu yake keko jina ke kaman ana juya tsinke arijiya" yay maganan yanajan towel ya nada a waist yawuceta yafita yasaka kaya yadau key mota yabar zuwa gidan marayUnshi direct, Fadila yakira yashiga kwakusanta as usual. 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 5️⃣9️⃣ Saida yagama tsaf sanan yakorata yay wanka ya shirya yafito yazauna office yay shiru yana tunani, thanks to 17m din da Ilham ta turamishi kwanakin baya suyaketa kashe wa agidan marayun nan, tunda yabude aka kawo yaran gidan jira yake gwamnati sufara kawomai tallafi sunki kawowa, staff din Waleed dasuka biyoshi daya bayan daya sai guduwa suke dan baya biyan su yanzu, ba makaranta yaran ba islamiyya kowa are just on their own, da kyar ya iya maintaining matar dake girkin gidan marayun but itama yasa tarage hannu sosai dan kudi sunsoma jamai kasa, yakira government officials harya gaji saidai su cemai ba'a riga an saki kudin ba but za'a saki soon sabida new gidan marayu ne it will take time kafin su shiga list, kullum sa ido yake but shiru haryau, dudda ya Gina gidan marayun shi, ya karbe ma Waleed yaran gidan marayun shi, ya karbe matarshi ta haifa mishi yao na farko yanzu tadauki na biyu he is still not satisfy, at this point of life baimasan meyake soba, komi yayi baya isanshi, shi yaki aure sanan he keep sleeping with this children kaman zaiga karshen mahaifansu but he is still not satisfy, hakanan yakeji akwai wani craving a zuciyan shi that is yet to be fulfilled, he wants to bring Waleed down completely, yanaso yaga Waleed yarasa komi yana kuka da idanunshi, yanason yarana shi da wanan matar daya aura yay kokari but gwamnati sunki bashi wani attention dayake so dazaisa a bashi goyon bayan dauko Widad, he wants to end Waleed, tsaki yayi yadauki ruwa yasha, haka yawuni babu wani tangible thing dayayi daga yakira wanan saiya kira wanan da magrib yabar gidan sai gidan Waleed. Sama yawuce direct yabude kofar dakin Waleed shi adole Mia gida yashiga ciki yana kwalama Ilham kira. "Ilham, Ilham" tana zaune kan gado Arham yay bacci taji ana kiranta fitowa tayi jin muryan Arham adakin Waleed bude dakin tayi ta shiga tana kallonshi cikeda mamaki irin me kakeyi anan. "zonan naduba cikina kokin zubar" batamai gardama ba tamaida kofar tarufe tazohar gabanshi ta tsaya tace "Arham banson yanda kake zuwa gidan nan kaman kana zuwa gidanka, wat if yan uwana sunzo sun ganka naceme, Waleed bansan ranan dazaizo ba yazo yaganka mezan cemai eh please kadena" tsaki yaja yana daga riganta yace "in kikaga nadena zuwa to kin haifamin d'ana, come here lemme give him food" yajata, kasa hanashi tayi dudda cin mutuncin daya mata dazu dasafe hakatabiye mishi dan wani shegen jaraba cikin kesata ta kosar dakanta. Wani irin shiri Uncle yake musu na dawowa dan gobe zasu koma Nigeria, yau kaman kullum an fito dinner sai kallon Widad yake dayaji yana bala'in sonta kodan sabida yanda ya lura Waleed na sonta ne oho but yana bala'in son yarinyar sosai yakejinta kaman yarda yahaifa, gashi tai wani irin mahaukacin kyau dashi kanshi Waleed har mamakin yanda take kara kyau yake kaman wata yar aljanu. Tashi yayi ahankali daga inda yakezaune yadawo ta bangaren ta inda take kusada Waleed, murmushi tayi tace "Uncle" kanta ya shafa sanan ahankali yaciro wani akwati daga aljihun shi da kanshi yabude mata taga key ne namota, da sauri ta ware ido tana kallonshi tama kasa magana, hannunta yakama yasaka mata key aciki yace "accept my little gift, car dinki ne you can go to the compound and see it, zan miki shipping nashi to Nigeria" kafinma tai ihu Waleed yarigata yi. "woooo our first car" hararan shi Uncle yayi yace "mind you gentleman her car not yours, nakine kinji" wani irin gyadama Uncle kai tayi cikeda murna saikuma ta rungumeshi sanan tasake shi ta rungume Mum tace "Mum Uncle yasaimin mota" cikeda murna Mom tace "congratulations beautiful" kallon Waleed tayi daya tsaya yana murmushi yana kallonta, murguda mai baki tayi tace "stop looking at me bazan baka kadana ba" tai maganan tareda wuceshi tai hanyar fita daga falon sabida taga motar, yabita da sauri ya fizge key yafita dagudu, kyalkyacewa daga Uncle har Mum sukai da dariya Uncle yace "Waleed da shegen neman tsokana" koda tafita taga motar hadaddiyar gaske bamata San sunan motarba, kofa Waleed yabude mata yana murmushi yamata alamu dakai data shiga, shiga tayi ahankali yamaida kofan yarufe sanan yazagaya ya shiga dayan bangaren yazauna yana kallonta sai murmushi take tana tattaba motar, hannunshi yamika ahankali ya rike hannunta hakan yasa ta kalleshi, wani cool love smile yasakin mata yace "congratulations Wife" fadawa jikinshi tayi da sauri ta kankameshi tana sauke ijiyan zuciya tace "I love you Cutest, don't ever live me kaji" murya chan kasa yana shafa bayanta yace "why do you say that"? Murmushi tamai tace "sabida anytime am with you good things happen to me, just look at my car" murmushi yamata yace "will you allow me to sex you to my content angel am hungry for you, this days kina sani yunwa just oneround ki koreni, will you" shiru tayi saikuma ta gyadamai kai tana murmushi takai hannunta kan wandonshi ta matse gabanshi da karfi har sauda yay kara tareda dago kanta ta kallai, murya chan kasa yace "sokike nai fitsari awando" gyadamai kai tayi tanajan zip din wandon ta tura hannunta cikin boxer dinshi tana chapko sleeping master dinshi, wani irin mannewa yayi da kujera yana runtse ido yace "Ya ilahi this girl wants to kill me, please don't turn me on baby, wlh I can pes on my trousers fitsari nakeji, am so press, Hoo Lord" kaman ma bada ita yakeba kamo kan crowns dinshi tayi still tana kallo idanunshi sanan tai grabbing lips dinshi gently kaman wacce ke aiki a striper club tai squeezing head dinshi daidai wajen hole din tana lailayawa, wani irin mikewa yayi dan sosai yaji fitsari zai fitomishi amman tahanashi tashi tacigaba da wani irin shafawa tana sidemai baki ahankali tana goga boobs dinta kan kirjinshi sanan takai dayan hannunta ta matse nipple dinshi, ihu sosai yasaki kaman yaro abakinta saiga fitsari ya wanke mata hannu dashi, wani irin fashewa da dariya tayi da bata tabayin irinshi yagani ba yarda tafi taciro hannunta tana kallo dayay fitsari akai tace a sabon motana kai fitsari shima kallon kanshi yake yarasa mesa Saheeba tasan Mumu button dinshi, tunda ta lura inta rikemai gaba haukane kawai bayayi yasa takemai yanda taga dama ganin ya yunkuro yasa tabude kofa tafita da gudu tai bangarensu shima yafito zai bita saikuma ya kalli fitsarin Allah yasa akwai ledoji akujerun amman dudda haka saida yasa dan aiki ya wanke cikin motan sanan yabita cikin bangaren su aikam saida yasa tasan cewa shitasa yay fitsari dan shima saida yasata tai squirting all over bed. Washegari har Airport Uncle da matarshi suka kaisu da kansu, private jet section sukaje danshi Uncle yamusu booking sukabi saida tai kuka dazata rabu da uncle da matarshi hakanan suka shiga jirgi aka tafi. Ammi kadai tasan da dawowan shi, kuma tasanar dashi suzo gidanta direct su sauka, karfe 7:30 na bayan magrib jirginsu yasauka a Nigeria, already direban Ammi na jiransu, suna gama komi suka shiga mota sai gida, wani irin murna Waleed yake kaman bai taba ganin Ammi shiba yay kewanta suna kaiwa gida kaman wani dan yaro tundaga tsakar gida yafara kwalama Ammi kira, da sauri Ammi tabude kofa tafito tana cikin shiga ta alfarma, Waleed na hangota yataho da gudu ya rungumeta harda dagata sama ihu Ammi tayi ta bugi kafadar shi, sauketa yayi yana dariya daidai Saheeba ta iso Ammi ta rungumeta tana murmushi sosai taji dadin yanda tagansu kyan dasukayi har abin nabata mamaki, Waleed dinta ya karayin jajur abunshi yay kiba kaman bashiba itama Widad haka, daki suka shiga dukansu Ammi tace kuje kuyi wanka ku sauko wanka duk sukayo bayan yakarbi hakkin shi abayi ko tausayi gajiyan dake tattare da ita bayaji saida yagama sanan sukai wanka suka fito daga bayi sukai salla suka sauka kasa, abinci sukaci Waleed sai surutu yakema Ammi yana bata labari itakuma Ammi takasa daina kallonsu, saida suka gamaci sanan sukatashi suka koma falo bayan tasa yan aiki su kwace Widad ta shiga tayasu, zama kusada Ammi yayi ahankali yace "Ammi please I need a favour, inaso Saheeba tazauna dake for one week naje nama Khadija one week dan bazata iya kwana ita kadai agidan taba kinji Ammi" gyadamai kai Ammi tayi tace "Alright ba matsala" tashi yayi ahankali yace "bari naje na shirya" yay maganan yana tafiya sama itakuma Widad yabarta akasa, shiryawa yayi cikin wata bugaggiyar shadda sanan yabude akwatinshi yahada kayan daya sayoma Ilham din tsaraba da Arham awani separate akwati sanan yajanyo akwatin yafito, Widad dake zaune kusada Ammi suna hira kamshin turaren shi kadai taji tadago kanta ta kallai hada ido yayi da ita saida gabanshi yafadi baisan mexaice mataba banda haka tun bayan aurensu today is the firstday dazai kwana batare da itaba, karasa saukowa yayi ganin yanda suke kallon juna yasa Ammi ta tashi tai stairs tace "inkin gama kizo dakina daughter bari nadan zaga" gyadama Ammi kai tayi tana kallon Waleed, ahankali ya ijiye akwatin a tsakar dakin sanan yazo kusada ita yazauna yana kallonta yarasa mezaicemata, murya chan kasa tace "where are you going"? Shiru yayi yakasa magana kuma baison yamata karya, yadade kafin yadan nisa yace "zandan fitane okay, go and stay with Ammi" yay maganan yana dagata sama, tashi tayi ahankali tashi shima yayi yay kissing lips dinta sanan yace "go" ahankali tai stairs ta tafi wajen Ammi, ganin ta tafi yasa yaja jakar yawuce yafita, motar Ammi yadauka yaja motar yabar gidan, awani babban super market ya tsaya yamasu sayyaya koba komi yakosa yaga yaronshi yasan yanzu yay girma sanan ya shiga mota har zuwa gidanshi, akofar gida yaga mai gadinshi na hira damasu gadin anguwan su da gudu yatashi saida yafara gaidashi sanan yashiga ciki yabude mishi gate Waleed yashigo yana kallon motar tsakar gidan dayagani a pake daya rasa motar waye, amman motar yamai kama da motar dayasani but yamanta daga ina, tabe baki yayi yace hala na yan uwanta ne sanan yafito daga motar bayan ya kashe direba yazo yace "yallabai meza'a shiga dashi ciki" girgixa maikai yayi yana murmushi yaciro kudi masu yawa yamikamai yace "barshi jeka cigaba da hiranku suna jiranka" sanan yaja akwatin inyaso yafito daga baya yashigo da shoppings din, ahankali yabude kofar falo ya shiga babu kowa afalo sai TV falo dake aiki dake kan tashar kwallo ga uban kara kaman gidan kurame, tsaki yaja ya shiga neman remote yarage karan baiganiba hakan yasa yay stairs yanajan akwatin ahankali, pant dayagani akan stairs din yasa ya tsaya chak yana kallon pant din irritatingly iron lafiyan Ilham zata saki pant dinta anan, tsugunnawa yayi yadauka sanan yacigaba da hawa stairs din yaka karasa hawa yaga bra dinta awurin da boxer din namiji, faduwa gabanshi yayi ganin boxer din dayasan banashi bane danshi baisa local boxer designers yake sakawa, bin falon saman yayi da kallo daidai gaban dakinshi yaga kayan namiji awurin akasa hakan yasa wanan karan gabanshi yay mummunan faduwa, sakin akwatin yayi akasa yabi stairs yakoma falo sanan yadaga kafarshi dakyar harya karasa gaban dakin nashi ya tsugunna yadauki kayan namijin yabude kayane masu kyau mai ruwan kasa sunsha aiki sakin kayan yayi akasa kirjinshi namai wani irin rawa yakai kunnenshi jikin kofan yanajin sound da groan. "oh God, Arham dan girman Allah karka dena, wlh ka iya cina samada Waleed, I swear kaji na rantse inhar kana cina haka wlh bazan zubar maka da wanan cikinba shima zan likama Waleed yana dawowa I will make sure I get him to sleep with me mu mannamai wanan kaman yanda muka mannamai Arham Little, a hhhhhh zan.......kawo" ta kwala wani ihu, jikin Waleed harwani rawa yake yadaga kafarshi amUgun zuciye yadaki kofar saida kofar ta balle straight up. [11/27, 9:54 PM] saleemah: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣0️⃣ Yanda yabuga kofar saida kofar ta balle tafadi akasa kusada gadon Allah ya sosu bata fado kansu ba, amugun firgice daga Arham har Ilham suka saki juna suka juyo suka kalli wurin kofa, wani irin runtse ido Waleed yayi ganin matarshi Khadija Ilham da babban abokin shi Arham tsirara haihuwan uwayensu kan gadonshi, adakinshi, acikin gidan dayagina da kudinshi, wani irin fitsari Ilham tasaki hannayenta duka narawa tasauka dagakan gadon tace "Waleed yaushe kadawo? Innalillahi yauna shiga uku, is not wat u think wlh wayyo Allah na, Waleed wlh I can explain" tabe baki Arham yayi yatashi dagakan gadon yana kama erection dinshi dudda kirjinshi nabugawa amman yadaure ya yatsine fuska yace "wat? Akaina aka fara kake wani kallona haka? You got married to a loose woman don't you know, tun muna Yankari nafara cinta kuma ita tanemeni" da sauri Ilham ta bugi bakinshi tace "Arham!" fizge bakinshi yayi yace "ke mehaka let him know, bari nagaya mishi who you are" yasake kallon Waleed yace "she texted me, she wanna see me naje hotel room dinku tacemin you dont sex her frequently, you are not sweet, not Man enough to make her come, I fucked the pussy u fucked and your wife, scream, cry and beg me not to stop, she cum excessively in ina gstsar ta, kafin tadauki cikinka tadauki nawa, yanzu ma harna mata nabiyu cikinta na neman two month+, remember abinda nafadi maka duk inda kataka saina taka, duk abinda kaci sainaci Waleed, duk matakin daka tsaya saina tsaya, now what can you do? Kaji dakanka, nakuma fadi dakaina yes, yes I've been sleeping with your wife tun tana Amarya, kana tafiya gidan marayu zan fito nazo nacita nima, takuma haifamin beautiful son what can you do you looser"? Yay maganan yana wani irin murmushin keta Ilham kuma tazube awajen tana kuka na bala'i. Juyawa Arham yayi yaballa mata harara ganin yanda take kuka tadaura hannayenta aka yawuce wanshi wajen kofa inda Waleed yake tsaye walking majestically daidai zaibi ta gefen Waleed yawuce Waleed yawani irin fizgoshi azuciye ya buga kanshi da bango da saida Ilham tai ihu danta zaci kanshi yafashe taga bai fasheba amman ya sume, shakeshi Waleed yayi amugun haukace Waleed ya jashi wani irin dagashi yayi yajefashi abene kaman ya jefa kara Arham ya shiga gangarawa yana tumble har kasa, cikeda wani irin zuciya idanun Waleed sun juya yana wani ihu yace "how dare you sleep with my wife, how dare you! Yauzan kashe ka nahuta Arham, I will kill you" yana karasa sauka yay wani ball da Arham da saida bayanshi ya bugu da kofar falon goshinshi na jini kanshi ya kumbura suntum, kofar falonshi Waleed yabude yaja hannun Arham din baya iya motsi kaman yakarye Waleed na ihu yace "yau saina kashe ka, I will kill you Arham" ihun da Waleed keyi yanajan Arham kiii akasa jini nabin interlock yasa gateman dake kofar gida tareda abokanenshi yadan bude gate kadan ya leko ganin abinda ke faruwa yasa yawani irin zabura tareda buga salati yashigo gidan dagudu abokanshi biyeda shi yayi kan Waleed dahar lokacin jan Arham dat was liveless yake yana kaishi towards wani karfe dake compound din da aka bishi da flower decoration Mai Gadi yace "yallabai meya faru tsakanin ka da aminin ka ai kullum saiyazo nadaika kaike aikoshi saisa bansa ido alamarin ku dan kashaidi nafarko dakamin kenan bayan kabani aiki bakasan sa'ido da gulma aikina nabudema duk wanda yazo gate daganan shikenan kuma kowayasanka da Mr Arham yana ganshi"? Cikin wani irin murya kaman namahaukata yace "kwarto ne, Kwarto ne, da matata yake kwanciya yausaina kwasheshi" "innalillahi wa innailaihi raji'un" dukansu masu gadinan suka dauka daidai Waleed nakase igiyan da aka daure awajen na shanya da hannu bai damu da ciwon ma dayajiba hannunshi na jini ya fizgo igiyan ya daga Arham dabaya iya budema ido bayaji da kyau sabida yanda kunnuwan shi suka bubbugu da bango ya mannashi da karfen yashiga daure shi da igiya duk su mai gadi na kallonshi dan zamasu tayashi cin ubanshi ne, gama daureshi tsirara rass Waleed yayi kaman wanda yasami tabuwan hankali yay generator house dinsu ya kinkimo 25litres gallon dinsu dake cikeda fuel yataho wajen, kafinma yakaraso Mai Gadi yatareshi da sauran abokanan shi yace "yallabai dan darajan Allah a'a ba wanan ba, kagamu zamamu tayaka likimar jakin kwarton, mumishi dan bura'uban duka mu kakkarya shege, amman banda kisa, bazamu taba barinka ka kona mutumin nan daranshi ba wanan irin hukuncin ubangiji kadai keda ikon yinshi badan adam ba yallabai ba'a hukunci da wuta" wani irin kallo Waleed yamai shida abokinshi da saida maigadi yaji cikinshi ya hantsire saiga wata tusa tazomai yace "koku bacemin daga gaba ko wlh nahada daku nakona, wanan yaron, wanan butulun, wanan wanan I don't even know the gaddamn name I will call him with yau sainaga karshen shi I want to set fire on him and watch him scream, beg me and finally burn down to ashes, I want to kill Arham nahuta, I made you this lemme kill him also" yay maganan yawani watsar dasu yay kan Arham, abokin mai gadi ne yace "wlh yallabai dinka baya hayyacinshi, na rantse da Allah baisan ma meyakeyi ba muka bari yay kisan kai harda mu hukuma zata dauka, bama hakaba yajuye ma yaron nan wanan man fetir din hatta shi, da gidan gabaki daya damu duka konewa zamuyi" kaman jira suke yay maganan dukansu su biyar sukai kan Waleed suka kamashi da kyar suka danne amman ina yafi karfin su, ganin haka yasa mai gadi yabarsu dashi yay dakinshi da gudu wayarshi yadauko yafita kofar gida kasancewan yanada number Ammi ya danna mata kira, ringing biyu Ammi tadauka, cikin wata irin muryan tashin hankali yace "Hajiya Ilu ne mai gadin gidan danki, Hajiya kiwa Allah kome kike kibarshi kizo gidan danki yanzun, danki baya hayyacinshi yana kokarin aikata abinda zaiyi nadama, Hajiya kizo kawai" bai tsaya amsa tambayan Ammi ba ya katse wayan yadawo ciki yay kansu inda har lokacin kokawa suke da Waleed suna dambe sosai suna cewa yallabai bazaka kasheahi ba shima ya shiga cikinsu ya danneshi. Ko kyakkyawan minti 15 Ammi bata daukaba direban ta yakawo ta gidan, agaban gidan yay parkin tafito da sauri direban ta biyeda ita daidai lokacin Waleed ya watsar dasu a haukace yatashi yama jarkan feul din dagawa daya yashiga tuttulama Arham, sanyi da Arham yaji yasa ya farka daga suman dayayi yabude idanunshi, dawani irin gudu daga Ammi har direban ta tayi daidai Waleed yajefar da jarkan akasa bayan yagama juyemishi tasha gabanshi tareda wani irin dakamai mummunan tsawa. "Waleed!" dago rinannun idanunshi yayi ya kalli Ammi saikuma yadauke kai ya shiga kalle kalle akasa yaga ashanan daya dauko yafadi akasa garin kokawan dayayi da masu gadi, kafin ya dauka Ammi ta dauka taredajan hannunshi ta dagashi sanan takaimai wasu lafiyayyan mari akunci, dafa wajen yayi yana kallonta Arham daya farka yafashe dawani irin mahaukacin dariya yana tofar da jinin bakinshi yace "ohhhhh poor you Waleed, ashe tsohuwan nan na iya dukanka" ya kyalkyace da dariya sanan ya kalli Ammi dahar lokacin Waleed take kallo yace "tell her mana Waleed or should I" yakara kyalkyacewa da dariyan iskanci yace "kinsan mesa danki yahaukace haka yakeson yakasheni tsohuwa?" yatambayi Ammi cikeda daga murya yace "because I slept with his wife!" wani irin juyo dakai Ammi tayi ta kalleshi yasake fashewa da dariya yace "yes I slept with his wife akan gadonshi na dakinshi a kuma cikin gidanshi bama gadon matarshi ba" yasake kyalkyacewa dawani mahaukacin dariyan dazai iyasa mutum yahadiye zuciya ya mutu yace "tun muna yankari tun Ilham tana Amarya nafara cinta inasa tana ihu, jikinta na rawa tanajin dadi wanda itada kanta tai confessing nafi danki dadi dan kayan dadin da danki keci sun kashemai karfin gaba da mazakuta muko rainon tuwo da miyan kuka ba rainon cheese ba inasa takawo sama da sau shidda, and do you even know the most interesting part Ammm.....mi"? yakira sunan Ammi stylishly damugun isgilanci yace "his first son was never his, wlh ba manniyin shi bane yay yaron nanba nawane, d'ana ne, nine ubanshi bashi ba, nakara baki another most exciting news da trust me kin dade bakiji irinshi ba wanda shike kara haukata danki abun pain the nigga" yay maganan yana wani mahaukacin dariya yana kallon Waleed dahar lokacin shafa inda Ammi ta mareshi yake yana kallon Ammi yace "Ilham na dauke da cikina ajikinta dakeda 2months and some days" ya kwashe dawani irin mahaukacin dariya da inda Ammi zatabi yanda shaidan ke tunzurata zatabar Waleed yakasheshi dinne wlh, Arham yace "ohhhh poor Waleed, badole ka hayayyako kace zaka kasheni ba, Waleed kakosan akan gadonka muke saduwa nabata zanin gadonka da manniyina all over sanan natashi naje nai wanka abayinka and use your towel sanan haka zaka dawo da daddare ka kwanta cikin sperm dina ohhhh Poor boy" yasake fashewa da dariya yace "Waleed ohh nooo you should be ashamed of yourself as a man kafin matar daka aura tadauki cikinka tadauki nawa ta haifamin baby mai kama dani, I fucked Ilham countless time in every corner of the house you built kai Waleed kabani tausayi" ya kyalkyace dawani irin dariya, sanan yabi Ammi da kallo daga sama har kasa yace "saura mahaifiyar ka, ai har yanzu baki wuce menopause bako yar tsohuwa? Daga gani your pussy will........" wani irin kkwace ashanar hannun Ammi Waleed yayi yay kanshi daidai ya kunna ashanar Ammi tasa hannunta ta damke asshanar, ihu Arham yayi yace "oh my God this is getting interesting, kibarshi mana old woman let him kill me pleaseeeee" ahankali Ammi ta girgiza ma Waleed kai tareda kai dayan hannunta kan fuskarshi cikeda tsantsan so dakuma wani irin tausayin Waleed tears sukai rolling down her cheeks murya chan kasa tace "calm down d'ana, kakuma tuna komi yay zafi maganinshi Allah ne, sanan katuna babu wanda Allah baya Jarabta arayuwan nan, banso saida komi yazo karshe ne zaka kasacin jarabawan, babu abinda yaron nan bai makaba har gidan marayun ka da yaranka ya kwace kai hakuri kabarwa Allah maisa yanzu kakeson gazawa eh d'ana"? Tai maganan dawata irin tausasshahshiyar murya dazatakai har karshen zuciyan Waleed sanan tace "hukunci da wuta hukuncin ubangiji ne Waleed, ko da ba Allah yahana ayimai hukunci da wuta balle mutum, irinsu Arham barinsu ake da halinsu at this point Arham yariga yasa he is down so neman wanda he wants to drag down with him yake, sokake ka kasheshi all this his sins harda na mahaifiyar shi duksu dawo kanka? Yaron nan nada enough load akai da baniso kowa yadaukan mai so kabarshi dasu kaji Waleed" tai maganan ahankali tana janshi jikinta tace "come here, hug Mummy and calm down" fadawa jikin Ammi yayi yay kasa yana wani irin kuka Ammi ma tabishi kasan Arham ya kyalkyace da dariya, cikin wani irin kuka da inkaga Waleed saika tayashi yi yace "Ammi I hates Arham, na tsani Arham dakomi na rayuwana, I want to kill him soo soooo bad Ammi, Ammi I hate friendship, na tsani abota, Ammi na tsani friendship, Ammi I hate myself for ever considering someone like Arham as my blood, Ammi I regret knowing Arham, I regret all I've done to him in this life, Ammi saida yabari yagama enjoying luxury din life dina, yagama school yasan komi nawa sanan ya cutardani, yay destroying dina and my world, Ammi wlh I will never forgive Arham, Ammi bazan yafemai ba har duniya tanade" Waleed yafashe da kuka he never liked Ilham yasani but baitaba sanin koda bakason matarka ba kaji wani ya kwanta da ita yanamaka ciwoba saiyau, cikin kuka sosai yace "I've been so stupid Ammi, I trusted Arham blindly har to think cewa Allah ne yabani d'a mai kamada shi not knowing danshi ne, Ammi Arham ya cutar dani Ammi I want to kill him so bad, Ammi Arham cheated me to the core, bazan yafemai ba, Ya Allah naji maganan Mahaifiyata nabarmaka komi Ya Allah ka gaggauta min sakayya" yafashe dawani irin kuka da saida masu gadima kowa ya shiga share hawaye, Waleed yabasu tausayi kaman me, da kyar Ammi taina maza ta share hawayenta sanan ta kalli direbanta tace "Adamu zoka tayani mu shiga dashi ciki" sanan ta kalli Ilu tace "Ilu ku kwance shi karkumai komi, kunemo kayanshi da komi nashi kubashi yabar gidan nan" da sauri Ilu yace "hala kayan kwarton na ciki" ahankali Ammi tace "ku shiga ku daukomai to" duk sukai ciki suka fito da kayan Arham din, sanan itada direbanta suka daga Waleed da kuka yake kuka mai tsuma zuciya sukai ciki dashi, a falo Ammi ta zaunar dashi tanabin bereziyan Ilham da kallo da pants duk a kasan bene daidai Ilham tafito towel kawai ta iya daUrawa tama kasa saka kaya tsabagen tashin hankali hannunta rikeda Arham daya tashi yana wasa kaganta batada banbanci da mahaukaciya, kallo daya Ammi tamata tadauke kai direba yajuya yafita ganin ba kayan kirki ajikin matar. [11/27, 9:55 PM] saleemah: 💫💫 _*DUNIYA BIYU MABANBANTA*_💫 💫 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣3️⃣ & 6️⃣4️⃣ *THIS NOVEL NA KUDI NE, IDAN KIKA KARANTA KO KIKA TURA MA WATA DA BATA BIYA BA BAN YAFEBA WALLAHI🤷🏻‍♀️* _*This novel is 500 Fanmily*❤_ _How to Subscribe to TWO DIFFERENT WORLD_ _zaki turo 500 to account 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment to watsapp number na 07012181461, sainai adding naki a group din danake posting DUNIYA BIYU MABANBANTA_ Adaddafe Arham ya iya jan motarshi yay parking agaban wani private asibiti, yafito kasama tafiya yayi yazube awajen akazo aka kwasheshi akai ciki bdashi Dr da nurses suka shiga kokarin ceto rayuwanshi. ** Bayan 3days. Ahankali yake bude idanunshi dasukamai nauyi sosai yanabin ko'ina nadakin da kallo sanan yagane asibiti yake ashe, yatsine fuska yayi yana wani irinjin ciwon jiki yatashi yazauna da kyar daidai anbude kofa an shigo wani Dr ne yana ganinshi yay murmushi yace "welcome back" gyadamai kai Arham yace "how much is my bill zan tafi ku sallaman" da sauri Dr yace "no baka gama warkewaba akwai matsaloli still tattare dakai" hararan shi Arham yayi yace "I don't care banma san in sani nace maka zan tafi, yau kwana na nawa?" "3days sir" Dr yafada cikeda girmamawa, zaro ido Arham yayi yay jumping up ya cisge karin ruwan yay hanyar waje da sauri Dr biyeda shi da Atm card dinshi yabiya komi sanan ya karbi magungunan da akamai prescribing yasha sanan yashiga mota yatafi direct gidan marayun shi, agate mai gadin yace "yallabai lafiya ba'a ganka ba yau kwana uku yara sai rashin lafiya suke" ahankali yace "nima banida lpy ne bari na shiga na gansu" yaja motarshi ciki, office dinshi yayi direct dayaga yaran gidan marayun sunyi layi ana jiranshi zasu faramai magana yace "am coming" office dinshi ya shiga yarufo kofa, bayinshi yashiga yay wanka da ruwa mai zafi sosai jikinshi namai wani irin ciwo sanan yafito ya shirya cikin suit bakake dasuka mai kyau yafito Office din, bude office din yayi yafito yana kallon yaran wajen, yawanci kananun yarane saisu Fadila gabaki dayansu su Takwas din idanunsu yay jajir duk basuda lafiya, anatse yace "lafiya meke muku ciwo"? Da masu kuka da masu iya magana kowa yahau cemishi basuda lafiya, yatsine fuska yayi yace "duk kuwuce kutafi hostel dinku yanzu zan kira Dr yazo yadubaku" yay maganan yana bude office dinshi yakoma ciki, zama yayi tareda jan tsaki yace "God! Am tired of spending my money on this children, idan gwamnati bazata kawo kudin tallafi ba watsar da yaran nan zanyi na saida gidan marayun" yay maganan yana kara wayan a kunne yay magana da likitan dake zuwa duba yaran yacemai yazo sanan ya katse wayan, cikin 30min Dr yazo, fita yayi tareda Dr sukai girls hostel din yana tsaye ake duba yaran one by one, yana diban jinin wasu harya gama tsaf sanan suka fito sukai office din Arham, yabawa Arham katon list din magungunan daza'a sayo dakuma list din wayanda za'ama test kafin afadi magugunan da za'a basu, cikeda bacin rai yace "kaman nawa magungunan nan zasuci" ahankali Dr yace "at least kabada 150k harda kudin test daza'a musu" bude ido Arham yayi yace "150k harda kudin service dinka ko" girgiza kai yayi yace "nop kudin magani da test ne nan kawai" kaman Arham zaiyi kuka ya mishi transfer kudin sanan yawuce yatafi ya sanar dashi zai dawo kafin yamma, Arham ya bishi sa harara. Wuraren 5:30 yana zaune cikin office dinshi akai knocking, murya chan kasa yace "ccome in" bude kofa Dr yayi ya shiga cikin office din hannunshi rike da jakunkuna dakuma katuwar ledar dake cikeda magunguna, ya ijiye duka akan table din yace "this are the drugs zan ma kowa prescribing yanda zai sha his those, saikuma result of the test" yay maganan yana mikama Arham takardun test din ya karba yana dubawa Dr yace "Mr Arham am curious about something, as u can see wayan nan takardun are lab result na test din da aka musu, most of this girl are 18, 20, 15, 17yrs gabaki daya range shekarun su kenan, how come yaran dake gidan marayu under you people's watch ace yan mata harsu 8 Curr duk suna dauke da juna biyu!" wani irin mummunan faduwa gaban Arham yayi baisan lokacin daya dagokai ya kalli Dr ba, Dr yace "that's not even all Mr Arham, can you believe duka yaran nan kusan lokaci daya duk sukai cikin dan suna dauke da cikin watanni biyu dayan kai, how come suna fita ne"? Kaman wani wawa Arham ya girgiza mai kai tsabagen rudanin daya shiga Dr yace "that means dole afara investigation inhar yaran ba'a barinsu sufita waje tayaya duk zasuyi ciki is either cikin ma'aikatan ka wani yamusu ciki kenan, but zan tayaka tambayan su" da sauri Arham bakinshi har rawa yake yace "no.....no need karka damu just bani magungunan masu cikin nizan san how I will get them to telling me wabda yamusu ciki" yay maganan gabanshi na mugun faduwa, Dr zai kara magana Arham yace "you no wat? Infavt bamasai kaduba yaran ba, kawai kai attaching magungunan kowa da file dinshi acikin ledanshi da yanda zasu sha zan basu bari naje wajen yaran" yafita daga office din dasauri Dr yabishi da kallo, hostel din yaran yaje yana tura gate yaga Hassana da Farida na amai agaban famfo yana tsaye yana kallonsu saiga Sakina ta kwaso dagudu itama ta jonasu suna amai, innalillahi wa innailaihi raji'un, faduwa gabanshi yashiga yi a ahankali yabude kofar gate din yajuya yafita da gudu, tayaya yama mata takwas ciki all at a time yahada dana Ilham tara, he is expecting yara tara nan da wata bakwai, yahada da Arham little cikin 1yr yasamu 10kids dukansu bata hanyar aure ba duka shegu, kodai Mama tamai bakine, yatambayi kanshi da kanshi saikuma yay shiru yana tunani toya zaiyi shidai bazai cire musu ciki ba, to kodai ya cire? Wata zuciyan tace sukaje suka mutu fa gasu yara, kawar da tunanin yayi da sauri maganan Ilham nafadomai a rai, gwara itama yaje gidansu ya shaidama iyayenta kar asake a zubar mai da ciki, yana gama tunanin yay office dinshi daidai Dr yagama, biyan Dr yayi kaman zaiyi kuka ya gaji da kashema shegun yaran nan kudin shi wat is this now, baicikudi ba yahau kashema wasu marasa asalin tsintattun yaran nan, wato gwamnati ma sunsan wasuke bama tallafi dayake Waleed nada connections basu taba tsallake month ba basu kawomai tallafi ba, shi yanzu gidan marayun nan na neman 3nonth kenan amman har yanzu shiru kakeji. Fitowa yayi yay wajen motarshi ranshi amugun bace ya shiga ciki yatada motar yaja har zuwa anguwan su Ilham, akofar gidan yay parking sanan yafito yamaida motar yarufe yay knocking gate din, bude gate din mai gadin yayi yafito yana kallon Arham dan baisan shiba, murmushi Arham ya kakalo yamai yace "ina Sallama da Alhaji ne yana gida kuwa yacemin nazo zan sameshi ware haka" washe baki mai gadi yayi yace "yana ciki, aitun jiya Alhaji na gida bai fitaba hakama duk yan uwa an zo, bansan ko wani biki ake shirin manaba, shigo namaka sallama dashi" shiga gidan Arham yayi mai gadi ya shigemai gaba har gaban flat dinsu Ilham, abakin kofan mai gadi yace "ka tsaya anan bari nashiga na sanar" gyadamai kai Arham yayi mai gadi ya shiga bai wani jimaba yace "ance ka shiga" mai gadin yawuce yatafi shikuma Arham yabude kofar falon ya shiga ciki, kusan gabaki dayan yan uwan su Ilham na falon, harda kanwan Mummy Lami, da yayyinta duka maza da mata dasukema nesa duk an kirasu, gata atsakaiyar dakin akasa tana sanye da bakin hijabi har kasa tana kuka sosai kanta akan kafafunta shikuma Arham little na hannun Mummy datake rike da yaron yay bacci, kasancewan su Anty Hassu ne kawai sukasan Arham din yasa suke kallonshi surprisingly shukuma sauran harda Baba kallonshi kawai suke sungadai kaman Arham little dashi but basusan wayeba, bako kunya while wearing a smile yakarasa kan 3sitter Royal kujeran da Baba ke zaune shi kadai yayi yazauna kusada Baba, Baba ya mikamai hannu yace "ance kaike nemana saidai ban sankaba?" wani irin smirk yasaki yana gyara zama yace "hakane Baba baka sanniba saidai babu abinda yarka batasani game daniba hatta dadi na saisa ta zabeni akan mijinta na sunna" gabaki daya dagokai akayi ana kallonshi harda Ilham da kanta kekan kafarta tana kuka sosai, wani irin zabura yayinta maza uku dukansu sukayi da sauri Baba yadaga hannu yace "ku koma ku zauna" kallonsu Arham yayi yana sake murmushi irin mai kularda mutum dinan yace "you guys heard abinda Oldman yace ku koma ku zauna" wani irin kallon Baba Ibrahima yayi dan Allah yazubamai mummunan zuciya Baba ya gyadamai kai alamun yazauna Jan hannunsu kannenshi sukayi hakan yasa yazauna, Arham yatabe baki yace "good for you" Baba baitanka shiba danyasan irin yaran nan yarane da iyayensu sun riga sun musu baki cikeda mutunci da kamala yace "maiya kawoka gidana Bawan Allah, mesa kakeson ganina"? Cikin wani irin yanayi na rashin kunya Arham yadaura kafa daya kan daya sanan yajuya yay facing Baba da kyau yace "na farko Oldman sunana ba Bawan Allah ba, sanan na biyu is that how u treat your guest babu kodan lemu"? Wani irin zabura Ilham tayi tamike tazo gabanshi tana kuka sosai tanuna Arham daya juyo yana kallonta da yatsa tace "Arham kaga I will not have you kanama mahaifina rashin kunya, katashi kabar gidan nan, ubana ba tsaran wasanka bane" wani irin kallo yamata from head to toe sanan yanuna ta da yatsa itama irin disgusting nunawan nan yace "look at this karuwa, kedakika ci amanan mijinki agidanshi akan gadonshi bama kan gadonki ba har kinada bakin cewa kar ama baban ki rashin kunya agidan shi, anyi to dakanni" wani irin yunkurawa Ibrahima yasake yi Baba yamai wani mugun kallo hakan yasa yakoma yazauna sanan yakalli Ilham dayake jin mugun haushin ta data Fashe da kuka sosai yace "wuce ki koma inda kike ki zauna kona kiraki ne"? Girgiza mai kai tayi tana kuka sosai tawuce takoma tazauna inka ganta saika mata kuka tsabagen yanda tadawo abin tausayi ga laulayin ciki, Baba yajuya yakalli Arham din yace "ina jinka, meyakawoka wajena"? Wani irin karkada kafa Arham yayi yana gyara zaman agogon rolex din hannunshi yace "let's just say abubuwa dayawa yakawoni wajenka Oldman" yay shiru sanan yadago kanshi ya kalli Baba jin yanda dakin yay tsit kaman ruwa yacisu shi kawai akewa wani irin kallon tsana kaman su aikashi lahira sukeji suhuta yadanyi dariya kaman wanda aka sama ciwon dariya yace "abu biyu suka kawoni, na farko dai nazo ne nakarbi d'ana Arham Arham Jikan Malamai" da gudu Ilham tadago kanta ta kallai gabanta nawani irin faduwa idan akwai abu daya da bazata iya rabuwa dashi ba shine danta Arham, Allah yazubamata son yaron nan, wani irin murmushi Arham yayi danya karanci fear dinta tsaf sanan yace "nabiyu kashaidi kokuma Ince gargadi nazo namaka Baba dakai da ahalin ka akan koda wasa, infact karma kuyi fatan wani ciwo yakama Ilham dazaisa cikina na jikinta ya fita, koda wasa naji cikin dana mata yafici zakuga abinda zanyi" cikeda kulewa dawani irin tsanarshi Baba while looking at him right in the eye yace "in anki fa"? Wani irin kallo Arham yamai, ganin Baba was so serious yanamai wani kallon tsana yasa yafashe da wani mahaukacin dariya dazai iyasa kahadiye zuciya kamutu da kyar yay shiru yana goge baki yace "wayyo Baba, Baba Baba, Baba kenan, like Baba are you seriously joking with me, ni dinan Arham? Ka kosan waye ni"? Yakara fashewa da dariya sanan yahadiye dariyan yayi kini kini da rai, yace "Baba idan kaki, kokuma idan kunki, kukaki ji kuka kashemin dan cikina, to ku tabbatar kuma zan kashe yarku kuwa Khadija" da sauri kowana dakin yabishi da kallo, dan tabe baki yayi yace "Well not really like nine zan kasheta hukuma zata kasheta" yaydan shiru sanan yace "Baba kakosan inada video nida yarka muna saduwa ina tsokala gabana acikin nata dake haukatata" wani irin runtse ido Baba yayi idanunshi sunyi jajir kaman zai fashe da kuka hakama yaranshi Mummy kam hawaye tadinga gogewa tana tir da halin Ilham dazata je harta taraiya da wanan la'anannen yaron. Arham yacigaba yace "Baba kasan dai ni banda aure nai zina ko, amusulunce bulala 80 za'amin wanda tsaf zan jure amin aini namiji ne, itako yarka tai zina tanada aure jefeta za'ayi da duwatsu harsai ta mutu, after all ga evidence na video na bayar, gakuma two more evidence, ko makaho yaga Arham Little yaganni yasan waye ubanshi balle kuma alkalin shari'a court, saikuma evidence nabiyu gashinan tana dauke dashi dudda dai lokacin dazan shigar da karan inkun cire cikin ne" yay maganan yana kallon Baba da kowa nama dakin, jikinsu yay wani irin sanyi bandama Baba dake kallonshi irin na kallon nan na abinda kamana kaima Allah zai maka yaro. Fashewa da mugun mahaukacin dariya Arham yayi yace "Oldman naga jikinka yayi sanyi ne, banfa gamaba that's not all" yay maganan yana zaro waya daga aljihu yace "Baba kasan kai dan siyasa ne, ga yaran ka nan maza manya manya masu mukamai awaje da dama, naji wanchan ma navy ne" yanuna Ya Ibrahima sanan yace "Baba Mahaifiyata ta rasu hakama mahaifina tun ina karami I got nothing, absolutely nothing to loose, I don't mind sharing wanan sex video na ni da yarka a internate ba, ga fuskarta da komi na jikinta yafito rass Baba kamasan mene itake kaina ma bani ke kanta ba kalla kagani" yay maganan yana kunna video yakai gaban fuskan Baba da kafinma yakawo video Baba yakauda kai, hakan yasa yakara karan video inda Ilham ke ihu. "Wayyoooo Arham kanada dadi, wlh kafi Waleed dadi, kafi likta dadi, please karka dena, wayyooo Baabaaaaaa" kyakkyawa da dariya Arham yayi yay pursing video daidai inda takira Baba yana kallon yanda tears sukai rolling down cheeks din Baba, matan dakin kuwa duk sukahau kuka, Anty Hassu kuwan datace bazata tausayama Ilham ba, dan tunkafin abu yay nisa ta tambayeta tamata karya saida tafashe da kuka at this point kanwarta Ilham ke bata tausayi, she pity Ilham sosai, dan wanan ma kadai azabane Allah ke azabtar da ita tun aduniya, ga ciki danye, yaro dan wata uku hannu, ga ubanshi nason yarabata dashi, gakuma Arham din daya tasata agaba threatening to leak their sex video, kaico! Baba yakai almost 10min hawaye fita suke daga idanunshi sanan yasa hannu yagoge fuskarshi tass yajuyo ya fuskanci Arham, yace "Bawan Alla....." da sauri Arham yace "Mr Arham zakace Baba" ahankali Baba yace "Mr Arham" dagamai gira daya Arham yayi, Baba yacigaba yace "Ilham tariga tama Allah zunubai da yawa, daman koda wasa banson nakara sa tai wani zunubin kokuma nima nayi, cire ciki kisan kaine sanan haramun ne amusulunce, ranan lahira suna kai karanka wajen Allah, koda bakazo ba daman banda niyyan cire cikin koma miye acikinta inaso ta haifi kayanta lami lafiya" lumshe ido Arham yayi yace "Good Oldman sai number 2" ahankali Baba yace "saikuma nabiyu wanda ita alfarma ce bawan....i mean Mr Arham" yaydan shiru sanan yace "look at that boy, ko kwana biyar baiyi da cika wata ukuba, at this stage of life yaro na bukatan mahaifiyar shi, yana bukatan kulawanta da nono inka rabashi da mahaifiyar shi wazaka kaiwa shi dazata kulada shi kaman mahaifiyar shi"? Tabe baki yayi yace "money is the key, first class US nani zan daukomai" lumshe ido Baba yayi yace "Mr Arham kayakuri, kabar yaron nan da mahaifiyarshi ko shekara ne yayi kafin ka amsheshi" cikeda isa yace "bazan iyaba old man" fashewa da kuka sosai Ilham tayi kaganta zaka zudda mata da hawaye da ace zata iya mayar da agogo baya data mayarda shi ta goge duk wani abu datayi da Arham because he is the worst mistake of her entire existence. Baba zai kara magana cikin wani irin zuciya Ya Ibrahima yace "Baba wai akanme Zak dinga saukar dakai kana rokon bawan Allah nan? Ga danka nan ka dauka, do us a favour kama kwakulo nacikin Ilham din duka ka tattara kai gaba dasu kazaci we want anything that has to do with you agidan nan ne? Dan kaga ana rokonka zaka dinga mana bori, ka kai video court ka watsa a internate saime, dan an jefeta ta mutu ai dama shine hukuncin ta she got wat she deserve" da sauri Mummy dakaman ta haukace tazube akasa tana hada hannaye tace "no Ibrahima keep quiet, banson y'ata ta mutu, banson Ilham ta wulakanta haka aduniya, Arham we are so sorry please don't leak d video, inhar kana ganin darajan mahaifiyar ka dakace mana tarasu kaya kuri kabar Arham ko shekara ne yayi sanan karkai leaking video please, inhar kanama mahaifiyar ka" shiru yayi yana kallon yanda Mummy tai kneeling agabanshi tana kuka sosai tahade hannayenta, wani irin tabe baki yayi yatashi yamike tsaye sanan yataka har gaban Ibrahima dake tsaye shima ya tsaya yana kallonshi right in the eyes sanan yace "for the sake of Mahaifiyata dakika kira nahakura, ki daga guiwanki daga kasa" yay maganan yana wani irin murmushi sabida abin yama Ibrahima ciwo, cikin wani irin yanayi na kuncinrai batare dakowa yaji mesuke cewaba Ibrahima yace "I will deal with you Arham, zan nuna maka ka shigo family da basa kyalewa, I will reap your apart and make you chop your own shit" wani irin murmushi Arham yamai yace "let's see how that goes, bye Wan karuwa" Arham yajuya wani irin fizgoshi Ibrahima yayi azuciye baiyi wata wataba yadaurama Arham mari jikake fau! Baya Arham yayi zai zube yadafa kujera, biyoshi Ibrahima yayi Baba yatareshi ta hanyar bashi kuncinshi yace "ni zaka mara bashiba Ibrahima sarkin zuciya" cikeda fada Ibrahima yace "Baba akanme zaka dinga lallaba dan iskan yaron chan, how do you expect us to sit and watch yaron dakai jika dashi yana gayama magana eh Baba? Insu Mustapha zasu jure I can't Baba I've said it I will so deal with this boy, wlh billahi I will deal with you Arham zan nunama you've messed with the wrong family" yay maganan yay kifa azuciye, Baba yajuya yakalli Arham zaiyi magana Arham yadaga mai hannu alamun yamai shiru sanan yatashi yawuce yafita daga dakin yay waje motarshi yashiga yaja, Ya Ibrahima dake tsaye cikin wani shago dake gaban gidansu yay dialing wata number yakai wayar kunnenshi yace "Inspector Alo, am sending you one plate number inaso kamin tracking dinshi right now" Turamai number plate number motar Arham yayi sanan yamaida wayan cikin aljihu ya karbi tabanshi daya tsaya ya saya yawuce cikin gidansu ya shiga motarshi yaja har zuwa navy barrack, matar shi ma namai magana bai kulata ba sabida yanda hankalinshi yake atasshe ranshi amugun bace ya shiga dakinshi yarufe yana kallon kiran Baba amman ko daukan wayan baiyiba, kiran wayan da aka sakeyi yasa yadauki wayan yakara a kunne, murmushi yayi sanan yace "thank you Alo, u deserve some ransom, just, just send me your details" sanan ya katse wayan yay dialing wani number ana dauka yace "sani a speaker Isa nasan su Jahid natare dakai" dan shiru yayi yace "listen boys, akwai wani aiki danake son nabaku, I trust you with this work sabida nasan you guys are damn loyal to me, I trust you guys, anyway abu daya kawai nakeso kumin akwai wani danakeso kumin stealing phone nashi, yanzu haka guy din na Oreo Cafe, that's the only thing kawai zakuyi, just steal his phone and bring it to me" ya katse wayan sanan yasake kiran wani number yace "George I have a work for you, zan turomaka wani address din orphanage, I want you to go to the CEO's office right now, hack all the system bayan kagama burn only the CEO's office down kabar wajen batare dakowa ya ganka ba" ya katse wayan sanan yakira wani yace "Hello Ahmad am calling cus I have a job for you, akwai wani guy by name Arham Jikan Malamai dress in suit baki, zai fito daga gidan marayun zakaga yay wajen wata mota Mercedes benz inaso kabishi, hit his car hakan zaisa yay parking yafito yana fitowa ka kamoshi just bring him straight to my warehouse inka kaishi ka kulleshi leave him dere for me I take it from dere" yana gama maganan ya katse wayan yace ""now kaike bani tausayi ba kanwata ba Arham"" yana maganan yabude kofar bathroom dinshi ya shiga. [11/27, 9:55 PM] saleemah: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣1️⃣ & 6️⃣2️⃣ Ahankali tasauko tazo har gaban Waleed dake kuka sosai kuka bana wasaba tai kneeling har kasa tareda ijiye Arham little agefenta tahade hannayenta cikin kuka tace "Ammi, Dr wlh banda abinda zance, amman na rokeku da girman Allah dakuma darajan Allah kurufamin asiri, Waleed kawa Allah da Annabi kayakuri nasan na cutar dakai dayawa Waleed, please forgive me, Ammi" wani irin kallo Ammi tamata tace "to think I take you as my own daughter Ilham amman kikamin abinda kikayi hmmmm" Ammi ma takasa magana tace "ranan dana fara daura yaron nan a ido naji a jikina ba dan d'ana bane, amman nahana kaina yarda dakaina ina cema kaina tsanan danama Arham yasa yanzu nadena ganin abu ayanda yake, nace ma kaina akanme zan zargi yarinya mai tarbiya irinki, tattara komi nayi na watsar nacire zagin a raina sanan zargi nabata komi Ilham amman ashe inada gaskiya, Ilham danadai kika cuta ko"? Girgiza kai Ilham tayi da sauri tana wani irin kuka, Ammi tasake cewa. "dana dai kika cuta ko Ilham" sake girhixama Ammi kai tayi Ammi tai kwafa tace "tashi kidauki danku yanda ubanshi yabar gidan nan kema kifita kibishi kutafi duk inda zaku, d'ana zai aiko miki da takardan ki har gidan ubanki, keda d'ana har abada, ko mata sun kare Waleed yagama zama dake wlh, ki tashi kirufawa kanki asiri kibar gidan nan sadaf sadaf kafin nasa a fitar dake" ayanda Ammi tai maganan tasan da gaske take tasa ta tashi da sauri tai sama dogon hijabinta kadai ta daura kan towel din jikinta tana kuka sosai tafito ta kinkimi Arham tawuce tafita daga dakin Ammi tabita da kallo sanan ta rungume Waleed sosai ajikinta tana shafashi tace "ya isa Waleed karka jawa kanka ciwon zuciya shi rayuwa yagaji haka daman, ba kowa nakusa dakai bane ke sonka, banda haka da makiyi na kusa gwara na waje, dan makiyin ka nakusa yafi kaika kasa, Waleed inda ace yau nabari ka kashe Arham da still u will never be free, wanan bakin cikin yana tattare dakai kuma hukuma takamaka kaima akasheka bayan kayi shekaru agidan yari, Waleed shi rayuwa dakake gani kome yasame ka kaddara ce anrubuta daman hakan zai faru, sabida halin Arham kuma don't let it discourage you kace bazaka kara taimakon wani ba, aduk lokacin dakake da halin taimako kayi, sanan wanan gidan marayun koda daga baya an baka shi back kayaha kudi kabarshi, Dear Son akwai thousands of abubuwa dazakayi mahaifinka yasami ladan, zaka iya zuwa kauyuka ki gina boholes islamiyu masallatai agaruruwa daban daban yanki daban daban, eradicate almajiran ci, duk wani yaro da aka turo almajiran ci send him back sanan katura kauyen su ataimaka musu agina musu schools, abasu tallafi, settle down Waleed, forget anything Arham and build your life back, tun bayan ya kwace maka gidan marayu lamarinka suka lalace, karufe babin Arham duka arayuwan ka and open a new chapter, ka koma aikin asibitin ka Zenith kokuma ka gina naka asibitin and kadinga duba mutane free, shima charity work ne amman gidan marayu kagama yinshi son, kamanta da Ilham dakomi nata, gidan nan sell it kika kyautar dan banson anything dazai dinga tunamaka dasu, kadage da addu'a, ka gyara tsakanin ka da Allah kaga yanda Allah shima sai tsaya maka, forget everything kana zaune xkaga sakayyan da Allah zai maka cikin gaggawa, is okay babyna kaji" Ammi tamai kiss a kumatu tana sharemai hawayen, kankameta yayi sosai yadaura kanshi kan kirjinta tana shafa bayanshi ahaka yay bacci ajikinta tanajin yanda yake sauke ijiyan zuciyan kuka, mayar da kanshi kan kafarta yayi ta gyaramai kwanciya tana kallonshi itama tabude nabin nata sabon kukan, tai kuka tai kuka tagodema Allah, wanan Jarabta da danta kegani yay yawa tamai addu'a sosai sanan zata sake tsayawa akanshi tsayin daka kar Arham ya kashe mata da. Ahaka har gari yawaye tana zaune yanda taga dare haka taga r'ana kanshi tashafa ahankali, bude idanunshi yayi ya kalli Ammi idanun sun kumbura sosai, murya chan kasa tace "gari yawaye tashi kai alwala kazo kai salla" tashi yayi ahankali yay bayin falon ya shiga itakuma tadauki wayarta text ta turawa Mom akan tazo gidan Waleed this morning, sanan tama Uncle message tasanar dashi komi dake faruwa sanan ta ijiye wayan, sama taje tadauko dadduma tadawo falon ta shimfida nai, fitowa yayi daga bayin yahau kan dadduman itama tawuce bayin ta dauro alwala tafito agefenshi ta tsaya tai salla duk suka idar, tana zaune kan dadduman tana lazimi taji anbude gate Mom ce tashigo gidan da saurinta itada Abdul danshi yatukota sukayo falo tana shigowa idanun Waleed kadai takalla tagane balafiya sabida yanda suka kumbura da sauri Abdul yay kanshi yakai hannunshi kan wuyanshi yace "Ya Waleed bakada lafiya ne meke damunka"? Kafin ma Waleed yace wani abu sukaji ansake bude gate, tashi Mom tayi ta leka ta window tace "Family su Ilham ne wats happening wai" ahankali Ammi ta tashi ta tashi ta zauna kan kujera Mom takoma kan kujeran datake zaune ta zauna Waleed da Abdul kuma na zaune akan dadduman Mahaifin Ilham ya rangada Sallama, Abdul ne ya amsa yatashi yay wajen kofan tareda bude musu kofa suka shigo, Baban ta, sai Mummy su, sai babban yayansu Ibrahima, sai Ya Hassu da Husai dakuma Ilham din da hijabin jiyane ajikinta har kasa idanunta sun kumbura suntum akasa Mummy narike da Arham, anatse Abdul yace "ku shigo" shigowa sukayi aka nennemi waje aka zauna Mummy kuma tai wajen kawarta tace "Ammi meya farune wai jibi idanuwanki" murmushi kawai Ammi takakalo mata batace komiba, gyaran muryan da mahaifin Ilham yay yasa duk akai shiru, yace "Assalamu Alaykum, sanan barkanku kokuma nace barkanmu da safiya gabaki daya, nasan kuna mamakin ganinmuda sassafe hakako" yaydan shiru yace "ayanayin yanda Ilham tashigo gidanmu jiya da daddare kaman wacce aljanu suka buge tana kuka tana ihu hakama dan karamin yaro ta yasa muka shiga damuwa ainun, da tun dare mukaso muzo amman mukace dare yayi a bari da safe saimu kawota muzo muji meya faru dan wlh bata gayamana komiba sai kuka datake yi, yanzu kuma damuka kawota mukaga kuma duk kunanan hakan yakara tabbatar min cewa da abinda ke faruwa, dan Allah kucire my daga duhu Hajiya" murmushi kawai Ammi tasaki sanan tazubama Ilham wasu irin idanu takira sunanta. "Khadija" dagokai ahankali Ilham tayi ta kalli Ammi suka hada ido, babu alamun wasa akan idanunta tace "gayama iyayenki abinda yafaru da abinda kikayi" gyadama Ammi kai tayi ahankali bakinta nawani irin rawa tana shirin fashewa da kuka sanan ta kalli mahaifinta da babban yayansu tace "Baba ummm......jiya Waleed yadawo daga tafiya da daddare, sh......shi.....ne y......ya.....ya kamani da......da...." wani irin mahaukacin tsawa babban yayansu Ya Ibrahim yadaka mata yace "yakamaki dame!" wani irin firgita tayi tasake fashewa da kuka tana komawa baya tace "yakamani da.....da babban aminin shi Baba" tafashe da mugun kuka tashiga komawa baya tai wajen kafafun Mom tarike kafan Mom gam, wani irin mugun kallo mahaifinta yamata yace "mekike nufi da mijinki yakamaki da amininshi Khadijatul Iman"? Baba yamata tambayan babuko digin wasa akan idanunshi, wani irin kuka take tana haki takara damke kafar Mom tace "Baba kuyakuri wlh naci amanar ku, Baba bansan meya shegeni ba, Arham mayaudari ne, maci amana, tun ina Amarya tun muna yankari nabiyemai muka fara tarayya da Arham, Baba kuyakuri ku gafartamin amma Arham little danshi ne bana Mijina ba, Mummy kin tuna ranan dana fita ina gida ina jego nace miki wajen Samira kawata zani, wlh Mummy ba wajenta najeba wajen Arham naje aranan kuma nadauki wanan sabon cikin dake jikina na wata biyu dayan kai, shine jiya Waleed yadawo yakamamu adakinshi akan saman gadonshi tsirara muna saduwa, Baba dan Allah kuyakuri kuyafemin karku tsanani dan girman Allah" tafashe da kuka, duka family ta kallonta suke babu wanda ya iya kwakkwaran motsi cikinsu jin abinda yarsu tafadi da bakinta inda ace wani yafadi zasu iya cewa shairi aka mata amman dagabakinta yake fitowa, Baban Yayansu ne yakasa daurewa sabida Allah yamai bakar zuciya yatashi ya shiga kalle kalle adakin, wayar gaban TV falon yaje baimasan wayan miyeba ya fizgo azuciye yayo kanta kankame kafar Mom tayi tana kuka sosai. "Mom zai kasheni wlh karki bari yadakan karki bari yadakan" fizga daya yamata ya fincikota yashiga zuba mata wayan wutarnan tako ina yasamu ajikinta yana hadamata da hannu gabaki dayan dakin babu wanda yay yunkurin hanashi sai ihunta dayacika ko'ina yana dukanta yace "I can't imagine what bawan Allah nan went through" yanuna Waleed da kanshi ke kasa, yace "I try to put myself in his shoes nakama matata da wani akan gadona agidana tsirara na rantse da Allah bazan bartada raiba, amman bawan Allah nan ko marinki baiyiba Ilham, tarbiyan da Baba da Mummy suka baki kenan, Ilham ki haifi shege sanan kina dauke da wani cikin shegen ajikinki yanzu haka, Innalillahi wa innailaihi raji'un, Ilham wlh kanki kika cuta bamuba" yacigaba da dukanta ganin yana neman kasheta numfashinta har neman daukewa yake yasa Ammi ta yunkura zata tashi riketa Mummy tayi tace "bazakije ba" fizge hannunta tayi ta tashi hannun Ibrahim takama da sauri tace "karka mata rauni Ibrahima ba ita kadai bane" cikin kumfan zuciya Ibrahim yace "Mummy kinsandai kin isa dani ko, tun ina yaro nasanki tareda Mummy mu, yanda na dauki uwata haka na daukeki Mummy ki kyaleni gwala na illatata, ta mutu daga ita har abin cikin nata, Mummy kinji abinda tamuku kuwa, Mummy ta cutar da ke da danki, Ilham taci amanar amintar da kawance da yardan dake tsakanin ki da mahaifiyar mu, Ilham taruguza komi da kukai building tun kafin ahaifo mu" girgixa kai Ammi tayi tace "bata bata komiba, nida mahaifiyar ku will always be aminan juna har duniya tanade, bani wayar wutan nan kaga" karban wayan tayi sanan tajashi tamaidashi kujeran dayake zaune kusada Baba, itakuma Ilham tazube ajikin bango bakinta na jini sosai goshinta ya kumbura fuskarta yay rudu rudu. Mummy daketa kallon Ammi jitayi kaman ta nutse akasa tahuta wani irin kunyan Ammi taji tanaji tama kasa magana same with Baba shima yakasa magana, yayyinta su Hassu ma haka dan abinda tayi mai girma ne sai karan kukanta daya cika dakin, gently Waleed yadafa kujera yamike tsaye da sauri Abdul yace "ina zaka Ya Waleed" ahankali yace "am coming" hanyar stairs yayi kowa yabishi da kallo yay sama, ko 5min cikakke bai bata asaman ba yafito rikeda wata envelope a hannunshi ya shigo har tsakiyan falon cikeda girmamawa yamikama Ibrahima takardan, kallonshi Ibrahim yayi saiyaji kaman yamai kuka sabida yanda idanun yaron suka kumbura sosai sukai jajir, karba yayi ahankali Waleed yajuya yakoma wajen zamanshi shikuma Ibrahima ya yage envelope din sanan yazaro takardan ciki ya warware yakaranta afili. "Ni Dr Waleed Warbai na saki Khadija Muhammad saki uku!!!" wani irin ihu Ilham ta kwarara tadaura hannunta biyu aka tace "na shiga uku na lalace, Waleed dan darajan iyayen ka kayakuri karkamin haka, Waleed wlh ina sonka sama da rayuwata bansan meya shigeni ba harnaje ina tarayya da babban amininka kayakuri Waleed" wani irin kallo Mahaifinta Babanta kemata sanan yakalli Waleed, cikin sassanyar murya yace "an cuceka Waleed, koda baka saketa ba dani saina saka ka saketa, Ilham ta cutar dakai Waleed" Baba yay shiru sanan yadaga idanunshi yakalli Ilham yace "ina mai tabbatar miki dakije ki nemi wani mahaifin baniba Khadija, sanan kije kinemi wani gidan uban banawa ba" ahankali Mummy tasauko daga kan kujera tamikama Hassu Arham lillte sanan ta tsugunna agaban Waleed takama hannun Waleed din ahankali saikuma tasake shi ta hade hannayenta biyu tasa guwianta akasa, da sauri Waleed yace "Mummy me haka please stop it" girgiza mai kai tayi zatai magana sai kuka tama kasa zaunar da ita Waleed yayi yace "Mummy sit please" zama tayi tana kuka sosai tace "Waleed bansan mezan cemaka ba, bankuma San dawani fuska zan kalli mahaifiyar kaba, amman wlh Waleed y'ata tacutar dakai, wlh bantaba koyamata abu makamancin hakaba, Waleed I am so sorry dan Allah, Waleed forgive me" yanda Mummy ke kuka yasa yaji tana neman tasa yafara kukan shima girgixa matakai yayi yace "bakomi Mummy kidena rokona" juyawa Mummy tayi tama kasa kallon Ammi tace "Ammi kuyakuri dan Allah" murmushi Ammi tamata tace "komi yawuce" tashi Baba yayi ya kalli yaranshi yace "mutafi" sanan yakalli Ammi yace "munbarku lafiya" yay hanyar waje su Hassu da Mummy suka bishi batare dasun kalli Ilham ba, wani irin tsawa Ibrahima yadaka mata yace "tashi mutafi" tashi tayi tana kuka sosai tazo ya hankadeta har tana bugewa da kofa suka wuce suka fita, motarshi yasata dan Baba ya rantse bazata shiganmai mota ba aka tafi. Ganin yanda dukansu sukai shiru duk suna tunani yasa Mom tace "Adda am thinking of something" da sauri Ammi tace "menene" ahankali Mom tace "how about dukanmu muyi tafiya mubar kasan kawai, let's all get away from this problem for a while and forget everything muyi kaman 6 months kafin mudawo" ahankali Ammi tace "ina zamuje"? Murmushi Mom tayi tace "nida baban su Abdul munce muje Qatar, in kinaso sai duka muje kawai and live like a family" shiru Ammi tayi tana kallon Waleed tasan he need it yabar environment dinan gabaki daya kawai for a while ya manta da komi dakuma kowa tace "shikenan done" takalli Abdul tace "Son handle everything book private jet for us gobe inma munsami yau dinan we move" murmushi Abdul yayi yace "tom Ammi" murmushi Ammi tayi tace "do you like the trip idea Waleed" gyadama Ammi kai yayi ahankali yana sauke ajiyan zuciya yace "Ammi mutafi yau please" ahankali Ammi tace "Abdul you heard him, tashi kaje kai komi to, bari muje gida muyi wanka, bama saikun shirya kaya ba masai kaya achan" tashi Abdul yayi Waleed ma yatashi da sauri Mom tace "ina zaka"? Cikin wata shaking voice yace "am going with Abdul muhadu a airport kawai" Mom zata kara magana Ammi ta girgiza matakai alamun tabarshi, fita sukayi Ammi ta tashi suka fita tareda kulle gidan sanan ta sallami mai gadi zasubar kasan sanan suka tafi gida, itakuma Mom tawuce nata dan taje su shirya suma. Tana shiga gida taga Widad zaune a falo sai kofa take kallo idanunta sunyi ja kaman tai kuka, murmushi ta kakalo taje kusada ita tazauna kafin ma tai magana Ammi tace "sorry daughter mun fita bamu sanar dakeba, mijinki yaje shirya mana tafiya anjima zamuje Qatar, muje natayaki gyara kayanki dudda ma agayre yake". Karfe shida duk tamasu Airport, ganin Asma'u yasa tadan saki ranta sai wurga ido take taga Waleed amman bata ganshi ba, sai acikin jirgi taganshi zaune ya lumshe ido, kujeran kusada Ammi tazauna sai satan kallon Waleed din take ganin yamata kama da mara lafiya. Da Asuba suka sauka a Qatar aka kwashwsu a mota wani dankareren family house taga sunje, kai kudi nada kyau, aka shiga ciki sanan Ammi takaita wani flat mai kyau tace "nanne bangaren ku keda mijinki jekiyi wanka kiyi salla ki kwanta ki rama bacci ga mijinki nan zuwa" tai maganan tana rufo mata kofa, ciki ta shiga tazauna abakin gado, jin shiru bai shigoba yasa ta tashi tacire kaya tashiga bathroom tayo wanka tafito daure da towel akirji. Akwatinsu tabude taciro wani light cloth tasaka sanan tasa hijabi ta kabbarta salla harta idar tai bacci ta tashi still bataga Waleed ba, koda Asma'u tashigo takirata sukaje falo cin abinci bata ganshi ba, kasa daurewa tayi saitafara kuka amman tai maza ta share hawayen duk Ammi na lurada ita wajajen 9 Ammi tace "tashi kije ki kwanta Daughter" gyadama Ammi kai tayi tawuce ta tafi itakuma Ammi ta tashi tai dakinsu Abdul tana bude kofa taganshi zaune kan gado duk yadawo wani kala kaman bashiba tace "what do you mean Waleed? Why are you avoiding your wife"? Ahankali yabude baki zaiyi magana Ammi ta dagamai hannu tace "whatever your reason is I don't wanna know, katashi kaje kasami yarinyar nan she has been looking for you tun dazu, am not gonna sit back and watch you ruin your life kaji, tashi katafi side dinku kafin nabata maka rai" ahankali yatashi yawuce Ammi tabishi da kallo sanan tabi bayanshi saida taga yabude kofar side dinsu ya shiga sanan ta sauke ijiyan zuciya takoma ciki. KUJI TSORON ALLAH VIP, DUK WACCE TAFITAR TAMA KANTA, KUMA KITUNA ALLAH NA NAN. Tana zaune kan gado tana kuka sosai taji anbude kofar falo, ahankali ta tashi tana goge hawayen ta tafito daga bedroom din ganin Waleed tsaye jikin kofa yazuba mata ido yasa tawani irin fashe da kuka tai wajenshi da gudu ta fada-jikinshi takankame shi, wani irin ijiyan zuciya yasauke hakanan saiyaji wata natsuwa ta shige shi ahankali ya daga hannayenshi ya rungumeta back yakai bakinshi saitin kunnenta murya chan ciki yace "am sorry for hurting you I don't know wat I was doing" dago kanta tayi ta kallai fuskarshi, hannunta takai kan fuskarshi tace "what happen to you? You cried? Who beat you? What happen to you"? Ta tambaye shi ahankali, hannunta datake shafa fuskarshi dashi yakama yarike gam yadaura kan kirjinshi yakira sunanta anatse kai tsaye. "Saheeba" murya chan kasa tace "na'am" sake kankame hannunta yayi yace "promise me that I will be the only man that will always know you amatsayin ki namace har karshen rayuwan ki, inada masifaffen kishi nakasa bringing kaina to accept cewa I will always be the man that will make love to you till eternity, Baby don't ever cheat on me, I love you beyond words Saheeba if u cheated on me wlh zan iya rasa raina, promise me I will be your first and last" daura hannunta tayi kan nashi ta kankame tana kallonshi tace "Ya Waleed you are the onlyman danake so, you are the onlyman that makes my heart skip, you are the only man your Saheeba love, and you will always be that man that spread my legs apart, I will never cheat on you, ina addu'a Allah karya nunamin ranan dazanyi cheating on this my handsome husband" tai maganan tana kissing hannunshi kafin ahankali tadago kanta tai grabbing lips dinshi tana kwancemai boturin riga ta cire rigan ta yar sanan tai wani irin tsalle ta dane kanshi yarike ta da kyau yana kissing dinta shima, sukai wajen gado, zaunar da ita yay abakin gado tasa hannu tana kwance belt din jikin jeans dinshi taja jeans din da boxer shi kasa takama huge manhood dinshi takai mouth nata, daura hannunshi yayi akanta yace "ohhhhh" head tashi bashi ganin yana neman suma yasa ya karbe ya kwantar da ita yana daga kafafunta sama yaja pant dinta ya yar yadaga kafar ya shigeta ahaka, kuka yafara sosai kaman zai sume ranan they make crazy love saida yaga kaman zata suma sanan ya kyaleta tai extreme gajiya, shima jiyayi yasami natsuwa hankalin shi ya kwanta, harta fara bacci tajishi kuma bata hanashi ba danta lura kaman yana cikin wani matsala inhar kuma samunta yanda yakeso zaisa ya warke matsalan ta gushe then she is ready to give me, tagaji iya gajiya, maranta nawani irin mahaukacin ciwo amman bata hanashi ba tabarshi, saida gari yawaye tsaf danko asuba baijeba sanan yabarta sauka yaga tai daga gadon da sauri daga kafa daya yaga tayi saikuma tazube asume dawani irin gudu yatashi yadauketa ganin jini nabin kafarta yasa gabanshi yafadi kaya yasaka da gudu ya nemo yasamata, fitawo waje yayi duksu Ammi na barshi direban gidan yasa yadauke shi sai asibiti, karbanta sukayi aka kwantar da ita, gwajin farko aka gano ciki gareta but yanaso yazube dan haka aka bata 30days bed rest ko kofi kar'a bari tadauka, Waleed sujjada kawai yayi lokacin da aka cemai +tanada ciki, Allah kenan Gaffur Rahima at a spot yanuna mai yaron dayake gani amatsayin nashi is not his ga nashi nan yabashi. 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣5️⃣ Wanka yayi yafito tsaf, sanan yabude wardrobe dinshi yaciro wasu kaya jeans da riga sanan yadau jacket yasaka, yazo gaban mirror yaja kujeran wajen yakai gaban wardrobe din yahau kan kujeran sanan yamika hannu yajawo wata akwati awajen sanan ya sauko daura akwatin yayi kan gado yabude akwatin, wasu hadaddun wukake ne masu kama da surgical blade amman ba surgical blades bane yana binsu da kallo jin anbude kofar dakinshi yasa yarufe box din da sauri ya kalli kofar matarshi ce ta shigo cikeda damuwa tana kallon fuskarshi tana kuma kallon akwatin gabanshi tace "Baby wat are you doing with that box? Bama wanan ba why are you so angry eh baby"? Murmushi yamata yajawota jikinshi rungumeta yayi tsamtsam yay lamo ajikinta, ahankali yace "wanine yama Baba rashin kunya agabanmu and in my life bazan iya yafema duk wanda yama iyayena rashin kunyaba kema kin sani, so zan fita am coming" yay maganan tareda sakinta ya sunkuci akwatin yafita har waje tabishi dan tasan halin mijinta Allah yamishi bakar zuciya, amman kafin tamai magana haryaja motarshi yafita daga gidan. Doguwar tafiya sosai yayi sanan ya shiga wani daji shima dogon tafiya yayi sanan yakai wani gida kwallin kwal dake cikin dajin, parking motar yayi agaban gidan sanan yafito ya kulle kofar yabude kofar baya yadauki akwatin wukaken sanan yamayar yarufe yabude kofar gidan ya shiga, babban gidane haka warehouse duk ciyayi dan tunda yagina warehouse acikin gari yadena amfani da wanan maida kofar gidan yayi yarufe sanan yakarasa gaban kofar dayaga anrufe da key an ijiye makullin a kasan wajen yadauka yadau key yabude kofar ya shiga ciki, dakin duhun bala'i saikuma motsin dayakeji motsin kacha. Hannu yasa ya kunna wutan wajen hakan yasa dakin yay haske sosai, Arham ne kwance akan wani katon table table din yafi girman table din masu nama na kasuwa, an kulle kafarshi da hannayenshi da kacha an budeshi haihuwar uwarshi, jikinshi narawa sosai, jin motsin mutum yasa ya karkato yajuyo da kanshi da kyar ya kalli Ibrahima daya shigo yana kokarin magana ya kasa sabida kulle bakinshi da akayi da seletef idanunshi sunyi jajir, wani irin murmushi Ibrahima yayi yatako daidai yazo tagabanshi inda Arham din zai ganshi da kyau sanan ya ijiye akwatin kan table din yana bin jikinshi dawani irin dirty look kafin yatura hannunshi cikin aljihu yazaro handglove yana sakawa a hannunshi yace "so da wanan abun kaman lagwani ne kacutar da kanwata ka wulakanta ta Mara kunya" wani irin girgixa mai kai Arham yayi gabanshi namugun faduwa kaman zai fashe. Ahankali Ibrahima yabude akwatin wukaken wata hadaddiyar wuka yaciro daga box din yanunama Arham yace "kaga yanda Ilham ke kuka? All because of you? Kadauka bamasan yar uwanmu ne? No Arham we love yar uwanmu but we despise laifin data aikata but at least tai nadama is obvious yarinyar nan tai danasanin abubuwan datayi dakai but kaifa? Babu anything like nadama tareda kai, kodanasani, kayi laifi but kanada guts kazo kana threatening namu kanama mahaifinmu rashin kunya kasan wayemu kuwa"? Yaydan shiru sanan yace "navy ne ni, kafin nasami navy nan na nemi aikin soja sau hudu, duk naje training but bana samu, banson raini banson yaron da baida alkunya, ban iya yafiya ba ko iyayena sunsan wanan ne jarantan da Allah yama rayuwana, kaga kukan dakasaka mahaifina, kaga kukan daka saka Mahaifiyata, kanwar Mahaifiyata, kanwata da yayyina u are about to cry times 100 of yanda sukayi" yay maganan yanakai hannunshi kan bakinshi ya dayemai saletef din, jikin Arham harwani rawa yake dudda tsoro yacikashi saida yadake yace "how dare you! Kasan ni waye dazakasa akawoni dajin nan and strip me naked a kulleni akan kujeran nan ko motsi bana iyayi, wlh ka kwance ni yanzun nan natafi wata kila zan iya yafemaka amman inhar baka kwance niba wlh your whole family will suffer for your act kadaisan inada evidence ko" dan murmushi Ibrahima yasakin mai yace "I love courage dinka da karfin halin ka, bakinka dai baya mutuwa" "bazai mutuba din bazaka kwance niba, wlh sister ka itace zata mutu akan this your act zansa ajefeta akotun musulunci, wlh kuwa" wani irin cool look Ibrahima yamai sanan yadaura hannunshi dake sanye cikin handglove kan joystick dinshi yarike daidai kan yakalli Arham din da jikinshi yashiga wani irin mahaukacin rawa yace "I don't know if u are a medical student but anyway zan maka tambayan dai, kasan menene Amputated Penis"? Wani irin rawa jikin Arham yake ko a shocking akasashi sai haka yana kallon wukarda Ibrahima ke rikeda ita a hannu yace "me haka kake rikemin gaba kana namiji kai gay ne? Look this is no joke ka kwanceni nasaka kayana naitafiyata I promise bazanma fadiwa kowaba" wani murmushi yayi yace "you didn't answer my question, nace maka kasan menene amputated penis"? Yay dan shiru yana kallon fuskarshi yanda zufa ke ketomai sanan yace "anyway lemme just tell you, amputated penis shine gaban da akayanke, gutsurarren gaba" kara jan joystick din yay ya fizgeshi sama kaman zai katsa harsaida Arham yay kara yace "you deceived my sister with this, and you ruin her life with this, kaga daidai kan nan, daidai kan kaciyan, crowns dinan naka daidai wajen zan yanke, banson na yanke gabaki dayan gaban naka, Nop6, nafison kullum ka kalli gaban kaganta amman babukan da sperm zai fito tashi, babukan dazaka shiga gaban mace dashi, Arham when I told you you were messing with the wrong family kazaci wasa nake" wani irin kwashewa da dariya Arham yayi kirjinshi kaman injin nika tsabagen yanda yake bugawa sabida tsoro, ya zazzaro ido yace "you are joking right, kasan mekake cewa kuwan? Kasandai mutuwa ake idan aka ya yankewa mutum gabako, please let's stop this joke" ahankali Ibrahima yakai wukan daidai kasan head din penis din yaja wukar ya tsaga, wani irin mahaukacin ihu Arham yayi yana kokarin kwace kanshi amman yakasa gabaki dayanshi a daure yake ko motsi baya iyawa, wani irin fuskan isgilanci Ibrahima yamai yana kallonshi yace "ahhhhnnnn I didn't expect you kafara kuka kana ihufa tun yanzu duk bakinka bawan......wai I mean Mr Arham" wani irin rawa jikin Arham yake yana kallon yanda jini kebin joystick dinshi yace "dan girman Allah kayakuri karka yankemin kan gaba, mutuwa zanyi kayanke min kan cilla, dan darajan Allah kayakuri, kaga na janye duka abubuwan dana fadi agidanku wlh wlh na janye da Allah kadena" kama kan da kyau yakai wukan yakara yankewa kadan yace "bazan maka yanka dayaba, banson narage maka azaban, I wabt want you to suffer and feel the pain bit by bit" "wayyo Allah na shiga uku na lalace, dan girman Allah kadena karka yankemin bura, wayyo Allah na burata, jama'a burata" wani cute smile Ibrahima yasakin mishi yace "seeing you cry gives me goosebumps poor Boy" yarike kan dakyau ya shiga yankawa kaman ana yanka naman rago washe garin salla. Wani irin ihun da Arham keyi saikaji tausayinshi. "Waleeeeeeedddddddd, Waleeeddddddddd, help me, wayyo Allah na zan mutu, Waleeeed" tsabagen azaba baimasan Waleed yake kiraba ya sume kawai warwas dan the pain was too much for him to bear, kan kaciyar na gab da tsinkewa Ibrahima ya cire wukar ya yar yana murmushi sanan yajuya riganshi da aka ciremai ya dauko ya yaga sanan yadawo yakama kan kaciyar dake lilo ya manna da asalin jikin joystick din ya kulle yace "I don't want you to loose to much blood and die, mutane irinku didn't deserve to die early, yakamata kuyi rayuwan wahala da kunci" ya kulle kan tass sabida jini yadena zuba sanan yay wajen wata botiki dake wajen, daukan botikin yayi yataho yadaga ruwan yajuyemai aka, wani irin firgita Arham yayi ya farka yana wani irin nishi gabanshi namai zafi sosai yawani irin fasheda kuka yana kallon yanda aka kulle wajen da tsumma yace "wayyo Allah zan mutu, kaciremin crowns, na shiga uku, wlh mutuwa zanyi, azaba yakemin, kawa Allah kabani pain killers, wlh bazan fadima kowaba kasaken natafi nakai kaina asibiti before I bleed to death" girgizamai kai Ibrahima yayi yawani irin kwanto da kanshi yana kallon kwayar idanunshi dake bulbulo da hawaye yace "am not done with you, saura harshenka shizan yanka yanzu I don't want you to be able to ever speak again, banson ka kara iya magana a duniyan nan" wani irin girgizakai kai Arham yakeyi, tunda yake bai taba sanin akwai tashin hankali and torture irin wanan ba, kasama magana yayi sabida baison yabude baki ya yankamai harshe sai hawaye dakebin gefen idanunshi suna gangarawa kunnenshi, kama bakinshi Ibrahima yayi ya matsa yadau wuka yarike a hannu mutuwa ne kawai Arham baiyiba tsabagen tsoro yasake sakin kuka yace "dan girman Allah inhar kanason mahaifin ka ka tsaya ka sauraran Ibrahima karka kasheni dan Ya Rasulullahi" tsayawa Ibrahima yayi yana kallonshi Arham nawani irin kuka yace "dan girman Allah, dan darajan Allah nace kayakuri, kayakuri kamin rai, wlh natuba, bazan kara, wlh ko ahanyar anguwanku ka ganni nabaka dama kamin duk abinda kaga dama, kaga wlh wlh sanan inkaji nafadima wani abunda yafaru kayi gunduwa gunduwa dani wlh, amman dan girman Allah karka yankamin harshe I need to go to the hospital now please kataimakamin" wani irin kallo Ibrahima yamai sanan yanunamai wukan yace "Arham!!! Ka gujeni ko kamshi na kaji kabar wajen kawai, shine kawai maganan dazan fadimaka akaina kakiyaye ni" gyadamai kai Arham yayi da sauri yace "uhm na yarda na yarda, na rantse da Allah, amman ka taimakamin kamin rai yanzu ka kaini asibiti" kwanceshi tass Ibrahima yayi sanan yawani irin fincikeshi ko tausayinshi baijiba da kyar Arham ke tafiya amman yajashi har motarshi ya wurgashi cikin motar ya shiga ya kullo baima damu da ba kaya ajikinshi ba yaja motar har cikin gari lokacin dare yayi, agaban wani asibiti ya tsaya sanan yafito yabude kofa yawani irin fincikoshi ya wurgardashi tsirara agaban asibitin yakoma cikin motarshi yaja motar abinshi batare dayakara waiwayowa yama kalleshi ba yana murmushi. [11/27, 9:55 PM] saleemah: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣6️⃣ _Qatar_ Bayan 5hrs akayi discharging dinsu suka bayan Dr yamai kashaidi sosai akanta, karya kara takurata, kar a bari tai any aiki, sanan karya nemeta for now dan yabata 1month bedrest, sanan yasai magungunan da aka musu prescribing yakai mota yadawo dakin, kin bari tai tafiya da kanta yayi yadauketa chak kaman baby yay mota da ita, koda yasata a motan komawa baccinta tayi haka yazaga ya shiga yaja motar suka koma gida. Yana parking Ammi yafara gani a tsakar gidan, tana ganinshi takaraso wajen motar tace "meya sameta Waleed"? Tai maganan tana leka Widad din dake baccinta, wani irin makirin murmushi yama Ammi yazagaya batare dayay magana ba ta bangaren Widad din yadaukota chak sanan ya kalli Ammi dake binshi da kallo yace "zazzabi ne" yasake sakin murmushi yay flat dinshi da ita, chak Ammi ta tsaya tana binshi da kallo bata yarda da suspicious smile dayake mataba, hango takarda da ledan magungunan datayi cikin motar yasa taciro ta kalli takardan, wani irin sassanyar ajiyan zuciya ta sauke ta ijiye takardan da ledan takoma ciki abinta cikeda farin ciki. Lallabata aka dinga yi agidan koh tsinke ba'a bari ta dauka, gabaki daya batada lpy, mugun laulayi take bana wasaba har tausaya mata mata Ammi da Mom suke, Waleed na mugun kulada ita yana bata magunguna akan lokaci, murna gun Ammi ba'a magana, she was so over the moon, itada kanta takema Widad din abincin larabawa dan sun lura shi kadai take iyaci d'a a restaurant Waleed ke sayomata Ammi tahana ita ke dafamata da kanta kuma tanaci sosai, Mom kam sai nan-nan takeyi da ita kamar egg da'ake tararraya kar ya fashe Asma'u ma na manne da ita sai in Waleed ya shigone yake kadata. Around 8:30 nadare Waleed yayi sallama dakin tare da shiga dakin Ammi, hango Widad yayi kwance kan gadon Ammi tana wasa da wayan Ammi, Ammi kuma kan kujera tana aiki da system, tsayawa yayi yana kallonta kamar ya samu hoto dan bamata lurada shiba hankalinta gabaki daya yanakan game din datake bugawa, wani irin haske takarayi kan haskenta kaman tana shafa man haske, ga wani kyalli datake tayi fatarta na walwal, kirjinta sun ciko looking not so little kaman kirjinta nada, gyaran muryan da Ammi tayi yasa yadawo hayyacinshi da sauri yazauna kusada Ammi yabata side hug tareda daura kanshi kan wuyanta yana kallon abinda takeyi a system ahankali yace "Ammi why do I like this girl so much"? Batare da Ammi ta kallai ba tana aikinta tace "because she's your first love" murmushi yama Ammi ya girgixa mata kai tareda kara rikemata kafada da kyau yace "Ammi that's not all" yay dan shiru sanan yace "I think the reason why I love Saheeba is because she is special ne Ammi, and my heart connect to her, Ammi duk in ina tareda ita ko I feel full and contented, I feel peace, I feel calm, akwai this genuine happiness danakeji anytime am together with her, Ammi I love her" juyowa Ammi tayi ta kallai ahankali tai cupping fuskarshi, saikuma tamai peck akan sajenshi tace "I love her also, because yarona nasonta, and I wish you guys endless happiness Waleed" murmushi yayi ya kankame Ammi abinshi, juyowa Ammi tayi ta kalleta ganin tayi bacci yasa ta maida kanta kan aikin datake, murya chan kasa kaman wani maraya yace "Ammi kice ta tashi muje mu kwanta" chak Ammi ta mike jan hannunshi Ammi tafarayi haka ta jashi har suka bar dakin suka sauka kasan falo tai wajen kofa dashi sanan ta tsaya tace "kaga doctor yace she needs total bed rest saboda haka I will keep her with me saboda in bata total care kaji Son, tunda tai bacci adakina kawai katafi" turo baki yayi kamar yaro yace " toh Ammi idan tana guna ai bashi zai hana tasamu total rest din ba, besides nima ai Dr ne, gaskiya ni Ammi ki bani matata" yay maganan yana bubbuga kafa akasa cikin sigar shagwaba da iskanci, cikeda lallabawa dan tasan in Mom tajisu zuwa zatayi ta shigan mai yasa tace "haba son wai kai meyasa bakada kunya ne, nidai I have tell you my mind I'm keeping her with me har tai one month da Dr ya fada hoope I'm clear?" Gyada maata Kai kawai yayi ranshi duk abace yajuya yafice, juyawa Ammi tayi ta wuce dakinta abinta tana murmushi kawai da mamakin irin son da Waleed kema yarinyar nan, deep down she is scared for him, saisa kwanan nan ta tashi tsaye ta dage tanamai addu'a sabida batasan abinda zakai yadawo ba but she pray Allah karyasa yarinyar nan taguje shi bayan tadawo hayyacinta. Washegari, da safe suka hadu a dinning area, kowana zaune banda Widad da babu ita babu alamarta, juye juye Waleed ya dingayi yagan kota ina zata fito amma babu ita babu alamarta har lokacin, abinci aka faraci bandashi dako kallon wanda Ammi ta zubamai baiyiba kasa daurewa yayi yace "Ammi ina sabeeha ban ganta ba?" dagokai Ammi tayi ta kalleshi tace "tun asuba ta tashi tanata amai but na bata Lipton tasha ta koma barci ne" tashi yayi yace "Okay, lemme go check on her" baima jira amsansu ba yay staira straight dakin Ammi ya shiga ya ganta kwance ta kudundune akan bed tana barci tanata sauke numfashi sama sama, zama yayi akan gadon ya dan ja blanket din kasa farin fatarta ya bayyana mai kama dana jarirai, hannunshi yakai yataba wuyanta yana feeling tempreture dinta yaji it's mild, gyara mata blanket din yayi ya tashi ya fita dagakan gadon ya kashe wutan dakin yafita yasauka kasa ya tarar harsun gama breakfast kowa ya tashi, straight kitchen yayi dan yasan Mom na wajen yawuce yabude kofar ya shiga cikin big kitchen dinsu, zama yayi kan Island yawani langabar da fuskar kamar yaron dake nemar abu gun mamashi yace "Mom please kice ma Ammi ta bani mata na, wlhy zan iya kula da ita, beside I'm a doctor I won't do anything to hurt her, she is getting more sick awajen Ammi wlh, pls Mom now, tana dawowa wajena zata warke" ya karashe maganar kamar zaiyi kuka, hararanshi tayi ta mikamai bowl data cika da pepper soup da spoon aciki tace "common, gashi jekai breakfast, anyway naji Dan yarona zan mata magana don't worry kaji" ijiye howl din yayi ya sauko ya rungumeta tareda pecking dinta a kumatu kafin yadau bowl din ya fita ranshi fess yaja mata kofa.... Yana fita itama Mom tafito ta wuce wajen Ammi data samu a falo tana kokarin chanza channel tace "Sannu da kokori Adda" "yauwa liitle sis, kinga yanzun nan nakada Ma'u ta daman" dariya Mom tayi tace "ai abinda tafi iyawa kenan surutu", dariya sukayi dukansu sanan Mom tace "Ammi gaskiya ki bama Waleed matarshi saboda yaron nan ya shiga wani hali, this is the first time daya samu ciki nashi da kanshi so please let him take care of his wife and baby, he needs them, he need his wife close to him gaskiya, I don't think its the best ki kwace mishi Mata kinji Adda" Shuru Ammi tayi tana nazarin maganar Mom kafin daga bisani tayi naam da maganar Mom din ahankali tace "shikenan" Wucewa sukayi dakin Ammi tare suka tarad da ita ta fito daga toilet da alamun wanka tayi saboda tana daure da towel ne, da taimakon Mom ta shirya taci abinci sannan Mom tarike hannunta ta kaita har gaban part dinsu tace mata tashiga. Sai daMom tagan ta bude kofa tashiga ciki sannan ta juya ta koma part dinta. Tana shiga ta zauna akan gado dakin yayi wani irin dimm kamar ba mutum aciki, jin karar ruwa from the toilet yasa tagane Waleed nacikin bathroom din yana wanka, Hijab na jikinta tacire sanan tafara kokarin cire bra saboda she wasn't feeling too comfortable with it. Tayi unhooking din bra din kenan Waleed ya shigo cikin dakin naked babu komai ajikinshi sai karamin towel dayake goge gashin shi dashi, ganin mutum zaune yaasa yajuya da sauri thinking koh Ammi ce though basa shigowa dakinshi unexpected and Widad was the last person dayike expecting yagani dan yasan Ammi tarike ta kuma bai gane ita bace saboda yanda dakin yayi duhu. Wani irin murmushi tayi tatashi, tsayawa yayi chak shima yana kallonta, takowa tayi tazo gabanshi sanan takoma ta bayanshi ta rungumeshi ta baya hannunta daya akan kirjinshi daya kuma akan cikinshi, shafa mishi ciki ta dungayi kafin murya chan kasa tace "Cutest i miss you" sauke ajiyan zuciya yayi dukda ya gane itace tun yanda tazo ta rungumeshi tabaya. " I miss you more pretty" still bai juyo ba ita kuma bata daina shafa mishi ciki ba da hannunta, taana shafa mishi ciki tana gangarowa da hannunta har zuwa kasan maranshi, ta dauki kusan 2mint tana shafa maranshi kafin daga bisani tayi grabbing manhood dinshi dawani irin sauri tana wani irin shafawa itama tai kewan abin sosai. Juyowa a yayi da sauri ya fuskanceta ya capko bakinta ya fara kissing dinta tana maida mishi da martani, sai da suka gan tsayuwa na nemar ya gagaresu ya dauketa ya ajiyeta akan gado shima ya hau kan gadon, cire mata riga yayi ya fara squeezing nata all over kaman wani mahaukaci saikuma yafara bata head dukansu rudewa sukayi kaman ba sune akace suje 30days bed rest ba, groaning ta dinga saki saikuma tai releasing. Waleed was so hard, sucking dinshi itama tayi shima yasamu yayi releasing sanan yadauketa wanka Suka shiga kafin sufito subi lafiyar gado. ******** *Agurguje* Haka rayuwansu yaci gaba da tafiya kullum sai sun gamsar da juna but not through sex, abinda ya luradashi was kamar cikin ya samata balain son sex but still yana hana kanshi yi dukda cewa shima he wants her too bad wani zubin da kyar yake samin bacci, yau kamar kullum garin was so quiet suna kwance akan gado widad tafara mishi kukan rigima tana tura mishi boobs dinta abakinshi alamun ya sha, she has been doing that lately, bude baki yayi yadan lashi nipple dinta da tougue dinshi ihu tayi ta rikeshi gamgam kamar her who life depend on it fara sucking yayi tanawani malalacin ihu alamun tana enjoying every single moment dasuke sharring at the moment, tashi tayi ta hau kanshi, ta zauna kanshi kadan tayi tanaso tasa manhood dinshi acikin pussy dinta, riketa yayi da sauri yace "Baby Dr said you need to rest for a whole month I don't wanna injure u" turomai baki tayi tareda makemai kafada tace "but i want this now" kallonta yayi da idonshi daya fara kankancewa shima mugun sha'awa ke cinshi yace " it is not good for y o u r h e.." kasa karasawa yayi sanadiyar zama datayi tawani zauna akai tana washe hakora smiling, moving gaba tayi suka saki morn tare dukansu, grabbing ass dinta yayi yay helping nata Up and down tafara yi akanshi yana wani irin kara yana turamata, ganin baisamunta yanda yakeso gashi tana stressing kanta sai ya kwantar da ita yafara ramming dinta loosing control dan yamanta the last time dayasameta haka, takawo kusan sau uku amman baikawo ba fara tureshi tayi but ko kadan baimasan tanayi ba, wani irin ciwo kanta yadauka yana wani tafarfasa kaman anjona awuta hakan yasa tashiga tureshi da karfi but baimasan tanayiba, wani irin sarawa kanta yayi tasume at a spot. Saida yayi kusan sau 4kafin ya barta assume yana sauke ajiyan zuciya, kwanciya yayi gafenta yakai hannunshi yataba boobs dinta yaji shiru babu response yasa ya juyo yakalleta yagan idonta a kulle yake alamar kamar tana barci ne. Tashi yayi ya kunna wutan dakin ya ganta kwance still ko motsi batayi ba, da sauri ya taho inda take yayi tapping dinta no response. Kirjinshi ne ya wani bada dummmmm yabi kafafunta da kallo ganin ba blood yasa yajidan dama dama, sauka yayi dagakan gadon toilet ne ya shiga ya hada ruwa mai dumi yaje ya daukota yasaka ta aciki. Wanke Mata fuska yayi yaji tasaki ajiyar zuciya tana kokarin bude ido, kallonta ya dingayi harta gama bude idonta dukka ta saukeshi akan na Waleed daketa mata murmushi murya chan kasa yace "lazy gurl" Kallonshi takeyi kuri kamar maison tuna wani abu.....chan kuma tasauke °kanta tana kallon kanta dake cikin ruwa a bathtub naked ga namiji agabanta, hannu tasa ta rufe kirjinta dashi kafin tayi wani irin ihu cikin harshen larabci takwalama Aby kira tana ture hannun Waleed dake jikinta tana komawa baya. "Abyyyyyyy, Amaaahh". [11/27, 9:55 PM] saleemah: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣8️⃣ & 6️⃣9️⃣ Agaban dankareren gidan dayay girman wani kauyen security guards suka taresu ina zasu, saukar da glass down akayi Widad ta leko suna ganinta duk mutuwan tsaye sukayi sunma kasa kiran sunanta tsabagen shock itama haka sai kawai suka kwasa dagudu sukai ciki suka budemusu gate suka shiga ciki, suna shiga ciki kafinma motar tai parking tabude marfin motar ta diro kasa, wani irin ihu ta kwala. "Abyyyyyyy, Abyyyyyyy, Abyyyyyyy!!!!!" babu inda baya amsa muryanta agidan nasu. Kaman amafarki yana kwance kan katafaren gadonshi ga karin ruwan da akemai yay busy busu, gumunshi so scatterd ba kyan gani ga uban furfura yana sanye da farin jallabiya da rawani akanshi as usual, Amah nakusa dashi tana shafa kanshi itama takode sosai kaman ba itaba, daidai Umm tabude kofar dakin ta shigo rikeda madara a cup sabida yace madara zaisha sukaji muryan Widad dukansu, Aby dake bacci wani irin zabura yayi yana bude ido yace "Widad!" shafa kanshi Amah tayi tace "mafarki kayi amman nima naji mafarki dan naji muryanta wlh, ga madaran kanan ankawo" sake kwalamai kira Widad tayi baisan lokacin daya zabura ya sauka daga kan gadonba yana cisge karin ruwan hannunshi yay wajen window dakinshi dakenan arufe Amah biyeda shi, wani irin bude window glass din yayi sukai wani irin kara da saida suma su Waleed dake tsaye charko charko atsakar gidan suka dago kansu dan suga meyay kara haka, daidai Aby ya yaye labulen ya kallo tsakar gidan, hada ido yayi da yarshi tilo aduniya Widad tana sanye da bakar doguwan riga, yatsanta tasa ahankali tai pointing fuskar Aby dayamata tsufa sosai kaman bashiba bakinta har rawa yake tace "A........bb.....by" shima kasa magana yayi yace "Wi.....d...." ganin yakasa kiran sunan yasa yajuya dagudu yay hanyar kofa itama Widad takwasa dagudu tai flat dinsu Waleed yabita dan baison yanda take gudun nan karamin cikin dake barazanar fita gareta, a daidai stairs tahadu da Aby tsayawa tayi chak wasu irin hawaye na gangaromata tace "Aby" ahankali yace "Widad" dawani irin gudu tai wani uban tsalle ta dane jikinshi ta kankameshi tafashe dawani mahaukacin kuka daidai Amah tafito tana dogara sanda, tsabagen sauri turgudewa tayi zata fadi Waleed baisan lokacin dayabi ta gefen su ba yasa hannunshi tafado kanshi yatareta, tsabagen dadi rungume Waleed din tayi tamai kiss a kumatu sanan ta tashi ta rungume Aby da Widad dukansu atare Waleed ya tsaya yana kallonsu ajikin benen, wata mata yagani itama fara tana sanye da doguwan riga tafito fuskarta kini kini kaman zata mutu tana kallonsu Aby tazo tagabanshi tawuce bayanta ya kalla tana rikeda wata wuka, daidai takai wajensu ta daga wukan kenan Waleed yawani irin fizge hannunta tareda murdewa ihu Umm tayi da sauri su Aby da Amah da Widad suak juyo, cikeda masifa cikin harshen larabci Umm tace "barni na kashe wanan annobar yarinyar da sabida ita nakasa samin soyayya da kudin mijina hakama y'ata takasa samun both of them, I make sure nama Widad abinda zaisa bazata taba dawowa ba, ubanta bazai taba ganinta ba, amman ya akayi mayyar tadawo, su wayeku, ka sakenmun hannu" cikin harshen larabci Waleed yace "so you are the famous Umm" balle hannunta yayi ras wukar yafadi akasa itama tazube akasa tana ihu, ahankali Aby yaciro wayarshi babban police din garin takura duk suna tsaye ko 5min ba'ayiba polisawa suka cika gidan abunku da babban mutum yakirasu akazo aka dauki statement dinsu sanan akai gaba da Umm tana kuka, sai a lokacin aka dan natsu Aby yace a zazzauna sanan ma'aikatan gidan suka shiga sintirin kawo musu abinci da abubuwan kwalama Widad na manne da mahaifinta daya kira Family su Ahmad dan Ahmad har yar hauka saida yayi, kafin kace me Family su Ahmad sun shigo, tunda ya shigo Waleed ke kallon Ahmad din dake sanye da kayan larabawan idanunshi kurr kan Widad dake mai wani irin kallon tsantsan so, tashi tayi ahankali zata rungume shi wani irin tsawa Waleed yadaka mata dahar saida su Aby suka kallesu yace "don't hug him Widad!" chak ta tsaya tana kallonshi kaman yanda Ahmad shima ya tsaya yana kallonshi, tashi Waleed yayi kaman wanda yasoma tabuwa yaje har inda Widad din take azuciye yasa hannunshi yakamata sanan yajawota kusadashi yana kallon fuskar Ahmad din babu ko alamun tsoro ko kunya atattare dashi yace "she is my wife Ahmad" shima Ahmad cikin fushi da tsantsan kishi yace "Widad can never be your wife, nobody can become can husband other than me, koma zata auri wani Widad can never marry a man from a Different world daba namuba" cikin wani irin yanayi na jarumta Waleed yasakin mai murmushi yace "let's just say TWO DIFFERENT WORLD meet" cikin fushi sosai Ahmad yanuna mai yatsa cikin harshen turenci yace "DUNIYA BIYU MABANBANTA bazasu taba iya haduwa ba, kataba ganin inda ruwa da desert suka hadu? Ai ruwa daban ne hakama desert, ka yarda dani inna fadamaka mu LARABAWA BAMAYI DAWATA KABILAR" yatsa Waleed yanuna mai yace "ka rubuta ka ijiye daga kaina LARABAWA ZASU KOMAYI DA KOWACE KABILAR" Ahmad zai kara magana Widad ta fizge hannunta daga na Waleed takoma bangaren Ahmad sanan tanuna Waleed da yatsa cikin harshen turenci da ta lura shine yaren dasuke mata tace "listen Dr, your Mom told me you were the one that helped me kamin komi, and I am grateful karubuta mana konawa ka kashemin Aby zai biyaku, Ahmad is my husband, shinake so tun ina yarinya, and nothing and nobody can change that, tayaya kake tunanin zanma iya auren wani daga chan wata duniyar? That's not even possible, please stop calling me your wife, I don't know know and I can never be your wife" wani irin murmushi Ahmad yayi zaiyi magana Aby yadaka musu tsawa yace "quiet" shiru sukayi sanan yanuna ma kowa wajen zama, duk zama akayi sanan ya kalli Widad yace "Widad haka nabaki tarbiya? Irin tarbiyan dana miki kenan? Mutumin daya taimaka miki kikema wanan tijaran"? Saukar da kanta kasa tayi sanan Aby ya kalli Ahmad da kanshi ke kasa yace "Ahmad ko kunyan mu iyaye dake nan wajen bakayiba, kai mutum ne ai da yakamata kazama na farko dazaka godema bawan Allah nan daya taimaki Widad yadawo mana ita cikin koshin lafiya amman kake gayamai DUNIYA BIYU MABANBANTA basa aiki, inda basa aiki aida basune zasu dawo mana da Widad ba da saidai yan duniyan mu larabawa su taimaketa su dawo da ita" dan tsaki Aby yaja sanan ya kalli Uncle wanda ya lura shine babba sosai cikinsu yahade hannayenshi biyu yace "please tuba suke kuma yaranmu hakuri" murmushi Uncle yayi yace "bakomi" anatse Aby yace "kaman yanda kuka gani nine mahaifin Widad, wanan kuma Mahaifiyata ce, kakan Widad" ya nuna mahaifin Ahmad yace "wanan surukina ne kuma abokin kasuwan cina mahaifin Ahmad yaron da Widad zata aura" wani irin ajiyan zuciya Waleed yasauke da saida kowa ya kallai adakin, saikuma Aby yacigaba yace "ranan bikinsu ana gab da za'a daura aurensu aka nemi Widad aka rasa" shiru yayi kaman wanda ke tuna ranan sanan yay murmushi mai kama dana ciwo yace "anyway I don't want to remember wat happen that day, I dont want to remember wat I and my Mum went through dakowa namu it was terrible experience anyway Alhamdulillah, baya yawuce let's just face the present banda hakama Allah ya riga yatona asirinta, Allah kuma yataimaken ban maida komi nawa ma sunan yarta datai aureba yanzu haka Sabeeha na gidan mijinta suna Dubai ma tabishi yin wani aiki, komi yawuce, ko zaku iya sanar damu yakuka sami y'ata maisa danku ke kiranta da matar shi" wani irin zama Uncle ya gyara sanan yashiga basu labari tiryan tiryan kafin yagama tsaf yabude yar briefcase din hannunshi yaciro marriage certificate dinsu yabama Aby, sanan yakarake da "yanzu haka Widad na dauke da juna biyu na wata daya dayan kwanaki"! Shiru kakejin dakin kaman ruwa ya cinyesu. Iyayen Ahmad kasa ko motsi yayi, Ahmad idanunshi sukai ja dan wanan ake cewa murna da bakin ciki duka atare, ga murnan ganinta gakuma bakin cikin wanan bakin labarin dayakeji yanzu, Widad wani irin kuka tafashe dashi tafada jikin Amah tana kuka, shi karan kanshi Aby da takardan ke hannunshi na certificate kasa magana yayi, ahankali yace "aure ciki!" gabaki dayan labarin ya diran musu as a shock ne, ganin duk yanayin dasuke ciki yasa Uncle yay murmushi yace "Alhaji mudai yanzu zamu tafi zamu koma masaukin mu, zamu baku lokaci kuyi tunani dan bazan boyemaka ba daga danmu har yarku suna bala'in son junansu sosai, sai yanzu data farfado ne but kubata lokaci karku yanke hukunci da wuri barinma wanan babban rabo haka daya gitta tsakaninsu na ciki, kubarta ta dawo hayyacinta da kyau komi daya sameta bayan tai losing memory din yadawo mata tasan waye mijinta Waleed, tagane shi sarai kafin ta yanke hukunci" tashi dukansu sukayi suka sake gaggaisawa da Aby da iyayen Ahmad suka rakosu har tsakar gida suka shiga motocin su sanan suka tafi suka barsu cikin tsantsan tashin hankali. Koda suka kai gida, kasa komi Waleed yayi, after seeing her family and everthing he's so scared of losing her, yasan larabawa tun mahaifinshi nada rai suke yawan zuwa garuruwan larabawa saisama yadan iya larabci, one thing he knows about them shine basa bama wani yare yaransu, basa auren bare, yisu yisu suke aurensu, balle ma shi dayake daga wata duniya daban chan Nigeria tayaya DUNIYA BIYU MABANBANTA zasu hadu harsuyi tarayya irin ta aure dasu? Dafa shi Uncle yayi yace "trust me everything is gonna work out fine" gyadama Uncle kai yayi yadaga kai yana kallon yanda Ammi ke kallonshi, cool smile tasakinmai sanan tashiga kitchen. _Bayan kwana bakwai_ Yau satinsu daya chur kenan agarin amman haryau basu sake kiransu ba, basu kuma sake kiransu ba, ga Uncle yahana su zuwa sujira kiransu acewansu, wasa wasa Waleed har neman xarewa yake, gani yake kaman sun kwacemai matarshi kenan, baya iyacin abinci baya iya komi baida aiki saidai ya shige daki ya rungume kayanta. Yaudai kaman kullum ganin yana neman rasa gane kanshi yasa ya shirya tsaf, yafito compound mota, mota daya yadauka cikin motocin su direban yajashi har zuwa gidansu Widad, ana ganinsu ba'a hanasu shiga gidan ba, shigasukayi direba yay parking bude motar yayi ahankali yafito yay falonsu, da sallama ya shiga falon wanda Aby da Amah ne kadai cikinshi zaune Aby ya kishingida akan wata kujera yana cin inibi, kallo daya dukansu sukama Waleed suka ganeshi cikeda girmamawa ya gaidasu, amsawa sukayi dukansu atare sanan yasami waje yazauna kanshi akasa yay shiru, sunkai kusan minti goma ahaka sanan Amah cikin harshen turenci tace "kaga dan arziki, kaje sama daki na uku na bangaren haggu nanne dakin da Widad take ciki, tashi kaje" harwani irin ijiyan zuciya yasauke yay sama da sauri yatafi. Kallon Amah Aby yayi, girgizamai kai Amah tayi tace "Son kai shaida ne kafi kowa sanin yanda nakeson Widad da Ahmad, kasan yanda nake matukar son Ahmad amman abu daya nakeso kagane wlh kaddaran haduwa da wanan yaron, sanan dakuma cikin dake jikinta ne yakai Widad Nigeria, shifa matar mutum kabarinsa, duk inda matarka ko mijinka yake ko asararin samaniya yake sai Allah yakaddaro yanda zaku hadu ayi aure, kaga na tsufa yarona, lokaci shike bayyana komi, ayanzu nayi girma nasan abubuwan dakai har yanzu bakakai matakin saniba, mubar kallon ala'danmu dama komi, nasan za'ayi magana but suyi magana bata kari, nasan za'ai cece kuce, duk suyi, inhar Widad tabude baki, aduk randa yarinyar nan tabude baki tace tanason yaran nan bashi ita zanyi tabi mijinta su tafi kalli yanda yaron ke sonta, jibi yanda yadawo, mudena tunanin komi muyi tunanin yarmu kawai anan, Ahmad zai iya hakuri ba matarshi bace, inda matarshi ce da a ranan da an daura aurensu kodako ba'a ganta dinma, amman inda zaka gane hikiman Allah shida kanshi ya furta adakatar da komi na auren anemi Widad tukunna katuna" shiru Aby yayi yana kallonta duk baice komiba, sanda Amah ta dauka tace "kaga tashi karakani na tattaka kafafu wana sunyi tsami" tashi Aby yayi batare dayay gardamaba yarike ta suka fita daga dakin sukai wajen gidan gabaki daya suna hira, kullum saiya fitar da ita haka dan ance tadan dinga wasa kafafun nata. Ahankali yabude daki na ukun da Amah tafadimai wani asirtaccen kamshi ya daki dodon hancinshi, dakine mai kyawun gaske dayasha carpet tako'in, maida kofar yayi ahankali yarufe yana kallon ko'ina ganin bai gantaba, kakarin amai dayaji abayi yasa yay kofar daya kyautata zaton bayine da sauri yasa hannu yabude bayin ya shiga, ganinta yayi tsaye gaban wash hand basin tarike cikinta tana kwara uban mai daidai ya shiga kuma tai luuuu kiri ya debeta, tareta yayi dawani irin sauri yasata ajikinshi ya rungumeta tsam tsam murya chan kasa yace "I gat you Pretty, I gat u ok" lamo tayi ajikinshi tana kara chusa kanta cikin kirjinshi hakanan taji for a while bataji wani abu dake kwantar mata da zuciya ba, but wanan turaren nashi yasa taji wani irin natsuwa ya shigeta, tashin da zuciyanta kemata na kwanciya, gabaki daya taji aman ma ya tsaya hakan yasa ya shige jikinshi sosai, sunkai kusan 10min ahaka atsaye abayin rungume da ita sanan murya chan kasa yana fito da ita daga jikinshi yace "zoki wanke bakinki" ahankali tadan kalli fuskarshi da shanyayyun idanunta kasa cemai komi tayi dan batada karfi ko kadan, ruwa yadena yakai bakinta, kadan tadeba ta kuskura baki ta zubar shikuma ya wanke mata fuska, zata fara tafiya tafita kawai jitayi yadauketa, abin ya mugun bata mamaki baima lura da yanda take kallonshi ba yabude kofar bayin suka fito, akan gadonta ya zaunar da ita, sanan yabude ledan magungunan daya bayar na shanta ne dan jikinta na zafi gani yayi duka batasha, juyawa yayi yanabin ko'ina da kallo ganin babu ruwa yasa yay hanyar fita daga dakin tasake binshi da kallo, ko 1min baiyiba ya shigo dauke da bottle water yazo kanta yabude ruwan yamika mata dudda so take tahana kanta amsa kasawa tayi tasa hannu ahankali takarba, shima cikeda tattausan murya yace "mesa bakishan magungunan ki eh? Idan bakisha haka zakiyita ciwo, please you need to be taking your drugs kinji" yay maganan yana mika mata kwayoyin maganin, karba tayi ta watsa abaki sanan ta korada ruwa, karban ruwan yayi yarufe ya ijiye sanan ahankali yazauna gefenta yana kallonta, sai yanzu ma yalura da kayan jikinta, doguwan rigane irin na indiyawa a jikinta orange, kanta babu dan kwali sai gashinta dayaga yanata sheki, sosai yake wani irin kallonta kaman yau yafara ganinta, kirjinta sun ciko kaman yakai hannunshi yatabasu sai wani shining take, dan gyara zama yayi yana hana kanshi samun erection din dayake shirin samu sanan ahankali yamika hannunshi yadaura kan hannunta dake ijiye kan cinyarta hakan yasa tadago kanta ta kallai, shima kallonta yake da shanyayyun idanunshi, murya chan cikin harshen turenci yana kara damke hannayenta yace "Wife, Widad, I know you are going through alot right now, nasani, nasan is not easy ki farka kiga wasu mutane daban arayuwanki sanan kiga kinyi aure, sanan kiganki dauke da ciki, I know is not easy, nasan al'adunku baku auren bare, auren bare kaman wani abune na tir dakuma nunawa ana maganganu akai, nasan bakisan komi tattare da duniyan danake ba, al'adunmu dakomi, but I believe the two of us can make a difference, zamu iya chanza perspective din kowa, let's create the road for others wayanda sukeson wasu daba yan garinsu ba" yaydan shiru yana kallonta kaman yanda take kallonshi da idanuwanta dake neman kwancemai kai, murya chan kasa yace "I don't wanna say this but.....bu.....t, I have to" yay dan shiru sanan ahankali yace "am afraid of loosing you, wlh I am so afraid of loosing you, I love you Widad, I love you beyond words and sentence, I love you with all my heart, please karkisa arabamu give me the chance to show you how strong my love for you is kinji Pretty" yay maganan ahankali yanakai fuskarshi kan nata yana goga mata soft sajenshi akan kumatunta, wani irin tashi tsigan jikinta yayi tawani irin sauke ijiyan zuciya tana lumshe ido, ganin yanda ta lumshe ido batare data hanashi ba yasa yasakinma kumatunta soft kiss da saida yaji yanda ta sauke numfashi, ahankali yakai bakinshi daidai saitin nata yana kallon closed eyes dinta yace "I love you Baby and I miss you badly" gently yay grabbing lips dinta yashiga kissing dinta anatse dake penetrating every organ na jikinta. "Widad"! Bude idonta da fizge bakinta tayi da sauri jin yanda Ahmad yakirata azafaffe ta kalli kofa kaman yanda Waleed ya kalli kofan, Ahmad ne tsaye a daidai kofan idanunshi sunyi ja da hannu ya nunata cikin harshen larabci yace "nazo inata knocking babu wanda ya amsani ashe abinda kikeyi da yaron nan kenan?" yanuna Waleed, yace "duk yanda muke baki taba barina na shigo dakin ki ba but wanan kin barshi, ni zaki yaudara"? Juyawa Ahmad yayi azuciye da sauri ta tashi zata bishi Waleed yarike mata hannu amugun zuciye, juyowa tayi ta kalleshi da idanunta dahar sunyi ja tace "kasaken" cikin wata irin dark voice yace "da aurena akanki bazan taba bari kije kina chasing another man ba kinyi kadan woman" yanda yamata maganan ita kanta saida gabanta yafadi kaman wani angry lion, cikin fushi da shegen tsiwa tace "stop calling me your wife, I will never marry a black African ba, Nigerian man ma Allah kyauta, and lemme tell you bazaka taba iya shigowa tsakanin soyayyata data Ahmad ba wlh cus he is the only man danake so and zan cigaba daso har karshen rayuwata, cikinka dakace yana jikina am is either kacire kayanka katafi dashi daman ance kai Dr ne kokuma ka zubarmin dashi, but don't ever call me your wife, am no way your class nor am I gonna marry a black African like you I am an Arab Man's wife" ta fizge hannunta tai kofa, ayanda zuciyan Waleed ke tafarfasa ko dukane yace zai mata zai iya kasheta daidai tasa hannu zata bude kofa yawani irin fizgota jikinshi tareda saka hannu ya murza key ajikin kofan, yace "bari na tabbatar miki da you are my wife, and you are not an Arab Man's wife rather you are a black African, Nigerian Man's Wife Widad"! Yay maganan ranshi abace yaja zip din bayan riganta kasa, wani irin rudewa tayi jin hannun namiji ajikinta tace "don't touch me, wat are you doing I said don't touch me wlh, zan kiramaka Aby" cikin fushi yace "yes please call them lady, nima inason ki kirasu let them hear our groan while we make love" fashewa da kuka tayi sosai ganin yaja riganta kasa daga ita sai dan pant da vest farare, tace "subhanallah pls stop touching me I will never talk to you rudely again am sorry, I didn't mean all wat I said wlh" wani irin wurgata kan gado yayi yafada kanta yace "you meant them all, and I meant mine nima" yay maganan yanajan pant dinta kasa, shimin jikinta barkeshi yayi boobs dinta suka bayyana, hannayenta takai zata rufesu ya kabar yakai bakinshi kan boobs din hannunshi akan dayan yana murzawa yana sha, wani irin abu taji da in her whole life bata tabaji ba tureshi ta shigayi da duka karfinta kafafuwanta nawani irin rawa jin yanda yakesha mata boobs dake neman sata ta zare, she has never experience this kaman zata suma takeji, gabaki dayan jikinta mutuwa yayi ta runtse idanunta gam tanajinshi jikinta nawani irin jin dadi tanaso ta kankameshi but kunyan yi take, saida yaga jikinta ya mutu lakas sanan yamaida fuskarshi daidai saitin kunnenta yana kara bude kafafuwanta yana karanto addu'an saduwa da ita, ahankali ya kazo kunnenta yana tura joystick dinshi in her wall yace "how do you feel me sweet right" kiss yasakin mata yace "I tot u wanted to call Aby, call him" dan cizo yasakin mata awuya da saida taji kaman fitsari yazubo mata ta kankameshi da saurinta tace "please karkamin komi my virginity is for Ahmad please, I don't know which magic kamin dayasa nakasa ihu but please karkamin komi" wani irin murmushi yasaki yace "there's no magic baby, tsabagen dadi nane yasa kika kasa ihu" kissing wuyanta yake yana tsotsan ko'ina that got her to be dripping wet tai fasha fasha da gadon, murya chan kasa yace "virginity wanan ai tun a naija na karba bakiga har ciki na dura mikiba, babu wanda ya isa yarabamu the more you try to go to Ahmad the more I keep hurting him and show him that I possess you" yay maganan yana danna joystick dinshi cikinta da bala'in karfi saida tasaki ihu ta kankameshi jikinta nawani irin rawa tasaki kuka sosai, murya chan kasa yace "wat is it"? Cikeda kuka tana rirrike dashi tace "it hurts" Gydamata kai yayi yace "yes am going to punish you for telling me your husband cewa kinason wani" yay maganan yana zaro joystick din waje gabaki daya sanan yakoma ciki dawani irin mahaukacin kafirin gudu, ihu tayi da duka karfinta dan har mahaifinta tajishi, murmushi yayi ko darr bayaji aranshi haka yakeso yasata kuka da ihu to the extend sai anbashi matarshi su tafi inba hakaba saiya mayar musu da gidan nan sex house wlh, he will show them the Nigerian man in him. Wani irin rawa jikinta yakeyi bata tabajin abu hakaba ya shigeta barinma da gudun nan saita farajin zafin shigan saikuma taji dadi kaman zata mutu she cannot hold it, fashewa da kuka sosai tayi ta rirrikeshi tace "please stop kaman zan sume" "suman dadi, your husband is huge and long, thick and a good fucker, I know your mumu corner in this hole, ina buga wajen baki lasting kike kawowa bari na nuna miki kiga" zarowa duka waje yayi, sanan yadaga kafafunta sama wajen kanta yakai joystick dn gaban hole din ya shigeta ramming side din damanta kaman zai bulata, wani irin ihu tayi saiga ruwa kaman fitsari chaaaaa, fashewa da dariya yayi itakuma tasaki kuka sosai tace "kaga kasa nai fitsari wlh bana fitsarin kwance" murmushi yayi yace "this is squirt not pis, I told you daman if I screw you that way baki lasting, and I need you to last danzan karbi wanda zaimin a week" ya saukar da kafafunta tana kokarin tashi ya danneta ya shigeta da karfi, zata iya cewa mutuwa ne kawai batayi ba at a point bama tasan metake cewaba, wani irin bad mugunta yamata dabai taba mataba ihun dayasa tayi saida yakusan fara gidan, saida yaga ko yatsanta bata iya dagawa yanuna mata what a black African Nigerian Man can do sanan yadagata yawuce bayinta wanka yayi yafito daure da pink towel dinta kallo daya tamai ta lumshe ido hawaye na gangaro mata, shiryawa yayi tsaf batare daya taimaka mataba danso yake su tarar da ita ahaka, ya yarda towel din akasa yataho har gabanta kiss yama lips dinta yace "ko labari kibari naji akan kin kula wani Ahmad kina matata, wanan kadan ne saina bulaki wlh, lazy gurl, I love you" yasake manna mata kiss sanan yawuce yafita abinshi ko ajikinshi yarufo mata kofa, yana fita ya sauka kasa, babu kowa a falo, atsakar gida yaga su Aby da Ahmad da Amah, ga mamakin shi koda yaje musu sallama yaga sun kasa hada ido dashi murmushi yayi aranshi yace "ko bakuma Allah saikun bani matata wlh" sanan yawuce ya shiga motar su ko kallon Ahmad baiyi ba dan bai isheshi kalloba he just show him Widad matarshi ce danya tabbatar sunji ihunta wlh dukansu haka suka bar gidan ranshi fess. Ina masu neman turare exotic ones, masu mugayen dadi, masu kama daki, masu dadi, da armashi, long lasting turaren gargajiya gashi sanyi yazo, Awwaba Scent got you covered, kayanta akwai sauki, tana delivery ko'ina, me kuka jira ne wai? 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Just chat her up kuga abun mamaki ga number tanan https://wa.me/+2348034236800 [11/27, 9:55 PM] saleemah: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 6️⃣7️⃣ "Abyyyyyyy, Amaaahh" tasake kwalamusu kira da duka muryanta tana kara nitsar da jikinta cikin ruwa ganin namiji agabanta yana kallonta haka, ganin situation dinta yasa yagane she just recall her past, hannu yadaga zai mata magana cikin tattausan murya yace "calm down le......" ihu tamai hawaye na gangarowa daga idanunta tace "man ant? Who are you"? Shiru yayi yama kasa amsata jin clearly larabci tamai bama turenci ba, cikeda tashin hankali tana kalle kallen bayin tace "aina ana? Wa aina walidaiyna? Ina nake ina iyayena suke"? Tasake wurgomai larabci, hannu yadaga mata yace "listen Saheeba I....." da sauri tace "Saheeba? Ismy Widad! Widad bin Othman Benjelloun" anatse yace "alright Calm down Widad, finish bathi....." da sauri batare data bari ya gama maganarshi ba tana kuka sosai tace "khuzni ilaa Waliday, ka kaini wajen iyayena" Allah ne kawai yasa yadan iya larabci dabaisan tayaya zai dinga jintaba gyadamata kai yayi yace "okay I will but stop crying ki gama wanka kufito muj....." dawani irin sauri kaman wacce ta tuna abu tace "Ah.....Ah...Ahmad, aina Habiby Ahmad, zaujy Ahmad" wani irin mummunan faduwa gabanshi yayi yamata wani irin kallo saikawai yatashi dawani irin gudu ta runtse idanunta gamgam ganin namiji agabanta tsirara saida taji yafita daga bayin sanan tabude idanunta ahankali, tashi tayi da sauri daga cikin ruwan tafito wani iri luuu taji tayi ko kadan batada karfi kaman zata fadi da sauri ta dafa bango ta tsaya tana sauke ijiyan zuciya, takai kusan 2min ahaka sanan ta iya mika hannu tazari towel tadaura tafito tana tafiya ahankali ahankali tana kallon ko'ina jikinta har rawa yake, ganin babu kowa adakin yasa tai wajen wardrobe budewa tayi ta shiga nema neman kaya, wani jallabiya datagani na larabawa baki ta zaro ta shirya tsaf cikinshi sanan ta nannada gyalen tasaka takalmanta da sauri bata tsaya neman komiba tai wajen kofa tafito da saurinta kaman zata tashi sama, su Ammi tagani a falo da Waleed daya sanya jeans da t-shirt, tsabagen tashin hankali ko boturan rigan yakasa rufewa sun tsaya charko charko, gani tafito daga bedroom dinsu yasa duk suka bita da kallo, kallo daya tamusu tadauke kai ganin bakaken fata da batasan meya hadata dasuba, hanyar kofar falon tayi da mugun saurinta tana kaiwa tafice ta kwasa da gudu tai Gate, da gudu shima Waleed yabita daidai gate yacinmata riketa yayi ta kwakusa wani irin bala'in ihu tana kwalama Babanta kira. "Abyyyyyyy, Abyyyyyyy, Abyyyyyyy" ta shiga dukan hannun Waleed dake jikinta alamun yasaketa, girgiza mata kai Waleed yayi yace "please Saheeba listen to me dan Allah, is me your Waleed, am not gonna hurt you stop being scared kinji Saheeba" tureshi tayi ta bubbuge hannayenshi looking at his face cikeda tsana irin yanda yake tabata dinan tace "don't touch me, stop touching me, and my name is Widad am not Saheeba, stop calling me Saheeba" tafashe da kuka sosai tana goge fuskarshi da gyalen data nannade cikin harshen larabci tace "menakeyi anan? Meneke yi daku? Is it all part of Umm's plan, I want to see my father and my grandmother" ganin yanda take kuka and Waleed is not in anyway helping the matters yasa Ammi ta tako wajen har kusada ita hannun Widad din takama tarike ahankali tace "Widad I know you understand English so I want you to listen to me please daughter" tsaigaita kukanta tayi tana kallon Ammi, ahankali Ammi tace "muje ciki mu zauna saimunyi magana ba anan gaban gateba" girgizama Ammi kai tayi tace "ni wajen Aby zani" tasake fashewa da kuka sosai, tausayinta Ammi taji tama kasa magana tadaga kai takalli Waleed da idanunshi harsunyi jajir yana kallonta hankalin shi tashe, tausayi shima yabata sosai duk abinnan tai tunani lokacin daya kawomata zancen zai aureta, da ace tahanashi da yanzu yana ganin bakinta yace tahanashi auren wanda yakeso hakama auren farkonshi tahadashi da wanda bayaso saisa ta barshi, ijiyan zuciya ta sauke tace "listen Widad, nasan bakisan muba amman one thing I can assure you is that I can never hurt you so now kizo muje daki kifada mana koke wacece sanan daga ina kike sanan muzo musan yanda zamuyi mu maidake wajen iyayenki dan munsan suma suna nemanki sabida kinfi shekara daya damu a Nigeria, muje ciki" ganin yanda yarinyar take dar dar dasu yasa takai hannunta tarike mata hannu sukai hanyar babban falo, zaunar da ita kan kujera Ammi tayi sanan kowa ya zauna, anatse Ammi tace "now I need you to calm down kidena kukan nan, we are ready to help you zamu kaiki wajen iyayenki" anatse itama Widad takai hannu ta share hawayenta tace "where is this place, how do I end up in Nigeria?" anatse Ammi ta nuna mata Waleed dake kallonta har lokacin idanunshi sunyi ja, kallo daya tamai tadauke kanta da sauri danta ganeshi shine wanda tagani abayi dazu tareda ita tsirara, ahankali Ammi tace "that's my son, Dr Waleed Warbai, yanada babban orphanage a Zaria, acikin wani jirgi aka kawoki garin nan aka jefar dake a ruwa, a ruwa aka tsinkeci aka kaiki gidan marayun d'ana dan yanada Big orphanage, he took you in sabida yanda kanki ke bleeding saida yamiki aiki akai, at first wasu irin behaviour kike abnormal ones sabida fluid din dake cikin kanki sai daga baya kuma kikazo kika dena har akai auren......" girgiza matakai Waleed yayi alamun karta fadi mata tsallake wajen Ammi tai nandai tabata labarin komi dayasa meta tas tas harda abinda yasa Waleed bai bada sanarwanta ba sabida karyazo koma waye yaso kasheta yadawo ya kasheta, kasa dena kuka tayi ahankali Ammi tace "kinsan waye keson kasheki, me kika tuna last na past life dinki"? Cikin wani irin muryan kuka tace "abinda natuna?" gyadamata kai Ammi tayi, shiru tayi kaman mai tunani sanan tace "ranan aurena da Ahmad komi yafaru" ba Waleed kadaiba kowa nadakin saida gabanshi ya Yanke yafadi, tacigaba. "Allah kadai yasan wani hali mijina yake ciki, kunce nayi morethan a year tareda ku anan, omg Ahmad, Aby da Amah must be super worried" tai maganan ahankali tana fashewa dawani irin kuka, Ammi bata hanata ba dan itama yanzu kukan takeso tama danta jin Widad nada miji wanan wani irin tashin hankali ne, takai kusan 5min tana kuka sanan tai shiru tace "sunana Widad Bint Othman Benjelloun, ni haifaffiyar yar Morroco ce, iyayena komi nawa daga chan ne, ina karatun mass com a Egypt ina shekarata na biyu agarin nema na iya wanan yaren nasaran dakukaji ina muku magana dashi, Mahaifiyata tarasu" taidan shiru tareda share hawayen dasuka zubomata sanan tace "cancer yakasheta, ni kadai mahaifina ya haifa step Mom dina Umm bata sona, ranan aurena bansan maiya faruba nadai farka naganni cikin wani jirgin awani daji......." nan tabasu duka labarin abinda yafaru sanan tace "yanzu I need to see Aby ku kaini wajenshi I need to tell him abinda Umm tamin karshima ta kasheshi sabida Umm is just after dukiyan Aby, please ku kaini gida yanzu" shiru Ammi tayisanan tanisa tace "Widad muba yan kasar morroco bane, koda yanzu zamuje garin dole muyi yan shirye shiryen takardun shiga kasar, bankuma son ki kira mahaifinki matarnan zata iyaji tayi wani mummunan abu in taji kina raye, gwara muje abazata saidai kawai ta ganmu, yanzu kiyi hakuri kibamu nanda kwana biyu zuwa uku muyi yan takardu sanan saimu dunguma mu maidake gidanku kinji" ahankali tace "to mijina fa shina kirashi Ahmad can keep secret inaso hankalinshi ya kwanta" wani irin tari Waleed ya shigayi da sauri Ammi ta tashi dagakan kujeran daga ita harsu Mom sukai kanshi, tari yake sosai Ammi batasan lokacin data saki salati ba. "Innalillahi wa innailaihi raji'un, innalillahi wa innailaihi raji'un, kai Waleed sha ruwa" aka kai ruwan da Abdul yadauko bakinshi amman kaman bashi ake bamawa ba sumewa kayi yayi warwas ya sandare awajen, haukane kawai Ammi batayiba da sauri Mom tarike Ammi tace "Adda ki kwantar da hankalinki dan Allah" cikin wani irin yanayi na kaman wacce ta zare Ammi tace "wlh in Waleed yarasa yarinyar nan mutuwa zaiyi mutuwa zaiyi" kallon Abdul Mom tayi tace "daukeshi mukai mota" ta kalli Ammi tace "ke ki zauna da ita kinsan itamaba lfy gareta ba, ki kira Babanshi(Uncle) yazo asan me ake ciki, Asma'u zauna dasu kema" gyadamata kai tayi suka dauki Waleed itada Abdul sukafitada shi sai mota Widad na binsu da kallo tana zaune inda take dan ba gane hausar dasukeyi takeba, zama Ammi tayi ta kalli Asma'u tace "kawomin wayata Ma'u" wayar Ma'u takawo tabama Ammi kira daya Uncle yadauka Ammi ta shiga sanar dashi abinda ke faruwa, shi yamafi Ammi rudewa da sauri yace kwantar da hankalin ki gani nan zuwa, am leaving office yanzun nan duk jirgin danasamu binshi zanyi ya katse wayan ya tashi xumbur. Itama Widad din zazzabi ne yarufeta tadinga amai da kyar Ammi da Asma'u suka samu bacci ya Kwasheta bayan tasha magungunan ta, Mom takirasu tacema Ammi jikin Waleed da sauki dukdan hankalinta ya kwanta nanko har lokacin bai farfado ba. Ahankali Waleed ke bude idanunshi dasukamai nauyi sama sama yaji ana kiran sunanshi "Waleed, Son, Son an you hear me" karasa bude idanunshi tass yayi ya saukesu kan Uncle dake zaune yana sanye da kayan wajen aiki, Waleed na ganinshi ya zabura zai tashi Uncle ya taimaka mai yazauna, Uncle yace "why will you kill yourself kan mace eh? Zuciyarka fa chak tsayawa tayi ta dena bugawa dasu Mom dinka basu kawoka asibiti dawuri ba daka mutu, listen boy ko yarinyar nan nada aure namaka alkawari saitadawo taka, sai inda karfina yakare wlh, ina mahaifinka inhar ban iya nabaka abinda kakeso ba after all you've went through Waleed in this life yaudaran mata da aboki me amfanina? Are you ready cus we are flying to morroco yau dinan da daddare" hannun Uncle yarike ahankali murya chan kasa kaman wani dan yaro yace "Uncle am scared, I've never been scared in my life like this, am afraid of losing the love of my life, banso muje morroco Uncle let's just go back to Nigeria zata hakura tazauna dani, in mukaje morroco shikenan narasata har abada wlh Uncle zan mutu, Dad I, I, I love Saheeba beyond much" sosai Uncle yaji jikinshi yamai sanyi, kamashi yayi ya sumbaci goshinshi yace "inhar ina tare dakai aduniyan nan don't ever be scared or afraid of anything, do you trust me Waleed?" gyadama Uncle kai yayi, ahankali Uncle yace "inhar you trust me then trust in me idan nace babu wanda ya isa yarabaka da matarka aduniyan nan kosu wayesu, let's so, duk su Mom nakadasu gida, stand up" daga Waleed din yayi yarikoshi suka fito dan already yariga yay clearing all bills sanan ya shigar dashi mota yaja motar har gida, lokacin yamma tayi, har dakinsu yakaishi yazauna yajirashi yay wanka sanan yafito mishi da kaya masu kyau ya saka ya feshe shi da turare sanan yajawo box dinshi yabude ganin marriage certificate dinsu aciki yasa hankalinshi ya kwanta ya shirya musu komi sanan yafito yasashi a kota dansu Mom na airport already, airport suka tafi private jet yamusu booking yana zuwa akai komi jirginsu yatashi sai satan kallon Widad yake da tunda yashigo jirgin daidai daso daya bata dago kanta ta kallai ba dudda taji anata gaisheahi ana mai yajiki, yanda gabanshi ke faduwa yasa Uncle yashafa kanshi yace "calm down, inhar yarinyar nan tasoka da yanzu ma zata soka it will only take time, what goes around comes around remember this" gyadama Uncle kai yayi haka uncle yadinga kwantar mai da hankali har jirginsu yasauka a airport din morroco karfe shidan safe. Uncle yariga yay handling accommodation dinsu dan babban gida ya kama musu a casablanca yanaso su dira gidan as manyan mutane dan ba raini, ana kiramai sunan mahaifin Widad din yasanshi dan shi yana dealing da manyan mutane a business, gidan suka fara zuwa dudda saida Widad tadinga musu kukan bala'i amman duk aka shareta, abinci akaci itama taci, sanan kowa yashiga wanka akayo shiga ta alfarma, Waleed baiso ya shirya amman saida Uncle yasa ya shirya cikin wasu fitinannun native na gizna white, ance duk inda zaka represent your culture, hausawa suka taimaki yarsu, sanan hausawa suka auri yarsu dan haka a hausawan su zasu shiga gidan larabawan wanan ake kira da TWO DIFFERENT WORLD wato DUNIYA MABANBANTA wanda ayau zasu hadu, shima Uncle sky-blue shadda yasaka yakafa hula, yadaura rolex agogo kaman yanda Waleed ma ya daura, Abdul ma haka, Ammi da Mom sukai shiga ta lace da zinarai daya bala'in amsansu, itakuma Asma'u ta shirya cikin atampa riga da sket ma codivore dayay mata kyau, ita kanta Widad dataki tai gayu binsu kawai da kallo take bata taba ganin wanan irin shigan ba amman sun mata kyau sosai dan is obvious takasa dena kallonsu duka, motocin da Uncle yamusu haya na company gidan dasuka kamane jeeps guda uku bakake suka iso, fita duk sukayi suka shiga motar da Widad keciki ne agaba danta nuna hanya aka dauki hanyar Mansion din gidan Othman Benjelloun. Ina masu neman turare exotic ones, masu mugayen dadi, masu kama daki, masu dadi, da armashi, long lasting turaren gargajiya gashi sanyi yazo, Awwaba Scent got you covered, kayanta akwai sauki, tana delivery ko'ina, me kuka jira ne wai? 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Just chat her up kuga abun mamaki ga number tanan https://wa.me/+2348034236800 [11/27, 9:56 PM] saleemah: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR 7️⃣0️⃣ Kasa koda motsi Widad tayi dagakan gadon, jitayi kaman yadauke duka mugun zazzabin dayake cinta tunda tazo gidan, babu abinda ke mata ciwo yanzu sai jikinta dataji yamata mugun tsami, hannu tasa ta share hawayen da suka zubomata yanzun shikenan she's this man's wife not Ahmad, jiba yanda yay having dinta in her father's house, takai kusan minti 20 kuka take akan gadon, da kyar ta lallaba ta tashi zaune, lallabawa tayi da rarrafe ta shiga bayi da ruwa mai zafin gaske tai wanka sanan taji wani irin karfi tadauro wani towel batare data kalli pink dinta daya daura dazuba tafito zanin gadon dasuka bata tacire takai bayi ta saka a washing machine tadawo tafito dawani ta shimfida ta tattare ko'ina da kyar ta iya tanemo wani simple gown tasaka sanan tadawo ta kwanta akan gadon, kamshin turaren shi datake mugun sone taji yana shiga hancinta juye juye ta shigayi kafin tagano daga filon daya daura kanshi ne takejin kamshin taja ta rungume tsamtsam ajikinta tana tunani, lumshe ido tayi tana ganin image dinta dashi suna dariya tana rungume shi duk a Nigeria, yatsine fuska tayi tacigaba da tunanin ahaka bacci yay awon gaba da ita, har dare yayi Aby dashi kanshi baya iya bacci in baizo yadubata ba yau kasa zuwa yayi hakama Amah haka kowa yay bacci ita takasa zuwa wajen su suma haka, washe gari ma haka tawuni adaki tana rungume da filon Waleed tana shakan kamshin shi deep down haka takeji kaman yazo yauma tasake ganinshi, tana zaune taji Ahmad yazo amman still takasa fita taganshi wasa wasa yau kwana uku kenan batabar dakin nanba. Tana zaune yauma kaman kullum akai knocking kofar dakin, anatse yay magana yace "is Ahmad, I come to talk to you" hakanan taji gabanta yafadi, hakanan kuma taji ta tuna kashaidin da Waleed yamata kan Ahmad ranan nan, kasa magana tayi tai shiru kaman batajishi ba, jin an murza hannun kofa yasa ta tashi da sauri zatai bayi daidai Ahmad ya shigo dakin, murya chan kasa yace "Widad" chak ta tsaya batare data juyoba, ahankali yace "you don't have to go to the toilet ki boye dan kawai bakison ki ganni, today is the fourth day nake zuwa nai knocking kimin shiru kiki amsani I simply come to talk kidawo ki zauna akan gadon ki please" yanda taji muryanshi yay rauni yasa tajuyo ta kalleshi gyadamata kai yayi yanuna mata kan gadon, dawowa tayi ahankali ta zauna kan gadon shikuma yaja kujeran gaban madubin kwalliyanta yazauna agaban gadon yana facing dinta. Anatse yafara magana yace "Widad me and you have come a very very long way, tunba yauba kinsha fadi cewa no one understands you better than I do, kinsha fadi da bakinki cewan kafinma ki furta abu nakan fahimci abinda kikeso kafinma kifadi kintuna"? yaymaganan yana murmushi, gyadamai kai tayi ahankali, dan ajiyan zuciya yasauke yace "na zauna nai tunani mai tsawo, sanan na azumimci ranaku uku duk akanki ina rokon Allah should guide me to the right path which I believe shine abinda yayi dahar yasa nasami courage nazoma da iyayenki da maganan nan kafin ma nazo miki nan da ita" yasakeyin shiru sanan yace "after all this long journey Widad I come to understand wanan mugun son danake miki ba kowace irin so bace face so so kaman irin na wa da kanwarshi, I care about you Widad, I go for anything that will make you happy, bayan kin bace haukacewa ne kawai banyiba babu inda bamusa hoton ki ba, but for once in my life Widad nai tunani ba akaina dakanki kadai ba, for the first time in my life nai tunani akaina, akanki dakuma akan abinda kike dauke dashi acikin cikin ki" yasake yin shiru sanan yace "Widad da ace ni dinan dakike gani ba'a gidan mahaifina nataso ba bazan tabayin farin cikin dazanji irinshi agidan asalin mahaifina ba, kowani d'a dakika gani aduniyan nan burinshi shine yataso cikin so dakuma gatan iyayenshi, daga lokacin da mace ta dauki juna biyu a lokacin ne zata dena tunanin kanta kanta ita kadai, alokacin ne zatafara tunanin what's best for her and her child, our parents sacrifice alot for us, mata nawane ke zama da mazajan da basuso badan komiba saidan kawai yayansu ballema wanan da deep down kinasan ubanshi Widad, u just needs to find where wanan son uban nashi yake azuciyanki, kwanakin baya danazo naganku tare I saw how u looked at his father and I see nothing but pure love in your eyes" yay maganan ahankali kaman abin namai ciwo, yakai kusan 5min yay shiru sanan ya nisa yacigaba. "just to be sure nasamu natsuwa cewan kina hannun wayanda zasu kula dake yasa I made a research akan family mijinki nagano wayesu, your husband is a goodman a humanitarian, an activist, a Dr and many many more , yesterday I had a one on one chat da mijinki Widad I must admit cewa yaron nan na sonki and trust me idan nace TWO DIFFERENT WORLD means shit inhar Love din is real, komi dakika gani mukaddari ne da ace guy dinan ba mijinki bane da babu abinda zai kaiki Nigeria da bamu da yan uwa ko guda achan, kowani musulmi dolene yay imani da Allah dakuma rana ta karshe, sanan ya yarda da kaddara, koma meyafaru tsakanina dake kaddara ne, take me as your brother wanda kuma ya isa dake Widad ayau ina gayamiki cewa nida kaina without anyone forced me that na janye duk wata kalman soyayya dana taba fada miki ada, na janyeta nahakura, nadauke ki amatsayin sister na, and inhar kin daukeni amatsayin yayanki wanda yakuma isa dake abu daya zangaya miki shine kibi mijinki sauda kafa domin ko yana sonki sosai, go and build your marital home, go and build your family Widad I wish you all the best in this life kinji" yay murmushi yana hana kanshi kuka ganin yanda take kuka sosai, ahankali yace "tashi muje tun dazu Aby yakira family mijinki duk suna falo kibisu kutafi, sunce Qatar zaku koma bayan kungama vacation saiku koma Nigeria ko, don't cry let's go" bude kofa yayi yafita da ita, a falo tagansu duka sai kallonta suke banda Waleed da kanshi ke kasa yanada mugun kishi saisa baimason yadaura idanunshi akanta da Ahmad dasuke fitowa tare, tana zuwa tafada jikin Aby tana kuka sosai, hadasu Aby yayi yamusu wa'axi sosai mai ratsa jiki, sanan agaban kowa ya kwaso paper's na kamfamonin shi yasa tai signing dudda za'a dinga yimata managing, hana kowa tafiya Aby yayi yace sai yahada musu gagaruman liyafa wanda za'ayi gobe sanan zasubar garin, dakanshi yakaisu wani hadadden bangare agidan itakuma Amah ta tafi da Widad shashinta tun dare takira masu gyara, ranan yan aiki basuyi barci ba aka shiga decorating. Da safe wuraren 9, designers Aby yatura side din su Ammi, aka dauki measurement din kowa sanan aka kawoma kowannensu Morrocan dress, wuraren 11 aka fara ceremony din, aka fitoda Widad da Waleed yakasa daina kallonta, dauke kai tayi daga kallonshi ita adole fushi take dashi ta ballamai harara sanan tashiga cikin masu rawan larabawa, Waleed was blown away dayaga tana rawa, subhanallah bura'uba baitaba ganin yarinyar data iya rawa irinta ba, she looks so happy adorable and charming suna hada ido zata ballamai harara, haka har wuraren 4 Aby yasa aka shirya musu tsaraba dan Uncle yasanar dasu cewa jirginsu 6 ne, Aby da Amah har Airport suka rakasu, aiko Widad tasha kuka kafin tarabu dasu. Nigeria Asibiti Case din Arham saida akai documenting nashi ababbban littafin da'ake recording incidence na bura, kwanan shi bakwai chur aka sallame shi daga asibitin bayan yayi clearing duka bill din dayacimai kudi sosai, bai wani damuba tunda yasamu andike fess yana iya fitsari, gabaki daya, adaidaita yatare for the first time tun bayan yaje gaisuwan Mama bayan tarasu saiyau kawai yaji yanaso yaje gidan mahaifiyar shi, keke yatare ya shiga yana tafiya yana dingishi har zuwa gidan, gani yayi an kulle gate din da makulli baida key hakan yasa yadau dutse ya balle key din ya shiga cikin gidan yana kallon ko'ina ga motar Mama da Waleed yasaimata apake a kasan tent, ahankali yake tafiya har zuwa gaban flat dinsu balla key shima yayi sanan yabude kofar, chak ya tsaya abakin kofa yana kallon falon yaga kanan zaiga Mama akan kujeran dayake yawan dawowa daga aiki yaganta, ahankali ya shiga cikin dakin zama yayi akan kujeran dayay kura sosai baima damuba yana kallon kujeran da Mama kezama kai yana ganin kaman ita ya kegani zaune tana kallonshi, yakai kusan 5min ahaka saiga hawaye ahankali ya zilalo mai murya chan kasa yace "Mama dan Allah kiyafemin, nasan sabida kin rasu da fushina a zuciyan ki saisa komi yafara juyamin up side down" shiru yayi yasa hannu ya share hawayen da suka zubomai murya chan kasa yace "Mama wani yakusan yankemin gaba, Mama Alhakin kine kona Waleed suke bina"? Ya tambayi kanshi kafin ahankali yace "Mama I feel so empty, na kwacema Waleed gidan marayun shi, yanzu haka baida gidan marayu, na kwacemai mata ta haifamin yaro ba mijinta ba yanzu tana dauke dana biyu, Mama inada katon gidan marayu, inada mota lambo kaman ta Waleed Tawa baka, Mama inada yara kananu masu danyen jini harsu takwas danake amfani dasu dukdan nafi Waleed jin dadin duniya suma sunada yet Mama am still not full am not satisfy, nothing seems to satisfy me, Mama pl......" bai karasa magana yaji anyi knocking kofar falon tareda shigowa duka at a spot, polisawa yagani guda biyar hade da government officials, babban cikinsu ne dake sanye da suit yay murmushi yace "good Day Mr Arham, yau kwana uku kenan muna nemanka aduk inda mukasan zamu sameka but bamu sameka ba sai yanzun nan informant din damuka ijiye awanan anguwan suka sanar damu sunga shigowanka anguwan ka shiga gida" wani irin gyada musu kai yayi gabanshi nafaduwa, mutumin yace "office dinka yakama da wuta an nemeka an rasa har saida aka turamu, anan muka tarar da gidan marayun ka yaran damuka aminta dakai muka kaisu gidanka sun wulakanta, basuda abincin ci yara duk ciwo suke, bayan series of tests muka gano mata takwas nada ciki, nan muka turkesu for investigation anan suka sanar damu komi tundaga abu nafarko daka fara sakasu suka maka na yima Mr Waleed Warbai shairi har muka kulle gidan marayunshi, kabiyasu kudi kasai musu kaya akan suma Waleed shairi cewan yamusu fyade, sabida kaga yarane basuda gata saikai kai amfani da kansu da maraicin su kace ka auresu a masallacin gidan marayu da babu wanda yabamu shaidan abu makamancin daurin aure yataba faruwa akan hakan on that note Mr Arham, you are hereby being arrested for rape and assault, dakuma shairi har kasa aka kulle gidan marayun Waleed, banda haka duk wani property dayake naka zamuyi auction nashi ayi amfani da kudin abiya yaran dakaci amanan su sanan acigaba da lurada su dakuma cikin dasuke dauke dashi, you have the right kai shiru inba hakaba kome kafadi za'ayi amfani dashi akanka at the court of law" yana gama maganan daya daga cikin polisawan yay kanshi ya shiga samai ankwa juyawa Arham yayi ya kalli kujeran dayake ganin Mama zaune akai kaman wanda yazare yace "nasan duk aikin kine daman abinda yasa kika jawoni nazo gidan dan akamani ko, na tsaneki, Allah ya isa tsakanina dake dakuma Waleed, wlh sainaga bayanku dukanku, zaku gani, sukuma su Hassana dasuka tona sainaga bayansu" ya shiga ihu kaman wanda ya haukace yana tutturjewa suna fisganshi basu damuba haka suka fizgeshi sukai waje dashi suka sashi amotarsu yana surutai kaman zararre sukabar anguwan dashi. Ina masu neman turare exotic ones, masu mugayen dadi, masu kama daki, masu dadi, da armashi, long lasting turaren gargajiya gashi sanyi yazo, Awwaba Scent got you covered, kayanta akwai sauki, tana delivery ko'ina, me kuka jira ne wai? 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼 Just chat her up kuga abun mamaki ga number tanan https://wa.me/+2348034236800 [11/27, 9:56 PM] saleemah: 💫 _TWO DIFFERENT WORLD_ 💫 ✍️ M SHAKUR END!!! Rayuwa kenan daman ance duk wanda ya chuka alkhairi zai gani wanda kuma ya shuka akasinta shima zai gani, ga Arham yanzu gabaki daya abubuwan dayamai sunyi backfiring sun dawo kanshi, ko amafarki baitaba tunanin shairin daya kullama Waleed za'a gano gaskiya ba gashinan yanzu shairin cost him all his property za'a biya yaran dayama ciki bayan sun haihu kuma za'a cigaba da kuladasu da kudin in yaran suka girma araba musu kudin, yanajin yana gani aka kaishi prison direct batare da hiring ba, kukuma a bashi chance din kiran lawyer shiba wanda hakan kuma duk aikin vice president ne abokin Ammi tunda aka sanar dashi angano gaskiyan shairi yama Waleed yabada izinin they should deal with him, ta karkashi za'a kulleshi karma aji news din, haka zaiyi rot in prison yamutu daga baya amman bazaibar prison ba yar abada, kaico! Allah karabamu da Hassada dakuma bakin zuciya, Allah kacire mana kwadayi dason abun wani, gashinan Arham da hannunshi yaje yakai kanshi ga halaka, abin tausayi baida kowa, tunda yasa kai yabar gidan marayun baikara dawowa daidai daso daya yagaida kanwar Mamanshi ba Maman Sadiya, har suka tattara suka bar gidan Ammi tasai musu wani gida daban tabude masu business sosai kuma Alhamdulillah ta chanza, tunda taga Arham baida lokacin su kuma bai shirya tubaba suka tattare shi suka linke dan basusan ina yakeba, su basusan kan Abuja ba balle suce zasu tashi suje su nemoshi hakan yasa sukabar zancen. Karfe biyun rana jirginsu ya sauka a Qatar, mota suka shiga tana kusada Ammi har zuwa gidansu, bayan sunkai gidan har flat dinsu Ammi ta kaita ta shigar da ita uwar daka ta zaunar da ita sanan itama ta zauna, ahankali tai cupping face din Widad din, murya chan kasa Ammi tace "alkawari daya zan miki bazaki taba nadaman auren Waleed ba, my son is a goodman, verysoft and very loving zakiji dadin Waleed, please kiso d'ana kaman yanda yake sonki he has been through alot wlh, tausayinshi nake dan ciwon zuciya na gab da kamashi" Ammi taidan shiru sanan tace "I am a mother am so worried for my son Widad, please kiso d'ana koma yayane" saiga hawaye da sauri Widad tasa hannunta ta sharema Ammi hawayen dasuka zubo mata sanan ta rungume Ammi ahankali, rungumeta back Ammi tayi sun dade ahaka sanan Ammi ta saketa tace "tashi kije kiyi wanka" gyadama Ammi kai tayi ta tashi tana kokarin cire kayan jikinta itakuma Ammi tawuce tafita daga dakin tarufo mata kofa. Tana fitowa daga bayin daure towel shikuma yana shigowa dakin dan tun dazu yana tareda Uncle a dakinshi, hada ido sukayi yabita da wani mayen kallo dauke kai tayi tai wajen wardrobe tabude batare datace mai komiba ta bude tashiga neman kaya, ganin baice mata komiba yasa tawani irin kama cikinta taredayin ihu. "wayyooo cikina" da sauri yazo wajen yadagota saikuma yadauketa yay kan gado da ita yace "menene Pretty ina ke miki ciwo"? Fadawa jikinshi tayi ta rungumeshi tsamtsam tana sauke ijiyan zuciya, jin yanda ta rungume shi yasa ya rungumeta back tareda manna mata kiss acikin gashinta yace "am happy my wife is back, Widad ina sonki kuma zan cigaba da sonki har karshen rayuwata, zamuyi rayuwan dazamu dinga shayar da junanmu soyayya mai tsafta" yay shiru yana shafa bayanta, shafa kirjinshi tayi ahankali tace "Ya Waleed Zaujy" wani irin sassanyar ijiyan zuciya ya sauke, ahankali tace "I've been wanting to thank you for all you've done to me, little by little inata tuna abinda yafaru dani bayan nahadu dakai dudda ban tuna komaiba but the little dana tuna give me more reason to love you and more reason to be your wife till eternity, kaine sanadin fadowata Nigeria, u are my destiny Ya Waleed, and am morethan ready to accept you as my husband, let's be the first people to show the world cewa DUNIYA BIYU MABANBANTA suhadu atarayya ta aure, sanan this same TWO DIFFERENT WORLD sun gina soyayyan da wayanda suke duniya dayama basu ginaba, I love you Dr Waleed Warbai" chak ya tsaya yana kallonta saikuma kawai yadagata sama ta kyalkyace da dariya yashiga mata chakulkuli kafin su fada gado suhau faranta ma junansu rai. Da daddare yana tareda Uncle yana aiki da system dinshi yaga shigowan email duba email din yayi yaga daga ministry aka turomai, suna bashi hakuri kan duk abubuwan da akamai akan yanzu sunsan gaskiya, sanan inya shirya yazo ya karbi komi dayake bukata yacigaba da running gidan marayun shi, yau kwana uku kenan suna neman wayanshi basa samu if he get this email yamusu reply, yanda fuskan shi yay wani irine yasa Uncle yace "menene son" ahankali ya sanar da Uncle abinda yagani, tabe baki Uncle yayi yace "kagama aiki agidan marayu daman cimaka time yake, ka gina masallatai, islamiyu, kagina ma alumma rijiyoyi da bohole, ka taimakama ma bukata ko wanan kadai ya isa, asibiti zaka koma da aikin ka ba gidan marayu ba, start planing on building your family ankusan fara haifo maka yara", murmushi yayi baice ma uncle komiba yana ganin fuskan Widad a system din. _Bayan nine month_ Ilham dasu Hassana kusan duk lokaci daya suka haihu banbancin kawai shine dan da Ilham ta haifa tun aciki aka sanar dasu yamutu aikima aka mata aka ciro kaman bazata rayuba tai ciwo kaman ta mutu, tun iyayenta da yan uwanta suna nuna mata tsana akan halin datayi har suka rungume abunsu suka shiga neman mata magani, ga Arham little sai girma yake yaron kamanshi daya sak da mahaifinshi, sosai ta wahala sanan aka samu ta samu lafiya, wani irin hankali natsuwa da nadama tashigayi tana istigifari kullum, tama dena fitada gyale kullum hijabi har kasa da Safa tazo ta natsu kaman ba itaba, yanda tadena ganin Arham dakuma denajin labarin shi ya bala'in mata dadi da kwantar matada hankali. Arham nada shekara hudu wani mai mata biyu malamin islamiyan su na matan aure datake zuwa yafito kan zai aureta, Baba ko musu baiyiba yahada aurensu haka aka kaita gidan mijinta bayan anmata fada sosai su Mummy suka karbe Arham karami yakoma hannunsu itakuma tacigaba da rayuwan gidan miji da mata biyu, yau dadi gobe wahala amman haka tadaure dan tariga ta tuba kuma tai nadama. Arham ko ba'a karajin duniyan shiba yanachan yana cin ubanshi a undisclosed gidan yaro da akekai wayanda gwamnati kejin haushinsu. Widad Twins ta haifo dukansu mata masu bala'in kama da Waleed, gashinta kawai suka dauko, Waleed yadinga kuka, a ranan data haiho ranan Aby yadiro Nigeria, dan baitaba zuwa Nigeria ba, kowa saida yasan Widad yar gatan Babanta ne sabida kyauta da Aby yayi, ranan suna yara sukaci suna Anan da Anah. Haka rayuwa tacigaba da tafiya, Widad batasan miye matsala ko fada da mijiba, hakama Waleed, baisan me fada da mataba, dan Widad sonshi take kaman ta cinyeshi bata kunyan nunama kowa hakama shima, bayan yan Biyun bata kara haihuwa ba dan takoma school saida tagama her dream course Mass com sanan tai wani cikin ta haifi da'a namiji. End!! Alhamdulillah anan nakawo karshen kagaggen labarin nan nawa mai suna DUNIYA BIYU MABANBANTA, kuskuren danayi ciki Allah ya yafemin, wani zubin don't just read book for fun take note of lessons din dake ciki, Allah ya shiryar damu gabaki daya, masu hali irin na Arham ku gyara, be your sister keeper, adena bakin ciki da hassada, kisani komi lokaci ne, kobaki kudi ko baki samu wata Nasara anan duniya ba ki kaddara naki Nasaran na lahira Allah ya ijiyemiki itane, Allah yasa mudace. _*duk wacce takaranta min littafin nan batare data biyaba, wlh ban yafemata ba, bazan kuma taba yafewa ba, subscribing fee na book dinan is 500, ya Allah kabimin hakkina akan duk wacce takaranta bata biyaba dan ban yafemiki ba*_ _I want to give a special thanks to Hajiya Asma'u wacce akafi sani da Moxi, bazan karyaba this woman help me alot akan al'adun morroco dama komi nasu, thank you so much and thank you for the support and love 😍_ _ina mika godiyata ga, Platinum, VIP, ICTM, GGM, you guys are great, you make me this M Shakur thank you so much I love you all_ To anan nace cemuku sai anjiman ku sai kunjini a littafi na nagaba. Aishat Muhammad M Shakur 🥰